Professional Documents
Culture Documents
ng ku ziyarci shafin na
www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na
yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu
kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama
sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana
magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci,
duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna
neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman
munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai
fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai
wayarku
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted
biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not
blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we
are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day,
any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF
or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT[20/03,
17:09] 80k: [10:45PM, 02/11/2016] Rahamat Nalele: 👯👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*
Part 1 to 5
*Nutsu da kyau me karatu ka karan farkwan labarin nan da kyau kuma kar kayi gigin
mantawa. Dan xai temakema wajan gane ya abin xai kasance nan gabah*
Ya kasance nika'daice tasa abin dubawarsa amma in aka cire iyayansa da qannansa
Ya kasan me hakuri sannan me kishi akaina
Ya kasance naxama nice madubin dubawarsa. Shikuma yaxama shakallo agareni
Bana burin Auran qaramin yaro kamar wanda ya girmeni da irin shekara uku haka
haka na saka araina baxan ta6ata auran qaramin yaro bah. dan na raina qarfinsa da
jarumtarsa
Acikin unguwarsu akwai wani gida me kyau da 'daukar hankali wanda ya kasance gidan
xuwana ne ako da yaushe naga damar xuwa
Inada aboki RAMADAN wanda shine ya kasance wanda yakejin sirrina
nayi matuqar shaquwa da RAMADAN irin shaquwar nan da akekira da inbakai baxan iya
rayuwa bah
Ina san RAMADAN dan ya kasance yaro memin ladabi da biyayya duk da shi 'din
miskiline
Amma ya ha'du tako ta ina dan ina qaruwa dashi tako ta ina
Dan yafini ilimi yafini hankali sannan ya fini nutsuwa
Duk shawarar da nanema agun RAMADAN idan yace min iyi kasa bar kaza nabarshi har
abada
Babana dacan yayi ku'di Sosai daga daga baya ne karayar arxiqi tasa meshi
Ayanxu bashi dashi Saidai bama rasa na sawa abakin salati
Abu 'dayane ya bari adukiyarsa. shine gidanmu.
Gidanmu babban gidane kuma ginin xamani
Dan a unguwarmu in kacire gidansu Ramadan akyau toh cika saka gidanmu
👯👯👯
Sunana RAMADAN Nasir yaro 'dan 20 years
Na kasance ina da buri 'daya arayuwata shine
natashi da maseefar san wata mace me kyan sura. Da komai
Tayi tako ta ina
Ina santa
Ina santa
Ina santa
Ina da abokana ye biyu Fawas da Khamis
Duk ra'ayinmu 'daya yake dasu
Amma mutane da dama suna cewa nafisu nutsuwa da hankali
*I luv u*
[8:29AM, 05/11/2016] Rahamat Nalele💋: 👯👯👯👯
Suna na KHAMIS
Inada shekara ashirin daidai yau
Ina da San mata Sosai kuma inada burin Auran mace wacce ta xarce shekaruna da kamar
shekara biyar haka ko shidda
Kuma bana san Auran wacce ta Waye nafisan Auran 'Yar qauye me halin yarinta
Tab😳
👯👯👯👯👯
Suna na Zainab Amma ana kirana da XEE dan nafisan akirani da hakan
Inada shekara ishirin da biyar.
👯👯👯👯
Suna na Hameeda Ya'u ina xaune a qauyan takai Babana ya rasu Mamana mah haka
Ina hannun qanwar babana Innah Hansai
Ba qaramin ganamin axaba take bah
Duk aikin gidan ni nakeyi duk wani aika ni nake xuwa mata haka duk wani Girki ni
nake yi
Duk da ko tanada yara Amma Sam bata sakasu sai ni
*Toh Madallah masu karatu kunji tushen kowa acikin wannan littafi nawa. dan haka
sai kugyara xama kusha karatu*
Zama na musamman samarin layin nasu suke dan kawai suga fitowarta
Duk unguwar ba wanda baisan SAILUBAH da halinta ba
Kyauta San Mutane San ku'di fa'dar Gaskiya..............
Koda ko kar sa'an babanta ne kayi abunda bai dace ba toko ba shakka saita wanke ka
da soso da sabulu
Duk unguwar ba Wanda baisan sha'kuwarta da RAMADAN ba
Suna San junansu Sosai dan shi'din abokinta ne
Mutane da dama idan sukaga SAILUBAH da RAMADAN xasu skull dake skull 'dinsu 'daya
ba qaramin sha'awa suke basu ba
Fa'di suke tsakanin SAILUBAH da RAMADAN wayafi kyau ne
Yana da da'din murya haka kallo 'daya xaki mai kisan anyi balaraban yaro
RAMADAN Yana da San karatu Sosai gashi da ilimi tunda ya taso ya fara xuwa
makaranta bai ta6a fa'duwa akan Komai bah
Yanxu haka saura bai fimai 1 year ya gama kammala karatunsa ba
Inda yake san xama cikakken likita wato doctor
Yaxama kenan ra'ayinsa 'daya da Auntyn Sa SAILUBAH
Idan Nace muku RAMADAN 'dan rainin hankali ne karku musa min
Haka KHAMIS iyayansa Suna da ku'di Sosai shima an shagwa6a shi Sosai da ku'di
Su biyu iyayansa suka Haifa
Ianada Yaya Rahamat tayi Aure tana garin Abujah da xama
Ganin hakan KHAMIS shi 'daya shiyasa shi abinda yakeso kuma iyayansa suka biye nasa
KHAMIS Yanada San karatu inda yakeso yaxama cikakken loya Wato ya karanci low
Yau take talata kuma antashi da ruwan sama yaf yaf yaf gwanin sha'awa
SAILUBAH sauri sauri gudu gudu takeyin Komai dan sunada karatu qarfe tara
RAMADAN ya shigo falan hannunshi 'dauke da Wasu takaddu Yace Auntyna lokaci ya fara
tafiya fah
Da sauri tajuyo xatayi magana sai kuma tatsaya kallansa kamar alokacin ta fara
ganinsa
Ya 'daga mata gira tare da qarasowa kusa da ita ya kar6i 'dan kunnan hanunta Yace
in saka miki ko
Tayi saurin 'dagamai kai Tace kayi kyau Sosai Qanina
Yayi Murmushi Yace Nagode Auntyna
By Hajju
[20/03, 17:09] 80k: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR👯*
Part 6 to 10
Gyarawa Sosai tayi ya saka mata 'dan kunnan ta'dauki gyalanta da 'yar jakarta
tamaqala
Idan RAMADAN na kanta yana qare mata kallo. Ta 'daga mai gira
Yayi murmushi Auntyna tsaya na photo
Wayanka saita cika da pix 'dina
Yace in bake acikinta Wlhi bata da amfani
Tace kayi breakfast kuwa
Ya 'dan Sosa qeya Yace nayi
Tabishi da kallo ka'dan hmm bakayi ba
Yace toh Kinga lokaci yayi........
Cire gyalanta tayi tashiga kitchen kawai. RAMADAN yaja numfashi tare da kallan
agogo yana tsaki
Bai ankareba sai gata qatan faranti ahannunta. Wanda ke 'dauke da lafiyayyan tia
da kuma soyayyan dankali da kwai
Ta dire a gabansa Tace nabaka minti uku kayi Maza
Yace Aunty banajin yunwa...
Ta katse shi da jefa mishi wata muguwar harara
Bashiri ya fara ci
Yayinda ita kuma ta xauna tana amsa waya
Hello Alhajina ina kan hanyar xuwa makaranta
Yace Amma naso inxo in ganki yanxu. Plx Ki bani ha'din kai yanxu naganki
Aini takace. Kabari ina dawowa xaka ganni.
Yace toh Allah ya dawomin dake lafiya
AmEEn Nagode. Tafa'di hakan da kashe wayan
RAMADAN najinta Yace Auntyna dawa kikayi waya
Ta gallamai harara cikin 'daure fuska Tace ban sani bah
Yayi Murmushi Yace pls gayamin Wlhi ba'abinda xai faru
Tace hmm yama faru Wlhi saina baka mamaki idan kayi sanadin da Alhaji Jamilu ya
dena xuwa gareni
Ya kalleta ka'dan dayin murmushin rainin hankali Yace baxanyi Komai bah Auntyna
Amma dan Allah gayamin yaushe kuka ha'du da har ya kasance ban sani bah
Tace jiya muka ha'du a jifatu yaje siyayya
Amma shine ko jamishi aji bakiyi ba kika amsheshi daga ganin farko
Ta gallamai harara Tace ban jah mishi ajinba
Yace me yasa
Cikin maseefa Tace saboda shi me ku'dine yayimin tun kallan farko dana masa
Yace Amma.........
Tayi saurin katse shi da cewa. Wlhi RAMADAN ba wani abu daxaka fa'damin inji inbar
mutumin nan dan yana da ku'di Sosai
Kyautar farko daya min jiya dubu 'dari uku ya ban
Yace haba Auntyna......
Na rantse da Allah ka cikani da surutu xakasha mari
Shuru RAMADAN yayi yaci gaba dacin abincinsa
Can ya kammala Yace toh mutafi ko. Yafa'da da 'daukar Wasu takaddunta
Suka fitoh ya bu'de mata gaban motarshi tashiga shima ya shiga da jansu suka ficce
daga gidan
Ya kulle motar tashi yana fa'din xanfi kowa farin cikin hakan. Maxe jeki kar darisa
Su wucceki da yawa
Ba musu Amina tabar gun cikin jin da'din Ganin masoyinnata
Karatu ne Wanda sukayin shi cikin nutsuwata ahaka suka tashi inda SAILUBAH ta kalli
RAMADAN Tace Amma fah abubuwa da dama na kasa fahimtarsu
XEE tayi dariya Tace aike Kullun a haka kike
Tayi Murmushi dacewa ai banda matsala tunda gani ga Qanina.
RAMADAN Yace aikuwa ammafa Auntyna kidinga lura saboda wata ranah.
Taturo baki da cewa toh naji muje gida nafara jin yunwa ba sai mun jira KHAMIS
ba .......
KHAMIS 'dinne ya katsesu da fa'din dawai tafiya xukuyi kubarni bayan yasan yau ban
fitoh da mota ba.
XEE ta kafeshi da ido Tace ya fa'da mana
Ammma fah kayi kyau sosai Tafa'da da shigewa motar Ganin SAILUBAH da RAMADAN sun
shige.
Yayi Murmushi Yace kai Aunty XEE ina wani kyau anan. Yafa'da shima yana mai shigewa
cikin motar
RAMADAN ya kalli Su SAILUBAH ka'dan Yace Auntys suna nan fah. Dan haka ka ankare.
RAMADAN ko gidansu yayi direct yayi part 'dinsa. Dan gidan nasu acike yake tam da
mutane 'yan biki
yaune walimar yayarsa Saudat gobe 'daurin Auranta
Ya baje a gado yanata bincikar wayan SAILUBAH.
Har yasami abinda yake nema watoh number Alhaji Jamilu Wanda SAILUBAH tayi waya
dashi 'daxo
Nan ya kirashi ringing biyu ya 'dauka cikin sauri yana fa'dan Allah yaja da
xamaninki tauraruwa
RAMADAN ya runtse ido Cikin kamilalliyar murya Yace ba ita bace na kiraka ne in
gaya maka wani abu
RAMADAN kenan ya tsani yaga kowa da Auntyn nasa. Shiyasa yake koran mata samarinta
sanranshi. Tayi fa'dan tayi maseefar Sam bayaji. Iya kacinsa da ita shine ya bata
hakuri
SAILUBAH ko daqar taci abincinta burinta tagama taje gun Qanin nata suyi shawara
Hakako akayi. Data gama Komai saitaje tasamu kakarta Tace kakane bara naje gidansu
RAMADAN
Tace har lokacin walimar yayi ne
SAILUBAH Tace wai walimar walimar Saudat
Tace eh mana. Taxoma nemanki 'daxo keda XEE wai kimata lalle ne kome tacene oho na
manta
Girgixa kai SAILUBAH tayi Tace sai qarfe hu'du walimar da sauran lokaci
Tana fa'din hakan tafito daga falan nasu
Tafi toh kenan idan ya sauka alungun Gidansu wata Baraka dake kusa dasu
Saita dinga jin kamar kukan yarinya. Cikin qarfin hali tayi lungun
Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Tafurta hakan da qarfi. Dan Ganin wani narkeken
qatan garde a'kalla xaiyi shekaru arba'in 40 Ya danne wata yarinyar makwaf ciyarsu
'Yar miciciya batafi shekara goma ba
Aiko SAILUBAH me xatayi inba kurma ihu ba. tana fa'din jama'a kuxo ga wani
axxalimin mutum yana San 6atama yarinya rayuwa.......
Kan kace me😳 tuni gun ya cika da jama'a Suna tafi da Allah wadai da shi da
mamakinsa
mutumin ya saka wandansa SAILUBAH ta cukume masa riga Tace Amma kai kam Allah yayi
tsinannan tsowo
Fasiqi axxalimi me mumunar xuciya 'dan iska
Kalli yarinya qarama kana san 6ata mata rayuwa
Idan iskancin kakeji mexai hana kaje gidan karuwai kayi da wacce ta dace dakai.
Tunda xuciyarka tamace da son abinda Allah bayaso
RAMADAN Wanda yafito dan rahotan da qanwarsa takai masa.
Xuciyarsa tacika da takaicin Auntyn tashi yayi dabarai kwatan mutumin
ahannunta........
Kan yayi magana sai gani sukayi
Iyayan yarinyar sun rufe mutumin da duka Sosai
Mutane na fa'din gwanda aci ubansa Suna tayasu dukansa
SAILUBAH takai hannu xata tayasu itama.....
RAMADAN yajah hannunta sai Gidansu
A farfajiyar gidan yasake mata hannun nata
Yace haba haba Auntyna meya kaiki aikata haka. Kamata yayi da kika gansa kimasa
wa'axi tsakaninki dashi. Amma bai dace kitara mishi jama'a haka ba
Tunan asiri bashi da kyau ai
cikin maseefa ta hayyaqu miki tace banyi hakan da kaso ba.
Irin sune 'yan iskan da in ba haka akayi musu bah baxasu dena abinda suke ba
Yace toh wai ke ina ruwanki meya shafeki kawai kinje kintara jama'a maxa da mata
kowa yana kallanki harda wani kai hannunki jikin qaxamin mutumin. kin dai kwafsa
kawai kiyarda da hakan
Yafa'da kamar xai rufeta da duka
By Hajju
[20/03, 17:09] 80k: [12:18PM, 09/11/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR👯*
Part 11 to 15
San da ta xauna kan kujera. Cikin lallami Yace am sorry Auntyna bana san 6acin ran
nan naki.
pls ki temaken Kisake min fuskarki ko nasamu nutsuwa araina dan Allah
Kamar yanda lamarin yasa ba faruwa mishi hakance tasake faruwa SAILUBAH taqara kai
mishi harara Tace Wato kai baxaka fita aharkar mata bako
Qanqanin yaro dakai Kasan kadinga yaudarar mata ko
RAMADAN ya xuba mata ido da fa'dawa tunin wai sai yau she ne Auntyn tashi xata dena
kiransa da yaro
Da 'daure fuska Yace shekarata ishirin xaki dinga kirana qaramin yaro
Haba dan Allah yanxu inda agaban budurwar tawace shikeban kinsa tarainani dan Allah
kidena kirana qaramin yaro
Tayi dariya dan ganin yanda yayi kicin kicin da fuska tunba yau ba
tasan RAMADAN baya san araina shi shiyasa yake ganawa Khairat axama qanwarshi dan
baqaramin tsoranshi take ba
Gashi dasan girma Sam baya SO ace wane ya girmeshi
Ita ka'daice xatace mishi qaramin yaro baxai CE mata Komai ba. Toh yau gashi yayi
kicin kicin da fuska
Tashi tayi taje gabansa ta manna masa kiss a kumatu kamar yanda tasaba yimai idan
ta 6atamai rai Tace sorry 'dan Qanina kai Babban yarone
Xaka kaimu walimar Saudat kajiramu.
Yace aa
Dan Allah
To naji
Tatashi xata fita Yace Auntyna yunwa nakeji
Tace toh bara na kawo maka abinci. Tafita
Yabita da kallo
Ka'dan yaci ya kora da drink kana yayi wanka Cikin qananan Kaya yakira FAWAS da
cemai Su ha'du a gidansu KHAMIS dan shi KHAMIS 'din yayi wani banxan kamu. Yace OK
Shiko yana fitowa daga gidan nasu idan shi ya sauka akan Jamila
Wato Jamila wata 'Yar unguwarsu CE tana MASEEFAR son RAMADAN
Tarigada tasan duk wani motsinsa dan haka kanya fitoh daga gida take kafawa ta
tsare akan wani dakali da yake fuskanta gidan nasu. Tun baya ganewa har ya ganota
suka fara gaisawa
Yafara sakar mata da kalamai. Shikenan fah ya hargitsa mata tunaninta
Kowa yasan soyayya suke
Ya sakar mata Murmushi cikin sanyin murya Yace Jamis tauraruwata yau baxa abari
naxo bane
[5:35PM, 09/11/2016] Rahamat Nalele 👯: Tace hmm nakasa hakurin hakanne shiyasa
kuma......
Bata izza xan canta bah ummi 'yar uwar shi 'yar qanwar momynsa taxo shigewa cikin
gidan nasu
da sauri Tace Ya RAMADAN tun safe naketa nemanka
Ya xuba mata ido dan ya da'de da sanin yarinyar ta fa'da tarkwan soyayyarsa Amma
Sam yaqi yarda ta bayyana masa
Yace ayya lafiya dai ko
Hawaye ya xubo mata Tace har yaushe xaka gane ina sanka
Asan mace da kame darajarta abin kunyane tacema namiji tana sanshi. Amma ni nafurta
hakan dan baxan iya jurewa ba
Aqallah ina da 'yan mata sunka 'dari idan na iyasce
Duk acikinsu ba wacce nafara furta kalmar so agareta. Kinga ko idan kinfara furtawa
baxanji Komai ba
Ki shiga ciki xan tunani akanki. RAMADAN Yafa'di hakan cikin rashin kulawa
Tace Amma........
Waccan mah budurwa tace ina santa. Ya katseta da fa'din hakan
Ummi talalli Jamila da tayi kicin kicin da fuska suka gallama juna harara sai
tashige gidan kawai batare da Tace Komai bah
Jamila Tace wacece ita. Yace wani abune. Tace aa kawai dai naji na tsaneta ne
Yace toh kiji kina santa dan 'yar Uwa tace
Yana fa'din yabarta nan tsaye
Duk 'yan unguwar kallansa suke cikin sha'awar tsaftarsa. Sam baxaka ta6a ganin
RAMADAN FAWAS KHAMIS cikin qaxanta ba
Haka suka fito sukayi wajan wankin motar da wannan yarinyar tabayar amata
KHAMIS Yace ta'ina xamu fara.....
Kan suyi magana idan FAWAS ya sauka cikin motar inda ya hango kamar Passport
'dinta
Yace ashe baxamu sha wahala ba
Nan ya bu'de yaga akwai address 'dinta
Cikin murna RAMADAN Yace Allah ya tenake muyi sauri ina da fitta da Auntyna.
FAWAS Yace Aunty LUUVAH (dake haka suke kiranta da shi)
KHAMIS Yace Kasan 'daxo sanda ta maimaita karatunta da xamu dawo gida har Aunty XEE
na tayata
Dama ai bakinsu 'daya. cewar FAWAS
Yace inaso nayi Aure cikin lokaci qanqani dan Aunty LUUVAH Wlhi
RAMADAN yayi Murmushi Yace ya kamata kam
Suka shige mitar sai Gidansu yarinyar
Bayan sunyi parking KHAMIS Yace kaduba yanda tayimin datti da mota
RAMADAN Yace toh miye
FAWAS Yace Bakomai tunda so ya kusan toka.
Suka fitoh Suna Tambayar megadi dan Allah miye sunan me motar da suka kawo mata
Yace Ameera
FAWAS Yace dan Allah koxa kamata magana
Yace badamuwa
Nan ya kirata
Tafi toh da rangwa'da kamar yanda KHAMIS ya basu labari
Tace sannunku FAWAS ne kawai ya amsa
Tana cema kallan RAMADAN
Shiko ya 'daure fuska Yace anwuni lafiya. Da sauri Tace lafiya lau
Yace Xan iya samun key na motar can
tace mexai hana bayan takuce
Nan tamiqa mishi
Yayi gun motar da kunnata sannan ya juyata FAWAS ya shiga motar
RAMADAN ya xuge gilashin motar ya kalli KHAMIS Yace muna jiranka a waje pls karka
'dau dogwan lokaci dan Kasan bana ha'da uxirin Auntyna dana kowa
Yana fa'din hakan yafitta da motar
Musamman SAILUBAH RAMADAN Yace toh sunfitoh mah wai gun walima xan kaisu
FAWAS Yace Aunty LUUVAH da Aunty XEE Yace eh
Nan suka qaraso Tace yauwa kunxo a dai-dai qannanmu
Saudat Tace toh gamunan muma.
SAILUBAH Tace toh
Suka shiga motar
XEE Tace harda kune arakiyar
SAILUBAH Tace eh mana Kinsan inba wani dalili ba ba'abinda yake raba kawunansu
Tace umm kumafa
Nan suka kaisu Shamsi hold
Sunyi parking sunfito kenan wani saurayi ya parka tashi motar da fitowa ya nufi
SAILUBAH aqallah xaikai shekara talatin da 'daya Yace dan Allah kijini ka'dan dan
tun daga layinmu nake binki
Ta 'daure fuska Tace inajinka.......
Kan yayi magana RAMADAN ya fitoh yaxo garesu Yace sannu
Cikin kulawa mutumin Yace yauwa Qanina da ganinka kai qanintane
RAMADAN ya gya'da kai Yace hakane
Mutumin yayi Murmushi Yace dan Allah ka bu'de min hanya dan nalura Auntyn taka xata
ban wahala
Yace kome yasa
Yace ina Santa ne ina qaunarta daxa ta ban ha'din kai Wlhi xanji da ita fiye da
tunaninta
Bu'dar bakin RAMADAN sai cewa yayi tab ai ammata miji.......
SAILUBAH da XEE da KHAMIS FAWAS suka saki baki da mamaki
Cikin wani yanayi mutumin ya kalleta Yace ayya kiyi hakuri dan Allah bansan sani
bane
RAMADAN yasan baxata iya cewa Komai ba awannan lokacin
Dan haka Yace la karka damu ai akwaita da yima irinku afuwa
Mutumin ya shiga motarsa ya tafi
SAILUBAH ta kalli RAMADAN Cikin bala'in 6acin rai
Sami sami yayi cikin motarsu yajata dan yasan ya bari tayi furucin bakinta bamai
kyau bane xai fito gareshi
By Hajju
[20/03, 17:09] 80k: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR👯*
Part 16 to 20
SAILUBAH tayi kwafah. Wlhi xan gyarama yaran nan xama. Cewarta
XEE tayi dariya Tace baxaki iya masa Komai bah aikun saba hakan
Haka suka shiga da jera kayansu drink da sauransu
Baifi minti biyar ba saiga Su Amarya Saudat
Nan aka fara gabatar da walima kamar yanda kuka sani. Anayin walima irin wannanne
dan Jan hankalin Amaryar tabi mijinta
Toh Madallah Gaskiya nasihar da Jan kunne ta ratsa xuciyar duk Wanda yake gun
Haka akaci akasha aka Washe
Surajo saurayin XEE shi yadawo dasu SAILUBAH gida
Tana kwance baje baje agado lokacin ana kiran sallar isha'i dama tana period
shiyasa batayi yun qurin yiba
Tunani take meya hana Alhaji Jamilu kiranta ko dama irin mayaudaran nan ne
Ta danna wayanta tana neman numbarsa.
Duk daba kiransa xatayi ba. Amma me sai tanemi numbar sama ko qasa ta rasa
Shuru tayi tana tunanin ya akayi haka itadai bata gogeba toh waya goge mata
Ai kamar an muntsineta tatashi. Ba shakka wannan aikin RAMADAN ne
Kut Amma fah yaran nan ya rainani
Baqin ciki ya cika xuciyarta
Ta'dau kusan awa 'daya tana saqa da warwara tasan bayan ya goge har blocking yayi
Tashiga tunanin sosao dan tanasan tasan hanyar da xatabi da Qanin nata
In zagine ba irin xagin da bata masa akan samarin nata ba. Ba irin jan kunnan da
bata masa ba akansu ba
Tabbas tasan indai xataci gaba da bayyana samarinta afili kuma ya gansu ba shakka
Saidai ta tsofe agida batayi Aure ba
Haka ko akayi kusan sha'dayan dare sun gama xagaye 'yan matansu
RAMADAN FAWAS KHAMIS sukayi club
Kamar yanda suka saba
'Yan matan mu musulmai sunfi yawa agun Wa'iyaxubillah
Yarane xaka gansu qanana dagasu sai rigar mama da 'dan qaramin siket Suna 'dirkar
rawa agun
(Toh Allah ya karesu ko agaba. HAYATUDDEEN Yace hmm da wiya in har xasuci gaba da
xuwa irin gura rannan Aunty Rahamat)
Nan ya maida kallansa gasu FAWAS. Inaaaa... sunyi nisa Sosai baxasuji kira cikin
Sauqi ba
Dan haka yajanye matan daga garesu ya tasasu agaba suka fitta daga gun.
lokacin kusan qarfe 2:30am
Kamar yanda yasaba buga gidan yayi ahankali megadin nasu ya bu'de mishi kofa.
RAMADAN ya bashi dubu biyu yayi part 'dinsa cikin san'da
SAILUBAH tayi Murmushi dan duk lokacin da RAMADAN ya dawo daga club idanta biyu
tana kan sallaya
Cikin baqin ciki ta kira wayansa
RAMADAN na Ganin kiranta yajah tsaki da fa'din ita wannan wai me yake hanata bacci
ne dan Allah Kullun sai taji dawowata .
Ya dai 'dauki wayar Tace ya maka kyau. kadawo ko
Yace Allah banje ba fah Auntyna
Tajah tsaki ta kashe wayan
RAMADAN yabi wayan da kallo......
By Hajju 07038260028
[20/03, 17:09] 80k: [4:32PM, 10/11/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR👯*
Part 21 to 25
SAILUBAH ko qa'idar tane ko tana period qarfe 2:00am nayi xata tashi tahau kan
sallaya tayita xikirorin Allah da yima Annabi salati wannan RAMADAN ne yayi nasarar
cusa mata ra'ayin hakan dasan ibada
Tunanin shi da rana kawai takeyi har abin ya shiga jikinta har cikin dare
Shi dai ya nuna mata ba halittar da Allah bayaso kamar mushe akwance
(Wato mutum yasaki baki yata bacci kamar wani wawa)
Yace tadinga tashi qarfe hu'du sallar Asuba tadinga samun
Ita kuma ganin xata iya tashi qarfe biyu shi yasa take tashi
har ya xaman mata jinin jikinta .
Ta juya ta kwanta tana tunanin wacce hanya xatabi tahana RAMADAN xuwa club
Nan bacci yayi awan gaba da ita tare da mafarkai barkatai duk nashi
Bayan sun shiga motarne cikin tsokana XEE Tace wannan wanka haka RAMADAN
Yace Aunty XEE kenan
Tace yau Asma'u ko Amina suka ganka saisun tsure.
Tayi Murmushi kawai
Surajo Yace kema kin yaba kenan
Tace kasan qannan namu akwai iya wanka Gaskiya na yaba Sosai Yace gashi ni ba
gwanin iya wanka ba bare inqara shiga ranki Tace karka damu soyayyarka ta isheni
ma haka. Inka qara da wanka xaka cutar dani.
Bana ganin wankan kowa sai naka wan nan ma dan qaninmu ne. Shiyani Yaba masa
RAMADAN ya kalli SAILUBAH cikin muryar can qasa kuma a shagwe6e Yace sun fara
damun kunnena fah Aunty
ki duba yanda suke kalamai agabana ina qanin su
Kan tayi magana XEE ta cafke da fa'din ayya Qanina mundena kaji.
Lokacin da suka tashi KHAMIS ya gyara faking 'din motarsa. Dan shi sun da'de da
futowa
Asma'u ta dafe kai Tace ban ta6a ganin 'dan iska 'dan rainin wayo irin RAMADAN ba.
Ko a ina ya ta6ajin an bada hutu a asoyayya oho 😆
[11:10PM, 10/11/2016] Rahamat Nalele 👯: Dake SAILUBAH Tace kanta na mata ciwo sai
kawai KHAMIS yasha Sha taletale ya fara saukesu ita da RAMADAN
Sannan yakai XEE ya wucce gida
In ta 'kaice muku awannan daran SAILUBAH tayi samari kusan shidda masu aji da nera
Kuma sanda suka Nace suka samu numbarta
Dukda ba magana take musu bah. XEE CE take aran bakinta
Gidan Amaryar Saudat yayi kyau Sosai dan Babban gidane. Saidai tana da abokiyar
xama Rabi'a.....
Abin takaici😔
Sunfito xasu koma gida. motar Abbas suka shiga inda yajasu sun hau titi yana jansu
ahankali dan bayaso yadena kallan masoyiyar tasa SAILUBAH
Basai XEE tahango saurayinta Surajo da wata mace a motarsa ba. Kasan cewar sun
kunna wutar motar yarinyar tana duba wani book dake hannunta
Kallo 'daya xaka musu Kasan suna cikin nisha'di.
Gaban XEE ya fa'di hankalinta ya tashi toh dama XEE kishine da ita Sosai akan
sahibin nata Surajo
Aiko cikin qara Tace Abbas yabi mata Su
Cikin rashin fahimtarta ko ya bishi
Har suka kai wata unguwa wai ita bacirawa inda sukayi parking a'kofar wani gida
Abbas ma yayi parking kusa dasu
Cikin Xafin nama tayi yunquri fitta daga motar... SAILUBAH tariqe hannunta Tace
karkiyi wani abu pls kibarsu mukuma gida
cikin xubar da hawaye Tace naga alamar bakisan kishi bah bakisan miye so ba. Tunda
baki ta6a tsaida mutum 'daya ya mantar dake duniyar marasa SOO bah
Wlhi kinji na rantse miki 'daukewar numfashine kawai xai hanani xuwa ga waccan maci
amanar
XEE tamata mugun kallo Tace bagaki gashi ba Ki tambaya shi man
Cukume wiyan rigarsa budurwar tayi cikin tashin hankali Tace idan kasaba yaudarar
mata ni baka isa ka yaudareni ba
Saura sati biyu Aurena dakai ashe kanacan kana neman wata harda kai sadakinta 'dan
rainin hankali ni xaka rainama wayo.....
XEE ta qara tsaida idanta akansa cikin sanyi Tace abinda Tafa'da gaskiya ne
Duk lallashin duniyar nan ba wannan SAILUBAH batama XEE akan tayi shuru tayi kuma
hakuri ba Amma taqi sauraranta
Haka Abbas ya kaita gidansu Sannan ya juyo da kan motarsa ya dawo da SAILUBAH gida
Akan idan RAMADAN yayi parking
Yace toh Allah ya tashemu lafiya dan nasan baxa ki tsaya saurara taba awannan
lokacin sai munyi waya
SAILUBAH tamai murmushin yaqe Tace toh. Dan ba qaramin ciwo kanta yake mata ba
Tana shiga gidan nasu RAMADAN ya bita har 'dakinta
Yace shi kuma wannan Waye
Ta kallesa ka'dan Tace ban sani bah
Yanayin da tayi magana dashi shiya tabbatar mishi ciwan kan nata bai saketa bah
Dan haka ya bu'de dirowar da take saka magun gunanta ya 'dauko mata maganin ciwan
kan ya bata da ruwa. Sai taqi kar6a
Sam SAILUBAH batasan magani danjinsu allura
Dake yasan da xaman wannan sai yahau lallashinta akan tasha
Tace nace baxan shabako. ko Ana dolene
cikin fusata Yace Wlhi saikin Sha so kike Ki hanani bacci cikin nutsuwata
Ta kalleshi cikin qarfin hali Tace wai me yasa kagama raina nine RAMADAN
Yace ba rainaki nayiba Auntyna kawai dai Kinsan baxan iya bacci bane kina Cikin
ciwan nan dan Allah dan Annabi kisha kitemaken
Sarai tasan inba Sha tayiba baxai barta ba. Kuma da gaske baxai iya yin baccin ba
Dan haka ta kar6a tasha kamar xatayi kuka
Yayi Murmushi dan yasan ba qaramin sa'arta yaciba wajan shan maganin da tayi
Sanda ya barta nakusan minti goma Sannan Yace dan Allah Auntyna Waye Wanda ya
saukeki amota
Ya sosa qeya Yace Wlhi nafi kowa damuwa da duk ciwan daxai cafkeki
Amma dan Allah kitemaken kigayamin Waye shi
Tace me sona ne
Yace tab yanxu kina sanshi kuma
Ta kallesa Sosai Tace ai kallo 'daya na mishi naji ina sansa har cikin xuciyata
RAMADAN ya galla mata wata muguwar harara batare daya San yayiba Yace hmm
Lalle bakiyi sa'ar masoyi ba
Tace meyasa
Yace kallo 'daya na mishi nasan bai cika sharu'dan da kikeso agun Wanda kikesan
aure ba
Tashi tayi daga gadan nata Tace me ka hango atare dashi wanda bai cika shara'di na
ba. Bayan yana da ku'di daga ganin motar daya ke tuqawa. kai ka sani
Yace eh da alama me ku'dinne Amma Wlhi xakisha kunya duk ranar da kika fitoh dashi
kika nuna ma jama'a shine mijin da xaki Aure
Ta waro ido. Me kake nufi
Yace yayi muni da yawa ga Wasu haqora da suka mishi cakaro cakaro abakinsa
SAILUBAH tayi shuru tana so ta hango Abbas a idanta Amma takasa dan ita ba kallan
tsaf tamasa ba
Kuma dama tacema RAMADAN tana san shine dan ya barta da surutunsa kanta namata ciwo
Ganin da RAMADAN yayi tashiga tunani shiya sashi shafa gefan fuskarta tuni ta
farfa'do daga tunanin nata
Yace gaki kyakkyawa abinki Amma xaki Auri me kama da aladu....😆
Part 31 to 35
XEE tajah numfashi Tace daga nan sai yayi saurin sakeni cikin 'dan nuna tsoro Yace
am sorry Aunty XEE nayi abinda bai dace bah dan Allah kayi hakuri
Nayi shuru ina kallansa
Ya marairaice tamkar xaiyi kuka kamar yanda RAMADAN yake miki inya miki lefi. yaci
gaba da fa'din. Xan shiga damuwa idan bakiyi magana bah
Nace hmm karka damu Bakomai bakayi abinda bai dace ba. Daka barni ai dana sha qasa
Qanina
Yace Yauwa dama naxo induba ko kin fitone. Mutafi in saukeki agida sai kuma naga
RAMADAN Yace min kina fitowa yanama Cikin motar ma
Nace toh muje
Kinsan Koda muka shiga motar sai Satar kallansa nake. Yayinda shi kuma ya sake
sunata hira da RAMADAN
Kina wani maganar ya rungumeki ni runguma nawa RAMADAN yayi min akan hakan
Kin san ta6a hannuna agun RAMADAN bakomai bane
Ya riga da ya sabarmin da hakan
Idan kuka nake rungumata yake yana lallashi inyi shuru. Haka idan shi yana cikin
damuwa kwantar da kansa yake ya shagwa6e tamkar jariri in lallashi
Agabanki yasha yimin kiss a kumatu a hannu Amma ni meyasa banji san shi ba
Eh idan ya ta6ani inajin xirrrr Amma ban 'dauki hakan a matsayin Komai ba dan dama
bansa wani abu araina bah
Kawai kinbi shshashar xuciyarki kinfa'da soyayyar qaramin yaro waima KHAMIS.
Tsaki XEE taja cikin takaicinta Tace hmm to dama ke me xakiji Bayan ba sanin
soyayyar ki kayi ba
Sam bakisan miye soyayya bah
Kina maganar na kamu da soyayyar qaramin yaro ai bani na halicci xuciyata bah
Inasan KHAMIS kuma Wlhi in ban Auresa ba baxan ta6a yin Aure ba kinji na rantse
Cikin Baqin ciki hawaye ya xuboma SAILUBAH Tace ai sai kije ki nemama kanki mafuta.
Tafa'da da Takaici
XEE takalleta Tace ki fahimce mana. Wlhi SO matsifane so balaqi ne. Shuru SAILUBAH
tayi mata
Haka XEE taqarashi kukunta ta hakura tatafi dan SAILUBAH Sosai takasa fahimtarta.
Koda RAMADAN yaxo gun SAILUBAH bai sameta da warwala ba sai yayi tunanin ko dan
rikicinsu na 'daxo ne. Yace waya ta6amin Auntyna. Taqi kulashi
Cikin kalar tausayi Yace Wlhi in bakiyimin magana bah Xanyi kuka
Ta kallesa. Dariya ta kamata. Toh kayi mana.
Yayi Murmushi ai kuma ya wucce tunda kinyi maganar harda dariya pls meyake damunki.
Ko wancan mutumin yaxo ne kuma kinji kina sansa haka a munin nasa
Ta 6ata fuska cikin shagwa6a Tace hmm yaxo Amma Nace mishi inada mijin Aurena
Cikin farin ciki Yace Allah Auntyna
Tace Wlhi
Yabata kiss a hannu Yace Yauwa gwara da kikace mai haka
Da xakiban dama da kin samu Wanda ya dace da ra'ayinki.
Tace kamar ya
Yaje feta da kallan nan nasa. Nanko jikinta ya mutu ta rikice mai
Dama haka yakeso danya samu yanda yake so
Hannunsa cikin nata idan shi ma cikin nata Yace so nake duk wani saurayin da kikayi
Ki fa'damin dan in tayaki gano Wanda ya dace dake da kuma ra'ayinki
Ya rigada ya gama kashe mata jiki saita 'daga mai kai kawai alamar toh
Yayi Murmushi da ficcewa daga 'dakin dan yasan hirar tasu taqare tunda jikinta ya
mutu
👯👯👯
Sun ha'du Su uku kamar yanda suka saba dan xuwa club. Amma sai FAWAS Yace suje
gidansu Aymana budurwarsa
Nan sukaje
tafitoh cikin nutsuwa. Yarinya 'danya shakaf.
[12:36PM, 14/11/2016] Rahamat Nalele 👯: Kallo 'daya xaku mata kugano nutsuwarta da
kyau da Allah yayi mata
Aymana tana MASEEFAR son FAWAS.
Sam duk abinda FAWAS xai mata xata bashi ha'din kai
Duk da wayan 'yan matansa hakan baisa ya rabu da ita ba. dan da gaske ya hango
maseefar son shi a kwayar idanta
RAMADAN da KHAMIS bar musu motar sukayi kamar yanda suka saba
FAWAS ya kalleta cikin so da qauna Yace yau kuma hijab aka samun dan karnaga
kwalliyar da kyau
Tace aini takace Tafa'da tana mai cire hijab 'din
FAWAS yabita da kallo Sosai
Ya gama gane yarinyar duk abinda yakeso agareta xata mishi dan yarigada ya gama da
xuciyarta ya 6ata mata xuciyarta ba wanda yake cikinta saishi. Kuma lokuta da dama
yana rungumarta yayi mata kiss ya ta6a duk inda yakeso ajikinta Amma Sam bata
hanashi
Shiyasa idan yaso kasancewa jikin mace ko basu RAMADAN xaije gareta yayi tsotse
tsotsanshi da ita Su rabu
A wahale FAWAS yasaki Aymana ya duba wayansa ganin RAMADAN yasan yayi hakanne dan
katse mishi jin da'dinsa
Ya kalli Aymana da jikinta yagama yin sanyi ya watsa mata wani kallo ta lumshe
Yace baby jeki gida sai munyi waya Tace ya kamata katuro iyayanka gidanmu
Ya waro ido tare dayin Murmushi Yace Karki damu ai dole suxo
Nan tafitoh jiki asanyaye
Taga RAMADAN da KHAMIS a 'kofar gidansu KHAMIS sai kallanta yake. Tana ha'da ido da
RAMADAN ya gallah mata harara tare da 'dan lasar le6ansa. Suka bar gun
tabisu da kallo
KHAMIS ne me tuqa motar cikin jin da'din tuqin ya kalli FAWAS Yace ka 'dan huta fah
yau
Yace danma 'dan iskan nan ya katseni
RAMADAN Yace xanso ganin Amina
Yace ba Asma'u ba
Yace na bata hutu ai
Haka sukayi gidansu Amina tana tare da wani saurayinta kallo 'daya xaka mata Kasan
tana hirarne batare da Santa ba
Tana ganin motar masoyin nata RAMADAN tasaki Murmushi
RAMADAN Yace mutafi kawai
FAWAS Yace inka isa in nutse anan 'dan rainin hankali kawai dan kaganta da wani
shine..........
Kanya qarasa Amina yaxo jikin motar tasu tabar wancan saurayin nata
Nan tagaisa dasu KHAMIS takalli RAMADAN Tace farin Cikin raina
Ya kalleta da Murmushi Yace na'am tauraruwata
Tace ban xaci ganinka ba
Yace Allah ko. Wancan shine Angwan naki
Da mamaki Tace ban gane ba
Yace ina nufin dai shi xaki Aura. Dan naga ya ha'de
Tace duk duniya ta shai da ba wanda nake so sai kai. Me xaisa kayi min irin wannan
wasan Bayan Kasan Kaine mijin Aurena
Ya waro ido Yace wai dama soyayya mukeyi da xaki Sa aranki xan xama miji
agareki......
Ba Amina ba hatta KHAMIS da FAWAS sanda suka waro ido😳 cikin tsoran furucinsa
Yaci gaba da cewa Wlhi tallahi ni qawa na 'daukeki ba Masoyiya ba
Atare dukkansu su ukun sukace Kut....
Tace RAMADAN dama haka kake
Ka cuceni ka cuci rayuwata
Ka hanani inso kowa a rayuwata dan mugunta yanxu kace wai qawa ka 'daukeni
Yace gaskiyar xancan kenan. Dama naxo ne in gaisheki inga kyakkyawar fuskarki dan
haka naganki Allah Ya tashemu lafiya saimun ha'du gobe....
kai KHAMIS jamu muje
Haka ta raba kanta daga motar KHAMIS yaja motar cikin jin tausayinta
Kamar yanda suka Sabah drink ne kala kala sai Wanda kakeso xakasha
Su Sha wannan susha wancan
Su rungumi mata da kissing da tsotse tsotse da dai sauran su.
Lokacin duk sunfita daga hayyacinsu. RAMADAN yaga kiran wayan Auntyn nasa. Ya waro
ido Cikin 'dan kuxari yaje harabar wajan ya 'dau kiran nata Yace my Aunty
Yanda SAILUBAH takejin ki'da na tashi shi ya tabbatar mata yanacan club 'din. Kamar
xata fashemai da kuka Tace Wato kanacan ko
Yace ina 'dakina kallo nakeyi Tace qaryane Wlhi
Yace toh kiyi hakuri yanxu xan dawo Tace karma kadawo ta kashe wayan
Bai sai taji hawaye ya xubu mata bah
Shiko RAMADAN kiranta ya hauyi yana San lallashinta karta tashi da fushi dashi gobe
Cikin fusata ta'dau wayan Tace karka kuskura kada man......
Ya katseta da fa'din Wlhi ganinan dawowa my Aunty ki dena kuka kinji
Tace wayace maka kuka nakeyi
Yace muryar kice ta gaya min hakan.
Tace minti biyar nabaka Naji dawowarka yanxu Wlhi
Yace angama Auntyna Tajah tsaki ta kashe wayan. Tare da miqewa tanajin xafi aranta
Shiko RAMADAN komawa yayi ya janyo Su KHAMIS suka fitta daga gun
RAMADAN natuqin FAWAS na maseefa akan lokacinsu yau bai cika ba ya wani janyosu
Yana jinshi ya masa shuru
Ba qaramin gudu ya dinga shararawa ba. Burinshi kawai Yakai gida nanda minti biyar
'din
Ko takan sauke KHAMIS baiyi ba yaje gidan nasu
Yana tsayawa da motar Yace toh sai da safe Yana fa'din hakan yaje ya kwankwasa
'kofar gidan nasu
nan megadi ya bu'demai ya sallameshi wajan bashi dubu biyunsa yayi part 'dinsa
cikin san'da
FAWAS ya kalli KHAMIS Yace kai xan fara saukewa ko insauke Kaina Yace fara dai
saukeni...
SAILUBAH najin sawowarsa tayi Murmushi dan ta'dauka xai xarce lokacin data saka
mishi
Tatura mishi da 'dan gajeran message cewa _ka tabbatar kaci abinci kafin ka kwanta_
Lokacin yayi wanka kenan yasa kayan bacci xaiyi Sallah yaga sakwan nata. Da
Murmushi ya karanta kana ya rubuta mata _xanci insha Allah Auntyna_
Washe gari Bayan sun ha'du da safe Tace dan Allah yaushe xaku dena xuwa club
Yayi mata sanyayyan murmushi me sata in 'dauke idanta akansa ya 'dan susa qeya Yace
sai randa mukayi Aure Auntyna
Tace Wato barin ba yanxu ba. Dan nasan xaku 'dau shekara goma Sha biyar nan gaba
kafin kuyi Auran dan ayanxu bamai hankalin daxai baku mata
Ya sheqe da wata dariya abinda ya bata mamaki dan tasan Murmushi ne abokin
tafiyarsa
Ya kama hannunta tare da kallan kwayar idanta Yace hakane Auntyna
Kin san na rabu da Amina jiya
Tace ayya yarinya me hankali ta tsaya 6atama kanta lokaci akanka. Me ya ha'daku
Ya kwashe Komai ya gaya mata yaqara da cewa Wlhi Auntyna taban tausayi
Tace kwarai Ko nima
Yace yau sha'daya muke da lectures
Tace ni baxanje ba fah
Yayi shuru yana kallanta can ya shafi gefan fuskarta Yace nadena matsa miki akan
hakan my Aunty
Tace kadena ta6amin fuska ni sa'arkace wai
Yace abin ya xaman min jiki ne Auntyna ko shima kinajin xirrrr 'din 'din ne
Ta gallamai harara Tace ko 'daya nidai......
Ya katseta da cewa nadena shikenan
Tace inaso kakaini gidansu XEE yau daga can kakaimu gidan Saudat tana ta kirana
bansan ko lafiya bah
Yace toh kishirya yanxu na kaiki kafin nagama shirin makaranta nasan kungama sai
nakai gidan Aunty Saudat 'din mubarki acan in muntashi daga skull sai mubiyo mu
'daukeki
Tace itama XEE baxa taje ba
Yata6e baki Yace hmm Allah ya ganar daku sanin mahimmancin ilimi
Ta harareshi ya futa daga kitchen 'din
Takira wayan XEE tana CE mata gatanan xuwa.
XEE Tace ki temaken kuxo da KHAMIS dan Allah dan SOYAYYARKI da manxan Allah
Jikin SAILUBAH yayi sanyi Tace toh
Nan takira RAMADAN Tace dama suje da KHAMIS Yace toh bara ya gayamai yaxo yasa memu
Tace Yauwa
Riga da siket tasa na atamfa 'dinkin ya amsheta Sosai tayi kyau ba'dan ka'dan ba
RAMADAN ya dinga 'daukarta a hoto
Bayan sun fitoh ne Yace Amma fa kayan nan sun matseki Tace toh yake nan
Yace danine ke da hijab xansa
Tayi dariya Tace tab toh bakai bane ni
KHAMIS Yace Aunty LUUVAH kinyi fah
Ta tallesa sosai eh da gaske KHAMIS na miji ne kuma kyakkyawa amma ita bataga abin
so a jikin qaramin yaro ba
Tace Kullun haka kuke cewa KHAMIS
Yayi Murmushi Yace ai hakanne
Bayan sunyi parking a Gidansu XEE suka shiga gidan kansu tsaye
A falo sukaga mamah da ita XEE 'din
Nan suka gaida maman tayi kitchen
KHAMIS Yace Aunty XEE
Tace yane Qanina
RAMADAN Yace naga kin fa'da tsakanin jiya da yau lafiya Tace hmm ganinan dai
RAMADAN so yanasan haukatar dani
SAILUBAH tagalla mata harara
Yace toh Allah ya kawo Sauqi Amma ciwan so maseefa ne.
Tace AmEEn hakane wlhi
SAILUBAH ta xungureta akan tadena kafe KHAMIS da ido haka
Itama ta harareta abayyane Tace Wlhi baxaki hanani ganin abinda ya hanani bacci ba
SAILUBAH Tace toh tashi muje 'daki
Tace qaramin minti biyu in sami nutsuwa dan Allah
Cikin Baqin ciki SAILUBAH tarabu da ita
Tana kallanta tanata Satar kallan KHAMIS
Shiko basan tanayi ba
Ta harari SAILUBAH idanta akan na KHAMIS ita kanta tsintar kanta tayi da shagwa6e
mai fuska Tace dan Allah kubari sai 'dan anjima
Yace Aunty XEE kiyi hakuri Kuba san karatu kuke ba. Muko munaso kibari in aka tashi
maxo. Yafa'di hakan cikin kulawa
RAMADAN ya kalli XEE Sannan ya maida kallansa ga KHAMIS ya kalli SAILUBAH sai yayi
Murmushi tagallamai harara.
Haka suka tashi suka tafi badan XEE taso ba
RAMADAN na tuqi ya kalli KHAMIS ka'dan Yace ka ankare da Aunty XEE fah
Cikin sauri KHAMIS ya kalli RAMADAN Yace ban gane ba pls ganar dani naji gabana ya
fa'di
RAMADAN ya ta6e baki Yace idan budurwa taga 'daya daga cikinmu tana so. kuma
'dayanmu ya gano hakan ai da wannan kalmar muke gayama juna dan ya ankare da ita ko
ka manta ne
Sakin wayar hannunshi KHAMIS yayi ya kama kansa da hannu biyu Yace innalillahi-
wa'inna'ilaihirraji'un
RAMADAN Yace xaku dace Sosai 😆
Part 26 to 30.
Taqara shagwa6a fuska Cikin shagwa6a Tace yanxu kenan idan yaxo gobe karna fitta
Yace in nine ke ba
Tace nifah bana san Auran mummuna
Yace na sani ai. mexai hana kice mishi ammiki Miji
Ta qura mishi ido tana san tunanin wani abu. yayi saurin katse mata tunanin da cewa
no fah. ki fita idan yaxo Amma kiqare mishi kallo Wlhi xaki yarda da xancena.
Yafa'da yana mai miqewa har yakai 'kofa. Tace ina fatan dai kaci abinci. Yace banci
bah dan abincin biki ne agidan
Tace ai yayi da'di
Yace tuwan 😳
Da suka sama miyar kabewa kai Gaskiya ba xanci ba Wlhi. Dan natsani kabewar nan
SAILUBAH tayi Murmushi dan tuno qiyayyar dake tsakaninsa da tuwo. Sam ya tsani tuwo
musamman asaka kabewa amiyar (kunsan kano da kabewa Allah ya basu hikimar
sarrafata😆 )
Ya san idan ya qara gigin kallanta tabbas xai hanata bacci yau
Dan haka batare da ya juyo ba Yace toh naji
Alkawari
Nayi
Ya fitta daga 'dakin
SAILUBAH sai taji hankalinta ya kwanta dan tasan tunda Yace baxaije bah toh baxai
je 'dinba
RAMADAN ko yana kallan Su FAWAS na shirin xuwa club Yace baxai jeba
Sukace me yasa Yace Auntyna ta hanani xuwa yau
Kai Aunty LUUVAH me yasa tayi haka. Cewar KHAMIS
FAWAS Yace share kawai muma mun fasa xuwa.
RAMADAN yayi dariya Yace nasan xa'ayi haka
KHAMIS yajah tsaki Yace naso hutawa Wlhi
Dole haka sai gun 'yan matan nasu sukaje kawai
Dake iyayan nan ne masu San 'ya'ya nan suka hau lallashinta da cewa gobe xasu aika
masa da sadakinsa basai ma yaxo bah
Yayi Murmushi Yace toh shikenan Allah yabaki lpy Auntyna saina dawo
Har yakai kofah Tace RAMADAN Yace na'am.
Taqara harararsa Tace kayi kyau Sosai. Tafa'da batare da tasaki fuskarta ba.
Yadawo gareta ya kama hannunta da shafa goshinta. Ba xafi agoshin Yace Allah yabaki
lafiya Auntyna kema kinkyau Sosai
Tace kaci abinci ko Ya'daga mata kai alamar eh kana ya mata kiss a hannu ya fitta
yana cewa natafi
Tabishi da kallo tana jin da'din qamshinsa.
Tace Kin san Allah na manta da wani Surajo dan nariga da nacireshi kwata kwata daga
raina
Ni damuwata itace KHAMIS
Wayyo Allah na SAILUBAH yau yarannan ya rikitani
Ya jefamin sanshi araina lokaci 'daya
ashe dama duk wannan burgenin da Nake cewa yana yimin Ashe na fara sanshi ne dama
haka so yake shiga xuciyar mutum farat 'daya
Wayyo ni XEE yaxanyi dasan Wanda na girma qaramin yaro
Saiga hawaye ya xubo mata
Cikin kuka tacigaba da fa'din watoh nafito daga department 'dinmu 'daxo ina tafiya
ahankali dan wata gajiyace ta kamani lokaci 'daya
Ban kalli gabana Sosai ba. basai kawai nayi tuntu6e ba. Nayi taga taga xan fa'di.
Sai gashi ya yanko kwana......
Cikin sauri ya kama hannuna da janyoni jikinsa.
SAILUBAH Kaina ya sauka a qijinsa
SAILUBAH na shaqi qamshinsa
SAILUBAH saida xuciyata tabuga hankalina ya tashi dan jin wani fitinannan filing
daya kusantoni
Tace wlhi jinayi dama in dauwama a haka a qirjinsa dan jin yanda qamshinsa yake
shiga hancina
By Hajju
Afuwa dan Allah MASOYA
[20/03, 17:09] 80k: [3:00PM, 17/11/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR👯*
Part 36 to 40
Tashi SAILUBAH tayi tashiga toilet can tafitoh. Tace yanxu xa muje gidan Saudat
'dinne. ko sai anjima.
XEE tayi Murmushi cikin jin da'din furucinta Tace nagode ma Allah dayasa kika
fahimceni
Wlhi baxan 6oye miki ba. Damuwata ta qasu kashi biyu ne. Da qin fahimtata da
kikayi da maseefar son KHAMIS
Naji sanyi araina ta 6angaranki. Yanxu yaxa muyi da KHAMIS
SAILUBAH tajah numfashi Tace inaso kirage xagewa akan san nashi
Tace ni Kaina bansan lokacin da xuciyata ta shagaltu da kallanshi 'daxo ba. Wlhi
SAILUBAH bansan ya akayi nakamu da sanshi ba. Ban sani ba. Ina da aji
inada kamun kai.
Ke kin sani Amma lokaci 'daya na burkice. Tafa'da hawaye na xubu mata.
Yanxu ne SAILUBAH taji tausayinta. Tayi shuru tana tunanin ta'ina xasu fara
Can dai Tace bama rasa mafuta XEE kwantar da hankalinki
Can da yanma sukayi gidan Saudat rijiyar xaki inda suka tarad da ita Cikin damuwa
XEE Tace ya naganki cikin damuwa kina amarya
Tace ke dai bari. Ashe Auran mijin da yake da mata maseefa ne
Atare SAILUBAH da XEE sukace lafiya
Tace ba lafiya ba
Kunsan tunda aka kawoni gidannan ban qara ganin idan Mijina ba
SAILUBAH Tace kamarya
Tace Wlhi SAILUBAH Saidai inji muryarshi da shewarshi a 'dakin kishiyar tawa
XEE tawaro ido Tace duk soyayyar daya nuna miki
SAILUBAH Tace tab kuma sai kika xuba musu ido
Tace toh ya xanyi
Tana dai xuwa ta kawomin abinci tajuya tatafi........
Kan SAILUBAH tayi magana sai sukaji muryan Megidan nasu shi dasu RAMADAN
Da 6arin jiki yake CE musu kushiga tana ciki
Dako kin temaki kanki dan Wlhi inda nice Sai dai axo rabamu dan ubanki xanci tunda
mjin ba naki bane ke ke 'daya. Cewar XEE
RAMADAN ya kalli Saudat Yace Wlhi Aunty kima mijinki ladabi da biyayya karki biyema
Auntyna Kinsan ita 6ata abu take Sam bata iya gyarawa ba
XEE ta kallesa Tace ai xata mishi biyayyan
SAILUBAH Tatashi tana cewa saita biyemun. kuma ban iya gyaran ba. Kasanni
she'daniyace. Wlhi RAMADAN kafita daga idona in rufe.
Suma tashi sukayi harda XEE
RAMADAN Ya ha'da hannuwansa biyu Yace iyi hakuri toh
Ko kulashi batayi ba tafita daga falan.
Har waje Saudat tarakosu
RAMADAN Yace Aunty XEE da mota biyu muka xo kinga.....
Xaki shiga tawace in kaiki gida ko KHAMIS ya kaiki.
Da sauri KHAMIS Yace kaji ka da wani kwa'du.
Aunty LUUVAH xaka 'dauka tunda layinku 'daya ko nace gidanku 'daya
ko ba haka ba Aunty XEE ni saina kaiki gidan. Ya fa'da da kallanta cikin murmusawa
SAILUBAH tayi Murmushi tana fa'din aranta Lalle yarannan sun raina musu hankali.
Yanxu haka sungama shirya abinsu xasu kawo musu wani alaye.
RAMADAN ya 'daga mishi gira. KHAMIS yayi Murmushi ya shige shima natare da Auntys
'din nasu sun ganosu bah
Da yayi parking a 'kofar gidansu ya kalleta cikin wani yanayi ya sanyaya murya Yace
my Aunty mun'iso
Duk da XEE tasan sun iso hakan bai hanata kallansa cikin sauri ba. Dan muryar da
yayi amfani da ita wajan yi mata maganar ta shigeta ba'dan ka'dan ba. Ya lura da
hakan sarai. saiya futa daga motar yaxo ya bu'de mata motar kamar yanda masoyi yake
yima masoyiyarsa
Tafi toh xata 'dau jakarta sai kawai yayi saurin 'dauka yana cewa da alamun gajiya
atare dake my Aunty xanso in kai miki har gida idan kin amince min. Yafa'da da
jifanta da wani kallo mesaka Sarki yayima Bawansa ladabi.
Da sauri Tace na amince. Ya qura mata ido
Tace lafiya kike kallona haka
Yayi Murmushi yace Wlhi wani tunani na shiga. Tunda nake dake Aunty XEE ban ta6a
jin da'din muryarki irin tayau bah.......
Da'di kamar ya kashe XEE Tace sai yau ka ta6aji
Ya waro ido Yace kinga xan 'daure Kaina. Ai Kullun muryarki acikin da'din sauraro
take
Tace toh Nagode
Ta shige gaba yana binta abaya yana qare mata kallo har suka iso falan gidan Yace
mamah bata nan ne. Tace gashi dai daga dukkan alamu
Ta ibo drink taxuba mai a cup itama tasaka ma kanta kana Tace xanso kasha Qanina
Ya kar6a da Murmushi Yace banso shaba dan banajin shan Komai saboda damuwa Amma
tunda kinaso nasha ba'abin da xai hanani Sha
Sanda ya Sha ka'dan Tace meya sakaka cikin damuwa Yace Wlhi Aunty wata nake So❤
saidai ta girmeni ban san ya xanyi bah
Da sauri ta furzar da drink 'din da yake bakinta ha'de da sakin cup 'din ya fa'di
qasa......
jikake tass ya fashe
Tayi saurin xamowa daga kan kujerar da take cikin tashin hankali Tace wa kakeso
kuma
Da sauri ya matso kusa da ita da ciro hankicif 'dinsa cikin nuna tsoro ya kama
hannunta taji wani shock shima yaji Amma ya share ya fara goge mata hannun nata da
gefan bakinta Yana cewa am sorry Aunty XEE na tada miki da hankali ko. Karki damu
nasan baxata soni bah. Sai dai Wlhi baxan ta6a Auran wata mace ba in ba ita ba. Ya
qarashe maganar da sake mata hannun nata
Aiko saiga hawaye ya xubo mata cikin kuka Tatashi xata bar falan.
Yace baxan ta6a yafema kaina ba idan har kika tafi cikin kukan nan kika barni
batare da kin gayamin dalilinki nayin shiba
Juyowa tayi ahankali Tace KHAMIS nakamu tasan wani yaro wanda na girme masa gashi
kaima kakamu dasan wacce ka girma. Ganin da nayi matsalarmu 'dayace shi yasani
rikicewa har nayi wannan kukan
KHAMIS yajah numfashi ha'de da lumshe idansa yanajin kukanta har cikin ransa kana
ya bu'de idan
Yace ki dena bana so bana san jin kukanki yana damun xuciyata pls kitsai dashi
karci sakani cikin wani dan Allah
Ahankali XEE ta qaraso gabansa Tace shin abinda kafa'da haka yake
Yace akan me xan miki qarya. Yafa'da yana mai goge mata hawayan
Kawai ki share my Aunty xan kiraki anjima kiban shawa'a akan ya xan 6ulloma da ita
budurwar tawa. Sannan kema kinemi shawarata akan wanda kikeso. Tunsa kinga mu
SAMAREEN BANAH ne xan iya baki shawara yanda xakiyi dashi kema Kinga kyabani
shawarar yanda xanyi da ita
Shuru tayi masa
Shiko har yakai 'Kofa ya juyo ya dawo dan yana so ya hanata bacci
Ya shafi gefan fuskarta Yace kimin alqawarin xaki cire damuwa aranki my Aunty
Tace idan na iya cire ko wacce damuwa araina ai baxan iya cire damuwar SO ba
Ya lakuce mata hanci Yace insha Allah xaki kasance da wanda kikeso dan shima yana
MASEEFAR SONKI
Tace ya akayi kasan hakan bayan.....
Ya katseta da cewa saboda ko makawone yaji wuccewarki kawai yanasan Allah yayi
halittar kyakkyawar mace anan
Tayi Murmushi Tace yanxu kai ka tabbatar da hakan
Yace Wlhi ayanxu bawanda ya kaini tabbatar da hakan koda ko Ya Surajo ne
Ta 'daure fuska xatayi magana Yace bye bye sai munyi waya Ya fitta
Tabishi da kallo
Sallar magriba SAILUBAH tayi tafa'da tunanin wani Alhaji Aliyu da ya kirata 'daxo
wai abikin Saudat ya ganta dan Allah dan annabi tabashi dama yaxo gareta. Yanda
yake rokwanta ne yasata bashi ixinin yaxo
Tana tunaninsa ne zaizo bayan Isha'i ne ko xaixo gobe bata sani ba
To ganin yanxu mah taji wayanta na ringing sai tayi tunanin shine
Ashe bashi bane wanine kuma wai Alhaji Aminu
Duk dai abikin Saudat ne suka ganta. Yana gaya mata dan Allah taso shi Yana Santa
yana garin Abuja da xama. Baida mata. Kuma da maganar Aure xaixo gareta dan Allah
tabashi dama yaxo gareta
Dan yanxu haka yana Cikin garin kano dan gobe yake san komawa Abuja
Toh fah😳 kunsan SAILUBAH da Alhazawan garin abuja ba qaramin so take musu ba dan
ku'dinsu nan take taji ya wanta mata arai dan muryarshi nada da'di
Amma danta gwada shi sai Tace hmm banajin yau xaka ganni dan nagaji da yawo sai
gobe
Kamar xai mata kuka yake mata magiyar tayi hakuri ya ganta dan Allah Tace toh kaxo
Amma kasani minti biyar kacal xan baka
Yace angama ranki ya da'de
Bayan tayi sallar isha'i. Kyalliya tayi Sosai RAMADAN Yace Auntyna wannan kwalliya
haka. Sam ta manta sunyi fa'da 'daxo taje takama hannunsa ta sakarmai kiss a kumatu
Tace yau burina ya fara cika nayi saurayi 'dan abuja anjima xaixo
Da tsoro RAMADAN ya waro ido cikin wani yanayi Yace pls Auntyna Karki soshi dan
Allah
Ta galla mai harara tare da sake hannunsa tana ta6e baki Tace Wlhi saina so shi
Kuma na ranshe da Allah kakorar min shi saina maka dukan tsiya
Yayi Murmushi Yace wasa nake miki baxan koreshi ba
Sam SAILUBAH bata yarda da murmushin da yayi ba. Dan tasan halinsa sarai fa'danta
da cika bakinta baya hanashi korar mata su. Dan haka sai Tace suje 'dakin shi xata
gaya mishi wani Abu
Haka ko sukayi gidansu dayin part 'dinshi
Suna shiga 'dakin tacire key 'din 'dakin nashi tafita da gudu ta kulle shi ta baya
tana ai nasan maganinka
Ta window ta leqo tasheqe mishi da dariya Tace in yaxo ya tafi xan dawo in bu'deka.
tana fa'din hakan tabar gun
Sosai mutumin ya tafi da imanin SAILUBAH dan ganinshi da tayi kyak kyawa ga
xaxxafar motar da yaxo da ita
Ta'dan dai bashi dama haka
Yace Yaji da'di xai turo iyayansa suxo dan bai ta6a SOYAYYA ba bayasan yaudarar
mata
Kuma komai xa'ayi shi da sauri
Tace toh itadai saita xanta da mahaifinta tabashi labarin yanda sukayi Yace duk da
haka xai turo iyayansa gobe
Daxai tafi saiya bu'de mata wani qaramin akwati Yace ta ibi iya adadin ku'din da
takeso
Nan cikin SAILUBAH ya mun'da dan ganin yawan ku'din kuma duk 'yan dubu dabu ne a
ciki
cikin wani yanayi Tace ka barshi Nagode
Yace aa fah ina San Ki 'dauka ko ku'din xai sami farin jini aguna kisa mai albarka
dan Allah
Tace aa dai ka barshi
'Daukar wata leda yayi yasaka mata bandir 'din ku'dinnan guda goma😳 miliyon 'daya
kenan a ha'duwar farko.
Ya saka mata akan cinyarta Yace nasanki da temako duk xaki iya bayar da wa'yan nan
Amma dan Allah ko naira biyar CE kici aciki
hakan xaisa inji da'di. Ga wannan cikakken bayanai ne akaina kiba Abbanki nasan mah
xaisan mahaifina
Shuru SAILUBAH tayi tafuta daga motan da ku'din a hannunta.
Tana kallansa yafita da motar tashi yana 'daga mata hannu
Bayan 6ace warsa tayi cikin gidansu da gudu tayi 'dakinta ta xaxxage ku'din a gado.
tana murna sai watsa ku'din take sama tana ta dariya
Can ta tuna da RAMADAN. Aiko da gudu ta'dau kin 'dakin nasa tafitoh xuwa Gidansu ko
gyale babu ajikinta sai 'dan kwalinta data rufe kanta dashi xuwa kafa'darta
Da sauri take bu'de 'dakin tana bu'dewa takama hannun RAMADAN tana jansa har cikin
gidan
Sanda sukaxo 'dakinta taja musu burki Tace kalli gadona
RAMADAN ya xaro ido cikin tsoro Yace Auntyna wannan ku'dinfah
Tayi dariya ta 'dane gadan ta watsa ku'din sama Tace aikin Alhaji Aminu ne
Sai kuma tasauko ta ta tsaya agabansa
Kaga burina xai cika xan xama matar Babban mutum. xan mallaki ku'da'de masu yawa.
xanje gidan marayu inbata tallafi. xanje asibitoci nakai xiyara.........
Ya isa da Allah Ki mayar masa da ku'dinsa
Cak ko ta tsaya da maganar tata
Tace kut......
Na lura ba qaramin Baqin ciki kake yimin bah. Wlhi inxaka mutu baxan mayar da
wannan ku'din bah
By hajju
[20/03, 17:09] 80k: [4:47PM, 19/11/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*👯
Part 41 to 45
Tace toh shi kenan karka kar kaje. Ainima nakusa yin mota xanje ko ina da kaina
basai nane mi ka kaini ba jeka nagode.......
Da mugun kallo yabita kana Yajuya ya futa xuciyarsa nayi masa xafi
SAILUBAH ta bishi da kallan harara. Kana ta ha'de ku'da'danta tanemi guri ta adana
Sannan tanemi kiran XEE.
Ha'da ido FAWAS da RAMADAN sukayi atare kuma suka saki Murmushi
KHAMIS yayi dariya Yace aina rigada na tarwatsa mata kwanyar dan Wlhi yau nayi
alqawarin saina hanata bacci
Yanxu haka nasan tana cikin damuwa dan na jefata cikinta
KHAMIS ya tashi yana dariya Yace Aunty LUUVAH ka sani kawai. Itace damuwarka karka
damu baxan bari she'daniyar xuciyata ta wahalar da Masoyiyata ba. Bare ta shafama
Auntynmu
XEEE wacce take kwance tana jinyar xuciyarta da tatafi da tunanin KHAMIS Wanda ya
hanata nutsuwa Sam.....
Aiko tanajin furucin SAILUBAH tadiro daga gado Tace what one million naira 😳
SAILUBAH tayi Murmushi Tace kema abin yabaki mamaki ko. Karya tsoratar dake dan
yanxu aka fara wasan
Inaso gobe kixo gida ki gani ganin idanki
idan kuma kintashi xuwa kixo da Wannan qaramar jakar taki dan ki sami rabanki
XEEE Tace abin mamaki dama nasan burinki xai cika. Xaki ganni qarfe tara gobe yanxu
ma dan dare yayine
SAILUBAH ta kwashe da dariya Tace shegiya XEEE taji maganar nera aiko goban xaki
wanke idanki dasu
Tace na sani aminiyata idan ina tare dake ban wanke idona da naira ba ai babu ranar
daxan wanke idan dasu
SAILUBAH tajah numfashi Tace ya kikayi da qaramin yaran naki
Tace hmm ina sane ai naqi kiranki dan ya burkitani
SAILUBAH Wlhi Wlhi Wlhi ina MASEEFAR SON KHAMIS Ya Xanyi
SAILUBAH tayi mata dariyar rainin hankali Tace karkiyi yunqurin ki ransa. ki bari
har sai shi yane meki akan ki bashi shawarar imba haka bah Wlhi ina tabbatar miki
saiya baki wahala yadinga garaki
Tace Kinga ko kiran shi ya shigo a qaramar wayata kamar yasan hirarshi muke
SAILUBAH Tace yauwa. Na sanki da rikicewa kinutsu karya rainaki da yawa pls
Tace hmm SAILUBAH kenan bakiji yanda jikina yake rawa ba.
SAILUBAH tajah tsaki Tace Gaskiya kinada matsala XEEE da Takaici
XEEE tayi dariya Tace hmm Allah ya jarrabeki dasan qaramin yaro kiji fiye da yanda
nakeji..........
Cikin maseefa Tace ba AmEEn ba 'yar is.......
XEEE ta katseta da cewa saida safe ta tsinke hirar tasu
SAILUBAH Tace tajah tsaki Tace Allah ya rabani da soyayyar qaramin yaro........
XEEE ko bajewa tayi agado tatattara nutsuwarta cikin bugun xuciya ta'dauki wayan
KHAMIS Wanda saura ka'dan tayanke a karo na biyu
Tace hello
Yace inata kira Aunty. Allah yasa jin da'dine da lafiya da kwanciyar hankali ya
hanaki 'dauka
Tayi murmushi Tace toh bansan me xance maka ba KHAMIS Amma ina cikin lafiya da
kwanciyar hankali musamman mah yanxu
Yace toh madallah dama nakiraki ne akan.........
Sai kuma yayi shuru
Cikin sanyi XEEE Tace akan nabaka shawara kan budurwarka ko
Tace eh Aunty Allah yasa baxan takura miki ba. Wlhi xuciyata CE take san xuwa
gareta yanxu gashi kuma idan naje bansan me zance mata ba
Shuru XEEE tayi kishi nacin xuciyarta.
Dama ace ina tare dake tana shafi gefan fuskarki na dawo dake daga tunanin da kika
fa'da
KHAMIS ya fa'da Cikin sanyin murya....
[7:24PM, 19/11/2016] Rahamat Nalele 👯: XEE tajah numfashi Tace hmm ba tunani na
fa'da ba kawai......
Yayi saurin katseta da cewa kar kiyi min musu Aunty inaso kawai naji me yajefaki
cikin tunani
Taja numfashi Tace tunani nakeyi yanxu idan Nace kar kaje gunta baxa kabi umarnina
ba kuma ni haka kawai Naji bana san kaje gunta wlhi kaje sai nayi kuka. shiyasa
kaga nayi shuru
Kuma baxan iya gaya maka dalilin hakan bah
KHAMIS ya lumshe ido tare da gyara kwanciya kallo 'daya xaka mishi Kasan yana cikin
wani hali na tafiya a cikin SO da qauna
Yace yanso ki gyara kwanciyarki
Tace nagyara
Yace haba Aunty. Me xaisa baxan bi umarnin ki bah.
Ki shareta kawai Wlhi ba xanje gareta ba na hakura. Dan da kiyi kuka gwara in
hakura da ita gabaki 'daya dan nasan kukanki xaifi damun xuciyata fiye da soyayyar
da nake mata
XEEE taqara qan qame wayan akunnan ta cikin muryar sanyi Tace ina sanka Qanina da
xaka ha'kura da ita gabaki 'daya da sai nafi kowa jin da'di.
Yayi Murmushi yana raina wayo irin nata. Ga wata xaxxafar soyayyarta da take cafkar
xuciyarsa
Yace LA
Idan hakan xai saki jin da'di Wlhi xan iya hakura da ita har abada Amma sai dai in
xaki.....
Sai ya kasa qara sawa
Cikin murna Tace Amma sai dai me
Yace ina jin tsoran qara sawa ne Aunty.
Tace kafa'da man. Karka damu. Tafa'da da San jin furucin nashi
Yace ki bani minti biyu kacal Xanyi addu'a kafin in fa'da miki. Xakiji shigowar
sako yanxu
Tace toh ina jira dan Allah karka wucce 2 minutes 'din
Yace angama Aunty....
Shuru XEEE tayi tana addu'ar Allah yasa ta mallaki KHAMIS a matsayin mijinta ita
ka'dai. Dan yayi mata tako ta'ina. Sai juyi take
KHAMIS ko dariya yayi Yace yes my Luv Allah yasa Ki xama mata agareni
Sannan yayi rubutu kamar haka......
_xan ha'kura da ita gabaki 'daya idan har xaki mayemin gwurbinta. Xanso Ki xama
mata agareni Ki haifamin yara kyawawa kamarki_
XEEE Ta rungume maman tana Tace yau Xanyi kwanan farin mamah nasamu wanda yafimin
Surajo
Din gure mata kai mamah tayi tajah tsaki Tace Nina 'dauka wani abunne Wlhi
Da dariya XEEE Tace aa ba Komai koma gun BABAH kawai
Fitta mamah tayi tana fa'din Allah ya shirya
XEEE ta koma gado tana da'da karanta sakwan nasa.
Kafin ta kashe wayan nata gabaki 'daya
Qarfe 11:30pm na dare SAILUBAH ta kwanta danyin bacci. Sai kuma tatuna bata tambayi
Qanin nata ko yaci abinci ba
Nan tafara Ne mansa a waya. Sai kuma tatuna sunyi fa'da tajah tsaki da dai kiran
nasa dan tasaba da hakan in bata kirasa ba hankalinta baxai kwanta bah
Lokacin sun dawo kenan daga wajan 'yan matansu FAWAS yayi gida shi kuma ya kwanta
kenan yaga kiranta
Yayi Murmushi dan yasan abinda xata tambayesa
Sai yaqi 'daukar wayan yana ji har takira sau uku
Daga qarshema ya kashe wayan gabaki 'daya yabi lafiyar gado
SAILUBAH tayi kwafah Tace Wlhi in dai akan Alhaji Aminu ne sai dai kata fishinka
tajah tsaki takwanta
Salloli tadinga yi tunda baccin yaqi 'daukarta kamar yanda shima ya kwana Yana
lafular
Washe gari Suna breakfast da Abbanta take bashi labarin Alhaji Aminu da kuma bashi
qarin bayanai akansa kamar yanda yabata jiya
Da murna Abban nata ya kar6i takaddun gannun nata yana dubawa
Can ya kalleta Yace ai wannan yaran Malam Saluhu ne
Kiga ikwan Allah ban sanshi da wannan 'dan ba
Kuma yaushe yayi ku'di haka
Hmm Allah me iko
SAILUBAH Tace Abba Waye mahaifin nasa
Yace baxaki sanshi ba
Amma acan baya da nake da ku'di yayi aiki a qarqashina mutumin kirkine
Tace ayya.
Yace Naji da'di Sosai da kika bi umarnina kika kawo min Wanda kikeso. Karki damu
xan nemi mahaifin nasa muxanta Tace toh
Abban nata na barin gidan tatashi dan xuwa lalla6o qanin nata
Sai matar Abban nata Tace xan samu dubu 'daya dan Allah agunki fita nake san nayi
Amma ba ishash shan ku'di a hannuna
SAILUBAH Tace eh xaki samu na manta in gaya miki jiya nasamu ku'di ahannun shi
Alhaji Aminun da yawa xan baki dubu 'dari biyu Amma Karki gayama Abba
Da wata irin murna ta rungumi SAILUBAH Tace Allah ya miki albarka kinji ai Wlhi ba
Wanda xaiji
SAILUBAH Tace toh Allah yasa
Nan taje ta ibo mata mata tabata
Kana taje gun Kakah Tace Kakah na kawo miki Wasu ku'dine da wani Alhaji Aminu
yabani
Tace aa ki barsu suyi miki amfani kinga ni ba abinda xasuyi min tunda na tsufah
SAILUBAH ta dafata Tace Karki damu dubu ashirin yaban shine nace bara na baki dan
ba'abinda Xanyi dasu yanxu kuma kinga inna ba Abba baxai kar6aba xaice in mayar
masa da ku'dinsa kuma kinga bakyau maida hannun kyauta baya shiyasa nakesan kikar6a
dan Allah
Kakah ta waro ido Tace har dubu ashirin gaskiya ku'din yay yawa Karki sake kar6ar
ku'dinsa haka
Tace toh. Da miqa mata
XEE na tashi da safe ko breakfast batayi tabu'de wayanta tana san qara karanta
sakwan masoyin nata......
Sai kuma ga kiransa ya shigo mata...
Ita kanta batasan ya akayi tayi saurin 'dauka ba da cewa hello.....
Kin hanani bacci jiya Aunty gashi yanxu yana damuna dan ma yau bani da lectures da
abin ya ha'du min biyu. dan Wlhi baxan iya xuwa ba. Xuciyar tacika da tunaninki da
fargaba. KHAMIS Yafa'da kamar xaisa ma XEEE kuka.....
Yayi Murmushi Yace da'dine yayi miki yawa my Luv. kawai ki kwanta kema xanxo miki
cikin baccinki na tayaki hira. Kuma xanso Ki canja min Suna daga Qanina
xuwa.........
Tayi saurin katse shi da cewa xuwa my sweetheart....
Yace yayi Sosai saikin ganni mun ha'du
(Toh ha'duwar XEEE da FAWAS kenan. Rahamat na gaisheku👯)
Shuru SAILUBAH tayi cikin mamakin ganin kofar RAMADAN akulle da'alamar xai
hukuntata ne kamar yanda yasa ban
Tayi kwafa xuciyarta nayi mata xafi tana kuma tsoranma kanta ciwo kamar yanda
lamarin ya saba xuwan mata.
Da kuka tayi part 'din momynsa tana tambayarta ina jaye.....
Momy Tayi Murmushi Tace lefin me kikamai haka.
Tace Wlhi Momy bawani abun xafi bane Amma yake san hukuntani kamar yanda ya saba.
danya samin ciwo😰
Khairat tayi dariya Tace Aunty LUUVAH wai yaushe xaku dena yin fa'dane ke da Ya
RAMADAN ya dena miki haka yana saki kuka
Ta harareta tare da kallan Momy Tace dan Allah Momy ina yake.....
By Hajju
[20/03, 17:09] 80k: [1:12PM, 21/11/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*👯
Part 46 to 50
Momy ta qarayin Murmushi Tace ban san inda yaje ba SAILUBAH. Amma ya shigo 'daxo
Cikin jin yunwa harna lalla6a shi yaci abinci daqar...
Goge hawayanta SAILUBAH tayi Tace toh bara naje waje ko Allah xaisa na gansa
Murmushi Momy tayi Tace toh Allah yasa ki ganshin
Khairat Tace nima futa xanyi Aunty mufuta tare
Sun fitoh harabar gidan ne SAILUBAH ta kalli Khairat Tace me Ya hanaki xuwa skull
yau
Tace kai Aunty LUUVAH. Ya RAMADAN yana neman har gitsaki amma ai yau ba ranar skull
bace
SAILUBAH tadafe kanta Tace na manta Wlhi
SAILUBAH tata6e baki Tatashi ta 'daukoma XEE ku'da 'dan nan ta dire a gabanta
Tace ayanda na rikice 'daxo. Kuma jiya na kasa yin bacci wanda har yanxu hankalina
atashe yake. Na kasa samun nutsuwa. Wlhi xan iya hakuri da Alhaji Aminu saboda
RAMADAN
Da na'dauka xan iya jurewa Ashe abin ba haka yake ba
RAMADAN ya shiga raina Sosai. Ayanxu nagane farin cikinsa shine nawa XEEE....
XEEE wacce tawaro dan ganin tulin ku'din da yake gabanta sam dena jin kalaman
SAILUBAH tayi dan tarikice da ganin ku'din Tace tab Amma wannan mutumin yaxo da
xafinsa. Kataqi 😳
SAILUBAH tajah numfashi Tace nayi kyauta da dubu 'dari biyu da ishirin
Yanxu ki ibi yanda yamiki. Sai muje gidan marayu in basu yanda natsara sai muje
wajan almajirai daga nan sai muje supermarket da biotic muyi siyayya ko
XEE ta washare baki Tace yayi yayi yayi SAILUBAH Gaskiya kin ha'du
Nan suka dinga tattaunawa har suka bar gidan
Ya kalleta da kyau. Kallo 'daya yayi mata ya gane yarinyar xatayi gaskiya. Xata
fa'deta komai 'dacinta yayi Murmushi Yace xaki soni Amma agidana
Ban ta6a soyayya ba sai akanki
A tunanina SAILUBAH tsayawa soyayya atiti rashin wayewa ne. Akan me xan xauna in
6ata mana lokaci gurin so bayan Auranki xanyi
Me xai hana muyi duk abinda xamuyi agidanmu
Sam baxan ta6a tsayawa yaudararki ba.
Kiyar dani baxan ta6a yarda in 6ata miki lokaci abanxa ba.
Ina sanki. Xakiji da'din Aurena. Kuma xaki soni fiye da yanda xaki so kanki
Ina rokwanki da Allah ki yarje min in mallakeki nan mah da sati biyu
SAILUBAH ta kallesa Tace ragewa mah kayi.
Yace aike 'dince akwai burkita mutum
Wlhi tunda na ganki nadena samun bacci Cikin kwanciyar hankali. Duk juyi idan nayi
tunaninki ne yake damuna.
Juya ido tayi Tace hmm Gaskiya sai nayi tunani dan bana san aikin gaggawa
Yace OK. 'daxoma mahaifina yake cemin xaixo ga Abbanki
Tace ba lefi Allah ya tabbatar da alkairi
Yace Ameen
XEEE na xaune kan kujera tana danna wayarta addu'a take Allah ya kawo mata sahibin
nata yanxun kamar yanda Yace mata....
Mama Tace naga kinyi wanka kinci ado kuma kin xauna badai fita xaki da'dayi ayammar
nan ba dai ko
Tace ba inda xani mamah kawai.....
Bata qarasa bah saiga KHAMIS yashigo harabar gidan nasu da motar shi
Daga window XEEE ta han goshi.
Mama Tace ga mutuminki KHAMIS
Tayi Murmushi cikin basarwa Tace bansan da xuwanshi bah dana fita shikenan yayi
rashin sa'a
Mamah Tace aikowa dai......
Daidai nan ya shigo falan ya durqusa ya gaida mamah Tace lafiya lau yaran kirki ina
ka baro RAMADAN da FAWAS yaran kirki
Yace Suna bayan layin nan wajan wani abokinmu nima inasan kar6ar wani abu ne gun
Aunty XEEE. Tace ayya Allah yayi muku albarka. Yace AmEEn. Tatashi tabar falan
KHAMIS yabi XEEE da kallo ka'dan Yace my Luv Kinsan baxan iya sakewa anan ba ko.
Pls temakeni muje mota kona samu na gaisheki cikin nutsuwata
Cikin sanyi Tace idan naqi fah
Yace sai in saka miki kuka
Tace toh 'danyi ka'dan inji ya kukanka yake
Tashi yayi yana murmushi Yace ba ruwana. Ina san kiyi bacci yau cikin kunciyar
hankali idan kuma nayi miki baxa kiyi shi cikin kwanciyar hankalin ba. ina jiranki
amota
Har ya kai 'kofah ya juyo.
Idan kintashi fitowa kifito min da dariyar ki me sani qara sanki. Yana fa'din haka
yaficce daga falan
XEEE tabishi da kallan so
Lalle 'da namiji bashi da kunya. Kuduba yanda KHAMIS ya rufe ido yayi fatali da
matsayin da yake bata ada na yayarsa yanxu ya juya shi ya koma na Masoyiya.
Tayi Murmushi Tace Allah na roqeka idan da aikairi soyayyata da wannan bawan naka
ina rokwanka kasa ya xama miji agareni ya soni fiye da San da nake masa
Idan ko ba alkairi acikin tafiyar Allah ka munsanya min da Wanda xai xama alkairi
agareni.
Ahaka tafitoh dama ya bu'de mata qofar sai kawai tashiga tarufe
Yace ina wini my Luv
lafiya lau
da fatan kinkai yammaci lafiya
lafiya qalau
Yace toh Madallah
Suka 'danyi shuru ka'dan can Tace ya kake jina aranka ne KHAMIS
Yace kamar yanda masoya sukeji aransu idan suka fa'da soyayya.
sai ya kama hannunta cikin yanayin damuwa Yace na sanki ina qaunarki my Luv dan
Allah ki riqeni amana.
Tace Kaine xaka riqeni amana
Bana san kishiya KHAMIS bana san in ganka da kowace mace ka temaken mu gina wata
rayuwa dagani sai kai
Yayi Murmushi Yace na miki alqawarin inhar kika iya dani ba wata mace da xata
mallakeni saike 'daya.
Tace Wlhi xan iya da kai Sosai masoyina
Yace toh Allah yasa
Can Tace wai ina RAMADAN ya shiga ne yau. Yace yata dama Aunty LUUVAH hankali ko
Tace sosai ma
Yace yana nan yana jinyar kansa. Ki share kawai. Dan kin san bayau suka saba ba.
Tace Hakka ne Amma fah kasan bana san damuwar SAILUBAH
Yace kar wani abu ya dameki. Kibari xan lalla6a yaje gareta
Tace dako ka kyauta.......
Qarfe Tara na dare SAILUBAH na tare da Abbanta itada Kakah yana gaya musu mahaifin
Aminun nata ne yaxo 'daxu shida qannansa kuma sun xanta yasamu gamshash shan
bayanai
Gashi yanxun sun bada kudin sadaki da nagani inaso da dai sauransu. Yaja nufashi
ka'dan kana yaci gaba da fa'din
Saiki shirya na basu KE nan da wata biyu xa'a 'daura muku Aure...........
[3:40PM, 21/11/2016] Rahamat Nalele 👯: SAILUBAH ta waro ido da dafe qirji Tace
kabasu ni
Yace eh dan sun nunamin yaran yana sanki Sosai kuma yana so ayi komai da wuri
danshi ba maxaunaci bane
SAILUBAH Tace jiya fah na fara ganinsa Abba akanme xan Auresa da wuri haka dan
Allah
Abba yajah numfashi Yace ko yau kuka gamu da juna tunda kika nunamin kina sanshi
kuma nayi bankice akansa nagane yaran kirkine dole Ki Auresa yanda na tsara
Tace haba Abba......
Yayi saurin katseta da fa'din kar kice min Komai. Dan baxan canja maganata ba.
SAILUBAH na kwance tana kuka dan Allah ya sani batasan ayi mata Aure yanxu
Can tafara kiran RAMADAN tana addu'ar Allah yasa ya kunna wayan nasa
Aiko bai kunna ba. Dan haka tayi firo da wayan takaicinta ya xaman mata biyu
Can Tatashi daniyar taqara xuwa gun Qanin nata......
Lokacin ko RAMADAN yana 'dakinsa shida FAWAS Suna gulmar wata yarinya da RAMADAN
'din ya burkitata yau
Fa'dama Fawas yake
Kasan kuna barin gurina 'daxu
Kawai saina fitoh dan shiga Jifatu.....
Basai kawai naci karo da ita ba.
Nace am sorry dan Allah bansan kin tawo bah
Ta kasa min magana
Niko na kwashe mata kayan nata na miqa mata ina qara bata hakuri
Kasan meys faru
FAWAS Yace aa
Yace dana kalli fuskarta sanda gabana ya fa'di
Bayanta Wasu manyane masu tsaranta
Kallo 'daya xaka musu Kasan ba imali atare dasu
'Daya daga cikinsu Yace kai Kasan wannan wacece da kayi kuskuran cin karo da ita.
Ayanda na lura suna da xafi
Sa6anin ita da takemin wani kallo me nuna alamun in ankare da ita
Ganin hakan yasa nayi Murmushi Nace Allah yajah da xamaninki gimbiya tauraruwa
kuskure nayi hakan baxata qara faruwa bah
Tace ayya karka damu me sunanka
Nace RAMADAN
Tace suna me da'di. Xansu kaban number naka dan ka iya kalamai idan naji sha'awar
hakan xan kiraka
Nace ba damuwa
'Daya daga cikinsu ya kar6i kayan ni kuma na kar6i number nata nakirata
Tayi Murmushi Tace saika jini
Nayi yaqe nace toh...
Muka rabu a haka
FAWAS Yace kyakkyawa CE ita 'din
RAMADAN yayi dariya Yace ina fa wani kyau mummuna da ita
Dana kalleta fah saida gabana yafa'di
FAWAS yayi dariya Yace saika shirya gaya mata kalamai idan ta kira ka
Kan yayi magana SAILUBAH tashigo 'dakin ahankali
Ta kallesa da muguwar harara.
Ya kafeta da ido Yace me yasa Ki kuka Auntyna
Cikin jin haushinsa Tace ban sani ba
Ina kashiga yau
Ya ta6e baki. Wani gu naje
Shine ban kai ka gaya min ba
Yace kinyi min lefi Auntyna ya xanyi in gaya miki.......
FAWAS Yace Barka da dare Aunty LUUVAH
Ta kallesa Sam batasan dashi bah Tace barka FAWAS ya Momynka Yace tana lafiya. Ya
fa'di hakan dasan ficcewa. yana me cewa kasameni a mota
RAMADAN Yace toh Amma fah sai naji da Auntyna
Yace nasan ai wannan dole ne
SAILUBAH Tace me yasa kake san jefani cikin damuwa ne RAMADAN
Kallanta yayi da qarasowa kusa da ita ya kama hanunta Yace ko wani ne yayi yun
qurin saki cikin damuwa saina 'dauki mummunan mataki akansa bare ni da Kaina
Ina San farin cikin ki Auntyna ki yarda dani.
Rai nane bai kwanta da wannan mumumin naki ba
Tace gashi har Abba ya basu ni wai nan da wata biyu biki da fashewa da kuka......
Arikice RAMADAN yasaki hannunta cikin tsoro Yace bar fa'da min dan Allah Auntyna
pls
Tace na rantse da Allah mana
Kuma gaskiya ni bana san Aure yanxu
Durqu sawa yayi a gabanta Yace innalillahi-wa'inna'ilaihir-raji'un
Haba Auntyna me yasa xaki min haka
Xan iya rasa rayuwata akan hakan. ki temaken dan Allah. Yafa'da kamar xai fashe
mata da kuka hankalinsa tashe
Cikin alamun damuwa ta durkusa. A gabansa cikin sanyi Tace me xaisa ka rasa
rayuwarka
Ya kalleta idan shi jajur Yace nima ban sani ba....
Ta kama fuskarshi cikin tashin hankali Tace ka gayamin dan Allah pls fa'damin.....
By Hajju
[20/03, 17:09] 80k: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir-rahmanurrahim*
*Part 51 to 55*
Shuru RAMADAN yayi dan yasan tunda FAWAS ya gigice saiya 'dorata akan hanya xaibar
qaunyan
KHAMIS na jinsu yayi shuru yace aransa Allah ya tsallakar dani saura ku
Ahaka sukaje gidan me gari sukayi gaisuwa dake yaran jikan gidanne
Duk da yake agidan mutuwa suke. Hakan bai hana mutanan qauyan xuwa ganinsu ba
Bayan sallar axahar kowa ya Washe suma suka shige mota dan xuwa gidansu HAMEEDA
Wani yaro suka samu me surutun tsiya. KHAMIS Yace Kasan gidansu wata budurwa
kyakkyawa haka
Tana da 'dan shekaru
Yaran ya 'daga kai yana kallan sama Cikin tunani Yace HAMEEDA wacce tayi bandaro.
RAMADAN Yace miye bandaro
Yaran ya kalli RAMADAN Yace yanxu bakasan miye bandaro ba
KHAMIS Yace eh miye
Yace bandaro shine abinda yaqi siyuwa a kasuwa
FAWAS Yace ita toh 'Yar tallece da taqi siyuwa
Yaran yayi dariya
Yace aa itafah ba wanda yake Santa ne dan sa'anninta duk sunyi Aure harda yara
itako tana gida ba mashin shini
Koda yake tana hannun wata qanwar babanta ne Innah Hansai
Sam bata santa aiki take sata Sosai ba qaramin gana mata axaba take bah........
RAMADAN Yace ya isa haka. Muje karakamu gunta ko itace wacce muke nema
Aiko yaran ya shiga motar tasu yanata murna yau gashi amota har suka iso gidansu
HAMEEDA
Yace toh ga gidan
FAWAS Yace jeka kira mana ita
Yace aiko naje innanta baxata bari ta fitoba
RAMADAN ya dafah yaran Yace akwai samari agidan
Yace eh mutum 'daya ne Alo
Yace OK yanxu dai ga wannan. Ya miqa mishi gudar 'dari biyu Yace ka sai littattafai
na makaranta kaji
Cikin farin ciki da murna Yace Nagode Yaya Allah yasaka da alkairi ya fitta daga
motar
Har yayi nisa ya dawo idanshi nakan RAMADAN Yace ko in shiga in yima innan tata
wayo sai in gayama HAMEEDAN xuwanku
FAWAS Yace Yauwa yaran kirki maxa jeka
Aiko ya shige gidan da gudu
A tsakar gidan yasamu HAMEEDA tana tanka'dan masara
Cikin farin ciki Yace HAMEEDA kinyi baqi 'yan gayu 'yan birrni
Tace suna ina Yace suna 'kofar gida
Tace bari toh nayi sauri naje kan innah ta dawo
Yace bata nanne
Tace eh taje gidan jummai
Yace kiyi sauri karsuyi xuciya Su tafi
Tace kafiye surutu Ya'u kace ina xuwa
Yace toh
Dama RAMADAN da KHAMIS Suna cikin mota ya yinda FAWAS ya fitoh ya jingida da motar
Aiko ya xuba mata ido
Taqarasa gareshi Tace wai da gaske kakeyi
Yayi Murmushi Yace eh kai. Ko baxaki soni bane da gaske in qara gaba
Tayi dariya Tace aitunda kai 'dan birnine baxan qika bah
Sai dai matsalar kai qaramin yaro ne.....
Ya katseta da fa'din. Naji ni qaramin yaro ne Amma xan iya riqe mace ai
Tace kai yanxu kasan me ake kira da Aure
Yace ban sani ba Amma inna aureki saiki sanar dani
Tace aini ba 'Yar iska bace
Yace oho nine 'dan iska
Tace nidai bance ba. kawai kashere batun son da kake min
Yace baxan share ba. Dan kinyi min tako ta ina
Tace me kake so kace
Ya wurga mata wani kallo nan take taji yayi mata wani bala'in kwarjini jikinta kuma
ya mutu cikin sauri ta sunkuyar da kanta qasa
Yayi murmushi dan ya hango yanayin data shi
Yace inaso ince ke kyakkyawace kuma abin San kowane 'da namiji
Da sauri ta kallesa Tace da gaske ni kyakkyawace
Kuma abin san kowane 'da namiji
Yace kwarai ma kuwa
Tace shege Iro 'dan iska Yace nafi kowa muni a qauyannan namu
FAWAS ya waro ido😳 kamar gaske Yace wanene shi haka in hukuntashi
Tace wani me satan kajin Mutane ne duk qauyannan sun sanshi Sam bashi da hali me
kyau
Dawai yana sona toh danace bana san shi shine ya gayamin baqaqen maganganu har
dacewa ni mummunace kuma wai ahaka xan dauwama agidan mu ba mashin shini bare inyi
Aure.
Ta qarashe da nuna damuwarta
FAWAS yajah numfashi Yace kalleni. Ahankali takallesa
Yaci gaba da fa'din. kina sona.
Ta lumshe da 'daga mai kai
Yayi Murmushi Yace kin yarda zaki Aunreni Ki nunamin me ake nufi da Aure
Ta rufe fuskarta Tace eh
Yace toh daga yau ko bananan Karki kuskura Ki kula wani saurayi dan ina da kishi
xan iya illata duk Wanda naxo nasamu dake
RAMADAN da KHAMIS suka fitoh daga motar suka sakama FAWAS dariya
RAMADAN Yace xakaci 'dan saluhu ko 'dan talatu tace maka ne ko Mene
By Hajju
Kunce kunaso ko ka'dan ne toh gashi nan 🙋🏼
[20/03, 17:09] 80k: [12:24PM, 22/11/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*👯
Part 46 to 50
Yayi Murmushi da janye hannunsa Yace in har baxaki iya takawar ba.
Ki fa'damin. Dan Wlhi 'daukarki baxai ban wahala ba. Kodako xanta yawo dakene ahaka
Tadaki girjinsa ka'dan cikin mutuwar jiki Tace saboda ka rainani danni macece.
Inxa'a duba na tabbata saina fika nauyi
Yace hmm toh naji muje in kaiki karki xube min ajiki dan naga baccin ya fara cin
qarfinki......
Tayi murmushi Tace kamar yanda kaji nace maka sunana shahuda. Ni 'yace ga Alhaji
iroro me harkar siyar da mai
Ni ka'daice 'yarsa muna xama a garin abuja unguwar maitama
Mahaifina cikakken me ku'dine bana wasa ba yana sanmu ni da mahaifiyata Sosai.
RAMADAN Yace daga kalamanki nagene ke me gaskiyace. Kuma baki so. ki yaudari mutum
a har karki dashi.
naji ina sanki dan inasan mutum mai wannan halin
Tayi dariya Tace Nagode sai mun sake waya ka gayamin kai ko waye gudnyt
Yace ok gudnyt
👯👯👯👯👯👯👯
*SAMAREEN BANAH*
👯👯👯👯👯👯👯
*tasu salan soyayyar*
?👯👯👯👯👯👯👯
[2:49PM, 22/11/2016] Rahamat Nalele 👯: Haka rayuwar tasu tacigaba da tafiya yau da
da'di gobe sa6anin haka
Soyayya me qarfice tashiga tsakanin KHAMIS da XEE
Ba Wanda bai sani ba har acikin makarantarsu
Mutum biyu ne basu sani bah. Sune iyayan XEE dana KHAMIS
Sam bata canja xali ba tsakanin SAILUBAH da XEE wajan qin karatu
Xa gwan qasa ya dinga mata tawajan Abbanta ya nuna mishi yana bala'in Santa ayi
Komai da wuri
Yana xuwa duk sati ya ganta ya kuma bata ku'di me tarin yawa
Ana saura sati biyu bikinne ya bata kyautar wata lafiyayyiyar mota Amma ta biyo ta
hannun Abbanta ne wanda daqer ya kar6e a cewarshi ai Auranta xaiyi yabari ayi Auran
ya bata
Ya nace dai saida Abbanta ya kar6a
Eh motar tatafi da hankalinta SAILUBAH Sosai
Amma ganin RAMADAN duk ya rikice mata shiyasata qin nuna farin Cikin nata
Dan yanxu ya canja mata gabaki 'daya...
Ita gani takeyi kamar haushinta yakeji
Yanxu haka xaune take ita da qawayanta wata tana mata gyaran jiki dan ginsu Su
dilke
jiya sukayi walima.
XEE Tace ikwan Allah kenan SAILUBAH. Ashe xaki rigani Aure.
Tace hmm Wlhi XEEE xuciyata xafi takemun kwata kwata na tsani Auran nan
Wata khamsa'u Tace meyasa
Tace hmm tunda RAMADAN ya nunamin baya so naji nima bana so
XEEE Tace na lura har ramewa kukayi ke dashi
Wata ummi takalli XEE Tace keko sabon da sukayi da juna na wasa ne
SAILUBAH Tace ni yanxu damuwa ta ya qaurace min kwata kwata
Na ne meshi awaya na rasa
Rabona dashi yau kwana hu'du kenan Wlhi xaxxa6in nan da nakeji duk na rashinsa ne
Nasan ina ganinsa Komai xaixo min da Sauqi
Wata humaira Tace hmm ki kwantar da hankalinki inda RAMADAN ne qila anjima kigansa
dan nasan duk inda yake yafiki shiga tashin hankali
SAILUBAH tayi tagumi
Anisa Tace nidai kuna burgeni yanda kuke San junanan nankun nan
XEE Tace 'dan iska KHAMIS yaqi gayamin inda yake
SAILUBAH Tace hmm xan ha'du da shine shima
Washe gari aka kawo kayan Sa Lalle da akwatuna goma Sha biyu reras
'Yan unguwa sai xuwa gani suke dan kayane nagani na fa'da
Anan ne fah tsoro ya kama SAILUBAH dan Alhaji Aminu ba qaramin ku'di ya kashe ba
Qarfe goma sha 'daya na safe SAILUBAH Tatashi hankalin XEE harda kuka ita dai suje
sunemo RAMADAN
Kamar yanda KHAMIS ya fa'dama XEE Suna kan hanyarsu ta xuwa takai. Toh haka abin
yake da gaske
FAWAS dake tuqasu ya kalli KHAMIS Yace Gaskiya soyayyarka da Aunty XEE tana tafiya
dani
Yace hmm ina Santa da yawa FAWAS
FAWAS yayi dariya Yace naji tana maganar Aunty LUUVAH
Yace eh. Yana me kallan RAMADAN dake karanta wata jarida
KHAMIS ya 'dora da. Toh 'dan iska hankalinka ya kwanta tunda ka sakatah kuka akanka
Katemaketa ka bu'de wayanka dan Allah danni ta Masoyiyata nakeyi
Dan nabata tabbacin xan saka ka bu'de wayanka
RAMADAN yajah tsaki Yace karka dameni dan Allah.
Yace Wlhi saika bu'de wayanka ko'dan Aunty XEE ya fa'da da 'dauko wayar
tasa..........
Kan RAMADAN yayi magana FAWAS yajah wani furgitaccan burki Wanda ya basu tsoro
Yana sauke numfashi sama sama idanshi na kan mudubi yana kallan bayansa
Cikin maseefa KHAMIS Yace wai kai wane irin 'dan iska ne xakaje ka kashemu dan
iskanci
Ni ban gaji da rayuwa ba dan ban ajiye 'ya'yana ba ehee
RAMADAN yayi Murmushin dole dan rabansa da Murmushi yafi sati uku
Yace ka lura man KHAMIS yagano wata xa6in shi ce
Kut😳kut😳kut Yace
Saka makwan ganin wata xanka'daxiiyar budurwa wacce take sheqa gudu tamkar xata
tashi sama
Ba gyale ajikinta
Wata fanka ceciyar rigace tasa sai xaninta da kallabi
Sai wani siririn gyale dataci 'dam mara dashi
Kallo 'daya xaka mata kagano Abu biyu
Tana da kyau na bam mamaki. tare da kuma matsanancin damuwa.
Yanda take gudun Komai na jikinta na rawa shi yasa FAWAS rufe idansa🙈 da hannu
biyu
KHAMIS yajah numfashi Yace eh Lalle yau Allah ya kawo maka xa6inka
Ganin takusa xuwa garesu yasa RAMADAN fitta daga motar yasha gabanta
Ta kallesa da wata muguwar harara Tace da Allah matsamin sauri nake
Yace tayaya ma xa'ayi im matsa miki bayan kina sheqa gudu haka
Tace toh ina ruwanka hakan na saba kuma ba Wanda ya ta6a tareni
Yace ko
Tace gaskiya man
Yace eh ba shakka dama haka kuke rayuwarku Ku 'yan qauye
HAMEEDA ta qare mishi kallo tun daga sama har qasa tabi motarsu da kallo
Kana ta dawo da kallanta kansa tatabbatar ba 'yan qauyansu bane
Allah yayota dasan 'yan burni
Da gaske RAMADAN yayi mata MASEEFAR kyau
Ita duk a iya gane gananta bata ta6a ganin namiji Wanda Komai ya masa dai dai kamar
RAMADAN ba
Atake tayi tunanin shi balarabe ne taji tana san shi Amma baxatace ga irin son
dataji ba
Ya 'daga mata gira. Nan tadawo daga tunanin
Tace gaka qaramin yaro Amma sai qarfin halin tare wacce ta girmeka
RAMADAN yaji kamar ya tsinka mata mari dan duk duniya ba wacce xatace mishi qaramin
yaro ya share sai Auntynsa
Yayi murmushin yake Cikin 'daga murya yace FAWAS kafito Wlhi. tunkan na tsinka mata
mata mari.
KHAMIS yayi dariya Yace aisai ka fitta Kasan ka'dan da aikinsa ya falleta da
marin...
FAWAS ya fito daga motar Yace sannu ko
Ta kallesa ka'dan. Gabanta yafa'di dan ganin wani kyakkyawan kuma
Tace yauwa
Ta maida kallanta ga RAMADAN Tace waxa ka mara
Yiyi mata wani mugun kallo
Yace ban dake akwai wata ne anan
Xatayi magana Yace Kinsan Allah kika qara bina da qaramin yaro Wlhi saina miki mari
biyu ajere.
Haba da Allah Daga ganina xaki kirani da qaramin yaro ke ba qaramar yarinyar bace
Tace kut😳 shekarata ashirin da hu'du ko kaffara baxanyi ba na girmeku karka qara
kirana da qaramar yarinya
RAMADAN yayi Murmushi dan ganin yarinyar 'Yar ayice
Yace oho Ashe ba da'di
Tajah tsaki xata wucce.....
Yace 'dan jini ka'dan mana
Tace lafiya
Yace atunaninki lafiyace xatasa na tsaidake
Yanuna FAWAS Yace sanki yakeyi da Aure dafatan xaki soshi
Tayi dariya Tace toh xan baka dama Amma sai nayi shawara da xuciyata
Tafa'da dasan barin gun
RAMADAN Yace da kata malama
Tace muryarka tana d.......
Kanta qarasa ya wurga mata wani mugun kallon da ya hanata qarasawa
Yace Ki fa'da mana gidanku
Itama harararshi tayi ta wucce shi
FAWAS Yace dan Allah Karki tafi da gudu. Tace naji Qanina tabar gun da sauri
Kuma daidai nan wayar RAMADAN ta fara ringing
RAMADAN ya kalli KHAMIS Yace wayace ka kunna min waya dan Allah
KHAMIS Yace Aunty LUUVAH CE dai
Ahankali ya kar6i wayan da 'dauka
Da kuka SAILUBAH Tace meyasa kakemin haka RAMADAN
Da sanyin murya Yace menayi Auntyna
Tace so kake ka kasheni
Yace idan na kasheki inyi rayuwa dawa......
By Hajju
Ku huta 'yan hanuna🙋🏼
[20/03, 17:09] 80k: [7:39PM, 24/11/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*
*Bismillahir-rahmanurrahim*
*PART 56 to 60*
Yace ai tunda yaqi yarda naje ga Auntyna Wlhi saina guma masa.
KHAMIS ya qara yin dariya
Da ace HAMEEDA tasan FAWAS toko da tagane yanacin 'dan malelanta ne tamkar xaiyi
kuka....
Cokali hu'du yayi yana tunanin inya qara na biyar toko ba abinda xai hanashi yin
amai
Ya kalleta ka'dan. Idanta nakansa. Yayi Murmushi Yace YAYATA.....
Da sauri ta sakar mai murmushi Tace na'am
Yace na koshi
Nan take annurin fuskarta ya 'dauke Tace meyasa ka koshi bayan.......
Saurin katseta yayi dan ganin annurin nata ya 'dauke
Yace wasa nake miki. Da xaki 'daure min fuskar nan taki me kyawun kallo.
Ta saki fuskar tata tare da rufe fuskar da hannu Tace har naji da'di Wlhi.
Ganin da gaske tana Cikin jin da'di shiyasa FAWAS daurewa ya dinga cin 'dan
malelannan har ya cinye
Da sauri Tace in qaro maka
Ya kalleta cikin marairai cewa Yace aa
Tace karka damu akwai da yawa
Ya qura mata ido yana kissima abubuwa da dama aransa akanta
RAMADAN ya kalli KHAMIS Yace Wlhi qiris FAWAS yake jira ya saki amai
KHAMIS Yace wlhi kuwa gashi ta kasa ganewa
Yace bara naje na 'dora mishi da nawa
Kan KHAMIS yayi magana RAMADAN ya fito daga mota ya nufusu da Murmushi Yace dan
Allah ki daure in akwai da yawa Ki qaro masa dan dama baici abincin rana ba
Haka kawai ya tsinci kansa da qinci. Ashe xaixo ne ya tarar dana masoyiyarsa ne.
Baki lura da yanda ya cinye bah pls yi sauri ki qaro masa mana
FAWAS ya maida kallansa qasa da dafe kansa.
HAMEEDA Tatashi da murna Tace aikuwa nayi da yawa
Daqar FAWAS Yace ka'dan xaki qaro pls.....
Bata jishi ba tayi Cikin gidan nasu da sauri burinta yayi ya gama kar innah ta dawo
Dama tana barin gun RAMADAN ya koma mota. FAWAS yabishi da kallan ramuko
Tayi shuru. Candai ta kar6a Tace Nagode Allah yasaka. Amma miye sana'arka.
Yace ina skull yanxu ina karantar kasuwanci ma'ana nan da Wasu 'Yan shekaru xan
xama cikakken 'dan Kasuwa
Tace shima dama kasuwancin karantarsa akeyi Yace eh ai ba abinda ba'a karantarsa
Tace tab ni ban San kasuwancin karantar sa ake ba.
Yace hmm kina karatu kuwa
Tace ban San ilimin boko ba. Nadai sauke alqur'ani da sanin Wasu takaddun musulunci
irinsu nahahu kawaqidi adaf hadis da dai sauransu
Yace eh lalle kice da malama nake
Ta kallesa cikin sanyi Tace nasamu wannan iliminne agun BABANA da'ace iyayena sun
mutu tun ina yarinya na tabbata baxan samu komai bah
Yayi Murmushi Yace daga nan shikenan kin xama tawa saiki koyar sani yanda Aure yake
ko.
Ta dariya da rufe fuska cikin shagwa6a da ta6ara Tace toh yaushe xaka dawo
Ya kwai kwa yi muryarta wajan cewa jibi idan kinaso
Ta qarayin dariya danjin yanda ya kwaikwayeta. Tace kaga banaso
Yace toh nadena 'dan bu'demin fuskar ka'dan ko na sami bacci cikin nutsuwa yau.
Tunda Allah yasa nayi gamu da kyakkyawa wacce tafi kyawawa kyau
Ta 'dauke hannunta daga fuskar tata ta kallesa damai fari da ido tana 'daga mai
gira irin tasu salan soyayyar ta qauyawa.......
Amai yakeji saboda ba qaramin cika cikin sa yayi bah. xuciyarshi tashi take sobada
bai saba da cimar data bashi ba. Burinshi takauce mata ya amayar da shi ko yasamu
kanciyar hankali
Yayi Murmushi dan ba qaramin burgeshi tayi ba. damai fari da idan da tayi
Ya tashi yana cewa wannan fari da ido haka. aisai kisa in sume a axaune
Ta rufe fuskarta Tace Allah
Yace kunyarki na burgeni
Tayimai shuru
Yayi Murmushi da cije le6ansa.
Ni xan tafi saikin ganni jibin
Tace kamar karka tafi Wlhi
Ya 'daga mata gira Yace idan bakyaso ai sai in tsaya har Innah tadawo immata
gaisuwa
Ta waro ido da cewa tab kace tarabani dakai kenan
Yace aini bamai rabumu sai Allah Ki kulamin da kanki pls bana San wani abu ya
sameki
Ta 'dagamai kai cikin Murmushi
Ya shige motar tasu
Ta 'dagamai hannu alamar bye bye
Shiko ya sakar mata wani kallo me kashe jiki
Nan ta'dauke hannunta cikin sanyi dan kallan ya shigeta
Suna fitta daga qauyan. FAWAS Yace pls bani minti biyu KHAMIS
Ba musu KHAMIS ya tsaya da motar agefan titi
Sosai FAWAS yadinga sharara amai kamar xai amayar da hanjin cikinsa
Yana gamawa RAMADAN ya bashi ruwan gora ya wanke bakinsa
Kana KHAMIS yajah motar
By hajju
Barka da dare masoyana
[20/03, 17:09] 80k: [9:34PM, 25/11/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
👯 *BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir-rahmanurrahim*
*PART 61 to 65*👯
Tana kwance a gado XEE na gefanta ga qawayanta nan sai hira suke
RAMADAN ya shigo 'dakin
XEE ta 6allamai harara Tace ban ta6a ganin qani mesa Auntyn shi cikin damuwa da
tashin hankali ba kamarka RAMADAN.......
Da sauri ya katseta da cewa haba Aunty XEE kidena haka. Yanxu xakisa taqara jin
haushina bayan KHAMIS ne Babban me lefi dayaqi gaya mata inda nake
Tace eh Gaskiya. dake gaka gata ai dole ka kanemi kare kanka. Karka wani saka
KHAMIS dan bashi da lefi
Ya kalleta da Murmushi Yace toh Naji bashi da lefi
Ya maida kallansa ga Auntyn tashi wacce ta kafeshi da ido tun shigowarshi
Yace Barka da yammaci my Aunty
Ta sauke ajiyar xuciya Tace me yasaka ramewa haka
Ya tashi yana cewa tunani da tashin hankali
Tashi itama tayi Tace muje
Ba musu suka jero tare har xuwa gidansu part 'dinsa
Ta xauna gefan gado shi kuma yana kan kujerar da take fuskantarta
Tace wane tunanine haka da tashin hankali yasaka ramewa
Ya kalleta ka'dan Yace kema ai kin rame Sosai
Tace kaban amsata
Yace hmm tunaninki Auntyna mana....
Wai a tunaninki rabuwa dake xai barni na xauna lafiya ne.
Hmm Sam hakan baxai yuhuba
Dan daga ranar da kika bar gidanku xuwa gidan wani toh Ki tabbatar baxan qara samun
kwanciyar hankali arayuwata bah
Saban danayi dake ya kai matsayin da in tunaninki yayimin yawa xan iya rasa
rayuwata........
Nayi addu'ar istahara nayi Sallah akan Allah ya bani haske akan lamarinki
dashi.....
nagani Cikin mafarkina Auran shi nadama ne agareki
Ni fah baxan 6oye miki ba. In bake baxan iya rayuwa sak kamar yanda aka sanni ba
Kuka take Sosai yana qara jefah mata qiyayyar Alhaji Aminu
Can dai dayaga kukan yayi yawa kuma yana maseefar damun xuciyarshi sai ya matso
kusa da ita ya kama hannunta
Yace toh kiyi shuru kidena kukan nan tunda kina sanshi baxan qara kushe miki shiba
tunda ranki na 6aci kiyi hakuri
Ki dena bana so. inba so kike Ki hanani bacci ba. Yafa'di hakan da leqa fuskarta
cikin kusanci dasan qara hargitsa mata kwanya
Aiko ta shaqa
Dan yanda yayi kusanci da ita ka'dan ya rage bakinsu ya ha'du dana juna
Ganin yasami abinda yakeso dan jikinta ya mutu mu'dus. qiris take jira ta xubemai
ajiki. Shiyasa ya 'dan janye kansa ka'dan daga gareta tare da jifanta da wani kallo
Wanda atake yasan ya gama kunce mata Komai.
Ta lumshe idanta tare da dafe kanta Tace bana sanshi bana sanshi
Na da'de dasanin Kaine kwanciyar hankalina RAMADAN
Ban San me yake damuna ba.
Kina sanshi tunda kike min kuka akansa. Kuma aida bakya sanshi ko kusa baxaji
sha'awar kar6ar abin hannunsa bah. RAMADAN Ya fa'da dasan qara harxuqa xuciyarta
Aiko cikin fusata Tace wai kai wane irin 'dan iskane
Nace bana sanshi bana sanshi bana sanshi Amma sai qara Sa xuciyata xafi kakeyi tun
kwanaki can da suka wucce nayi dana sanin sanin shi
Dan narigada na auna na garo ba abinda yake tadamin hankali kamar rashinka kusa
dani
Dan haka cikin yi mata baxata ya rungumeta da kashe murya irinta Wanda yake yin
kuka
Yace kimin rai auntyna kiyafemin nasan narabu dake kenan yau har abada. baxan ta6a
yafema kaina bah idan har xuciyarki batayi sanyi munyi bankwana cikin farin ciki
bah.......
Tundaga tsayar kan SAILUBAH taji wani abu na yawo ajikinta Wanda yasa ta rikice
Komai na jikinta ya tsaya cak.....
By Hajju
Asuba ta gari
[9:35PM, 25/11/2016] Rahamat Nalele 👯: *R*
[20/03, 17:09] 80k: [12:55PM, 26/11/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir-rahmanurrahim*
*PART 66 to 70*
XEE tatareshi a farfajiyar gidan Tace shigowarku 'daxo naga SAILUBAH daga dukkan
alamu tayi kuka
Yanxu kuma kafitoh kana Murmushi wai me yasa Sam bakaso kaganta cikin kwanciyar
hankaline
Yace Aunty XEE kenan. Wlhi duk duniya bawanda yafini San ganin kwanciyar hankalinta
Wannan dare duk ya rikita mutane hu'du 4 idan ka cire XEE da KHAMIS Wanda yanxu
yake tare da ita kusan qarfe tare da rabi na dare.
*Luv*💔 suke xugawa tamkar xasu ha'diye junansu
Sam XEE manta kanta take idan tana tare da KHAMIS
Ya kalleta cikin wani yanayi Yace my Luv
Tace na'am sweetheart
Yace dama ace yanda muke xaunan nan matsayin ma'aurata muke
Tace lokacin na xuwa MENI
Yace kinga mun kusa gama skull ya kamata iyayanmu Susan da xaman soyayyarmu.
Tace mu qara lokaci ka'dan sweetheart
Yace aa fah. nagaji da mafarkan ganinki da yarana inasan inga hakan axahiri
Ta kallesa Tace xaka fara ko
Yace kona fara yanxu dai baxai tabbata ba. Tunda masu ha'dawan basusan da xaman
soyayyarmu bah
( *XEE da KHAMIS kenan*)
*Sa6anin SAILUBAH*
Data kwana kuka da damuwar aranta
Ko wane juyi idan tayi ganinta take rungume da RAMADAN tana shaqar qamshinsa
Wannan abu shiyafi damun xuciyarta
Sam yau bataji Tatashi tayi lafula ba.
*FAWAS ko*
Rasa nutsuwarshi yayi gabaki 'daya
HAMEEDA ta rikitashi
Ta hanashi bacci Sam
Duk juyin da xaiyi hotan fuskarta yake gani tare da jin muryarta tana mishi kurwa
akunne
Haka kawai nima Rahamat na tsinci kaina da fa'duwar gaba Ganin yanda mutane suka
cika layinsu SAILUBAH dan 'daurin Aure
Na kalli RAMADAN Wanda yayi kyau cikin shigar wani yadi me ruwan madara
Yayi kyau sai Qamshi yake
Haka FAWAS da KHAMIS ma dan anko sukayi
Duk inda kakai da hassadarka saikace yes wa'yannan sun dace da'a kirasu da
*~```SAMAREEN BANAH```~*
SAILUBAH na kwance akan cinyar XEE xaxxa6i na cafkarta damuwarta taji ance amfasa
'daurin Auran
Dan 'daxo da Asuba tasa Abbanta tayi agaba kan yayi hakuri karya Aura mata Alhaji
Aminu
Sai kawai ya kalleta Yace tatashi tabashi guri
Toh shine take cikin wasi-wasi xai Aura mata shine ko aa
By Hajju 👯:
R🅰HAⓂAT
[20/03, 17:09] 80k: [6:42PM, 27/11/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir-rahmanurrahim*
SAILUBAH Bata samu kanta bah har wajan qarfe biyar na yamma
Lokacin 'yan Uwa da abokan axxiqi suke ta shirin kaita gidan mijinta
Fa'di Take XEE ina RAMADAN. XEE Tace ya shigo 'daxu baki farfa'do ba
Tace xan iya ganinshi yanxu
Tace kai daka mar wiya
Lumshe ido tayi batare da Tace Komai ba
Acikin yamman nan suka 'dauki hanyar Abujah. Basu sami kansu sai qarfe tara na
dare
👯👯👯👯👯
SAMAREEN BANAH 👯
👯👯👯👯👯
Wai meyasa tunda aka 'daura Auran nan nata baka mata fatan alkairi ne. Cewar FAWAS
KHAMIS Yace bar 'dan iska insha Allah baxata fitto ba
RAMADAN yayi dariya Yace kamar yanda nasaba gaya muku xance ya tabbata haka wannan
mah baxai Sha ruwa bah
FAWAS Yace hmm ni inata nemanta awaya na rasata
KHAMIS Yace Wlhi nima 'daxuma Aunty XEE take gayamin itama ta rasata a waya.
RAMADAN yayi shuru can ya ta6e baki Yace Allah yasa ba aiki ya fara mata yanxu ba
Ya maida kallanshi ga FAWAS daya saki baki yana kallansa Yace HAMEEDA na jiran
xuwanka fah. Kuma lokaci na wuccewa pls muje banaso dare yayi mana scan
FAWAS yajah numfashi Yace Wlhi RAMADAN kana bani tsoro wani xubin
KHAMIS Yace aha
Na xata baxa kace bah.....
Ta hanaka bacci na kwana 'daya idan kabari yauma ta hanaka Wlhi gobe da Asuba
xakayi qauyan takai
RAMADAN ya fa'da hakan dasan kawar da hiran da Murmushi akan fuskarsa
FAWAS Yace kamar ko kasani. Yarinya kamar Aljana tabi ta rikitani ta hanani sukuni
KHAMIS yayi murmushi dan tuno da 'dan malelan data bashi Yace kace yauma xaka qara
cin wannan abun
Gaban FAWAS ya fa'di cikin sanyi Yace eh. in har tace sainaci Kasan ba abinda xai
hanani ci
RAMADAN ya tada mota suka nufi supermarket siyayya Sosai FAWAS yayi mata
Sukayi biotic ananma yasiya mata Kaya danginsu dogayan riguna da riga da siket
Ya siya mata qaramar waya dasa mata layi
Kana suka nufi qauyan takai
HAMEEDA na ixa wutta tana hawaye wani yaro yashigo gidan nasu cikin ra'da yake CE
mata tayi ba'ki Wasu kyawawa masu ku'di
Da sauri tasaki Murmushi Tace kaje kace FAWAS ne
Cikin san'da yaran yaje gasu RAMADAN Yace wai FAWAS ne
FAWAS ya fitoh daga motar Yace kace mata eh shine
FAWAS yaba yaran ku'di ya maida kallansa kanta Yace naxata baxaki fito ba gabana
yanata fa'duwa sai kuma gaki
Tayi Murmushi Tace Barka da ranah
Yace Barka dai ya gida.
Tace lafiya lau
Yace toh Madallah
Tace ai baxanqi fitowa bah
Yanxu hakama innah bacci takeyi shine na lalla6a na fitoh naganka kona sami sanyi
araina
Da Murmushi FAWAS ya kalleta Yace na 'dauka ni ka'dai na rasa nutsuwata Ashe harda
ke
Tace kai😳
Hmm dama haka masoya sukeji idan sun fa'da soyayya
Yace wani abu ne YAYATA.......
KHAMIS da suke Cikin mota shida RAMADAN Yace wannan 'Yar surutu CE
RAMADAN Yace nalura kam. idan suka cigaba ko kisa tayi xata gaya masa Komai.
Saurara kaji cewa xatayi takasa bacci ranar daya tafi ya barta
KHAMIS yayi dariya Yace da tayi hakuri shi xai fara gaya mata
RAMADAN Yace kaidai jisu ka'dan kaji
Tace daka tafi ban shiga gida ba har sanda Innah tadawo
Har mari nasha wajan shagalewa da tunaninka
Ata qaice wannan ranar ban iyayin bacci bah. Tunaninka yadami xuciyata
FAWAS ya qura mata ido Yace yayi daidai hakan dan nima hakance ta faru dani
Yakai hannun shi faskarta yana shafawa ahankali yaciga da fa'din Wlhi da badan
Innah bace ta mareki da anyi 'dan qaramin yaqi akan hakan
Kanta tayi magana Innah ta leqo idanta ko ya sauke a fuskar HAMEEDA Wanda har
lokacin FAWAS bai cire hannunsa bah
Innah ta doka salati tana fa'din mexan gani haka ni Hansai
FAWAS ya janye hannunsu
Cikin tsoro da tashin hankali HAMEEDA Tace Wlhi innah baiyi min komai bah
Kuraje yagani afuskar tawa shine yake ta6awa dan yaban magani
FAWAS yabi HAMEEDA da kallo dan jin yanda ta tsara magana cikin sakwanni qalilan
Ta kallesa cikin shagwa6e fuska tacigaba da fa'din. Ina hakane....
Da sauri FAWAS 'daga mata
Taqara shagwa6e fuskar hawaye nasan xubo mata Tace kayi magana mana
Cikin wani yanayi FAWAS ya kalli Innah Yace xan iya rantse miki da Allah abinda
tafa'da hakane
Innah ta gyara tsayuwa
Tace Naji
Ku suwaye
RAMADAN yafitoh Yace aikomu akayi
Tace Waye ya aiko ku
Yace gwamnati CE
Innah tawaro ido😳 Tace miye ha'dinmu da gwamnati
Yace kayane taturo mu mu rabama mutane. Toh acikin wa'yanda xamu rabawa hadda
HAMEEDA aciki
Yanuna FAWAS
Wannan yanada sani akan quraje shine yake tambayarta ya akayi quraje suka 6ata mata
fuska
Innah tasaki ranta Tace aiho toh ina kayan
FAWAS yabu'de motar suka ibo kayan da suka siyama HAMEEDA suka dire mata agaba
Tabi kayan da kallo Tace Naga harda kayan 'yan iska
KHAMIS ya fito yana cewa eh haka oganmu na 'yan sanda yace tasasu haka ba'a yarda
wani yasa mata ba. Duk Wanda yasa mata xai turo 'yan sanda Su kamashi
Cikin Innah Hansai ya 'doru ruwa cikin sanyi da tsoro Tace insha Allahu bamai Sa
mata
Ganin tsoran data shiga yasa RAMADAN qarawa da cewa yana nuna FAWAS yace wannan
'dan shugaban 'yan sanda ne
Yana San HAMEEDA dafatan Allah yasa Ki amince ta aureshi
Da sauri Innah Tace Xanyi magana da ita wannan aiba matsala bane
Yanda jikinta yake rawa shiyasa KHAMIS yin dariya cikin ransa yake fa'din 'dan
qauye da tsoran 'dan sanda
👯👯
FAWAS yayi Murmushi yama rasa mexaice mata. Wlhi shi mamaki ma take bashi
Yace nima ina sanki Sosai da ace kina tare dani yanxu dana nuna miki *WATA RAYUWA*.
RAMADAN ya kalleshi Yace 'dan iska duk abinka saika 'daga mah wannan qafa
FAWAS ya shareshi yaci gaba da fa'da mata kalamai masu kashe jiki
SAILUBAH tanemi wayanta sama ko qasa ta rasa. Ita kuma da kanta ta ajiyeta Bayan
tafiyarsu XEE
Tafitoh falan nata taga wata 'yar budurwa kyakkyawa haka tana kwashe kayan abincin
dasu XEE suka 6ata Tace ke bakiga waya ba da Allah anan gun
Tace aa Saidai yanxu Alhaji ya 'dauki wata akan kujera ya futa
SAILUBAH tayi shuru wato ya shigo ya fitta bai nemeta ba Tace Samsung ko
Tace tabbas ita nagani ahannunsa
Tace ke miye aikinki agidannan Tace jiya aka kawoni wai xandinga temaka miki da
aiki
A ina kike
Tace suleja
Owkie SAILUBAH Tace tashige bet room.
Dare yayi SAILUBAH taji ango baixo gareta ba. Har safiya
Abin fah yabata mamaki yanda taga ta'dau sati ba Ango ba alamarsa
Saidai taci abinci tayi wanka tayi kallo damuwa da kewar gida da RAMADAN 'dinta ya
dameta
Taxo daf da shiga falan gun wani murtuqeqen mutum Yace sannu Hajjiya wani abu kike
buqata.......
Kan tayi magana sai taga wani qatan mutumin baqi qirin dashi yaxo ya wucce da sauri
da kan yarinyar da taga Alhaji Aminun ya shigo da ita. Wato anfille mata kai ga
jini nan kaca kaca ahannun mutumin Sam bai lura da itaba yashigesu ya shiga wani
'daki da kan yarinyar ba gangar jiki.........
Wannan qatan mutumin ya'dauketa kamar wata baby ya kaita shashinta. Kana yaje
yagama ogansu Alhaji Aminun Hajjiya fah taga kisan da yayi
Cikin maseefa Alhaji Aminun yace ya'ayi kabarta taxo tagani
Yace nima ganinta kawai nayi
Yace yanxu tana ina
Yace nakaita shashinta
Ya tashi ya nufi gunta cikin xafin rai
Aminu ganin irin ku'din da ogan nasa yake sake masa shi yasashi cemai yanaso ya
xama kamarshi
Ogan yayi Murmushi Yace xaka iya kisa kuma kasha jini kuma kullun akayi amfani da
yara da manya ishirin arana
Aminu Yace eh kai. inhar xan xama me ku'di kamarka
Ogan yayi Murmushi Yace toh daga yau kaxama Alhaji Aminu
Sai hankalinsa ya tashi akanta yaji yana San ya mallaketa a matsayin mata
Gashi shi ba iyayene dashi bah
Nan yasa amasa bincike akanta da kuma Abbanta
Nan aka bashi tabbacin Abbanta yayi ku'da kuma ita tana da burin Auran me ku'di
Yace toh acikin wa'yanda sukayi aiki a qarqashin Abban nata da can'din anemo masa
'daya☝🏻wanda yake cikin talauci yaxama uba agaresa dan maganar gaskiya xai Auri
SAILUBAH dan tayi mishi tako ta'ina
Nan suka samo masa Malam saluhu Wanda Abban SAILUBAH yayarda da gaskiyanshi da
Amanarsa
Alhaji Aminu ya cikasa da ku'di da siya mishi qaramin gida da xuba mishi 'danyakun
abinci kala kala
Sannan ya gabatar mishi da 'kudirinshi nasan mallakar SAILUBAH gashi bashi da iyaye
yanaso ya xama uba agareshi
Sam Malam Saluhu bai wani yi mishi gaddama ba. ya amince da 'kudirinsa tunda yanxu
rayuwar taxama babu🙅🏼. marasa tsoran Allah komai akace suyi yi suke dan kare
kansu daga yunwa.
To yanda akayi kenan Alhaji Aminu yasamu SAILUBAH batare da wata matsala ba
_______________
Da xafin rai yashiga falan SAILUBAN......
Saidai ganinta kwance kan kujera asume shiyasa shi 'dauke fushin nashi ya xauna daf
da ita yana qare mata kallo musamman kyakkyawar fuskarta.
Ya xubama breast 'dinta ido ya lumshe idon dan bashi da damar amfani da mace wannan
dokace a kwungiyarsa
Ya dinga bin kowane lungu da saqo na jikinta da kallo
Maseefar sonta na qara mamaye masa xuciyarsa. Yaji aduniya ba abinda yake so
kamarta.
Yayi murmushi Yace abayyane shegiya kintara abubuwan more rayuwa da yawa. Wannan
duk Wanda yanemi hutawa dake xai more Sosai 😍
.
[6:43PM, 27/11/2016] Rahamat Nalele 👯: Ya 'dauki ruwa ya watsa mata...
Ta farfa'do ta xubamai ido
Nan take ta tuno meya faru
Da sauri tatashi ta kallesa sama da qasa xatayi magana.Yace dakata. Nasan me xakice
bara nabaki haske
Ni 'dan ma'digo ne kuma 'dan kwungiya me kisa nasan Kinga kisan da nayi
Karki tada hankalinki akan hakan pls
Cukumeshi SAILUBAH tayi cikin maseefa Tace kai ka Isa ka rainamin hankali Wlhi kayi
nadamar sanina dan saina tona asirinka 'dan iska mugu axxalimi mara imali
'Yar yarinyar nan me tasani meta sani daxaka fille maka kai
Saika sakeni
Yace ke kina da hankali kuwa
Taqara cukumeshi Tace bandashi
Xanci uwarka im baka sakeni ba
Nafika maseefa da tashin hankali kwanciyar hankalinka 'daya ka sakeni
Yace ni kuma baxan sakeki bah
Bari kiji Wlhi inxaki ihun duniya ba Wanda xai jiki agidan
Ba kuma Wanda xai barki Ki fita daga gidan.
Sannan xanja miki kinne Karki qara gangancin cukumeni danni......
Lokacin RAMADAN Suna shirin xuwa qauyan takai shika'dai FAWAS da KHAMIS suke jira
amota ya tsaya saka wani takalminsa
Kwana hu'du kenan suna jelan xuwa qauyan dan FAWAS ya Riqe wutta Sam baya wasa da
xuwa gun HAMEEDAN sa.....
Da tashin hankali RAMADAN Yace Ki nutsu Auntyna kidena kukan nan kimin magana Cikin
nutsuwarki pls
By Hajju
[20/03, 17:09] 80k: [2:09PM, 29/11/2016] Rahamat Nalele 👯: [12:18PM, 29/11/2016]
Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*
👯👯👯👯
*👯TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir-*
*rahmanurrahim*
*PART 81*
Sun sami XEE a harabar gidan tana wanke gyalinlikanta sai surutu takeyi ita 'daya
cikin damuwa
Duk suka fito daga motar ta sakar musu Murmushi Tace kaga *SAMAREEN BANAH* Na Aunty
Rahamat daga ina haka kuma xuwa ina
KHAMIS ya saka hannunshi cikin wankin yana tayata da jefah mata wani kallo irin na
tuhuman nan
FAWAS Yace daga gida Aunty...
RAMADAN ya xauna kusa da ita Yace Aunty XEE bayani xakimin akan inda gidan Auntyna
yake
Ta kallesa da sauri tace aha.....
Yanxu kuma kana buqata ne
Yace Sosai mah dan xuwa xanyi gobe
Tace hmm yanxu nake magana kamar wata ta6a66iya akan na rasata awaya kuma gabana
sai fa'duwa yake Sosai akanta. Tafa'da da damuwa akan fuskarta...
RAMADAN Yace hmm Karki damu insha Allah ba wani Abu.
Tace Allah yasa
Yace AmEEn
Nan tayi mishi bayanin gidan. Yako fahimceta Sosai dan bayau yasaba xuwa Abujah ba
dan Qanin Dadyn shi acan yake
Tace kushiga falo mana
RAMADAN ya tashi Yana cewa aa
Ya maida kallansa ga KHAMIS daya xage yana tayata wankin. Yace muna jiranka a waje
Yace OK. Suka fitta
XEE takalli KHAMIS Tace my Luv baka iya wankin nan ba pls bar shin kawai
Ya kalleta yayi Murmushi Yace dama ke kike wanki ina injin 'dinku
Tace aa yau dai nayi niya ne bakaga bashi da yawa ba kuma dan ba wutta ne
Jiya na barki kina mura. Har yau bata canja xani ba. Kin wani kama wanki da yamman
nan. Kalan Ki jaxa min tashin hankali ciwan yafi haka muni ko.
Ta gallamai harara fuska 'daure Tace kafita kafin raina yafi hakan 6aci
Yace kwantar da hankalinki my luv Ki sakarmin mara dan da gaske kin sani jin
futsari...
Na rantse miki da Allah ba budurwata bace
Tayi Murmushi da cewa ban yarda ba
Yace ki yarda pls
ina tare dake baxan ta6a ganin kyawun wata 'ya mace bah
.
[2:08PM, 29/11/2016] Rahamat Nalele 👯: Misalin qarfe takwas ne 8:00pm ne na dare
RAMADAN yasami mahaifan nasa a falo Suna hira cikin kwanciyar hankali
Ya xauna kusa da Dadyn nashi bayan ya gaidasu Yace ina San xuwa Abujah dad
Dadyn nashi ya waro ido Yace me yasa
Yace xanga Auntyna Sannan na da'de banga Dadyn Yusra ba
Dadyn shi yayi shuru Yace skull fah
Yace akwai sauran lokaci ba damuwa
Dadyn ya gyara xama cikin damuwa Yace yaxo garin Abujah yau kwanansa uku bana San
Su ha'du
Momy tayi saurin cewa bafah ni ka'dai bace
Cikin sauri Dadyn yanemi gyara kansa da cewa Nace wani abu ko
RAMADAN ya kallesa da mamaki Yace kace mana dad
Waye shi da bakasan na ha'du dashi
Dadyn Yace ba dakai nake nufi ba
RAMADAN ya ta6e baki Yace Owkie yanxu dai afara min shiri dad
Baiyi mamakin ganin direban Su Yusra yana xaune xaman saukar shi ba
Dan haka suka tafah da Adam direba Yace mutumina ka ha'du fah. Kaga yanda ka girma
RAMADAN yayi Murmushi Yace Yaya Adam kenan har yanxu kananan da barkwancin ka
Yace toh yaxanyi RAMADAN bayan gaskiya nake fa'da
RAMADAN Yace kaga Malam muje daga nan ka 'dorani akan inda katsaya
Da dariya Adam ya tada motar
Ayanda RAMADAN ya fuskanta gidan Auntyn nashi bayi da wani nisa da gidan kawun nasa
Sun isa gidan babban gida murna ta cika gidan Wlcm Ya RAMADAN Wlcm
Baiyi mamakin farin cikinsu ba dan yasan masu qaunarsa ne
Toh Madallah. RAMADAN ya fa'da da maida kallansa ga Yusra Yace qanwata yadai rufe
bakin mana Tace Ya RAMADAN kenan nayi farin ciki Sosai da wannan xuwan baxatan da
kamana
Yace naji da'di da kika ji da'din hakan
Dady da momynsu sai Murmushi suke dan Allah ya 'dora musu san RAMADAN Suna sanshi
Sosai
Dady Yace jiya ai Dadyn naka yake gayamin wai haka kawai kace kanasan xuwa garemu
Yace eh Dady kuma inasan Ganin Auntyna mah
Momy Tace SAILUBAH ko
Yace eh Momy ita
Yusra Tace xan rakaka in xakaje gareta
Yayi Murmushi Yace ai kuma tunda naxo shikenan fah na shiga uku agunki
Duk sukayi dariya ya tashi yana kallan Amar Yace toh brother muje inyi wanka in
huta...
Dady Yace badai har ka qoshi ba
Yace ai naci da yawa
Yusra tayi dariya Tace nifah na dafa maka
Yace hmm ban yarda ba dan nasan baki iya girki bah
Tace Allah nice nayi Yace na yarda dama nasan qanwar tawa ta iya girki wasa nakeyi
tayi dariya....
Ya tasa Amar agaba sukayi shashinsa
Bayan RAMADAN yayi wanka ya miqe a gado yana san yin tunanin Auntyn tashi da yanda
xaije gareta gobe. Kiran wayan shi ya katseshi
Yana dubawa yaga shahuda.....
Da jan tsaki ya picking da Alo
Tace haba RAMADAN lefin menayi kadena 'daukar wayata
Yace wane ke da lefi ai bakya lefi
'Dan jini ka'dan kiji
Tace ina ji
Yace kwana biyu ban riqe wayar bane shi yasa naketa kar6ar hukunci agun mutane pls
kar kema Ki hukuntani dan Allah
Tace wane ni
Kana ina ne yanxu
Yace bu'de kunanki kiji dakyau
Tace aha na bu'de
Yace ina garinku kuma inda yake shashinku
Tace dan Allah fah
Yace fa'di abinda xan miki ya tabbatar miki da hakan
Tace yanxu naganka
Yace wa'yanda nake gidansu baxa su barni fitta yau ba
Tace toh gobe na ganka Yace Allah ya karmu
Tace bara na barka ka huta gajiya ko
Yace Saidai ban gaji da jin dad'dar muryarki bah
Tace hmm baka da dama Wlhi
Yace Gaskiya
Ya durqusa ya kama fuskarta yakai bakinsa cikin nata yabata wani make✔ kiss me
tsayawa arai
Yace shegiya Kinga 'dan saurayi ko.
Nafi qarfinki Wlhi
Haka kawai kin shirya magana dan kinaso nayi kissing 'dinki ko
Tofah😳.
By Hajju
[2:11PM, 29/11/2016] Rahamat Nalele 👯: RAHAⓂ🅰T
[20/03, 17:09] 80k: 👯👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*
👯👯👯👯
*👯TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir*-
*rahmanurrahim*
*PART 83*
Ya kalli shahuda Cikin wani hali Yace wai me nayima Dad 'dinki ne daxai qaqabamin
bindigogi haka
Ta qura mishi ido takasa bashi amsa dan rasama me xatace mishi tayi....
Bata idda tunaninta ba taji Dadyn nata yana bashi amsa
Yace Lalle kacika 'dan iska xahiri
Ko Mantawa kayi in tuna maka
Kuxo jiya kumin fashi yanxu kafara tambayar me kayi
RAMADAN Yace fashi😳.....
Wlhi bani bane. Yafa'da cike da tsoro da kallan shahuda
Tayaya Xanyi fashi
Me nake nema haka dana rasa dahar xanyi fashi.....
Cikin fusata shahuda Tace Amma kai dai kacika 'dan rainin hankali....
Dadynta ya amshe da cewa bar 'dan iska yaudai qaryarka taqare kai da uban naka
Wlhi kaji narantse indan har uban naka bai dawomin da ku'dina ba na rantse saina
kasheka natura mishi da gawarka kuma........
Bai qarasa furucinsa ba
Saiga wasu samari biyu sun shigo gidan da manya manyan jakunkuna sun dire agabansa
da fa'din wai xaka iya qirgawa ko daidai suke
Dadyn shahuda ya washare baki da murmushin jin da'di Ganin ku'dinsa sun dawo
Yace shege Jibiril yaji anta6o farin cikinsa
Ya fa'da yana mai bu'de jakunkunan. Aiko saiga ku'dinsa nan muraran
Ayanda yalura ko 'daya baiyi ciwan kai ba.
Ya kalli wa'yanda suka takura RAMADAN da bindigogi Yace kusake shi ya tafi.
Nan ko suka bar gun.
RAMADAN yajah numfashi yana kallan ikwan Allah da mamakin abin....
Cikin sanyin yanayi ya shige motarsa shahuda tabishi da kallan harara
Shidai ya fitta yana hamdala ga Allah daya ku6urar dashi
Da wannan tunanin ya iso gidan kawun nasa
Wanka yayi yayo alwala yayi sallah dake lokacin La'asar ta gabatoh
Saiya kwanta yana tuna lamarin
Har bacci ya 'dauke shi bai gane me lamarin yake nufi ba.
Malam habibu wani shahararran malamine acikin garin kano awata unguwa da ake kira
bacirawa
Yana da mata biyu Hauwa da Asabe.
Hauwa itace wacce ta Haifa mishi yara uku wato Jibiril da Naziru da Auwal
Sai Asabe ta Haifa mishi Jabiru
Yaransa sun kama hu'du kenan
Jibiril shine Babba sai Naziru sai Auwal sai autansu Jabiru
Bayan sun girma sun mallaki hankalin kansu Allah yayima iyayan nasu rasuwa
Farko Asabe mahaifitar Jabiru CE tafara rasuwa sai Hauwa tabi bayanta sai megidan
nasu Malam Habibu
Haka suka taso gurin kawunsu wato qanin mahaifinsu Wanda yayi musu rikwan tsakani
da Allah yabasu tarbiya da ilimi
Lamarin yafarune lokacin daya farayin ku'di duk saiya doke yayun nasa aku'di
Yaje ga sauran yayun nasa yana nuna musu baidace yaya Jibiril yadinga nuna masa
Hakka ba
Ha'kuri suka bashi dan dukkansu tsoran shi Jibiril 'din suke
Jibiril ko San mata yasa agaba damuwar shi ya aikata xina da 'Yar mutane ya biyata
Anan duk ku'din da yake samu suke qarewa yaqiyin Aure sam
Sunxo sauke faraline saudiya shine Jabiru yaga Khamsa'u suka fa'da qaunar juna
Soyayya tayi qarfi tsakaninta da jabiru har magana tayi xafi iyaye suka shiga
xancan
Dan koyaushe Jabiru yana hanyar garinsu Harif
Daqar magana tayi qarfi har Allah yasa Khamsa'u taxama mata ga Jabiru
Iyayanta sukace baxai kawo musu 'ya Nigeria ba Saidai ya xauna da ita a qasar Saudi
dan tafi kusa da qasarsu
Dake Jabiru ya mutu kan Santa haka ya yarda yasai gida aqasar saudiya suka tare da
Amaryar tasa.
Tunda Jibiril yaje yaga maxaunin qanin nasa Jabiru yaga sai hankalinsa ya tashi
maqin cikinsa yaci karfinsa nan yafara tunanin Hanyar da xaiyi ya kashe Jabiru
danya mallaki dukiyarsa
Lokacin ko idan Jabiru yaqara wayewa dan shiga qasashe da yakeyi shida matarsa
Khamsa'u
Nan yasa hannun jarinsa a qasar Kuwait yasaka a England yasaka a American
Wa'yannan qasashe uku dayasa hannun jarinsa sune silar qara ha66akar axxiqinsa
Mutum ne me San temako me ibada da San Allah da Manzansa
Hakance tasa yaware kasu mafi tsoka daga dukiyarsa yaba yayun nasa
Naziru da Auwal ne kawai sukayi farin ciki da kyautar suka dinga murna dasama qanin
nasu albarka
Jibiril najinsu yajah tsaki Yace wai murnar mesukeyi dan yabasu 'yan ku'din dabai
taka kara ya karya bah
Duk da kallan mamaki suka bishi dashi kana suka hango tarin baqin ciki da hassadace
take damun yayan nasu
Sam Naziru da Auwal sukaqi yarda da hakan dan sunasan Jabiru abin duniyarsa bai
rufe musu ido bah
Yace toh shikenan shi xai aikata kuma Wlhi suka fidda wannan xance saiya hallakasu
suma
Naziru Yace ai Yaya bame harnakawa sai Allah haka kuma baxai baka damar cin galaba
akansu ba
Auwal Yace hakane kam
Murmushin mugunta Jibiril yayi Yace xaku gani
Da ido suka bishi Suna mai addu'ar Allah yayaye mishi Baqin ciki
Ana saura wata 'daya Khamsa'u ta aihu tadanqama mijinta Jabiru dukiyarta me tarin
yawa Tace yajuya mata
Wata qanwar babanta Amme Salima wacce take Aure anan qasar saudiya da Naziru da
Auwal Yayun shi jabiru sune suke da shaida akan mallaka mishi dukiyar tata da tayi
Nan yasa mata Su a hannun jari na qasashen da yake harda
Kuma duk dukiyar tashi da tata yasaka musu Suna 'daya dashi ne mutum yake da damar
mallakar wannan dukiyoyin ko bayan ransu
Wato wannan sunan shine sunanta Wato ( *Khamsa'u* )
Indai bada wannan sunan kayi amfani ba kaje kar6ar wani ku'di a American England
Kuwait toko in aka kamaka 'daurin rai-rai ne dan ansan ba naka bane
Toh Jabiru ya ke6e da 'yan uwansa biyu wa'yanda ya da'de da sanin SOYAYYAR gaskiya
suke masa Wato Naziru da Auwal
Dan haka yagaya Komai akan dukiyarsa data matarsa
Sun jinjina masa kuma suntabbatar masa bamaijin wannan sirrin nasa
Dan Jibiril ya samu nasarar harbe Jabiru qiri qiri acikin gidansa lokacin Khamsa'u
tafuta tirenin 'din masu cika nan kusa da gidanta
Aiko tana dawowa taga gawar mijinta alamar kasheshi akayi.
Nan tashin hankali ya sata na'kudar dole
'Yan aikin gidannane suka kaita asibiti
Annan ta haifi RAMADAN da RAMADAN junior
Bayan aihuwarsu da tayi da minti biyu tace ga garinmu nan. Rai yayi halinsa
Kuka Sosai Naziru da Auwal sukayi ganin gawar 'dan uwan nasu da matarsa
Abin takaici Jibiril ya tabbatar musu da cewa shiya kashe Jabiru
Basuyi mamaki ba dan sunsan dama tunda Yace saiya kasheshi ikwan Allah ne xai
hanashi aikatawa
Amme Salima tanemi da Jibiril da Auwal Naziru subata 'yan biyun nan Amma sukaqi
musamman Auwal dayace shixai 'dau 'daya shi kuma Naziru ya 'dau 'daya
Haka tanaji tana gani suka qi batasu Amma sun bata tabbacin xasu dinga kawo mata Su
tana Ganinsu
Tayarda da hakan
Bayan sun rabu ne akan hakan Jibiril ya bu'de musu wutta akan Saidai subashi yaran
Sukuma suka mishi Jan wiya akan baxasu bashi suba ya kashesu
Daqar yasamu kansu suka bashi 'daya bayan yayi musu rantsuwa akan baixai cutar da
yaran ba
Su temaka mishi xaisamu me shayarwa ta shayar dasu
Sam sukaqi
Daga baya dai suka bashi 'daya Wato junior RAMADAN qaramin ciki kenan
Jibiril dama bashi da niyar kuma kashe junior RAMADAN dan Hakka kawai Allah ya
jarrabeshi dasan yaran
Abinda yakeso dai yasamu
Danya samu dukiyar Jabiru
Dangin Su gidajan da filiyan da yasiya a nan gida Nigeria sudai ya samu
Dan baisan da wancan hannun jarin da Jabiru yake dashi a American England Kuwait ba
Tafiya tai tafiya har ya cinye komai. To dama hakkin marayuu ina xai kaisa
Ganin haka yasa yayi wani rikakken 'dan fashi
Anan ya shige harkar
Aikowa yaxama wani Babba a harkar
Haka 'yan uwansa Auwal da Naziru suke mishi nacin ya kawo musu shi Kullun saidai
yadinga turo musu da hotansa
Wata ranah Amme Salima taje gidan Jabiru dan tunawa da 'Yar 'dan uwan nata
Tana binciken kayanta sai kawai taga diarys biyu nan ta karanta na farko taga na
Khamsa'u ne
Ta karanta nabiyu saitaga na Jabiru ne
Dan haka saita kaima Alhaji Jibiril har garin Abujah Tace ya ajiyema Su RAMADAN xai
musu amfani wata ranah
Yabama junior RAMADAN ilimi da kulawa shiyasa Sam junior RAMADAN yataso a shagwa6e
saidai akwai aiki da hankali da ilimi
Yana karatu a qasar England inda yakesan xama cikakken doctor
Duk lokacin dayaxo hutune Alhaji Jibiril yake turashi yin fashi da makami
Dan ayanxu mah hutune ya kawoshi Abujah shine Alhaji Jibiril "din ya turashi fashi
gidan Dadyn shahuda.
👯👯👯👯👯
*SAMAREEN BANAH*
👯👯👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*
Junior RAMADAN yaja numfashi dan kammala karanta diaries 'din da yayi
Kanshi ya 'dau caji yagano tabbas mahaifinsu ba mutuwar Allah da Annabi yayi Bah.
Kasheshi akayi.....
Kuma yana xargin Alhaji Jibiril da kisan
Dan rubutun mahaifin nasu yatsaya mai a inda ya gayama yayunsa biyu akan hannun
jarin da yasa a qasashe uku
sukace bawanda xaiji wannan sirri nasa
Ya qara jan numfashi yana San sanin ya akayi mahaifunsu ya mutu da mahaifiyarsu
Dole yaje ga Dadyn brother 'dinnan nasa yaji ya abin ya kasance
Wanka yayi yayi. Sallah kana yabi lafiyar gado da tunanin Yayan nasa RAMADAN ko
yanxu an sake shi ko ba'a sakeshi ba oho
Koma miye yabarma awa 'daya kacal...👌🏻
Idan yatashi yaji komai.....
By Hajju
[20/03, 17:09] 80k: [8:27PM, 01/12/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*
👯👯👯👯
*👯TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir*-
*rahmanurrahim*
*PART 82*
Yusra CE ta shigo 'dakin da RAMADAN yake tana tafiya ahankali ahankali har taxo
gareshi
Dake ya juya mata baya Sam baisan da shigowarta ba
Sanda yaji qashin turare ya doki hancinsa yayi Murmushi dan yasan Yusran CE
Yace Wlcm my qanwa
Tayi dariya Tace naso na baka tsoro Yace ahaa
Me ya kawoki da wannan lokacin 10:37pm
Tace gani nayi Ya Amar yana can ga budurwarshi kai kuma ya barka kanata aikin
tunani. Shine Nace bara naxo na tayaka hira
Yayi Murmushi Yace hmm qanwata kenan
Ai baije ko ina ba yana toilet
Yama xa'ayi yabarni ni 'daya haka...
Tayi saurin rufe bakinta tana dariya Tace Allah naxata ya tafi garetane Kasan fah
ba qaramin Santa yake ba
Banyi tunanin xai iya in xuwa gareta yau ba.
Kan RAMADAN yayi magana Amar ya fitoh daga toilet Yace toh munafuka brother yafimin
ita....
Xan iya hakurin ganin har tsawan lokacin daxai tafi
Tace La......
Ya katseta da fa'din. Jeki pls kafin im mangareki
Yusra sanin halin yayan nata yatasa kallan RAMADAN Tace sai da safe
Da murmushi Yace mutashi lpy my qanwa
Nanfa ta fucce
😰😰😰
Washe gari?
SAILUBAH tana kwance afalanta sai saqa da warwara take tasan tunda RAMADAN Yace
mata xaixo toko insha Allah xata gansa ko dako xata qara kwana 'Dari tasan duk inda
hankalinsa yake yana kanta
Sai dai gabanta na fa'duwa idan ta'daga kanta takalli makeken gidan nata da kuma
masu tsaran nasa.
sai taji gabanta ya fa'di. Takuma shiga tunanin ta'ina xai shigo har tafi da ita
batare da an'ankare dasu ba.
Ashe kallansu kawai takeyi dan yanke kan mutane suke susha jini. Ku'din bana Allah
da Annabi bane
Duk saitaji tatsani kanta da duk wani 'dan garin Abujah
(SAILUBAH kenan ba dukka bane aka ha'du aka xama)
Da qarfe biyu RAMADAN yanufi gidan Auntyn tashi batare da 'dan rakiya bah
Cikin sa'a yaga megadin gidan ya fitoh yana Alwala akofar gidan
Cikin girmamawa RAMADAN ya gaisheshi dayin yunqurin shiga gidan...
Amma sai megadin ya katseshi da fa'din samaree wa kake nema
RAMADAN ya dawo gareshi Yace gun YAYATA naxo
Yace me sunanta Yace SAILUBAH
Shuru me gadin yayi da tsaida Alwalar tasa can Yace kayi hakuri samaree banan bane
Cikin damuwa RAMADAN ya kalli gidan xuciyarshi tana gaya mishi Wlhi gidan ne kuma
Auntyn shi na ciki
Yace dan Allah BABAH kamin rai inganta....
Da sauri me gadin ya katseshi da fa'din baxan maka qaryaba samaree kaje gidan gaba
qila shine
RAMADAN ya rausayar da kai yanemi guri kusa dame gadin ya xauna Yace xan baka
tsabar ku'di daga naira 'daya har million indai xakamin hanyar daxan ganta
Megadin ya waro ido Yace million 😳
RAMADAN ya gya'da mishi kai
Cikin sanyin yanayi Yace axahirin Gaskiya samaree nan ne gidan. Saidai baxan iya
temakwanka ba. Gashi naji kwa'dayin ku'din daka ambata baxan 6oye maka ba
RAMADAN Yace me yasa baxaka iya temako na ba
Megadin ya numfasa Yace xan gaya maka ne dan naji qaunarka araina
RAMADAN ya gyara xama Yace ina jinka baba
Megadin Yace megidan nan Alhaji Aminu ya garga'di duk Wanda yake cikin wannan gidan
akan duk wanda yaxo akan dangin Matarsa ne SAILUBAH kar'a barshi ya shiga dan
tagano koshi Waye
Duk wanda ko yayi gangancin barin wani nata yashigar masa gida toko Wlhi saiya
kashe shi
In yana da iyali takansu xai fara
Kagako samaree ni inada mata da yara aqauye inajin da'din aiki dashi dan baya
tauyemin hakkina. Kaga ya dace in barka kashiga
RAMADAN ya girgixa kai
Yace Gaskiya bai dace kabarni ba
Amma inaso kamin temako 'daya shine ga wannan.....
Ya miqa mishi wata takadda yaci gaba da fa'din
kasan yanda xakayi ka bata dan Allah
Cikin tsoro megadin Yace baxan kar6aba samaree dan duk abinda xai jawomin matsala
da me gidana bana san kusantarshi
RAMADAN ya karkace ya xaro mishi bandin 'din 'yan dubu dubu guda 'daya ya dire
mishi kan cinyarsa Yace kamin rai babah itace farin ciki na
Ba musu saurayin yashige motar tasa yanata kallan RAMADAN harya tada motar ya tafi
Acikin gidan ko
Megadi yayi nasarar yin shashin SAILUBAH batare da wani ya gansa ba
Yayi mamakin hakan dan yasan mutum sunfi goma wa'yanda suke tsaranta
_Ameenci ya tabbata agareki ya Auntyna. Da fatan kinci abinci dan shine abinda yafi
damuna_
Yanda yabar RAMADAN haka yasame shi. Ya gayamai duk abinda SAILUBAH Tace mai
Da sauri tayi cilli da wayan tanufi 'dakin Dadynta tana kwala mishi kira
Fa'di Tace Dady gasu nan sun dawo suna harabar gidan nan fitoh da bindiganka
Cikin tashin hankali Dadyn nata ya waro ido shida momynta Yace da gaske tace Wlhi
Cikin burkicewa ko bindigar bai 'dauka bah. tunaninshi ya 'dauka suka nufu harabar
gidan ita dashi da momynta
👯〰👯
*New RAMADAN*
Junior RAMADAN ya danna wajan 'dauka ya qara volume dan yaga kamar Dad 'din nasa
yana jin qiwar 'dauka ne
Aiko Dadyn shahuda ya fashe da dariya Yace Alhaji Jibiril kenan
Kaga kamun Allah ko
Saiya dawo min da 'danka ba makami ba komai
Yanxu haka gashi a hannuna.
Alhaji Jibiril Yace wane yaran nawa
Yace kanada wani 'dane banda RAMADAN
Shinake nufi
Yanxu xan turo maka da video nasa narantse da Allah in baka dawomin da ku'dina
yanxu ba Wlhi saina kasheshi kuma nasa akawo maka gawarsa...
Yana fa'din haka ya kashe wayan
Iya gigicewa Alhaji Jibiril ya gigice ya kalli 'dan nasa RAMADAN ya maida kallansa
ga wayan yana addu'a axuciyarsa Allah yasa kar asirinsa ya tonu yau.....
Kanya tattaro tunaninsa videon ya shigo
Aiko da sauri junior RAMADAN ya 'dauki wayan ya duba videon
Abin mamaki sai yaga saurayi kamarsa ba abunda ya rabashi da wannan saurayin an
sassaka mishi bindiga yana yin motsi Komai xai iya faruwa
Cikin tsoro da mamaki yaba Dad 'din nasa waya Yace Waye shi Dad
Alhaji Jibiril ya murgina kai ya kalli videon Yace bansan Waye shiba
Qare ma mahaifin nashi kallo yayi junior RAMADAN na'dan wani lokaci yana naxarinsa
Kana ya tashi yana Murmushi yaxuba drink a cup Yace ko Dad
Amma da mamaki
Dan Kallo 'dayan nan dana masa na gane 'dan uwa nane fa'damin ya abin yake dan naji
qaunarshi Sosai araina
Cikin wani hali Alhaji Jibiril Yace ban San ko Waye shiba kashare kawai......
Kaine kuma ka haifemu. Jinior RAMADAN ya fa'da da San abashi amsa da sauri
Junior RAMADAN ya saki cup 'din hannunsa da wani murmushi wanda yaqara Alhaji
Jibiril tsoro
Yace hmm ai dama nasan qarshen furucinka gareni kenan kace ni ba 'danka bane.
Alhaji Jibiril ya kallesa da sauri
Yace bana buqatar jinta bakinka. Dan ban hango gaskiya a tattare dakai bah.
Ya fa'da dasan barin falan xuwa part 'dinsa
Goge xufah Alhaji Jibiril yahau yi Cikin tashin hankali shima ya kallesu Yace dole
Ku kashe min shi
Atare sukace wah😳
Yace RAMADAN.....
Sukace wannan na nan gidan ko nacan hannun Babban yarinyar can
Yace nanan gidan.
By Hajju 👯
RAHAⓂ🅰T
[20/03, 17:09] 80k: [12:26PM, 05/12/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*
👯👯👯👯
*👯TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir*-
*rahmanurrahim*
*PART 85*
Da misalin qarfe biyar inuwa ya kawoma junior RAMADAN rahotan Komai na RAMADAN
Da yanda yake dasu KHAMIS da FAWAS da yanda ya shaqu da Auntynsa SAILUBAH
Komai dai sanda junior RAMADAN yaji
Yayi Murmushi kawai
Qarfe takwas ko nayi na dare junior RAMADAN sukama Alhaji Aminu dirar makiya
Yana Cikin 'dakin da Yakama a hotel 'din
Junior RAMADAN da Isma'il suka buqaci ma'aikacin wajan daya gaya musu wane 'daki
yake
Da farko Yace dokace ba'a fa'din inda mutum yake a hotel
Amma dayaga ku'di ai bashiri Yace musu yana 'daki mai number goma Sha shidda
Haka ko sukaje gareshi
Kofarma abu'de take
Sai kawai suka shiga suka dannama "kofar key
Alhaji Aminu Wanda yake cin abinci ga wani saurayi najiranshi yagama sufa'da
masha'a. Sai kawai yabi junior RAMADAN da kallo
Cikin mamaki Yace RAMADAN meya kawoka nan
Junior RAMADAN yayi Murmushi ya 'dora qafarshi 'daya a table 'din da yake cin
abincin yana juya bindiga Yace abu 'daya ne ya kawoni
Cikin tsoran yanda yake juya bindiga Alhaji Aminu Yace miye shi kuma meyasa naganka
cikin wannan yanayin bayan nasan kaime nutsuwa ne gashi kamar ba imani atattare
dakai
Alhaji Aminu yayi shuru ya bishi da ido da mamakinsa da kuma tsoran yanayinsa
Junior yaci gaba da fa'din. Toh dan ubanka idan kana iskanci mu asamanka muke
Duk da bama ko 'daya acikin abinda kakeyi Amma nafika iskanci Wlhi
Cikin maseefar tsoro Alhaji Aminu Yace na roqeka da Allah karka kasheni inasan
rayuwa ban gaji da ita ba.
Bayan angama mishi Komai ya xauna hutawa kafin ya nufu gidan nasa.
Junior RAMADAN ko da qarfe goma Sha 'daya ya kwanta dan jiyayi kansa nayi masa ciwo
Kuje gareshi kuce mishi baxaku iyaba shi yaxo da kansa ya kashenin
Yajah numfashi Yace hmm nasani baxaku iyaba. musamman idan kuka tuna alkairan da
yakema iyayanku.
Kuje karku damu xansan yanda Xanyi dashi.
By Hajju
RAHAⓂ🅰T
[20/03, 17:09] 80k: [8:29PM, 04/12/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*
👯👯👯👯
*👯TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir*-
*rahmanurrahim*
*PART 84*
Nan dai da Isma'il ya samu abinda yakeso yayima megadin sallama ya tafi
Shiko yanata murna yau sai samun ku'di yake
Isma'il Yace idanko haka ne ya kamata kasa mishi hannu oga dan baxai iya fidda ita
daga wannan gidan bah
Yace Hakka Amma ya xanyi in gansa shi Alhaji Aminun
Isma'in yace nasan wani hotel da yake xuwa cin abinci qarfe takwas na dare
Washe gari ko kusan qarfe biyu RAMADAN yayi parking 'din motarsa a 'kofar gidan
Auntyn tasa.....
Kamar yanda megadi yace mai xai jira xuwansa hakance ta kasance
SAILUBAH na xaune tana kallo lokaci lokaci tana kallan agogo addu'arta Allah yasa
taji qanin nata yanxu
Kamar yanda take fata ko sai ganin megadi tayi
Tace yanxu naketa sake saken xuwanka
Yamiqa mata ledar hannun nasa cikin ladabi
Ta kar6a jiki na rawa
Tana bu'de ledan taga wata qaramar wayar RAMADAN ce
Farin ciki kamar ya kasheta Tace shikenan babah megadi jeka
Yatafi yana Murmushi har yaxo ga RAMADAN.
By Hajju
RAHAⓂ🅰T
[20/03, 17:09] 80k: [10:31PM, 07/12/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*
👯👯👯👯
*👯TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir-*
*rahmanurrahim*
*PART 87*
Isma'il Yace Amiien. Kana sukaja motarsu junior bai dena ganin fuskar SAILUBAH a
idanshi bah
RAMADAN ya miqa musu ATM dinsa Yace inaso kuje Ku fitomin duk ku'din da yake ciki
Da mamaki sukace toh.
Dan dai sunsan ba qaramin ku'dine a ciki ba
Bayan sun tafi ne ya fa'da tunanin SAILUBAH da Yayan nasa
Sintiri yake tayi dan xuciyarsa cakarsa take tana qara cusa mishi soyayyarta
Shi kuma yana quqarin yakiceta
Saidai so baisan haka bah
Bai San adadin lokacin daya 'dauka yana tunanin ba. Saida yaji xuciyarsa nayi masa
xafi Sannan yayima kansa gata wajan yin Alwala ya gabatar da sallar axahar
Da sanyi suka fitta Suna waiwayansa. Yayinda Isma'il yaqi tafiya ya tsaya da kasan
sa ahannu
Da mamakinsa junior RAMADAN Yace me katsaya yi kai
Cikin xubar hawaye Yace Wlhi oga nafisan kasancewata dakai akan in kar6i ku'dinnan
na barka
Junior yayi Murmushi ya da'de da sanin Isma'il masoyinsa ne na Gaskiya yana hango
soyayyarsa acikin kwayar idansa
Yace karka damu kana da number na. Xaka iya jina akowane lokaci kakeso
Yace yanxu bakamin katanka da kanka ba
Ya 'daga mai kai da fa'din eh
Isma'il yayi Murmushi da 'daga mai hannu Yace bye Allah ya dubeka ya baka nasara
akan duk abinda kakesan aiwatarwa
Da farin ciki Sosai Yace AmEEn nafah goge
Yace karka damu
Kana ya ficce. Junior ya bishi da kallan qauna
Senior RAMADAN ko
Tafiyarsu suke ahankali. Sam basu damu da sukai da wurri ba
Hira suke cikin jin da'di dan kallo 'daya xaka musu subaka sha'awa.
Alhaji Aminu yayi Murmushi ganin Abban nata bai yarda da abinda taceba tunda har
yana neman jin ta bakinsa
Yace Wlhi Abba kamar kasani. Haka kawai tasani agaba wai saina saketa harda nunamin
wuqa. Ni kuma na tsorata da yanayinta har ban san lokacin dana mata saki uku bah.
Sannan naji tana fa'din wai saita kwullamin sharri agunka bansan me tace maka ba.
Cikin 6acin rai Abban Yace hmmm toh shi kenan tunda Komai ya abku
Yace kayi hakuri Abba dan Allah
Yace aa karka damu Allah yabaka wacce tafita
Yace AmEEn sukayi sallama
Da 6acin rai Abban nata ya kalli kakah Yace hmm aidama nasani kin dai ji abinda
yace da kunnanki
Kantayi magana SAILUBAH ta cafke cikin sauri da fa'din Wlhi qarya ya gaya maka Abba
na rantse maka
Ya kalleta da Takaici yanaji aransa kamar yatashi ya na'da mata dukan tsiya Amma ya
'daure Yace tunda ban isa dake ba ai shikenan kije xan nemeki Amma kisani nabaki
watanni takwas kifitoh min da Wanda kikeso.
Na rantse da Allah kika xarce haka da Almajiri xan ha'daki dashi
Kuma kika qara kasowa Saidai kinemi wani uban ba niba.
Tashi kiban waje
Oho dai SAILUBAH Tace aranta dan ta'dauka wani mummunar hukunci xai 'dauka akanta
sai taga sa6anin haka. Dan wannan mesauqine xata tsaida wani
Nan tatashi sumi sumi tayi 'dakinta......
Kanta shiga kakah Tace ya 'dora miki idda ne
Da sauri SAILUBAH Tace aa
Da saurin fa'dawa 'dakin nata
Tanajin Kakah na fa'din aigwara haka danni Sam dama bai kwantamin arai bah
Abba yatashi yayi 'dakin matarsa batare dayace mata Komai dan Takaici
SAILUBAH tajah numfashi dan ganin 'dakin nata Yana nan yanda yake harda kayanta dan
ba'a kyautar ba kamar yanda tace
Tayi Murmushi da fara tsaftace 'dakin cikin rera waqar *M shariff*
*Bismillahir-*
*rahmanurrahim*
*PART 86*
Washe gari ko tun qarfe 6:00pm tayi wanka taxauna xaman jiran qarfe gomah
Alokacin ne RAMADAN yaga sakwanta
Cikin farin ciki ya kirata ta'dauka
Yace Auntyna da gaske
Tace Wlhi har yana cewa qarfe goma xai barni na tafi.
Yace alhamdunillah
Yanxu kinga bara nafara shiri sai na musu sallama daga nan sai naxo kawai mu wucce
Tace toh ina jiranka Qanina
Yace Aha my Aunty
Kana ajiye wayan ya kalli Amar Yace yau xantafi fah
Da mamaki Yace mai yau
Yace yah. Da barin 'dakin
Amar ya bishi da kallo
Anan falan ya tarar da Momy da kawun nasa Yace dad mum kumin afuwa yau xan koma
gida
Suka CE lafiya Yace Wlhi qalau😀
Auntyna CE xata gida yau shine naga dacewar mutafi tare
Sukace Amma bamuji da'di
Yace hmm aixan qara dawowa ne
Dad Yace kan kadawon ai saika ibi shakaru
Mum Tace qilama sai Auransa in munje ma gansa kawai
Yayi Murmushi Yace kai mum
Tace eh ai gaskiya ne
Yace toh bara naje in sharya xuwa 9:30am nakesan tafiya
Mum Tace toh Allah ya nuna mana lokacin
AmEEn dad Yace
Yusra Tace gaskiya banji da'di
Yace Karki damu qanwata ina tare dake ai
Junior RAMADAN da Isma'il ko qarfe 9:00am dai-dai tayi musu ne qofar gidan Alhaji
Aminu
junior ya matsar da motar tashi can gaba yanda xaiga fitowar SAILUBAH da xuwan
Yayan nasa
Yace naxa'ku naqara ganinsa
Isma'il Yace ai yanxu haka ma qila yana hanya
Yace Wato Isma'il Wlhi kallo 'daya namishi Naji qaunarsa cikin raina
Yace sai shima ya ganka na tabbata saiyaji sanka fiye da yanda kaji nasa
Yace Allah yasa
Haka suka dinga hira har xuwa lokacin da Senior RAMADAN ya iso
Ya fitoh daga motar tashi yana kallan agogo
Junior RAMADAN ya qura masa ido tabbas ya ha'du sai kace ba tashin Nigeria ba ya
iya wanka
Isma'il Yace hakane.
Yace kin manta da kuka kike cemin dan Allah kaxo ka'daukeni Wlhi kasheni xaiyi dan
Allah Ni dai kaxo kawai ka 'daukeni.....
Ya qarashe da kwaikwayan muryanta
Ta kallesa ka'dan suka sheqe da dariya a lokaci 'daya☝🏻
Innalillahi'wa'inna'ilaihirraji'un
Shine abinda junior RAMADAN yafurta hannunsa dafe da qirjinsa
Nishi yake sama sama can jadawo normal 'dinsa cikin wani hali Yace bala'i......
Isma'il Yace karo na farko kenan da wata yarinya taburkitaka arayuwarka
Yace tayi tayi tayi... Ta ha'du. Kuma tayimin
Kamar yanda kifiya take xuwa da gudu take cakar mutum wlhi haka naji maseefar sonta
ya caki xuciyata.
Isma'il Yace ai kashiga kawai. Naga kamar bata da matsala.....
By Hajju
[20/03, 17:09] 80k: [9:09PM, 09/12/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*
👯👯👯👯
*👯TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir-*
*rahmanurrahim*
*PART 88*
SAILUBAH mah da tayi wanka kiran XEE tayi Tace shegiya ta KHAMIS kina cikin
kwanciyar hankali kin cafke yaro kin hanashi saqat😀
XEE da take kwance kanta na mata ciwo dan sun sami sa6ani KHAMIS jiya shine har
yau abin yake damun xuciyarta.
Ai tuni Tatashi xuciyarta cike da San jin qawartata Tace haba Qawa me yayi xafi
xaki tadamin hankali haka
Kinsan Allah gobe nake cewa Xan biyo RAMADAN
SAILUBAH tayi dariya Tace basai kin biyo shi ba. Dan yanxu haka ina gida
XEE tawaro ido😳 kana kuma tayi dariya😀 Tace anyi 'Yar iska anan. wannan ai story
ne
Cikin San tabbatar mata SAILUBAH tagyara kwanciya Tace Wlhi da gaske
XEE Tace kin rantse fah😳
Kar kisa inxo yanxu dan tabbatarwa
Tace Allah ya kaimu gobe kixo kisha mamaki Amma yanxu ko kinxu a gajiye nake
XEE Tace ai ba'a qarya kusa da gida. Bani labari pls
SAILUBAH tayi dariya Tace Allah sai mun ha'du gobe
Kinga bacci nake ji......
Ta katse wayan da dariya
Tagyara kwanciyarta
Sai kuma tafara kiran RAMADAN
Yace yane my Aunty
Tace lau kaci abinci Yace eh
Tace tsakani da Allah
Yayi Murmushi Yace Abba yayi fa'da ko
Tace hmmm kadai bari Ashe maxa ma sun'iya yanko qarya
Yace Sosai mah
Ban labari plx
Tace bacci fah nakeji
Yace nasani pls bani ka'dan👌🏻 mana my Aunty
Tayi Murmushi da kwashe yanda sukayi ta gayamai
Yace tab yanxu waxaki fidda
Tace ina xan sani. Amma ai Kasan baxan rasa bah
Yayi Murmushi Yace Hakka ne. Musamman idan na tayaki xa6e
Tace hmm pls karka dawomin da halin ka fah
Yace Auntyna kenan. Karki damu da wannan kinji
Tace yauwa 'dan Qanina kaci abinci pls
Yace Allah naci
Tace toh gudnyt
Tace Yah nyt my Aunty......
Washe gariko a Abujah junior ne ya fitoh cikin shiri Yace toh Dad ni natafi
Kano.....
Alhaji Aminu Yace katenaken karkaje
Yace Wlhi Dad ba abinda xai hanani tafiyar nan sai mutuwa.
Alhaji Aminu yayi shuru cikin wani hali
Ganin haka junior yayi Murmushi Yace Nagode da ilimin da kabani sasai kuma yanxu na
canja shawara xanci gaba da kiranka Dad 'dina dan soyayyata da nake hangowa a
kwayar idanka.....
Yanxu sauramin sati uku hutuna ya qare. Xan qarasa shi acan. daga nan xan wucce
skull akwai Wasu ku'dade a hannuna.
Na barka lafiya my Dad
Hakan ya tada motarsa tagani tafa'da ya bar harabar gidan yana yimata kallan qarshe
dan yasa aransa baxai qara dawowa qaxamin gida irin wannan ba
Xan nemi nashi na kansa
( RAMADAN junior kenan. Idanshi ya rigada ya bu'de da lera shiyasa Sam bai maida
Komai komai ba. )
Haka Yana motar nan wutta yana san isa cikin sauri
Qarfe 1:30pm na rana SAILUBAH ce me cin abinci cikin nutsuwa saiga XEE
Tace 'Yar Uwa ya haka
SAILUBAH Tace xauna kisha labari
Aiko XEE tabaje tana fuskantarta
SAILUBAH takwashe Komai ta gayama XEEE
Taqara dacewa naga maseefa ganin idona.
Kan yarinya nagani ancire mata fah😳
XEE ta doka salati Tace Allah ne ya temakeki daya cinye mana ke😟
Tace kedai bari. Aini yanxu ni da alhazawan garin Abujah sai ido
XEE tayi dariya 😀 Tace naso ganin idanki lokacin da kika gano Gaskiyar shi Waye
Tace ai kika ganni alokacin tausayina xakiji
Tace hmm naji SAILUBAH dan Allah ya ku6utar dake hankali ya kwanta ta 6angaranki
😂😂😂😂
Me SAILUBAH xatayi imba dariya Tace ke tsinannan kishinki baxai barki kixauna
lafiya ba
KHAMIS ko idansu ya da'de da bu'dewa akan mata
Kigafah yanda matan suke binsu suke sharesu
Sannan kice baxai ta6aki ba baxai kuma ta6a wata ba.
Ya kalli Saudat dake tafitoh daga betroom ya durqusa a gabanta yace dan Allah dan
Annabi Aunty ki temaken kibata hakuri wlhi sharrin she'dan kuma wlhi banxan qara ba
Saudat tace ni basan kan xancan ba faroshi daga Farko
Kamar xai gaya mata sai kuma Yace hmm ina San im mayar da ita gidane kuma taqi
Tace toh kabarta man
Bayan yanxu taxo
Xaiyi magana....
Ta ta katseshi da fa'din kamin rai KHAMIS kabarta ina cikin wani hali Wlhi. Shawara
nake nema kaga ba SAILUBAH
Ya kallan na gallamai harara
Cikin tsoro Yace in jiraki
Na bishi da mugun kallo da cewa Wlhi baxan bika bah. Katafi kawai idan nadawo xan
nemeka
Daqar ya tashi ya tafi
Wlhi ji nake kamar in sami yarinyar inja mata kunne akansa. Ke koma inci ubanta
inhuta
SAILUBAH tayi dariya har sanda XEE ta qulu Tace Kinsan me xakiyi yanxu kisami
nutsuwa.
Cikin 6acin rai Tace dana sani koji xakiyi ne
Sarai SAILUBAH tasan ta qulu dan haka Tace toh kiyi hakuri naga ranki ya 6aci
XEE tajah numfashi Tace gaskiya baxan iya shareshi na tsawan sati 'daya ba. Gaskiya
yayi yawa
SAILUBAH tajah tsaki Tace toh ai shikenan kije kiyi abinda yadace miki
Dan gaskiya shawarar daxan iya baki kenan......
Kan XEE tayi magana wayarta ta'dau ruri
Tana dubawa taga KHAMIS 'din ne
Tayi shuru tana naxari
SAILUBAH Tace ki'dauka kawai horan da kika masa jiyama ya isa...
Cikin sanyi ko ta'dauka. SAILUBAH taji kamar tashaqeta dan gatse tamata Amma sai
ta'dauka.
Cikin sauri Yace Wlhi da baki 'dauka ba dasai dai kijini a gadan asibiti
Tace naji da Allah miye Yace kiyi hakuri Wlhi baxan qara ba
Tace toh naji
Yace inxo in ganki yanxu
Tace aa
Yace dan Allah
Tace aa
Yace xan miki kuka fah Tace toh ina gidansu SAILUBAH
Yace toh ganinan
Tace ka nutsu kayi breakfast da wanka fah
Yace kamar Kinsan banyi ko 'daya daga ciki ba
Tace toh kayi pls
Yace angama my Luv I Luv u
Tace me 2
Suka ajiye waya.....
XEE tabi wayan da kallo tana raya Gaskiya so maseefa ne
SAILUBAH Tace kin samu nutsuwa ko
Tace Sosai mah.
Agidansu RAMADAN ko Dad 'dinsa ne ya sami momy cikin farin ciki yake CE mata Yayah
Jibiril ne yakirani yanxu wai 'dan namu xai kawo mana xiyara yau yana kan hanya
Momy ta waro ido Tace da gaske
Yace sharrin ku kenan wasu matan ba dama megida ya fa'di xance sai kunsashi
rantsewa
Tayi Murmushi Tace ayya kayi hakuri abinne yaban mamaki yau RAMADAN xaiga 'dan
uwansa
Yace aikuwa dai
Dan haka a shiryamai abubuwa masu da'di dan ya tabbatarmin baya wasa da cikinsa
Tace toh angama dadynsu
Yayi dariya Yace harnatashi daga Dadyn RAMADAN nakoma Dadynsu
Tace eh mana. Dan ga 'dayan yana San bayyana
Yace yama bayya
Kinsan farin cikin da nake ciki kuwa
Tace aibasai kace bah.
Dan Komai naka ya bayyana hakan
Yace bari nakira Auwal na gaya mai
Tace ya dace kam
RAMADAN ko Tambayar wani 'dan department 'dinsu yayi qarfe nawa yau suke da
lectures Yace biyu
Yace Owkie.
Hakan ne ya bashi damar sakankan cewa yaci gaba da baccinsa
Yana cikin baccinne FAWAS ya shigo 'dakin nasa ya tasheshi da cewa 'dan is ya
Abujah
RAMADAN ya tashi yana fa'din Kasan da Auntyna nadawo
FAWAS ya waro ido Yace ban gajine bah
Yace mijinne ya saketa FAWAS yace bani labari pls naji xuciyata na bugawa
RAMADAN yayi dariya Yace tadena toh dan Allah
Amma me😳
Yana futuwa sai ganin junior RAMADAN yayi ya tsaya da mota yafitoh yana qarema
unguwar kallo
KHAMIS ya kallesa dakyau Cikin bala'in tsoro Yace RAMADAN yaushe kafitoh
Junior ya kallesa Cikin San basar da xancan nasa Yace dan Allah ina tambayar gidan
Alhaji Naziru ne
Cikin qara ru'dewa KHAMIS yajah da baya ya shige cikin gidansu SAILUBAH da gudu
yana fa'din innalillahi.....
By Hajju
R🇦H🇦M🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [11:46PM, 13/12/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*
👯👯👯👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*👯
👯
*PART 89*
Yana ido biyu da junior gabansa ya fa'da cikin wani yanayi na mamaki da Al'ajabi ya
nuna junior da hannu Yace innalillahi
Dady yatashi yaxo gareshi ya kama hannunshi ya xaunar dashi Yace ga 'dan uwanka
RAMADAN
Senior ya kasa 'dauke idanshi akansa
Yace ko bakace bah Dady kallan dana masa naji gabana ya fa'da tabbas wannan 'dan
uwana ne
Dady Yace haka abin yake Ku 'yan biyune
Ahankali RAMADAN yakai hannunsa jikin junior ya ta6a kafa'darsa.....
Momy da Dady suka fashe da dariya. Junior yayi Murmushi Yace kanutsu brother nine
dai 'dan uwanka
Momy Tace kai shi yayi wanka anshirya mishi abinci
Senior RAMADAN Yace toh Amma..... sai kuma yayi shuru
Suka tashi atare senior sai kallanshi yakeyi. Candai ya kasa jurewa sai kawai ya
ware hannunshi alamar ya rungumeshi
Aiko nan take junior ya rungumeshi Yace I miss u my brother
Senior Yace miss 2 den I Luv u
Me 2 junior Yace
Momy da Dady da suke bakin 'kofah suke kallansu sai xuciyoyinsu suka cika da
tausayinsu musamman ma Dady
KHAMIS ko yana shiga gidansu SAILUBAH jingina yayi da bango yanata nanata
inna'lillahi
Ya 'dauki lokaci kafin ya leqo.....
Baiga kowa bah. Dan lokacin har junior ya shige gidansu Yayansa RAMADAN
Ganin hakan KHAMIS yayi tunanin kodai idanshine ya nuna mai haka
Ko kuma aljani ya gani ne
Haka dai ya dinga tsaqar xuci har ya kai falansu SAILUBAH
Anan yaga tauraruwarsa XEE
Yace Barka da ranah Aunty LUUVAH
Tace barka KHAMIS nasa meku lafiya
Yace lafiya lau
Tace sai kawai kaganni.....
Yace eh Wlhi ya abin yake
SAILUBAH takama baki Tace ni dana Aure 'dan shan jini me kisa kuma 'dan luwa'du
Yace dama fah ni ban wani yarda dashi bah
Tace hmm kaidai bari kawai
Yace nabari tunda bai ta6a mana lafiyarki ba. Dan da yayi gangancin yin haka da sai
yayi tuntu6e da Babban maseefar da baxata barshi ba har qarshen rayuwarsa
SAILUBAH Tatashi tana Murmushi Tace hmm kunaji dani qannena
Yace Sosai my Aunty.
Ta qarayin Murmushi tanufi 'dakin Kakah tana fa'din kuji da'dinku masoya
Senior RAMADAN ya xauna daf da 'dan uwan nasa Yace xanso kaban labarinka
Junior yayi Murmushi Yace ahannun Dady Jibiril nataso
Saidai duk Wasu abubuwana a waje nake yinsu
Senior Yace kana nufin Kaine 'dan uwan da momyna take gayamin yana wajan Dady
Jibiril
Junior ya gya'da mishi kai
Yace watoh 'dan Uwa akwai cakwakiya acikin tarihin rayuwarsu
Xakaji Komai Amma lefin nan bara naci abinci muyi Sallah idan na hutta na baka
labari ko da dare ne
Senior Yace Owkie
Suna xaune kan dining Suna cin abinci Amma banda Senior RAMADAN
Dan danne dannansa kawai yakeyi awaya
Junior ya kalli kwayar idan Dady Yace ba da'dewa Xanyi ba.
Kwata kwata sati uku ne ya ragemin in koma skull
Senior RAMADAN Yace nayi tunanin kadawo garenine gabaki 'daya
Yace eh haka ne
Dan nabar hannun Dady Jibiril kenan ko Baku
Dady ya ajiye cokalin hannunsa Yace da gaske kakeyi
Yace gaskiyar kenan dad
Tunda nagane akwai wani abu aqasa Wanda kuka da'de da 6oyewa shikenan fah naji
banisan qara xama kusa dashi
Cikin sanyi Dady ya kalli Momy alamar ya shiga damuwa
Daidai nan 'din junior ya tashi yana yana goge baki da tishu ya ficce daga falan
xuwa part 'din senior RAMADAN
Momy Tace lokaci yayi daxaku fayyace musu Komai dansu fuskanci rayuwa
Dady ya kalli Momy Yace Wlhi yanda nake san yarannan ko 'ya'yana bana jinsu kamarsu
Momy tayi Murmushi Sam mijin nata bai iya 6oye gaskiyarsa ba
Shiyasa take qara sanshi
Idan abu ya kasance gaskiyar shine baya damuwa da ranta ya sosu ko karya sosu fa'da
mata kawai xaiyi
Tace nima ina matuqar sansu Allah ya dubesu ya rayasu
Yace AmEEn
Sosai junior yake bacci hankali kwance yayinda senior yagama karance diarys 'din
nan tsaf
Hawaye ne kawai yake sauka afuskarshi
Na Farko abinda ya sashi kuka na mutuwar iyayan nasu dan yasan da mahaifinsu yana
nan dole ya bayyana garesu
Toh ya akayi ya mutu kasheshi akayi ko haka kawai ya mutu
Tabbas xaiso yaji wannan
Na biyu kuma yanda Dadyn shi Alhaji Naziru yanunamai qauna fiye da 'ya'yansa
Baya ha'da soyayyar da yake masa da kowa agidan
Tabbas yanuna mishi qauna ta qarshe
Yana nuna mishi SOYAYYAR DA BATA DA QARSHE 😀
Senior yayi saurin cewa aa banasan kayi yunqurin yin Komai idan na isa dakai
Junior yayi mata kallo 'daya xuciyarsa na bugawa fat fat fat
Ai bai ankareba yajita kusa dashi. Qamshinta ya bigeshi ya lumshe ido cikin basarwa
Tabishi da kallan shagwa6a ta kama hannunsa Tace Abban nan nawa kamar mai aljanu
kaga yacanja tsarin nasa yanxu wai wata biyu yaban nafito da Wanda nake so. Tunda
wancan bai 'doramin idda ba.
Nufinshi yajanye wata takwas 'din da Yace kenan
Wai inda nafitoh da Wanda nakeso hankalinshi xaifi kwanciya Koda baxa'ayi bikin nan
kusa bah
Pls ka temaken Qanina ya xanyi.
Taqarashe kamar xatayi kuka
Tace kut😳
Amma shine Komai naku 'daya
Xama yayi kusa da ita lokacin junior ya shige toilet
Xatayi magana junior ya fitto bai kallesu ba ya shinfi'da sallaya zai hauyin Sallah
senior Tace am 'dan uwa gafah Auntyna ta Kaina inaji da ita over kaso pls dan zanji
da'din hakan....
Cikin maseefa SAILUBAH Tace karma yasoni mana
Junior ya kalleta araini Yace gaskiya brother na rainata. Ma'ana baxan sota ba
Dan banga abin San bah
Cikin sauri senior RAMADAN Yace bafah wancan san ba.
Junior yayi Murmushi Yace ai in wancanne tayimin yarinya
Ina nufin baxan sota bane kwata kwata dan bakai nabata kowane irin matsayi na so
ba......
Ya qarashe da tada abbara cikin halin ko in kula.
Kut😳 SAILUBAH Tace ta kalli senior. Yayi saurin marairaice murya cikin kunya da
nadamar gabatar da ita gareshi
Yace am sorry my Aunty karkiji Komai aranki dan furucinsa Wlhi qarya yakeyi ke abar
San kowa ne
Tace Amma wannan akwai 'dan iska mara mutunci shege
Nixai kalla Yace baiga abin so ba
Ni sa'arsace
Shuru senior ya mata dan yasan ta shaqa kuma baisan me xai kuma CE mata bah
Itama shurun tayi tana jiran ya idar ta tsefeshi tamkar senior yasan me take saqawa
saiya kama hannuta Yace kanya idar xo in nuna miki wani abu da Dady ya siyamin
Batayi musu ba tabishi har harabar gidan
Yace am sorry my aunty Ki yafe mishi banasan tashin hankalinki
Xan mishi magana Sosai akanki
Yasan girmanki daatsayinki
Tace dama wayo kamin dankar in tsefeshi
Yace aa ni na'isa in miki wayo. Fatana dai Kiyi hakuri dan Allah
Tace toh naji
Wlhi saina mishi rashin mutunci baxan hakura ba
Dafe kai RAMADAN yayi. Yayi shuru dan ya hango rashin hakurin nata axahiri
Wannan dare Sam RAMADAN bai bar qanin nasa ba yana tare dashi yana nuna mishi
tsantsar qauna
FAWAS ko sha'awa suka dinga bashi
KHAMIS ko damuwa da tashin hankaline yayi mishi yawa dan ya tabbatar da xancan
senior RAMADAN akan Ameeran da Momyn shi Tace yaje dubata
Shegiyar yarinya qiri qiri tafitoh tace tana sanshi
Wani ihu KHAMIS ya kwalla🙆🏼 ha'de da wani tsalle ya dire agaban Dadyn nashi Yace
Dady kamin rai Wlhi bana santa.
Ina skull Dady pls karkamin haka
Dadyn yayi murmushi irin nasu na manya
Yace Wlhi baxaka jawomin abin kunya ba saina maka Aure tunda kanuna shi kakeso
Atarihin KHAMIS tunda yataso da wayansa bai ta6a ginin ranar da iyayan nasa suka
dakesa ba
Amma yau sanadin masoyiyarsa yasha mari agun momynsa
Aikan tafuta KHAMIS yasa mata kuka fa'di yake mum ina Santa Wlhi kuka rabani da
ita mutuwa Xanyi
Tace toh ka mutun mana....
Taficce
Kuka Sosai KHAMIS yasa
Toh yatake ne XEE
👯 matsala kenan👯
By Hajju
[11:52PM, 13/12/2016] Rahamat Nalele 👯: R🇦H🇦M🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [11:03PM, 15/12/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
*👯TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir-*
*rahmanurrahim*
*PART 90*
Senior yayi Murmushi Bayan ya fuskanci qanin nasa yayi nisa a tafiya da kalamai
Ya ta6e baki da fa'din nima bari naji da Auntyna aransa
Lokacin SAILUBAH na chat awata sabuwar wayarta da XEE tasiyo mata 'daxu
SAILUBAH tajah numfashi fuskarta cike da annuri ta gyara kwanciya da cigaba da chat
'dinta
RAMADAN mah gyara kwanciyarsa yayi. Yana sauraran junior Wanda har lokacin bai gama
wayan nasa bah
Can yagama ya kalli senior Yace brother dawa kayi waya
Yace Auntyna SAILUBAH
Yace naga alama kam
Senior Yace alamar me kagani Yace nalura da farin cikin da nagani a fuskarka ne
Yace Hakkane 'dan Uwa
Idan ina tare da ita ina samun kaina Cikin nutsuwata
Idan kuma ina waya da ita ina tsintar kaina cikin farin ciki
Junior ya ta6e baki Yace kana Santa kenan Yace Sosai mah.
Yace toh Allah yabarku tare😊
AmEEn Senior Yace kana ya'dora da fa'din wacece shakiran da kaketa wani amsa
wayarta kamar bakaso
Junior yayi Murmushi Yace kai brother har kariqe sunanta daga furtawa so 'daya
Senior yayi Murmushi Yace sunan nata ne so sweet
Junior Yace tnx
Sunanta kenan
Ban ta6a Santa bah
Saidai ina more rayuwa da ita Sosai
Dan tasan darajata
Karuwace ada
Amma ayanxu tawace ni 'daya
Tana xama a Dubai balarabiyace ta gaske gata 'yar babba haka
Dan ayanxu xata kai 26 years
Senior yajah numfashi Yace idan na fahimceka kana harkar xinah kenan......
By Hajju
[11:05PM, 15/12/2016] Rahamat Nalele 👯: RAHAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [2:36PM, 17/12/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
*Bismillahir-rahmanurrahim*
*PART 92*👯
Yafara tunanin ta inda xai lallasheta
Aiko dabara tafa'do masa
Yacire bell 'din jikinsa ya miqa mata Yace gashi Ki xanenin dan sauri nake amma
ahannnu xakimin
SAILUBAH ta kar6a dan xuciyarta xafi take mata
Amma me😳
Kunsan ance kowane bawa da qaddararsa arayuwarshi
Wani Kaga Allah yasa mishi tsoran abinda bai taka kara ya karya ba.
SAILUBAH tabi kyenkyason da kallo kana ta kallesa tana rayawa aranta gaskiya bata
ta6a ganin 'dan iska 'dan rainin wayo kamar junior ba
😳😳😳
Abin mamaki hawaye tagani yana xubamai pls dan Allah Ki kukoreshi xan mutu
Nan taga idanshi yafara juyawa yana kakkafewa jikinsa na rawa
Yana kallan kyenkyason cike da tsoro
Aiko nan take tayi cilli da bell 'din hannunta ta bu'de furiji ta 'dauki ruwa ta
watsa masa
Ina Junior bai farfa'do ba
Hankalin SAILUBAH ya tashi. ta hango tashin hankalin da tsoran da yake tare dashi.
cikin sauri Tatashi Tace toh kayi shuru manah.
Hankicif ya 'dauka ya goge fuskarshi dashi.
Yana kallanta ta'dauki kyenkyason ta'daureshi a baqar leda tasa a abin xuba sharan
senior tarufe shi
Sannan Tace kaga nasashi Cikin nan kuma yana leda mah shikenan 🙅🏼 ko
Yayi saurin 'daga mata kai tare da xuwa gefanta ya sakar mata kiss a kumatu Yace
nagode Auntyn brother yafa'da da Murmushi akan fuskarshi
Tace kaifah 'dan iska ne
Wayace kamin kiss
Yace namiki ne dan nuna godiyata gareki bawai dan kinkai ba
By Hajju
[2:37PM, 17/12/2016] Rahamat Nalele 👯: RAHAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [10:34PM, 17/12/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
*Bismillahir-rahmanurrahim*
*PART 93*
Daga jiya xuwa yau har 'yan unguwar sunsan Auran SAILUBAH mutuwa yayi
Dan ita kanta in katambayeta cewa take mijin bame halin kirki bane shiyasa barinma
Auransa
Can wajan qarfe uku RAMADAN senior ne da FAWAS da KHAMIS agidansu FAWAS
Tana gaban mulhu kamar Kullun. Yaran Yace ana sallama dake HAMEEDA
Tace Waye
Yace wasu 'yan gayune a mota
Da sauri ta 'dauki hijabinta dake rataye a igiya
Tashige 'dakinta tafeshe shi da turare tasaka
Kana tayi niyar ficcewa......
Inna tace toh akuya me San Maza sunyi kira jiki na 6ari anfeso hijabi da turare ko
Tace aa fah Innah
Tace nayi qarya kenan
Shuru HAMEEDA tayi
Innah tajah tsaki Cikin baqin ciki Tace saiki gaya masa sakwan kawun naki
Wlhi idan bai turo iyayansa acikin sati biyu bah toh kitabbata Auran Alo ya hau
kanki.
Tace toh xangaya mai
jah tsaki innan tayi
HAMEEDA ko tayi futowarta
Sanyayyar ajiyar xuciya FAWAS yasake dan yanxu hankalinsa ya kwanta dayaji gar
Yace yauwa YAYATA dan Allah Karki bari kalma 'daya tashiga tsakaninki dashi
Tace toh
Yace batun iyayena ko xan gaya musu
Tace toh
Yace toh gayamin
Tace wani abu
Yace dabaki ganni kwana biyu bah me kikaji aranki
Tace baqin ciki da tashin hankali mana
Ya gya'da kai
Yace dama kina sona har haka
Tace Kaine farin cikin ruhina Kaine farin Cikin xuciyata Kaine farin cikin idanuna
Ina sanka FAWAS
Kana hanani bacci
Idan na rufe idona ganinka nakeyi cikin mafarkaina
Idan nabu'de hotan fuskarka nake gani ga kowane halitta idan nayi ido hu'du da ita
Idan ina aiki tunaninka yafiyin aikin nawa yawa
Sai inta kwa6a innah tata xagina
Ina sanka ina sanka ina sanka
Bansan yaushene xuciyata takamu da sanka har haka ba.
Farin ciki yacika xuciyar FAWAS Yace Allah kanunamin ranar daxan mallakeki
amatsayin matata
Tace AmEEn
In kawo maka 'dan wake
Yayi saurin girgixa kai alamar aa
Tace meyasa
Yace haka dai
Tace haka kawai
Yace naci abinci ne
Tace toh meyasa kaci Bayan nace kidenaci in xakaxo gareni
Yace mantawa nakeyi
Tace meyasa dukkan wani abu baka mantashi sai wannan
Tace eh
Ni shi nake so
Baban nata yaxuba mata ido Yace Zainab baki da hankali
KHAMIS ba sa'an Auranki bane
Yayi yaro
Kin girmeshi da shekara kusan shidda.
Kiyi tunani mana
Tayi shuru
Yace kirabu dashi kinji
Hawaye ya xubo mata. Tace Wlhi BABAH baxan iya rayuwa ba KHAMIS ba......
Gauuu mamah tafalleta da mari
Tace sai yau nasan baki da hankali. Ko kinsha giyar wake iyayansa ba yarda xasuyi
ya aureki ba
BABAH Yace koni baxan yarda ta aureshi ba.
XEE tafashe da kuka da barin falan
Mamakinta yacika iyayan nata
Tana fa'dawa gado takira SAILUBAH wacce take kwance har lokacin tana tuna junior
dana dariya wani lokacin taji tausayinshi
Gashi tana so senior yaxo tabashi labari......
XEE tajah numfashi Tace wato duk Wanda Allah ya jarrabeshi da SOO toh yagode masa
SAILUBAH ba ciwan dayafi so xafi da ra'da'di
SAILUBAH Tace hmm Allah ya futar da kowa daga matsalar da yake ciki
Tace AmEEn
Suka ajiye waya
SAILUBAH tayi dariya Sosai
Tana cikin yine senior ya shigo
Yaqare mata kallo Yace Auntyna wannan dariya haka
Tace kadai bari so maseefa ne
RAMADAN yayi Murmushi Yace Sosai
Kin fa'da San wani ne
Tace ni😳
Yace eh
Tace aa
Yace hmm dama naxone kibani labarin yanda akayi 'daxo junior yace baxai kwana a
room 'dina ba
Na tambayeshi Yace in tambayeki
SAILUBAH tagyara xama tabashi labari tiryan tiryan
Abin yaba RAMADAN tsoro tausayin 'dan uwan nashi ya kamashi
Yace toh kidena dariya dan Allah
Tace tunda nasan me yake sashi tsoro ya shiga uku aguna Wlhi
Yace kai Auntyna
Tace sai da safe Yace Aunty
Tace miye
Yace kiyafe mishi pls
Tace hmmm kabarni dashi dan saina koya mishi yanda ake bin naga
Ta6e baki RAMADAN yayi yatashi yaje yayi mata kiss ahannu
Yace bye bye gud night Tace Yah night
By hajju
[10:35PM, 17/12/2016] Rahamat Nalele 👯: RAHAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [12:18PM, 18/12/2016] Rahamat Nalele 👯: RAHAⓂ🇦T 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
*Bismillahir-rahmanurrahim*
*PART 94*
Daqar Dady da Senior RAMADAN suka lallashi junior ya hakura ya kuma room 'din
senior bayan an caje 'dakin tas an tabbatar ba wani kyenkyaso😬
Ya 'dauki minti biyu yana kallan gidan shin Ya shiga ne ko ya tura Yaro yakai
mata.......
Abbas ya dafashi Yace abokina lokaci na tafiya fah
Yayi Murmushi Yace 'dan jirani ka'dan👌🏻
Yana fa'din hakan ya shiga gidan
Yayi Murmushi Yace hmm nakamu dasan wata Amma baxan sameta bah
Abbas Yace me yasa
Yace haka dai
Yace toh basai kasamu wata ba ka.........
Abbas bai idda xancansa ba sakamakwan wata budurwa data Sha gaban motarsu......
Yayi saurin taka burki cikin 6acin rai ya fitto xai sauke mata maseefa.....
Saidai ganin hankalinta tashe shiyasa shi harararta Yace da Allah malama matsa min
ahanya
Wawiya da yanxu na ka'deki fah
Cikin raunanniyar murya Tace dan Allah Ku tamakeni wasune suke bina xasu 6atamin
rayuwa dan Allah kutemakeni........
Kan Abbas yabata amsa wata mota daxo tayi wani wawan parking a kusa dasu
Maxa hu'du suka fitto daga cikinta
Da sauri taje bayan Abbas tana fa'din kagansu ko
'Dayansu ne Yace kina 6ata mana lokaci fah
Dalla xoki shige cikin
Abbas ne ya janye junior xuwa mota da janta cikin sauri ganin mutane sun fara
taruwa
Haka suka sauketa akan layinsu Tace mah Abbas dan Allah ban number naka mana
Baiyi musu bah ya bata dan yana lura da mayataccen kallan da take bin junior dashi
Sanda tajuya junior yabita da kallo kana yajah tsaki Yace kagafah shigar da tayi
badole 'yan iska suji sha'awarta bah
Abbas dai jan motar tasu yayi yana cewa hmm sai ahankali
Ya kuma jan tsaki Yace Mai dani gida pls....
Abbas Yace tajama yawanmu kenan
Shuru junior yayi masa
🙆🏼🙆🏼wayyo ni Rahamat🙆🏼🙆🏼
Mahaifin Mubarak yasa ayima Mubarak 'din Duba na musamman cikin qanqanin lokaci dan
tabbatar da lafiyan gabansa
Likitoci sun gano mararshice tayi bala'in buguwa Amma bugun bai ta6a gabansa bah
Wannan kenan
Gidansu XEE ya fara xuwa ya sauketa kafin yaje ga gidansu SAILUBAH ya sauketa itama
Sam qin bashi damar maganarta tayi
Yace dan Allah in dawo anjima
Cikin gajiyawa da nacinsa Tace saidai gobe da safe
Xaiyi magana tayi cikin gidansu
Yayi Murmushi kawai ya tada motarsa
*Bismillahir-rahmanurrahim*
*PART 95*
Ilai kuwa. SAILUBAH na xaune tabaje a falo tana shan ice-cream senior ya cimmata
Ya xauña kusa da ita Yace my Aunty
Tace na'am 'dan Qanina
Yace waye ya saukeki
Ta kallesa ka'dan. Ta watsar batare da tace mai Komai bah
Yaci gaba da fa'din ki gayamin mana Auntyna
Cikin fusata Tace wai RAMADAN me yake damunka ne.
Saika dinga sani agaba kamar wani abana kana tirkeni akan samarina. ina ruwanka
dasu
Yayi mata shuru
Taci gaba. Toh saurayina ne
Yace yaushe kuka ha'du
Ta galla mishi harara Tace yanxu
Yace wai meyasa Sam Aunty bakya jama maxa ajii ne
Daga kin ha'du da mutum yace yana sanki sai kawai Ki lamunce masa sai kace wacce
take neman kai da kanta
Ran SAILUBAH ya6aci
Tasan ko xaginsa tayi indai akan samareenta ne bayajin komai
Dan haka tajah bakinta tamai shuru
Shiko ya nace saitayi magana
Dan haka ya ta6e baki Yace baiyi bah
Sam bai dace dake
Ina xaki kaisa da munin nan nasa
Tayi dariya Tace ina sanshi haka.
Komin muninsa yayi min
Shikenan ko
Ya harareta ka'dan xaiyi magana wayarta ta'dau qara.
Tana jinta har takatse taqi 'dauka
Can kiran yaqara shigowa. Ta'dauka da fa'din hello
Daga can me kiran nata Yace Mustafa ne
Tace ayya ya akayi
Yace muna 'kofar gidanku dan Allah karkice baxaki fittoba
Tace aiko baxan sami fitowa bah
Dan Allah kayi hakuri kaxo gobe
Tana fa'din haka ta kashe wayan gabaki 'daya
RAMADAN daya gama jin Komai
Sai yayi kalar sanyi Yace Aunty
Ta kallesa
Shi kuma wannan Waye
Tace Mustafah
A ina kuka ha'du
'Daxu. Tabashi amsa
Yace kut😳
Ta kallesa da mamakin yanda yaxaro ido
Tace menene
Yace ina xaki kai maxa biyu alokaci 'daya
SAILUBAH tagyara xama Tace kaga wannan Mustafan kyakkyawa ne kuma da alama me
ku'dine gashi nutsattse na lura baxaiyi girman kai ba....
Naji ina sanshi da gaske RAMADAN wannan shine maganar Gaskiya
Katayani da addu'a Allah yasa mutumin kirkine na tsaidashi amatsayin mijina.
RAMADAN yayi wani shegen Murmushi Yace ai daga jin muryarsa nasan wannan ha'daddene
Tace Ashe kaji
Yace Sosai mah. Amma baki bashi lokacin daxaixo goben bah
Tace inna kunna wayata anjima ya qara kira na gaya masa
Yace Yauwa inkin gaya masa saiki gayamin dan nagansa
SAILUBAH takallesa Tace aa basai ka gansa bah
Yace Allah ba abinda xai fa'ru bayan namiki alqawari ko kin manta ne
Tace hmm ban yarda dakai ba kabarni kawai
Yace haba Aunty yanxu yadace wanda yakesan Auntyna yaxo naqi xuwa gaidashi
Tace hmm makircinka nake jin tsoro RAMADAN
Indai akan samarina ne kota ina 6ullomin kakeyi. Gwara kawai kasha xamanka Nagode
Ya matso kusa da ita da 'daukar ice-cream 'din nata ya fara bata tana Sha
Yace Allah Auntyna wannan karan ba abinda xanyi kiyarda dani.
Tace ka'dau alqawari
Yace eh
Tace toh shikenan
Sanda ya gama bata tas Sannan Yace toh shi wannan daya saukeki yaushe xai dawo.
Tace nadai CE mai da safe
RAMADAN yajah numfashi Yace bara naje nayi Sallah in rokwan miki Allah ko
Tace yauwa Qanina
Ya shafi gefan fuskarta Yace Aunty fuskarki da'din ta6awa
Ta harareshi
Yajanye hannunsa yana cigaba da cewa ina sanki Auntyna
Tace nima haka 'dan Qanina
Ya tashi Yace toh bye bye
Tace kaci abinci fah Yace toh da ficcewa
Tabishi da kallan jin da'di
Ya kalli junior dake danne danne a waya Yace nadawo 'dan Uwa Yace ta gayama Waye
shi
Yace ai dolanta
Yace toh Madallah
Senior Ya 'dan jah tsaki ka'dan Yace harsy biyu ne fah......
Junior ya kallesa yajah numfashi Yace wai danma kanada nutsuwa ne shiyasa har yanxu
takasa ganoka.
Yace kai dai bari. Ina ganin harsai na mallaketa nayi ram da ita xata ankare da
soyayyata
Junior yayi Murmushi Yace mai xai hana in gaya mata dan tadena cutarmin dakai
Yace barta kawai mutafi ahakan xan gyara mata tunaninta
Junior yayi dariya Sosai Yace wayaga LEEKITAN ZUCIYAH
Senior ya camke da sauri Yace inji AUNTY RAHAMAT tace yaxo ya gyara tunanin
NUFAISAT da TAUDAT.
A tare suka bushe da dariya😂
Washe gari KHAMIS ne yafitoh daga wanka yasaka kayansa wa'yanda suka kar6esa ya
shafah mai 'dinsa me da'din qamshi. Ya feshe jikinsa da turare
Kana ya kalli agogo yaga kusan sha'daya 11:00Am haka kawai yakeso yau yaga
taurayuwar tasa yanxu......
Cikinsa ne ya mur'damai da sauri ya fitoh falo ya addu'ar Allah yasa yanxu mum 'din
tasa ta ajiyemai breakfast 'din nasa
Yana duba dining ko yaga Komai da xafinsa yaxauna yaci ya koshi. Sannan ya nufi
falan mum 'din......
Kaga Dadyn KHAMIS mukai sadakin yarinyar nan kawai amasa Auran nan da wuri in yaga
haka ya ha'kura da Zainab 'din
Dady Yace shashaba bah. Ko ina xaikaita oho
Momy tayi dariya Tace hmm bar yaran nan Dady kana rainasu sai subaka mamaki
Yace ai na hango hakanne shi yasa hankalina ya tashi akansa sai ya iya jamin abin
kunya
Tace aikuwa
Yace toh yanxu xanje gidan Yayan Madi na gaya masa Komai ko xuwa gobene sai akai
sadakin ko
Cikin murmusawa Momy Tace hakan shi yafi.......
Wani qara KHAMIS yasaka ya shiga 'dakin da sauri da durquwa gaban iyayan nasa Yace
pls mum Dad kutemakeni Wlhi bana santa nidai Aunty XEE nakeso....
Momy tajah tsaki Tace kafita saga idona fah KHAMIS in rufe
Aiko sai yafe da kuka Sosai yana fa'din nidai Wlhi bana Santa Zainab nakeso kuma
aka 'daura min Aure da wannan narantse wahala xataci aguna.😰
Momy da Dady suka xubamai ido ganin irin kukan da yake. Sam sai suka kasa cemai
Komai
Can dai Dady Yace sai dai kabata wahalan dan saimun aura maka ita
Kuma Aure tsakaninka da Zainab babu shi
Tashi KHAMIS yayi hankalinsa tashe ya bar 'dakin
Yayinda jikin Momy yayi. Batasan abinda xaisa ma KHAMIS 'dinta kuka Amma duk da
haka itadai batasan Auransa da XEE
Aiko ko cikakken minti biyu basuyi ba saiga wannan Alhajin daya sauke SAILUBAH jiya
yaxo yayi parking motarsa a'kofar gidan nasu
Suna kallo yaciro waya yayi kira kafin ya ajiye
Aiko kamar yanda suka xata ita ya kira hakanne. Dan sai Ganin SAILUBAH sukayi
tafitoh tana bah me gadinsu Amarni ya bu'de get tana da baqo.
Nan tajanyo kujerun roba da suke harabar gidan tasaka Su a'inda ya dace kafin
takoma cikin falansu
Senior yayi Murmushi yace wannan ya samu shiga da yawa
Junior ya ta6e baki Yace kar dai ka barta ta xaqe da yawa dan komai xai iya faruwa
Senior Yace ban gane bah
Junior ya kallesa da kyau Yace idan kabari hirarsu tayi tsayi. Ina tabbatar maka
xata baka mummunan labari
Senior Yace ko
Yace ko shakka babu. Da maida kallansa cikin harabar gidan wanda har SAILUBAH
tafitoh cikin kyakkyawar shiga tajera abin Sha agaban Alhajin wanda ya kame akan
kujerar rubar kana ta xauna tana fa'din Barka da safiya Alhaji
Yace barka SAILUBAH da fatan kintashi lapia
Tace lafiya lau
Ya akayi kasan sunana. Kuma kasamu number ta
Yace nasani ne lokacin da qawarki XEE tace miki toh SAILUBAH Allah ya tashemu
lapia.
Number mah agunta nasamu dan jiya daga nan gidansu nakoma
Tace ayya
Yace wato SAILUBAH agurguje nake akan San da nake Miki
Ina sanki sosai. na yaba da tarbiyarki da halayanki. dan nasamu bayanai akanki
Sosai tsakanin jiya da yau.
Sai Naji naqara kwa'dai tuwa daki xama mata agareni.
Sunana Alhaji Auwal me katifah
Inada mata biyu. Xanso ki xama ta ukunsu idai kin iya da al'amurana to shikenan kin
rufe musu qofah ba xuwanta hu'du
Ina da yara goma cif.....
Yace toh maixai hana ka turani in bashi tsoro dan nalura ya fara tafiya da ita
bakaga har Murmushi take ba.
Xuwa anjima xata fara dariya
Kaga daga wannan lokacin xuciyarka xata iya samun matsala
Senior yayi tsaki yana bin SAILUBAH da muguwar harara batare da tasan yanayi
ba.......
Senior yayi murmushin yaqe Yace yanxu idan naturaka mai xaka mata
Yace abu mai sauqi aguna Amma agunta me xafi
Yace toh jeka.
Junior yayi murmushin jin da'di ya juya yabar barandar
Senior ya bishi da kallan qauna
Yana kallo ya shiga gidansu SAILUBAN
Alhaji ya gyara xama Yace yanxu kin kar6eni a matsayin wanda xaki tsaida matsayin
Mijinki.......
Shuru SAILUBAH tamai ganin junior Yana nufusu cikin Murmushi tunaninta senior ne
Alhaji ya kalli SAILUBAH data sake baki da tana kallan junior wanda ko kallanta bai
qara yi bah
Yace Amma a binciken danayi banji ancemin tanada miji ba.
Kuma nima idan ina ganinka xan iya yin Komai dan qetarar da Auran kawuna daga
tanga'din da takesan yayi
Alhaji Auwal me katifah yagoge gumi ya tashi yana kallan SAILUBAH Yace kima
iyayanki biyayyah hakan xaisa kidace duniya wala hira
Yana fa'din hakan yanufi barin gidan
SAILUBAH na kallansa harya ficce daga gidan cikin damuwa
Kana takalli junior Wanda duk tunaninta senior ne Tace mexance maka
Ya 6allah mata harara dayi mata kallan raini kamar yanda yasaba..
Yace oho miki
Nan ta tsaida idanta akansa Sosai taga 'dan iskan nata ne.
Ashe ba senior bane
Junior ya kalli sama inda senior yake. Yaga yana nan yana kallansu
Hakan yasa ya mayar da abinda xuciyarsa ta kisa masa yayi mata ayanxu
Amma yasa aransa Wlhi saiya aikata mata shi da ita. Qila daga wannan ranar tadena
kiransa da 'dan iska.
Yace xan hukuntaki ne saina baki mamaki wawiya kawai me tunanin jarirai
Ya qarashe da nuna mata senior da hannu Cikin raini yaciga da cewa shiya turoni
Aiko SAILUBAH Suna ha'da ido da senior yayi saurin ha'de hannunsa biyu 👏🏻 alamar
ban haku'ri da furta kalmar Sowie my Aunty
Junior ya fara tafiya yana cewa baxan fa'da b. Idan kin matsu da San ganin nasa Ki
kirasa mana. Ko angaya miki ni sakaran namjine da qaramar mace kamarki xata aikeni
kuma naje
By Hajju
RAHAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [12:28PM, 23/12/2016] RAHAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
*TASU SALAN SOYAYYAR*👯
*Bismillahir-rahmanurrahim*
*PART 96*
Lura da hakan da yayine yasashi cewa dan Allah kiyi hakuri Aunty
Wlhi baxan qara bah kinji
Yafa'da dasan tayi mai magana
Amma sam taqi
Saiya marairaice mata kamar xaiyi kuka Yace Aunty yunwa nakeji
Dan haka saiya dinga 'daukawa yana direwa agabanta 'daya Bayan 'daya har yagama
Kafin ya xauna agabanta ya ha'da tia ya 'dauki dankalin 'daya Yace toh bu'de
bakinki in baki
Sam batayi musu bah yadinga bata Komai tanaci tana kallansa
Sanda taji taqoshi Tace toh kaima kaci mana
Yayi Murmushi Yace naci 'daxo
Tace saika rantse xan yarda Yace narantse miki
Shuru sukayi na'dan wani lokaci. Candai Tace nahakura da samari RAMADAN tunda na
fuskanci har abada baxaka barni dasu bah
Yace kiyi hakuri Auntyna xan samu miki daidai da xa6inki me kyau me ku'di me aji me
meshakaru
Kallansa kawai tayi
Yaciga da fa'din hmm Auntyna...
Tace menene
Yace shi Mustafan da kukayi waya dashi jiya xaixo ne anjima
Tace xaka koreshi ne
Yayi Murmushi damarairai cewa Yace eh.
Dan bana sanki da kowa Auntyna
Janyo wayarta SAILUBAH tayi Tace tamiqa masa Tace xakaga Mustafah aciki daga nan
saika 'dora makircin naka akansa
Ya kar6a a sanyaye ha'de da jin tausayinta
SAILUBAH na kallo yayi blocking number nashin Sannan ya kalleta Yace akwai wani
Mamaki Al'ajabi ya cika SAILUBAH tayi shuru kawai tana kallansa
Ya matso kusa da ita.
Kifa'da man Aunty
Sam rasa me xatace mishi tayi
Ganin da tayi ya kafeta da ido Yana yana aika mata da furgitaccen kallan nasa
shiyasata cewa baga wayan ahannunka ba. Kaduba mana
Yayi Murmushi da dora mata wayan kan cinyarta Yace aa basai na duba ba dan na yarda
dake. Ya qarashe da dire kallansa a bakinta
Tace RAMADAN
Yace na'am
Tace kashirya kalaman da xaka gayamin wanda xan fa'dama Abbana daxaran wa'adin daya
saka min yacika
Sosai ya qara matsawa kusa da ita yana Murmushi yasaka hannunsa yana shafa fuskarta
Yace Aunty narigada na da'de shirya kalmomin da zan gaya miki kigaya masa
Fatana dai kimin alqawarin kinbar kula kowane 'da namiji kenan
Tace hmm aitunda Nace ma na hakura kaima kasan nasallami namarin kenan
Amma kasani idan lokacin yayi baka bani gamsasun kalmomi ba. Kasani nabarka kenan
har abada....
Tasan nacin RAMADAN sarai tunda yacire kunya ya gaya mata sai yayi xai barta.
Dan haka tanunanai goshinta Tace oya
Ya girgixa mata kai yana kallan bakinta
Nan take tagane a inda yakesan yayi mata. Dan haka tamai banxa
Shima shuru yayi mata yana qarema fuskarta kallo lungu da saqo
Kunsan ance kallo gubana
Dan SAILUBAH ji tayi duk jikinta yasake ta'dago suka ha'da ido tagalla mai harara
Tace kafara damuna da kallo fah
Yace toh inyi miki sai natafi.
Banxa tamai
Shiko yayi saurin kai bakinsa Cikin nata ya sakar mata shock kiss me tafiya da
jinin mutum na wasu sakanni
Sannan ya janye kansa daga gareta yana cewa bye bye my Aunty
Da kallo tabishi harya ficce. Tasauke ajiyar xuciya Tace nashiga uku😰 ni SAILUBAH
me yake damuna akan RAMADAN.....
Wayarta CE tayi qara tana ganin XEE CE tayi saurin 'dauka
Tana cewa Qawata
XEE Tace abokin Mustafan nanne wanda muka ha'du dasu jiya shine ya kirani wai
qaninki yakira mustafan Yace mishi wai Auranki nanda wata biyu
Tace hmmm kadai bari XEE dan agabana RAMADAN ya kirashi yagama yimin qarya bayan
junior qaninsa yagama yimin
XEE tawaro😳 Tace qiri qiri agabanki
Tace Wlhi XEE tamkar ya tofeni da addu'a Nace mai na hakura da samarin tunda na
lura har abada baxai barni dasu ba.
XEE tayi salati Tace Lalle an gaida ke.
Yanxu ya xakiyi da Abban naki
Tace oho fah
Na dai CE mishi ya shirya kalmomin daxai gayamin wa'yanda xan tunkari Abban dashi
Yace wai yarigada ya gama shiryasu
XEE tayi dariya Tace hmm Wlhi RAMADAN ya gama samunki SAILUBAH. Gashi yafitoh da
manufarsa qiri qiri akanki. xai juyaki kamar waina. Kuma gashi qaramin yaran da
kika raina. Shiyake qoqarin lalata miki tunani
SAILUBAH tajah tsaki Tace ina ganin fah jifana yake da addu'a dan kinsan gwanine
wajan addu'a
XEE Tace aikema ba baya bah
Saiki bishi da taki
Tace Xanyi qoqarin yin hakan
Ni yanxu damuwata 'daya kar lokacin da Abban nawa ya ibam min yacika RAMADAN 'din
ya tiqani da qasa
XEE tayi dariya Tace shegen yarone ya iya da kansa. Sai kiga kuma ya baki mamaki
xuwan lokacin
By Hajju
[12:29PM, 23/12/2016] RAHAⓂ🇦T Nalele👯: R🇦HAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [11:17AM, 17/12/2016] Rahamat Nalele 👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
*Bismillahir-rahmanurrahim*
*PART 91*👯
Yace Dady😳
Yace my son
Shiru senior yayi
Can yatashi ba tare daya gaba breakfast 'dinba xai fita
Momy tariqe hannunsa Tace katemaken kayi break 'dinnan. Kafah dena wasa da cikinka
Yace hmm xanje gun Auntyna naci ne
Tace toh me Aunty daga can xaka wucce ne
Ya turo baki dacewa eh
Tasaki hannunshi ya fitta....
Junior ya bishi da kallo da 'Yar dariya ka'dan
Dady Yace kaima ina xuwa gareka
Shuru junior yayi
Can Yace Nagano Dady Jibiril ne ya kashe mana mahaifinmu.......
Waro ido Dady yayi Cikin shaqewa Yace bashi bane my son
Junior yayi Murmushi Yace Wlhi shine
Ni naji da kunnena yana gayama wani
Shuru Dady yayi
Can Yace banasan kace xakayi wani abu akai
Yace naso kasheshi nadai fasa dan bansan abinda Allah yake nufi ba da har yabari
narayu ahannunsa ya kuma tusa masa qaunata
Momy Tace kayi kyan tunani
Allah yayi muku albarka
Yace Amiien
Dady Yace toh yanxu xansa a binciko muku dukiyarku ta Dubai da Kuwait da America
Muji ya suke
Junior ya tashi yana cewa toh ni bara naje 'daki nayi wanka kafin wani abokina yaxo
Momy Tace toh
RAMADAN senior ko saka SAILUBAH yayi agaba yanata mata shagwa6a da kashe mata jiki
Ya kama hannunta Yace my Aunty kinji wai Dady Aure xaiyi min a this year ko
SAILUBAH tayi dariya Tace toh miye 'dan Qanina ai gwara ayi maka dan kadena xuwa
yawon club
Kasan har kuka nakeyi idan nasan katafi can
Kallan da suke yima junansu yayi yawa. Hakan yasa xuciyar SAILUBAH tafara bugawa
Tamkar yasan xuciyar tata bugawan take...
Yace Aunty I luv u......
Wata sanyayyiyar ajiyar xuciya SAILUBAH ta sauke da Murmushi akan fuskarta takai
bakinta kumatunsa ta sakar mai kiss
Abinda yasaba ji shidai yaji
Taqara bashi a kumatu.
Yana kallanta
Tace nagode Qanina
Tashi yayi yana Murmushi Yace toh ni nayi skull xan duba miki Komai gobe sai
mutafi tare ko
Tace nifah nagama skull
Yace yi hakuri mana mu'danje gobe
Taturo baki ka'dan Tace kanasan takura min ko
Yace aa my Aunty
Tace toh Allah ya kaimu
Ina wannan mara kunyan
Yace 'dan uwana
Tace koma Waye
Yace yana 'daki yace ma yana gaidake
Tace kafiya kare mutum
Yayi Murmushi da bata kiss ahannu yafita tabishi da kallo.
Xuciyarta cike da San qanin nata
Yana fitta yakira KHAMIS da FAWAS Yace musu gays akwai matsala fah
FAWAS Yace nafi kowa shiga cikinta xa'a rabani da HAMEEDA
KHAMIS Yace hmm muha'du a skull pls xan rasa Aunty XEE.....
SAILUBAH ko RAMADAN na fitta da minti goma ta'dauki gyalanta sai 'dakinsa dan
tatashi da abinda junior yayi mata jiya
Xuciyarta na gaya mata gwara tacimishi mutunci ko tasami nutsuwa
Aiko tana turo 'dakin tagansa yana Reding wani novel
Suka kalli juna
Nan take xuciyoyinsu suka bada dam fa'duwar gaba tabayyana a fuskokinsu
Taqare mishi kallo tsaf kana Tace naxo inja maka kunne👂🏻kaji da kyau ni ba
sa'arka bace. Naga iskanci da rashin kunya Suna maka yawo akah. Toh ni 'dinnan xan
sauke makasu
Mara mutunci kawai har xaka kalleni kace baxaka bani kowane irin matsayi na SOO bah
Ni sa'arkace daxaka bari baxan tunaninka ya saka furtamin wannan Kalmar.
Ko ajikina Kaga anrubuta ina buqatar soyayyar qaramin Yaro 'dan iska mara kunya
kamarka ne iye tambayarka nakeyi
Toh na yaushe
Bayan banxar xuciyarki da wawan tunaninki ya kasa wayar miki da kai ki fahimci
kinda'de da fa'dawa soyayyar qaramin Yaran
Kuka take Sosai dan tunda uwarta ta haifeta ba'a ta6a cimata mutunci irin wannan ba
Kuka take hawaye na xuba mata.
xan cikan sa nayi mata yawo acikin kwanyarta
By Hajju
[11:19AM, 17/12/2016] Rahamat Nalele 👯: RAHAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [3:44PM, 24/12/2016] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
*Bismillahir-rahmanurrahim*
*PART 97*
FAWAS ne yasaka Dadynsa agaba yana xuba mar shagwa6a fa'di yake. Dan Allah Dady
kuje gidansu HAMEEDA da gaske xa'a 'Aurar da ita ga 'dan uwanta.
Banaso na rasata
Dadyn nasa ya kallesa Yace katabbatar yanda kake santa haka take sanka Yace Wlhi
Dady fiye da yanda nake Santa take sona
Dadyn ya ta6e baki Yace ai shikenan.
FAWAS ya rungumi Dadyn nasa Yace I luv u Dady
Yace me 2 my son
Yace toh yaushe xaku
Yace gobe
Wani tsalle FAWAS ya daka yana murna Yace Allah ya barmin kai my Dady.......
Ni kuma ya kashe maka ni ko
Momy tafa'di hakan tana shigowa room 'din
Xuwa FAWAS yayi Yakama hannunta yayi mata kiss. Yace idan kika tafi Momy nima binki
Xanyi
Yana fa'din hakan yabar room 'din dan yaga fuskarta a murtuqe yana tsayawa dogon
magana qila ta canjama Dadyn nasa ra'ayi
Taxauna kusa da Dadyn Tace ina rokwanka da Allah karka biyema banxan tunanin FAWAS
Akan me xaije ya 'daukomin 'YAR QAUYE ga 'YAN BIRNI masu aji yaje ya kwasu mana
wahala
Gaskiya ban yarda da wannan Auran nasa bah
Dan haka kawai naji natsani yarinyar
Dadyn yajah numfashi Yace kiyi hakuri Momyn FAWAS baxan iya barin 'dana cikin
damuwa ba
Shi ka'dai Allah yabani ina sanshi bana San tashin hankalinsa
Tunda Yace yaji ya gani yana Santa ni kuma xan xanje ga iyayañta dan Aura masa ita
Ke in banda abinki idan ya Aurota basai Ki maida ita 'Yar birnin bah
Shuru Momyn tayi dan tasan tunda yace xai Aure masa ita tatabbata baxai fasa ba
Nan taji wata tsanar HAMEEDA ta kamata cikin ranta
Ta kuma sa aran nata xataci ubanta inhar tayi kuskuran yarda ta Auran mata 'da....
Farin ciki fal xuciyar FAWAS yake shiri dan kaima abokana yan nasa labari
Sosai ya shirya cikin shigar qananun Kaya ya 'dauki wayarsa yana niyar kiran
KHAMIS dan suha'du gidansu RAMADAN....
KHAMIS ko fa'dawarsa gado bayan yagama waya da RAMADAN bacci yayi abinsa bai samu
tashi ba har sai kusan qarfe 1:20pm
Ya sake wanka yayi Sallah Sannan yahau shirya kansa
Yana feshe jikinsa da turarene yaga kiran FAWAS ya shigo wayar tasa
Nan KHAMIS ya ibi ku'di da'dan yawa yana tuna jiya ya hango jakar tauraruwar tasa
ba ku'di
Ya fitto falo ne yaga Dad 'din nasa da mum Suna cin abinci
Ya kallesu ka'dan Yace barka da ranah mum Dad
KHAMIS ya kalli direban gidan nasu Wanda yake kai Momy unguwa Yace yau banajin fita
da mota pls kaini gidansu RAMADAN
Yace toh ranka ya da'de
Senior RAMADAN da junior ko wani Kaya suka saka iri 'daya Wanda ya bala'in kar6arsu
Dadyn nasu ne ya kawo musu
Duk iya ha'duwarka idan kayi tuxali dasu saikaso ka qaraci kalanka akansu
Senior da junior sun ha'du iyakar ha'duwa
Baka isa ka banbance tsakaninsu waye kasani bah
Kamar tasu ta6aci
Abu 'dayane xai saka gane waye wannan waye wancan shine wayewarsu
Junior yafi senior wayewa nesa ba kusa ba
Dan daga idanshi da kallansa xaka gane hakan shiyasa yakejin kansa as big gay
Junior ya kalli 'dan uwan nasa Yace 'daxo kada'de agun Auntynka Allah yasa dai ta
yafe maka
Yayi Murmushi Yace ai bayanda xatayi dani 'dan Uwa dole ta yafemin
Junior yayi Murmushi Yace salan soyayyarku tana burgeni Sosai brother.
Idan kuka xama ma'Aurata abin xaiyi da'di da bada sha'awa.
FAWAS ya xauna kusa da junior yana bashi amsa da cewa aikuwa kayi gaskiya
Senior Yace yadai
Yace kaidai bari
Yau ina cikin farin ciki over
Senior Yace kamar ammaka albishir da cewa gobe HAMEEDA xata xama mata agareka
FAWAS yayi dariya Yace kusan haka
Nan ya kwashe yanda sukayi da Dadyn shi ya gaya masa
Junior yayi Murmushi Yace angama da shafinka Saura KHAMIS da brother
FAWAS yayi Murmushi Yace aikowa danni yanxu 'dan tayasu addu'a ne
Senior yayi yaqe Yace hmm kunsan Auntyna ahannuna take sai yanda nayi da ita
Ina tabbatar muku har ayanxu nafiko kwanciyar hankali a soyayya
FAWAS ya 6ata fuska Yace ban gane bah
Senior yayi dariya Yace nufina kai momynka bata lamunce maka ba.
Ni kuwa fah😳
ina yin ihu na kwanta ciwon qarya ayanda Abban Auntyna yake kan dukin xuciya da ita
Nace ita nake so xai Auramin ita.
Yace baxata CE ba
Saidai xata ban wahala Sosai 👌🏻
Tana kallo suka shige mota junior ya rufe yana fa'din saisun dawo suka ficce daga
gidan
Aikine da Momyn
xatayi wasu baqi 'yan uwanta shine takesan Su ha'da musu abinci merai da lpy
Kafin sufara SAILUBAH Tace bara na'dauko wayata agida Momy Tace toh kiyi sauri
Tace toh
Direct SAILUBAH gun megadin gidansu tayi Tace BABAH megadi kasamo kyenkyasun Yace
eh. Yamiqa mata Su a baqar leta taduba taga sunkai biyar tayi murmushin mugunta
Tace nagode Sosai
SAILUBAH dai shuru tamai tana jin rashin kunyar da yake xuba mata
Bata ankare ba sai ganinsa tayi agabanta Yace waye 'dan iska.....
R🇦HAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [5:33PM, 25/12/2016] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
*PART 98*
Yanda yaga tana qoqarin sakar masa wanine shiyasa shi runtse ido. hawaye ya xubumai
Yace AUNTY..... Dan Allah kibarni haka....
Cak SAILUBAH tatsaya dan yanda ya ambaci sunan nata saitaga kamar senior ne yake
rokwanta....
Tayi shuru....
Jin shurun yayi yawa ne shiyasa ya bu'de idansa ya sauke akanta
Ta hararesa dayin kwafah Tace kaci darajar Yayan ka
Tafa'da da ficcewa .
Su senior ko direct gidansu XEE suka nufa Saidai KHAMIS yayi mugun gani dan sun
tarar da ita XEE 'din tana hira da Ameer
Wato abokin Mustafan dayaso SAILUBAH
Ikwan Allah kuma shima xuwanshi kenan
Tunda XEE ta hango motar RAMADAN tasan KHAMIS na cikin motar
Nan take sai hankalinta yakaso gida biyu
Sam sai tadena jin me Ameer 'din yake CE mata
KHAMIS dai shuru yayi musu danji yayi xuciyarsa na masa xafi kuma tana bugawa fat
fat fat
Nan take hankalinsa ya tashi
Ya qurama Ameer 'din ido yanaso ya hango me tagani atare dashi dahar yaburgeta
yasata tsayawa dashi....
Bai hango Komai bah. acewarsa sai muninshi daya gani da kuma rashin dacewarsu
😬😬😬
Cikin 6acin rai ya bu'de motar ya fitoh RAMADAN Yace kayi aiki da hankali 'dan Uwa
danna lura da yanda hankalinta ya bar kansa yayo kammu
KHAMIS yajah tsaki Yace story kenan...
Atare FAWAS da RAMADAN suka samai dariya. Yana jinsu ya sharesu
Ameer Yace eh
Yace toh itadin ta Yayana CE
Dan haka kabarta kawai
Ameer yayi Murmushi Yace naga alama samaree
Danga kishi na yawo a kwayar idanka
Yace nifah ba neman maganarka nake bah. Kawai kabar nan
Saura sati 'daya bikinta Amma kawani xo kana san ka 6ata mata tunani
pls Malam jeja da Allah
XEE taqurama KHAMIS ido tana hango maseefar kishin da yake mishi yawo a fuskarsa
FAWAS da RAMADAN sun fahimci meyake damunsa kishi. dan haka sukaqi kulasa Sai
hirarsu sukeyi har suka iso qauyan takai
Kamar Kullun tana cikin hayaqi innah na surfah mata bala'i dan yau tunsafe take
mata shi
Dan kawai tayi mata asarar tulu wajan ibo ruwa......
Innah taqara katseta da cewa. Kisan yanda xakiyi kisamammin ku'din tulu na
Toh HAMEEDA Tace mata
😳😳
Atare shi da ita suka waro ido
Dan harga Allah tunaninsa axuci yafa'di xancan
Ashe abayyane ya fa'deshi
Tace LA LA LA 😳
Dama kaima irin 'yan iskannanne wa'yanda nake ganinsu a film irin turawan nan
Cikin ankarewa Yace nima wani naji yagayama budurwarsa acikin irin film 'din
FAWAS Murmushi yayi ya shafi gefan fuskarta Yace baxan qaraba YAYATA shikenan
Ta 'dagamai kai da qara turo bakin
Yace Allah in baki dena turowa bah. xan qara fa'da
Ta hararesa Tace toh kaqara mana
Allah sai in denah kulaka
Ya waro ido 😳 da Murmushi Yace kika dena kulani ai na shiga uku na banu
Yanda ya xaro idan shiya bata dariya Tace nima ai nashiga ukun
dan nayi gangancin da xuciyata taxugani nadena kulaka. Na tabbatar saina kwanta
ciwo
Ya qara shafar fuskarta Yace toh YAYATA ga wannan nina tafi bye bye ta kar6i ku'din
tana cewa karka kalli kowace mace dan Allah Yace toh YAYATA
Wayar KHAMIS tayi qara yana dubawa yaga tauraruwar tasace XEE. Yajah tsaki dan
baidena hangota da Ameer bah. Wanda hakan yake qara sa xuciyarsa jin xafinta.
Yaqara jan tsaki batare daya 'dauka bah. Yace xanyi maganinki ne
RAMADAN yayi Murmushi Yace pls ka 'dauka
Yace Wlhi baxan 'dauka bah saina hukuntata.......
By Hajju
R🇦HAⓂ🇦T
[5:33PM, 25/12/2016] R🇦HAⓂ🇦T.
[20/03, 17:09] 80k: [12:17AM, 27/12/2016] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
*PART 99*
FAWAS yayi dariya Yace 'dan iska karka 'dauka mana natabbatar yau dai baxayi baccin
farin ciki ba
Yace mexai hanani yi
Yace dan baka tsaya kaji kalmominta ba
Tsaki kawai KHAMIS yayi Sannan yama kashe wayarsa gabaki 'daya
_______
Kusan qarfe goma Sha 'dayane na dare duk Suna tare yau club xasu
Junior na kallansu yanajin hirarrakinsu
Fawas ne mecewa Wlhi ba abinda nake sha'a ayanxu irin kiss
Senior Yace Shege HAMEEDA ta rikitaka kenan
Yace hmmm naso in rage xafi da Aymana
KHAMIS yajah wani dogwan tsaki.....
Atare senior RAMADAN da FAWAS suka kwashe da dariya
FAWAS Yace dallah Malam ka dememu da tsaki. Idan kana San kwanciyar hankalinka
kabu'de wayanka mana
RAMADAN Yace bar 'dan iska karya bu'de yata tsakin.
FAWAS Yace ni tausayin Aunty XEE nema ya kamani Wlhi.
RAMADAN Yace nima haka. Nasan yanxu tanacan cikin damuwa ya hanata samun
nutsuwarta......
Da 6acin rai KHAMIS Yace lokaci na tafiya in baxa kuje ba nayi gida
Suna tafiya acikin motane junior Yace dan Allah brothers a ina xan sami kuliya
Da sauri senior Yace kuliya....
Yace eh
FAWAS Yace me xakayi da ita
Yace kawai inasan inyi amfani da itane wajan ba wani abokina tsoro
FAWAS Yace momyna tana da ita in ba damuwa gobe xan kawo maka
Yace Yauwa nagode
Senior Yace Auntyna tana jin tsoran kuliya Sosai dan Allah 'dan uwa karka bari
taganta pls
KHAMIS yayi dariya baice Komai ba
FAWAS Yace ita da Aunty XEE bansan Wanda yafi wani bah
Senior Yace tafi Aunty XEE tsoranta kamanta itafah sumewa takeyi
Gwara Aunty XEE xata iya ganinta tagudu
Itafa👈🏻
Kaima Kasan Saidai axo asameta axube
Junior yayi wata shegiyar dariya Yace hmm Allah yakaimu gobe
KHAMIS Yace AmEEn
Washe gari
Da misalin qarfe 2:30pm XEE ce da SAILUBAH suke wajan shaqatawa dan shan ice-cream
Sosai suke cikin jin da'din wajan
Yama hargixaki XEE danga damuwa nan tana yawo ajikinki tako ta ina
Cewar SAILUBAH
XEE Tajah tsaki Tace damuwata ya bu'de wayansa. 'dan iska yaqi bu'dewa
XEE tagirgixa kai Tace ina..... Baxan iya sharesa bah gaskiya
Qarfe uku daidai suka ha'du dan xasu taya wani abokinsu murnar cikarsa shekara
ashirin d'aya
Senior Yace ka kalli fuskarsa man. Xaka hango tarin muguntar da take fuskarsa
Dan tunda kabashi kuliyar nan yaketa Murmushi
KHAMIS Yace toh ina ruwanka
Yace nima ban meyasa na damu ba saidai haka kawai naji gabana yana fa'duwa akan
wannan ramukwan da yake sanyi
Sanda ya bada taxarar rabin awa ya tabbatar da tafiyansu sunbar gidan. Sannan
yafito da kuliyar ahannunsa yanufu gidan nasu SAILUBAH wanda ita da XEE dawowarsu
kenan kamar yasani......
Ya shiga harabar gidan kenan saiga matar baban SAILUBAH tafitoh. Da alama unguwa
xata. Ya gaisheta cikin ladabi. Ta kallesa da mamaki Tace yau Kaine da kuliya
RAMADAN😳
Ko kamanta Auntyn taka bataso
Junior yayi Murmushi ya Sosa qeye danya San tunaninta senior ne
Yace eh mamah lefi tamin
Tace tab aiko Suna falo ita da XEE Amma dakayi hakuri
Yace Karki karyarmun da xuciyar mamah.
Tace toh aishekenan. Tafa'da taficcewa tana rayawa aranta wane Babban lefi SAILUBAH
tayi masa daxai hukuntata da abinda yake sumar da ita
Abin da yasata yin hakanko shine. Kamar ance takalli bayan junior tayi hu'du da
kuliya.... Shiyata kwallah qara tadire akofar 'dakin SAILUBAH hakan bai mata bah
sanda tashige ciki ta danno sakata.
SAILUBAH tabita da kallo kana takalli junior. Ya 'daga mata gira Yace ta kankare ne
Tace Dame
Yace jiya kinsani suma sau biyu ba tausayawa ko
Gaban SAILUBAH yafa'di jin kukan kuliyar da taji
Cikin marairaicewa Tace pls SADEEQ junior dan Allah karka bari in ganta sumewa
xanyi
Yayi Murmushi Yace ke kin"isa kisani kuka na barki kixauna lafiya
Junior ya qarasa shiga falan ya yayyafah mata ruwa tajah numfashi tabu'de idanta
Yayi Murmushi Yace nayi alqawarin saikin suma sau 4
SAILUBAH tasamai kukan shagwa6a Tace dan Allah.....
Basu da'de da shiga gidansu abokin nasu ba. Senior RAMADAN yaga kiran wayar Auntyn
tasa
Ya 'dauka Yana cewa Auntyna......
Yaji shuru nan yaqara volume 'din wayan
Senior ya rumtse ido gabansa yafa'di dan yasan tsoran kuliya irin nata
Senior RAMADAN yajah numfashi yana tafiya asalan yanda take maganarta kamar wata
baby
Yace pls Aunty kinutsu dan Allah kin fara tayar min da hankali
kibar kukannan haka pls yana damun xuciyata
Tun shigowarsu FAWAS unguwar idan Mubarak yasauka akan senior RAMADAN.
Tunaninshi junior ne
Dan haka suka kafa suka tsare akan ba abinda xai hanasu yimishi dukan kawo wuqa
Nan shida mijin Saudat suka shigar dasu mota awahale dan xuwa asibiti
Tun kan Su iso gida suka san junior ne ya 6atama su Mubarak 'din.
Shine ganin Senior tunaninsu Junior 'dinnan shine suka musu haka
gashi har KHAMIS ya samu nashi raban
By hajju
[12:18AM, 27/12/2016] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: R🇦HAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [9:47PM, 27/12/2016] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
*PART 100*
Matsowa jikinsa tayi Sosai kamar xata shige cikinsa Tace kuliya RAMADAN kuliya
Yace tana ina
Tace yafuta da ita Amma ban dena ganinta cikin idona ba
Yayi Murmushi Yace tashi kiyo Alwala kiyi sallar La'asar hakan xai cire miki
tsoranta
Takallesa Tace toh meya sameku haka naganku da raunuka
KHAMIS Yace share kawai Aunty LUUVAH.
Tace pls kugaya min
Yace wlhi junior ne ya jawo mana
Tace shi kuma
Yace eh. Da bata labarin komai
Tace hmmm ai 'dan iska ne
Bakuga yanda ya sumar dani 'daxu bah
SAILUBAH ce tafitoh da dadduma da hijab tana fa'din wane hukunci xan yankema shegen
yarannan
XEE Tace ki barshi kawai tunda kokin mai hukuncin saiya ramah
Tajah tsaki dayin kwafah
Saka junior Su KHAMIS sukayi agaba Suna tambayarsa wai meya ha'dashi da wa'yan nan
yaran
Bayan futan FAWAS senior ya kalli junior Yace Ashe farin Cikina xaka bama tsoro da
kuliyar nan
Yace ai. Har tagayama Senior ya harareshi Yace eh
Junior yayi Murmushi Yace toh am sorry. Baxan qara ba
Yace promise
Yace Yah am promise
Senior yajah numfashi Yace aisai kaxo kayi jinyata
Ba musu junior ya tashi daga kan gado yana cewa kwanta toh sai in dinga kallanka
irinna jimamin nan da masu lapia sukema marashi
Bugar qirjinsa Senior yayi
Sukayi dariya atare
Junior ya rungumi Senior Yace em so sorry my brother
Senior ya Shafa kansa Yace no iz Owkie.....
______
Abinda ya faruko shine da Dadyn FAWAS da Qaninsa da sukaje qauyan takai direct
gidan megari suka yada xango
Megari yaji da'di Sosai da yanda yaji neman Auranta suka xoyi
Haka suka rankwa6a gidansu HAMEEDAN
Allah yasa Kawun nata yana nan
Danta gaya mishi zuwansu jiya
Anan Dadyn FAWAS yake gaya musu yanxu dawowarsu kenan daga qauyen takai
Dadyn RAMADAN Yace meya kaiku
Yace ai acan shi FAWAS 'din yaga wacce yakeso
Nan dai ya kwashe Komai yagaya musu
Jikin Dadyn KHAMIS ne yayi sanyi Yace yanxu kuma kabiye mishi xaka aura mishi wacce
tagirme masa
Yace toh Alhaji yaxanyi
Nasoqi yafara birkicemin kuma kaga shi 'daya na mallaka
In ban faranta ransa da abinda yake so ba ai baxanga daidai
Dadyn KHAMIS yajah numfashi ya kwashe yanda shima sukayi da KHAMIS ya gaya musu
'Dari bisa 'dari suka bashi shawarar yayarda da Auransa da Zainab XEE
Dadyn RAMADAN ya qara dace mishi kaga xamani yacanja abin da kake ganin xaixo musu
da matsala saikaga abin yaxo ba haka bah
Kuma ka lura yaran yanxu da wayansu sunada wayewa bakamar nada bah
Ka Aura masa ita inhar katabbatar itama tana sanshi
Yace toh Allah ya shige mana gaba. bara in nemi shi mahaifin nata naji ta bakinsa
Dadyn FAWAS Yace ya kamata kam
To bayan Dadyn FAWAS 'din ya dawone shine ya kirashi dan yaxanta da d'an nasa
Yayi dariya Yana cewa Wlhi Dady Momy ta'iya harara. Ka duba kamar idanta xai fa'do
Hmmm baruwa inya fa'do Dady kishiya xai miki Wlhi......
Da sauri Momyn ta waro ido😳
Dadyn yayi dariya yana shafa kansa Yace kai kace sirikar tawa kyakkyawa CE
FAWAS ya Sosa qeye Yace tayi ko Dadyna........
By Hajju
[9:48PM, 27/12/2016] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: R🇦HAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [3:56PM, 29/12/2016] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
*PART 102*
Yajah numfashi cikin sanyayyiyar murya Yace Aunty Allah yayi miki baki me kyau
Akowane lokaci idanuna akansa suke
Nasha gwada qin bin umarninta ina daurewa. Amma ayanxu abin yaci qarfina
Auntyna....
Idan bam miki ba hankakina baxai kwanta bah.
Pls kayi hakuri Xan gaba da 'daurewa kamar da. wayan ganin banqara yi miki bah
Senior yayi murmushin jin da'di dan yasa aranta yanxu yadena barin abubuwa aransa
xai dinga gaya mata dan yagaji 6oye mata kansa tunda ita takasa ganewa
Junior yiyi Murmushi shidai baisan yaxaiyi da ransa akan Yayan nasa da SAILUBAH bah
Yasani baxai ta6a samunta bah.....
Shiyasa ya fara yakiceta aransa
Amma kamar tinxira xuciyar tashi ake akanta
Allah kabani mafuta
Yafa'di hakan a bayyane
Senior Yace meyake damunka Yace SOO
Yace nawa
Yace nawata CE
A ina take
Nima bansani ba
Toh Allah ya baiyana maka ita
Yace AmEEn
Sosai KHAMIS ya nutsu a qawataccen ofishin nashi yana jin yanda mahaifin nashi
yake gaya mishi yanda xai tafiyar da harkokin kasuwancin nasu
Haka ma FAWAS....
RAMADAN ma mah kallo 'daya yayima masana'antar Dadyn nasu yasan baxaisha wahalar da
yake tunani ba
Sosai ofishin nasa ya burgesa
Yace Dady ina ganin jibi xan fara xuwa aiki
Junior dashima ya rakosu
Yace xan dinga rakoka kan lokacin tafiyata yayi
Sosai Dadyn nasu yaji da'di
Yace Allah yayi musu albarka
AmEEn sukace
XEE da KHAMIS da suka ke6e ba qaramin murna ga junansu suka nuna bah
Dan ganin sunkusa xama mallakin juna
A washe garin ranar Senior RAMADAN da KHAMIS suka raka FAWAS qauyan takai
Sosai HAMEEDA tanunamai jin da'dinta na suma sun kusa zama mallakin juna
Dadyn RAMADAN da Qaninsa Dady Auwal sunsami nasarar kar6oma Senior RAMADAN da
junior RAMADAN dukiyarsu tagadan mahaifansu na qasashe biyu Wato Dubai da Kuwait
Dake junior RAMADAN yasan kan ku'da'de ba qaramin mamakin jin wayan ku'din da yayi
ba
Sosai FAWAS da Senior RAMADAN da KHAMIS suka qara xama manyan yara
Dan Komai nasu namasu aji sukeyi
Yaja numfashi Yace Allah yasa naxama LEEKITAN ZUCIYAH dan nagyra tunanina
Tare da cire soyayar SAILUVAH araina
Sam kuma junior bai dena tsugama SAILUBAH rashin kunya bah
Danko bata kulashi bah saiya kulata......
😀😀😀😀
Komai yayi daidai dan yanxu qiri qiri senior RAMADAN yake nunamah SAILUBAH
iskancinsa
Kamar yau junior ne yagama shirinsa tsaf na tafiya England dan kumawa karatu.
Hutunsa ya qare
Hawaye Senior yake tayi danya saba da 'dan uwan nasa 'dan xaman da sukayi ba
qaramin sabu yayi da 'dan uwan nasa ba
Kama kumatunsa junior yayi Yace tab kumatunka sunfi nawa girmah ashe😳
Dole senior yayi dariya dama haka junior yake son gani
Senior ya lakuce mai hanci Yace qaryane Bayan nagano mah nafika kyau nesa ba kusa
bah
Yayi dariya Yace tab kafini kyau aina dinga xuwa gun Auntyna Rahamat tanamin gyara
dan nafika kyen Kasan tafi'sona
Yace hmmm ruwan ido ne da ita ai da farko ni tace tafiso
Momy Tace wacece Rahamat
Dady Yace wata Auntynsu CE
Tace shine bansanta bah
SAILUBAH Tace Karki damu Momy xan baki labarinta
Tace ya kamata kam 'yata
Rungumar juna Senior da junior sukayi dan jin ankira sunan junior
FAWAS da KHAMIS suka tafah har Suna ha'da baki wajan cewa abin sha'awa
Haka sunaji Suna gani junior yatafi ya barsu kamar yanda yaxo ya samesu
Aiko gallamai wata muguwar harara tayi Tace iskancinka Yafara isata RAMADAN wai me
kakeso na xama maka ne
*_MATATA KUMA UWAR 'Ya'Yana_*
By Hajju
[3:56PM, 29/12/2016] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: R🇦HAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [3:53PM, 28/12/2016] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
*PART 101*
Haka KHAMIS Bayan ya koma gida Momy take tambayarsa me meya sameshi haka da
raununka jikinsa Yace fa'da sukayi da wasu
Tace wasu wah😳
Yace shima bai sansu ba
Tace toh Allah ya sawake
Danta lura bayasan tatakura masa da tambaya
Ina sanka my son plx kayi abinda xanji da'di araina kan wannan kasuwancin banaso
ma'aikatan ciki susami matsala dakai
KHAMIS yajah numfashi Yace Insha Allah Dady xaka sami Komai yanda kakeso
Amma yaushe ne abin
______
Dai dai qarfe Tara ne Dadynsu RAMADAN yake xaune dasu suna hira sama sama
Dan hankalin senior yana kan SAILUBAH so yake yaganta kan yayi bacci. Tunda yau ba
yawo dan yanayin jikin nasa
Yayinda junior yaketa wasa da Khairat abinsa kallo 'daya xaka mai Kasan bashi da
wata matsala
Dady ya kalli Senior Yace my son Yace na'am Dady
Yace kaga 'dan uwanka komawa karatu zaiyi
Gashi ni da kawunku Auwal munsami nasarar gano muku dukiyarku ta qasar Dubai da
Kuwait
Dukiyace me darin yawa
Saunjuya sun da'da juyata
Wlhi a bayanan da sukeyi sunce sun'dauki shekaru Suna neman mahaifinku
Duk kawunku Auwal ne yayi bincike akan hakan
Acikin satin nan nakesan muje dashi qasashan dan mukar6o muku dukiyar daku
Junior ya waro ido😳 Yace Dady bana san harkar kasuwanci shiyasa naxa6i naxama
doctor...
Dady yayi Murmushi Yace 'dan uwanka mah abinda yaxa6a kenan
Ai hausawa Suna cewa gida biyu maganin gobara
Dukiyarku tanada yawan gaske dole akasa muku ita gida gida
Yanxu xanfara binciken fili. Dan gida muku asibiti naku na kansu
Murmushi Junior yayi Yace wow Dad in kayi haka kacikamin burina.
Amma maixai hana acanja mah 'dan uwana karatunsa ya koma waje ina ganin xaifi kasan
matsalar qasarnan
Dady ya shafah kan junior Yace aa kabarshi anan
Yana karatun yana luramin da camfanina
Gyefe guda kuma ina gida muku asibiti
Kaga kana dawowa saika fara aiki acikinsa nasan inhar kafara aiki acikinsa shima
baxai da'de bah xai fara aikin acikinsa
Tace dan kai na xauna anan tun 'daxo narasa yanda xanyi Ashe jikin da Sauqi
Wlhi duk na matsu naganka ko hankalina xai kwanta
Gashi nakira number naka akashe sai gwadawa nake tayi kagani
Ta qarashe tana nunamai wayarta
Tace nika samamma nutsuwa. dan na tabbatar inda bakaxo ba Saidai in kwana anan.....
Yace Allah Auntyna
Tace Allah
Yace toh bacci nakeji my aunty.
Tace xansu kaje ka kwanta
Yace Aunty kinsan abinda xai sani farin ciki ayanxu
Ta girgikai alamar aa
Yace ki'danyi min kiss
SAILUBAH tayi Murmushi Tace na lura kwanan nan iskanci kakeji ko dai junior ya koya
maka ne
Yayi Murmushi Yace aa nidai kimin in tafi
Bai bari ta qarasa ba taji bakin shi cikin nata ya sakar mata kiss.....
Kanta tattaro nutsuwarta sai ganinsa tayi a'kofar gidansu yana 'daga mata hannu
alamar bye bye
Ta gallamai harara da juyawa cikin gidan nasu tana tunanin waye iskanci ne yake
damun RAMADAN ne yanxu nasan yadinga kissing 'dinta
By Hajju
R🇦HAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 103*
Bai bari furucin nasa ya fitoh fili bah
Dan haka ganin yamata shuru shiya sata cigaba da fa'din
Kamai dani 'Yar iskar ka
Saina dinga maka kiss kamar wata matar ka
In 'iskanci kakeji kafudda 'daya daga Cikin 'yan matarka mana amaka Aure da ita
mana. Amma dake ni........
Cak tatsaya da maganarta ganin duk maseefar da take masa bakinta kawai yake bii da
kallo
Tajah numfashi dasan ficcewa daga motar dan yanxu tatabbatar RAMADAN yaxama 'dan
iska. Gawani shegen kwarjini da yake qara yimata
Kuma yarasa wacce xai saukema iskancin nashi sai ita...
Yayi Murmushi Yace da ruwanki mana dan kika bari ta fashe Wlhi kamaki xa'ayi dan
kinyi kisa aSO❤
Ta gallamai harara tare da Jan tsaki Tace mukwana ahaka
Dan Wlhi na dena maka kiss har abada
Yace Wlhi baki isa bah....
Ta kallesa da sauri
Ya watsa mata wani narkakken kallo Wanda ya tabbatar ya gabama da duk wani ruwa da
jini na jikinta
SAILUBAH tawaro ido 😳 Tace wai yaushe kaima ka xama 'dan iska ne.
Bata kulasa ba. Tayi cikin falansu dan tasan in tatsaya bashi amsa ba makawa saiya
qara kaima bakinta wani kiss 'din
Dan talura da yanda yake qarema bakin nata kallo
SAILUBAH Sallah tayi ta'daga hannu xata roqi Allah akansa Amma saita mance memah
xatace
Dan haka sai tatashi kawai tanufi gidansu
Afalo tatarar da momynsa
Tace Momy naxo miki da wata magana ne
Tace ina jinki SAILUBAH fa'di
Tace Wlhi Momy ayima RAMADAN Aure yanxu
Dan na lura akwai abinda yake damunsa
Momy ko bin SAILUBAH tayi da ido. tana tunanin itadai tana hango soyayyar SAILUBAH
a idan RAMADAN
Gashi ita SAILUBAN har yanxu bata gane soyayyar da yake yi mata ba.
Cikin nutsuwa Momy tacigaba da fa'din. Inaso Ki lallasheshi cikin nutsuwa harya
gaya miki wacce yake so
Dan munan munyi munyi dashi ya gayama mana wacce yake so Yaqi fa'da
Kinga in ke kika lallasheshi qila ya gaya miki
Shikenan saimu masa Aure
Toh SAILUBAH Tace
____
Suna ha'duwa takama hannayansa Tace plx RAMADAN ka gayamin acikin 'yan matanka
waccece wacce takwanta maka arai
Yayi Murmushi idan shi cikin nata
Yace wani abune
Tace eh mana
Toh gayamin
Ya fa'da hakan cikin muryar ra'da
Taji hakan har cikin ranta
Tace idan nasani sai ingayama Su Momy kaga sai amaka Auran ko
Cikin damuwa SAILUBAH tajah numfashi Tace ya xanyi ne XEE ya kike san nayi
Har Saina fitoh naga miki cewa yanxu RAMADAN yaxama 'dan iska. Bayan kina gani da
idanki
Inya ibo iskancinsa sai yaxo ya sauke aguna
Ni sa'arsa CE daxai dinga yimin kiss tamkar wata matarsa
Idan na kwanta bacci sai indinga ganina dashi cikin wata rayuwa irinta ma'Aurata
Duk yabi ya birkita kwakwal wata wajan tunaninsa dasan kasan cewa dashi.
Kullun natashi daniyar cimai mutunci muna ha'duwa yana jefamin shegen kallansa xan
rasa nutsuwata
Me kikeso nayi anan bayan in ne santa kan nawa dashi
XEE tayi kalar tausayi dariya fam cikin ranta da jin da'di
Amma ko kusa baxata iya nuna hakan bah
Tace toh ai naga hanashi ganin kanki da kikayin. Damuwar kanki take komawa
Dan gashi kin rame sai uban haske da kika qarayi
Ga damuwa nan da tashin hankali da suka baiyana kansu agareki.
Tace ni ban damu da ramar da nayi bah. Ko tashin hankalin daya baiyana agareni ba
Fatana Allah ya yayemin tunaninsa
XEE RAMADAN haukatani yake sanyi
Yace ya xanyi my Luv tashina kenan fah FAWAS yaxo har office ya 'daukeni
Shine fah nace bara in kiraki nasamu nutsuwa
Tace toh xan iya ganinka yanxu
Yace naso dai namiyo miki wanka nacanja Kaya dan kiganni da kyau Sosai.
Tace ai kai kobakayi wanka bah kyanka karuwa yake agareni
Yace Naji dai
Dan nalura wayo kike san kiyi min
xamuje qauye ne ni da RAMADAN da FAWAS yanxu haka
Idan muka dawo na'dan huta xaki ganni.
Ta shagwa6e murya Tace ni dai yanxu nakesan ganinka.
Kallan FAWAS KHAMIS yayi Yace toh Aunty XEE nasan ganina kuma nima ina buqatar
ganinta
RAMADAN Yace tambayar min ita Auntyna tana gidan ne
KHAMIS Yace my Luv Aunty LUUVAH na tare dake ne
Tace eh gatanan.
KHAMIS ya 'dagama RAMADAN kai
Murmushi yayi Yace toh kuyi shawara pls lokaci na tafiya kunsan ahakan mah sai
munyi dare Sosai yau.
KHAMIS Yace toh my Luv ganinan xuwa
XEE tayi Murmushi Tace ina jira.... Da kashe wayan
XEE da KHAMIS baqaramin mamaki sukayi ba wajan ganin RAMADAN ya Sha gabanta
Dan basu san wane irin gudu yayi bah
By Hajju
[20/03, 17:09] 80k: [10:17PM, 31/12/2016] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 104*
FAWAS ya qaraso garesu Yace Aminci ya tabbata agareki YAYATA kuma wacce takusa xama
mata agareni...
FAWAS yayi murmushi dan yanxu yadena mamakin Yayar tasa wajan 6arar da kalamai
Na soyayya dana shirme dana abin dariya
Yace Naji da'din furucin nan naki. Saidai naga baquwar fuska agareki abinda ban
ta6a gani ba kenan
HAMEEDA tayi Murmushi Tace ita ka'daice wacce na 'dauketa 'Yar Uwa a qawayena
Yayi kyau hakan. Yafa'da da kallan Mero. Tare da qarawa da cewa. Toh sannu qawar
YAYATA
Mero tawashe yalan haquranta Tace Barka da xuwa dai 'dan birni
Ya kalli HAMEEDA Yace toh Kinga kayan kwa'dayi nasiya miki yau
Dafatan sun isheki cika cikinki yanxu ame makwan kici abincin dare
HAMEEDA takar6i ledar xata bu'de.....
Yayi saurin katseta da fa'din aa karki bu'de yanxu harsai na tafi
Diremai couscous tayi Wanda yasha kayan lambo danginsu karas fiss koran tattasai
Sai farfesun kayan ciki da drink 😬
Takallesa da sauri
Ya 'daga mata gira dama ya fa'di hakanne danta kulashi
Aiko Tace Waye mijin
Ya tashi ganin ya qoshi da abincin. ya sakar mata kiss a wiya kafin Yace wasa nake
miki
Zan kiraki can ajima in miki sai da safe
Tace bana buqata kawai sai Allah ya tashemu
Ya sakar mata shegen kallansa
Nan take jikinta yamutu
Yace pls manah
Tace toh saika kira
Yayi Murmushi da shafar gefan fuskarta
Kafin ya ficce daga harabar gidan
SAILUBAH tabishi da kallo tana kissima abubuwa da dama aranta game da shi
Can wajan sha biyu da rabi na daran tayi nisa abaccinta taji ringing 'din wayar
tata
'Dauka tayi batare data duba ba. Dan tasan 'dan rikicin nata ne
Yace Auntyna.....
Tace na'am
Yace tashi pls muyi hira
Tace bacci RAMADAN
Yace pls my Aunty tashi dan Allah
Tajah numfashi Tace darene fah RAMADAN pls kabarni
Kamar xai mata kuka Yace nasani pls ki jini ka'dan👌🏻 dan Allah
Cikin shagwa6e mata Yace nidai ki fa'damin in barki kiyi bacci naji yana damunki
Kashe murya yayi dagaske kamar xaisa mata kuka Yace dan Allah Auntyna.....
SAILUBAH taji muryar tashi har cikin ranta
Tace ina sanka toh 'dan Qanina kayi me da'di
Yajah numfashi Yace inaso gobe kishirya muje inda xa'a fara koya miki mota
Tace nagode 'dan Qanina
Yace Wlcm my Aunty.
Kidaure kiyi mafarkina yau.
Ashagwa6e Tace ai Kullun a cikin mafarkinka nake
Kamar xatayi kuka Tace Bayan ka 6ata tunanina da tunaninka ko xama nayi tunaninka
nakeyi bare kuma bacci Kasan ba abinda baxan gani bah
Washe gari yana qaryawa da iyayan nasa ya kalli Dadyn nasa Wanda kwanansa biyu uku
kenan da dawowa daga England daya kaima junior xiraya
Yace Dady baka gama ban labarin yanda kagano min junior ba
Dady yayi murmushi Yace ai nagama baka labarin komai
Yana cikin goshin lafiya
Momy Tace karka damu gaba mu biyu xamu ni da kai
Khairat Tace dani Momy
RAMADAN Yace aikuwa.
Ganin yanda tamishi kyau cikin wani yadi me kalar jah an mata doguwar riga irin A
shape 'din nan
Shiyasa shi 'daukarsu hoto
Yace Aunty kinyi kyau Sosai
Amma saidai kisa hijabi
SAILUBAH tawaro ido Tace hijab
Yace eh
Tace tab😬 baxan saba
Shaga6e mata yayi kamar xaiyi kuka ya dinga lallashinta kafin tayarda tasaka
Tana maseefar karya qara takura mata akan hakan
Shuru yamata tunda dai tasa kishinsa ya ragu
Direct kaita yayi inda ake koyan motar ya biya Komai harda na Aunty XEE yana gaya
mata anjima KHAMIS xai kawota
Tace toh
Ya xuba mata ido yanda taketa murna abin ya masa da'di
Can Yace Aunty xan tafi
Ta kallesa yayi mata kallan qasa qasa
Nan tagane nufin shi
Saita share shi
Murmushi yayi Yace akwai lokaci me xuwa wanda idan yaxo baxaki shareni bah Auntyna
Tace naji jeka sai anjima
Murmushi yaqara yi kafin yatashi motarsa
👯👯👯👯👯👯👯
England junior RAMADAN ne yashigo 'dakin nasa agajiya dan yau bayanan karatun nasa
sun caja mishi kwakwalwa
👯👯👯👯👯
SAILUBAH dai sai ahankali dan yanxu bata da abinyi sai tunanin RAMADAN 'dinta
Shiko yasa meta yanda yake so sai 6ata mata tunani yake yi
XEE ko ba abinda yake damunta dan sai tsula soyayyarsu suke yi ita da gwanin
tafiyar nata KHAMIS.....
Da misalin qarfe tara na safe ne Abban SAILUBAH yasata aga akan tagaya masa wata
fitar matsayin mijin Auranta
Tace Abban dan Allah kayi hakuri
Yace kinyi kuskure dan Wlhi baxanyi kaffara ba. yanda Nace in baki kawo min Wanda
kikeso ba. xan ha'daki da wanda naso. toh yanxu mah bata canjah xani bah.
Tace toh xan gayama anjima da daddare
Ya harareta Yace Allah ya kaimu
Aiko tasa RAMADAN tayi agaba akan yagaya mata mexatace mah Abban nata
RAMADAN yayi qif qif da ido Yace am so sorry my Aunty
Ta kallesa arikice cikin maseefa Tace me kake nufi
Kana nufin dama baka shiryama wannan ranar Komai bah agareni kahanani tsayawa da
kowa.
Ya 'daga mata kai a shagwa6e alamar eh......
😂😂😂
😂😂😂
😂😂😂
Tunda aka haifi RAMADAN baita6a jin kalma me da'di kamar wannan bah
Da'din ya cika xuciyarsa Sosai👌🏻
Amma azahiri sai yayi saurin jah da baya tare da xaro ido😳 Yace aa aa Aunty in
Aureki in kaiki ina. Ina qaramin yaro😳
SAILUBAH taci gaba da kukanta tana cewa Wlhi saika Aure ni
Dawo wah gabanta yayi cikin lallashi Yace xan Aureki Auntyna Amma da shara'di uku
Dare nayi tagayama Abban nata RAMADAN ta tsayar a matsayin MIJIN AURANTA
Da mamaki Abban nata Yace RAMADAN Tace eh
Shuru yayi mata na'dan wani 'dan lokaci. Can Yace taje saiya nemeta
Shima RAMADAN Suna xaune da iyayan nasa Yace Dady na samo wacce nakeso Yace toh
Madallah wacece
Ya Sosa qeya Yace Aunty SAILUBAH
Wannan kenan👌🏻
Toh ance wai rana bata qarya wai saidai uwar 'diya taji kunya....
Toh mai xaisa baxan nuna farin cikina bah💃🏻💃🏻💃🏻 da xuwan bikin FAWAS da
HAMEEDA
Yau takasance laraba qanwar Momyn FAWAS CE da 'yan dangi xasu kai kayan Auran
HAMEEDA
By R🇦HAⓂ🇦T
[10:17PM, 31/12/2016] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯.
[20/03, 17:09] 80k: [11:47PM, 04/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 106*
Shiko shuru yayi mata Yana aika mata da wani shegen kallo fuska 'daure
SAILUBAH tajah tsaki dan tarigada tasaba da wannan yanayin nashi yanxu
Watoh ya gaya mata magana San ransa kuma a dun qule
Amma fah taso yaci abincin dan abin ya rigada ya xame mata jiki in baici bah
hankalinta baya kwanciya
FAWAS dai mamakin Momyn nashine ya cika xuciyarsa. Ga tausayin kansa daya dami
kwakwal warsa
Ahaka ya gamah yaje shirya kansa
Yace Dady sai kaxo
Yace yau ba lectures ne
Yace eh da ficcewa
HAMEEDA ko Bayan tagama Komai ta'dauki turarukan cikin akwatinta tafeshe dukkanin
'dakulan da falan
Tayi wanka da saka shadda 'daya daga cikin akwatinan nata
Nan tafitoh a Amaryar
Momy takalleta da fara'a Tace toh dama abinda xance miki shine
Inaso kima mijinki wani uxiri 'daya
Baxai dinga xuwa gareki bah harna tsawan wani lokaci
Sannan idan kika tashi da safe inaso kidinga xuwa muna ha'da breakfast abin karin
kumallo dake
Haka da ranah haka da dare
Inaso kidinga tayani aikace aikacen gida
Kuma duk abinda yake damunki banaso Ki 6oyemin kidinga fa'dimin dan yanxu nice
Komai naki
Bana San nuqu nuqu a tafiyata
Ki saki jiki Ki sake dani Ki 'dauke matsayin uwar data tsugunna ta harfeki
Sannan anjima wani telana xaixo shida yarinyar aikinsa
Kifitoh da kayan auranki tsaf xata gwadaki. Xan rabama telolina uku kayan. dan
inaso a dinke miki Su tsaf
Dan kidinga shiga kina fata a cikin sutura me inganci
Kuma kidena saka hijabi nan
Da xaran kinyi wanka kinsaka Kaya kixauna haka cikin kyawunki
Da fatan kinji duk abinda Nace
HAMEEDA Tace eh Momy naji Insha Allah xaki sameni me ladabi akan Komai
Tace toh Madallah yanxu muje kitchen ki tayani ha'da farfesun ranah
Dadynku yana dawowa cin abincin ranah kinga dole ayi abu mekyau ko
HAMEEDA Murmushi
Haka Momy tasa HAMEEDA aiki Sosai tana koya mata yanda Komai yake ita da Hinde
Toh dama ita HAMEEDA akwaita dasan akoya mata abu dan haka taxage dantse ba raki
tadinga yin Komai anutse
Tashi FAWAS yayi cikin murmushin jin da'di Yace duk da hakan kunsan bazankai da
nisa bah
Dan kunsan yanxu ba samun lokacin kammu muke bah
Koda yake xan 'dan sami salamah akan hakan ka'dan....
RAMADAN Yace yauwa abokina
Xan tayaka da addu'ar Allah yasa musamu baby nan kusa.
KHAMIS yayi dariya Yace tab ina tabbatar maka ayanda yace wai bata tunanin lamunce
mishi ita nan kusa
Na tabbatar maka saina rigashi samun baby😀
FAWAS ya 'daka mishi duka Yace 'dan iska Insha Allah saina rigaka
RAMADAN yayi Murmushi kawai yana tuno ranar da xaixama kamar FAWAS Auntynsa ta
kasance qarqashin ikwansa
Abin ya bashi mamaki dan Sosai ya hango kishinsa a kwayar idanta duk da dama yasaba
ganinsa lokaci lokaci
Dan haka yau da wani jiji da kansa yaxo mata ta'di (xance) acewarsa
Bayan tafitoh ne yafara bata labarin budurwar da take damunsa masana'antar tasu
yau wai ita Iyami
Shuru yayi mata da xubawa bakinta ido xuciyarsa nayi masa da'di dan kishi ya
kusantota
Tashi yayi ya matsu kusa da ita Yace wai Fushin da maseefar da akemin ta miye ce
Tamai shuru dan ya ritsata
Sosai ya matsa kusa da ita yaci gaba da fa'din
Kawai dan ina miki hirar 'yan mata na saiki hauni da maseefa kamar wata masoyiyata
wacce takamu da maseefar sonah
Tace kadena matsuwa kusa dani haka
Yace kinajin wani abune
Cikin sanyi kuma a shagwa6e ta 'dagamai kai
Yace hmmm toh gayamin kamar me kike ji
Tace dan Allah RAMADAN kabari
Yace me nayi miki Auntyna
Tace nidai kakai jikinka jikina xan iya rasa nutsuwata
Yace Auntyna nine xan rasa nutsuwata bakeba.
Tace to to toh kamatsa mana
Yace abu 'daya xan gayamiki kedena yimin maseefa
Tace na dena
Yace promise Tace Ya am promise
Yayi wani shegen murmushi yana kallanta qasa qasa.
Ya shafi gefan fuskarta Yace kiyi mafarkina me kyau na 'dauke xuciyar masoyi
Amaryata. Yana fa'din hakan ya juya ya 'dau wayarsa ya ficce daga gidan
SAILUBAH tabishi da kallo tana 'dauke ajiyar xuciya........
Dake Momyn FAWAS ta'dora HAMEEDA akan mayuka masu tsada da gyara fata
Xo kuga yanda tayi wani maseefar kyau
Ta goge fatarta tayi kyau dan haskenta ya qara futowa
Ga girki kala kala Momyn take koya mata
Sosai HAMEEDA tayi kyau
Sai shiga take tana futa na sutura
Dan ankawo mata kayanta tsaf na wajan telolin da Momyn tabayar Su 'dinka mata
HAMEEDA talura Momy akwaita dasan tsafta da gayu
Tace aranta qila ita FAWAS ya gado
Ga maganin Mata masu kyau da nagarta da Momyn take bata
Sosai take k'ishirruwan San kasancewa da mijin nata
Amma ya xatayi ita dashi sai gaisuwa da bi da ido
Yau take Alhamis da miqalin qarfe 2:00pm XEE da SAILUBAH da qawayansu sai shirye
shiryan xuwa walimar XEE suke
Dan gobe jumma'ane d'aurin Auran KHAMIS da XEE
Wa'axi me ratsa xuciya da 6argo ne yayima xuciyoyin duk Wanda yake gun mugun kamo
Sosai suka nutsu wajan sauraran malaman
Ahaka akaci akasha akayi hotuna abin gwanin ban sha'awa.
Xuwa qarfe hu'du suka taso
A daran Momyn KHAMIS tasa 'yan uwanta suka kai kayan Auran na XEE
Akwatina manya manya irin na *MATAN ALFARMA*
Sukansu SAILUBAH da XEE 'din sunsha mamakin dukiyar da aka kashe
RAMADAN ne yake tuqi ahankali lokaci lokaci yana kallan Auntynsa
Ya 'daukota ne daga gidansu XEE dan maidata gida
Yace Auntyna
Tace Mene ne
Yace Komai ya burgeki na wannan Auran ko
Tace Sosai mah
Yace bakiji aranki dama kece Aunty XEE bah
Ta hararareshi Tace nibanji Komai bah
Yace toni naji Komai
SAILUBAH tata6e baki Tace story kawai. Kasani Aurena dakai na wata biyar ne.
Karkayi kuskuran saka wani abu aranka
Yayi Murmushi Yace toh Auntyna
Tashiga a sulkunce ganin yanda ya xubah mata ido kuma da yanda yayi mata wani
maseefar kyau.
Tashi yayi yaje ga wani aqaramin furiji ya 'dauko wata sanyayyiyar madara ya xuba a
cup yaxo ya mika mata
Ahankali Tatashi tsaye ta kar6i Tace mexanyi da ita
Yace sonake kisha
Tace toh baka Sha maganin naka bah
Yace narigada na warke tunda na ganki adaidai lokacin da nake buqatarki
Tace Amma........
Yayi saurin katseta da cewa pls kisha niba surutu na tambayeki kiyi min bah
Shuru HAMEEDA tayi masa takafah kai tasha kusan rabi
Ya kar6i cup 'din ya ajiye yana cewa dts gud my baby...
Yanxu Kinga naci minti 'daya da sakwanni alokacina dan haka gyaramin da kyau nayi
abun ranar
Yafa'di hakan dayi mata wata kyakkawar runguma.
Ya kama qugunta cikin wani salo ya fara aika mata da sakwannin da sukafi na ranar
daya sami damar kissing 'dinta
By Hajju
*PART 105*
Kayane nagani na fa'da Wanda Dadyn FAWAS 'dinne da Kansa yaje Dubai dan ha'do mishi
tunda Momy taqi bada ha'din kai
Wasunsu a 'dinke suke dangin Su shadda
Sosai RAMADAN da KHAMIS da Ango FAWAS suke shiri dan xuwa 'daurin Aure.....
In da sukayi kyau Sosai cikin shigar manyan Kaya.
Abinka da wa'yanda basu saba sawa bah. Duk sai sukayi wani iri aciki
KHAMIS Yace Wlhi baxan iya da wannan rigar ba (Watoh 'Yar saman )
FAWAS Yace Allah nima
RAMADAN Yace aikai ko kaqi Allah saikasata
Dan Ni kam xansa dan tun yanxu Auntyna tasa aranta namu yana xuwa
KHAMIS yayi dariya
Yace wayaga Aunty LUUVAH da kai matsayin ma'Aurata
Yace hmm Wlhi ina tuna ranar wane farin ciki xan shiga
FAWAS yayi Murmushi kawai batare da Yace Komai bah
Sanda suka gama tsaf Suna shiga gidansu SAILUBAH suka ha'du dasu ita da XEE da wata
qawarsu Maryam
RAMADAN Yace Auntyna munyi kyau
SAILUBAH tadafa XEE ta kwashe da dariya Tace Sosai mah
Ni dai wannan abu yaqi wucce min arai
Wai yanxu kai FAWAS Kaine xa'abama mata yau
Yace kai Aunty LUUVAH me kikesan cewa ne
Tace gaskiya mana
KHAMIS yayi dariya Yace idan kabiye na Aunty LUUVAH harsai a 'daura muna tare da
ita tana bamu Takaici dan haka pls muqara gaba
RAMADAN Yace Auntyna.....
Tace wani abu
Yace koda yake saidai nadawo
Haka suka ficce daga gidan Cikin farin cikin yau Abokinsu FAWAS xai xama Ango
SAILUBAH tabisu da kallan mamaki
Washe gari suka tarkata suka tafi sukabar HAMEEDA da Momyn FAWAS agida d'aya ☝🏻
Tun shigowarta falan momyn taxubah mata ido gabanta kuma ya fa'di
Sam batayi tunanin HAMEEDAN haka take Yarinya kyakkyawa da ita bah
Cikin mutuwar jiki Tace lafiya lau da fatan kintashi lafiya
Tace lafiya lau
Idan kadawo kasameta anan kuyi gaisuwar yamma idanko baku ha'duba shikenan.
Kuma Wlhi ko shiga 'dakinka kayi kakirata awaya ban yafe maka bah.......
Tace kuma naji ka gayama dadynka wani Abu cikin abinnan da nace Wlhi sai kaga 6acin
raina irin Wanda baka 6ata gani bah.
Tana kaiwa nan Tatashi da cewa.
kabani guri nagama maganar dakai
RAMADAN Wanda yake kwance agadansa yana huta gajiya da tunanin Auntynsa SAILUBAH
akan yanasan yaje ya ganta koya sami nutsuwa.
Arikice KHAMIS ya kira RAMADAN Yace yanxu nima haka momyna xata rabani da Aunty XEE
RAMADAN yayi Murmushi Yace toh waya sani ne
HAMEEDA ko ganin HABIBIN nata bai dawo bah sai kawai takwanta abinta
RAMADAN ya sauka daga kan gadansa cikin tausayin FAWAS yayi gun Auntynsa
Da kwafah SAILUBAH Tatashi dan ganin ko tama Kakah gaddama a nacin RAMADAN baxai
barta bah
Sunfitoh rahabar gidan ta kallesa Tace wane saban salone kuma wannan.......
Karfa kaga na nemi hakan ta kasance na Auranka kanemi raina min hankali
Tafa'da cikin 6acin rai da San komawa falan nasu........
Yayi mutmushin idansa akanta Yace kawai kimin hirar soyayyah inji da'di araina
Tace Amma aini ba sa'arka bace.
kaje gun 'Yan matanka mana
Yace baxan jebah naki kalamanki nakeso yau
SAILUBAH tatsaida idanta sosai akansa nan tagano futunar tasa CE tatashi yanxu
RAMADAN ya dafe kai. Daba dan yayi alqawari aransa bah daya kai hannu gareta ya
nuna mata yanda ake so yake
Ya 'dago da kansa agankali Yace oho kawai kalamai nake buqata na SOO shine magana
Dan idan naje wajan 'Yan mata nah kalamai suke gayamin masu da'di
irinsu
Ina sanka Honey
Ina sanka baby
Inasan ka xama uban 'ya'yana
Ina sanka har qarshen rayuwata
Ina sanka Darling
Ina San in kasance tare dakai........
Shuru RAMADAN yayi ganin tasake baki da waro ido tana kallansa
Ya harareta
Yace saina gaya miki ko xakice bakisan wa'yannan bah
Kai 👈🏻 innalillahi. duk Wanda ya mallakeki matsayin Matarsa Auntyna xaisha fama
kafin ya 'doraki akan hanya
Danke ba abinda kike ganewa wlhi
Ina cikin matsala ni RAMADAN 😔
By Hajju
[2:41PM, 03/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: R🇦HAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [5:16PM, 05/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 107*
Shuru HAMEEDA tayi hankalinta tashe jin yanda yake sarrafata abin ya bata tsoro da
mamaki
pls YAYATA Karki hanani ina cikin wani hani ina buqatarki plsss. Yafa'di hakan da
kwantar da ita akan li'imantaccen gadansa...
Jikin HAMEEDA yacigaba da karkarwa daidai lokacin yasamu nasarar ganin dukiyar
funaninta......
Nan yafara aikin daya furgitata....
Saidai kash.....
Baiyi nisa ba wajan cinma burin nasa kamar yanda yaso qarar wayansa ta katse mishi
abinda yake muradi
jin hakan yasa HAMEEDA tayi saurin kare k'irjin nata da hannu cikin yiwa Allah
godiya
A wahale ya 'dauki wayan nasa batare da ya duba bah. Nan yaji muryan Momy tana
cemai ina fatan dai HAMEEDA tatafi 'dakinta
Da sauri FAWAS ya rintse ido ya aro jarumta da saita muryarsa Yace Momy tatafi
Tace toh Madallah ka kula da kanka my son
Yace toh Momy
Tana xuwa part 'dinta Tafa'da gado tana maida numfashi tare da tuno Komai
A hankali numfashinta ya daidaita
Ta lumshe ido tana rayawa aranta duk randa mijin nata yayi nasarar samunta xataci
ubanta agunsa
Dan yamata baxata Sosai Ashe dama haka Yake.
Tana mishi kallan biri ashe shi kallan ayaba yake mata......
Shiko FAWAS Sosai yayi jinyar kansa dan wannan dare yayi dana sanin ta6a matar
tasa
Dan daxaran ya rufe ido saiya dinga cin karo da dukiyarta wacce ganinta yasa yayi
mamaki Sosai
Washe gari Bayan sun idar da breakfast sai yayi shashinsa dan shiryawa
Dady ya ficce yana cemah Momy kice my son yayi sauri yaxo ya saman
Tace toh
Xata tashi kenan taga HAMEEDA na qoqarin shiga kitchen
Takirata tana cewa yau kamar baku gaisa da FAWAS ba
HAMEEDA ta sunkwai dakai Tace eh Momy dan ban ganshi bah
Tace jeku gaisa saiki kira min shi Tace toh
Da nufar part din nasa bakinta 'dauke da addu'ar karya ritsata irin na jiya
Bu'de kofar tayi da sallama lokacin ya gama Komai yana 'daukar laptop 'dinsa
Haka suka fitoh gwanin ban sha'awa tayi kitchen shi kuma yayi gun Momyn
Alhamdulillah
Yau bayan an idar daga sallar jumma'a *aka d'aura Auran KHAMIS da ZAINAB*
Dan ginsu KHAMIS basu bar Amarya XEE takai dare bah suka sunkuci abinsu sai gidansu
KHAMIS
Sosai XEE tayi kukan rabuwa da iyayanta
An dankama momyn KHAMIS amanar XEE nan takar6a. Suka kaita part dinta Wanda KHAMIS
ya tsigunta mata akan gidansu da Dadyn nashi yake qarasa musu...
By Hajju
[5:17PM, 05/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: R🇦HAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [11:21AM, 07/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 108*
SAILUBAH tajah tsaki Tace barshi kawai da Allah dan nafara gajiya da futunarta
XEE tayi dariya Tace 'daxo naga bakinki da magana pls gayamin
SAILUBAH ta Murmushi Tace cewa Xanyi yau Xaki cafke sandar girman👍🏻 qaramin Yaro
XEE tawaro ido kana tayi murmushin yaqe Tace hmm toh saime
Addu'ace dai na miki
Wlhi ina tabbatar miki qaramin Yaro ne xai haqe miki wannan rijiyar taki
SAILUBAH tayi murmushin Takaici Tace ai narigada naci fariyar qaramin yaro bai isa
ya kwashi romona bah
XEE tajah numfashi Tace kikiyayi ranar da xanganki kina amai ko kina xubda yawu
SAILUBAH tasheqe da dariyar rainin hankali xatayi magana wayarta takatseta
Shuru tamishi Ganin ba alamar ciwo ajikinsa shiyasata ganewa wayo yayi mata.
SAILUBAH tadafe kai Tace wataya da jakata Suna can gidan fah....
Yace saiki barmah gobe
Tace akwai hirar da xamuyi wajan chat da qawayena qarfe gomah
Yace toh Naji
Tace mu juya pls
Ya galla mata harara Yace wlhi baxan juya bah
Shuru SAILUBAH tayi tana tunanin wai yaushe RAMADAN ya rainata ne.....
Pls FAWAS inka shirya xuwa gida ka'dan tawomin da jakar Auntyna da wayanta yanxu
dan Allah
Ok
Tnx. Saiya kashe wayan
Yayi Murmushi cikin muryar qasa qasa Yace xanso ko kixama cikakkiyar karuwan acikin
gidana ya kasance Kullun acikin yimin karuwancin kike
😳😳😳😳
😳😳😳
😳😳
Sosai SAILUBAH tawaro ido cikin matuqar mamakinsa😧
Ganin tashiga yanayin da yaso shiyasa yayi saurin jan motar tasa baya ya fitar da
ita xuwa gidansu yana Murmushi......
SAILUBAH ko mamakin bakin da RAMADAN yayi da rashin kunyar da take damunsa CE tah
cikata. Haka dai takwanta da mamakinsa batare da taga qeyar jakarta da wayanta bah
KHAMIS Ango ko shigarsa gidan nasu gun Momynsa yayi direct bakinsa 'dauke da
xaxxafar addu'ar Allah yasa karta fitoh mishi da nata salan kamar yanda Momyn FAWAS
ta kawo nata.
Tana turo 'kofar da sallamah shi tagani a tsaye yana ganinta ya rungumeta da saurin
kai bakinsa cikin nata yana aika mata da sakwanni kalakala a burkice
Tasan bata isa ta kwaci kanta bah shiyasa tabarshi yadinga juyata San ranshi
KHAMIS ko yana shiga bet room 'din matar tasa. Jikin nasa a sanyaye haka yaje ya
rungumeta Yace masha Allah yau burina ya cika.
Tace nima haka
Yace dare yayi xanso kiyo Alwala muyi sallar godiya ga daya cika mana burinmu
Tace toh
Hakan sukayi Sallah ya kama kanta yayi mata addu'a da yin fuska Yace my Luv 'dan
gayamin yanda kikeyin wankan tsarki
XEE tayi shuru
Ganin shima shurun yayi shiyasata mai bayanai dalla dalla
Yayi Murmushi da tura mata xaka da madara ganin tafa'di yanda yaso yaji
Sosai XEE taci yana tayata bata
Dan yanda take hango futuna a kwayar idansa ta tabbatar ba barinta xaiyi bah
Sanda takoshi
Yace bara yake 'dakinsa dake jikin nata yayi wanka
Tace Owkie
Yana fitta taje itama tashige toilet danyin wankan
Bayan tafitoh tamulke jikinta da humra me da'din qamshi tasaka wata dogowar rigar
baccinta me rigar mama. Tayi mata kyau Sosai
Sai tayi addu'a ta kwanta
Can shima yasaka kayan baccinsa saiya 'dauki wayansa ya turama RAMADAN da text
message kamar haka
_Abin tausayi ya rigani Amma xan rigashi angwancewa toh miye marabarka da RAMADAN
gauro😂_
Yayi Murmushi yana qoqarin rabata da rigarta Yana fa'din aina dena maraicin kwana
ni 'daya☝🏻😆
Cikin nisha'di KHAMIS ya rungumeta Yace Wlhi kinutsu kibarni na sami nutsuwa.......
By Hajju
[11:21AM, 07/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: R🇦HAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [7:34PM, 09/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 109*
Lokacin daya samu nasarar kawar mata da budurcinta ba qaramin qara tasake bah
Duk da yaficce daga hayyacinsa hakan bainashi ji qarar nata har Cikin ransa bah
Yasa mu nasarar rufe mata baki da bakinsa. Sosai ya wahalar da ita harda kukanta.
Murmushi yayi dan yasan ya sameta da yawa dan haka yaqara maqaleta sukasha
baccinsu.
Washe gari bayan sunyi wanka sun ha'de sai qamshi suke. Dan kallo 'daya xaka musu
kahango hasken amarci na haskesu
Suna qaryawa afalon nasu XEE dai sai satar kallan mijin nata take tana mamakinsa
Ashe dai ba'a raina namiji Komai 'kan'kantarsa
Ya tsaida idansa sosai akanta Yace ina godema Allah daya temakeni ya mallakamin ke
matsayin matata
Tace nimah haka
Ya matso kusa da ita cikin muryar qasa qasa Yace naga sai satar kallona kikeyi
Kodai in qara jin da'di nane
Ta gallamai hararar masoya
Tace wane kuma jin da'di
Yayi Murmushi da matseta Sosai ajikin nasa Yace najiya mana Wanda saboda tsabar
da'di har cewa kike dan Allah karka barni inka barni mutuwa xanyi.....
XEE tawaro ido😳 Tace sharri xakamin
Yace tuna dai
Ta shagwa6e fuska Tace toh ai kaine kake fa'da bani bah
Takama fuskarsa tasakar mai kiss abaki Tace ni dakai mutu kara ba takalmin kaxa
uban 'ya'yana
Murmushi yayi yafara kissing 'dinta tunda ta6u'de mai hanya
Haka ko akayi yana gabah tana binshi abaya har sukakai falan Momyn nashi
Ta durqusa tagaisheta cikin ladabi da kunya
Momy ta amsa da kulawa
Taqara da cewa matso 'yata gareni..
Haka XEE tamatso kusa da ita. Aiko ta 'dora hannunta akanta Tace Allah yayi miki
albarka ya baku xuri'a 'dayyiba kamila
Wacce musulunci xaisan da xamanta
Ba kunya KHAMIS ya saqalo da duk hannayansa tabayan Momyn. Ya rungume momyn Yace
AmEEn momyna kina San jikoki Sosai ne
Ta make kansa Tace rashin kunya ko
Yayi Murmushi Yace toh shikenan tunda baxaki ban amsa bah bara naje na tambayi
Dadyna
Yafa'di hakan da xame hannunsa daga gareta
Momy tayi murmushi da bin 'dannata da kallo
XEE Tace Momy kinada aiki ne
Tace a'a kije Ki huta kinji
XEE Tace toh
Haka tatashi ahankali tafice daga falan Momy batayi mamakin canjawar tafiyar
tatabah🙈
FAWAS ko bayan sungama breakfast xai tashi kenan yaji Momyn shi nacema Dady tanaso
taje gidan qanwarta dake nasarawa
Yace ba lefi tadawo lpy
Qawata kixo kisha labari pls. Kuma kar kice min baxa kixo bah....😔
RAMADAN yayi Murmushi Yace am sorry Aunty XEE ban kaimata wayan nata bah.
Amma bara na kai mata yanxu
XEE Tace toh RAMADAN pls kaimata da sauri dan Allah
Tace toh
Da sauri RAMADAN ya rufe mata baki kuma ya waro ido ka'dan alamar nuna tsoro
Bakin XEE na qaiqayi batabar SAILUBAH haka bah sanda tabata labarin wahalar da
KHAMIS ya bata
SAILUBAH tawaro ido Tace 'dan qaramin yaran nan ne xai wahalar dake😳 Wlhi
qaryane 😀
XEE Tace narantse miki da Allah
SAILUBAH tayi dariya Tace story kawai amma maixai iya wannan yaran😂
Tsaki XEE tajah takashe wayanta dan tafi kowa sanin rashin ganewa irin na SAILUBAH
idan akan abin data raina ne
FAWAS ne xaune a office 'dinsa yana kallan wani fatan daya futar na wata atamfah da
sukesan Su futar.
Bayan ya gama ne yakira Momyn shi yana cewa mum kin dawo ne
Tace aa saidai ina....
Sam bai jira qarashan xancanta bah ya kashe wayan dan jin yaji abinta yake fatan
ji....
Yana qoqarin tashi Dadyn nashi ya shigo yana cewa naga naka my son
Ya juyo mishi da laptop 'din gabansa
Murmushi Dadyn nasa yasakar masa da shafah kansa yana cewa dts gud my son
Hmmm Yayi kyau Sosai
FAWAS yayi dariya Yace dama Dady inasan xuwa gida yanxu ne
Yace ba lefi my son Amma karka 'dau lokaci Yace toh
Gudu Sosai yakeyi burinshi kawai yakai gidan nasu ya rage xafi da matar tashi
[5:45PM, 09/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: Aiko yana yin parking ya fitoh da gudunsa
Sam baiyi shashin HAMEEDAN bah. Dan yasan uwar 'Yan surutu CE yana da tabbacin
tana tare da babah Hinde
Dan haka yayi part 'din Momyn nasa.
Nan ko sukaci karo da juna. Ita tatawo da niyar fitta shikuma ya sawo kai
Da sauri tamatsa baya tana cewa kayi hakuri bansan katawo ba.
HAMEEDA taqara jah da baya ganin yanda yake matsowa kusa da ita
Ga kuma momy afalan. Ta lura Sam baisan da xaman Momyn ba. Kuwai iskanci ne
agabansa
Dan haka saita fara mishi nuni da ita da ido Amma ina FAWAS yayi nisa
Kunya Baqin ciki takaici suka cika HAMEEDA tamkar xatayi kuka Tace Momy Momy Momy
fah.....
Bai bari ta qarasa ba ya katseta da cewa kimin Shuru uwar 'yan magana. dan nasan
momyn bata nan Kinga kuwa idan zakiyi iwun duniyar nan sai dai baba Hinde tajiki
Kuma ita ba kawo miki 'dauki xatayi bah dan taganni. Tasan nine na ritsaki...
Waima in tambayeki
shin baki San aljannah ne.
Yafa'di hakan da nufin kai bakinsa cikin.
Da sauri Tace gafa Momyn nan.....
Ahankali FAWAS yakai kallansa inda take mishi nuni da Momyn nashi.....
Yayi daidai da lokacin da itama momyn takai kallannata kansa
Aiko da sauri yasake HAMEEDA ya ficce daga falan da wani shegen dugu saboda wata
kunyarta da takama shi.....
Haka batare da wani 6ata lokaci ba. itama HAMEEDA tabishi da nata gudun xuwa part
'dinta tanaji kamar qasa tatsage tashige ciki
Yamma can suka ha'du Su uku inda suka xubama KHAMIS ido👀 ganin yanda yake cikin
nisha'di
RAMADAN Yace shegen ka kashe bos kenan irin wannan annuri haka
KHAMIS yayi Murmushi da tashi ya dafah RAMADAN Yace fatana kayi saurin mallakar
Aunty LUUVAH. Nasan idan kaji Komai daga nesa xaka dinga sakar mana dariyar farin
ciki....
Wata shegiyar dariya RAMADAN yayi Yace tab kace Kullun saiya kwana da ciwan ciki
kenan
KHAMIS Yace toh yaxaiyi
RAMADAN yace ai ina tabbatar maka baxai kai wata ahaka ba
Dan nasan in yagaji cire kunya xaiyi ya saka momyn tashi agaba yasa mata kuka akan
tabashi Matarsa.
Aiko KHAMIS ya qara saka dariya
FAWAS najinsu yayi musu shuru har suka qaracimai iskancinsu suka barshi
Sanda HAMEEDA takai kwana biyar Sannan tafara sakewa da Momy kamar da
Momyn na kallansu duk da HAMEEDAN bata shigowa saita tabbatar da FAWAS yabar
gidan Sannan xatayi part 'din Momyn tagaisheta
KHAMIS ko yasami XEE yanda yakeso sai kwasar amarci yakeyi abinsa
Yana wani qara haske sheqi daga shi 'din har ita
RAMADAN ko kallan Aunty kawai yakeyi yana addu'a Allah ya nuna masa ranar da xata
xama mata agaresa
Yau take laha'di Bayan sunkaima 'Yan matansu xiyara Su biyu Suna Hanyar dawowane
wayar FAWAS tafara ringing
Da sauri ya 'dauka Ganin momyn shice
Yace yes mum
Tace kaxo gida yanxu ina nemanka.
Yace ganinan toh
Dake XEE tama KHAMIS kamun kaxar kuka Sam Mantawa yayi da wasu 'Yan matansa😆
Sai yabar RAMADAN da FAWAS sunata fama
Dan haka yanxuma Su biyu ne suka fitta
RAMADAN Yace sai kayi sauri ka saukeni da alama yau ango kake
FAWAS Yace kai share banji hakan ajikina bah
RAMADAN yayi Murmushi Yace idan hakan ta kasance ka 'daukar min alqawarin xaka
jajirce har Allah yasa kasamar mana baby acikin wannan daran
FAWAS yayi dariya Yace idan har hakan takasance nayi maka alqawarin wannan sallar
da xamuyi xan roqi Allah yasa nasamu baby acikin daran
RAMADAN yafitta daga motar yana cewa toh ina maka fatan alkairi
Yace nagode Sosai 'dan uwa...
RAMADAN ya qarayin Murmushi Yace Wlhi kayi guxurin kaxar cin amarcin naka dan da
gaske naji ajikina
Toh FAWAS Yace mai yana dariya
Gun Auntyn nashi RAMADAN yanufah da rikici dan yau iskancin nasa ya motsa
Sosai yakesan ya kalle bakinta da tsokanarta
Yana kallo tayo Alwala ya tashi sukayi sallar yayi mata addu'a Sosai da tambayarta
yanda take tsarki
Tagayamai Komai anutse
Sosai ya rungumeta kamar wani xai kwacemai ita yana wani lalla6a kamar kwai
Tanajinsa talangwa6e mai tana kuma yima Momy addu'ar Allah yasaka mata da alkairi
Washe gari haka FAWAS yadinga nan nan da ita cikin so da qauna
Da wayowayo sanda ya qara jin da'dinsa da ita. Nan tafara jin 'dan tsoransa ka'dan
Kallo 'daya xaka mishi kasan yana cikin tsananin farin ciki
Dariya KHAMIS da RAMADAN sukayima FAWAS sukace Alhamdulillah mun tayaka murnah
Yace Allah abin godiya nagode yanxu Saura kai.
RAMADAN yayi Murmushi Yace nima gani akan hanya ai
👯👯👯👯.....
____________________
Sama kuma 2 bet room ne na mata da miji sai qayataccen falo da ke6antaccen wajan
hutawan masoyan da suke shirin mallakan gidan
Idan kafito harabar gidan babbar barandace gefe guda wacce xata iya 'daukar motoci
uku batare da takura bah
Idan kuma kakalli 6angaranka na hagu qaramin ciki da falone ta toilet aka fittar
dan xaman wanda yaxoma masoyan xuwan xuwan baxata
RAMADAN ya kalli Dadynsa Yace gashi qaramin gida sai dai yaxo da kyau kuma tsarin
ya burgeni
Dadyn nashi yayi Murmushi Yace toh my son anan xaka xauna kai da Matarka.
Kan kayi tunanin fitar da naka tsarin gidan
RAMADAN yayi Murmushi Yace nagode Dadyna Amman wannan ciki da falan daka ke6ance
shi fah
RAMADAN da yake tuqa Dadyn nasa Yace kaga Dady tunda sauran sati 'daya da kwanaki
bikin xanso inje inga junior kafin lokacin
Dady Yace balefi sai kuje da Momynka...
kufara shiri tun yau gobe jibi saiku 'daga
Da murna RAMADAN Yace tnx my Dad
Amma fah banaso kagayama junior xuwanmu dan inaso in masa baxata
Yace balefi
Ahaka suka dawo gida Suna hira cikin jin da'di Sosai
A daran RAMADAN yake gayama SAILUBAH xaije kaima 'dan uwan nasa xiraya tata6e baki
Tace daka barsa dan Wlhi baqaramin kewarka Xanyi bah
Yakama fuskarta Yace Karki damu Auntyna Bayan kwana uku kawai Xanyi
Cikin shagwa6a Tace nidai.....
Ya katseta dacewa kedai Mene Tace kayi kwana biyu
Tace angama Auntyna ko kwana 'daya kikace haka Xanyi fatana dai ki kulamin da kanki
Tamai kiss agoshi Tace kaima kakula min danaka kan
Yayi Murmushi da cewa Kullun a kula miki da kaina nake
Haka Washe gari har kuka sanda SAILUBAH tamai. Daqar dai ya lallasheta....
Suka samu suka cilla qasar England
Bayan sun huta RAMADAN yayi wanka Khairat na bacci Yace mah Momy bara naje na
rigaki ganinsa
Tace hhmm aini sai gobema xan gansa
Junior ya rikice da ganin 'dan uwan nasa dan haka da sauri yabar harkar tashi da
Shakira wacce tasaki baki tana kallan junior Tace dama Ku twice ne
Yace eh shine Babba pls kiyi sauri kibar nan yanxu
Yafa'da lokacin da yake xuwa jallabiya
Junior yamarairaice mah Senior waishi ala dole saiya yarda dashi
Senior RAMADAN yayi Murmushi Yace wai na tambayeka ne...
Cikin sanyi junior ya girgixa masa kai alamar aa
Yace ya isa haka....
Dan haka bani rungumah inji 'duminka kafin in hukuntaka...
Da sauri junior ya rungumeshi sukayi dariya cikin qaunar juna
By Hajju
👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
Ni 'Yar Luv CE ba abinda nasani kamar soyayya. Dan haka kumin afuwa masoyana dan
so yayi min mugun kamu👯
Haka xanta suburbu'do muku Littattafan akan sOO💔 👯
By Hajju
[7:35PM, 09/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: R🇦HAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [11:59PM, 11/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 110*
Bayan sun gama murnar ganin junannasu ne senior ya hauyima junior wa'axi me ratsa
jiki
Yana nunan mishi illar xina da abinda take haifarwa
Sosai jikin junior yayi sanyi ya 'daukarma 'dan uwan nasa alqawarin xaiyi qoqari
wajan ganin ya dena aikatata
Senior Yace kadena kawai. Junior yayi Murmushi Yace nadena brother Insha Allah
Sosai suke shan hira junior yayi Murmushi Yace yanxu fah Saura kwanaki kaxama Ango
ko
Senior Yace kana mamaki ko
Yace kwarai kuwa
Yace toh kadena mamakin dan ina tabbatar maka Saidai kaxo ka sameni da babyn ka
Junior ya qarayin Murmushi Yace idan hakan ta kasance xanfi kowa farin ciki
Yace xata kasance ......
Tace muma haka SADEEQ ya karatu Yace lpy lau Momy ina Khairat tawa.......
Da gudu Khairat tafitoh daga bet room tana cewa Ya junior nah
Cak tatsaya tana kallansu
Momy Tace yana tambayarki kina futuwa
Tace Momy gaya min wanene aciki
Momy tayi Murmushi Tace ki gano shi da kanki dan baxan nuna miki shi bah
winin ranar haka junior yata yawo da senior RAMADAN Yana nuna masa gurare da dama
Hakama Washe gari har da Momy suka fitta
Sai dare suka dawo
Tun adaran Senior RAMADAN ya hau shiri dan tafiya gobe
Ya kira Dadyn nasa dan ya gaya masa Saidai bai 'dauki wayan bah
Yace Momy bai 'dauka bah
Tace qila yana masallaci ne
Ni daka bari sai jibi ma tawo gabaki 'daya kaga sai kaxa6ar mata wasu kayan
lefan.....
Senior yayi Murmushi Yace no Momy basai na xa6a mata ba. Aikema kinsan kayan datafi
so
Junior Yace wai LUUVAH.....
Momy Tace eh
Senior ya gallamai harara Yace watoh LUUVAH kai tsaye
Junior yayi dariya Yace toh kayi hakuri Aunty LUUVAH....
Momy tayi dariya Tace ai kaikam ka shiga uku tunda kaxo a qani
Yace aikowa kam Momy
Wayar senior tayi qara ya 'dauka da sauri ganin Dadyn nasa ne
Yace gabe ina tafe Dady kaxo ka'daukeni tara xamu taso
Yace toh my son Allah ya dawo min dakai lafiya bani junior najishi Yace AmEEn da
miqama junior wayan
Bayan sun gamah wayan ne junior Yace pls mana brother kabari kutafi da Momy mana
Senior ya waro ido Yace rufamin asiri dan kuka wiwi Auntyna tasa min 'daxu😳
Yace to saime
Yace sai in rasa nutsuwata
Shuru junior yayi ya tashi dan ficcewa daga 'dakin yana turo baki....
Da sauri senior yasha gabansa yana cewa toh kayi hakuri mana 'dan uwana kafahimceni
bana San tashin hankalinta
Junior yajah tsaki cikin wani hali Yace Wlhi brother kadena biyemah duk abinda
takeso saboda wata ranah
Yace toh naji kayi hakuri
Yace ya zanyi dakai kabari mace ta shanyeka
Rungumarsa Senior yayi yana Murmushi Cikin ra'da Yace baka San sO bah
Shima cikin ra'dan Yace hmmm abar kaxa acikin gashinta dai brother
Yace na barta.......
Washe gari da misalin qarfe tara ko haka RAMADAN ya bar 'dan uwan nasa kamar yanda
ya sameshi yayo qasarmu mai da'di
Lokacin da jirginsu ya sauka yana fitowa ko yaga Dadyn nasa ya rungumesa suka tayo
gida Cikin farin ciki
Dady ya kallesa Yace nayi kewarka my son 'dan kwana biyun nan
Yace Wlhi nima Dady
Sanda yayi wanka yaci abinci Sannan. Ya kira FAWAS da KHAMIS ya gaya musu dawowar
tashi
Aiko haka sukabar abinda suke sukaxo gareshi
Sunyi murna Sosai da dawowarsa
FAWAS Yace Allah rashinka kusa samu RAMADAN matsala ne
KHAMIS Yace Wlhi kuwa.
Murmushi RAMADAN yayi Yace toh mutuwa dai nanan..
FAWAS Yace tare xata 'daukemu ai
Yace toh Allah yasa
KHAMIS Yace ya kaga Aunty LUUVAH
RAMADAN Yace ai batasan na dawoba
Yanxu dai nakesan xuwa gareta in bata mamaki
KHAMIS Yace inajinta 'daxo da Aunty XEE tana cewa rashinka kusa da ita maseefa ne
SAILUBAH tana kwance sai tunanin Qanin nata takeyi. Dan kwana biyun nan da tayi
bata sakashi a idanta bah duk saita nemi rasa nutsuwarta. Shiyasa 'daxomah tasamai
kuka......
Jin anshafi gefan fuskarta ne yasa tadawo daga tunanin nata ha'de da waro ido
Kiss tayi masa agoshi Tace Wlhi bana San kayi nisa dani
Yace baxan qara nisa dake bah. Dan ban manta kukan da kikasamin 'daxo ba...........
Sosai SAILUBAH ta tsure da ganin kayan taje tasaka RAMADAN agaba Tace Kasan ba
da'dewa xamuyi bah Amma kabari Momy taha'do wannan uban lefan😳
Yace aiba damuwa my Aunty kan murabu basai kidinga min ado dasu bah
Cikin marairai cewa Tace nifah nafara tsorata fah 😳 dan jikina yana bani kamar
Auren xai xama ba yanda muka tsara bah😳
RAMADAN yayi wani shegen Murmushi da wurga mata wani kallo Wanda yasan yamata mugun
shiga Yace hmm Aunty kenan
Karfah wani abu yasa tunaninki ya samu tangar'da
Tace nidai....
Ya katseta da cewa Aunty
Tace RAMADAN
Yace muje in rakaki Ki kwanta kiyi bacci kawai
Tace da tsakar ranan nan
Yace toh ai kina buqata ne
Tace toh aa
Yace toh mucanja hira
Tace toh wacce
Yace ta soyayya
Ta harareshi Tace ban iya bah
Yace xan koya miki
Tashi tayi taficce daga 'dakin. Yabi bayanta da kallo.......
_____________________
Ina gwanin wani ga nawa 😀👈👈🏻
Washe gari dukkaninsu tashi sukayi da wani ni'imantaccen farin ciki sakama kwan
*'daura Auran MUH'MD RAMADAN da FATEEMAH SAILUBAH da akayi*
Tunda aka 'daura gaban SAILUBAH ya tsinke ya fa'da
Takwantar da kanta kan cinyar XEE Tace naji wani XEE kema kinji irin shi lokacin
naki
Tace Sosai mah
HAMEEDA wacce RAMADAN ya matsamah FAWAS saiya kawota takalli SAILUBAH Tace Aunty
kice Alhamdulillah xakiji sanyi
Ga RAMADAN ko ana 'daurawa bayan manya sun gamah sukamah Auran albarka xamewa yayi
ya shige gida yaje yayi alwa'la yayi Sallah raka'a biyu. Ya 'daga hannunsa samah ya
fara addu'a kamar haka.........
Haka SAILUBAH na gani kowa ya Washe ya barta ita ka'dai a part 'dinta
Amma tanajin motsin innah Yalwa....
RAMADAN ko yana can kofar gidan nasa sanda ya tabbatar da tafiyan kowa Sannan ya
kira junior yana bashi labarin Komai
Murmushin yaqe junior yayi Wanda ake cewa kafi kuka ciwo
Yace toh brother ka shige gidan ka kulle da addu'a Sannan banaso ka tausaya mata
kayi qoqarin samarmin baby....
Yace Insha Allah 'dan Uwa na
Bayan sungama hirar tasu ne junior yaci kukansa yatashi yafara lafula na RAMADAN
akan Allah yayaye mishi soyayyar SAILUBAH
Sosai yasami nutsuwa sosai Amma bawai dan San nata ya ragu mai ba😰
Am so sorry my junior RAMADAN😰
Ahankali ya tura 'kofar bet room 'din nata daidai da lokacin data fitoh daga wanka
daga ita sai tawul.....
Ta waro ido waje👀 arikice tafara neman babban abinda xata suturce kanta dashi
Shiko sake baki yayi yana wani yarfe hannu Yace LA LA LA LA😧 Aunty......
Dama haka cinyoyinki suke da kyau😊
Kallesu 'yan mulu mulu dasu
Cikin maseefa Tace kafita kafita kafita manah
Yayi Murmushi ya haye gadan Yace Auntyna baxaki saka Kaya bane
Ta hararesa
Ya share da cigaba da cewa Aunty haka nonon.ki suke manya manya....
SAILUBAH tawaro ido 😳 cikin matsalancin kunya kamar xatayi kuka Tace dan Allah dan
Annabi ka fitta plssss
Yace xan fitta Auntyna Amma saikin bari na shafah miki mai kinga na qara ganin
cinyoyinki da nonan........
Bata bari ya qarasa ba ta jefashi da filo tana cewa Ashe dama kai 'dan iska ne.....
Jin abin da tace yasa RAMADAN yin Murmushi ya matso kusa da ita Sosai xai yaye
bargwan ta riqe gam idanta yaciko da kwalla
Tace RAMADAN
Yace wlhi Auntyna saina gani tunda kika cemin 'dan iska
Ba abinda xai hanani ganinsu kuma har in ta6asu in nuna miki iskancin
nawa .........
By Hajju
[11:59PM, 11/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele👯: R🇦HAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [6:50PM, 13/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T: 👯👯👯👯
*SAMAREEN*
*👯BANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 111*
Ai dajin haka tasamai kuka tana qara qamqame jikinta dan ita tunda aka 'daura
Auran nata dashi tashiga shakka akansa
Shuru yayi yana kallanta dan kuka take tsakaninta da Allah
SAILUBAH tawaro ido xata fashe da kuka yayi saurin katseta da cewa dakata fah
malama
Dama ai abaya Nace miki ina da shara'do'di uku kitsaya kijini kikaqi tsayàwa
kintuna
Wiwi SAILUBAH tasake mishi kuka tana cewa Wlhi baxan yarda da wannan labarin qanxan
kuregen naka ba
Ni sa'arkace da xakamin ciki kuma ai bah akan haka Nace ka Aureni ba.......
Ko mawa gadan RAMADAN yayi da qarfin tsiya yayaye bargwan jikin nata saita kasance
daga ita sai tawul 'dinta
Aiko ya matseta yakai bakinshi cikin nata yana aika mata da wani shu'umin kiss. Duk
yanda SAILUBAH taso kwatan kanta hakan kasa faruwa tayi. Sannu ahankali yakai
hanushi girjinta ya warware tawul 'din yafara sarrafah girjinta
Ji SAILUBAH tayi kamar xata sume. Takasa hanashi haka ya 'dau lokaci yana wasa da
budirinsa da breast 'din
Sanda taji sunfara mata xafi Sannan taqara volume 'din kukanta
Iya rikicewa RAMADAN ya rikicemah Auntyn tasa
Ganin hakàn ne yasashi kallanta ahankali idanshi jajir Yace Aunty kiyi hakuri baxan
iya barinki yau ba
Na umarceki daki tashi kiyi Alwala muyi Sallah kafin Komai ya wakana
Ni yanxu mijinki ne Auntyna baxan iya jure waccan rayuwar da kikesan muyi
bah........
Yana fa'din hakan yafara janta har sanda tasauka daga gadan ...
Ba musu Alwala ta 'dauro tasaka kaya sukayi Sallah raka'a biyu tana mamakin tsoran
daya kamata akansa yanxu. Har yatasa yimishi musu
Sosai ya dafah kanta yayi mata addu'a.
Ya kalleta Yace Aunty ya kikeyin wankan Sarki da Sallah
Ananne fah tagallamai harara Cikin raini Tace ban sani ba
Ya matso kusa da ita yana Murmushi tacikin kunnanta ya ra'da mata kusai naqara
shan breast 'dina tukunna sai kigaya min
Kunya da takaici suka cika xuciyar SAILUBAH ba shiri tafara bayani ganin yafara
qoqarin nemansu
Yayi Murmushi Yace naji Komai my Aunty dai dai kikeyin komai Allah narni dake
Da Asuba Bayan ya dawo daga masallacin unguwar ya mul'da kofar 'dakin nata
Lokacin ta'idar da laximi kenan dan haka tabu'de mishi
Yana shigowa ya rungumeta yana cewa ina kwana Auntyna ni 'daya☝🏻
Ta fara qoqarin kwatan kanta tana cewa lafiya sakarni mana
Yace aa. Tace dan Allah
Yasaketa yana cewa kika qara kullemin 'kofa Wlhi saina hukuntaki
Ta harareshi Tace aikowa da 'dakinsa meye saika shigomin nawa
Yace xan gaya ki da Abba Wlhi ince kina kullemin 'kofa dan karki bani hak'kina na
Aure
SAILUBAH ta waro ido
Dan tuna kashedin da Abban nata yayi mata
Aiko saiga hawaye Tace yanxu sai ka iya gaya masa haka
Yace eh mana Auntyna.😀 dan yanxu naxama Mara kunya tunda naga breast 'dinki kuma
har nasha kinga ai kunyata ragaggiyace.......
Tura shi falo tayi ta rufe kofarta tana mamakin damah RAMADAN 'dinta haka yake
Qarfe Tara tayi wanka tasaka wata riga da siket ta atamfah tsinkin ya matseta Sosai
ga Komai nata ya bayyana
Tafitoh falan nata tana tsaftace shi tana addu'ar Allah yasa karya fitoh har
tagama......
Jitayi tayi ana kwankwasa kofar tasu tana bu'dewa taga direban Momyn RAMADAN ne
'dinne da abinci
Ta kar6a da fara'a yana gaisheta
Tace ka kaima Innah Yalwa nata
Yace eh Tace mah ingayama Momyn gobe karta aiko ita xata muku
SAILUBAH tayi Murmushi Tace xandai mana ina ita ina wani yin abinci kagaishe min da
Momyn kawai Yace toh sai anjima
Tace mu yini lpy
Taje tajera Komai a dining tana juyowa suka ha'da ido da 'dan Qanin nata
Yayi wani qif qif da ido yana kallanta
Sanda takwashe tsaf tana niyar fitowa saijinta tayi rungume ajikinsa kansa bisa
qirjinta
Tace yaushe kakigo har kaban tsoro Yace yanxu Aunty
Tace toh muje
'Dago da kansa yayi ahankali ya kalleta Yace Aunty I Luv u
Tace me 2 .
Ya 'dan marairaice ka'dan Yace Aunty xaki haifamin yara da yawa
Tayi saurin girgixa mai kai alamar aa
Yace Aunty toh meyasa
Tace katsaya a Qanina dan Allah
Yace Aunty nidai baxan tsaya awannan matsayin bah yanxu
Kar6ar cup 'din hannunta yayi ya ajiye gefe ya qara rungumaita idanshi cikin nata
Yace nima ban san lokacin bah. Amma nasan na ibu shekaru masu yawa Auntyna...
Hawaye ya xuboma SAILUBAH Tace Amma kacuceni RAMADAN kana nufin burina baxai cika
ba kenan. Ya kama fuskarta da hannunsa biyu ya fara tsotsar bakinta cikin wani
yanayi na nutsuwa yanayi tana biye masa....
Sosai ya fara burkitata.
Can ta fara qoqarin kwacen kanta dan ganin ya dawo kan breast 'dinta
Tace kabarni haka RAMADAN yaqi kulata sai tasamai kuka
Awale ya barta....
Aiko da gudu tabar kitchen tayi bedroom 'dinta ta fa'da gado tana kuka qasa qasa
Da sauri ya bita ya haye gadan ya rabata da rigarta arikice ya hau tsotsarta tana
kuka yana sauke ajiyar xuciya daci gaba da budurinsa
Sanda yaga kukan nata yayi yawa ya barta Amma tana maqale ajikinsa
Sosai ta sake mai jikinta ya gyara mata kwanciya Yana shafa bayanta har bacci yayi
Awan gaba da ita daga bisani shima baccin ya 'daukesa tare da mafarkan junansu
Basu tashi farkawa bah sai gab axahar wannan mah yunwace ta tatashesu badan sungaji
dajin 'dimin junansu bah
Itace tafara tashi ta xubama Qanin nata ido tana tunani barkatai akansa....
Kamar yasani ya bu'de idansa ahankali ya sauka cikin nata Yace Aunty kinyarda inyi
miki ciki in sami yara masu albarka agareki
Ta 'dagamai kai da cewa na da'da'de da sanin Kaine farin cikina RAMADAN. xuciyata
Kullun so take tadinga Kasan cewa da kai. Nima ina maka irin San da kakemin.
Ya lumshe ido ahankali ya bu'de Yace Aunty kiss me
Aiko ba musu takai bakinta cikin nasa tana tsotsa ahankali ahankali. bai tayata bah
Amma yana jin da'di Sosai
Sanda tayimai San ranta ya fara wasa da breast dinta tace aranta aifah sun shiga
uku
Daqar ta lalla6ashi ya barta dan tana tsoran karya xarce.
Haka takaisa har toilet 'dinsa itama tayi nata dan qarayin wanka
Suna dining tana bashi abincin yana xuba mata shagwa6a da ta6ara iri iri dan xaune
yake kan cinyarta saiya ta6a nan ajikinta ya ta6a can
Duk yabi ya isheta Tace wai yaushe kaxama haka ne RAMADAN
Yace jiya Auntyna
Xatayi magana ya shagwa6e mata kamar xaiyi kuka Yace Aunty yau Xan xama Ango ko.
Tace aa
Yace dan Allah mana
Tace mexaka iya yi min Qanina
Yayi Murmushi Yace abubuwa da yawa Aunty.
Tace kai 'din
Ya gutsiri kwai yasaka mata abaki Yace eh manah .
Tace toh naji
Ya kwantoh da Kansa kafa'darta cikin sanyi Yace Xaki barni in girma yau ko
Tace xandai 6areka aleda
Yayi dariya Yace kodai ni in 6areki aledar ba
Tace xamu gani
Yace Allah ya kaimu daran Wlhi kika fara min kuka saina cinye bakin kukan
Ta harareshi Tace tashimin daga kan cinya Yace inna tashi na xauna akan tawa Tace
akujera
Yace aa nidai kibarni inna gamah jin 'diminki na tashi. Ya fa'di hakan da qara
qanqameta cikin sO da qauna
Dake ya gyara tunaninta akan san shi harta ankare tabashi ha'din kai
Yinin ranar nan haka suka dinga nunama junansu sOyayya taban mamaki
Dare nayi daya fara harka da ita kuka tasamai dan abin yaxo mata a baxata da tsoro
da kuma mamaki da al'ajabi gami da tunani
Tana kuka yana yimata ihu qasa qasa tare da wani maseefar sonta da yake kamashi.
Ashe sumewa tayi jin shurunta da yayi...
Bai tsaida buqatarsa bah. Sanda yasamu cikakkiyar nutsuwa sannan ya kaita toilet
anutse ya sata cikin ruwa
Da kuka ta farfa'do
Ya dinga lallashinta harta tsaftace kanta
Ya canja xanin gadan taxo takwanta
Ya koma yayo Alwala ya dinga lafula yana godema Allah daya mallaka masa Auntyn tasa
matsayin mata
Washe gari taga sO agunsa Amma duk da hakan baibar mata shagwa6a bah
Tun jiya take neman wayanta Amma shuru bata ganta bah
Nanko RAMADAN ne ya 'dauke ya 6oye acewarshi saiya gama cin amarcinsa xai bata
wayan sayi gwulmarsun dakyau ita da Aunty XEE
Yanxu ko so yake yagama 6ata mata tunaninta da soyayyarsa dan ko tashi wayan mah
bai bu'de bah
Xusu gaida Innah Yalwa ne RAMADAN ya qarema Auntyn tashi kallo Yace Auntyna...
Tace Mene ne
Yace tafiyarki tacanjah fah😳
Kiduba yanda kike tafiya a'dan tale😬
Duk da taji kunyar maganar tashi sharewa tayi dan tasan tabbas so yake yacire duk
wata kunya tsakaninsa da ita
Ta gallamai harara Tace Waye ya canjamin itace
Kai mata kiss yayi yana cewa da haka xaki saba Aunty
Tace nidai kabarni Yace Wlhi baxan barki bah saina gyara miki tafiyarki. KosO kike
Innah Yalwa tagano ban maidake cikakkiyar mace ba. Tayi min dariya
Tace toh miye
Yace abin kunya ne Wlhi aganki ahaka😬
Xare kanta tayi daga gareshi ya riqe hannunta sukaje suka gaishe da Innan
Ta kallesu cikin sha'awa Tace Allah ya albarkaceku
Sukace AmEEn
Dabara Tafa'do masa Yace Auntyna naga wayarki 'daxo a Bayan kujera.
Da sauri tatashi Tace yauwa bara in 'dauka
Tana fitta ya bita Innah Yalwa tabishi da Murmushi irin nasu na manya
Rungumarta yayi afalan ya hau shafata yana cewa Aunty breast Tace baka gajiya ne
RAMADAN Ashe wayo mah kayimin.
Shuru yayi mata suka xube a kijera bayan ya samu abinda yake so
Nanko nasan lpy lau take. kana nan ne kana 6ata mata tunani
RAMADAN yayi Murmushi Yace toh kabata hakuri banso sakar mata wayan yanxu bah
Naso Suna fara magana tabata kyakkyawan labarin samun baby...
KHAMIS Yace Wlhi kabi mana Aunty LUUVAH a hankaki inba haka bah xamuxo yimaka xanga
xanga har cikin 'dakinka
Dariya RAMADAN yayi ya kashe wayan dan yasan KHAMIS ba gajiya yake da hira bah
Saidai in yana cikin damuwa
By Hajju.....
SAMAREEN BANA: allah ya qarq miki hazqqa,baseera, lapia y kuma taimakeki aduk inda
kike.
Kinasan so. Nima INA SANKI, INA SANKI, INA SANKI 💔💔💔💔💔💔💔💔 love so much ss.
[4:22PM, 13/01/2017] :
*🇸AMAREEN*
*👯🇧ANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 112*
Yanda Momy da Dady sukaga RAMADAN cikin farin ciki da annushuwa shiyasasu ganewa
Lalle SAILUBAH taji da d'an nasu
Cikin siyasa da dabara da wayo irin nasu na manya Dady yadinga shigarma da RAMADAN
kalamai masu ratsa jiki akan yanda xai tafiyar da Auran nasa
Har kunya sanda RAMADAN yaji dan sarai yagane mai Dadyn nasa yake San cewa
Yace nabaka sati 'daya my son kaci amarci kanka dawo office. Saidai kawai kadinga
xuwa skull
Yace toh Dady
Sun ha'du Su uku KHAMIS Yace gaskiya ne d'an Uwa Aunty LUUVAH tayi dakai wannan duk
annushuwan da annurin da suke haske fuskarka duk na Luv ne
FAWAS Yace kaji ka KHAMIS da wani xance idan bai 6ata mata tunani bah ai baxaka
ganshi haka vah
RAMADAN yayi Murmushi Yace kwaji dashi
Murmushi tayi Tace bamai min haka sai mijina uban 'ya'yana
Xagowa yayi ya xauna kan cinyarta yayi mata kiss Yace Allah Aunty naxata xan dawo
naganki gun Innah ne.
Tace dame xai faru
Yace da kuka xansa miki Kinsan 'daxo qiris ya rage na fashe miki dashi Allah ya
temaken dabarar qaryar ganin wayarki tafa'domin
Murmushi SAILUBAH tayi takama fuskarsa ta tsotsi bakinsa san ranta Tace ai nima na
lura da hakanne shiyasa natashi da sauri
Ya rungumeta yana cewa muje kimin wanka Aunty
Tace aa
Yace dan Allah ya kuri kinji
Tace gaskiya aa dan nasan tirkeni xakayi da wannan wayan naka
Sai kawani marairai cemin
Nan ko a gado kai jarimi ne
Suna xuwa bedroom tatsaya Yace mushiga dan Wlhi baxa kiyi min wayo bah
Tace wai wace irin funace dakai RAMADAN ta'ina xan farayi maka wanka.
Yace ta'inda kike yima Aunty....
Yafa'di hakan yana cire kayan jikinsa
Daga shi sai gajeran wando
SAILUBAH tasaki baki tana kallansa
Kama hannunta yayi yana cewa oh Su Aunty ba kunya kike kallam min abuna😀
In kinyi hakuri ai xan gyara miki tafiyarki anjimah ka'dan👌🏻
Kunya takama SAILUBAH kamar kasa ta tsage tanitse haka taji
kuma Wlhi bata kalli abar tasa ba. Sharrine kawai irin na RAMADAN🙈
Da qer ta'iya cewa na kallah 'din
nima meyasa kake kallanmin breast 'dina. Kake damunshi da futuna
Yace toh ai breast 'dinane ni ka'dai☝🏻
Wannan ko kunada damar mallakarsa ku hud'u 4.
Kunya ta qara kama SAILUBAH Tace nama fasa yimaka wannan 😂
Da sauri ya marairaice ya cewa Wlhi takice ke ka'dai Auntyna
Dan ba wata mace da take da damar mallakar miki ita.....
Kuma Allah kina yimin wankan kika ban abinci xan qara yimiki irin najiya tunda kina
so.......
By Rahamat
😂😂😂😂
Saidai kumin abinda xakumin
Ka'dan nayi
Hindatu danke nayi dan yau kisamu baccin ranah😂 nasan jiya da soyayyar SAMAREEN
BANAH kika kwana 😬
[11:50AM, 15/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T: R🇦HAⓂ🇦T
[20/03, 17:09] 80k: [10:48PM, 19/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T: 👯👯👯👯
*🇸AMAREEN*
*👯🇧ANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 113*
Murmushi tayi dan ganin yanda yayi maganar a 'dan tsorace. Saita watsa mishi ruwa
afuska. Da sauri ya lumshe idansa
Tana ganin haka tatashi da nufin barin toilet 'din. Aiko da sauri Yace Aunty......
Ta kallesa da gallamai harara. Tace ina nagamayi maka.
Ya girgixa mata kai yana wani kallanta qasaqasa.
Yace nidai kidawo pls
Kumawa tayi gareshi Tace toh gani....
Bugar qafarta yayi tayi taga taga xata fa'di yayi saurin jawota gareshi.....
Sauke ajiyar xuciya SAILUBAH tayi Tace Wato sanda ka 6atan kwalliyata ko .
Ya qara maqaleta yana cewa xanyi miki wata
Wanka sukayi wankan futuna. Acewar SAILUBAH. Dan daqar ta sami akanta agunsa dan
futunarsa
Koda suka dawo bedroom da sauri tabar mishi nan tayi 'dakinta.
Murmushi kawai RAMADAN yayi dan Sosai yake hango tsoranshi a idanta
Idan Nace yanda tasha wahala jiya haka tasha yau banyi mata adalci ba
Amma taji Maza
Dake yana jin maseefar tausayinta Sosai yabi da ita ahankali bai bata wani wahala
bah
Washe gari suna kitchen tana tana ha'da musu breakfast yana gefanta wai yana tayata
Ta ha'dashi da firar dankali
Sosai ya dage yana ferewa. Can yayanke hannun nasa........
Da sauri yayar da wuqar yana wàyyo Auntyna wayyo hannuna
Arikice SAILUBAH takama hannun tana wanke mai jinin. Fa'di takeyi dama ai sanda
nace kar kayi Amma kaqijina
Shuru yayi mata kawai yana kallan yanda tarikice
Bayan tatsayar mai da da xubar jinin ne Tace toh jeka falo na gode ahaka mah
Yace aa
Tace pls mana
Yace. Kibarni Ba abinda xanyi kawai kallanki xan dinga yi Auntyna
Tace ahakan mah ba barina xakayi bah
Isata xakayi da kira Aunty kaxa Aunty kaxa
pls muje in rakakah
Tana gaba yana binta abaya da qarema bayan nata kallo
Har dining takaishi Tace karka kuskura naqara ganin qafarka a kitchen d'ina
Yayi Murmushi Yace toh Aunty amma kika da'de saina biyoki
Tayi dariya da cewa nako xane ka
Ya waro ido ka'dan👌🏻 Yace baxan mah biyoki bah toh😀
Tayi Murmushi da mai gwalo Tace katemaki kanka
da kallan murmushi RAMADAN ya bita dashi yana godiya ga Allah daya bashi Auntyn
tasa matsayin matarsa
Qarayin Murmushi yayi Yafa'da tunanin gashi shi da ita tah haifamai yara goma
kyawawa
matan sunyo kamarta
Mazan sunyo kamarshi
😳😳😳😳
Waro ido RAMADAN yayi cikin tsoro Yace yanxu Auntyna xaki iya 'kona ni
Tace sosai mah
Yace wayyo Allah
Ya xanyi da Asma'u yanxu
Cikin 6acin rai Tace Allah kaqara kiran sunan wata 'ya mace a gabana Wlhi sai mun
samu mummunan sa6ani dakai
Murmushi SAILUBAH tayi Tace ina sanka mijina. Allah yabarmu cikin qaunar juna da
aminci
Amiien AmEEn yace da tashi ya rungumeta Yana cigaba da fa'din toh kixauna mana
Tace naqi wayan. In xauna ka 'danemin cinya ko
Ahankali ya 'daga mata kai da cewa pls Aunty kibani da sauri Kinga yau inadà
lectures
Ta waro ido Tace shine baka gayamin tun 'daxo ba
Nagaya miki yanxu Aunty
Qara rungumarsa tayi Tace yaushe xan koma ni.
Yace ba rana bare wata inji yara🙄
Tace haba 'dan Qanina 👌🏻
Yace Allah Auntyna
Xata qara magana yayi saurin hanata tawajan kaima bakin nata cafka
Taqar ta kwaci kanta ganin xai xarce
Tace Allah ka xarce kuka xan samah
Yace ina ankare dake ai baxan bari inkai nan gun ba
Sosai ya maqale mata kan cinyarta tana bashi Suna cigaba da hirarsu irin wacce
yalura tafisu
Anan ya bata wayanta tayi mamaki Sosai da mai kallan tuhumah
Yace Karki tambayeni dalilin da yasa na 6oye miki ita. Shuru tayi tarabu dashi dan
tasan tunda yace haka bako xaice mata Komai bah
Bayan tagama bashi brek 'din da lallami ta lalla6ashi yatafi 'daukar darasin nashi
badan yaso bah
Dajin Haka kunya taqara kama SAILUBAH Tace wane shi ai da wannan jiriyar
Ai mai samunta sai me shekarun daya xarce nashi
Dariya XEE tayi Tace shegiya Qawata kina wuta muna binki fetir Allah yakai RAMADAN
matsayin Babba
_ayyà kai shi matsayin. dan ya ban mamaki Sosai dayimin ba xata. tunda ya amshe
budurcina dama ai nashi ne_
SAILUBAH Tafa'di hakan aranta dan tanajin kunyan tacema XEE ya haqe rijiyar😂
Yau she Xaki xone pls ina san ganinki. SAILUBAH Tafa'di hakan dasan 6atar da xancan
XEE Tace tab ai sai kinyi wata hu'du kafin naxo dan wani ra'ayi nawa
SAILUBAH Tace miye shi ra'ayin naki
Tace sai RAMADAN ya gyaramin ke Wlhi xanxo
SAILUBAH tayi Murmushi Tace bangane bah
Tace Xaki gane nan gaba ai
Ta qarashe da dariya kana ta kashe wayan.......
*********************************
Dan haka Ahankali ya qarasa cikin kitchen 'din da rungumarta ta baya aiko tana
juyowa ta sakar mai wani amai gudun gaske
Saka makwan qamshin turaransa da ayanxu batasan qamshinsa
Waro ido HAMEEDA tayi da marairai cewa Tace kayi hakuri HABIBINA
Cikin damuwa Yace meyake damunki YAYATA
Tace tun safe nakasa cin Komai kuma inajin yunwa ga cikina Yana min wani iri
Kuma banasan qamshin turaranka
Ta qarashe da rushewa da kuka wiwi dan Sosai takejin yunwa
Am Sowie HA🇲IDA...😆
By Rahamat
Hajju 😜
👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
[,10:32AM, 15/01/2017]
Sunana Kadeejah
Wllh samareen bana yayi dadi dan yataba shigen tawa rayuwar nima inason kanin
kawata shima yana sona sosai kuma kanina nake cemai shikuma yace auntyna munshaku
sosai kamar da luva d Ramadan wllh dannima inyace karnai Abu to wllh bazanba amma
ni 😭😭😭😭akarshe iyayena suka hada aurena d wani bansaniba saida akakusa biki 😭
😭😭akamin auren dole Yusuf yaita rashin lpy nahakura yanzu yarana biyu shine Dana
karanta samaren bana nakome irin nawa nida Yusuf amma karshe ya bambamta ina godiya
dannayi farinciki lbr shigen nawa👍👍👍👍👍👍
Allah yakara basira
*AmEEN Amiien nagode kadeejah*
*Haqiqa mutane da dama sukan kirani awaya ko suyimin message akan labaraina yana
xuwa shige da labarin rayuwarsu*
*Ina jin da'din hakan Sosai kuma ina godiya ga Allah daya bani baiwar qiqirar
labarai irin naku*
*nasan xaku karanta wannan 'dan takaitattcan bayani nawa*
*ni Rahamat labaraina qirqirane kawai da baiwa da Allah da yayi min*
*nagode maka Allah daka 'daukaka darajata har ka'aramin tunin da nake rubuta labari
batare dana hange na wani bah*
*ina rokwanka Allah daka barni da masoyana mucigaba da qaunar juna har qarshen
rayuwarmu*
*xan fa'do muku yanda nafaro SAMAREEN BANAH insha Allah idan nagama shi*
👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
*Toh kadeejah naji SAILUBAH da RAMADAN sun birgeki har sukayi sanadin da kika tuna
da Qaninki YUSUF masoyinki adah*
😬
[10:49PM, 19/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T: R🇦HAⓂA🇹
[20/03, 17:09] 80k: [1:44PM, 26/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele: [8:37AM, 26/01/2017] R🇦
HAⓂ🇦T: 👯👯👯👯
*🇸AMAREEN*
*👯🇧ANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 114*
Ba qaramin rikicewa FAWAS yayi ba. Cikin tashin hankali Yace toh ya isa kukan haka
pls
Ya fa'da dajanta xuwa part 'dinsu
Toilet ya shiga ya gyara kansa itama tagyara nata kan
Ta shinshina Su....
Aiko taji qamshin da bataso. Ta nunamai
Yace Yauwa saiki 6oyeshi karna manta nasa
Tayi Murmushi ha'de da tashi tana cewa meya dawo dakai ne yanxu
Yace Wlhi YAYATA buqatarki.
Tace wayyo masoyina
Rungumarta yayi Yace Karki damu YAYATA Xanyi miki hakuri xuwa dare.
Tace mace tagari xuciyarta akullun so take tadinga farinta ran mijinta
Ya qara qanqameta Yace inyi abuna kenan
Ta 'dagamai kai Cikin wani salo takai bakinta cikin nashi tayimai mai kiss me
'daukar hankali. Kana Tace Komai ajikina mallakinka ne
Kayi yanda kakeso dani aduk lokacin da kayi ra'ayi...
Sun fitoh gwanin ban sha'awa Tace yauwa na tuna Momy tana San magana dani 'daxo
Mu duba ko tadawo
Yace aitun lokacin da nashigo tadawo
HAMEEDA tawaro ido cikin shagwa6a Tace shine kuma baka gayamin bah
Ya watsa mata wani kallo Yace ai bansan da hakan ba
Oho dai HAMEEDA tace aranta dan bata san inda xancansu ya dosa ba dan haka Tatashi
suka ficce xuciyar momy cike da farin ciki .
Koda doctor Marwan ya gamah binkicansa ya gano cikine da HAMEEDA na watanni biyu
Da FAWAS ya gamah jin bayanan doctor 'din rugumarsa yayi
Cikin jin da'di Yace Allah na godemah
Doctor yayi Murmushi yana mamakin FAWAS
Gashi dai qaramin Yaro Amma sai murna yakeyi da samun Cikin matar tasa....
HAMEEDA kam shuru tayi tabarshi dan har lokacin bata fahimci Komai bah
Dan da harshen turanci suke maganar
Sanda taga sun ke6e wajan ni'imantaccen shaqatawar Tace wai HABIBINA murnar miyene
haka tun a gida gashi mah a asibiti
Kuma kana kallona kana Murmushi ko farin Cikin daga gareni yake ne
FAWAS ya qara fa'da'da murmushinsa Yace YAYATA gayamin
Tace me fah
Yace kina San yara .
Tayi Murmushi Tace Sosai mah
Jan ajiyar xuciya yayi Yace toh kinada ciki...
HAMEEDA tawaro ido😳 Tace da gaske
Yace Wlhi da gaske.....
Da sauri tatashi Tace wayyo da'di nima yanxu xan Haifa yara doxin doxin 😆
Dariya FAWAS ya fashe da ita Yace aikowa kam. Kishirya bani yara masu yawan gaske
Wlhi ina matuqar MASEEFAR sansu
Tayi Murmushi Tace Allah ya kawo masu albarka ni kuma nayi maka alqawarin xanta
baka Su doxin doxin
Yace nako gode YAYATA
Tace Amma kajama wannan yaran naka kunne ko yarinyace tadena hanani cin abinci....
Janta motarsu FAWAS yayi sanda suka bar wajan ya tsaida motarsa can gefan titi ya
mannamah cikin nata kiss Yace pls baby ko boy kadena hana YAYATA cin abinci
HAMEEDA tayi dariya Tace lallemah
An gayamah yana jine
Da sauri FAWAS ya harareta Yace angaya miki kurmane
Murmushi kawai tayi ganin yanda yake shafah Cikinta cikin farin ciki
Momy ko jin xarginta ya tabbata Su HAMEEDA na barin falan tatashi ta'dan taka rawa
tana cewa Allah nagodema ka azirtani da 'daya☝🏻 ka azirtani da jikoki masu yawan
gaske.....
Amiien AmEEn taji ance
Tana 'dago kanta taga Dadyn FAWAS ne
Tace sirikarka tana da ciki Dadyn FAWAS
Yace ai tunda naga kintaka rawa nasan ba qaramin abu bane ya faranta ranki
Amma naji da'di Sosai Allah ya sauketa lpy
Tace Amiien....
RAMADAN na manne da SAILUBAH yana bata mata tunaninta dukta sakarmai imaninta
Sukaji kwan kwan
Awahale RAMADAN Yace Aunty FAWAS ne
Tace har yaxo
Yace kinsanshi da bada himma
Tace aikam tashimin a cinya Yace idan naqi fah
Tace saimu barshi yata tsayuwa har yagani yatafi. Kaga kenan bai baka make news ba
Murmushi yayi ya tashi yana lakuce mata hanci Yace kin wani kananna'dani kin hanani
xuwa ga Dad
Dariya😂 Sosai FAWAS ya kwashe da ita Yace kace ni an'dan min sausaici ka'dan
RAMADAN Yace hmm yanxu ina xaka
Yace ga KHAMIS xani pls muje muji tare dan Allah
Tas tashanye agwali6an tana xaune tana karanta wani Littafi waishi *LEEKITAN
ZUCIYAH*
```ita ka'dai Rahamat tabama aranshi banda su siS ummu Yahaya da siS Hajjaju masu
leqan samareen banah```😂
RAMADAN ya 'dane kan cinyarta yana leqa fuskarta Yace lalle Aunty. Shine harda
shanyewa baki ragemin bah.....
Kantayi magana yayi saurin ha'de bakinsa da nata
Ta tureshi Tace baka gajiya RAMADAN
Fakar idan Innah tayi tashafa cikin nata soyayyar shi tacika xuciyarta🙂
XEE takalli FAWAS Tace yadai naganka Cikin farin ciki haka
Yace kedai bari kawai Aunty XEE
Tace baxa dai agayamin bah kenan
Murmushi yayi yace xan gaya miki amma saikin fara amai😀
Harararsa tayi tace kariqe abinka Toh
Tafa'di hakan ranta 6ace da ficcewa daga falan
Murmushi KHAMIS yayi yana rayawa aransa yaushe xaiga ranar da xata fara laulayi
Kullun maganarsa gareta kenan
Da farko dai baso takeyi ba. Aganinta bataci amarci ba
Dan haka takemai da'din baki akan tana so
Amma yanxu da taga yana so Sosai sai kawai tasa aranta itama tanaso
Amma har yanxu shuru kakeji...
Abin ai na Allah ne 😀wai budurwa da jika baxawa bata samu ba
Haka KHAMIS yatashi sukaje suka suyo masu kayan kwa'dayi kala kala
Kafin suka rabu kowa yayi office
Yace kaga Su brother Aunty SAILUVAH.... Ta maqaleka sai yanxu tabarka kajini ko
Yace Allah Sarki ka'dauki haqqinta
Junior yayi Murmushi Yace toh fa'damin dan Dady ya kirani 'daxo akan maganar wannan
ku'da'dan har kun gama lissafin ne
RAMADAN yayi Murmushi Yace eh Kasan na tsorata da dukiyan
Yace nasani ai dan idanka bai bu'de akan naira ba
Yace sonake muba Dadynmu da Dady Auwal da Dady Jibiril wani Abu a cikin duniyar.
Junior yajah numfashi Yace ya dace kam kabasu abinda ya dace cikin nawa kasan Amma
banda Dady Jibiril
Haka kaima banyarda ka bashi naka bah....
RAMADAN Yace mexai haka muyafe mishi mubarsa da Allah mudena Duba abinda yayi mana
abaya mu fuskanci gaba
Tsaki junior yajah Yace kana da takaici brother nagayama ban yarda kacire ko sisi
cikin dukiyarnan kabashi ba
Idan kuma kaqibin xancena kayi abinda xakayi kawai
Yace am Sowie 'dan uwana
Naji xanyi yanda kakeso aman muyafe mishi
Yace mudai barshi da Allah kawai
Ba wani maganar yafiya
Ya kashe mana iyayan namu bamu 'dauki fansa ba sannan kace muyafe masa inaaa
Wannan kuma shida mahaliccinsa
RAMADAN Yace rayuwar daxamu barta mexai kawo rashin yafiya cikinta.....
Junior ya katseshi da cewa sai anjima da Allah
Amma kafin nan kashafa cikin matarka ka gaisar min da Babyna
Dan jiya nayi mafarkin harta haifa maka twice bye.....
Yana fa'din haka ya kashe wayan
RAMADAN yabi wayan da kallo yana mamakin xafin rai irin na 'dan uwannan nasa
Tunani yayi Sosai kafin ya koma ga Dadyn nasa yana cemai toh Dady abin da yadace
yanxu araba dukiyata kashi biyu aban kashi 'daya
Sauran Kusan yanda xakuyi da ita kai da Dady Auwal
Hakama ta 'dan uwana
Murmushi Dadyn yayi Yace RAMADAN kenan
yanxu tsofa yaxo mana ba'abinda Xamuyi da dukiya me tarin yawa haka
Xadai mu 'dauki abinda yadace mubar muku sauran
RAMADAN Yace toh
Karabata kashi uku ka'dau 'daya kaban 'daya inyaso saika ajiyemin 'dayan
Hakama xakayimah ta 'dan Uwana
Nan Dadyn yakira junior RAMADAN yake qara labarta miki yanda sukayi da RAMADAN Yace
ba Komai ai Dady albarkarku kawai muke nemah
Yace kunsamu my son ayi kararu lapia Yace toh Dady
Tana kitchen tana 'dan wanke wanke ya rungumeta ta baya Yace Auntyna...
Ta wanke hannunta da juyo ta rungumeshi tana cewa Wlcm 'dan Qanina kuma mijinta..
Jan ajiyar xuciya yayi jin yanda qamshin sanyayyan turaranta yanda yake shigarsa
Ya lumshe ido ya 'dago da kansa a hankali suka ha'da ido
Yace Aunty....
Tace kadawo da futuna ko
'Daga mata kai yayi Cikin yimata kallan qaunah Tace toh baqona yaxo
'Dan waro ido yayi Yace aike dashi saikin haifamin Babyna...
'Dan uwana yayi mafarkin kin haifa min kyawawa biyu masu kamarki
Tace waya ganni da 'yan biyu. Kabarni dai da 'dayan
Qara rungumeta yayi Yace Wlhi xaxxafar addu'a nayi miki akan Allah yabaki 'Yan biyu
sau uku
Kafin ya bara baki 'yan 'dad'daya 😀
SAILUBAH tawa waro ido 😳 Tace tab wannan story ne
A'inama kata6a jin anyi haka
Yace xa'a fara daga kanki
Nasiya miki kayan kwa'dayi da yawa tunda nalura babyn nawa kwa'dayayyene
Tace aidama shine yake sani kwa'dayi
Yace eh mana kuma shinema ya qara miki da'din wannan abun
Ya qarashe maganar da shafa bayanta
Murmushi tayi dakai nakinta cikin nashi yana aika mata da sakwanni itamah tana
bashi nata salan....
Ganin da tayi yafara rikice mata ne tajashi bedroom nasa
Ya rigada ya sabar mata dayi masa wanka dan haka yanxu mah itace tayi masa
Saidai Suna fitowa ya ya rungume abarsa sanda yasami cikakkiyar nutsuwa da gamsuwa
sannan ya xuba mata ido
Yace Auntyna dana rasaki matsayin matata dana shiga uku.
Tace ai tun ran farko ni taka CE RAMADAN
Shiyasa kake samun sa'a akaina kaketa juyani San ranka.......
Wasa yahauyi da qirjinta yana cewa jifan ki nadinyi da addu'a shiyasa
Shuru tayi masa Ganin yana san qara samin nutsuwa
Sosai taqara bashi ha'dinkai. Sanda suka 'dauki lokaci me tsawo kafin suka tsaftace
jikinsu
Tana gyafan gado tana tsame gashinta ne taga message 'din nasa
Gyara xamah tayi Sosai ta waro ido Cikin matuqar raxana Tace kaikakai
RAMADAN ya rungumeta ta baya Yace lapia Aunty
Tace kaduba maqudan ku'din daka turomin😳
Toh menene
Yafa'di hakan da kissing 'din wiyanta
Tace miliyoyun ku'dine fah RAMADAN kaduba fah😳
Yace eh nagani
Tace toh ai ban sanka dasu bah......
Juyowa yayi gabanta ya 'dane cinyarta hannunsa saqale da wiyanta ya manna mata kiss
Yace kinutsu Auntyna kijini dakyau
Cikin damuwa Tace ina jinka mijina
Yace Ni da d'an Uwa na junior marayune fah...
Arikice ta qara tsaida idanta gareshi
Kwantar da kansa yayi ga qirjinta yafara bata labarinsu. Tas ya gaya mata Komai
Tuni xuciyar SAILUBAH tacika da qaunar mijinta da 'dan uwansa
Ita bata ta6a sanin Dady da Momy basu suka haifesu bah
Rungumar mijinta tayi Tace Allah yasaka muku MUH'MD RAMADAN yabi muku haqqin kisan
da Dady Jibiril yayi ma Dadynku
Sannan Allah yaji qan Momy da shi
Ina sanka mijina xanci gaba da baka farin ciki na har abada
Tafa'di hakan hawaye na xubar mata
AmEEn RAMADAN Yace Yana lasar hawayan nata dayi mata nuni akan tadeba bayaso
Sam sun shagala dajin 'dimin juna sai kawai jin kiran sallar Isha'i sukayi
Anan suka ankare
Washe gari Suna breakfast Tace ni mai Xanyi da wa'yannan ku'da'dan mijina
Sunyi yawa sun xarce burika nah
Murmushi RAMADAN yayi Yace kisan yanda xakiyi dasu Auntyna nidai nagama nawa
Tace toh kaini gida inyi shawara da Abbana da Kakah
Pls ka kashe wanan ranar gareni kakaini gidan marayu asibitoci da sauransu
Yace sai dai gobe muje
Tace meyasa
Yace Aunty XEE tace min in gaya miki xataxo yau
Tace ok Allah ya kawota
Yace Amiien sai kiyi addu'a Allah yasa gobe banda lectures
Tace hmm kundai kusa gamawa muhuta da maganar karatunnan
Yace kifara shan allurai bah😀
ko Minti ishirin RAMADAN baiyi Da fitta ba saiga XEE Tace qawata naga sai kyau kike
kina wani cika
SAILUBAH tajah numfashi Tace kedai bari XEE
*Ciki ne dani*
Sai yamma can ya sauketa a gida ya kalleta cikin murmushin soyayya Yace Ki
kulamin da kanki da kuma Babyna yanxu xan dawo pls karkayi Komai kihuta dan Allah
kinji
Tace angama mijinna
****
Bayan sati 'daya RAMADAN ya mallaka ma SAILUBAH wata xaxxafar mota
*************
Haka dangi kowa yasan da xuwan ku'dinsu RAMADAN
Albarka yabo fatan alkairi ba irin Wanda RAMADAN baya Sha
Haka agyefan SAILUBAH mah
.
[8:37AM, 26/01/2017] R🇦HAⓂ🇦T: Bayan watanni shidda
******************************
Allah Sarki rayuwa yau taxo maka da da'di gobe sa6anin haka
Tun safe HAMEEDA take naquda bata tashi aihuwa ba sai Cikin dare kusan qarfe 1
'daya
Lokacin FAWAS yana kan sallaya yana yima matar tasa addu'a
Baibi takan Babyn ba saboda kunya. Sai kawai yaje ga matarsa Yace sannu my MEEDAT
Tace Yauwa
Yace nagode da baby sai naga ko
Da sauri tawo ido da harararsa Tace Wlhi na gamah
Yace tab mekikayi
Aisai namiki kinta ban doxin doxin 😀
Kuka tasa mishi wiwi
Momy tashigo tana cewa ina kuka ya qare tunda kin sauka 'yata
Tace wlhi momy shine yasani kukan
Momy takallesa Tace aa toh tashi kabar nan toh
Murmushi yayi kawai
XEE ta qanqame KHAMIS kamar xata shige cikinsa Tace wayyo Allah
Yace menene
Tace kuliya
Dariya FAWAS yayi ya futar da ita daga 'dakin yana cewa harna tuna ranar da junior
ya sumar da Aunty LUUVAH sanadinta
XEE Tace au dama kai kabashi
Yace eh
Tace ai banta6a ganin 'dan iska irin junior ba
Ko tausaya mata baiyi ba ya callah mata
KHAMIS Yace naso dake ya cillamah inga ya xakiyi
Tace tab😳
ainima sumewan Xanyi kamar ita......
Kan KHAMIS yayi magana saiga RAMADAN da SAILUBAH sai wani qanqameshi takeyi tana
tafiya daqar daqar da wani tulelen cikinta😆 aihuwa yau ko gobe
Da sauri XEE Tace bana ce Karki xo ba
Tace tab'di inajin yanda RAMADAN yake xuxutamin kyan yaran saina xauna kallo ya
shigeni....
KHAMIS ya miqa mata babyn Yana cewa dan Allah Aunty LUUVAH kidena fitta
Tace ai daga wannan KHAMIS nadena
RAMADAN Yace sannu me jego
Tace ina yininku
SAILUBAH Tace lafiyanki
Dariya sukayi atare
XEE Tace yaushe Xaki dena hausar qauye ne HAMEEDA cewa fah xakiyi Barka da ranah
Amota XEE Tace wai yaushe SAILUBAH xata dinga ankarewa da abubuwa ne
KHAMIS yayi Murmushi Yace kibarta indai RAMADAN ne xai gyara tunaninta da ankarar
da ita cikin salansa
Bai kai qarashen xancansa ba momyn shi tashigo 'dakin tana cewa tashi kikoma part
'dina
FAWAS yaarairaice Yace pls Momy kibarta anan
Tace aa nagyara mata 'dakina
Baxata dawo nan ba sai tayi arba'in kashiryo mata kayanta yanxu
Shuru FAWAS yayi
Washe gari da FAWAS da KHAMIS sukayi qauyan takai suka fa'dama Innah Hansai aihuwar
HAMEEDAN
Sosai tayi mamaki dan kwanaki da taxo mata Sam bata lura da Cikin ba
Tace Insha Allah ana gobe Suna xasuxo sai sukwana washegarin sunah sai sudawo
FAWAS Yace toh Allah ya kawoku
Hakan ko akayi ana gobe Suna dangin HAMEEDA sukaxo gidan nasu
Sosai Momy ta kar6esu
Washe garin Sunan ne ko da qarfe goma sha biyu na ranah SAILUBAH tana xaune a
'dakin Innah Yalwa naquda tatasan mata.....
Dama Innah a ankare take da ita dan haka tafara temakwanta irin nasu na manya
Da dugu yayi mota Momy da Khairat sukabi bayansa Suna masu farin ciki
Qar6a yayi yana tuqin yakira Junior ya gaya mishi Yace aidama na gaya maka ka
shafamin Kansu kafin naxo garesu murmushi RAMADAN yayi
haka KHAMIS mah yagaya mishi kana ya kira FAWAS shima yaji
Momy ko dangi tadinga kira tana gaya musu
By Hajju
*🇸AMAREEN*
*👯🇧ANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 115*
Hmmmm RAMADAN takan yaransa yafara bi. Sam baibi tàkan SAILUBAH
'Daya na hannun Momy 'daya na hannunsa sai Murmushi yake
Ya kalli Momy Yace idan Auntyna sukayo Momy kuma kiduba yatsunsu irin na junior ne
Tace aikowa gashi nan kam
Saidai Komai na jikin junior irin naka ne ai
Innah tayi Murmushi Tace aiya fa'di Hakkanne dan yasan shi sukayo
Momy tace lah na sha'afah wlhi
Murmushi RAMADAN yayi kawai ganin Innah ta ramfoshi
da matuqar farin ciki KHAMIS yake cewa waw Aunty LUUVAH abani wannan
Murmushi SAILUBAH tayi Tace anbaka KHAMIS
FAWAS Yace xamu rabaki dasu gabaki 'daya dan nima 'dauke 'dayar zanyi
Tace Bakomai FAWAS 'dauketa kaima
XEE Tace ka 'dauka Wlhi xuwa xanyi in 'dauke Ahmad
FAWAS yayi Murmushi Yace ainaki ne Aunty XEE baxanji Komai ba
Murmushi Momy tayi Tace Allah yayi muku albarka yarannan kucigaba da kulawa da
Kansu
AmEEn sukace gabaki 'dayansu Cikin farin ciki
Tace Innah ba wani matsala atare da ita ko.
Innah Tace eh. Abin yaban mamaki ai
kigansu manya dasu Amma basu qarata ba
Momy Tace toh Madallah bara in kira doctor Anisa taqara dubata
Innah Tace ya kamata kam
Saidai tabata wani magana wanda xaiyi saurin fitar da sauran jinin nata
Taba nanda kwana gobe sha biyar tace xata dena fudda jinin
Sannan kuma taba wasu magunguna Tace Bayan 'daukewar jinin nata tayi amfani dasu na
kwana biyar xasu tsuketa tamkar budurwa taqara da cewa magungunan Suna da kyau Wlhi
tayi amfani dasu marabarta da budurwa shine furta Auran da tayine
SAILUBAH tayi mata godiya Sosai Tace xan qara dana HAUSA dan banaso ni kaina
nayarda na aihu
Doctor Anisa tayi dariya Tace shegiya SAILUBAH kin camke RAMADAN pls karki xautar
dashi dan Allah
SAILUBAH tayi Murmushi tayi Tace hmm Aunty kenan. xan kiyaye
Kantayi magana XEE tashigo 'dakin Tace wai Aunty Anisa wane gwulma kukeyi ne haka
Tace ina GYARA qanwar tawa ne
XEE ta waro ido Tace kai Aunty tun yanxu
Tace eh mana. Sauran ke ki haife kiga GYARA
SAILUBAH Tace ita kam tukunna dan haryansu shuru
Tace Ayya zansa qanina KHAMIS ya qara dagewa
XEE Tace tab ya kasheni kenan 😰
Dariya suka mata
Doctor Anisa ta numfasa. Inya kasheki yarasa nutsuwarsa kenan har abada dan ban
manta kallan tsantsar qaunar da naga yana yi miki 'daxo bah.
SAILUBAH Tace kai Aunty dasa ido kike
Tace Wlhi ba qarya nayi bah na lura Sosai kun asirce maxajanku
XEE Tace da ayar Allah ba
Ni dai ba ma'a bociyar sallar dare bace Amma danaga kansa na rawa Sosai natashi
tsaye wajan gaida Allah cikin dare ina jifansa da addu'a
SAILUBAH tayi dariya Tace Allah Sarki RAMADAN shiyake tashina yanxu dan da'din
'dumin jikinsa sani yake namanta kaina
XEE Tace ai RAMADAN ba daga nan ba
Duk shi ya 'durasu akan hanya
Doctor Anisa Tace shiyasa duk fuskarsu take cika da annuri da hasken kwarjini
Pls kuriqe maxajanku dan Wlhi kunfi kowa tashin hankali ayanxu
Dan maxajanku yara ne masu aji da tashen balaga da ku'di ga kyau da Allah yayi
musu kallo 'daya xakuyi musu kusan dole mata subisu
Toh bare insu kansu sun furta kalmar sO agaresu
Kunga sai Luv kenan Su Auro muku su
XEE Tace afurgice. Wlhi inna tuno haka gabana mugun fa'duwa yake
yayinda hankalina yake tashi
Yanxu ya xamuyi ni ZAINAB
Tace abinyi shine ku kula dasu
SAILUBAH Tace Allah duk wacce tayi gigin Shuguwa gidana saina babbakata 😬
Tace toh SAILUBAH ya xakiyi da qadda idan tahau kanki
Tace haquri
Tace toh kidage daba mijinki kulawa kawai
Tace xan qara dagewa
Anisa taqara jan numfashi Tace Da xanga matar FAWAS dana ja mata kunne Sosai akansa
Dan akwai wata yarinyar unguwarmu Aymana Sosai takesan FAWAS kuma haryanxu Suna
tare. Ba wani makawa FAWAS Yana Santa dan Sun da'de da juna mah
XEE Tace tabbas nata6a jin KHAMIS yana cemah FAWAS 'din yau wajan Aymana zamu ko
Dake lokacin kishina na kusa bakiga rikicin da mukayi ba
Duk dako ya rantsemin ba budurwarsa bace
Tace toh Wlhi ta FAWAS CE
XEE ta kalli SAILUBAH cikin tsokana Tace ya dai Qawata kina xaunan kika haife
biyun. Saiji kawai kikayi sun fitto sululub ko😀
SAILUBAH ta harareta Tace Allah na'dauka da gaske RAMADAN yakemin
Ashe gaskiyar HAMEEDA ne da tace ciwan haihuwa yafi kowane ciwo xafi aduniya
gaskiyane haka abin yake
Dariya XEE tayi kawai
Bayan su XEE sun tafi ne RAMADAN ya lalla6o gareta yabarsu Momy a falo
Duk da hutun da SAILUBAH take nemah bai hana shi d'anewa kan ciyarta ba. Ya hau
kissing 'dinta yana cewa wayyo Auntyna na gode miki dan kinbani abinda yafi Komai
faranta min rai ayau
Tace naji tashimin ajiki
Ya maqale mata kafa'da alamar aa
Yana shafata tako ta ina
Momy kalli Innah Tace toh Innah saiki komah 'dakin SAILUBAH har tayi arba'in
Tace aikuwa haka xa'ayi dan nalura yaran naki ba damah
Cikin jin kunya Momy Tace ai yaran xamani ne Innah
SAILUBAH ko taji da'din hakan dan ita tasan halin mijin nata...
Takanas ta Kano 'Yan unguwarsu sukayo group dan kawai suga babis 'din SAILUBAH da
RAMADAN 'din
Sunko ganowa kansu dan sunga kyawawan yara gwanin ban sha'awa
Kallo 'daya xaka musu kasan ubansu sukayo
Ba abinda yarabasu da RAMADAN Senior n junior
Cikin qasa qasa da murya RAMADAN ya rungumeta ta baya yake ra'da mata ta cikin
akunnanta
Qila sunbarma ubansu ne
Yafa'da yana qoqarin kama breast 'dinta
Aiko cikin sauri ta kwaci kanta
Harara SAILUBAH tagalla masa Tace kakamasu Wlhi kuka xansa maka
Yace ai nasani musamman da yanxu suka cika suna buqatar me shansu Saidai anyi
rashin sa'a masu shan sunqi Sha toh abarni nasha mana Tace anqi
Yace zasu miki tsami fah😳
Tace toh ina ruwanka suyi mana
Murmushi Murmushi yayi Yace xan miki afuwa xuwa kwana arba'in 'din
Wlhi kosunfi haka cika saina xuqesu dan baxan barki da Kaya Suna daminki bah
Ta qara gallamai harara Tace kabarni da abuna haka mana. bana so katakura min su
pls
Yace Allah baxan barki dasu bah. Naji da'din yanda Babyna suka barni dasu. Kuma ki
qara hararata kigani Wlhi ayanxu xan maqureki naxuqe abuna
Gaban SAILUBAH ya fa'di taqarema 'dakin kallo taga xahiri daga ita saishi ne. Xai
iya yimata Komai dan tasan futunarsa tafi qarfin tunaninta gata da jego dan haka
saita hau lalla6a shi har tasamu ya barta batare daya ta6osu bah
Haka dai ya ficce daga 'dakin yana Murmushi dan sarai ya gane lalla6ashin da tayi
bana Allah bane
Yanako fitta Innah tashigo 'dakin tana cewa meya fitta da ita haka.....
Shuru SAILUBAH tayi mata har sukayi part 'din nata
👯💃🏼👯💃🏾👯💃🏻👯💃👯💃🏿
Munga baqaqe munga koraye munga jajaye munga farare a sunan *KAULAT DA KAULET*
Junior yaga hotonan babys 'din nasa dan FAWAS ya tura masa
Haka KHAMIS
Bare gogan RAMADAN harda Wanda ya tadama da Junior hankali sanda RAMADAN ya tura
masa.
Wanda suke qale da juna shi da Auntyn SA
******************
FAWAS ya shiga tashin hankali Sosai dan baqaramin buqatar Matarsa yakeyi ba
*to kai kayi hakuri mana tunda mah acikin jini take. Me xata iya yi maka. Rahamat
Nalele CE mai wannan furucin*😂
Yau yayi ram da ita a kitchen tana tana San 'daukar Abu
Yace dan Allah Aunty MEEDAT kitemaken nasamu nutsuwa
Dariya ta kamata wai harda wani cemata Aunty. Tadai gimtse dariyar Tace Wlhi ina
jini HABIBINA
Yace qaryane in gani
Tace Wlhi da gaske
Janta part 'dinsa yayi na falan
Yace toh nunamin
Ba musu tanuna mai
********
Anan ko byan sati biyu RAMADAN ne maqale da SAILUBAH akan tabashi hakkinsa sai wani
lalla6ata yakeyi
Dariya itama tadinga yi masa Tace ai in mace ta haihu jini baya 'dauke mata sai
tayi wata biyu
Toh bare ni dana haifi 'Yan biyu.
Kaga wata hu'du kenan Xanyi
Iya gigicewa RAMADAN ya gigicewa da sauri ya saki hannunta cikin tsoro Yace haba my
Aunty fa'damin gaskiya
Auntyna yaxanyi
Nayi sabo da 'dumin jikinki
Nayi sabo da xumarki
Nayi sabo da Komai na halittarki
Wlhi baqaramin daurewa nayi akwanakin nan ba......
Tace ya'isa haka Babyna xanyi maka qoqarin kaina kaji
Yaqara lafe mata yana cewa Aunty bacci yaxo min banasan raba jikina da naki
Tace toh kayi abinka in kayi nisa na gyara maka kwanciyarka nakomah 'dakina ko
Shuru yayi mata da qara kananna 'deta yana sauke ajiyar xuciya
Minti biyar bacci ya 'daukeshi
Sanda tabari yayi nisa Sosai Sannan taxare jikinta ta ha'dashi da fito tafice daga
'dakin tana dariya😂
A falo sukaci karo da Innah Tace SAILUBAH Karki biyema RAMADAN fah
Tace lah bashi da lafiyane innah shine yasa na kai mishi magani
Tace aiho. naga kin fara Sallah ne ai.........
By Hajju
*🇸AMAREEN*
*👯🇧ANAH*👯
👯👯👯👯
*PART 116*
Wasa wasa sanda SAILUBAH tahana RAMADAN kanta gashi har yau takai wata biyu da
sati 'daya
Gwara HAMEEDA tabada kai tuni ganin irin nacin da FAWAS yake mata
2:03 Wednesday
*****
Yau RAMADAN yaxoma da SAILUBAH da takaddunsa akan sun xana exam 'din qarshe
anturasu asibitin Aminu kano
Murmushi SAILUBAH tayi
Tace Allah ya temaka
Amiien Yace yana kallanta
Tace lafiya kake kallona haka
Yace Bakomai
Xama tayi kusa dashi ya kwantar da kansa bisa cinyarta. Yace Aunty nagaji
Tace Qanina dame ka gaji
Yajah numfashi yana xuge mata zif 'din rigarta ta gaba yana cewa Wlhi kisan yanda
xakiyi Ki Kore jinin nan inba haka ba kishiya xan miki nanda kwana uku
SAILUBAH tawaro ido da sheqewa da dariya Tace kishiya fah kace
Yace eh
Dan a iya saninah jinin mace baya kaiwa kwana arba'in
Dake ba wanda yasan gaibu sai Allah shiyasa aka barku a kwana arba'in 'din
Yanxu fah naki yaxama na ciwo😳
Tunda ya xarce kwana arba'in 'din
Dan haka Wlhi kitashi muje munemi magani
Dariya sosai SAILUBAH tayi tare da xare hannunsa daga kan breast 'dinta Tace nifah
gado nayi agun momyna. Dan Kakah tata6a gayamin cewa lokacin da momoyn nawa ta
haifeni sanda tayi wata biyu kafin jini ya 'dauke mata
2:30pm Wednesday
*******
XEE ce tsaye a kitchen tana ha'da abincin ranah Momy tashigo kitchen 'din da
maganin gargajiya na ice a hannunta
Tace Zainab ga wannan maganin na haihuwa ne
Xaki dafashi wannan da jar kwanwa kisha na kwana bakwai
Sannan wannan kijiqa da tsamiya kisha na kwana uku
Insha Allah xa'a dace
XEE taja numfashi tana jinjina San jikoki irinna Momy
Tace toh nagode
Jiyama da naje gida muke xantawa da mamana cemin tayi sanda tayi shekara uku kafin
ta haifeni.
Shine nace konima irin nata xanyi watoh nayo gadanta....
Murmushi Momy tayi Tace Zainab kenan xai iya yuhuwa haka kam
Amma kigwada amfani da wannan 'din inbaiyi sai muzubama sarautar Allah ido mugani
XEE Tace toh....
Momy na fitta daga kitchen din KHAMIS yashigo. Kallo 'daya xakamai kasan yana cikin
farin ciki
Ai XEE najin batun kishiya ta bu'de kitchen din tana cewa mekace
Yayi Murmushi Yace bance Komai ba
Harararsa tayi Cikin wani salo na Soyayyah.
Shiko rungumeta yayi
8:00pm Wednesday
*****
Misalin qarfe 8:00pm na dare ne FAWAS yake kwance a gadansa yana wasa da yaransa
Ahmed. HAMEEDA tafitoh daga toilet tana cewa yau bai maka kuka ba Yace xaiyi in
tafiya tai tafiya
Murmushi tayi tana qarema mijin nata kallo yayi kyau Sosai cikin shigarsa ta
qananun Kaya sai qamshi yakeyi tagyara 'daurin 'dan kwalinta Tace naji kayi magana
'daxo ina toilet dafatan ba cemin xakayi xaka fitta bah.
Xaiyi magana takatseshi da cigaba da cewa✋🏻 Wacece Aymana.....
A gigicewa ya qara tsaida idanshi akanta Yace ban sanda bafah wlhi😳
Tace koh
Yace ba shakka aciki
Tace yayi. Kuma na yarda dakai
Amma ina kake shirin xuwa yanxu.
Da sauri Yace Dady ne ya aikeni kar6o mishi wani aika a gidan abokinsa....
Cike da jin haushin xaman da yayi tun'daxu Tace shine kazauna baka tafi ba
Yace nayi hakanne dan in gaya miki Karki xargeni da xuwa inda Kullun xuciyarki take
kitsa miki
Tayi Murmushi Tace Ayya HABIBINA bai dace ka tsaya sanar dani umarnin Dady ko Momy
ba
Kasandai idan kadawo kafa'damin sune suka aikeka Kasan xan gamsu da kai
Murmushi FAWAS yayi da kissing 'din Ahmed kana yatashi yana da'da qaremah fuskarta
kallo Santa na ratsashi ya shafi gefan fuskar tata Yace saina dawo Matata. Pls Ki
shirya min kanki da kyau
Tace angama mijina.....
KHAMIS ya sheqe da dariya Yace ai Aunty XEE ko kukan mutuwa xanyi saifata
hukuntani kunsan tafi kowa kishi😂
Haka RAMADAN yayi parking a kofar gidansu Aymana suna gwulmar matansu
Ahankali ya kalli FAWAS Yace toh gareka FAWAS mun iso. Pls karka 'dau lokaci kana
matse musu 'ya dan awa 'daya garemu.
Da rangaji da wata shegiyar tafiya ha'de da girgixa da faro da ido Aymana tafitoh
Wlhi FAWAS kasameni yanda kakeso. Aymana tafa'di hakan tana harararsa
Yajah mufashi da cewa kimin afuwa dan daqerma nasamu na fitto
Tace wai wacece wannan matar takace
Meyasa ta cutar dani
Meyasa ta rabani dakai. Bayan nice nadace danaxama mata agareka
Wlhi FAWAS ina so in ganta danna tsaneta.....
Na fitoh da niyar ganinki naqara samun farin ciki da nutsuwa kamar yanda naso
Saidai kin 6ata min dan haka nabarki lpy
Ya qarashe da San shigewa cikin mota....
Aiko tasauri tatareshi tana cewa ni yanxu naqara girmah nasan abinda xai 6atamin da
kuma abinda xai faranta min
Dan haka daga yau FAWAS kabarni.....
Yace au dama nariqeki ne ban sani bah
Takaici yacika xuciyar Aymana nan take tasamai kuka Tace Allah ya isa tsakanina
dakai FAWAS. Ka cuci rayuwata ka 6ata min xuciyata da soyayyarka
Gashi yanxu nace kabarni kana fa'damin dama kariqenine Ashe duk alqawarin da
kakemin na qaryane na yaudara ne
Amma yanxu kinsa na koyi qarya dan kawai na faranta ranmu ni dake
Duk sanda xanxo gareki ayanxu saina shararamah matata qarya
Wannan bai isa kigane cewa ina sanki bah
Tace qarya kake baka sona tunda ka'iya Auranta bani ba.
Kaje kawai FAWAS na yafe maka saboda baxan iya yimah masoyina baki ba
Amma kasani da sanka zan rayu har qarshen rayuwata
Tana fa'din hakan tashige gidansu tana kuka ta fa'da agadan kakarta
Murmushinki kawai nake san ji da kuma kiss 'dinki dan nakwana da tunanin dan Allah
Murmushin tayi kana kuma tasakar mai kiss tana cewa nayi
Yace nagode kisharemin hawayanki dan inasO kiyi mafarkina
Idan kuma kin kasa sharewa kifitoh in share miki pls
Tace Xanso na qara shaqar qamshin turaranka.Yace xanso naqara ganin kyakkyawar
masoyiyata
Tace toh ganinan
Shigewa zauran gidan nasu FAWAS yayi dan iskancin nashi ya motsa
Sosai yanutsu bayan yaji muryar HAMEEDAN tashi cikin wayar tasa. Yace kiyi my
MEEDAT gani kan hanya yanxu
RAMADAN da KHAMIS Suna jinta Tace dan Allah kayi sauri in baso kake xuciyata ta
buga ba. Dan wlhi 'duminka take san ji
Yanxu haka ina kwance HABIBINA
Murmushi yayi Yace rufe idanki yanxun nan Xaki ganni
Tace tohhh narufe...
Kashe wayan yayi ya kalli KHAMIS Yace Wlhi maidani gida
RAMADAN Yace ai baka isa bah Wlhi sai yaje ga MEENAT ya kuma saukeni a gida
Wayyo Allah FAWAS yace
KHAMIS yace am sowie.
RMADAN ya gyara xama Yace karabu da Aymana mana FAWAS kaga 6ata mata tunanina kawai
kakeyi
KHAMIS Yace hmm rabu dashi tunda koya barta ita ba barinsa xatayi bah
RAMADAN yajah tsaki Yace Amma dai Kasan yana cutar da ita ko
Yace eh toh da wannan dan wannan (wai antura tsowan banxa biko)
Yanda baka duba dacewar ni yakamata da in xama matarka ba hakanne yasani Kasa yarda
cewa kayi Aure dan haka idan Sonah kakeyi nimah ka Aurani yanxu.
Kaga tafiyata. 'dan rainin hankali kawai. Wlhi kadena 6atamin tunani
Kuma kasani 'daxo na kiraka matar taka ta'dauka nace mata nice meenat me shigowa
gidanka matsayin matarka ta biyu.....
Tana fa'din haka tashige gidan nasu
Shuru KHAMIS yayi kana ya shiga motar RAMADAN yajah yana murmushi
FAWAS yayi Dariya Yace sai da safe a shafamin kan 'Yan matana
Insha Allah RAMADAN Yace da shigewa gidan nashi yana 'dagawa KHAMIS hannu
Da gudu gudo sauri sauri FAWAS yake tuqi damuwarsa ya kai gida da sauri ya kalli
KHAMIS Yace kaje mata da addu'a kawai
bu'dar bakin HAMEEDA cewa tayi Daka shigo naji qamshin turaran wata ajikinka
Waro ido FAWAS yayi
Yace badai turareba
Tashi HAMEEDA tayi shima ya tashi
Ta qura mishi ido Tace gayamin gaskiya daga Aiken gun Dady kawucce gun Aymana ko
'Dan rikicewa ka'dan yayi Yace nace miki bansan wata Aymana ba
Tace koh
Ya 'daga mata kai
Tace banyar dakai bah FAWAS......
Jin haka yasa yayi Saurin cewa wani turarene fah na siyamah Dady tun jiya shine
dana ganshi Cikin mota shine fa na'dan fesa
Tace hmm ai baka fitta da mota ba
Yace kanna fitane nayi niyar fita da motar sai kuma nafasa ganin turaran yasa
nafesa
Murmushi Hameeda tayi Tace OK shikenan
Ya kama hannunta Yace pls kiyarda dani
Ta kallesa Tace Wlhi nayarda da abinda kace
Rungumarta yayi ya rayawa aransa yabar ta6a jikin Aymana daga yau dan bayasan
xargin matar tasa
Sosa qeya KHAMIS yayi Yace qila tafa'di hakan ne dan ta6a miki rai
Tace KHAMIS kaji tsoran Allah Wlhi kamin kishiya mutuwa Xanyi 😰
Qara Tsaida idansa yayi akan fararan idanuwanta wa'yan da suke birgeshi. Kuma sanda
da qaunarta na qara mamaye xuciyarsa Yace Wlhi dake ka'dai nakesan rayuwa matata.
Pls kikwantar da hankalinki narantse miki kika mutu nima binki Xanyi....
Ya fa'di hakan yana me rungumarta da kissing 'dinta.........
RAMADAN na shiga gidan nasa yayi part 'dinsu kawai dan yasan Innah Yalwa tayi bacci
yanxu
Ganin haka yasashi shagwa6e mata yana wani yimata qif qif da ido da cigaba da cewa
dan Allah Auntyna Karki hukuntani kinji
Tunda nagaya miki gaskiya😬
Murmushi tayi Tace naji Amma daga yau kadena fitta da daddare Wlhi
Yace indai baxaki hukuntani yanxu bah nayarda
Tace inasan jin 'duminka mijinta
Da sauri ya rungumeta Yace nima haka Auntyna
Ahankali takai bakinta cikin nashi tana tsotsa. Yana lumshe mata ido
Sanda taga yana qoqarin yi mata bacci atsaye sannan taxare shi daga jikinta tana
cewa a tsaje xaka min bacci
Ta qara shi da xamah a dining
Yayi mata sanyayyan Murmushi Yace ina yarana suke Aunty
Tace ai kasani Suna tare da Innah
Yace O yah Allah gashi sunyi bacci yanxu
Tata6e baki Tace aikasan da wuri sukayi dake yau bakaso jin 'diminsu ba shiyasaka
shantakewa......
Da gudu tayi bedroom tana qoqarin rufe qofar ya shiga da nasa gudun
Numfashi tajah ta manne a bango ya harareta Yace wannan ka'dai ya tabbatar min da
cewa da tsarkinki
Tayi mai shuru
Yayi murmushin Takaici da ciga da cewa watoh kinda'de dayin tsaki shine kika barni
kicin bala'i ko
Tace toh ai jiya nayi tsarkin
Shuru RAMADAN yayi yana tunanin yanafah ganin tada'de dayin tsarkin qilamah ba jiya
bane
Yace ai shekaran jiya ma naganki kina Sallah
Tace eh waccan shekaran jiyan nasamu tsarkin
Yace kikace jiya kuma
A shagwa6e Tace kana burkini RAMADAN pls kabarni haka
Yace koh
Tace eh
Yace ai ban burkitaki bamah tukunna sai kin tuna ranar farkonmu dana sami nasarar
kar6ar hakkina
By Rahamat Hajju
[5:58PM, 01/02/2017] R🇦HAⓂ🇦T Nalele:
Zainab
Sadiya
Haleema Auwal
Salmah
Meelat
Hajjaju 😀
Sis Manuh geee Allah ya qara basira
Hindatu
Fatima
Maryam
Xarah
Maman sam...
Nagode da addu'arki 😀
Luvr gal
Zulfau Mustaph
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu
kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama
sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana
magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci,
duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna
neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman
munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai
fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai
wayarku
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted
biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not
blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we
are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day,
any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF
or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT