Professional Documents
Culture Documents
ng ku ziyarci
shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama
daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu
kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama
sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana
magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci,
duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna
neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman
munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai
fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai
wayarku
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to
download it online
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography
including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490
its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted
biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not
blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we
are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day,
any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF
or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
KISHI DA BUZUWA SAI KA KWANTAR DA HANKALI KA KAI AIKI DA HIKIMAR KA WAYEWA DA ILIMI
BAI FITAR DAKAI A GARESU, , , ,
GODIYA GARE KUMA KARANTA NOVEL DINA DA KUKE KOKARIN DAUREWA DA HAKKURI WURIN
KARANTA LABARAINA WANDA ABUBUWAN DAKE YAWAN FARUWA A NAHIYAR MUCE MUKE TABOWA DON
HASKA KAN YAN UWA DAMA MU DUKA.
NOVEL DINA NA KAUYAWA NE BABU YAWAN KARAYAN ARZIKI A CIKIN SHI SAI DAI ABINDA
LABARIN YAZO DASHI BABU FAYYACE FITSA A FILI YADDA WASU KE SON IN SAUYA ZUWA HADI
DA FITSARA NA KASANCEWAN MACE DA NA MIJI A GADO A HAKKAN KUMA NAKE DA DINBIN MASOYA
MASU KARANTA SHI A HAKAN, GODIYA GARE KU HAR KULUN MASOYA DA MASU KAUNA NA.
GAMA SU SON NOVEL DIN ZAKU IYA KIRA NA DA WANAN LAYIN DON NEMAN KARIN BAYANI
DARI UKU NE GA MAI SON BIYA TA WANAN ACCOUNT DIN 2254380105 ZAINAB IDRIS MAKAWA
ZINETH BANK
09026931792 KO 08036959257
Hadari ne ya hade garin sosai baka ganin komai sai walkiya da kara kainan motoci a
lokacin wanda suke haskawa don ganin gaban su.
A daidai wanan lokacin ne motoci guda uku da suka karyo titin a jera wanda ke
nuna wani mai akwaine tafe a lokacin yadda mutane suke ta kaucewa a titin suna basu
wuri.
Wasu daga bakin titi ke fadin yanzun haka ma ba maigidan bane tafe wanan
fitsarariyar matan tashine haka da bata ganin kowa da mutunci a idon ta.
Wani gida motocin suka shiga a lokacin gini ne na zamani motan ne suka dan tsaya
da alama magana akeyi da wani a cikin gidan.
Ba a dade ba suka wuce zuwa cikin gidan kai tsaye security ne suka fito don bude
motar nan naga wata farar mata buzuwa ta fito tasha ado na fada da gani daga saman
ta har kasanta kwaliya ne.
Doguwa ce sosai ga fari sai dai idan ka kura mata ido zaka iya gano farin ne
kawai ke aki yake rudin mutane don kyau akwai kyau inda bamu matan mu na Nigeria
masu kyan asali da dire bayan farin da gashi da kuma tsayi babu abin da suka dara
matan Nigeria dashi na fannin kyauwo.
Tana wani tako ta shige ciki zuwa part din ta ta dan jima ciki ta fito tana
kwala ma wata mata mai suna Labara kira da karfi .
Da saurin matar ta iso gareta tana dukawa tare da fadin hajiya barka da zuwa an
dawo lafiya yaya han, , , ,
Dakata tace wa matar yaya naga witan part din can a kunne ko mara zuciyar nan ta
dawo ne kuma ?
Matar ta dago kai a hankali tace wa hajiya babba kike nufi waye hajiya baba ina
nufin fatima matar wancan shiyan ta fada a fusace jin an kira uwar gidan nata da
hajiya babba taji haushi.
Eh ta dawo laraba tace ai tun ranan da kuka wuce washe gari ta dawo kutawa tayi
tare da juyawa da karfi ta shige part din ta a hasale.
Anan tabar laraba da kallon mamaki ta nisa tana fadin ikon Allah mata da mijin ta
kinzo kin hana zaman lafiya a tsakanin su haka ?
Ita kuma a daki sai faman huce takeyi ita daya nan ta dauki waya ta kira mijin
nasu da suka rabu yau ya tafi waje yin wani aiki.
Duk da tasan dare ne a duk inda yake amma bai hanata kiran shi ba a wanan
lokacin saboda tsananin kishin dake damun ta a lokacin.
Kiran farko ya tsunke bata hakkura ba ta sake kira a karo na biyu bai daga ba
sai wayan na gap da katsewa ya dauka da alaman barci yake a lokacin .
Murya irin ta masu barci ya daga wayan tare da fadin Nafisa lafiya kira da dare
haka yanzu fa kin san dare ne nan sosai a wanan lokacin.
Bata jira ya gama magana ba tace watau munafuntana zakayi ashe kasan matar ka ta
dawo shine baka fada min ba tun muna tare sai kawai in dawo in samu ta dawo gidan.
Ajiyan zuciya ya sauke tare da fadin tadawo fa ni ban san ta dawo ba don basu
fada min da cewa zata dawo ba ma kit ta kashe wayan.
Ta wurga a gefen gadon ta tana fadi a fili duk sai nayi maganin shegun tsofin don
sai auren nan ya mutu inga ta bakin naci irin nasu.
A daidai lokacin ne kuma aka turo kofan side din nata wata matace cikin dogon
riga ta dora hijjab a saman rigan nata.
Fuska da murmshi tace mutanen Abuja ashe kuna tafe yanzu ne an sauka lafiya yaya
hanya fuska a daure ta juyo tana fadin eh muna tafe ko idan zan dawo sai na sanar
da wani akace ko ma ?
Ke yanzu don baki da zuciya dawowa kikayi duk da maigidan ya nuna baiyi dake
saboda rashin zuciya irin naki sai da kika dawo kamar ana zama dole ne.
Matar tadan sake murmushin dabai kai ciki ba tace nake ganin ke nan haka amma ni
nasan yana yi dani har gobe ke ce dai ganin ki ke rudin ki ga hakan don ko na bar
gidan shi bamu rabuba don ga diya ga zumunci a tsakanin mu.
Fati ke nan zakiko ga abinda ba daidai ba wallahi in dan kin nace sai kin zauna
min da miji don sai na rami ya fiki shan iska a gidan nan tunda haka kika zaba wa
kanki sannu sugar mai iyali ko tasbi sarkin zumunci shida bakajan da daya bai biyo
ka ba .
Murmshi tayi Allah na tare da mai gaskiya dama jin kin dawo ne yasa nazo taron
ki da dawowa ba wani abu ya kawo ni ba a huta lafiya bata tsanmanin ta amsa mata ta
fice daga dakin .
Zuciyar ta yana ciki da mamakin fitsara irin na Nafisa wanda sam babu kunya a
cikin shi ko kadan sai zallah cin fuska da fitsara filli.
Daki ta nufa a daidai lokacin da ruwa ya gauce sosai a garin na kaduna kamar da
bakin kwarya da sauri ta isa ta rufe mirrow da sauran abinda baison walkiya a dakin
saboda tsaro wanda ba kowa ke wanan ba a wanan lokacin sai masu sani da hakan a
baya suka saura rufe irin wa yan nan abubuwan a daki yayin da ruwan sama ke zubuwa
daga samaniya don kariya daga fitinan walkiya.
Falo ta dawo ta zauna tare da yaranta dake cin abinci a wanan lokacin ido ta
tsurawa yaran biyu sai da ba wai don tana kallon su hankalin ta yana gare ta ba ne
tunane takeyi a zuciyar ta na irin rayuwan da ta tsunci kanta a ciki yanzu.
Tun shigowan Nafisa cikin su komai na rayuwan ta da mijin nata ya sauya sallo a
lokaci daya ba yadda suka saba gudanar da rayuwan su ba suda yaran su da sauran yan
uwa.
Hatta yaran yanzu a matse suke da zama gidan mahaifin nasu sun fison zama a
gidan kakanin su da zaman gidan nasu saboda matsin da suke ciki a yanzu.
Ita dai tasan aure ne a tsakanin ta da mijin ta na soyayya tun tana karama
soyayyan su ta samu asali don gidajen su basu da nisa da juna shi din abokin yayan
ta ne.
Kuma akwai zumunci na makwabtaka da ya koma kaman na jini daya a tsakanin
gidajen su tun kakan su zumunci ya kulu a tsakanin gidajen biyu.
Wanda yakai bako ba zai iya banbanta tsakanin su ba sai wanda yasan tushen abin
koda ta girma bai daina kulata ba cikin yan uwa haka ya kai har aure ya kullu a
tsakanin su.
Tayi haihuwan farko lafiya ga cikin na biyune ya samu aiki kano suka koma can
sun koma bada dadewa ba ya hadu da Nafisa yar mutan Niger da suka shigo Nigeria
neman kudi da iyayyenta ta lake mai tun bai kula ta har ya soma kulata don suna
sayar masu da abinci a bakin ma,iakatar su ne.
Yaron ta ne dayazo inda take zaune tana tunane ya katse da da fadin mama daddyn
mu bai dawo bane naga anty ta dawo.
Shafa kan yaron tayi taja sauke ajiyan zuciya tace bai dawo ba Affan da kaga ya
shigo nan ai anty ce ta dawo ita kadai.
Yaushe daddy zai dawo mama yaron ya kara jefa mata tambaya kuma tace Affan ban
sani ba idan ya dawo ai zaku ganshi.
Bai barta ta huta ba ya sake jefo mata tambaya again yace mama ai anty ce bata
bari mu ganshi ko munje wurin shi sai tace mu fito muna damun shi yana hutawa.
Murmushi tayi tace kai Affan ba yana zuwa nan ida muke kuna ganin shi ba to may
kuma kake so shiru yaron yayi kamar yana tunane a zuciyar shi.
Sai kuma yace ni mama ban ma son ya dawo saboda may Affan uwar ta tambaye shi
yace saboda idan ya dawo sai ki ta kuka mama su kuma suna dariya da anty kuma su
fita tare.
Affan ban son yawan surutu fa ka faye surutu ina jin tsoron wanan bakin naka
kullu naji ka kara fadawa wani matsalan mu sai na yanke ma kunne daya.
Shiru yaron yayi yana tunanen kada uwar ta yanke mai kune kamar yadda tace din
kayan da sukaci abinci ta kawar ta gyara wurin suka shige dakin kwanan su.
Da safe bata fito ba sai da ta gyara part din nata ta nufi kitchen don dafa ma
yara abincin zuwa school sai ta samu kitchen din a rufe.
Dakin kwanan laraba mai aiki ta nufa a nan ta samay ta tace yau laraba lafiya
naga kitchen a rufe Labara tace aikin hajiya karama ne hakan.
Nima na fito zan gyara tace na barshi taja kofa ta rufe nayi tunanen zaki fito
don saboda abincin yara gashi kuma ta kulle kitchen din.
Dan jimm tayi tana tunane a ranta wai may Nafisa take nufi da ita ne haka
abinci dai na kowa ne a gidan amma haka take mata idan ta bushi iska sai tace wai
ana barnan abinci da yawa gidan.
Bayan abinci ma da take ita daya sai ta ba wasu balle yanzu da ya samu karin
girma sosai a wurin aikin shi basu da talaucin komai a rayuwan su.
Muryan Laraba ne ke fadin sai hakkuri hajiya idan mutum ya ci gaban ka sai dai bi
wallahi gama tana ganin ta samu miji a hannu sai abinda tace a gidan.
Ba komai Laraba na gode badin tura su can cikin gida wurin hajiya su karba haka
ta juya ta wuce zuwa part din ta tabar Laranba a wurin tana jin tausayin ta.
Daki ta koma ta shirya yaran ta fito dasu da kanta ta mika wa kanin mijin su
dake zaune dasu a gidan ya kaisu cikin gida wurin hajiya a basu abinci.
Yace yau kun makara ne tace eh salis koda na tashi har gari ya haska sosai
wallahi kaga idan nace zan tsaya dafa masu yanzu sai su makara.
Ta koma ciki ya kwashe yaran zuwa gidan su dasu don duk a unguwa daya suke zaune
da iyayyen nasu gida uku ne a haka kuma Nafisa ke tsula tsiyar ta a gidan.
Don tafi son zaman kaduna saboda anan kawayen ta suka fi yawa da yan yaren su na
buza da suke kara zugata tana iya shegen.
Salis na shiga gidan kafin ya isa part din mahaifiyar mijin nasu da yaran matan
gidan suka fara magana a, a su Affan ne haka yau da safe nan.
Salis yace eh maman su ta makara ne yau bata tashi da wuri tayi masu abin
karyawa ba shine zasu zo nan su dauka.
Murmushi hajiya kubura tayi tace Fatice zata makara da safe kawai dai yar bakin
halin gidan su ta dawo jiya akwai da wata a kasa.
Ba an mayar da Fati bata san tadawo ba shine ta dawo ta samay su bakin halin nata
na banza ya tashi yanzu ta soma ke nan har sai ta kure ta ta tanka mata.
Allah dai ya sauwa dayar matar gidan ta fada daga daki tace shi kuma da yazo sai
ya biyewa iya shegen nata ba daga daki suke magana.
Sun shiga gun kakan su tana ganin su tace ai na sani ba yar iskan yarinyar nan
ance ta dawo jiya ba nan yanzu tsiya zai tashi a gidan wanan karo ko ba zan
saurara mata ba wallahi.
Salis yace cewa tayi makara tayi fa bata samu dafa masu abinci ba yau yaya
maganan ku yazo daya da na mommy ne ?
Hajiya bata iyayin magana ba sai jan yaran datayi zuwa cikin part din ta ta zuba
masu abincin da tayiwa yan marayun jikokin ta da suke hannun ta.
Bayan ta gama sallaman yaran ne ta dauki waya ta kira Fati din tace wai may ke
faruwa ne yau a gidan naku cikin fara a ta fara gaida surukar nata da bata ko tsaya
gaisawa da ita ba.
Amsawa tayi sama sama dakyat tare da maimaita tambayan ta a gare ta tace hajiya
makara nayi tace jinan fati na san komai walahi nasan abinda yar banzan yarinyarin
nan zata iya.
A sanyaye fati tace hajiya ba haka bane makara nayi yau din ban samu dafawa ba
kashe wayan hajiya tayi badon ta yarda ba.
Kashe wayan nata yayi daidai da shigowan hajiya kubura wurin ta tace sai gasu
Affan na ga sun zo karban abinci kuma ?
Bari hajiya Kubura duk da uwarsu ta boye min na san akwai wata a kasa wallahi bai
yuyuwa haka kawai taki tanadarwa yara abin zuwa makaranta.
Nan suka zauna suna maganan hajiya kubura tace idan ita fatin bata iya magana mu
ba kyalewa zamuyi ba ai ana horo da yuwa ne kuma ?
Kai hajiya ta dafe tace Allah ya kawo muna karshen wanan yarinyar a gidan nan
hajiya kubura tace amin tana mikewa tare da fadin bari mu gani zuwa rana idan har
sun dawo nan kin ga hasashen mu ya tabbata ke nan ta rufe kitchen din nasu ke nan.
Ta fice ta bar hajiya a cikin bacin rai tana tausaya ma wanan rayuwa da yayan
nasu suka tsunci kan su a ciki na bamin auren buzuwa da ya dorawa rayuwan shi yana
zaune kalau da matar shi ya jajibo masu wahala haka.
A gidan Fati kuma bata karya ba tun safe ba tunanen kanta takeyi ba a yanzu sai
tunanen idan yaran sun dawo may zata basu idomie ne ya fado mata arai ta sayo ta
dafa masu suci.
Damay zaki dafa wani zuciya yace mata tsaki taja tana tausaya masu a ransu take
tunanen da can baya lokacin tana ita kaida ya fado mata a rai.
Abinci sai wanda ransu ke so zata dafa da ita da yaranta da maigidan ta har sai
taba makwatab wani lokaci yau kuma gashi a sanadiyar kishi da buzuwa har horo yakai
ga a rufe store da madafar abincin gidan baki daya.
Babu wanda zata kara kai kara gareshi tunda baji mijin nasu keyi ba ko ta fada
karshe ma ya dawo ya hauta da masifa gashi ita ba son masifa take ba a rayuwan ta.
Haka ta taso da tsoro sam bata fada ko kadan saboda ruwan ciki irin na matan
hausawa da ta taso a cikin shi wanda a cikin tarbiyan diyan hausa yake.
Kamun kaina a diyan hausawa rasgin hayani da fada da mutane barkatai wanda
akasarin matan hausawa hake ne ke cutar su a gidan mazaje su da gun kishiyoyin su
yan bana bakwai.
Tana tuna yadda Nafisa tazo gidan daga ita sai ghana most go din yan kayan ta a
ciki amma yau ta koma kamar wata hamshikiya a gida.
Auren ta da aka dauro ba tare da sanin iyayyen su ba can bariki suka dauro auren
su da ita inda ta tare a gidan da yake a lokacin a kano.
Sannu a hankali har ya samu iyayyen shi suka hakkura ta fara shiga cikin su inda
take baiyana harin ta na zahiri a hankali.
Da farko ta yaudari mutane inda taja yan uwan miji a jikinta duk suka yarda da
ita ta gama jin sirin su kaf kafin daga baya data bunkasa ta fara fitar da kalan ta
ga mutane.
Inda yanzu kowa ya gama gane ta wasu masu zuciyar imani sun gujeta masu kwadai
kuma har wanan lokacin suna tare da ita duk da abin hannun ta bai ban baruwa wasan
dadi sai kayi mata bauta kafin kaci abu daga gare ta.
Don haka take kallon kowa a wullakance sai uan uwanta dakan zo jefi jefi cin
arziki wurin ta wanda ba a wuce wata daya basu zo gidan ba.
Tazo da wata yarinya da take cewa wai kaunar tane sai da tafiya yai tafi aka gane
cewa yar tace ta cikin ta yarinyar.
Nafisa zata girmay ma Fati ga shekaru haka yasa tafi fati wayo sosai har take
jin tsoron ga fin karfi ga sihiri don bata shigo haka kai tsaye ba sai da ta shirya
ta shigo gidan .
Shi kan shi maigidan ba a banza ta barshi ko yanzu kuma bawai ta fasa abinda
takeyi din bane sai ma abinda yaci gaba a cikin halayen nata.
Duk da kasalan dake damu na a lokacin bai hanani tashi in girkawa kaina abinda
zanci ba lokacin bayan na gama ne na fitar da kayan da nayi aiki na wanka na shiga
bayi na watsa ruwa masu zafi don ruwan sama bai bani amana ajikina.
Ina fitowa daga bayi ne mukai kicibis da zarah da ta shigo dakin nawa a lokacin
wanda alama ya nuna yanzu ta dawo daga cikin gari sabada ledan da take dauke dashi
a hannun ta.
Nasan key din dakin ta tazo dauka tana saye da wasu kaya da ya matse mata jiki
sosai kin dawo nace mata eh kin gani sai yanzu na dawo wallahi.
Inda key din yake na nufa in dauko mata na mika mata leda daya ta aje min daga
cikin ledejoji dake rike a hanun ta nace lah dakin dauka wallahi na fada maki ai
ban son komai daga irin abinda kike dawowa dashi.
Lumshe idon ta tayi cike da jin takaici na tace na sani amma wanan ba inda kike
zato na samo shi ba sako ne da samu an kawo min daga gida naga idan na barshi ma a
hannu na baci zai yi shiyasa nace bari kawai in mika maki.
Ledan nabi da kallo a raina nace watau sakon da iyayyen ta suka aiko mata dashi
bai da wani amfani a gare ta sai na mazan da take bi ke nan.
Karban key din ta tayi ta fita dakin na bita da kallo tana saye da kayan da ya
matse mata jiki sosai ga kitson kanta da ta sako su har kafadan ta.
Tsuki nayi na shimfida anbin sallah na tayar da sallah na na idar na koma na
jingina da katifa na ina jan casbi a hankali waya na dake gefe yayi kara a
lokacin.
Number ne ba suna na daga ina mamaki waye mai wanan special number yake kirana
kuma kusan kiran zai katse na dauka.
Da sallama a baki na sai naji shiru kara maimaita sallaman nayi wanan karon sai
aka amsa min a gadarance kamar naso in sheda mai kiran amma na kasa canka.
Shiru har lokacin na sake cewa hello naji ance ina jinki nace wai waye please ko
wrong number aka kira ne yace ke kina magana da Abdulsamad Abdulrahim ne .
Nace waye haka kuma bazaki sani ba don ba lallai ne ki sani din ba nace kai ta
shafa wanan kuma banda lokacin irin ku haka kuke kiran mutane don bata masu lokaci
kawai.
Ke ban son rashin kuyan da kika iya ke har a wayan ma sai kin nunawa mutane halin
ki ba wani abu yasa na kiraki yanzu sai don inji wayarasu hajiya ta tafi zariya.
Au kace min miskilin mijin buzuwa ne nikan ina zan sani kaji ka da wani magana ni
zaka tambaya wa hajiya ta rasa kuma ?
A har zuke yace eh don a bakin ki mukaji ta tafi zariya shiyasa nake son jin
wanda muka rasa din bawai na kiraki bane kimin rashin kunya.
To ban sani ba kuma kada ka kara kiran layi na kaji na fada maka zan kashe nace
wai ma a ina ka samu layina dan fitina ?
Wanda kika ba ya bani layin ki mara kunyar yarinyar kawai zaki gane baki da wayau
idan na kama ki don naga rashi kunya yana nema yakawo kaina.
Kit na kashe wayan ban bari ya gama fadin abinda yake fadi ba don ba zan iya
tsaya in saurare shi ba nace wanan wani iri fitina ne kuma?
Ina ruwan shi dani da zai wani bugo min waya wai yana tambayana wa mahaifiyar shi
ta rasa da ta tafi zariya gaisu dan rainin wayau shi ba danta bane baifini kusa da
ita ba waini may hadina da wa yan nan mutanen ne haka da suke son su shiga min
rayuwana ina zaune kallau.
Shiko a ban garen shi ji yayi kamar ya samay ni ya fafala min mari ya sauke haushi
yaya akayi ne na raina shi haka ne.
Yaja tsuki ya fara laluben nomban mahaifiyar tashi dole ba don yaso ba yaji may
yasa har abu na faruwa irin haka take nisan ta shi da ita duk da yasan fushin da
hajiyan keyi dashi a kan Fati ne ba komai ba.
Kamar bata dauka ta dauka tare da fadin sallamu alaikum ya karba mata a cikin
ladabi sai ya fara gaida ita bayan gaisuwa ne yace cikin kwantar da murya hajiya
naji ance anyi maki rasuwa a gida kin tafi ?
Eh haka ne nayi rashi amma ni ya shafa ai rashin da nayi don jin ka baida wani
amfani a gareni inda dai dangin ka na kauyen maradi ne da ka tafi ko tuntuni.
Shiru yayi yana sauraren zafafan maganan da mahaifiyar shi take fada mai tace wai
tunkuna ma wani dan karabanin ya fada ma nayi rashi a dangina har kaji duk da nasan
ba kiran mutane yanzun kake yi ba buzuwan matar ka da dangin ta sun ishe ka.
Hajiya kiyi hakkuri nima a wurin yariyar nan Yusuf ya jiyo muna shine nace ba a
fada min ba tunda har zaki je zaria ki kwana biyu haka ba karamin rashi kika yi ba.
Tace wace yarinya ke nan kake magana a kanta yace yarinyar da kika hadamu da ita
kwanaki muka taho abuja sai dai yarinyar bata da kunya ban gane inda maganan ta ya
dosa ba.
Au khadija kake nufi ko wa yace ina ganin sunanta ke nan Yusuf ya hadu da ita
take fada mai yaban layin ta na kirata tana karanta min shirmay .
Tace Ladi ce matar kawun ka Allah ya karbi abinshi shine nazo ita khadijan kuma
ta damu da nine shiyasa tasan damuwa na har taji.
Yanzun kai bakaji kunya ba ace wai har khadija zata ji zance na kai bakaji ba
haduwan ka da yarinyar gaba daya ya canza muna kai kana ko tuna makomar ka ga
Allah.
Bani ba ba mahaifinka ba duk kayi watsi da alamarin kowa kana ganin buzuwa da yan
uwan ta sun isheka rayuwan duniya.
Mu din dai da kake gudu din mune dai iyayyen naka har gobe zance guda ne abin nan
da ka guje mu akan shi yana nan yana jiran ka .
Sannan da kake kiran khadija mara kunya ita ma ka sa mata tsanar ne na babu gaira
babu dalili saboda da tafi karfin matar son naka ko may .
Zai yi magana ta kashe wayan ta ta kyale shi ranshi yaji ya baci sosai da
maganan hajiya yasan akan Fati take wanan fushin haka dashi to shi may ye laifin
shi a ciki.
Hajiya suna gama waya binta ta kira tana tambayan ta ko sunyi waya da khadija
tace mama ta kura tana tambaya na ke nace kin tafi zariya an maki rasuwa acan zaki
kwana biyu.
Tace oho yanzu yayan ku ya kira waya wai sin hadu da yusuf take fada mai a wurin
ta suke jin an min rasuwa don baida kunya har khadija taji abu ya samay ni tana
jajantawa amma shi bai ji ba.
Sai kokarin son ya zagi yar mutane yake wai bata da kunya shi waya fishi rashin
kunya yanzu shida ya nuna muna ba komai muke a gare shi ba.
Sun gama da binta gulma ya ci binta sai ga kiranta ina shirin kwaciya ya shigo
min.
NOVEL DIN NAN NA KUDI BIYA DARI UKU KO KATIN DARI UKU TA WANAN ACCOUNT DIN
2254380105 ZAINAN IDRIS MAKAWA ZINETH BANK KO KI KIRA TA WANAN LAYIN 09026931792 KO
08036959257 ASHA KARATU LAFIYA
Hayaniyar yaran da suka dawo daga makaranta ya dawo da ita ga tunen tace shike nan
nawa ta samay ga Affan da dan banzan wayo kawai na shiryasu zuwa cikin gida wurin
kakanin su tasan idan sunje can sa samu abinda sukaci a cikin su.
Yaran suna shigowa suka fada mata a jiki suna fadin mama mun dawo yunwa nakeji
sosai wallahi karamin ya fada take taji gabanta ya fadi don hakan halin su ne .
Sai subar abinci a cooler makarantarsu su dawo dashi kuma suce yunwa suke ji
halin yaro ke nan oya a cire uniform kuje cikin gida wurin su hajiya kwaci abinci a
can banson yawan hayaniya yau.
Acan cikin gida kuma dawowan yaran gidan makaranta yasa hajiya ta kasa kunne
taji shigowan jikokin nata da take zaman jiran tsamanin su tunda safe.
Ba afi min ashrin ba ta fara tsinkayo hayaniyar su daga kofan shigowa gidan tace
a ranta nasan a rina dama tabbas hashe na ya tabbata ke nan wanan yarinyar har
takai can.
Yaran suka shigo dakin da murnan su don anan kawai suke samu su sake suyi yadda
suke so batare da wani tsangwama ba.
Suna shiga Affan ya cire rigan jikin shi ya rage daga shi sai singlet yana fadin
hajiya maman mu tace muzo nan muci abinci a wurin ki wai yau bata son damuwa.
Yar ta Aisha ta kwala wa kira tazo ta basu abinci sai gata ta fito daga daki
tana saye da dogon riga a jikin ta tana ganin yaran tace a a su Affan ne yau da
rana tsaka anan zakuci abincin rana ke nan ?
Hajiya tace zuba masu Abinci don Allah ki kawo masu nan ta wuce kitchen cika
umurnin mahaifiyar nata da sauri sai gata dauke da plate din abinci ta kawo masu.
Hajiya na zaune gefe ta kurawa yaran ido tana kallon yadda suke cin abincin
gwanin ban tausayi dasu tunane tayi aranta da yau babu ita fa kamar yadda babu ran
kakarsu ta wajen uwa yaya Fatima zatayi da wanan ukuban haka ?
Hajiya kubura da take matse ita tunda rana sai gata ta shigo wurin hajiyan da
mamaki a fuskanta tana fadin yaya kin ga hasashen yana son ya tabbata a kan
yarinyar nan ko sai ga hajiya karima uwargidan su tashigo a bayan su tace tabbas
maganan mu ya zama gaskiya.
Ya tabbata ke nan ta ki bari yarinyar nan ta girka abinda zasuci a gidan abin
har ya tashi ga ta hana mai aiki yi masu girki suci ya koma ta hana masu abinci.
Sallama ake daga kofan shigowa dayar yarinyar gidan ta leko daga kofan hajiya
karima tana fadin sannu da zuwa yaya Suraj.
Bai amsa mata gaisuwa ba sai tambaya yayi ba kowa a gidan ne ina sallama gidan
shiru tace suna dakin hajiya mama ina gani can yanufa dakin don yasan idan sunyi
irin wanan taron akwai abinda ke faruwa da ya shafi dayan su ne don don iyayyen
nasu nada hadin kao sosai a gidan.
In ka debe ko wanan ya kasance amaryan su Asiya bata gida ne a lokacin da su
hudu zasu hade a dakin kofan ya nufa yana saye cikin uniform din shi na sojoji.
Sallama yayi a bakin kofan daga ciki suka amsa mashi mahaifiyar shi hajiya
karima tace kamar muryan suraj nake ji a kofa yace nine ummi.
Dakin ya shiga kallo daya yayiwa iyayyen nashi alokaci guda ya gane akwai wani
matsalan da suke fuskanta wanda ya shafi hajiya mama a gidan.
Gaida su ya fara yi a cikin ladabi kamar ba soja ya samu wuri ya zauna bayan sun
karba mai gaisuwa.
Duban hajiya kubura yayi yace mommy akwai matsalane su Affan dake cin abincin su
hankali kwance ta nuna mai tana fadin wanan fitinaniyar matar uban tasu ce kila ta
rufe dakin girkin gidan ne yau ko da safe a nan suka dauki abincin zuwa makaranta.
Yanzun kuma kaga uwarsu ta turo su nan su da sauri yace ita Fatin fa may zataci
to ya tamnaya yana kallon fuskokin su gason jin amsan su.
Mommy tace ai shi muke tunane a nan dafe kai yayi yace wanan mata ban san abinda
take nufi ba a gidan nan tana son mayar muna da dan uwa binan.
Kada kaga laifin ta ai shine mai babban laifi mama ta fadi a hasale sai mummy
tace ba yin kanshi bane yaya bar irin shuuman matan nan wallahi.
Suraj ya mike a hasale yana fadin yau sai naci mata mutunci idan haka gaskiya ne
wallahi ko a gidan maza ana ma mutum horo da yunwa ne balle gidan brother za a ce
anyiwa mutum haka.
Ko maigadin gida ai yana iya kyauta da abinci tunda bai rasa ba balle diyan shi
ummi ta kalle shi lokacin da yake shirin fita daga dakin tana fadin ina zaka ?
Kai tsaye yace gidan zanje wallahi idan na samu gaskiya ne yau sai tabar gidan
nan wallahi ummi tayi saurin cewa dashi kaifa mahaukaci ne na sani a dai karbe key
din ka bude wurin shike nan.
Kasan yadda dan uwanka ke son ta hakan zai iya kawo matsala a tsakanin ku yace
wallahi sai dai ya kawo ummi wanan wani irin bakin haline haka ?
Ai haka suke mommy tace mashi abinda ake mai gudu ke jan tun farko bai gane ba
basu son kowa sai kan su da yan uwan su kawai wanan halin su ba wai ba.
Mama dai ta rike goshin tada hannun ta sai wanda duk yai magana cikin su ta
bishi da ido kawai shine nata yayin da zuciyar ta ke mata soya a ciki tana jin wani
irin ba dadi a ranta.
Yana tsaye daga kofa mommy tace bari muje tare dakai zaifi da sauri ummi tace
haka zaifi kan don wanan kin san mahaukaci ne ya shawo Alluran shi ja sojoji kar
yaje ya sauke wa yar mutane a kai.
Ai da zai sauke din haka zai fi gani take duk ta gama da kowa a gidan babu wanda
bata iya takawa shiyasa take abinda taga dama inji mama.
Yanzun dai bari mu tafi idan munje ni zan fara shiga wuri ta inji ba asin yin
hakan da tayi sai asan abinyi sukace yayi kyau hakan mikewa tayi zuwa dakin ta ta
dauko hijjib din ta ta saka suka fice da suraj din a motar shi suka karasa gidan.
Daidai lokacin Abba ya dawo shi da anty amarya daga asibiti da dan ta da bai da
lafiya ganin motar suraj ya gilma ya nufi gidan dan uwan nashi yasa suke mamaki.
Anty amarya ke fadin yau suraj ziyara zaikai gidan Abdul ne haka mahaifin nasu
yace kila yazo ya samu Fati ta koma dakin ta ne zai dubuta.
Sai da suka shiga gidan ne suke jin abinda ke faruwa karban key anty Amraya tayi
bata shiga dakin taba ta bar yaron wirin uwar gidan nata ta mara masu baya.
Sun samu kofar gidan a rufe wai taba maigadi sallahu cewa kada ya bari kowa ya
shigo gidan ya damay ta don yanzu ta dawo da yarta daga makaranta zasu huta.
Da kyat ya bude masu kofa sai da suraj yayi mashi jan ido wanan abin shiya kara
harzuka suraj din rashi ya baci sosai kusan a tare suka shiga gidan da anty amarya
don samun delay din shiga da sukayi.
Bin gidan Suraj yayi da kallo daga sama har kasa kafin ya karasa fitowa daga
motar shi cikin hasala mommy tace ashe kun dawo ke nan take cewa anty amarya tace
mun dawo ina shiga ake fada min abinda ke faruwa nace barin biyo ku don ba mutunci
ne da ita ba.
Anty tasan ida take rashin mutunci ta ai nika yau idan tayi min wallahi balbalata
zanyi in daki banza sai dai mu rufe da mijin ta ai mun saba.
A tare suka shiga gida jin karan bude get din gida ta fito a fusace tana fadin
maigadi wani dan bura, uba kabudewa, , , , , ganin su mommy yasa tayi shiru ta juya
da saurin tana zaton basu ganta ba suko sun ganta.
Kafin su iso ta wuce part din ta ko da sauri don tasan ba bakin ta bane na Fati
ne don ita suke zuwa gidan su .
Tunda ta sallamay sallah la,asar take zaune saman sallaya ta tun tana addua ta
koma tunane ga tunanen ya bowayeta don yunwan da ke cin ta.
Sun shiga da sallaman su aka gaisu tace mommy kune tafe ashe mune fati har kasa
takai tana kara gaida su cikin mutunci suka amsa mata ta dago tana fadin yaya Suraj
marmari daga nesa.
Ke kin ci abinci yau ko baki ci tambayan da ya jefo mata ke nan a lokaci daya
tayi murmushi tace kajika da wani magana kuma ba a gida ka samay ni ba zakai min
wanan tambaya haka ?
Mommy tace Fati ba tambaya muka zo yi ba don mun san abinda ke wakana a gidan ko
yau dai bakici komai ba tunda garin Allah ya waye haka ne ko ba haka ba.
Kai ta sadda kasa tace hakane mommy tace to akan may Fati zaki zauna ana maki
horo da yunwa dake da diyan ko haka abincin nan akwaishi ba babuba kuma.
Mommy yau fitina take ji tun jiya data dawo ta samu na dawo gidan ta fada min
bakaken magana har tana ikirarin sai na rami ya fini shan iska a gidan nan.
Shine yau da safe zan shiga kitchen na samu ta kulle komai tunda asuba wai kada
a dora girki a gidan ta fadawa Laraba ni kuma ban koma ta kanta ba tunda nasan don
ni tayi hakana.
Haba Fati sai ki zauna da yunwa ai zaki kashe kanki ne idan kina haka yanzu bari
muje mu samay ta muji may take nufi wai.
Suraj bai bisu ba ya dan tsaya ganin Fati din yana kuma tambayan ta may zataci
yaje ya sayo mata tace duk abinda ta samu yace kayan tea fa tace suna store acen
muke ajewa fita ya yi ya mara masu baya.
Sun shiga da sallama cikin isa ta karba masu sai suka tsaya gaisawa da ita tunda
iyayye ne su bayan gama gaisuwan mommy tace munzo ne dama muji dalilin rufe kitchen
da tsore din gidan da akayi wa mutanen gidan.
Hajiya nan fa gida na ne ina da daman da zan rufe ko ina nake son don Abdul bai
bar abinci da Fati a gidan nan ba tunda bai cata dawo ba ta dowo don haka sai ta
jira idan ya dawo ya bata abinci ita da diyan ta suci.
Karya kike yi munafukar Allah kuma baki isa ba wallahi muryan Suraj ne da batayi
tsamani ba ya fado dakin yana zazzare mata ido a cikin hasala yake magana yana
huci.
Tare da daka mata tsayawa yana fadin ban makulin nan tun ban balbalaki yanzu a
wurin nan in kuma sa sojoji suzo su kwashe ki sukaiki barikin mu su daure har ranan
da miji ku ya dawo inji shiku idan shiya ai horo da yunwa haka.
Kallo da tayi wa Suraj raga fuskan nan nashi ba imani a cikin sa zai iya aikata
abinda yace a kanta tsoran ta Allah tsoran ta soja da sauri ta mike ta shige dakin
ta yabi ta da harara.
Yadawo da fuskan shi kan yar ta dake cin abincin da tayo masu take away a hanyan
dawowanta gida ya watsa ma yarinyar harara da sauri ta noke kanta kasa ta kasa cin
abincin da tun shigowan su dacin abincin ta take yi bata ko gaida su ba.
Da sauri tafito daga dakin dauke da key din a hannun ta tana mika mashi cikin
ladabi ya fisge a hannun ta har ya fara tafiya su mommy zasu bishi sai kuma ya juyo
yana fadin.
Ina ne kitchen din da tsore suke ki taso muje yau za a yi ta ta kare and idan
bayan tafiya ko harara naji kin ma yar uwa wallahi yau ba ubanda zai hanani daureki
a garin nan jiki na rawa ta bi bayan shi zuwa tsore din yace ta bude da kanta ta
bude.
Laraba da mai masu aikin gida namiji da ta dauko dan kabilar su can garin su
wanda ya zama kamar CID din ta ga komi a gidan ko tana nan ko bata nan ya kira.
Komai na tsore din aka fito dashi waje aka kasa uku yace Fati ta kwashi kashi
biyu ita da diyan ta kashi daya ta dauka nata ne.
Ga abin magana ba halin yi don tsoron soja da ke zuciyan ta tun da zasu shigo
Nigeria sojoji suka latsu a hanya take tsoran soja inda duk ta ganshi.
Yana tsaye a rike kunkurun shi da hannayen shi biyu yake tambayan fati akwai
wani tsore da kitchen a gidan tace eh akwaishi a part din ta wanan nata ne ita
fatin suke amfani dashi in generar.
Kwashi naki kikai part din ki da sauri taja wani kwali da kyat tana fadin kasiye
dauko mun sauran ta matsu tabar wiein wanan dan banzan soja mara hankali dake
gabanta.
Dama tun zuwan ta gida da ta fara ganin shi aka nuna mashi ita a matsayin sabuwar
matar wan shi bai yi murna da ganin ta ba a fili ya nuna hakan kowa ya gani.
Don shi kyamar irin su yake yi bai dauke su wasu cikakkun mutane ba a idon shi,
yafi daukan mayaudara aduk inda ya gasu haka yake kallon su a yatsune.
Shine dan uwan shi ja jini ya auro ya kawo ta cikin zurian su take juya mutane
yadda ta ga dama a gidan da takaicin ta ya juya tafi bai shiga gidan nasu ba a
lokacin mommy tare da anty Amarya suka koma gida bayan sun yiwa Fati nasiha kadan.
Nan suka tafi suka bar Fati da tsoro a zuciyar ta fam sai dai abinda bata sani ba
a halin yanzu Nafisa tafita shiga tashin hankali don tsoranta Allah tsoron ta Suraj
soja.
Wanda ta hango mugunta zalla cikin kwanyan idon shi abinda ya fadi tasan karamin
aikin soja ne yayi shi ya aiwatar da abinda ya fada din dole ga magana nacin ta da
zata fadawa Fati a yau sai dai babu halin yin hakan gare ta dole ta kawo ido ta
saka mata a gidan tana jiran dawowan mijin nasu wanda zata sa ya ci fuskan Fati din
a gidan.
Ai idan sun san wata basu san wata da makirici zataci galaban su gaba daya don ta
gane yan uwan mijin da iyayyen shi duk munafukai ne a kanta.
Can gidan su hajiya sun koma kumshe da dariya a cikin su sai da suka shiga mota
suka fara dariyan abinda suraj din yayi wa Nafisa .
Yanzu sun gano takon ta Suraj ne zai dinga mata hukunci irin nasu na sojoji na
rashin imani sun shiga gida nan suke bada labarin abinda ya wakana a gidan.
Mama taji dadin har cikin ranta ko banza Suraj ya kwantarwa Fati incin ta yau
wanda inba shi din ba, ba wanda ya isa yayi haka a zauna lafiya da ita tunda tayi
niya.
Maganan mommy ne ya dakatar da ita da taji abinda Nafisan ke fadi a lokacin
shigan su gida da take fadin wai babu rabon su Fati da yayan ta ga abinda maigidan
ya bari a gidan.
Lalaima wanan matar tantiriya danta ya dauko mata ba kwai ba donge amma har take
ikirarin cewa wai ba abincin su a gidan.
Wani zafi na bakin ciki irin wanda iyayye ke ji a gamay da diyan su idan sun yi
abu ba daidai a cikin alumma wanda sai uwa ko mahaifi suka san da irin zafin da
mama taji a lokacin.
Haka dai ta shige daki a dadafe bakin ciki da takaicin da matan dan nata ke
kumsa mata a zuciyar ta yayi yawa kuma dan nata ya sani amma bai iya daukan wani
mataki akan hakan.
Wunin ranan haka suka kare shi da maganan Nafisa wanda hakan ba bakon abu bane
agurin anyi sau tari da yawa sai dai na yau din ya banbanta da sauri don ta fito ta
nuna masu karfin iko da izan da take dashi a cikin kan dan nasu .
Wanda suka haifa suka tarbiyartar da hannun su kuma ya tashi da tarbiya suke saka
ran samun farin ciki a wurin shi kamar yadda duk wasu iyayyen ke fata ga diyan su
idan su samu
Amma lokaci guda Nasifa ta shiga rayuwan dan nasu wanda ya watsar da duk wani
rayuwan farin ciki da suke hasashen samu daga gare shi.
Gashi a yanzu yana a cikin ganiyan samun duniyan shi wanda bai zauna ba tsaye
yake wurin neman na kanshi a rayuwan wanda ba komai yakawo hakan ba sai addun
mahaifa da yawaita ta sadaka akan diya yake bibiyan shi a yanzu.
Don a baya in zata iya tunawa bata da aiki sai yawai ta sadaka fiye da kowa a
gidan in anyi magana sai tace ba neman duniya nake wa kaina nemawa na baya nake
madogara.
Ga yawan taimakon na kasa da ita tundai idan ance yaro maraya ne sai mama tasan
yadda takai alherin ta ga yaron ko ta saka yayan ta suyi mai alheri daga abinda
suke dashi na jikin su mai kyau wanda zai farauta ran yaron da za a ba abin.
Don Allah iyayye mata mu kula kada muyi sakaci da wanan dama akan marayu da muke
gani zaki iya dafa kan yaro maraye zai ji dadin hakan da kikai mai har a cikin
ranshi.
Bawai duka maraye bane zai bukaci taimako wasa ma da dariya a gare su sadaka ce
dan abinda zai farauta masu rai sadaka ne Allah ya bamu ikon yi ga maratun dake a
kusa damu.
3�⃣
Tsaye take gaban mirrow tana gyara rigar da ta sa a jikin ta na tampha wanda akai
mata dogon riga dashi mai wani launi kamar jikin damisa brown colour.
Dinkin mai dan kwala sai da wuyan rigan V neck akayishi wanda yasa gaban ta ya
fito dakyau daga cikin rigar kasan rigan ma an bude shi free yadda zata iya walla
kafafuwan ta ba cikin matsuwa ba.
Turare ta dauka ta feshe jikin ta dashi ta juya ta dauko gyalen ta dake saman
godo gefe ta fesa mashi turare ta mayar a hand bag din ta dan kwali ta dauko ta dan
daki lokaci tana daurawa take fuskanta ya fito tsonen a jikin mudubin.
Duk wanan shirin da take yi ranta ba dadi don bata son zancen zuwa kaduna a
zuciyar ta tafi son tayi rayuwan ta a gidan ubanta dake a cikin garin Minna.
Inda gidan su yake a kwangila road asalin su su hausawa ne zamane na kakan ni ya
kawo su garin minna har suka zama yan ainihin gari baza kace su bakin gari bane
yanzu don kowa nasu anan aka haifeshi.
Daga wajen gidan wanda irin ginan da can bayane na siminti wani murya ya kirata
da fadin Khadija kina makara fa a cikin irin hausan mutane Niger shiba kananci kuma
ba hausa pure ba do ya dan hade da surkin harshe.
Muryan Khadija ne ke fadin mama shiri nakeyi gani fitowa yanzu da sauri ta karasa
shirin ta jawo dan trolley din da ta sa tufafin ta a ciki tare da rataya handbag
din ta a kafada ta fito waje.
Kallon ta mama tayi wace zance a wurin ta khadija ta debo kyau da na saba kafin
in ga mahaifin ta farar mace ce doguwa yar kabilan gwarin may kunkele dake a cikin
minna din.
Kallon yar nata tayi tace kin fi son ko yaushe kiyi tafiyan marance mama nina
fison in shiga da yamma yafi ba wanda yasan zuwan ka sai dai a ganka.
Maimakon tayi haraman tafiya sai ta ja kujera roban dake gefenta ta zauna kallon
ta uwar tayi tare da fadin yaya haka kuma ?
Banbara nake jira na aika a sayo dashi zan tafi bana son in mising din shine idan
naje ke dai yanzu na gane baki son zuwa wurin yar uwan naki tunda kika girma kika
fara karatun jamia .
Ta dan ya motsa fuska mai kama da sallo ko yanga wanda ba haka bane kusan yanayin
yan garin ne haka suke maganan su da kamar sallo da yanga tace ni nafison in yi
hutu na a gida.
Amma ita ya Amina kullun sai tace sai mutum tafi wurin ta hutu yanzu kuma ba da
bane ban son ina missing din gida sosai murmushi kawai uwar tayi don tasan halin
yar nata.
Ba ajima ba mahaifinta ya shigo gidan yana ganin ta yace a Khadija an fito ke nan
eh baba zan tafi hannu yasa ya fara laluban aljihun shi sai ya fito da dubu biyu ya
cire guda ya miko mata.
Kai ta girgiza mai tace baba ka barshi kawai kudin da anty ta turo min zai ishe
ni na gadone a daidai lokacin yaron da ta aika ya sawo mata banbara ya iso da leda
a hannun shi yana mika mata da canjin karike canjin tana bude ledan ta debo
banbaran ta mika mai ta mike tana gyara jakkan ta yaron ya taima ya fita mata da
kaya ida ta tare Napep zuwa Abdulsalam garej .
Tana isa saura mutum daya ta biya suka shiga suka kama hanyan garin kaduna yamma
lis suka shiga gari lokacin kuma akai hadarin marancen nan da Nafisa ta dawo ta
samu Napep din da zai kaita unguwar da yar uwar nata ke aure wanda kusan rabin
zaman ta a baya a nan tayi shi sai data girma ta koma gida karutun da take yi Abuja
yanzu shine silar mayar da rayuwan Khadija gida Niger state.
Tun ranan da khadija tazo kaduna bata fita ba tana daga daki sai falo indan ta
fito ko kuma ta shiga kitchen tayi masu girki a gidan.
Yau da yamma ya Amina ne ke kwala mata kira tana zaune tana cin banbara da tayi
worming din shi kamar yanzu akayi shi bai kwana ba.
Ya Amina gani ta fito tana fadi cikin ranshin kallon fuskanta don Allah zo ki
shiga gidan su mommy ki karbo min sako tace yanzu in tura a karbo min.
Fuska khadija ta ya motsa tace ni ban shiga ba tunda nazo banje na gaidasu ba
Amina tace wai khadija may ke damun ki ne haka ?
Ke a rayuwan ki sam baki son shiga jamma a ban san inda kike dauko wanan rayuwa
naki ba haka cikin bacin rai ta juya dauko gyalen ta kayan da tazo dasu garin ta
kara sakawa a jikin ta.
Yaran anty nata biyu ta, ta kira su rakata gidan da aka aike ta din fitowan su
bakin get din gidan yayi dai da zuwan wata mota a guje ta watso masu ruwan dake
kwance a wani dan rami saman hanya.
Cikin bacin rai Khadija ta dago kai tana fadin you are very stupeid bakya gani ne
kika watso ma mutane ruwa haka.
Horn kawai Nafisa tayi masu ba tare da ta tsaya khadija tabi motar da hararan
takaici tana dan kakabe riganta da ruwan ya dan taba a lokacin.
Raina yayi matukar baci haka muka doshi gidan mutane ina mita wani saurayi dake
tafe a bayan mu naji yace yar iskan buzuwan nan ne haka take tuki kamar mahaukaciya
wallahi.
Dan juyawa nayi na kalli mai maganan nace sannu yace yawa bata dai zuba maku
ruwan sosai ba ko nace kadan ya taba mu inayi har lokacin ina kakaban ruwa a
jikina.
Gidan muka shiga wanda har lokacin raina a bace yake da buzuwar da naji saurayin
nan yace min da sallama muka shiga gidan.
Wanda sai kawuce kofan falon gidan kabi wani dan siririn hanya da zai sadaka da
cikin gidan da muka shiga wanda babban gida na ba yau bane farkon shigana gidan don
duk zuwa nayi sai anty ta aike da gidan ina shiga akai akai yanzu tunda na girma
bani shiga idan nazo sai da wani dalili.
Sallama mukayi inda kofan uwargidan ne fara isa sai na mama daga can ciki sai
kuma wasu biyu dake kallon nasu din na mommy dana anty Amarya ke facing din su.
Hajiya ummi da yaranta nake jiyo hayaniyar su daga kofan part din ta na dan matsa
daga kofan dakin ina gaida su dakyat aka amsa min ban tsaya ba na wuce.
Lekowa akayi daga dakin ummi don ganin mai gaidasu din da bai shigo ba bata gane
ni ba alokacin har nakai kofan mama shiyasa ban son shiga wanan gidan don yawan
dake garesu kuma sai kabi kowa kagaida shi dole don hadin kai irin na matan gidan.
Koda baka gaida mutum ba wanda kaje wurin shi zaice dakai ka ko gaida mutanen
gidan sanin haka danayi yasa na fara binsu daga daga ina gaida su.
Dakin mama ma a kofa naja na tsaya ina fadin ina kwana mama ta amsa min daga ciki
tana fadin waye shigo mana ciki.
Dole na shiga daga cikin dakin tare da kara gaida ita inda nakai gwiwana duka
biyu a kasa irin gaisuwan mu na mutanen Niger.
Daga kuryan dakin ta aka fadin muryan wa nake ji kamar khadija Adamu da sauri mai
maganan ta fito falon ida nake wani irin ihu ta sake a lokaci daya tare da kwalawa
binta kira tana fadin ga khadija Adamu ashe tana garin nan mukayi maganan ta jiya.
Murmushi nayi ina dagowa daga gaida mama da nake nan suka shiritar dani nace
anty ta aiko ni wurin mommy.
Bayan nagaida amaryan su ne na wuce zuwa dakin mommy ta tareni da fara anta mun
dade tana jana da hira wanda ni ban iya sake jiki dasu muyi hiran sosai saboda
mutunci da girma da nake gani a idona.
Sakon ta dauko min na fita mukai sallama dasu nan suka rakoni suna dan taka min
in baki mantaba mai karatu na fada maki a nan kaduna nayi rabin rayuwa na.
Kamar abin tsokana wanan motar dai ne na dazun ta dawo a guje ta kara yin facali
da ruwa a take nace wanan wani irin iskanci ne wai haka ?
Har motar ta wuce sai ta dawo baya a hankali zuwa gare mu a lokacin zainab ke
fadin Nafisa ce fa ta dawo zai tai muna cin mutunci kila taji zagin da khadija tayi
ne.
Gab damu ta tsaya tare da sauke glass din motar wata farar mata nagani ciki
tare da wata zaune a gefen mai zaman banza.
Tace wace yar iska ce cikin ku take zagina shiru naji sunyi suna soke kai kasa
nan san lokacin da nace mata kece dai yar iskan da baki san darajan mutane ba kika
gudu da mota haka a wulkance cikin gari kamar yar koyo.
Ke tafadi a zafafe tana kokarin bude kofan motan da sauri naji su Binta da
zainab na fadin yi hakkuri anty bata san ke bace .
Cikin zafin rai nace ke wacece da zaki watsa ma mutane ruwa kice kada ayi maki
magana wallahi ko diyar shugaban kasa kike sai nayi maki magana .
Karasa fitowa tayi daga motan tana fadin ke yar gidan uban waye a garin nan take
raina ya kara baci nace kedin yar gidan uban waye da baki da tarbiya fada min naki
in fada maki nawa.
Fisgan hannu na Zainab keyi ni kuma ina turjewa don ban ga wani kimar ta da suke
gani ba idons a lokacin don sam ban da tsoro akan gaskiya na.
Ke yar waye da zaki tsaya kina fada min magana son ranki nace ni yar gidan ubane
ke kuma cewa akai titin na gidan ubanki ne da zaki dinga gudu kina watsa ma mutane
kura da ruwan titi.
Yadda taga ina yi sai ta tsaya tana kallo na kafin ta mayar da fadan akan su
Binta da zainab din tana fadin zamu hadu da kune wallahi don nasan da sanin ku take
min hakan.
Nace wai kun san wanan banzan ce da kuka tsaya tana fada maku maganan banza
saman hanya haka ?
A harzuke tace nice banza nace an fada maki idan ba banza kike ba may kike zaki
tsaya kina ma mutane son raki ke gaki mai kudi ki takamu ki wuce lafiya kin taki
banza ko ?
Zaki gane kurenki wallahi wani kallon banza na watsa mata nace sai dai mu gane
kuren mu amfada maki don kina da kudi zanji tsoron ki ne ko may kudin ki bai damay
ni ba tunda ban taba zuwa wurin ki neman wani abu ba.
Matar da take cikin mota ne taji abin yayi yawa kuma dukkan mu munki bari ta bude
mota ta fito tana jan ta tana fadin haba Nafisa zaki tsaya kan wanan karamar mara
kunya kuna raba hali a saman hanya ai sai ta ja maki raini ga jama, a.
Kuta tayi ta watsa min harara na mayar mats ta shiga mota tana fadin zaki san kin
shiga hurumi na nace inga alheri .
Fisgan mota tayi sai da yayi wani irin kugi suka nufi hanyan cikin gari zainab
tace wai Khadija kin san kowacece ita din ?
Wacece kuwa banda kila matar wani ko wata kusan gwaunati shike nan don muna kasa
sai ta rena mu Binta ce ta katse ni da fadin matar yayan mi ne kishiyar anty Fati.
Inda motar yabi nabi da kallo nace yanzu wanan matar matar dan uwan ku ne
wallahi na dauka irin matan bariki din nan ne masu zaman kasu nima ban san yaya
akayi idona ya rufe haka ba naci mata mutunci.
Nan nake fada masu abinda tayi muna da zamu shiga gidan su yanzu kuma ta sake
maimaita muna shiyasa raina ya baci don naga kamar da gaiyya tayi hakan amma kuyi
hakkuri don Allah.
Binta tace ai mu yau kin muna daidai wallahi don ba karamin dadi naji ba da
kikaci mata mutunci nan a gaban mu.
Mun da jima a tsaye dasu karshe mukai sallama muka shige gidajen mu har lokacin
ina da zafin matar nan a raina.
Nafisa ko sai fada take kawar ta na bata hakkuri tana fadin ban son ki biye mata
ba tunda kinga kannen mijin ki a wurin may yuyuwa tasan ki ke baki santa ba.
Zanyi maganin ta wallahi sai ta rena kanta zata san ba a taba ni a zauna lafiya
ko wacci tuwo dani miya ya sha na san dai ba yar gidan uban kowa bane ita.
Su zainab na shiga gidan su suka fara bada labarin arangaman mu da matar yayan
nasu nan mutanen gidan suka fito suna sauraren su.
Mommy tace kai amma wanan yarinyar wallahi ta burge ni sosai yau da haka Fati ke
daurewa ta mayar mata da martani da abin nata ya rage.
Anty amarya tace ai ba zata iya ba ne don ta riga tasa mata tsoron ta a zuciya
kuna ganin a banza ta bar mutane ne haka da kowa ke shayin ta.
Ummi tace kwarai ai irin su ba a banza suke barin gida ba sai sun kama bakin kowa
sun daure yadda ba mai iya motsawa a kan su.
Sai lokacin mama tayi magana tace aini wanan yarinyar ta gama shereni wallahi
tayi min daidai yanzu zata san in ta daure bakin wasu bata iya daure na wasu.
Nikan da muka shiga gida ya Amina tana daki mika mata sakon nayi a cikin wani
dan leda wanda ban san abinda ke ciki ba dakina nakoma na fara rage kayan jikina.
Na mayar da dan riga mai karamin hannu da bujen body hook dana cire sai hula
dana dora a kaina kitchen na nufa don dora abincin dare saboda yamma yayi.
Kafin wani lokaci har na kammala na gyara wurin na mayar da kauan da nayi aiki a
inda suke daki na kofa nayi wanka kafin a kira sallah na fito na canza kayan
jikina.
Kananan kaya na kara sawa a jikina don idan ina gida sune kayan sawa na wayata
na jawo ina duba sakon dana samu daga abokaina da muke karatu dasu.
Lokacin sallah yayi na mike na gabatar da sallah ban daga ba sai da na yi har
isha,i na nike abin sallah na fito din in ba yaran anty na abinci.
Anty ce ta fito daga dakin kwanan ta muryan ta naji daga baya na tana fadin har
kin fito eh kawai nace mata ba tare da na juya ba ina zuba abincin a plate na mika
ma yaran dake zaune suna jirana.
Juyowa nayi inda nake tsanmanin take zaune nace in zuba mata abincin yanzu ne
kallo na naga tanayi cikin mamaki tambayan da ta jefo min a lokacin ban zaci ji ba.
Khadija may ya hada ki da buzuwa yau kin ko san waye buzu kin san ko matar waye
don Allah ki rufa min asiri tunda nake unguwan nan ban taba fada da wani ko wata ba
ina jin tsoron rashin tsoran nan naki wallahi.
Kara daure fuska nayi nace ina ruwa da wata buzuwa ko baturiya take ba zan yarda
ta wullakantani ba ga banza don tana takama tana da kudi tunda ba kudin ta nace ta
bani ba.
Don Allah dai ki bari ban son irin haka ni na dauka kin bar halin nan naki yanzu
da kika girma ashe halin na nan baije ko ina ba.
Mijin ta fa na iya sakawa a kore mu a unguwan nan wallahi don suke fada aji yanzu
a garin don Allah dai ki bari.
Kamar zan yi magana sai nayi shiru ranan banci abinci ba saboda haushin buzuwan
nan dake ci min rai haka na kwana da tunane kala kala a raina.
Hajiya mama haka ranan itama ta kwana tana tunane a ranta kan yadda zatayi da
danta akan buzuwan da ta zama masu fitina da masifa a cikin zuri,an su.
Dan ta ya zubar mata da mutunci da kimar da mutane ge gani nata duk a kan auren
wanan matar da bata darajja mutane da halin ta.
Da safe nafito na hada breakfast har na gama ya Amina bata fito ba tana daki na
gyara ko ina na gidan sai na koma na shiga wanka na fito na shirya tare da hayewa
gado in dan huta.
Sai lokacin na fara jin hayaniyar su a falon gida alaman sun tashi ke nan daga
barci hakan baisa na fito ba sai kara lafewa danayi saman gadon barci ne ke son
dauka na a lokacin.
Muryan ya Amina naji na bude idona a hankali ina kallan ta daga inda nake kwance
nake mata ina kwana murshi tayi ta karaso gare ni tana fadin.
Har kin gama kin kwanta yau barci ne ya dauke ni tana fadi tana kaiwa zaune a
saman gadon da nake kwance jin banyi magana sai naji tayi murmushi .
Tace khadija fushi kike yi akan maganan da nayi maki jiya akan buzuwan nan bata
da mutunci ne khadija shiyasa kowa ke tsoron shiga tsabganta don mijin ta zai iya
keta ma kowa a kanta yadda yake son ta.
Dagowa nayi nace OK shike nan don mijin ta na da kudi ko mulki ba zanyi fada
akan dama na na dan adam ba murmushi naji tasake yi tace khadija ina raba ki da
shiga tsabgan irin mutanen nan.
Kai na kawar gefe ina hade miyau takaici da yazo min a lokacin haka abin yai ta
cina har na gaji na sake na manta da wata can a zuciya.
Jin shiru da su Binta sukayi yasa su ranan biyo ni gida a falo suka samay mu
dukkan mu nan muka zauna har anty muna hira suna min korafi wai kullun ina gida
kumshe ban fita.
Zainab tace kodai kina tsoron haduwan ki da Nafisa ce nace waye Nafisa kuma tace
matar yayan mu mana da kuka kwasa ranan .
Oh kuce mi buzuwa mana ai sai in gane ba Nafisa ashe sunan ta ke nan ni na fi
gane ma buzuwa ai Binta tace ai bata son a kira da buzuwa shiya sunan ya mutu a
bakin mu.
Ranan da ra kai kara wajen yayan a gidan bakiga irin fadan da yai muna ba ni tun
lokacin gidan ya fita raina wallahi.
Ashe ya zama mijin buzuwa ke nan yar sani in fika wai agola da rabon gida ina
kika san yar sani in fika ne ai sai kin ga yadda ta mayar da anty Fati a gidan.
Ita da mijin ta yanzu ta koma yar kallo a gidan ko dan aikin gidan yafi ta
daraja a gidan kwanan fa sai da ta fito aka maida ita kin san may ?
Da ta koma bata gidan tana dawowa sai cewa tayi wai uban wa yace ta dawo gidan
sai ta kama kitchen da komai tarufe na gidan ta hana ma anty Fati da yaranta.
Sai lokacin anty dake gefe ta saka baki a hiran da mukeyi a falon tace amma samun
wurin nata yayi yawa wallahi nace wai wace anty fati kuke magana haka ?
Wanan da ta taba haihuwa har mukai fati daku a baya dan tunane nayi nace nagane
ta itace mijin ta ya auri wanan matar wallahi itace inji Binta zainab dai sai
dakilan wayanta takeyi tana charting.
Anty ce tace yanzun yaya akayi akan abincin nan dai take fada muna yadda suka
kwashe da suraj anty ce ke dariya ni banga abin dariya ba tunda ba dukan ta naji
yayi ba.
Sun kai wani lokaci suka ce zasu tafi na mike na dan taka masu har bakin get din
gidan anty na na dawo ciki.
Tun asuba yake tayar da ita ta tashi tayi sallah amma tana kwance tana barcin ta
har yagaji yatayar da ita da karfin tsiya ta zauna tana mustsukan ido alaman barcin
bai isheta ba har lokacin yana ganin ta tashine yasa shi fita daga dakin azaton shi
zata tashi tayi sallah.
Ya fita zuwa dakin motsa jikin shi da yakeyi duk safe inda kuma yake aje wasu
kayan amfanin shi jiya anan yabar wayan shi yana canji ya je ya kwanta yana tunanen
rashin son ibadan da batayi.
Ya gama komai na motsa jiki da yakanyi da safe ya wuce zuwa inda wayan shi yake
jone ya dauko din ka idan shine sai takwas yake bude waya da safe.
Budan wayan yasa sakon da suka taru mai shigowa ya gane su wanda farko budewa
nawa ne ya shigo da farkon.
Mamaki yayi don ba suna sai lamba ga dogon sako kuma da maishi ya turo mashi
kamar kada ya karanta tunda baisan mai sakon ba sai kuma wata zuciya tace dashi
karanta kaji mana abinda sakon ya kumsa kila mai amfani ne gare ka.
Fara karanta sakon ne yaji ranshi ya baci don ya fahinci inda sakon ya fito don
ganin farkon rubutun nawa kamar haka
Mijin buzuwa a zaton ka zaka iya rabani da hajiya mamane ko ka zubar min da
mutucina da take gani kayi kuskure wallahi kuma kayi karya don bakina da naka ban
fada ma hajiya mama tana gida an mata rasuwa ba.
Ga wanda yasan mutuncinta yasan darajan ta na fadawa shida ya tambaye ni ko ina
da labarin su bakai da buzuwa wace bata da daraja da galihu tasa ka zubar da matan
ka da yayan ka da kowa naka kana ganin tsohuwar buzuwa tana maka rudi da huduban
shedan kullun.
Kai bari ma kaji wallahi wanan buzuwar ta zubar ma da kima da komai naka a idon
duniya tunda kiri kiri ta mai dakai mijin hajiya.
Ga mutum har mutum amma baida ta cewa saboda mace macen kuma buzuwa wace bata san
Allah how dear you kaida mace bata bari ka zauna dako matar sunnan ka har kake da
bakin yi mun hadi a wurin mama, , , ,
Jikin shi har rawa yakeyi da yake karata text din kasa kai kashen rubutun daki
ya nufa da sauri da zuman ya shiga yai wanka ya fita ya samu Yusuf shida yaja mashi
rene da wullakanci wurin yar karamar yarinya harta iya turo mashi text din banza
haka.
Sai yayi magani na a garin sai yasa na raina kaina may nike dashi may nake
takama dashi da zan iya yimai cin fuska haka ina aibanta shi shi da matar shi.
Waya ya fada min maganan da sukayi da hajiyan su hajiyan ne zata fada min kowa
komai dai may nene sai ya rena min wayo sai na gane banda wayo yau a garin nan duk
inda na shige sai ya tononi a cikin garin nan yayi min wulkanci
Sai dai yana shiga dakin su kuma sai bacin ran nashi ya karu ganin Nafisa kwance
tana barcin ta hankali kwace rashi ne ya kara baci ya tuna abinda nace a text dina.
Bai san lokacin da ya isa wurin ta yakai mata mugun maka a tsakar bayan ta ba ta
mike firgigit tana fadin Samad may nayi maka ?
Tsawa ya daka mata yace wanan abin zai hada ni dake ke sai yaushe ne zaki rike
ibada a zuciyar ki ne yaja tsuki ya shige wanka.
Da sauri ya watsa ya fito ranan ya fito bai wani dauki dogon lokaci ba ya shirya
ya fita daga gidan koda ta fito ta samu baya gidan.
Tun a mota ya kira Yusuf yana fadin kana inane yanzu?
Gani gidana ya bashi amsa OK kajirani ganin zuwa yanzu gidan yace eh mamaki
Yusuf yaji yana tunanen mai zai kawo Samad gidan shi wanan lokacin haka.
Don ka idar shine sai takwas yake fitowa ko takwas da rabi ware hannu yayi alaman
shi ya sani ya mike ya shiga wanka kada yai mashi girshi.
Yana shiri ya sake bugo mai waya gashi kofa gidan shi ya fito ya karasa ya fito
ya samay shi don ko driver bai fito dashi ba Yusuf din na gani haka ya rufo gidan
nashi ya fito ya samay shi.
Anan ya bude mai mota ya shiga yarufe sai ya dauki hanya batare da yasan inda
zasu nufa ba sai yaga ya miki mashi wayan shi duban wayan yake da mamaki yake fadin
na maye wanan kuma ?
Ka duba mana cewa fuska a daure ya karbi wayan ya fara karantawa a hankali yana
sake murmushi ya gaba yana mika mai wayan yace kai amma wanan yarinyar takai jaruma
wallahi haduwan zai zama abin shaawa ga mai kallo.
May ne kace yanzun kai baka ga abin jin haushi ba a nan yace ban gani ba sai ma
wani abin da na hango na daban tsakanin ka da beauty din.
Yau sai nanu namata ita ba kowa bane a garin nan sai na wullakanta ta a garin
nan dariya yayi sosai yace da kaima kan ka wallahi da ka tozarta kan kuwa.
Wai kaiko kaga yadda kukai balain dacewa da yarinyar nan kuwa wallahi ni abin
naku burgeni yake yi idan kuna yi har wani dadi nake ji.
May kake nufi ne wai yace abinda idona ya hango min mana a kai saidai fatan
alheri amma zancen ka ci mata mutunci bai taso ba ko kaje ka tozartata duk ba wanan
a tsakanin ku ko kamanta da hikimar hajiya na hada ka da wanan yarinyar ne ko kana
nufin kai baka gane hakan ba.
To bari kaji Khadija itace zata iya fitar dakai daga zargin da ake maka na cewa
Nafisa ta gama dakai da cewan da ake saboda ita ka kasa zama da Fati.
Akan wani dalili zata fitar dani ta yaya din zata fitar dani yace muje zuwa nan
gaba zaka sani idan lokacin hakan yayi yanzo ina zamu ne kadauko ni tunda safe
haka.
Wurin ta zamu in gwada mata ita din ba kowa bace ya kwashe mai da dariya yace ta
zama kowan ke nan tunda har zaka iya biye ma shirmay ta na mata.
Bai kara magana ba sai juya kan motar yayi zuwa office din su ya shige bai tsaya
jiran Yusuf din ba.
Anan malam musa driver ya tsayar dashi yana fadin yana da magana dashi na siri
da yake son suyi a tsakanin su yace da malam sani din wani abu ya faru ne yace eh
to sai dai maganan nason siri gaskiya yace dashi babu damuwa kasa may ni a gida da
yamma idan mun tashi.
Ga haka suka bar zancen da malam sani din sai dai ya barshi da tunane a zuciyar
shi ko akan may yake bukatan kebewa dashi bai sani ba ya san dai abune mai
muhinmanci sosai.
Shiko gogan acikin office maganan da sukayi da Yusuf ne yake ta mashi yawo arai
wai zata zama mai garkuwa a kan matsalan shi da Fati da Nafisa ta yaya ma haka zai
faru .
Nan dai ya watsar da maganan ya ci gaba da aikin dake gaban shi sai dai yanayi
yana tuna zancen a zuciyar shi.
Kai tsaye da na fito kamar yadda na saba gidan da muke na nufa yau yawan ci basu da
lectures sai karan gida ke tashi ko ina a cikin gida.
Yunwa nake ji don ban tsaya nayi karin kwarai ba da safe sallah nayi sana fara
hada tea na nasha sai da na dan huta a wurin na mike ina sauya kayan jikina.
Na saka dan guntun rigan da nake zama a daki dashi gyaran dakin nayi na gyaro ko
ina na dakin sai na dora girkin dare don shinkafa da miya nake son yi irin na yan
makaranta.
Bayan na gama miya na dora shinkafan na koma na zauna a bakin katifa ina tunane
zarah ne ta fado min a rai yau in zan lissafa kwananta biyar bata dawo ba.
Zarah tana daya daga cikin "ya"ya dake cin amanan iyayyen su don babu inda suka
rageta don koba a fada ba zarah tafi gata don sati biyu bai shigewa iyayyen ta basu
turo mata da sako ba.
Amma duk ta watsar da wanan gatan nata tabi ra,ayin kwadan abin hannun samari
wanda ya rufe mata ido a yanzu har yakai ga ta watsar da karatun ta.
Ido na lumshe tare da girgiza kaina ina cewa ubangiji katsare mu ka karemu ya
Allah kasa mufi karfin zuciyar mu don yanzu rayuwa abin tsorone .
Sai gata washe gari ta dawo dakina ta nufa don karban key din ta koda ta shige
ban sake mata fuska ba daga inda nake kwance ta tambayi key din ta na nuna mata da
hannu kawai ta nufi wurin ta dauka.
Harara na bita dashi tana ficewa daga dakin andan jima kadan sai gata ta dawo
dakin daga ita sai wani dan guntun tawul da ta daura iya cinyan ta tana tambayana
wai ban rage abinci ba in bata.
Wani kallo nayi mata nace inda kika fito gantalin ki kwana da kwanaki baki kici
abinci bane acan ?
Tace kin san yanzu wata yayi nisa ba wani abin kirki ake samu ba sai maneji nace
sai ki je gaba ki nema ni banyi abinci ba yau.
Ta ce khady yaushe kika fara rowa haka ba halinki bane rowa nace ban dafa ba
nace maki ashe karyan iskanci kike yi da zaki dawo kwana da kwanaki hannu empty.
Ta dan tsaya jin ganin ban kulataba ina karatuna sai ta fice min daga dakin
dagowa nayi nabita da kallon mai kama da harara har tafice daga dakin.
Bayan ya gama saurare abinda malam sani ya gaya mashi jikin shi ne yayi sanyi
karshe yayi mai godiya tare da jaddada mashi kan kada ya fada ma Nafisa komai ya
dai saka ido ga alamarin ta kawai.
Bayan fitan shi gidan nine na fado mashi a rai wayana ya kira mun gaisa dayake
shi mai son wasa ne nan yajani da wasa wanda bai wuce hiran mijin buzuwa.
Yace gobe dai weekend ne ba shiga aji ke nan nace eh sai dai ina son zan fita
zuwa wurin wankin kai don ina son gyaran jiki gobe dai.
Yace ashe shi gyaran ma sai anje wani guri yin shi dariya yaban don irin zolayar
shi nace ana mace ba gyara ne yace kwarai kuwa har in ta san kanta.
Karfe nawa zaki ya tambaya nace wuraren goma zan tafi nasan zuwa karfe sha biyu
ko da rabi na gama yace da safe banda time da nazo na kaiki sai dai ki fada min
sallin din da kike zuwa in duba ki idan na rarage abinda nake yi.
Nace No kabarshi kawai ba wani nisa yake dashi da inda muke ba nagode yace aini
nace ki fada min ko nace beauty hair drasses na fada mai layin da yake a saman
babban titi.
Munyi sallama ina mamikin halin shi da saurin sabo irin nashi na zauna na tsefe
kaina a cikin daren nan don kada in makara in samu mutane a wurin.
Washegari da safe na shirya na isa sallon din ba wasu mutane dayawa don haka nabi
layi sai da akawanke min akai min drying din shi kafin su fara min kitso.
Ranan nasha gyara sosai na jiki daidai zan fito sai ga wayan Yusuf shigo yana
tambayana ina wurin ko wuce nace an kusa gamawa nan da minti talatin zanbar wurin .
Nakashe wayan akaci gaba da min gyara sai yaba yawan gashina da tsayi suke yi
nidai murmushi kawai nake masu ban wani dogon magana da kowa a wurin.
Sun fito daga kubuwa duban fili da sukaje gani a hanyansu na komawa gida yaga
Yusuf ya dauki hanya bai iya magana ba yana aiki a system din shi kan shi a duke
yake.
Sai dai yasan ba hanyan gida Yusuf ya nufa dasu ba aikin da yakeyi ya dauke mashi
hankali a lokacin ganin ya tsaya a bakin wani gyaran jiki na mata yasa shi dago kai
yana tambayan shi ina ne nan kuma ?
Kafin ya bashi amsa yaji yana fadi a wayan shi fito gamu a kofa idan an gama maki
nace gani tafe na fito tun fitowa na ya hango nice tafe kallon mamaki yake wa Yusuf
din.
Har na karaso bakin motar nasu sai a lokacin nasan tare suke dashi fadi yusuf ke
yi da na karaso wai wanan haduwa haka fa kanwata .
Kaike kara zuzuta yayi maganar kamar bashi ya fada ba yace ba dole ba in zuzuta
kanwata yar gidan mama wanan ai kyasa ayi karo a hanya nidai murmushi kawai nayi
mashi.
Na fara gaida su yace shigo mu sauke ki mana ba hostel zaki koma ba nace a a
nagode yayana ku tafi abinku kawai dakai dayane zan shiga amma dai ku tafi kawai.
Yace au don wanan miin buzuwan da kika gani ai bashi ke jan motar ba ko shiga
muje don ki kawai muka biyo nan fa.
Jin haka yasa na bude motar na shiga batare da na sake wani magana ba shiko sai
aikin shi yake yi kawai ana tafiya mun kai wurin wani babban shago yace don Allah
ku bani minti biyu in dawo.
Ya faka motar yafita sai mu biyu a cikin motar kowa da abinda yake yi a lokacin
sai can naji yaja tsuki yana kallon shagon na dauka dani yake yi nace dakata malam
bafa kai ka dauko ni ba da zaka ja min tsuki haka.
Da mamaki ya dago kai yana kallo yace ke dani kike nace da wani nake haka kawai
zaka kama jamin tsuki a mota da mamaki yake kallo na yace ke wata irin yarinya ce
da bata da tarbiya.
Kadai gyara maganan ka malam tarbiya ai ko makaho yasan akwaishi nan sai dai a
lalaba a gani ai ba bace marasa tarbiya suke ba.
Bai kai karshen magana ba cikin zafin nama da kunar zuciya ya juyo inda nake yace
wa kike nufi baida tarbiya cikin muryan nan nashi mai dadin saurare da yake rowan
ta.
Tsoro naji ganin irin kallon da yake bina dashi mai kama da harara ko tsana sai
nayi kasa da kaina na kasa furta komai don kwarjin da yai min a idona
Ya nuno yatsan shi daidai saitin fuska na tare da tsure ni da idanuwan shi
lumsarsu yana fadin ke in badan Yusuf da bai san ciwon kan shi ba har kucaka irin
ki ta isa ta shiga min mota na a tare dani.
Yace kallani nan ko a hanya nagan ki baki isheni kallo ba a cikin mata don banga
abin gani a wurin irin ki ba cikin dakiya da dauriya nake kallan shi ina jin
kalamin shi har cikin raina sai dai ina tara abinda zan mayar mashi ne a zuciya ta
duk da naji tsoran yanayin shi.
Yaci gaba da fadin idan baki hankali da ni ba watarana sai na balbala ki wallahi
don ni mace bata kawo min raini nace dashi.
Don Allah malam matsamin bakumayi mamaki jin haka don ba abin mamaki bane don ka
fadi hakan tunda dama kai irin maza nan ne dake raina jinsin su sai kai ido ga mata
ketere saboda zalama irin na rashin sanin ciwon kai.
Don wanan matar taka abin kyama ga jamma a da kai ka mayar mutum har kake ganin
tafi ko wace macen kasan nan dadin abin dai kaima macen kasan nan ta haife , , , ,
Fat naji yakai min bugu a baki don zafi sai da na dafe baki na ina dubawa ko
jini yake min ban san lokacin da idona ya fara fitar da hawaye ba na yun kura zan
fita daga motar yasa hannu ya danna lock mutar ta rufe kit yace kuma ki saurare ni.
Duk kika sake ganina a mota kikayi gigin shigan shi sai ya jefar dake a waje mota
ya take ki kin mutum in kashe ki in kashe bazan .
Nace ni wallahi ba banzan bace sai dai in kaine yace bakin naki bai mutu bako
yana kokarin kai hannun shi ya kamo baki na na noke kaina a kafana sai bai samu
kama bakin nawa ba.
A daidai lokacin Yusuf ya iso wurin da manyan ledoji a hannun shi yana bude motan
zai sa ganin mu haka yasa shi ya sake murmushi.
Ina jin shi nayi saurin dago kai nace mugu kawai azzalumi yace kai yaya haka may
kai mata don Allah take kuka kuma ya waigo zai kara jamin baki na noke ina son fita
a motan Yusuf ya tare ni yana fadin haba dai yaya zakaci zalun ta kuma haka ?
May tayi maka haka wai kasa ta kuka ya juya yana cewa bakin nan mai rashin kunya
na daka ido ya zaro yana cewa ka dake ta Abdul ?
Kadan ma ke nan nayi mata ai fita nake son yi ba hanya don Yusuf dake wurin yayi
rufe kofan ya zagaya ya shigo motar sai da muka fara tafiya yace ka bata hakkuri
Abdul.
Ina baya ina kuka naji ya fada mai hakan yace nace ka bata hakkuri yace wani
zanba wanan yariyar hakuri ko wa yace bakai ka zalunce ta don may bazaka bata
hakkuri ba ko kafin ka tafi da hakkin ta ne a kanka ?
Baiyi magana ba sai aikin shi dayaci gaba dayi yace wai may ya hada kune haka da
sauri nace zagina yayi na rama.
Motar ya tsaya a kofa gidajen mu na fita da sauri ya biyo ni yana kirana ban
tsaya ba wata yar gidan yaba kayan ta shigo min dasu suka tafi ban san yadda suka
karata ba.
Tun asuba yake tayar da ita ta tashi tayi sallah amma tana kwance tana barcin ta
har yagaji yatayar da ita da karfin tsiya ta zauna tana mustsukan ido alaman barcin
bai isheta ba har lokacin yana ganin ta tashine yasa shi fita daga dakin azaton shi
zata tashi tayi sallah.
Ya fita zuwa dakin motsa jikin shi da yakeyi duk safe inda kuma yake aje wasu
kayan amfanin shi jiya anan yabar wayan shi yana canji ya je ya kwanta yana tunanen
rashin son ibadan da batayi.
Ya gama komai na motsa jiki da yakanyi da safe ya wuce zuwa inda wayan shi yake
jone ya dauko din ka idan shine sai takwas yake bude waya da safe.
Budan wayan yasa sakon da suka taru mai shigowa ya gane su wanda farko budewa
nawa ne ya shigo da farkon.
Mamaki yayi don ba suna sai lamba ga dogon sako kuma da maishi ya turo mashi
kamar kada ya karanta tunda baisan mai sakon ba sai kuma wata zuciya tace dashi
karanta kaji mana abinda sakon ya kumsa kila mai amfani ne gare ka.
Fara karanta sakon ne yaji ranshi ya baci don ya fahinci inda sakon ya fito don
ganin farkon rubutun nawa kamar haka
Mijin buzuwa a zaton ka zaka iya rabani da hajiya mamane ko ka zubar min da
mutucina da take gani kayi kuskure wallahi kuma kayi karya don bakina da naka ban
fada ma hajiya mama tana gida an mata rasuwa ba.
Ga wanda yasan mutuncinta yasan darajan ta na fadawa shida ya tambaye ni ko ina
da labarin su bakai da buzuwa wace bata da daraja da galihu tasa ka zubar da matan
ka da yayan ka da kowa naka kana ganin tsohuwar buzuwa tana maka rudi da huduban
shedan kullun.
Kai bari ma kaji wallahi wanan buzuwar ta zubar ma da kima da komai naka a idon
duniya tunda kiri kiri ta mai dakai mijin hajiya.
Ga mutum har mutum amma baida ta cewa saboda mace macen kuma buzuwa wace bata san
Allah how dear you kaida mace bata bari ka zauna dako matar sunnan ka har kake da
bakin yi mun hadi a wurin mama, , , ,
Jikin shi har rawa yakeyi da yake karata text din kasa kai kashen rubutun daki
ya nufa da sauri da zuman ya shiga yai wanka ya fita ya samu Yusuf shida yaja mashi
rene da wullakanci wurin yar karamar yarinya harta iya turo mashi text din banza
haka.
Sai yayi magani na a garin sai yasa na raina kaina may nike dashi may nake
takama dashi da zan iya yimai cin fuska haka ina aibanta shi shi da matar shi.
Waya ya fada min maganan da sukayi da hajiyan su hajiyan ne zata fada min kowa
komai dai may nene sai ya rena min wayo sai na gane banda wayo yau a garin nan duk
inda na shige sai ya tononi a cikin garin nan yayi min wulkanci
Sai dai yana shiga dakin su kuma sai bacin ran nashi ya karu ganin Nafisa kwance
tana barcin ta hankali kwace rashi ne ya kara baci ya tuna abinda nace a text dina.
Bai san lokacin da ya isa wurin ta yakai mata mugun maka a tsakar bayan ta ba ta
mike firgigit tana fadin Samad may nayi maka ?
Tsawa ya daka mata yace wanan abin zai hada ni dake ke sai yaushe ne zaki rike
ibada a zuciyar ki ne yaja tsuki ya shige wanka.
Da sauri ya watsa ya fito ranan ya fito bai wani dauki dogon lokaci ba ya shirya
ya fita daga gidan koda ta fito ta samu baya gidan.
Tun a mota ya kira Yusuf yana fadin kana inane yanzu?
Gani gidana ya bashi amsa OK kajirani ganin zuwa yanzu gidan yace eh mamaki
Yusuf yaji yana tunanen mai zai kawo Samad gidan shi wanan lokacin haka.
Don ka idar shine sai takwas yake fitowa ko takwas da rabi ware hannu yayi alaman
shi ya sani ya mike ya shiga wanka kada yai mashi girshi.
Yana shiri ya sake bugo mai waya gashi kofa gidan shi ya fito ya karasa ya fito
ya samay shi don ko driver bai fito dashi ba Yusuf din na gani haka ya rufo gidan
nashi ya fito ya samay shi.
Anan ya bude mai mota ya shiga yarufe sai ya dauki hanya batare da yasan inda
zasu nufa ba sai yaga ya miki mashi wayan shi duban wayan yake da mamaki yake fadin
na maye wanan kuma ?
Ka duba mana cewa fuska a daure ya karbi wayan ya fara karantawa a hankali yana
sake murmushi ya gaba yana mika mai wayan yace kai amma wanan yarinyar takai jaruma
wallahi haduwan zai zama abin shaawa ga mai kallo.
May ne kace yanzun kai baka ga abin jin haushi ba a nan yace ban gani ba sai ma
wani abin da na hango na daban tsakanin ka da beauty din.
Yau sai nanu namata ita ba kowa bane a garin nan sai na wullakanta ta a garin
nan dariya yayi sosai yace da kaima kan ka wallahi da ka tozarta kan kuwa.
Wai kaiko kaga yadda kukai balain dacewa da yarinyar nan kuwa wallahi ni abin
naku burgeni yake yi idan kuna yi har wani dadi nake ji.
May kake nufi ne wai yace abinda idona ya hango min mana a kai saidai fatan
alheri amma zancen ka ci mata mutunci bai taso ba ko kaje ka tozartata duk ba wanan
a tsakanin ku ko kamanta da hikimar hajiya na hada ka da wanan yarinyar ne ko kana
nufin kai baka gane hakan ba.
To bari kaji Khadija itace zata iya fitar dakai daga zargin da ake maka na cewa
Nafisa ta gama dakai da cewan da ake saboda ita ka kasa zama da Fati.
Akan wani dalili zata fitar dani ta yaya din zata fitar dani yace muje zuwa nan
gaba zaka sani idan lokacin hakan yayi yanzo ina zamu ne kadauko ni tunda safe
haka.
Wurin ta zamu in gwada mata ita din ba kowa bace ya kwashe mai da dariya yace ta
zama kowan ke nan tunda har zaka iya biye ma shirmay ta na mata.
Bai kara magana ba sai juya kan motar yayi zuwa office din su ya shige bai tsaya
jiran Yusuf din ba.
Anan malam musa driver ya tsayar dashi yana fadin yana da magana dashi na siri
da yake son suyi a tsakanin su yace da malam sani din wani abu ya faru ne yace eh
to sai dai maganan nason siri gaskiya yace dashi babu damuwa kasa may ni a gida da
yamma idan mun tashi.
Ga haka suka bar zancen da malam sani din sai dai ya barshi da tunane a zuciyar
shi ko akan may yake bukatan kebewa dashi bai sani ba ya san dai abune mai
muhinmanci sosai.
Shiko gogan acikin office maganan da sukayi da Yusuf ne yake ta mashi yawo arai
wai zata zama mai garkuwa a kan matsalan shi da Fati da Nafisa ta yaya ma haka zai
faru .
Nan dai ya watsar da maganan ya ci gaba da aikin dake gaban shi sai dai yanayi
yana tuna zancen a zuciyar shi.
Kai tsaye da na fito kamar yadda na saba gidan da muke na nufa yau yawan ci basu da
lectures sai karan gida ke tashi ko ina a cikin gida.
Yunwa nake ji don ban tsaya nayi karin kwarai ba da safe sallah nayi sana fara
hada tea na nasha sai da na dan huta a wurin na mike ina sauya kayan jikina.
Na saka dan guntun rigan da nake zama a daki dashi gyaran dakin nayi na gyaro ko
ina na dakin sai na dora girkin dare don shinkafa da miya nake son yi irin na yan
makaranta.
Bayan na gama miya na dora shinkafan na koma na zauna a bakin katifa ina tunane
zarah ne ta fado min a rai yau in zan lissafa kwananta biyar bata dawo ba.
Zarah tana daya daga cikin "ya"ya dake cin amanan iyayyen su don babu inda suka
rageta don koba a fada ba zarah tafi gata don sati biyu bai shigewa iyayyen ta basu
turo mata da sako ba.
Amma duk ta watsar da wanan gatan nata tabi ra,ayin kwadan abin hannun samari
wanda ya rufe mata ido a yanzu har yakai ga ta watsar da karatun ta.
Ido na lumshe tare da girgiza kaina ina cewa ubangiji katsare mu ka karemu ya
Allah kasa mufi karfin zuciyar mu don yanzu rayuwa abin tsorone .
Sai gata washe gari ta dawo dakina ta nufa don karban key din ta koda ta shige
ban sake mata fuska ba daga inda nake kwance ta tambayi key din ta na nuna mata da
hannu kawai ta nufi wurin ta dauka.
Harara na bita dashi tana ficewa daga dakin andan jima kadan sai gata ta dawo
dakin daga ita sai wani dan guntun tawul da ta daura iya cinyan ta tana tambayana
wai ban rage abinci ba in bata.
Wani kallo nayi mata nace inda kika fito gantalin ki kwana da kwanaki baki kici
abinci bane acan ?
Tace kin san yanzu wata yayi nisa ba wani abin kirki ake samu ba sai maneji nace
sai ki je gaba ki nema ni banyi abinci ba yau.
Ta ce khady yaushe kika fara rowa haka ba halinki bane rowa nace ban dafa ba
nace maki ashe karyan iskanci kike yi da zaki dawo kwana da kwanaki hannu empty.
Ta dan tsaya jin ganin ban kulataba ina karatuna sai ta fice min daga dakin
dagowa nayi nabita da kallon mai kama da harara har tafice daga dakin.
Bayan ya gama saurare abinda malam sani ya gaya mashi jikin shi ne yayi sanyi
karshe yayi mai godiya tare da jaddada mashi kan kada ya fada ma Nafisa komai ya
dai saka ido ga alamarin ta kawai.
Bayan fitan shi gidan nine na fado mashi a rai wayana ya kira mun gaisa dayake
shi mai son wasa ne nan yajani da wasa wanda bai wuce hiran mijin buzuwa.
Yace gobe dai weekend ne ba shiga aji ke nan nace eh sai dai ina son zan fita
zuwa wurin wankin kai don ina son gyaran jiki gobe dai.
Yace ashe shi gyaran ma sai anje wani guri yin shi dariya yaban don irin zolayar
shi nace ana mace ba gyara ne yace kwarai kuwa har in ta san kanta.
Karfe nawa zaki ya tambaya nace wuraren goma zan tafi nasan zuwa karfe sha biyu
ko da rabi na gama yace da safe banda time da nazo na kaiki sai dai ki fada min
sallin din da kike zuwa in duba ki idan na rarage abinda nake yi.
Nace No kabarshi kawai ba wani nisa yake dashi da inda muke ba nagode yace aini
nace ki fada min ko nace beauty hair drasses na fada mai layin da yake a saman
babban titi.
Munyi sallama ina mamikin halin shi da saurin sabo irin nashi na zauna na tsefe
kaina a cikin daren nan don kada in makara in samu mutane a wurin.
Washegari da safe na shirya na isa sallon din ba wasu mutane dayawa don haka nabi
layi sai da akawanke min akai min drying din shi kafin su fara min kitso.
Ranan nasha gyara sosai na jiki daidai zan fito sai ga wayan Yusuf shigo yana
tambayana ina wurin ko wuce nace an kusa gamawa nan da minti talatin zanbar wurin .
Nakashe wayan akaci gaba da min gyara sai yaba yawan gashina da tsayi suke yi
nidai murmushi kawai nake masu ban wani dogon magana da kowa a wurin.
Sun fito daga kubuwa duban fili da sukaje gani a hanyansu na komawa gida yaga
Yusuf ya dauki hanya bai iya magana ba yana aiki a system din shi kan shi a duke
yake.
Sai dai yasan ba hanyan gida Yusuf ya nufa dasu ba aikin da yakeyi ya dauke mashi
hankali a lokacin ganin ya tsaya a bakin wani gyaran jiki na mata yasa shi dago kai
yana tambayan shi ina ne nan kuma ?
Kafin ya bashi amsa yaji yana fadi a wayan shi fito gamu a kofa idan an gama maki
nace gani tafe na fito tun fitowa na ya hango nice tafe kallon mamaki yake wa Yusuf
din.
Har na karaso bakin motar nasu sai a lokacin nasan tare suke dashi fadi yusuf ke
yi da na karaso wai wanan haduwa haka fa kanwata .
Kaike kara zuzuta yayi maganar kamar bashi ya fada ba yace ba dole ba in zuzuta
kanwata yar gidan mama wanan ai kyasa ayi karo a hanya nidai murmushi kawai nayi
mashi.
Na fara gaida su yace shigo mu sauke ki mana ba hostel zaki koma ba nace a a
nagode yayana ku tafi abinku kawai dakai dayane zan shiga amma dai ku tafi kawai.
Yace au don wanan miin buzuwan da kika gani ai bashi ke jan motar ba ko shiga
muje don ki kawai muka biyo nan fa.
Jin haka yasa na bude motar na shiga batare da na sake wani magana ba shiko sai
aikin shi yake yi kawai ana tafiya mun kai wurin wani babban shago yace don Allah
ku bani minti biyu in dawo.
Ya faka motar yafita sai mu biyu a cikin motar kowa da abinda yake yi a lokacin
sai can naji yaja tsuki yana kallon shagon na dauka dani yake yi nace dakata malam
bafa kai ka dauko ni ba da zaka ja min tsuki haka.
Da mamaki ya dago kai yana kallo yace ke dani kike nace da wani nake haka kawai
zaka kama jamin tsuki a mota da mamaki yake kallo na yace ke wata irin yarinya ce
da bata da tarbiya.
Kadai gyara maganan ka malam tarbiya ai ko makaho yasan akwaishi nan sai dai a
lalaba a gani ai ba bace marasa tarbiya suke ba.
Bai kai karshen magana ba cikin zafin nama da kunar zuciya ya juyo inda nake yace
wa kike nufi baida tarbiya cikin muryan nan nashi mai dadin saurare da yake rowan
ta.
Tsoro naji ganin irin kallon da yake bina dashi mai kama da harara ko tsana sai
nayi kasa da kaina na kasa furta komai don kwarjin da yai min a idona
Ya nuno yatsan shi daidai saitin fuska na tare da tsure ni da idanuwan shi
lumsarsu yana fadin ke in badan Yusuf da bai san ciwon kan shi ba har kucaka irin
ki ta isa ta shiga min mota na a tare dani.
Yace kallani nan ko a hanya nagan ki baki isheni kallo ba a cikin mata don banga
abin gani a wurin irin ki ba cikin dakiya da dauriya nake kallan shi ina jin
kalamin shi har cikin raina sai dai ina tara abinda zan mayar mashi ne a zuciya ta
duk da naji tsoran yanayin shi.
Yaci gaba da fadin idan baki hankali da ni ba watarana sai na balbala ki wallahi
don ni mace bata kawo min raini nace dashi.
Don Allah malam matsamin bakumayi mamaki jin haka don ba abin mamaki bane don ka
fadi hakan tunda dama kai irin maza nan ne dake raina jinsin su sai kai ido ga mata
ketere saboda zalama irin na rashin sanin ciwon kai.
Don wanan matar taka abin kyama ga jamma a da kai ka mayar mutum har kake ganin
tafi ko wace macen kasan nan dadin abin dai kaima macen kasan nan ta haife , , , ,
Fat naji yakai min bugu a baki don zafi sai da na dafe baki na ina dubawa ko
jini yake min ban san lokacin da idona ya fara fitar da hawaye ba na yun kura zan
fita daga motar yasa hannu ya danna lock mutar ta rufe kit yace kuma ki saurare ni.
Duk kika sake ganina a mota kikayi gigin shigan shi sai ya jefar dake a waje mota
ya take ki kin mutum in kashe ki in kashe bazan .
Nace ni wallahi ba banzan bace sai dai in kaine yace bakin naki bai mutu bako
yana kokarin kai hannun shi ya kamo baki na na noke kaina a kafana sai bai samu
kama bakin nawa ba.
A daidai lokacin Yusuf ya iso wurin da manyan ledoji a hannun shi yana bude motan
zai sa ganin mu haka yasa shi ya sake murmushi.
Ina jin shi nayi saurin dago kai nace mugu kawai azzalumi yace kai yaya haka may
kai mata don Allah take kuka kuma ya waigo zai kara jamin baki na noke ina son fita
a motan Yusuf ya tare ni yana fadin haba dai yaya zakaci zalun ta kuma haka ?
May tayi maka haka wai kasa ta kuka ya juya yana cewa bakin nan mai rashin kunya
na daka ido ya zaro yana cewa ka dake ta Abdul ?
Kadan ma ke nan nayi mata ai fita nake son yi ba hanya don Yusuf dake wurin yayi
rufe kofan ya zagaya ya shigo motar sai da muka fara tafiya yace ka bata hakkuri
Abdul.
Ina baya ina kuka naji ya fada mai hakan yace nace ka bata hakkuri yace wani
zanba wanan yariyar hakuri ko wa yace bakai ka zalunce ta don may bazaka bata
hakkuri ba ko kafin ka tafi da hakkin ta ne a kanka ?
Baiyi magana ba sai aikin shi dayaci gaba dayi yace wai may ya hada kune haka da
sauri nace zagina yayi na rama.
Motar ya tsaya a kofa gidajen mu na fita da sauri ya biyo ni yana kirana ban
tsaya ba wata yar gidan yaba kayan ta shigo min dasu suka tafi ban san yadda suka
karata ba.
A hankali ya shigo gidan babban falon su ya samu su hidaya da sauran yan su zaune
suna shan bakin shayin su na buzaye.
Gaisuwa sukayi bai tsaya ta kansu ba ya shige ciki bai jin dadin yadda suke cika
mashi gida a ko wani lokaci haka.
Duk da wani lokaci abin yana taba mashi zuciya ganin yanzu babu wani nashi da
yake zuwa wurin shi kamar lokacin da suke zaune kano da fati .
Yan uwan shi na yawan ziyarar su maza da mata amma tunda abin ya juye haka sai
dai kulun idan ya dawo gidan ace mai akwai bakin da suka zo daga kauyen maradi.
Dakin ya nufa ya tura kofa a hankali dakin na nan a yarda ya barshi da safe ba a
gyara shi ba in zai iya tunawa yau kwana uku ke nan bai samu lokacin da zai tsaya
ya gyara dakin ba.
Don cikin yan kwana kin nan suna zirga zirgan filin da suke son saya a kubuwa ga
kuma wanan shirin da Yusuf yake son yi a kan shi.
Rigar shi ta sama ya jefar a saman gado ya kara bin dakin da kallo ya ja tsuki
ya nufi yanyar bathroom din shi wani zarni ne ya daki hancin shi da sauri ya fito
ya nufi hanya wajen dakin.
Dakin Nafisa ya shiga don yana kyautata zoton tana ciki tunda bai ganta falo ba
kuma bai ganta a nan dakin shi ba.
Yana shiga nan ma wani tsami ya tare shi mai kama da karni karni yabi dakin da
kallo ga kaya a ko ina watse a dakin tana kwance saman godon dake tule da kayan da
bai san ko na maynene ba.
Nafisa na ganin shi tace ka dawo ashe yanzu nake tunanen ka fa a raina nace ko
ina ka shiga tunda ka fita da safe baku dawo ba.
Haushine ya kamashi yadda take kwance ta mike kafa sai kadasu take yi tana
magana kamar wata basaraka da ita.
Kallon da yake mata ne yasa ta tsargu yace Nafisa wai ke dadin may kike ji ga
kazantar nan naki ne haka don Allah dubi dakin da mutun ke rayuwa wai a cikin sa.
Kina mace kice ba zaki iya gyaran muhalin ki ba sai wasu sunyi maki wai ma ina
masu aikin da kikace kin dauka ban ga wani abinda suke a yi a gidan nan ba.
Tace Samad yan uwana ne fa ko kuma yanzu kana bakin ciki da zaman su ne a gidan
ko suyi aiki ko kada suyi zasu dai zauna anan tare dani ne ko ?
Nasan wanan munufakin kila yaka su hadiye a falo ya zuga kwanan nan sai nayi
maganin shi wallahi ni banga dalili da zai sa yayi ta shigo min gida ba haka ba
gaira ba dalili yana sa muna ido.
Ke na fada maki duk abinda zakiyi idon ki ya fita ga Yusuf don idan kikace
zakiyi kokarin raba ni dashi kan ki zakiyi wa kin dai san halina and kuma ki tashi
kije ki pulloshing din rubish din da kikayi min a bandaki tunda ba dakin ki bane.
May nayi kuma kewayawa fa kawai nayi a ciki na fito yace zaki tashi ko sai na
bata maki rai yanzu ya fadi yana dan zare mata idon shi.
Mikewa tayi da kyar tazo ta wuce shi zuwa dakin ya bita da harara ya mara mata
baya yana sa kai warin bayin ya ji har cikin dakin da sauri yafita zuwa dakin hutun
shi tare da rufo kofan da key don bai son damuwa.
Anan ya cire kayan shi ya yi wanka ya fito sallah ya gabatar ya dade zaune a
wurin yana tunanen halin Nafisa ga gida da ta cika mai da yan uwanta babu halin ya
zauna a tsararen falon shi ya sha iska a ciki.
Tsuki yaja ya mike don ya kwanta nan yaga wayan shi da ya jefar saman gadon daya
shigo dakin kafin ya kewaya dauko wayan yayi yana duba lokacin maganan Yusuf ya
fado mashi a rai.
Da yake ce mashi kabi yarinyar nan a sanun har mu cin ma manufar mu a kan hajiya
ba wai nace kaso ta bane dole a a wanan wani dama ne da muka samu zamuyi amfani
dashi.
Nomba na ya bida a wayan da ya rubuta ma tsoturburn girl ya danna kira sai ko
kiran ya shiga tunanen ya fara yi idan na dauka may zai ce min sai yaji na dauki
wayan da sallama a bakina.
Queen yar matsala yaya kika shiga gida yaya kuma ruwa i hope bai taba ki ba
dai ?
Murmushi nayi sai da yaji shi cikin zuciyar shi nace au mijin buzuwa ne a layi
lallai kana son aikin nan da zan maka ke nan ?
Yace to yaya na iya tunda Yusuf yace ke ce maganin matsalata yanzu indai har zaki
min hakan ai ya zama dole in koyi zama dake da halin ki .
Nace ashe shiyasa na samu queen din yan matsala yace idan akwai abinda yafi
queen din su kinci a baki wanan muka min.
Murmushi na sake yi nace nace nako gode da wanan sunan da aka rada min sai dai
ina ganin bada ni sunan ya dace ba yanzu ai.
Da sauri yace dawa ya dace nace kaida buzuwar matarka mana fara yar dagwas mai
gashi har baya sai dai kassh kuma gashin sai naga kamar bai samun gyaran da ya dace
dashi balle har kaji dadin shakan shi dakyau.
Ke kada fa kiga na kiraki ki nemi tozarta min matata don kin san tafi komai da
kike takama don wanan banzan dalilin na Yusuf da yakawo bashi ne zai sa ki samu
daman fada min maganan banza ba.
Wanan kuma fadi kayi mijin buzuwa don yanzun haka ma nasan tunanen yar asaline
ya hana ka shakat sai da ka kirani kaji yaya nake sai dai kana tsoron buzuwar ka
nasan ma yanzu haka wani wuri ka samu ka labe kake wanan waya dani.
Idiout stupied girl kawai ya fada ya ja tsuki ya kashe wayan yana huci wai may
yarinyar nan take takama dashi ne wai zuciyar shi tace kyau ilimi tsabta da fadin
gaskiya.
Idon shi ya lumshe yana tunane sai kuma ya sake guntun murmshi a yadda yake
rigingine a kwace taba kofan da Nafisa keyi yasa shi bude idon yana jin ta har ta
soma bugun kofan bai tashi ya bude mata ba sai gyara kwanciyar shi yayi dakyau ya
fara adduan barci haka har barcin ya dauke shi yana tunane.
Wayan aminiyar ta takira cikin tashin hankali take mata bayani tana kuka wai
samad din ta yana son juya mata baya a lokaci daya .
Don ma idon ta naga ala,amarin shi ne yasa tayi saurin ganewa da wuri ta kare da
cewa na shiga uku madam tawa ta samay ne wallahi idan Samad ya fara neman mata ni
yaya zanyi.
Tace haba ki kwantar da hankalin ki tunda akwai mafita zamu iya kaishi wurin mai
rafanne yasan yadda ya lankwasa muna shi ko uwar shi indai mace ce ya dinga jin ko
ganin ta kamar jaba.
Ke dai kada ki nuna mai kin fahince shi lankwasa shi zamu a cikin ruwan sanyi
batare da wani hayaniya ba.
Wa ni tun yaushe nagama buda mai wuta wai fa satin nan har kaduna ya shiga ba
tare da sani ba kinga ke nan abubuwan sun lalace don samad bai taba shawaran zuwa
gida batare dani nabashi shawaran ya tafi ba ko shi sai idan ina da abinyi acan.
Don haka nayi mai kaca kaca kafin yatafi wai ma kin san may wanan zuwan don ki
san komai ya fara lalacewa har sayayya yayi masu da zai tafi abinda ban taba gani
ba tun zuwa na gidan nan.
Madam tace matsalan ki ke nan Nafisa baki da kwanciyan hankali idan abu yazo maki
abishi a sannu sai kinyi hargowan nan naki da kika saba ko yaushe.
Don haka yanzu ki kwanta kamar komai bai faru ba yadda muka saba ta haka zamu
fito mashi mu kara kaifin aikin mu a kansa don ba zamuyi sanyi muna kallo Samad ya
kubuce muna ba don muna samu a wurin shi sosai.
Don haka ki kwantar da hankalin ki zan shigo gidan naki sai mu tsara yadda zamu
shawo kan ala,amarin tace da ita
Madam hankalina baya kwanci don natsani in bude ido inga samad yana mu,amula koda
na aiki ko na yan uwantaka da wata mace a duniyan nan musan man matan hausawa yan
uwanshi.
Kada ki damu madam tace da ita zanzo gobe sai muyi magana a tsanake amma fa sai
kin kwantar da hankalin ki .
Ajiyan zuciya ta sauke tana fadin zanyi kokari hakan suna gama waya ta sake kiran
wata wai hajiya Auta da ke mata shige shige a kaduna.
Itama bayani tayi mata na halinda take ciki tace kada ta damu gobe zata je mata
zaria wurin malamin da take zuwa tayi mashi bayanin halinda take ciki.
Daga nan kuma gida Niger ta kira tayi ma yar ta wace ke mata shige shige acan
bayanin halin da take fuskanta daga Abdulsamad din yanzu tace kada ta damu za,a yi
komai yadda ya dace.
Sai lokacin hankalinta ya kwanta don tana ganin kamar har anyi aikin mako don ta
yi believe da aikin bokaya da malamanta sosai.
Shawaran da madam ta bata take so ta fara aiwatarwa indan ya dawo daga kadunan
inda take sa ran dawowan shi yau din don tasan ba zai wuce kwana daya ba can tunda
ba tare suka tafi ba.
Nikan nace Abdulsamad da sauran mazan dake cikin irin halin nan sun shiga uku ga
matan su ruwan sha surukule abinci ma haka wurin kwanciya ma hakane Allah ya tsare
ya kare ya shirya zukantan mu.
Baidawo ba ranan kamar yadda tayi tsamani abinda ya kara tayar mata da hankali
ke nan ta kwana a cikin tashin hankali da damuwa.
Yana gurfane a gaban hajiya mama yana mata sallama zasu tafi inda take zaune
akan kujera falon ta .
Akwai wani nauyi da kawaici dake tsakanin shi da mahaifiyar tashi tun farko
kansancewar shi dan fari a gurin ta ba wani sakewa ko shakuwa mai yawa a tsakanin
su tun farko don kawaici.
Ya dubeta sanan ya sunkuyar da kanshi tare da fadin hajiya mu zamu koma ke nan ta
dan dubeshi ta kawar da kai gefe tace.
Allah ya kai lafiya mun gode da hindiman da akaimu Allah ya karams dukiya albarka
cikin sauri suke hada baki da Yusuf wurin cewa amin hajiya mungode.
Sai dai kuma rufe bakin su yayi daidai da cewan ta yaya zancen iyali ka kuma har
yanzu bamuji shawaran da ka yanke a kai ba kai suka dukar kasa gaba dayan su don
basu zaci hajiya zata kawo wanan zancen ba a yanzu.
Taci gaba da fadin babangida kayiwa yarinyar nan adalci da diyan ka don ko sune
ne jigon ka watarana kana ganin wanan abinda ka dauko na tallaban wata wace ko
haihuwa bakuyi da ita ba zai haifa maka da mai ido gobe.
Yaran nan fa girma suke yi yanzu idan har suka san abinda kake yi ma uwar su kana
ganin abin ba zai shafe ruwan ka ba wataran.
Yusuf ne ya kawar da shirun dakin bayan hajiya ta gama magana yace hajiya a
dan bamu lokaci kadan don Allah akwai shirin da muke yi komai zai zama daidai bada
dadewa ba da yardan Allah.
Sai dai a taya mu da addua da rokon Allah wanda shi muke bukata gare ku yanzu
amma nan gaba kowa zai dara in Allah ya yarda.
Allah ya yarda tace dashi bata kara magana ba suka mike suna fadin zasu tafi ta
bisu da addua wanda yasa zuciyar shi jin kamar an gafarta mashi a lokacin.
Abinda ya dade bai samu ba daga gare ta idan yazo da fada sukan rabu a gidan
rayuka sukan baci sosai.
Tunda suka kama hanya ba wanda ya iya magana a cikin su kowa da abinda yake
tunane aranshi saida sukai nisa Yusuf yace wanan abin yayi min dadi matuka.
Yau hajiya ta rakamu da addua tare da fatan alheri a gare mu abinda ta dade batai
muna fatan alheri da sakin fuskan da muka samu gareta ba irin yau.
Murmushi yayi tare da kwantar da kan shi saman widow motar yana lumshe idon shi
cikin jin wani irin yanayi a jikin shi.
Har suka iso Abuja kamar bai cikin motar gida ya wuce dashi direct inda ya samu
gidan kamar yadda ya barshi Nafisa ce da yan uwanta suke yadda suke so su kadai a
gidan babu kowa nashi a ciki.
Bayan sun gaisa ne ya haura zuwa sama dakin shi ya fara rage kayan jikin shi don
ya dan watsa ruwa ya kwanta ya dauki lokaci a bayin kafin ya fito ya fara saka wasu
kaya masu sauki a jikin shi don ya sha iska.
Yana saka kayan Nafisa ta shigo dakin bako sallama tana cewa kun dawo ashe yadan
juyo ya kalleta ya mayar da hankali ga abinda yake yi din.
Ba laifi yau ta sa kaya masu dan kyau a jikin ta da alama kila tafita ne ko zata
fita din don idan ba fita zatayi ba ita kwalliya bai damay ta ba haka take zama a
gida ga kaya nan kamar ya kashe ta kuma bata kyauta wasan dadi.
Cike da sallo ta karaso gare shi ta amshi dan tawul din da yake tsane jiki dashi
tana goge mai kai tare da fadin kaje gida hankalin ka ya kwanta ke nan ?
Bai mata magana ba haka kuma bai saki fuskan shi ba har lokacin tace nayi
mamakin zuwan ka gida a wanan lokacin bayan ba haka muka saba zuwa ba.
Yace banda daman zuwa ganin mahaifana sai mun tsara dake ko may ba haka nake
nufi ba gani nayi ya kamata ace nasan da zuwan ka tun wuri ai.
Sai da ya soma tafiya yace yanzu na canza sallon tafiya ne ba dole bane sai naje
dake indan zan tafi don kema idan zaki gida ba binki nakeyi ba ai.
Cikin yanayi mamaki tasha gaban shi tace may kake nufi da fadin ka canza tsarin
ka yanzu yace komai ma don na fahinci baki kaunar yan uwana yanzu da ci gabana.
Na fahinci sakin fuskan da nake maki ne ya jawo min abubuwa da dama daga gare ki
na koma nine mata kece miji a yanzu gidan nan.
Don zan tafi wurin iyayyena har kike tayar da jijiyoyin wuya wai jayi masu
sayayya ke nawa nake baki idan tafiya gida ya kama ki.
Kuka ta sa mashi wai yayi mata gori kan abinda yake mata ita da iyayyen ta kallon
ta kawai yayi ya fara kakabe gadon shi inda yake son ya kwanta cikin kuna rai.
Ta dawo bakin gadon bayan ya gama kakabewa ya kwanta ta zauna a bakin gadon
tashi gaba tana kukan munafunci.
Sai da kukan ya ishe ne ya juyo gare ta yana fadin kukan ya isheni hakana in
zaki gyara ki gyara dan gaba tace haba Samad may kake nufi da maganan da ka fada
min.
Kana nufin ina hanaka yiwa yan uwanka alheri ke nan yace baki hanawa kikayi bakin
ciki ga abinda zan dan kai masu a gaban kowa.
Tace kowa su wa baidai Yusuf bane gurin da sauran drivobin ka yace su ba mutane
bane komai tace to kayi hakkuri haka ba zai sake faruwa ba insha Allahu.
Nasan ban kyauta raina ne ya baci a lokacin bayin kaina bane ka sani son kane ya
rufe min zuciya na.
Yadan dubeta yace don kina sona sai ki hanani yima iyayyena da iyalina alheri ko
may kai min afuwa ba zan sake ba tana fitar da hawaye gwanin ban tausayi.
Nace naji ya wuce kuma kada ki sake yi min haka don ranki zai baci dani idan kin
sake ina son in kwanta in huta ne haka yasa ta mike ta fita jiki a sabule da ita.
Mamaki take a zuciyar ta yau ita Samad ke da bakin fada mata haka da bakin shi
babu shayi ko tsoron da yake gwada mata.
Tace zaka san koni waye idan na kulleka a wuri daya a karkshin ikona ba yan
uwanka ba har iyayyenka da iyalin ka sai abinda nace maka a kan su.
Kwantawa yayi don ya huta amma ya kasa samun sukuni a lokacin saboda damuwa
dayayi mashi yawa ga tunanen zuwa ya duba khadija ya damay shi ga kuma Nafisa da ta
fita tana kuka yanzu a dakin.
Mun gama exam na dawo hostel tun jiya da na shigo ba fita ko kofan gida ba ina
jin ya gidan nata parkin suna fita daya bayan daya a gidan.
Kwaciya na gyara ina jan tsoki haka kawai an tsayar dani don wani bukatan da ban
sani ba an bata min lokaci na ga banza.
Da yanzu ina gida don tun da yamman jiya naso wucewa tunda ba wanj mugun nisa ke
ga Abuja zuwa minna ba ko goma na dare zan iya tafiya gida idan na so.
Wayana yayi tsuwa ban yi saurin dagawa ba sai da na lalabo na dauka naga ya
Aminace take kirana a lokacin .
Dauka nayi ina mata sallama bayan mun gaisa da ita ne take tambaya na kama hanya
karya nayi mata nace ban gama ba sai gobe zan gama sai in tafi tace Allah ya kaimu.
Na tambaye ta ina su boy yaron ta tace sun shiga wurin mommy ta aike su can.
Nace ke dai da mommy sai Allah anty tace suna da kirkine mutanen akwaisu da so
jamma,a sosai wallahi.
Dan murmushi nayi kawai tace ah ai na manta in fada maki mutumin ki fa yazo gida
ya kawo wa iyayyen shi da matar shi alheri da yan uwa kowa yana ta mamakin sauyi da
aka gani a gare shi.
Nace ah haba dai don Allah tace wallahi baki ga irin alherin da ya kawo masu bane
khadija nima da na shiga gidan mommy take nuna min .
Nace shidai ya sani ai kila buzuwan matar shi ta barshi ya kawo masu ne tace bai
ma zo da ita ba ai shika dai yazo wanan karon.
Nace kila shiyasa ya samu kawo masu alheri tace waya sani khadija Allah dai ya
kyau ni ba kishiya nake gudu ba irin wa yan nan matan dake juye kan miji a lokaci
daya ka rasa gane kan mijinka ne abin tsoro ai.
Nace da sauri No no ya Amina don Allah kada ki hada yaya da wanan mutumin don ba
halin su daya ba ma tace saboda may shima ba namiji bane irin sa nace na fada maki
ba daya suke ba ya Amina.
Tace Allah ya sauwaka nace amin tare da kawar da zancen nace idan naje gida may
zance ma daddy tace nima ai zanzo kafin ku koma school idan anty hauwa ta haifu.
Don ina ganin tun last month ake sa ran haihuwan ta gata ta wuce lokacin ta nace
ashe cikin ya tsufa haka ne muna gida zata haihu ke nan tace insha Allahu.
Mun gama waya mun kashe na ci gaba da tunanen hiran mu da ya Amina din murmushi
nayi nace baki san komai ba yar uwa.
Zaki sha mamaki idan kin san nice mai shirya wanan plain din haka murmushi na
dan sake nace ashe nima shu,umar kaina ne ban sani ba.
Kiran Yusuf ne ya shigo min yana tambayan ina ina nace hostel a takaice yace
akwai mutane ne nace akwai su amma kadan yace gashi nan zuwa yanzu sai kazo nace
dashi ya kashe wayan.
Maryam ta dawo daga wurin gyaran kai ta samay ni akwace take fadin ai na dauka
barci kike yi nace na fara ya Amina ta tayar dani ga waya.
Nan nake bata labari hiran ya Amina dani tayi dariya tana bude tukuyan abincin
mu tace bata san ke ce mai director ba yanzu na zuciyar shi.
Da sauri nace zuciyar shi fa kikace tace uhumm wai ke baki sani ba idan baso a
tsakanin ku kina nufin zai ko kalle ki ne ma.
Shiru nayi ban bata amsa ba sai da ta zauna nace wai ke da tunanen ki ke nan akai
mu tace bani ba kowa ma saboda kun dace dashi.
Nace baki ji ba ke nan don babu ta ida muka dace dashi wallahi ni ina ni ina
wanan miskilin mara dariya da fara,a.
Zaiyi dariya wata rana sai kinyi mamaki zakice nace maki watarana amma fa idan
kinyi nasaran canza shi din don kan ki ne zaki taimaka ba wani ba.
Nace a a gyara maganan ki dai maryam don ba gaskiya zuciyar ki take fada maki ba
tayi murmushi ta soma cin abincin ta.
Yusuf ya kirani yace fito gani a waje ban bata lokaci ba na mike saboda na matsu
inji abinda yasa suka tsayar dani garin har wanan lokaci.
Dan simple makeup nayi na fito a can nesa da mu na hango motar su a fake na
karasa inda yake da sallama na gareshi.
Na gama shiga da komai daki na da taimakon wata yar gidan namu da ta dawo tagan
ni da kaya ta tsaya taimaka min.
Kayan jikina na fara cirewa san nan na fara gyara kayan ina aje komai a inda nake
bukatan shi na gama na zauna ina tunane a raina.
Bakomai nake tunane ba sai mijin buzuwa da Allah ya jefo a rayuwana a dan lokaci
ya taimaka min yau gani da kudi a hannu na wanda yakai dubu dari ta dalilin mijin
buxuwa da iyayyen shi duk na samay su.
Waya na dako a cikin handbag dina ina neman layin ya Amina don in fada mata
abinda ya faru don komai ya faru dama nakan kirata in fada mata.
Kira uku ta daga wayan ina ji bata kusa da wayan ne a lokacin mun gaisa nake
tambayan yaranta tace suna lafiya sun tafi islamiya.
Nace anty kin san wani abu da ya faru yau tace ina zan sani Khady nidake kaduna
zaune kina abuja ke.
Nace anty yau na hadu da mijin buzuwa danaje sayayya tace kun sake haduwa kuma
again nace wallahi anty wai duk wanan uban kayan da na sawo nazo biya sai ake ce
min ai ya biya bayan da suka sauke ni ranan ya ba driver dubu hamsim ya bani.
Kai da gaske khadija nace wallahi anty kuma su suka kaini gida sai dai shi bai
so su dauke ni ba sai abukin shi ne yace saboda mama ne suke min haka.
Dariya tayi tace to Allah ya saka da alheri ki dai bi a hankali inda duk kuka
hadu don buzuwan nan ba imani ke gare ta tana iya komai akan mijin ta.
Ya Amina ni inama zan kara ganin shi kuma Allah dai ya tsaga rabona daga Aljihun
shi wanan karon mutumin da ko yaushe take a cikin hade fuska banda gaisuwa may zai
hada ni dashi kuma.
Daga haka muka kawar da zancen shi muka dauko na iyayyen take fada min cewa sunyi
waya da baba yana fada mata kudin su na ritaya ya kusa fitowa kwanan nan.
Ihun jin dadi nayi don murnan iyayyen mu zasu fita acikin hali talaucin da suka
shiga na ritayan da mahaifin namu yayi muke cikin halin kaka nakayi.
Tace ai zan riga ki ji idan kudin sun sauka don haka sai abinda kika samu daga
baya nace ai ni indai daddy zai samu bukata na ya biya ke nan.
Yanzun ma shawara nakeyi inje banki gobe in tura mai kudin da mijin buzuwa ya
bani don akwai kudaden da zasu isheni a hannu na tunda ina da abinci waddatace .
Tace haka akeso mutum idan ya samu ya tuna da iyayyen shi dama dako kin kyauta
wallahi dama sallaman ki ya hanani tura mashi kudi wanan watan.
Haka dai mukai ta hira da ita daga karshe mukayi sallama na kashe wayan tare da
mikewa na jona electric dina don in dafa dan abinda zanci da dare.
Kira, a na saka a wayana ina aiki ina bin kira a don ni gwanace a wurin iya
hadda tun ina yar shekara sha hudu na sauke alkurani mai girma na sake maimaitawa
yakai kashi uku yanzu don duk wanda yasan yaran minna ya sansu da ibada da kamun
kai ga girmama na gaba dasu a duk inda suke.
Da wanan halin namu nake shiga ran mutane farat daya kowa tsakani na dashi
gaisuwa ne na mutunci da sani girman wanda ya girmay mun.
Na gama na zuba a plate na dauko ledan ruwa guda cikin wanda na sayo na aje a
dakin na zauna don in fara cin abincin sai ga kiran waya ya shigo min.
Binta ce ta kirani a lokacin na dauka kafin wayan ya tsunke hiran mukayi sosai
ranan da ita har nake mamakin ko nawa ta sa awayan ta haka don da mun sake wanan
hiran take dauko min wani.
Har take fada min yadda akayi ranan da zamu wuto da buzuwar yayan su tace bazata
shiga mota dani ba mama ta dage daya zo mata da maganan kan lalai sai sun tafi
dani.
Nace kin ko ga tunda muka kama hanya batai min magana ba nima ban masu ba daga
ita har mijin ta.
Tace wanan ai dama shi miskili ne magana kamar aiki yake ganin sa a gare shi zai
iya zama da kai kuyi awa daya baice uffan ba haka kuma matar shi anty fati itama
take shiru shiru bata magana.
Nace aiyanzu sun samu mai magana a tsakanin su haka yasa ta samu daman musguna
mata yadda take so ai.
Tace ke kin ko san halin wanan matar shu,uma ce wallahi ta karshi da farko da
tazo boye halin ta tayi kamar wata mutumiyar kwarai da ita.
Sai daga bayane ta fitar da kalar ta kowa ya sani bata kaunan ko dan uwan yaya ta
ganshi a gidan nan wallahi.
Nace wuri ta samu wallahi ni kar nake kallon ta don banga abin tsoro ba anan ku
dai na fahince ku kuna bata girma ne don mijin ta yana da hali a cikin ku.
Tace ga tsiya nace eh mana haka din ne amma in bashi ba ta yaya zaku zauna wanan
matar ta dinga raina maku hakali har tace wai idan tana wuri kada ayi dariya .
Tace ina ma kika sani khadija ai sai wani lokaci da mukaje hutu wurin su a abuja
ba girma muka dawo gida kwanan mu biyar ko sati bamu kai ba matsi yai muna yawa a
gidan.
Muka matsa ma yaya zamu dawo ga yan uwanta nan muna ganin yadda take ji dasu amma
mu ko falo ta hana mu fito muka koma kamar wasu bare ba yan uwan maigidan ba.
Dariya nake mata sosai tace Allah ko magana mai karfi wai ba ai mata a gida tace
ba kallo ba komai sai zagi da hattara ga anty Fati damu da ita duk muka koma daya.
Bayan mun dawo sai ga anty Fati ma ta dawo wai a kaduna zata zauna bata iya zama
da buzuwa a abuja bata bari ko miji ta gani idan yana gida.
Nace ke ki bari don Allah ashe ba karamar shuuma bace tace baki santa bane Khady
wanan fa ko kashe mutu tana iyawa fa.
Nace wanda Allah yabata ikon kashewa ba wani kan ai yafi karfin ta wallahi ba
abinda zata iya wanda Allah bai tashi yi da bawan shi ba.
Ni don Allah har kin ban haushi da wanan maganan naki don ba a gidan ku nake ba
wallahi da taga tsiya a guri na nifa irin matan barikin nan haushi irin su nake ji.
Zako kiji nata don bata da hali mai kyau ko kadan akan mijin ta zata iya yiwa
mutum komai musan man ma ce ko waya tayi da wata ranan sai sunyi jidali sosai da
ita ke ta zama mai kaya ko shi yanzu bai da yadda zaiyi da ita ne kawai wallahi.
Nace ya dai ga dama ne Binta idan ka ganshi ga mutum har mutum amma baida kuzari
gun mace tir yayan ku ya zama mijin hajiya wallahi.
Haushin abinda na fadi taji da fada muka karasa wayan a rana na kashe ina mata
dariyan shakiyanci na gama na wanke kayan na samu wuri na kwanta.
Washe gari da wuri na fita don ban yarda in makara in ba wani dalili ya tsayar
dani ba mai karfi shi kadai zai sani makara kawai.
Ban da yawan kawaye sai mutum biyu yan department din mu kosu shirin mu dasu don
sun ga nafisu kawo wuta sosai a class din shine likewan su dani.
Banda wasa ga abinda ya kaini abujan daga school sai gidan mu sai ko idan wani
dalili zai sa na fita a ranan zan fita.
Yau ya dawo a gajiye don daga wurin aiki ya wuce wuri wasan polo da suke yi don
dan wasan ni ne sosai wanda yana daya daga cikin abinda ke kawo mashi kudi a
lokacin bai dogara ga aikin shi ba yana buga buga irin na maza gida da waje shike
sa yana samun mahaukacin kudin da yake riko.
Wanka yayi yana saka kaya a jikin shi ta shigo dakin dan juyawa yayi ya kalle ta
ya kawar da kan shi yaci gaba da abinda yake yi.
Karaso wa tayi gare shi tana wani rangaji na daukan hankalin shi ta sake abinda
yake so ya sauko mata har mazaunan ta.
Cike da sallo ta iso gare shi sai dai tsiyan shi da ita duk gayun ta bata damu
da saka kamshi ba kuma har yanzu ba gwanewa tayi ba da iya kwalliya shine ma yake
kokarin wurin gyara mata idan tayi wani kwaliyan zasu fita.
Gata da son karya sai dai ko bokon kasar su bata samu ba kuma babu na Allah a
tare da ita abin ya taru yai mata yawa amma hakan bai hana shi son abin shi ba.
Rungumoshi tayi ta bayan shi ya sauke wani ajiyan zuciya yana dan murmushin jin
dadin ganin ta tace yau ina ka shige haka ne ta dawo ta gaban shi suna fuskantar
juna.
Bai ce komai ba yadan jajeyeta ya dauko turare yana fesa ma jikin shi tace har
da daren ma sai an feshe jiki da turare ko fita zakayi ne haka ?
Sai lokacin yayi magana yace sai zan fita ne zan saka kamshi a jiki na ke baki
son kamshine ashe yasa baki sakawa .
Taji zafin maganan amma ta daure don in da sabo ta saba da gorin saka kamshin da
yake mata din ko yaushe kuma hakan bai sa ta saba da sakawa ba.
Tace muje kaci abinci yace na koshi ta dubeshi da sauri tace tare da fadin ban
gane ba yace mun ci abinci da Yusuf kafin in dawo.
Juyawa yayi ya nufi saman gadon su yana jawo laptop din shi tasan idan ya fara
dakilan laptop sai ranta ya baci kafin ya gama.
Idan tayi magana kuma yace business yake a ciki shi ko wani abin dariya tayi ya
dago yana duban ta na lafiyan ki kalau kuwa ?
Sai yaji tace maganan turaren da kayi ne dai yaban dariya har na tuna da yarinyar
da mama ta saka mu dauko ranan.
Bakaji wani irin kamshi tiraren da takeyi ba kamar tayi wanka dashi yace tasan
kan ta ne yasa ta saka turaren haka don kada a raina ta.
Tace shi saka turare kuma har wani sanin kai ne dashi wai ma may ye alakan ta da
mama ne data nace sai mu dauko ta wai ?
Yana bude laptop din yace sai yanzu kike son jin halakan su da mama da kishi ya
rufe maki ido baki tsaya tambayan ta ba da farko.
Tace kayi hakkuri cikin yanayin tausasa harshe tace nasan ban kyauta ba kishin
ganin ka kusa da wata mace nakeyi tundai irin wanan yarinyar dake cikin ganuwan
kurciyan ta ga kyau kuma da gani tana kuri da ilimin ta.
Ina tsoron ka hango kyawon tane wallahi kazo kace zaka dauko min ita a gidan nan
wata rana son ka nake har karshen zuciya ta ka sani.
Ya tsaya yana mata wani irin kallo yace don kina kishina sai ki min hauka mata
nawa nake gani a rana da ina raayin mata ne zaki san lokacin da zan nemay su ne.
Har kina fada min cewa mahaifiya ta da biyu ta hadamu tafiya da yarinyar don in
so ta kika haukace har kina fashe fashe a gida.
Kwantowa tayi a jikin shi ta dan shafi kan shi tace kai min afuwa don Allah haka
ba zai sake faruwa ba a tsakanin mu.
Yaji hakkurin da ta bashi har cikin ranshi yace ki rage kishin nan nake don ni
din mijin mace hudu ne watarana.
Da sauri ta rufe mai baki tana fadin don Allah ka daina fadin haka don kana sa
zuciya ta tana bugawa da wanan zancen kishiyar da kake min.
Yace idan lokaci yayi ai yi zanyi sai dai ki tausasa zuciyar nan naki bakiga
mahaifina matan shi hudu ba kin sani ko in gado shi nima ?
Kuka ta soma mashi tana fitar da hawayen munafunci a idon ta dariya yayi mata
yace akan kishiya kike wanan kukan haka fati fa ba kishiyar ki bace kin ga ai ko
yanzu kina da ita ke nan.
A bar maganan Fati tace don ni kaina ma kunya nakeji ace wai ita din kishiya ta
ce balle kai ace matar ka ce Fati ta sunna.
Ohh kin fison indan zai ne ma yanzu in nemo wace idon ta ya bude sosai don itace
ta dace dani tace ba haka nake nufi ba don Allah mu bar zancen kishiyan nan haka
na.
Tambayan ka nayi cewa wacece wanan yarinyar ne sai ka dauko min wani dogon zance
kuma akan kishiya ?
Yace nima ban san ta ba a gurin mama wanan zuwan da nayi na fara gani ta koma
waye dai ita nasan alakar ta da mama mai muhinmaci ne sosai.
Shiru tayi tana nazarin maganan shi daga karshe dai data ga ya fara aikin shi ta
kwanta tana ci gaba da tunane kala kala a zuciyar ta.
Dakin shi ya nufa ya fara cire kayan shi zuciyar shi yana mai soya yana jin kamar
ya ganin a gaban shi ya shake ni don haushi da takaicina da yake ji.
Nafisa ce tazo dakin har lokacin a hasale take daidai ya fito daga wanka ta yi
mai wani mugun kallo tace yau sai ka fada min gurin wace kaje har ta dauki wayan ka
ta kirani dashi.
Baiyi magana ba sai kokarin saka jallabiyan da yake yi a jikin shi ta karaso
tana ce mai wata yar iska yar kasada ke son shiga rayuwan ka Samad ?
Ido kawai ya tsura mata yana kallon ta batare da yayi mata magana ba ta sake
maimaita tambayan shi samad ka fada min wa cece kaje wurin ta har ta dauki wayan ka
?
Ta karaso tana rike mai kwalar dogon rigan da ya a jikin shi yanzu kama hannuwan
nata yayi ya murde ya wurgata saman goda ya nufi inda turaren shi suke ya dauko
yana fesawa jikin shi.
Ta kara juyowa ta nufo shi a hasale tana cewa kunji kun gama iskancin ku shine ka
dawo gidana kana min wankan tsarki anan.
Da mamaki yake kallon ta ya bude baki da kyar yace Nafisa yau ni kike wa zargin
aikata zina da wata kace tace dole in maka samad may ye hadin ka da wata mace , ?
Yace dani mazanaci da akan ki zan fara tunda dashi kika gabatar min da soyayyan
ki farkon haduwan mu dake.
Haushin maganan shi taji sai ko ta haushi da duka da yakusa tana ture shi tsayawa
yayi yana kallon ta da mamaki.
Jayeta ya kara yi ya hakadata gefe ya fice daga dakin ta biyo shi tana zagi ta
uwa ta uba ya shige dayan dakin ya kyale ta.
Yana shiga wayan shi na kara ya dauka Yusuf ne yake son fada mashi ya gama tsara
masu tafiyan da zasuyi kaduna.
Yace sai dai abinda zamu saya wa yaran nake son mu dauko khadija ta zaba muna
abinda ya dace dasu tunda mu ba zaben kayan yara muka iya ba.
Yusuf ya ambaci sunan shi a kasalance Yusuf din ya amsa mai yace don Allah ka
rabani da wanan yarinyar dake batun tarwatsa min gida da rayuwa na.
Cikin mamaki Yusuf din yace tayi ma wani abune kuma ban sani ba yace may ne ma
batai min ba yanzun haka in ka saurara zaka iya jiyo hargowan Nafisa akan khadija.
Da sauri Yusuf din yace dashi kai haba sun hadu ne komai ko ta samu labarin
khadija din ne yace basu hadu ba sai dai yau kaddara ya hadasu a wayana.
Nan ya koro mai abinda ya faru yau din dariya sosai Yusuf ya kwashe dashi lokaci
guda yace kai khadija akwai jan magana da rashin tsoro.
Yace ni yau taja min masifa da fushin Nafisa a gidan nan ban son wanan bakin
kishin na Nafisa wallahi idan ya tashi bataji bata gani imagine wai har ni Nafisa
ke ma zargin zina yau.
Intrested ashe yau tasan zaka iya kara aure ko wani lokaci ke nan wow i am
impress da jin wanan labarin Allah yasa haka yasa ta fara gyara halin ta.
Rikici kake son jawo min Yusuf da ka hada ni wanan aljanan yarinyar mai shegen
rigima wai dole sai itace zatai min wanan aikin ne ?
Kana son mu canza wata ce ya tambaya shi a cikin gatse yace No da sauri yace ta
faye matsala ne wallahi.
Yace da matsalan nata za a gyara komai kai dai ka kara hakuri don Allah yace
wallahi yarinyar ta fara shiga raina amma kuma ta faye matsala ne ai.
Yanzu yaya zan iya shawo kan Nafisa a gidan nan gaba daya ta birkice min yau kan
kishin wace ma bata sani ba har da duka na fa takeyi.
Duka kuma subbahanallahi kai kuma sai kai tsaye tana dukan ka ko mai yace to may
zan mata Yusuf kit Yusuf din ya kashe waya alaman yaji haushin maganan abokin
nashi.
Dariya ya soma yi bayan ya kashe ma Samad waya yace komai na zuwa yadda nake so
da alama samad ya fara son khadija.
Wayana ya kira bayan mun gaisa yake tambayana ashe yau mutumin yazo gurin ki shi
kadai nace eh dan matsalan yazo min wai bashi da lafiya.
Sai bayan na taimaka mai da magani yaji sauki ya soma karanta min haukan shi wai
na fita mai a motar shi tunbai balbalani ba.
Dariya yayi yace may ya hada ku har haka nace bakin rigima na yasani daukar mai
wayan matarshi da take neman shi ganin kamar barci yake wayan nata ruri nikuma sai
na dauka.
Dariya yayi sosai a lokacin yace aiko nasan yau suna can suna tafka fitina a
tsakanin su kin ja mashi aiki yau
Nace shi ta sha matsoracin namiji kawai wanan ma ko ga maza yan uwan shi nasan
matsoracine wallahi dariya Yusuf yayi sosai.
Yace to yanzu na kiraki ne don Allah gobe indan kina free zaki taimaka muna da
sayen kayan yaran samad don Friday zamu shiga kaduna insha Allahu.
Nace idan dashi ne gaskiya ba zan tafi ba yace saboda may khadija kefa kika kawo
wanan idea din zaki ce kuma bazaki tafi ba.
Ki daure ki karasa ladan ki don Allah ai ba don shi zakiyi ba yaran fa kika dauki
alkawarin taimakawa saboda Allah shiru nayi yace may kikace nace a hankali naji sai
dai idan ya wuce gobe ba zan samu fita ba don ina da exam talata kuma zan wuce
gida.
Yace nagode khadija Allah ya biyaki da alherin sa yadda kike muna Allah ne kadai
zai saka miki sai mun hadu goben zamuyi magana Allah ya kai mu nace dashi.
Na kwanta cike da tunane a raina wai dama da gaske akwai mazan da suke irin
wanan rayuwan a gidajen su don dai ni nasan mahaifin mu zaki ne a gidan shi akan
iyalin shi.
Wai duk gidajen masu kudi haka yake ne rayuwan su sai mata ke juya su yadda suka
ga dama idan ka gansu awaje sai kai masu kallon isa da izza amma a gidajen su sai
ka raina su.
Yaya matashi kamar Samad zai zauna mace tana juya shi haka yadda take so wai
kuma yana sunan miji a gidan shi gashi da ilimi daya dace yayi amfani dashi ako ina
ya kama amma mace ta na juya shi son ranta.
Kwafa nayi nace wallahi gobe zasu ga tsiya don sayayya zanyi masu kamar na hauka
inta gani ta haukace da tushe.
Washe gari nace ma maryam ta shirya zamu fita da su yaya Samad zasu zo mu muyi
wa iyalin shi sayayya tace tau da murnan ta.
Mun shirya tsab don Yusuf ya bugo min waya suna kan hanya zuwa wani dan abu ne
ya tsayar dasu yanzu.
Sun iso wayan Yusuf ya shigo min gasu a kofan mu nace gamu tafe yace keda wa
khadija nace da kawata maryam zata tayani zaben kayan ne sai kun fito yace min.
Mun fito daga gidan kwanan namu na dalibai muka hango su can nesa kadan inda
suka aje motar su muka karaso wurin .
Motar Yusuf ya fito ya bude muna muka shiga ya rufe sai da muka zauna muka fara
gaida su wanda nidai kusan Yusuf kawai na gayar maryam ne tace da Samad yaya jikin
shi yace cikin daga hannu da sauki.
Sai looacin ciwon kan da yazo dashi jiya ya fado mashi a rai don fitinan da suka
kwana sunayi da Nafisa yasa ya manta da komai nashi.
Kawar ki bata magana ne Yusuf ya kawar dashirun da motar yayi a lokacin maryam
ne ta bashi amsa da fadin ai itace dai magana ya zama aiki a gare ta nikan ko aku
ya ganeni ya kauce min wurin zuba.
Ashe kuna da aiki shi yasa abin yazo maku daidai naji mamakin da kika iya zama da
wanan mai zubin yan ruwan dariya ta danyi tana cewa ashe kaima kyaunta na ruda ka
haka.
Haka take ruda maza a cikin makarantar dama wajen makarantar amma kunsan may
wai duk wanan bata ga may mata ba har yanzu ga kyau yana tafiya a banza a gurin
maza.
Tsuki yaja tare da juyowa ya dan watsa mata harara lokacin da take fadin ni
wallahi ina son ganin lucky man din zai iya sace zuciyar wanan yar kwalisan
yarinyar.
Zaki ko sha zaman jira don maza basu son zuben mace irin wanan da ko ina tabi
surar ta na rawa sun fi son mace mai natsuwa da kamala.
Yusuf yace har kin sa yau na fahinci wani abu da kika kawo wanan maganan haka
nayi real sign ba karamin kyau ki ga khadija ba da har na kasa fahintar abinda yasa
abokina yake yawan rudewa idan ya hadu da khadija ashe kyawon tane yake yawan
tsorata shi yana mata kallo mai kama da tsoro but still yanzu da yai maganan nan
sai na gane kyauta ne yake yawan ruda shi.
Da na dan shiga rudanin wanan abin amma yanzu maganan nan da kikayi yasani a
hanya watau a takaice aboki na yana rudewa idan yaga khadija sai take mashi zubin
yan ruwa idan ya kalle ta.
Tayi saurin fadin ya gano sirin da Allah ya boye ne anan ai khadija matar manya
ce wallahi duk namijin da yai saa ta kalleshi da manyan idanun nan nata yakan shiga
rudu ne ya rasa inda yake ina ga shiya take tsoron fita wallahi.
Don Allah malam idan kun gama kaja mota kakai mu inda zamu ko ka mayar damu inda
ka dauko mu zaifi ya fada batare da ya juyo gare shi ba
Yi hakkuri malam abinda na gani na fada yasin khadija ta hadu ba karya a gurin nan
kai mai dani inda ka dauko ni ya fada a dake.
Nidai nayi kamar badani suke yi ba kaina yana duke ina danna wayana dake hannu na
muna charting da zarah.
Yusuf yace karkai fushi dani abokina gaskiya muka fada anan take a deep breath
and confess khadija ta fi matan da kake gani haduwa.
Bude baki yayi ya zaro ido yana kallon yusuf da mamaki kalaman shi dayaji na
bazata yasan Yusuf ne kadai duk duniya yake iya fahintar shi lokaci daya.
Yusuf ya sake kallo shi ya dan lagabe kai tare da girgiza mashi kai yace dont
give me that look just say yes to your mind she is realy beautiful as you see.
Take ya daure fuskan shi tamau tankar bai taba dariya ba yace Yusuf kayi kuskuren
furtan hakan a gare ni don kafi kowa sanin banda lokacin yin hakan .
Nace kunyi babban kuskure Yusuf da kuke son kamanta da wanan mutum matsoraci ko
kuna zaton sakewan da nayi daku kun dauke shi da wani manufane ?
Ba so ko wani abu makamancin haka cikin zuciyana don ban taba daukan haka ba a
tsakanina dakai sai mutunci da niyar taimakon ka a zuciyata don rayuwan ka na
bukatan taimako da agaji ga wanda yasan shi.
Tsakanina daku kuma sai dangantarkar irin na zumunci na an fito wuri daya da biye
min da kukeyi da kyautatawa .
Da ka sani da baka dauki haka ba da zafi don zuciyar ka ta baka ba daidai ba me
yasa zakayi zaton soyayye zai yuyu a tsakanin mu don kana kyakyawa mai kudi maiji
da ilimi da wayewa ko may ?
To ni duk wanan nasaban naka baya burge ni don ni ina fatan samun miji ne wanda
yasan kanshi yake iya mulkata ba in mulkeshi ba ko wata tana mulkanshi.
Barin fada maka ban taba jin son ka wallahi a raina don halinka bai mun ba bai
kuma taba burgeni ba tausayi ne da fatan alheri ka shirya da iyayyen ka takowani
hali .
Don halinka da dabiar ka yanayin rayuwan da ka shiga da komai naka yana bukatan
gyara a yanzu.
Ya isa yace da karfi ya fada cikin kuna rai, yayin da maryam tunda na fara
magana take rufe min baki waina bar maganan .
Idon shi yayi mai jawur hankalin shi yana neman barin jikin shi zuciyar shi yana
son tarwatse mai yace ba laifin ki ba ne.
Yaja wani irin huci ya furzar a bakin shi yace Yusuf ka juya mu sauke su inda ka
dauko su don Allah.
Bana son inkara ganin fuskan yarinyar nan na tsane ta wallahi bana son kara
haduwa da ita a rayuwa na .
Shiko Yusuf a ranshi ya gigice da fadan mu sosai yana rayawa yaushe ne zai samu
cin ma manufar shi a kan mu yaushe zasu bar wanan halin may yasa Samad ke biye mata
suna haka kamar wasu yara kanana.
Ya zama mai dole ya shiri mu tun yanzu tun kan mu rabu a hakan ba wani ci gaba
gashi ya fara ganin hasken alamarin tun ba a je ko ina ba.
Ya zama dole ya gyara wanan abin tun anan don ba zai yarda abokin nashi yaci gaba
da zama haka ba yanzu in ya bari muka watse a hakan abin bayi ba wallahi.
Naji Yusuf din yace Khadija ba nufin abokina ke nan ba baki fahince shi bane tun
farko kin san tun jiya fa yana da haushin ki a ranshi don haka don Allah bashi
hakkuri ya huce dake haka please.
Yadan juyo yana kashe min ido sai na gane manufarshi da sauri sai da na hade
wani bakin ciki na iya furta to kayi hakkuri don Allah ban fahince ka bane na fada
a sanyaye.
Da kyau Khadija matar na tuba ko bata laifi komai rintsi ya juya gurin shi yace
kayi tsamanin jin hakan daga bakin ta yanzu a yadda tahau din nan.
Wani iri yaji yace a ranshi may yasa na kasa fahintar wanan yarinyar ne wai me
yasa na fadi wanan maganganun masu zafi gareta yanzu bayan nasan gaskiya Yusuf suka
fada.
Halinta daban ne da na sauran matan dake bina suna ribibin in so su kai tsaye
zata iya fada ma gaskiya batare da tsoron komai ba kuma ya amfane ka.
A sanyaye yace Yusuf ban san may yasa take son bata min rai ko da yaushe muka
hadu ba zan bata dama taci gaba da min yadda take so ko yaushe.
Motar ta tsaya a bakin wani plaza babba ba wanda yayi magana Yusuf ne yace
bissimila mun iso mu shiga mu fito tukun.
Fita mukayi a motan har lokacin jikina a sanyaye nake jin shi don abinda ya faru
a motan Yusuf ne yazo daidai inda nake yace khadija na gode da kika fahince ni ba
komai nace dashi cikin yake.
Muna shiga shi yana bayan mu yana tako a cikin izza da kamala maryam tazo daidai
kunne na tace dan dakata mai ku jera mana.
Hara na aika mata nace sai dai ya mutu idan sai na jera dashi din ya dai ci
albarkacin Yusuf da kuma na iyayye wallahi.
Ban garen kayan yara muka nufa inda maryam ta fara duba kayan ina tayata har
lokacin ban sake ba nan muka shiga jidan ma yaran kayan sawa da sauran abubwan
yara.
Mu koma bangaren takalma da dasu sauran abin bukatan yara harda su tawul da
sabule da su kulan zuwa school muka hado dashi a hankali na taka wurin kayan mata
na zaba ma anty fati kusan kala goma masu kyau da tsada.
Su dai ido kawai suka saka min har lokacin da muka gama Yusuf yace mu zabi abinda
muke so ni wani jakka da takalma kawai na dauka maryam kuma ta dauki wani dogon
riga da jakka.
Munje gun biya muka da ja baya naga ya ciro katin shi na bakin ya basu suka debe
kudin su suka miko mai mun shiga motar mun zauna.
Yace kina ganin mun sai komai da zasu buta nace insha Allahu har maman su ma da
sauri ya juyo yadan kalle ni kamar zaiyi magana sai kuma ya fasa yusuf yaja motan
muka tafi.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
1/2/21, 7:38 AM - Xxxxx: Hutun sati uku kacal muka samu wanan karshen zangon don
haka naji dadi sosai da bai kasance dogon hutu bane don zan samu zama a minna tare
da iyayyena in yi hutu.
Wanda rabo da in samu kasancewa dasu haka a wadace har na manta yanzun haka na
fito daga zana jerabawan karshe na wanan zangon da mukayi da yazo min da rikicin
haduwa da Abdulsamad da abokin shi Yusuf.
Ba ranan zan tafi ba sai washe gari don haka maryam ta tsaya jirana don taso muje
gidan yayar ta na nuna mata ban son zuwa can din.
Komai na gama shiryawa a dakin sai kayan da zan saka ne da katifa ban samu daga
wa sama ba don kwantawa da zanyi na yau kawai da safe in dage shi sama in tafi
gida.
Bayan mun rabu dasu yusuf ya kirani yana tanbaya na ya muka isa hostel din mu
tare da kara yi min godiya .
Bayan mun kashe wayan gidan Abdulsamad suka nufa sun kusa shiga gidan ne
Abdulsamad din yace dashi idan sun tafi kada a sauke kaya da aka sayo a gidan shi
abar kayan acikin mota kawai idan sun isa Yusuf yagane manufan shi na fadin haka.
Sai dai bai ma abokin nashi magana ba gamay da abinda ya fahinta na son kada a
sauke kayan dayace kada ayi har lokacin gidan ba dadi tsakanin su da Nafisa.
Wanka ya fito yana goge ruwa akanshi ta shigo dakin har lokacin tana nan cikin
fushinta da shi zuwa tayi tambayan shi kudin da tayi requesting wana zata yi tafiya
zuwa gida.
Tace Samad kwanaki na ta matsowa har yanzu bakai magana kan abinda na bukaci ka
bani ba wanda zan je gida dashi indan zan tafi sai in wuce dashi.
Yadda take magana bai sa ya daga kai ya kalle ta ba Samad dakai fa nake magana
ya dan wuce ta zuwa bakin gado ya zauna .
Ta juyo gareshi tace magana fa nakeyi maka kana ji kuma ta fadi a hasale sai
lokacin ya dago yace kada ki kara yi min maganan nan.
Don bashi ke gaba na ba gobe kaduna zan tafi in daba iyayye da iyali na wani irin
gumzi tayi tayo kan shi tana fadin wallahi baka isa ba.
Ba kuma inda zaka kaje na fada ma don baka fada min zancen tafiya ka ba don haka
ban shirya ma tafiyan ka yanzu.
Murmushi yayi yace kice ma mai shirya min tafiyan don kece zaki sallamay ke nan
ko ?
May kake nufi da wanan maganan haka ban ci na sani bane idan za kai tafiya yanzu
koma ko da da kake fada min ni nake sa ka fada min .
Yace shine kuskuren da na aikata a baya yanzun kuma a shirye nake da na gyara
komai da ya faru ido ta zuba mai cikin firgici take.
Ganin zata damay shi yasa ya fice ya bar mata dakin don da dakin yaso ya gyara
kafin ya kwanta don ya kwana biyu ba samu tsayawa ya gyara ba.
Don yanzu gyaran dakin kwanan nashi ya dawo kan shi saboda indan yan uwan nata
sun mashi gyara sai abubuwan da dama suyi ta bacewa a dakin.
Wanan yasa ya daina bari su shiga mai daki suyi mashi gyara sai shi ya ke gyaran
dakin nashi da kanshi ya don yafi mai sauki idan bai gyara ba ita bata da lokacin
gyaran .
Haka kuma zata shigo ta kwanta a cikin dakin ba kunya ba tsoron Allah haka dai
ake rayuwan a dunkule ba wani jin dadin irin na aure tsakanin mata da miji.
Laptop din shi ya dauko ya na dubawa sai dai tunane ya hana shi yin wani aiki a
ciki bakomai yake tunane ba sai irin maganan da nake fada mai, mai kama da shagube
yana jin haushi na ashe gaskiya nake fada mashi.
Yaushe rabon shi da yaran shi suzo kusa dashi su zauna a matsayin shi na mahaifin
su suji dadi babu.
Ya tanbatar da ya tafka babban kuskure da Allah zai iya kama shi da laifin da ba
zai iya amsawa ba gobe kiyama.
Khadija khadija ya furta a hankali kin taimake kin ceci rayuwana ta yadda ban
taba zato ba wanan wace irin yarinya ce mai hikimà da basira.
Ya dade a wurin zaune har ya kai kwance sai da wayan shi yayi ringing ya daga
wani yaron shi na wurin aiki ke gaya mai an samu wasu filaye ns gwaunati a
gwagwalada da wasu mutane ke son ci.
Yace da yaron nashi ya bari sai next week za a duba case din idan Allah ya kaimu
sun gama waya kiran Yusuf ya sake shigo mai inda yake fada mai gashi a kofan gidan
shi sin dawo da motaci an gama duba su .
Yace gaya nan fito mikewa yayi ya zura santala santalan kafan shi cikin wasu
budaddun takalma ya sauko zuwa kasa inda ya samu falon cike da yan uwan Nafisa
kamar suna shawara.
Ganin yadda ya fito yasa ta dago kai tana kallon shi ya fito ya samu Yusuf din
zaune a saman dan wani dakali yana jiran fitowan shi.
Ya fito ya fara mai baiyanin komai basuyi aune ba sai ganin Nafisa sukayi a gaban
su tana huci ba bata lokaci ta shiga dura ma Yusuf din zagi tana ai banta shi.
Bai tanka ta ba sai faman kururuwa take masu a kai tana kiran da munafuki dan
bakin ciki ko bai so sai ya gansu da Samad agidan shi.
Dama tasan duk wani munafuncin da ga wurin shi yake fitowa daga shi har samad din
sai ta dauki mataki a kansu.
Amma dai karki manta bakece Allah ba ko don haka babu wani abin da zaki iya muna
sai Allah don in da sabo ya saba da wanan halin na Nafisa.
Sau da yawa idan sun kwaso rikici da mijin ta a kanshi take saukewa don tana
ganin shine mai zuga shi sai taga ta kamo shi da kyau dan lokaci kadan kuma sai
abin ya juye mata.
Wanda take ganin Yusuf din ne ke mata zagon kasa a hakan sai dai bai nasaran
rabata da Yusuf din da yake son yi ko yaushe.
Da kyat yan uwanta suka samu takoma ciki bayan sun kare masu kallon banza suka
shige da ita cikin gida tana ta haure hauren rashin mutunci.
Washe gari tun da safe ya shirya Yusuf yazo zasu tafi kamar yadda ya saba motoci
uku zasuyi tafiyan da shi sai dai wanan karon tafiyan ya canza masu sallo.
Na farko su kadai ne ba tare da buzuwa ba na biyu kuma tare da a abin arzikin da
bai saba tafiya dashi ba zasu dunfari gidan.
Ana kara gyara kaya kamar daga sama sai ganin ta sukayi a wurin motacin tana
ganin kayan ta shiga tonawa har ta gano abinda ke cikin buhuhunan da akayi siling
din su din.
Ranan sun ga masifa haka sukaja mota suka tafi ransu bace da halin da Nafisa ta
nuna masu din sun isa a cikin lokaci gari bai je gidan ba sai da ya karasa gidan
shi ya huta don sun iso kan shi yana mashi ciwo sosai saboda hayaniyar da baiso.
Tunda Yusuf ya sauke shi yanufo gidan nasu da abinda suka zo inda sai gani
motane keyi anata shiga da kaya a cikin gidan ana jibgeasu a kofan hajiya mama
kamar yadda ya umurce shi da yi.
Sun kasa boye mamakin su anty amarya ce ta fara tambaya anya wanan abin da
Nafisa ko aka zo wanan karon dariya Yusuf yayi yace bada ita bace anty muka dai
muka zo.
Mommu tace abin kan da mamaki gaskiya Allah yasa babangida ya canza daga wanan
karon dariya Yusuf yayi yace insha Allahu mommy kudai taya mu da addua.
Ya shiga dakin hajiya mama don ya gai da ita ya samay ta da yan matan ta suna
mamakin wanan sayyayan da suka gani haka wai daga gun Abdulsamad ya fito haka ?
Ya shiga dakin sai da ya zube kasa ya fara gaida ita sai faman murmushi take yi
har lokacin ta kasa boye mamakin ta bayan sun gama gaisawa dakin take tambayan shi
wanan sauyin yanan Abdul din data gani.
Yace hajiya adai taya mu da addua kusan kece sillar canzawan nan nashi lokacin
fada maki komai baiyi ba amma nan gaba insha Allahu zan sanar dake komai so nake
komai ya tafi haka yadda muke so dashi .
Don yanzu insha Allahu akwai canji sosai wallahi nan dai suka dan taba hira yace
Abdulsamad na tafe zamuyi bayananin komai idan ya shigo.
Duk da zaman lafiyan da akeyi gidan bai hana a kebe gefe ba ana gulman wanan
sabon yanayin da aka hango a gare shi.
Sai dai kowa ya matsu yaga abinda ke cikin buhuhunan wanda ba wanda ya iya gane
komau ye a cikin su su indan gaiyan aikin nasu ya shigo.
Saida suka sauko sallah jumma a ya shiga gidan iyayyen nashi a falon Alhajin su
ya fara shiga ya gaida shi da mashi yaya jiki ranan yaga sauyi sosai na sakin fuska
a wurin mahaifin nashi wanda ya dade bai gani ba.
Bayan sun gama da mahaifin nashi ne ya shiga ciki ya fara gaida ummi sai mommy
sai anty amarya ya wuce dakin hajiya mama wanda dama kullun itace karshen shiga da
yafito kuma sai ya bar gidan.
Sun gaisa da ita acikin sakin fuska ya dubi Affan dake zaune gefenta yana cin
abinci ya kira yaron saboda rashin sabon da basuyi ba dashi ya dago ya kalle shi
kawai ya gaida shi.
Sai baiji dadin yadda yaron yayi mashi ba shiru ya dan biyo dakin take tambayan
shi iyali ya amsa da duk sina lafiya hajiya tace dole ita da yan uwanta zamu
tambaye ka don sune yanzu iyalin naka.
Babangida yanzu kana ganin abinda kakeyi kana aikata daidai a rayuwanka mutum ya
watsar da iyalin shi ya rugumi wasu bare can.
Shiru yayi ya dukar da kanshi tace kaima kanka fada kada ka mutu a cikin wanan
halin kasan Allah na zai barka ba Yusuf ne yace ayi hakkuri hajiya komai zai zo
daidai in Allah ya yarda adai tayamu da addua.
Nan ya fara mata bayanin kayan da suka zo dashi inda ta fahinci komai yace saura
kayan abinci muyi magana ko za a kawo zuwa yamma sai a raba yadda ya kamata.
Yayi mamakin yadda yaji mahaifiyar tashi tana kwararo mashi addua yau da saka
mashi albarka wanda ya dade baiji ba daga gare ta duk zuwan da yake yi da fada
sukan kare ya fita rai a bace.
Yau sai gashi sanadin yarinyar da yake gani mai matsala a gare shi yaja mai samun
addua irin haka a gurin mahaifan shi bai fita gidan ba sai da yayi masu alheri
yakuma mata alkawari zai je zaria yayi masu taaziyan rashin da akayi can.
Taji dadin jin hakan sosai na ya fito ya barsu a cikin farin ciki ya koma gidan
shi don yana bukatan hutu a lokacin bayan fitar shine hajiya ta kira su mommy tana
masu bayani aka shiga bude kayan da ta nuna masu din.
Kowa yayi mamakin ganin hakan don basu zaci haka ba yanzu a gare shi sai addua
suke mashi da fatan gamawa lafiya kowa aka cire mai nasa cikin farin ciki da jin
dadi.
Tunda ya koma wake kwance a dakin shi na gidan ba abinda yake tunane sai irin
yadda na fada mai magana mai amfani acikin gatse kuma yayi mai tasiri.
Yani yace a ranshi lalai ya zama dole in san yadda zan gyara alamarina da
yarinyar nan don ita din ba abin yar wa bace .
Cikin dan lokacin kadan tayi min sanadin dawo min da farin ciki tsakani na da
iyayyen har da yan uwa wanda wanan tunanen bai taba zuwa min ba ko wani ya tsayar
dani ya fada min gaskiya yadda take fada min kai tsaye.
Tayi namijin kokari wurin ganin ta tsaya ta fada min maganna irin haka kai tsaye
bataji shakka ko nauyin fada min yadda kowa ke shayi na ba.
Wayan shi aka kira ya daga Faiza ce take mai godiyan abinda aka kawo masu yace
babu komai ta kashe kuma Lawisa yar wurin ummi ma ta kirashi tana mashi godiya haka
suka dinga kiran shi sai da yagaji ya kashe wayan shi ranan.
Wani irin farin ciki yake jin kanshi ciki mara misaltuwa da wanan kiran da yan
uwan shi suke mai a lokacin don ba zai ce ga ranan da suka kirashi karshe ba.
Ya zama dole gare shi ya san yadda ya gyara mu,amulan shi da duk wani dan uwa
nashi da ya watsar da farko.
Sai yaji yana sha, awan ya kira layin khadija a lokacin yayi mata godiya haka
yasa ya jawo wayan shi ya kira layin ta.
Ina fitowa cikin makaranta na samu guri na zauna ina jiran maryam tafito mu wuce
cikin gidajen mu don an kara muna kwana daya yanzu.
Kiran shine ya shigo min wanda tun bayan rabuwar mu ranan ban kara ji daga gare
ba sai yanzun da ya kirani din na tuna dashi.
A hasale na dauki wayan ba tare da nayi magana ba don na gane shine jin shiru ya
danyi yawa banyan na dauki wayan sai nace
A hasale nake fadin lafiya ka kirani ko ka kirane ka fada min ka tsane ni din da
kake fada min ko yaushe ?.
Murmushi naji yayi kasa kasa sai ya sake kiran suna full yace khadija a zuciye
nace ina jinka ai yace ba wanan kiran nayi maki ba yanzu.
Nace may ye ka kira malam ni kada ka bata min lokaci haushi ne ya ishe shi a
lokacin yana rayawa a ranshi yaya zai yi dani ne wai ?
Cikin sanyi murya yace min thanks khadija na gode kwarai da taimakon ki gare ni
sai dai don Allah, , , ,
Dama abinda yasa ka kirani ke nan don ka samu wani sabon yaudara ka zageni kuma
dashi na fahince ka don haka banda lokacin ka ni yanzu.
Na fadi a cikin tsigar tsokana tare da saurin kashe wayan sai dai a zahiri
jikina yayi sanyi da yadda naju yana maganan cikin wani yanayi.
Shiko ina kashe wayan yabi wayan da kallo kamar nice wayar ya sauke wani irin
ajiyan zuciya yana fadi a fili shi kadai a daki.
Wanan yarinyar ni yaya zanyi da ita ne wai ta fahince ni yanzu ya girgiza kai
yace kina da matsala khadija yarinya haka bata da kwaciyar hankalin fahinta.
Why why khadija baki so na da kwanciyan hankali a tare dani yanzu ne mikewa yayi
daga kwancen da yake ya nufi fridge ya dauko goran ruwa mai sanyi a ciki ya
kwankwada tare da wurgi da goran ya fito falon shi.
Mutane ya samu sunzo gaida shi inda ya bisu da alheri sai yamma lis ya samu suka
rage nan ya nufi bathroom din shi don ya dan watsa ma jikin shi ruwa ko zai ji
sanyi.
Dan ruwan dumi ya hada saboda yanayin garin na kaduna ya shige jacuzzi ya dan
dauki lokaci yana tunane kafin ya fito ya sa kaya a jikin shi ranan a maslcin
uguwan su yayi sallah magariba tare da jamma, an unguwa da mahaifin shi aciki.
Ba abinda yake tunane sai yadda zai samu mu shirya a tsakanin mu gashi dan
lokaci kadan yarinyar ta shiga zuciyana ta samu wuri a ciki.
Tunanin yadda zai shawo kaina amma ya kasa samun mafita har wanan lokacin
shigowan suraj soja wurin shi yasa ya matan halin da yake ciki don sun dauki lokaci
dashi suna fira kafin Yusuf ya shigo mai da abincin da mommy ta girka masu.
A tare da Suraj da Yusuf din sukaci abincin suna hira a tsakanin su bayan fitan
Suraj ne suka samu kebewa da Yusuf wanda tun bayan zuwan su basu samu zama a tare
ba.
Nan yake kara mai godiyan kokarin da yake mashi inda yake sanar dashi ya kira ni
don yai min godiya amma naki fahintar shi Yusuf din yace ya sake kirana zan fahince
a hankali.
Ba laifi yace dashi sun dan dauki lokaci sukayi sallama akan da safe zai shigo su
tafi zaria idan sun dawo yana son kuma ya dan je wurare masu muhinmanci a kaduna
daya dade bai tafi ba.
Yusuf na fita ya kira waya maryam ta dauka ta miko min bayan ta dana recieve na
dauka da sallama na kara a kunne na.
Bayan mun gaisa ne yake rokona da in karba wayan abokin shi inji may zai fada min
dariya nayi tare da fadin abokin nan naka ne ai sai a solo baida mutunci.
Yace kada kice haka Khadija baki fahince shi bane amma abokina mutumin kirki ne
wallahi ki bashi dama ku fahinci juna yanzu zai bugo waya godiya yake son yi maki
akan taimakon da kikai mashi na bashi shara kuma yabi yaji dadin shawaran ki shine
zai maki godiya akai.
Munyi sallama dashi ranan maryam tazo dakina wai a nan zata kwana saboda exam
din da zatayi washegari yana da zafi ita kuma tana son tayi karatu a daren ranan.
Muna tsaka ga karatu wayana yayi kara na daga tare da karawa a kunne na muryan
shi naji yana tambayana har yanzu baki barci bane.
Karatu mukeyi na bashi amsa yace OK dazun na kiraki in maki godiya kika kashe
waya nace ina busy ne a lokacin.
Khadija ya kira sunana amsawa nayi ciki ciki yace please ki bani dama in maki
godiya akan abinda kikai min shiru nayi na kasa magana.
Khadija kina jina nace ina jin ka mana sai naji tayi wani kasalalen murmushi
yace in tambaye ke zaki ban amsa tsakani da Allah ?
Nace sosai makuwa idan har na sani may zai sa in boye maka tunda ba rike min
baki zakayi ba.
Ajiyan zuciya naji ya sauke sai can yace may yasa kike son yawan bata min kina
son ganin hasalana ni koda ban tashi hasala ba ?
Kin tsane ni kin ki jini baki kaunar ki ganin a cikin farin ciki why khadija why
kika zabi wanan rayuwan a tsakanin mu.
Shiru nayi na kasa magana nauyin shi da kunyanshine suka kamani a lokaci daya na
rasa may zance dashi don yadda yake magana bazakace shi din bane mai izza da jiji
da kai.
Nasan kin san bawai son soyayya ne a tsakanin mu ba amma kuma kika zabi yin haka
a gare ni ki fada min may ke sakina tsana na haka da yawa.
Dan murmushi nayi tare da fadin yaya Abdulsamad ke nan ni nasan babu dingo
soyayya ma a tsakani mu tun farko sanan kuma ni ko in so ka ko da so ka ba abinda
zai ragaka dashi duk dayane a wurin ka.
Ni dama ba kai na tsana halin ka na tsana da matar ka da bata san mutucin yan
uwanka ba har hali ku ya juye iri daya da ita.
A yau in rayuka zai sauya kasan mutucin kan ka dana yan uwanka ka farga ka dawo
yadda mahaifan ka suke son ganin ka da yan uwanka ka san darajan su da mutuncin su
fiye da kowa.
Amma ni may zai sa na tsane ka kana a matsayin yayana aiko don mama zan so ka
zanyi muamula dakai kamar kowa.
Don dama ba kinka nayi bani halin ka dai na tsana bani ba kowa ma zai so ya kulla
halaka dakai ta yadda baka zata ba.
Murmushin da naji yayi yasani shiru yace khadija idan nace maki ashiri nake da in
caza yanzun zaki yarda koma in ce dake din na canza a sanadiya ki.
Jin shi kawai nakeyi ta yaya ni zan iya canza mutum kamar Abdulsamad a lokaci
daya haka.
Muryan shi naji yana fadin kina mamaki abinda na fada ne yanzu yace yes ke
khadija kin tunatar dani abinda na manta acikin abinda nake dauka shirmay kukeyi ke
da Yusuf a lokacin.
Nace ba abinda mukayi da har zai kawo sauyi gare ka haka da wuri sai dai idan
dama Allah ya kaddara tamu din abin zai fito ma.
Kuma ina mai farin ciki da jin haka idan ya kasance gaskiya ne maganar ka da sai
nafi kowa farin cikin haka a duniya.
Yace to ki fara farin ciki daga yau don ko kin sa iyayyena sun min abinda suka
dade basu min ba a yau don haka khadija ban san ta yaya zan gode maki ba da tunatar
dani da ki kayi ga abinda na manta hakki na ne yinsa a baya.
Koda da wasa ko gatse kika fada min wanan magana to ki sani your words inspired
me har nakai ga samun kalmar albarka a bakin iyayyena yau abinda na dade baji ba a
gun su.
Yau kin dawo min da farin cikin dana rasa da dadewa a tare dani kalman ki na
ranan gare ni sun sa na dawo da natsuwana.
Ya kuma fara dawo min da respect da power na ga idon mutane dana rasa a baya wa
yanda ya kamata ace komai wuya komai dadi ina tare dasu.
Ba zan iya kwantata maki dadin da naji ba yadda na kasance da yan uwana da abokai
kai har ma da makwabta na ayau suna murna da zuwa gare su.
Don haka yazama dole in gode maki please khadija kada kiki fada min gaskiya a duk
lokacin da kika ga na kauce ma hanya.
Murmushi nayi nace naji dadi kuma na tayaka murnan dawowa farin cikin ka gare ka
don ko yau ranan kace ranan farin cikin ka.
Ka kuma gode ma Allah da bai sa ranan ya kasance ranan nadamar ka bace ya fargar
dakai da wuri haka.
Allah ya kars shirya zukatan mu ni zan kashe karatu nakeyi ka tsayar dani don
gobe zamu gama exam jibi gida zamu.
Da sauri yace jibi wata rana nace talata inda Allah ya kaimu da safe zan tafi
gida don yin hutu a can.
Yace No kada ki tafi don Allah ranan ki jira in dawo akwai abinda nake son in
shirya akan tafiyan ki nace Allah sarki dama ka hutar da kan ka don ni a shirye
nake yanzun haka.
Gyaran kai da jiki mukayi na zuwa gida don haka agajiye muka shigo hostel din mu
maryam ta zauna dafa muna abinci ni wanka nashiga don zafi nake ji jikina ina ganin
yayi min dauda.
Tsab na fito nayi sallah a wirin na jawo ledan ice cream din da maryam ta sayo
muna na fara sha a hankali maryam tace wallahi ji jake kamar kada ai hutun nan da
za ayi.
Da sauri na juyo ina ce mata saboda may maryam kika fadi haka tace ban son
rabuwar mu wallahi yanzu ko ja koma gida banda wata abokiyar hira a kusa dani don
anty na ba zama takeyi ba tana da yawan tafiye tafiye kullon don ita business woman
ce .
Nace ko dai ai koya nene kyayi kewan gida mana ni banki ba yanzun haka in bude
ido in gani a cikin garin minna ma.
Tace kin ji dadin ki wallahi khadija na yarda ba jin dadi bane farin ciki don ko
dashi ne da bazan fadi haka ba farin ciki yana ga inda kake da sukunin aiwatar da
komai.
Kafin in magana wayana yayi kara na dauka kina ina nace maynene yace ki ban amsa
kada ki min halin ku na yan African don Allah .
Katambayi mutum ya mayar ma da tambaya shi kuma nace ina hostel mana yace ok
kawai ya kashe wayan shi dip bin wayan nayi da kallo nace miskilin banza kawai.
Maryam ta gama abinci wanda indomei da kwai ta dafa muna wanda yaji danyen
attarudu mai yaji a ciki zubawa tayi a plate guda ta dauko muna lemon kwali a cikin
fridge din ta wanda muke ajewa yanzu a ciki ida mun samu.
Na fara cin abincin ke nan cibi biyu kawai nayi wayana yayi ringing na duba yaya
Samad nagani a layin kamar kada in dauka dai na dauka kuma gani a kofan ku ya fada
kawai.
Kofan mu na maimaita da mamaki nace may kazo yi a nan kuma ban sani ba yace idan
zaki fito ki fito sai ya kashe wayan kawai.
Tsaki nayi na wurgar da wayan tare da fadin dan wahala kawai maryam dake zaune ta
tsura min ido tana kallo na murmushi tayi tace.
Uhm wani lucky guy din ne yazo haka ake ja mashi aji kuma abinda wasu ke nema ido
rufe a zo gurin su anzo kike wanan masifa haka ?
Nace sister kin faye bin kwakwafi wanan fa ba masoyi na bane zuwa kawai yayi ya
bata min lokaci na ina zaune kalau.
Don Allah ko may ya kawo shi kije ki saurare shi ba dadi mutum yazo wurin don ka
ka wullakanta shi haka muje in zaba maki kayan da zaki saka in maki rakiya.
Dole na mike muka tafi dakina ita da kanta ta zaba mi wani dogon riga mai ruwan
ganye da dan karamin gyale shi sai da na shirya tsab a cikin rigan tabi jikina ta
feshe da turararuka masu kamshi muka rufo kofan muka fito tare.
Yana zaune a cikin motar shi riga da wandon shadace mai guntun hannu rigar ma
iya ciya dinkin yake light green kayan su matukar karban jikin shi da dinkin .
Wurin dirkekiyar motar shi da ke fake a kofan can dan nesa kadan damu muka nufa
ko ganin maryam ya hana shi fada ban sani ba sai cewan da yayi.
Ita ko maryam tunane take a ranta ina tasan fuskan nan nashi ne ya katse mu da
cewa kin san ina waje zaki shanyani a wanan wurin naku mai kazantar tsiya haka ?
Nayi dan dariya tare da cewa cikin wayance abinda yafa da nace ga kawata maryam
tazo gaida kai don ma ita ta matsa min in fito yanzun haka.
Anyway maryam ga yayan mu Abdulsamad Abdulrahim nan ku gaisa tace dama nace kamar
nasan fuskan nan ai tace ina wuni yayan mu anzo lafiya yaya iyali.
Yace lafiya kalau yaya karatu koda yake exam kukeyi yanzu ko yana wani kauda kai
yana basarwa .
Tace karatu Alhamdullahi mun kusa cin ma karshen shi da yardan Allah ai a huta
gajiya dama nace barin zo mu gaisa ne kawai yace to na gode kwarai da alama kin fi
kawar taki kirki sosai.
Dariya tayi tace a a wallahi ai kirkin khadija na daban ne wallahi tana da kiki
matuka shiyasa ma nake jin dadin zama da ita wallahi.
Baki ya tabe ta juya ta tafi tana mashi a huta gajiya ta nufi hanyan shiga
hostel din namu sai lokacin na sauke ajiyan zuciya bayan tafiyan ta.
Katse ni yayi da fadin tsaye zaki min sai kace wanda tazo tadi da buduruwar shi
haka bude kofan motar shi yayi na zagaya na shiga sai naji ya rufe motar.
Shiru daga ni harshi ba wanda ya iya magana a lokacin sai ma gyara kwanciya yayi
a motar bansan lokacin da nace dashi baka da lafiya ne Yaya Samad.
Shiru yayi kamar baiji ni ba sai can yace may kika gani a tare da ni nace yau na
ganka so weak ne ba miskilancin nan naka yasa na gane bakajin dadi ko baka cikin
good mode.
Wai ke aljana ce ko may dazun kin fada min magana akan ahalina ya zama gaskiya
yanzu kuma waya fada maki banjin dadin jikina ?
Nace yanayin ka ya nuna min haka sai ya dago da sauri ya na kallo na nima kallon
shi nake yi sai dai ba zan iya jimirin kallon nashi ba a lokacin saboda kwarjin shi
da ya cika min fuska a lokaci daya dukar da kaina nayi kasa ina wasa da yan tsun
hannu na.
Yau ina bakin naki ya shiga nace ko don Yusuf ne dama kike da bakin a gaban shi
nace da sauri ko daya wallahi gani nayi yau kana bukatan kulawa don baka cikin
hayacin ka sosai.
Don jikina ya bani baka da lafiya sai naga ya koma ya kwanta kamar yadda yake da
farko ya fadi a kasalance cewa kaina kamar zai rabe biyu nake jin shi khadija.
Kasha magani na tambaye shi da sauri yace ban sha ba wani magani kake sha yace
panadol extra nakan sha wani lokaci.
Wayana na fara dannawa ina neman layin maryam ta dauka nace fito min da panadol
extra din nan da goran ruwa don Allah yaya Samad bai jin dadin jikin shi tace to da
sauri na kashe wayan.
Motar shiru ba a dauki lokaci ba sai ga maryam ta iso da maganin ta kwankwasa
glass din motar ya bude mata karba nayi ina mata godiya tace babu komai mana Allah
ya bashi lafiya.
Maida marfin motar nayi na rufe na fara kokarin bare mashi maganin tare da bude
goran ruwan nace mai gashi ka sha.
Ya dago kanshi da kyat ya kalleni ya kalli maganin da ruwan da nake mika mai sai
naga ya bude min bakin shi alaman in bashi da kaina .
Dan rankwafawa nayi ina saka mashi maganin a baki na kawo goran ruwan na bashi ya
hadiye da kyat yana wani lumshe idonun shi yana bata fuska.
Komawa yayi ya kwanta tare da fadin thanks nace Allah ya baka lafiya amin yace
da kyat ni dai komawa nayi na zauna na zuba mai ido.
Wasu irin jijiyoyi naga sun fito rada rada saman goshin nashi wanda ban taba
kula ko yana dasu bane dama tsoro ne ya kamani kada wani abu yazo ya samay shi fa a
nan wurina nawa ya samay ni kuma.
Shiru daga ni har shi ba wanda yayi magana a cikin mu har mintina na shudewa a
hakan suna batun zama awa daya muna nan a hakan dashi kamar mai barci.
Abu daya ne yasa hankalina dan kwantawa ganin yana numfashin shi normal a
lokacin yasa nayi shiru tare da zuba mashi ido kawai ina kallon ikon Allah.
Wayan shi dake aje a motan ne ke ringing ganin anata kira bai dauka ba yasa na
daga kiran don ba suna batare da na saurari mai magana ba nace mai wayan bai da
lafiya please.
Naji muryan mace tana fadin ke wacece da sauri ya dago ya kwace wayan a hannu na
ya katse kiran yace akan may zaki daga min waya waya baki wanan damar da ikon daga
min kira a wayana.
Zanyi magana yace get out tunda ka samu lafiya yanzu zaka iya ci min mutunci sai
dai ka sani ba zan ce ma komai a yanzu ba don yanayin da kake ciki na bukatan
natsuwa.
Get out i said na bude motar na fita ba tare da na juya na kalle shi ba naji ya
tayar da motar ya jata da karfi yabar gurin nashige ciki abina.
Dakina na shiga na wurgar da sauran maganin saman katifana na fara kokarin cire
kaya a jikina sai ga maryam ta shigo tace ashe kin dawo.
Eh ya tafi ya samu lafiya ai nace mata ina daura zanin a jikina na nike kayan na
za saman jakkunan kayana dake gefe daya a dakin.
Shiko tunda ya kama hanya yake jin wani bacin rai da bakin ciki a ranshi yana
fadin wanan aljanan yarinyar sai ta kasheni wata rana.
Yarinya yanzu ta sauke min bacin raina yanzu kuma ta kara sakani a wani anya ma
mutnce kuwa dai , ?
Yana shiga gidan a hargitse ya samay su duk kan su Nafisa ta haukace masu daga
ita sai dan buje a jikin ta tana fadin yaushe samad ya fara cin amana na haka ?
Yaushe samad ya canza ban sani ba nayi sakaci da yawa har na bari haka ya faru a
yau da ban dauki mataki ba.
Haka ya shigo ya samay ta tana wanan sambatun a cikin yan uwanta da suke ririke
da ita kamar sabuwar mahaukaciya.
Nan ya shigo baice da kowa kalaba cikin fushi ya shigo gidan don haka basu ga
fuskan wani magana a gareshi ba.
Tayo cikin shi da zagi tana fadin macuci mayaudari sai Allah ya isar min a gare
ka har zaka dauki waya kabawa wata mace ta fada min wai baka da lafiya a wurin ta.
Da karfi ya banbare hannun ta da ta rike mai wuyan rigar jikin shi ya fisge ya
shige dakin shi a hasale.
Madam ranan a gidan Nafisa ta wuni sun kule a dakinta suna jiran kiran Auta daga
zaria suji abinda malam zai fada masu.
Madam ta kawar da shirun da cewa wai shi wanan mijin naki wani irin mutum ne da
baijin magani haka sai anyi kamar an samu kanshi sai abu ya zo daga baya ya can
baki daya.
Tace shike damu na madam dubi irin kudin da nake zubawa akan bawan Allah nan sai
naga nasara daga baya sai komai ya lalace.
Komai zan iya yi akan Samad din in dsi zan samu ya kawar da ido akan ko wace
mace a dunuyan nan.
Madam tace idan shiya kawar da idon shi a kan mata su matan kina tsamani zasu
kawar da ido su ne akan shi dole suma dole da tasu shirin da suke don suga sun kamo
shi.
Don shegen kyau da daukan hankalina da wanan mijin naki ga abinda mata keso a
tare dashi kudi da kyawo da hali.
Hankalin Nafisa ne ya tashi sosai da maganan madam tace wallahi da ina da hali da
boye shi zan dinga yi a gida.
Dariya madam tayi tace idan kika boye shi kuce may ke da yan uwan ki Nafisa karki
matanta shine hannu da kafar ku kaf zurian ku.
Yanzun dai zan tafi Ondo ance akwai wani boka acan may aiki kamar yanka yuka wata
kawatace ta gano hakan.
Nikan ina can na dan samu karfin jikina shiryawa nayi zan leka cikin makaranta
don kada a wuce ni da karatu da nazo yi.
Daddy ya kira Abdul yana mashi godiyan kaini asibitin dayayi yace ba komai insha
Allahu zai kula dani kamar yadda zai kula da kaunar shi.
Bayan ya gama abinda yake ya kira Yusuf don su leka wurina kafin yaje gida Yusuf
din yabar abinda yakeyi yazo suka tafi.
Sun samu na dawo ke nan ya kirani a waya na fito na samay su a waje lokacin da
na karaso wurin su na samu suna magana suna kallon laptop din dake a saman kafan
Abdul din nasan wani abu suke duba a ciki.
Karasowana suka bar abinda sukeyi din tare da maida hankalin su a gareni Yusuf
ke fadin lalai jiki yayi sauki kauna na sai dai har kin dan fada kadan wallahi.
Murmushi nayi na dan jingina jikina ga motar su nace naji sauki sosai yusuf yace
barin in dan je can inga shagon yan makaranta indawo ina son duba wani abu a gurin.
Nasan yayi haka ne don ya bamu wuri mu gana dashi wuce wanshi yace dan gyara zama
yana fadin abin ya daina zuba ke nan ko ?
Harara na aika mai tare da fadin ban sani ba sai ka fito ka duba ai tunda kana
son sani ne sai yau naga dariyan shi yace kin dai ji abinda likita ya fada saukin
abin ai.
Banji ba kuma bana son naji tunda ba kai ke da lalurar ba au yanzu tunda kinji
sauki kina da bakin magana ashe jiya fa nan kike ta murdemurde ina tausaya maki.
Kawar da kainayi gefe guda ban bashi amsa ba na share shi yace na tambaye ki
jiya ciwo ya hana ki ban amsa na.
Nace may ka tambaye ni jiya din yace kwana nawa kike dauka kina off shiru nayi
tare da bashi ba a raina ina fadin wai shi baisan ina matukar jin kunyanshi bane da
yasan abin dake damu na.
Gashi kuma ya tsare ni da tambaya irin haka da zai sani jin kunya da nauyin shi
ai wanan kamar kamar yar iska ya dauke ni.
Niko gidan mu in badon ciwon mara ba har zanyi in gama basu sani ba ji nayi yace
may nene abin jin kuya kibani amsa na kawai don ya kama ne in sani.
Nace don Allah yaya Abdul ka daina wanan zancen naji yace na daina tunda baki son
zancen yanzu.
Badai kina shan maganin ki ba akai akai nace ina sha na gode daddy ma ya bugo
waya nake fada mai ka kaini asibiti yace zai kiraka yayi ma godiya.
Yace ya kirani ai dazun sai danace mai kaina nayiwa aiki ba sai ya godd min ba
nace ka fada ma daddy hakan ?
Yes ya dace ne in fada mai don lokaci yayi da zai fahinci hakan daga inda Yusuf
yake tsaye yake kallon mu yana jin farin ciki a ranshi.
Hikimar yin haka da yayi ke nan a gusa daga wurin don mu samu daman sakewa da
junan mu don idan yana wurin komai bazai wakana ba a tsakani karshe ma muna iya yin
abinda muka saba fada ke nan.
Ka samu zuwa duban su Affan kuwa na kawar da zancen da wanan tambayan murmushi
yayi yace ban samu komawa ba sai dai na fara shirin komawa.
Sai dai wanan karon ban san wani shiri kikai ma tafiyan nawa ba idan zan koma
nace dama idan zaka nike shirya maka tafiyan.
Yanzu shirin ya dawo kan ki don haka kece mai shirya komai ta wanan bangaren ya
kamata ace na fara maki albashi a wanan bangaren don kin ci hakan a gare ni .
So ki fara shirya min nan da two weeks zan tafi ina jira inji shirin da kai ma
tafiyan nawa da abubuwan da zan yi a can.
Yusuf ne ya iso gurin yana fadin mu tafi ko kada lokaci ya kure maka anan tunda
munga lafiyan kaunar tawa sauki ya samu.
Har kagama duba shagon nace mai yace ko dai in koma ne kada in takura maku kuna
hiran ku na jin dadi zan katse ku kai haba yayana wani hira kuma a haka ?
Ni dai daukar shi ku tafi kada yar buzaye tace ina shigewa mijin ta yanzu Abdul
yace kina tsoron ta ke nan ?
Nayi saurin fadin tsoro fa tsoron mace yar uwana kuma macen ma kuma buzuwa da
kyau kauna ta haka nake son naji mace jaruma wallahi.
Kai kaji ya juya wurin Abdul din yana fuskantar shi tare da fadin na fada ma
kauna ta jaruma ce ba irin ka ba mai tsoron buzaye yan haure.
Idan bata tsoro ai sai mu gani a kasa ba cika baki a nan ba nace ko agaban ta
wallahi zan cika baki idan ya kama in cika akan may zanji tsoronta ne wai ?
Mace ce fa yar uwata kowa sai ya gwada sa an shi yayi mai fishe shi duk abinda
take takama dashi wallahi ni khadija ina dashi fari kyau da tsayi kagako ba zanji
wani shakkata ba.
Irin kallon da yake jifana dashi daga cikin motar yasa nayi shiru dole don
kallone da ke dauke da fassara irin mai nuna feeling ga mutum din nan.
Mun gama shan matan juna suka ja motar su suka tafi ni kuma na koma ciki tare da
tunanen da yawa a raina na canjin yanayin da na hango a kwayar idon shi.
Wanan karon Nafisa bata yar da ba dakanta ta shirya tafiya zuwa kaduna bayan ta
dawo Niger don an bata labarin wani sabon malami a Kusfa.
Abdulsamad bai hanata zuwa ba don tace kaduna zata leka don ta kwana biyu da
zuwa shiri sosai yayi mata don zuwa kadunan a ganin shi ai gida zata.
Ranan da ta isa kaduna bata samu zuwa ko ina ba sai washegari suka tafi ita da
Auta yar take ga su Abdul din sai dai halin kwadai irin nata zata iyayin komai akan
kudi.
Haka yasa suka kule sosai da Nafisa har aminci ya shiga tsakanin su tana mata
shige shige dama Auta irin yan duniyan matan nan ne tunda ta fito gidan mijin ta
bata sake aure ba tana zaman rayuwa kawai a gida.
Su biyu sukai tafiyan sai driver daya kaisu bayan sun gama yi ma malamin bayanin
komai ne malamin yayi dariya yace kamar yadda take zargi gaskiyan maganan ke nan
ya fada tarkon son wata yarinya a yanzu sai dai abin bai wani yi nisa sosai ba.
Idan kuma bata bi alamarin a hankali ba zafin kishin da take nunawa ne zai sa
komai ya iya faruwa da ita.
Hakalin ta ya tashi sosai wanan ne mutum na biyu daya fada mata haka malamin yace
alamarin yarinyar yana da karfi sosai.
Don asiri baya kamata kai tsaye da zaran zamcen yakai ga iyayyen shi komai zai
iya faruwa a tsakanin su a yadda bata zata ba.
Don haka sai kin natsu aiki zamuyi maki wanda zaki kama mijin ki a hannun ki
indan shi ya kamu yadda muke so komai zai iya zo maki da sauki.
Amma koda zakici nasara akan hakan sai kin bi a sannu don yarinyar tafiki komai
da kike tunanen kina dashi abune wanda sai an aiwatar dashi a sannu saboda mijin ki
yana mata mugun son da bai san yana mata ba.
Nashiga uku tace malam tafini komai fa kace yace kwarai da gaske don gata nan a
gaban mu kina gani ta shige maki gaba ko a wurin shi.
Kuka ta fara tana fadin don Allah malam kai min rai ka taimake ni ko nawane zan
iya baka indai zaka min aikin da za a raba su hayatan hayatan ya ji bai kaunar ta
ko kadan.
Gaba daya yanzu na daina gane kan shi ada komai yana min kai tsaye yanzu sai yaja
min rai yake min abu da na dauka ko cikin dake gare ni ne yasa yake min hakan.
Yace magana dai guda ce ga yarinyar nan kina gani taurarin ta na da matukar haske
sosai duk abinda ta sama gaba takan cin ma nasara a kan shi lokaci daya.
Yana nuna masu zanen da yayi a kasa wanda su basu fahintar abinda ya zana sai dai
bayanin da yake masu wanda ke matukar tayar wa Nafisa da hankali.
Yace saukin abin daya ne yarinyar mijin ki baya gabanta don wani dalili nata amma
shi yana kokarin cusa kanshi ko yaushe a wurin ta ne.
Tace da karfi shi samad din malam yace kwarai kuwa muddin muka ce zamuyi aiki na
gagawa komai zai iya faruwa na fada maki.
Idan baki yarda ba zaki iya zuwa gurin wani kiji nasan duk wanda zai fada maki
tsakani da Allah ba zai fada maki sabanin abinda na fada maki ba.
Tana share hawayen dake zubo mata take fadin malam yanzu may ye abin yi don ko
yanzu da dabara na samu nazo nan din.
Wanan ba wani matsala bane aiki zamuyi mashi wanda hankalin shi zai fita a kan
wata mace baki daya sai mu cus mashi kaunar ki ke kadai.
Ta gyara zama tana fadin in hakan zai samu malam shi nafi bukatan ai min a kan
shi a raba shi da ko wace yar iska ce kison tayi min kutse a gidana.
Ya zayyana masu aikin da zai masu din ta yarda ta amince zata biya makam din
abinda ya bukata a wurin ta suka biya shi ba tare da taji komai ba sukai mashi
sallama.
Tun a mota take zazaga balai tana zaginshi da iyayyen shi Auta tana kara zugata
da fadin wanan wata irin yarinyar ce da za a ce ta fiki komai har kyau ke nan malam
yake nufi ko may.
Don banda kyau babu wani abu da Nafisa ke kadagi dashi don ba arabi ba boko haka
take dip dinta bakauya kuma.
Koda ta dawo kaduna bata biya gidan su Abdul din ba bata mayi tunanen shiga gurin
su ba don daukan su take a makiyan ta dama balle yanzu da sunan su ya fito ga
zancen.
Kwanata uku a kaduna bayan Auta ta koma ta koma ta karbo abinda zasuyi amfani
dashi idan ta koma sauran sai ya hada yace zai kira Auta ta karban mata don sai ya
nemi abin hadi.
Haka ta shirya sai da zata wuce ne ta dan shiga tsatsaye ta gaida su hajiyan shi
da sauran mutanen gidan ta juya suka tafi.
Almarina kuwa tunda na dawo sau daya muka hadu dashi koshi a tsatsaye don ina sauri
zan tafi class karatu don muna da test din da zamuyi washe gari.
Yazo min da provition mai yawa kamar ba gobe har sai danace kayan suyi min yawa
yace naci da kawayena.
Sun tafi abisa alkawrin zamuyi waya amma har wani lokaci bai kirani ba Yusuf ma
haka bai kira ba nikan haka yafi min nono fari.
Don dama neman mafita nake dashi kuma na samu yanzu sun sarara min ranan muna
hira da maryam take tambaya na su.
Nace banji komai daga gare su ba na nuna mata ni basu gabana yanzu abinda ya kawo
ni nakeyi.
Tace kai amna abin mamaki ne khadija ace sun share ki haka ba labarin komai daga
wurin su ko yusuf ai ya kamata ace ya kira musan halin da suke ciki.
Ke kuma baki neme su ba halarci baice haka ba fa khadija shiru nayi mata don mu
kawar da zancen su da ta dauko min ina zaune kalau.
Sai bayan da na kwanta sai kuma maganan ya damay ni a rai gaskiya maryam ta fada
min ya kamata ka kula mai kula ka koba komai zai san ka damu dashi ai.
Ranan da kyat na samu nayi barci da tunanen su a raina sai dai ni ba zan iya
kiran shi ba sai dai dan dama dama Yusuf din.
Washe gari haka na tashi da jin bakin rai a zuciyata sai dai kawai na danne abin
a raina don na kudurta a raina ba zan taba kiranshi ba indai nice zakira inji ko
lafiya suke.
Tunda dama ba wani soyayya ko wani abu ke tsakanin mu haka ba mai karfi kawai dai
ya gaji danine shima ya hutar da kan shi.
Na share kawai kada maryam ta fahince ni na shirya muka nufi cikin school don
daukan lectures na watsar da maganan su a raina kada in sa wa kaina damuwa a banza.
Alamarin gidan shi kuwa yanzu tun dawowan Nafisa daga kaduna sallon zaman su ya
sauya don yana dan samun kulan daya kamata daga gareta duk da ba wani dadin yake ji
ga hakan ba don baya samun sakewa har yanzu a gidan shi yadda yake so.
Shima Abdulsamad din ina a ranshi yakan so ya kirani yaji lafiyata sai dai yanzu
duk lokacin shi na aiki ne dana Nafisa a haka har yayi tafiya tare suka ketara da
nafisa zuwa wanan tafiyan.
Satin su biyu suka dawo Nigeria koda suka dawo abuja bai samu kafan kiran na ba
don Nafisa ta mamaye komai a lokacin.
Yau suna tare da Yusuf a office din shi Yusuf ma wanda yayi tafiya yake tambayan
shi labarina ya yamutsa fuska yana fadin wallahi banda labarin ta itama bata neme
ni ba.
Yusuf yace haba kai ma kasan bazata nemay ka ai, amma hakan bai mun dadi ba
wallahi dakace baka kirata ba waya ya dauko daga Aljihun shi ya fara neman layina a
lokacin.
Ban shiga school ba ranan don na tashi da ciwon mara ina kwance a dakin mu ko
karyawa ban yi ba har lokacin don haka ina cikin barci mai nauyi daya dauke ni naji
kira a wayana.
Da kyat na lalubo wayan dake gefe na ina jan tsakin wanda ya tayar dani a wanan
lokacin dana dan samu sa,ida na samu barci ya dauke ni.
Koda na dauko har kiran ya katse sunan Yusuf na gani akan wayan ban kai ga tunane
ba wani kiran ya sake shigowa again.
Tunane nake a raina may kuma zai fada min yanzu mutanen da suka shareni kusan
wata daya ke nan yanzu kuma zai kirani yace min may ?
Kamar in share shi kiran ya katse sai dai na danna recieve inji abinda zai fada
min a lokacin na amsa da sallama cikin muryan barci da yanayin ciwo a tare dani.
Naji yace subbahanallahi khadija baki da lafiya ne may ya samay ki naji muryan ki
a haka ?
Da sauri ya dago kai yana kallon Yusuf dake magana a waya yaji yace ayya sorry
sannu ko kin je asibiti ne nace nasha magani ai ba sai naje asibiti ba.
Idon shi har lokacin yana akan Yusuf din yace may ke damun ta ne naji Yusuf din
na fada mai wai banda lafiya ne a kwance nake ma.
Taje asibiti Yusuf yace tace ba sai taje asibiti ba wai karban wayan yayi daga
hannun Yusuf din naji muryan shi yana fadin ki shirya yanzu gani nan zuwa nakai ki
asibiti ya fada kai tsaye.
Nace naji sauki ba sai kazo ba na kashe wayan wayan ya kalla tare da mikewa tsaye
yana rufe file din dake gaban shi ya fara tafiya.
Yisuf dake zaune ya mike juyowa yayi yana fadin ka zauna ka karasa aikin barin
je na ganta in dawo Yusuf yace amma kana ganin zata saurare ka idan kaje kai kadai.
Wani kallo yayiwa Yusuf din kamar zaiyi magana sai kuma ya juya ya fita Yusuf ta
girgiza kai yana murmushi halin abikin nashi na bashi mamaki ace mutum haka da
girman kai.
Nikan ina kashe wayan naja tsuki nace mayaudari kawai naja filo na gyara kwanciya
na barcin da ban koma ba kenan idona a rufe nake tunane nace yanzu na tabbatar da
karkashin mace yake.
Wata kila matan shi tasamu labari ne ta hana shi kula kowa yanzu ya dawo zai
yaudare ni kuma ya bata min lokacina a banza.
Dama ban sa zancen ko kadan a raina ba balle ya damay ni in ma junin shi iya
yaudaran mata ne ya bata masu lokaci Allah ba zai bashi saa ba anan naja tsuki na
gyara kwanciyana.
Na samu barci ya fara dauka na naji wayan shi ya shigo min na duba na bar wayan
nata ruri har ya katse kira uku yai min ban daga ba .
Ranshi ne ya baci sosai yana shirin juyawa sai ga maryam kamar daga sama ta dawo
don hankalin ta bai kwanta a yadda ta barni ta dawo ta dubani.
Sai ganin shi tayi yana shirin juyawa da sauri ta karsa wurin shi tana gaidashi
tare da fadin wallahi tana ciki bata da lafiya ne tun jiya nima yanzu na dawo in
dubatane.
Yace shi yakawo ni yazu asibiti nake son zuwa da ita a ranta tace boye min
khadija ke nan rayi ashe suna waya dashi shine take boye min.
Taji yace nakira wayan ta taki ta ga bayan yanzu Yusuf ya gama waya da ita ta
fada mai bata da lafiya tace barin shiga in fito maka da ita nasan fushi take daku.
Fushi ya tambaya da mamaki dariya tayi tace ina zuwa don Allah ta wuce ya bita da
kallo har tabace yana mamakin kalamin ta wai fushi take da ku fushi akan may ?
Tana shiga dakina ta nufa ta samay ni a kwance zama tayi a gefe na tana min
sannu tare da fadin ga mutumin ki nan a bakin get yana jiran ki wai kuje asibiti
yanzu.
Wani kallo mai kama da harara na watsa mata nace rabu da mayaudari nine zai kai
asibiti akan may zai zo min a yanzu da bana son ganin shi.
Haba khadija kin san uzurin da ya tsayar dasu basu nemay ki ba tunda har yanzu ya
iya zuwa da jin baki da lafiya ai ya kamata ki saurare shi.
Haba maryam abinda kika sani ne nafi jin dadin zaman da nake yanzu babu takuran
kowa a kaina akan may kuma kike son in kara fadawa tarkon mayaudari irin wanan
mutumin da matar shi tafi karfin shi kuma.
Kada kice haka khadija ko ba komai ya nuna kulawan shi a kan ki yanzu ina laifin
wanda ya nuna maka haka a lokacin da kake cikin halin ciwo.
Don Allah ki tashi ki daure badon ni ba sai don Allah ki tafi ki ganshi ko ba
komai zakiji abinda ya tsayar dasu kwanaki mai tsawo haka baki ji su ba.
Allah da kika hadani dashi ne zai sa in tafi badon wani abu ba can nasa, don ina
son inyi nisa da shuumancin su yanzu tace daure kiwa Allah da kika ce zato kike
yanzu kila ma ba matar shi bace ta hana ya kulaki.
Kalaman ta yayi tasiri sosai a raina koba komai ina son jin abinda ya hana injisu
kwana biyu don ban sin jawa kaina wulakanci ko kadan.
Ita ta taimaka min na shirya atamfa na daura don yanayin da nake ciki tare muka
fito zuwa ida yake zaune a motar shi.
Yana yi yana kallon agogon hannunshi can ya ga fitowan mu tare da maryam ina
tafiya da kyat yanayin ina jin jikin nawa sosai.
Har muka karaso bai dauke idon shi a kan mu ba yi hakkuri mun barka kana jira
wallahi barci na samu tanayi yanzu na tayar da ita.
Bai yi magana ba sai kallona yayi yana fadin shiga mota mu tafi nace basai naje
asibiti ba na sha magani naji sauki ina magana da kyat cikin daure fuska.
Shiga muje nace maki da sauri maryam ta riko min hannu ta nufi gefen mai zaman
banza tana bude min motar tare da fadin sai kun dawo Allah ya sauwaka.
Sai da na zauna da kyau ya tayar da motan muka hau dogon titin da zai kaimu
cikin gari sai da mukai nisa kaina da duke na dafe goshina da hannu na daya naji
yace.
May damun ki ne haka ban bashi amsa ba sai gyara zama da nayi ina cije baki don
dan motsawan da nayi maran yana min ciwo yanzu.
May damun ki ya sake maimaitawa shiru nayi can nadan sauke nufashi nace da kyar
banda lafiya ne kawai tare da dan dafe mara na.
Au ko abin ne yazo maki na manta yanzu kike cikin time din period din ki ko
hararan shi nayi tare da kawar da kai ina cewa a raina kaji min mutum da bin didigi
haka ?
Kwana nawa yakeyi halan sake dago kai nayi na kalle shi kamar bashi yake maganan
ba nayi saurin kawar da kaina daga kallon shi.
Yace bakiji bane kwana nawa kike dauka kina period din nace ya fada tare da dan
kallo na nace ban sani ba kada ka wuce hurumin da ba naka ba mana na fada ina
kwantar da kaina.
Murmushi yayi yace haka kike ce ko nace na fada din ni banga dalilin tambayana
haka ba kai ba likita ba wani sai nayi shiru.
Yace go ahead you say your words out, shiru nayi tare da kawar da kaina gareshi
gaba daya ya sake fadin you free to say komai zaki iya fada don ance fushi kike
damu.
Da sauri na jiyo ina kallon shi nace fushi fa akan may zanyi fushi daku in ba ina
son sama kaina nauyin da bai hauni ba ?
Murmushi yayi da sai ka saurara zakaji shi yace kwana biyu bamu kasan ne daga ni
har Yusuf na fita da madam dina ne mun tafi check up ciki ke bata matsala.
Don Allah malam ni ban tambaye ka ba in zaku iya ma ku tare a can ba damuwa na
bane wanan ciki kuma Allah ya bata lafiya ya sauketa lafiya amma mi ya hadani da
tafiyan ku kuma.
Kwana yasha muka shiga wani clinic inda yasa na fito muka shiga guri ya sama min
na zauna ya nufi gurin tankan kati ba mu dade ba duk da mun samu mutane a gurin
yace in taso mushiga gurin likita.
Mun shi likitan yare ne don turanci suke dashi sun gaisa naji likita na cewa kayi
sabin aure ne ashe yace mashi eh yace madam ta kwana biyu bata shigo ciki ya zaunu
ko yace eh a gadarance yake ma mashi magana yace ina son ka duba min ita tana fama
da mesturalpain ne.
Yace ayya sorry madam yakamata ace ya rage maki ciwo yanzu da kiyi aure ya
kamata ace kin rage jinshi haka indan zakiyi period don agana kawai matsalan hakan.
Nauyi kunya ya rufe ni a wurin na kasa daga kaina shima wayan shi yake dakila
baibi ta kan likitan ba sai da likitan ya fara tambayana ina mashi bayanin ya dago
yana kallo na.
Tashi nayi zuwa inda likitan yace in kwanta ya dan dadana cikin nawa na dan sake
kara daidai kasan mara na daya tausa da dan karfi yace in tashi ya dawo ya zauna
yana rubutu a wani farin takarda ya mika mai lokacin na dawo na zauna dakyat dafe
da marana dake min tsananin ciwo sosai.
Bayan ya mika mai yayi mai bayanin anemi wanan maganin in sha zasuyi min allura
kuma zan samu sauki da yardan Allah ya mika mai hannu tare da fada mai inda zamu
kai takardan a duba ni.
Sai da muka gama komai muka fito yana min sannu muka dauki hanya wani shago ya
tsaya yace min yana zuwa ya shiga ciki yadan jima sai gashi ya fito yaron shagon na
binshi a baya dauke da wasu manyan ledoji biyu a hannun shi.
Ya saka bayan motar ya shiga muka tafi bayan ya mikawa yaron kudi yana mashi
godiya kaina na duke yace sannu likita yace zaki samu sauki dan anjima kadan amma
zaki barci sosai ki ci wani abu don kince baki karya ba.
Bana jin shi do murdan da mara na keyi ina dan cije baki ina jijiga kafa na da
matse hannaye na duk yadda na so in daure na kasa sai da na yi ya gani a bakin down
hostel din mu ya tsaya da motar shi.
Zaki kara kawar ki ta taimaka maki ne ko in taimaka maki ki fita duk da ciwon da
nake ji sai dana harare shi na bude motan na fita ko godiya ban mashi ba.
Ina fita yace turo min kawar ki ta daukan maki magani kai na iya dagawa na shige
ciki na samu maryam na girki a dakina din bata da kiuyar girki ita tana gani na
tace har kun dawo kaina gyada mata na fada saman katifa nace yana kiranki a waje.
A saka hijab da sauri ta fita daga dakin zuwa wurin shi bata jima ba ta dawo
dauke da ledojin nan da ya sayo tace yana maki sannu wai sai kunyi waya yace kici
wani abu kafin ki kwanta.
Itace ta zauna ta bude ledan kayan ciyeciye ne a cikin dana sha tarkace dai gasu
nan sai dayan ledan dake dauke da pad din mata always kamar mai bude shago dashi
ban san ranan da zai kare ba.
Abinci ta debo min na dan ci kadan na kwanta sai barci mai nauyi ya dauke ni a
gurin ban kara sanin inda nake ba kuma.
Yana fita ya daga wayan shi six miscall ya gani na Nafisa da sauri ya danna
wayan ya kirata yana fadin sorry ina wani abune yasa banga kiran ki ba.
Tace Samad ina kaje wacece akace mi an ganku tare a asibitin doctor Bisi yanzu
waka kai asibiti wata macs ce aka gan ku tare tare ta fada cikin tashin hankali.
Sai dare sosai suka shiga Abuja inda Yusuf ya aje shi gida ya nufi nashi gidan da
motar shi da ya bari gidan don tafiya da ba shiri sukayi.
Ko da yashigo gidan shiru yaji kamar yau mutanen gidan nashi basu ciki bai tsaya
falon ba ya haura sama inda dakunan kwanan su yake.
Ga kaya nan ko ina a warwatse ko ina agidan anyi amfani dasu an kasa kawar dasu
don tsabagen kiuya da lalaci har ya kai kofan dakin ya tura a hankali ya shiga.
Baiyi mamakin ganin ta a yanayin da ya samay ta ba don duk kwanankin nan a
yamutse take a gidan ba wani gyara ko kwaliya da take samun yi .
Tana zaune saman gado gashin kanta a wawatse ba gyara ta dago ido ta kalle shi
tare da kallon agogon bangon dake dakin tace Samad ina kafito a wanan lokacin.
Aikena kikayi da kike tambayana ya bata amsa tare da wuce wa wurin wardrobe din
shi yana rage kayan jikin shi.
Samad neman mata kafara ko mai yace idan na nemay su ba namiji nake ba wallahi
baka isa ba ta fadi da karfi ya juyo gare ta yace ban isa ba fa ki ka ce Nafisa.
Tace baka isa ba wallahi may na rage ka dashi a wanda ban baka da har zaka
lakanci neman mata a yanzu daga sama.
Ya ciro wani dogon jallabiya baka yana fadin waya san iyaka Nafisa baki san komai
ba banda son kan ki da kashin kudi abaki kuma baki godiya.
Kudi dole ne ka bani don kasan sune buri na kuma akwaisu bathroom ya shiga ya
barta ta ta fadin bakaken maganganu gare shi har ya fito bata fasa magana ba.
Gadon ya duba yace duba don Allah wai a inda mutum zai kwanta ke nan ya fara
kakabe shimfidar da wani dan karamin towel daya fito dashi daga ban dakin.
Yace mace sai tarin kazanta na fada maki bani son wanan kazantar taki amma ke
abin sai gaba yake yi gare ki.
Ai kasan a haka nake kuma ka aure ni na dauka idan kin shigo cikin daula zaki
canza ne ashe ni ban san abin a jinin ki yake ba.
Kazantar ne a jina na yake Samad yace in ba ajiin ki yake ba za a ce duk yawan ku
baku iya gyaran wuri tace samad wa kake so in sa aiki a cikin gidan nan.
Kafa san daga kanne na sai yayyena anan sai kuma kawu naina da gwago na yace may
yasa kika boye min hakan da farko kin fada min yan aiki ne kika samo min kuma biyan
su nake duk wata.
Sai yanzu zaki ce min wai yan uwan ki ne na jini baki iya saka su aiki a gidan
nan kin zo gidan nan kin samu masu aiki kika ce baki yarda dasu ba.
Na baki go ahead da zaki kawo wanda kika yarda su suyi mana aiki ashe ke
yaudarana kikayi ki kwaso yan uwanki kika cika min gida dasu.
Samad ta fada da karfi kawo yan uwana danayi a gidan shi ne kake kira da yaudara
yace yaudara ne mana mutum da gidan shi ba dama ya shigo ya huta a ciki yaji dadin
ranshi.
Samad yau ni kake fada ma haka don ka gani da ciki kake kokarin ka wulakantani
yanzu ko may babu zancen wullakanci sai maganar gaskiya.
Haukace mai tayi ranan tana fadin bai isa ya rabata da yan uwanta ba don tare ya
gansu ya kuma yarda ya aureta a hakan.
Haka ya kwana da tarin bakin ciki babu kunya washe gari kuma sai gata ta neman
sulhu dashi don dai kawai ya biya mata bukatan ta don bata iya hakkuri dashi duk
yadda ranta ya baci dashi ga wasu kudi da take son karba a wurin shi masu yawa don
ai mata aiki a kan shi.
Bata samu ko daya ba ranan don asubanci yayi ya fita wirin aiki da wuri koda yaje
gurin aikin bai iya aiwatar da komai ba.
Yusuf ya shigo ya samay shi a haka yake tambayan shi wai may ke faruwa dashi ne
bai tsaya boye mashi ba ya sanar dashi halin da yake ciki da nafisa a gidan shi.
Da yan uwanta da suka cika maigida da sunan yan aiki ta kwaso yana biyan su a
wata ashe ba haka abin yake ba.
Kai inji Yusuf lamarin Nafisa akwai daure kai wallahi Abdul yace nima bashi ba
kazantar nan ke damuna Yusuf.
Ka san dai halina da kyakyami wallahi komai na gidan nan yanzu kazantar shi nake
ji in ba ruwan gora ba ban iya cin komai a gida na .
Yusuf yaya zanyi da wanan masifa dana dauko ma kaina nasan ina son nafisa sosai
why da ba zata gyara halin ta ba may ye ban ma Nafisa a rayuwan ta.
Kamar karta samu cikin nan yanzu abin ya karkare jagule mata mace ba wanka ba
saka sutura a jiki idan anyi magana sai tace wai lalurar cikine haka take cikin ta.
Au dama ta taba ciki ke nan naga auren budurwa mukai mata wani kallo ya jefe shi
dashi yace Nenan yar waye idan bata taba haihuwa ba nima daga bayan nan na fahinci
yar tace ashe.
Yanzun haka zan kare ga yawon restaurant ina cin abinci a garin nan kamar wani
mara galihu dani.
Kai innalillahi abin nakune akwai daure kai wallahi saukin abin khadija zata
dawo next week zaka dan samu sauki a awurin ta.
Saukin may zan samu a gurin ta ya tambayi Yusuf a yanayin rashin fahintar
maganan shi Yusuf yace koba komai tunda ta iya girki naga ai zata dan dinga maka
idan tana da time.
No ban san in jefa rayuwan yarinyar ga halaka ko kadan nafi son ayi komai a
kaidance yace kana nufin auren ta zakayi.
Shiru yayi ya dafe kanshi bai sake magana ba ya fahinci bai son maganan don haka
ya kyale shi tare da canza topic.
Yusuf na fita ya jawo wayan shi ya kira layina muna gida ya Hauwa mai jego ya
kira wayana ina wanke kayan miya a kitchen aka kawo min wayan.
Sai da ya kusa katsewa na dauka tare da sallama yace ina kika shiga kika bar
waya na ruri haka nace ina kitchen ina girki wa ya hauwa da ta haihu.
Kuna gidan ta ke nan ya tambaya nace eh may kike girka mata nace miyar shuwaka
zanyi mata da tuwon shikafa.
Ke wa ya koya maki girki haka ne wai nace girkin ma har sai an koya ma mutum
yin shi idai kana mace ai zaka iya girki ko wani iri dole.
Aranshi yace ga macen da ta san kanta ba sai kuma yace ke wace irin yarinyace da
baki iya kiran mutane kiji ko sun sauka lafiya ?
Na aiku tafiyan dare ne ko ni na saka ku yin tafiyan da kuyi din yace OK haka
zaki ce ma nace haka din ne ma ai.
Sai naji ya kashe wayan dariya nayi nace zaka kaji ai ka daina in yar da magoro
in huta da kuda har dare muna gidan sai tara muka dawo gida a gajiye .
Ban kara bi ta kanshi ba har akai bukin suna aka watse lafiya drinks din da suka
kawo muna yayi muna rana do shi mukai amfani dashi wurin taron sunan.
Mun fara shiri don tare da yaAmina zamuyi tafiyan kamar yadda na fada mata yace
zai turo mota hakan ne ya faru sai ga mota zuwa sha biyun rana ya tsaya a kofan
gidan mu.
Nan muka fito mukayi haraman tafiya nasha nashi ha a wurin mama da daddy kafin
mu wuce muka dauki hanyar Abuja tare da ita don zata kwana a wurin mu.
Nafisa da madam murnan tafiyan shi kaduna a satin sukayi don dama kafan zuwa ondo
take nema don Abdulsamad ya hanata tafiya yanzu ko ina.
Tafiya sukayi sosai tun suna na dadin rai har ta fara galabaita ga tafiya don
dan karan nisan da garin ke da tsakanin shi da Abuja.
Bata dauka nisan shi yakai haka ba sai da suka fara hanya duk wanan bakar wahalan
bai sa ta janye kudirinta na zuwa wurin wanan bokan dataji ana yabon aikin sa ba.
Ko da suka isa ondo da safe wani motar suka kara bi zuwa kauyen da bokan
bayaeraben yake zaune sun isa a wahalce don har amai da zazzabi sai da tayi a
hanya.
Sun isa dajin mai kama da gari da baifi yan gidaje a kirga ba sai da suka huta
kafin su samu ganin bokan don ranan suke son su koma Akure su shiga motan dare su
koma abuja.
Bayan ta gama fadin abinda take son yai mata nan boka ya fara surukule shi ya
dago yana kallon ta na dan lokaci.
Sai duk suka tsargu da irin kallon da yake masu wanda ke nuna akwai magana kai ya
girgiza sanan yace aikin ta akwai dan wahala a cikin sa.
Don yanzu haka mijin ta yana tare da wata yarinya sai dai bai hango soyayya
tsakanin su ba amma akwai aure har da haihuwa a ciki.
Kirjin ta ta doka tana fadin ta shiga uku ita samad zaiwa kishiya wacece zai aura
har su haihu ?
Sam ta mace da Fati ma mallakin mijin ta ne har da diya shi boka Allah bai bashi
ikon tsafin shi ya hasko ni ba nan tasa ai mata aikin da za a raba tsakanin shi da
ko wacece .
Akuma fitar da ranshi ga ko wace mace a rayuwan shi sai ita kadai ya kara yin
saddabarun shi na bokayen da suka gwane da tsafi yace ya ga wata mace sai dai baiga
gaban ta sai bayan ta kamar tana son shiga rayuwar mijin ta amma dai bari ya mata
aiki akan wace ta baiyana in yaso daga baya aikin da zaiyi zai gusar da waccan
matar da yaga bayanta din.
Tace tana son koda kashewa ne a kashe mata wace aka gani ko a haukatata gaba daya
kowa ya huta.
Yace an gama sai dai aikin ta na da tsada sosai tace kada yaji komai indai aikin
zaiyi kyau nan ya shiga hada mata irin nashi surukulle da bayanun yadda zatai
amfani dashi ba tare da kuskure ba.
Yace ba mijin ta ba wata mace da zai duba a duniya muddin tayi abinda ya fada
mata daidai suka kama hanya komawa gida bayan ta cika shi da kudi.
Sam bata san Abdul kwana biyu zaiyi a kaduna ba lokacin da Abdul ya iso gida ya
neme ta sai cewa sukayi ta tafi unguwane.
Har ya shiga ya huta ya dan kwanta bata dawo ba ran shi ne ya baci sosai da ita
yaji yana son fita don haka ya shirya ya fito dan yasan kafin ya dawo ta dawo gida
a lokacin.
Sai dai abinda ke bashi mamaki baifi ganin motocin shi duka dayayi ba a gidan
yana tambayan kan shi da wace mota nafisa ta fita ?
Yana fita batare da sanin inda zai tafi ba har ya yanke shawaran zuwa wurin Yusuf
sai ya fasa don ya san yanzu shima hutawa yake a gidan shi kada yaje ya damay shi.
Sai kawai ya yanke shawaran ya leka khadija don ya kwana biyu da ganin ta hanyar
hostel din mu ya dauka sai da ya iso ya kira waya gashi abakin hostel.
Nace da yamman nan yace na koma ne nace gani fitowa yaja iska ya kashe wayan na
fito ina tako dadaya wanda ni ban san inayi ba ma.
Na karaso wurin motar cikin yar murya na nace dashi sannu da zuwa baki maraba da
zuwa na bane ko may ?
Murmushi nayi tare da fadin naga baka fita a wanan lokacin ne kawai har ina da
lokacin fitane na daban da ban sani ba yace shigo mota mana.
Ina shiga sai kawai ya tayar da motar nace da sauri sata na zakayi ko may ?
Bai bani amsa ba yaci gaba da kallon titi may zan sata anan, nace mutum, dariya
yayi yace kan nan naki kuwa zaiyi kudi sosai nace ai kafin ka sai da nawa ka fara
sayar da na buzuwar ka ita bakuwar haure,
Kuff naji yake ma bakina dan bugu da sauri na dafe bakin nace saboda buzuwa ka
dukar min baki ?
Yace ban san hadinki da wanan buzuwar ba nace halinta halinta bai mun bane don
tana da ji da kai da son wullakanta mutane.
Ita abi kyama ba a kyamace ta ba sai itace zata kyamace mutane matar tawa ce abin
kyama khadija ?
Ba ita duk buzaye abin kyama ne gare mu yan Nigeria sai iri kune dake mai dasu
mutane kawai baku kyaman su don su din ba abin yarda bane mazan su da matan su.
Sai mutum ya yarda dasu daga baya su zo su yaudare shi yaudara a wurin su ba
abin kunya bane don su din basu da kunya ko kadan.
Shiru yayi yana tunane a ran shi bai bani amsan magana na ba nace kuma gasu da
son raba mutum da yan uwan shi su cika gida da nasu yan uwan.
Ga kazatar tsiya da son mamaye komai ya koma nasu su kadai koda kuwa sun samu
wasu mata ne a gidan shiru nayi don na dauka bai saurare na a lokacin.
Sai naji yace uhmm go on yaya kikai shiru ba labari kike bani ba nace au na
dauka baka sauraro na ai gasu da dan banzan bin malamai da bokaye basu yarda da
kowa ba sai kan su suna iya yiwa yan uwan su yankar baya su zauna da mijin yar uwar
su.
Zasu iya ketarowa da auren su suzo su auri wani anan alhalin duna da mazan da
suka baro a gida sai lokaci lokaci suke lekasu.
Kai bazaye muggan mutane ne sosai wallahi duk wayon ka zasu san yadda suka juya
ka indai na miji ne ji nayi ya tsayar da motar da karfi yace bari inyi sallah
please sai kici gaba da bani labarin ki.
Fita yayi a motar ya nufi wani gu sai yanzu na duba naga ashe massalaci ne a
wurin shiga yayi a ciki na mayar da kaina akan sit din motar ina kallon mutanen da
ke gurin.
Ya dan jima a ciki ya fito ya shiga motar ya kama hanya mun dan taba tafiya ba
tare da nasan ida zamu nufa ba.
Yace bissimila cigaba da labarin ki nace labarin yai ma dadi ke nan kwarai kuwa
ina jin dadin labarin sosai nace toba zan kara fada ba.
Don may ko don kar naji halin buzaye nace ba wanda baka sani ba a cikin wanan
kai da ke da ita a gida may ya rage da baka sani ba.
Ina ga saura bani kuddi baba ko a yaye ka kafa ka wayi gari ka samu ta ketara
kasan su da dukiyar ka.
Yace da taci rabon ta ashe idan ta iya ketara kasa da dukiyana duka eh tunda a
banza kake samun kudin yace haka kike zato ashe ?
Ni ba ragon namiji bane ko da yaushe ina tsaye da kafana wurin neman na kaina
zaune a office din nace mai.
Au haka kike dauka na ni ko a gidana nake ina neman na kai na nace gun buzuwa ke
nan kai ya girgiza min.
Koda yake dama abinda kuke nema a wurin su na daban ne da sauri ya juyo yace
may muke nema a gun su nayi shiru tare da kawar da kai gefe.
Fada min may muke name muka aure su nace su mana tunda irin su ne ku din jara, , ,
, shiru nayi karasa mana ina jin ki.
Hannu yakai yana kamo min baki nayi saurin rike hannun nashi a karo na farko
dana taba taba jikin shi da sauri na sake hannun nashi.
Na kawar da kai na gefe hannun nashi ya duba a hankali sai naga ya sauke
murmushi a fuskan shi yace how lucky you're ?
Ke ce mace ta uku da na taba hada jiki da ita a duniya nace nima ina regreting
din hakan da nayi wallahi.
Shiru mukayi yaci gaba da tuki wani guri ya shiga da motar mai yawan ginene
gine da sasa da yawa yace kin san wanan gurin tsoro ne ya kama ni dana kalli gurin
sai na dauka ko hotel ne.
Kai na girgiza alaman tsoro ya kamani sai naji yace nan ne ma,aikatar mu wanda
daga MD din mu sai ni a gurin.
Da sauri na kalle shi yace ko kina bukatan shiga kiga gurin da sauri na girgiza
kaina nace a,a don Allah ka mayar dani hostel inda ka dauko ni.
Ai bamu gama ba don baki ban amsata ba da sauri nace tamay yace irin mu da kika
fara fadi baki karasa ba nace maganar yawuce ai.
Yace a gunki ya wuce ni a wurina bai wuce ba sai naji karasan maganan ki ko mu
kwana a nan da sauri na dago ina kallon shi don Allah dai kayi hakkuri ka mayar
dani inda ka dauko.
Maimakon yayi abinda na nace sai naga ya gyara set din motar ya kwantar dashi
tare da sa hannayen shi yayi matashi dashi yakai kwance.
Muna wurin shiru ba wanda yai magana a cikin mu sai tsukin da nake ja can yace a
kasalance kada ki kara jamin tsuki a mota yanzu na fitar dake na wuce.
Kayi hakkuri don Allah ka maidani hostel ina da exam next tomorrow ban son in
fadi wani mutum ne ya dun faro inda muke yana haska toci a hannun shi.
Ni dake zaune nake iya ganin mitumin dake tafe nace ga wani nan yana zuwa gurin
nan fa bai damu da abinda nace ba yana kwance abinshi yadda yake.
Har mutumin ya karaso ko ya sheda motar shine sai naga ya dan tsaya daga nesa
damu yana fadin barka da dare yallabai an wuni lafiya cikin harshen turanci.
Ya dago yana amsa mashi da lafiya kawai sai mutumin ya juya ya koma ciki ban san
na firgice ba sai bayan wucewan mutumin yace lafiya kika shige min a jiki haka ?
Ko kina son jin abinda buzuwa ke ji ne ajikina ta leke min da sauri nayi kokarin
jaye jikina dana dan manna da nashi sai naji ya riko ni.
Ta yadda har muke iyajin saukar numfashin junan mu a lokacin ka sake ni don Allah
wai may kake nufi da nine haka wai ?
Fada min amsan tambayana mubar aurin nan kada masu gadin nan su dauke ni dan
iska nace sake ni in fada ma to yace sai kin fada jin irin rikon da yaimin yana
kara manna ni a jikin shi nace jarabbabu irin su mana.
Sake ni yayi ya daga bai ce komai ba ya tayar da motar muka bar gurin sai da
naga mun hau titin da zai sada mu da hostel din mu hankalina ya kwanta dashi.
Don yadda a lokaci daya naga canjin yanayi a gare shi ya firgitani ainun sai da
muka dauki hanyar hostel din yace ki shirya shiga cikin jarababbun mutane daga
yanzu.
Ban iya magana ba bukata na shine inga kafata a kasa yanzu a wani shago ya tsaya
ya shiga har ya dan dade sai gashi ya fito ina hangen shi tun daga nesa na raya a
raina Allah yayi halitan namiji a nan .
Baya ya bude aka saka mai kayan a ciki ya sallami yaron ya shiga muka tafi bakin
hostel din mu ya tsaya bai bude motar ba niko a kage nake da in fita daga motar.
Yace zan yi tafiya may yuyuwa baza mu hadu ba sai idan na dawo Allah ya tsare
hanya nace dashi tare da kallon shi ya bude min motar.
Kina level nawa yanzu a karatun ki nace two a takaice yace yayi nisa da yawa
gaskiya nace ai ni ke yi ba wani ba ban ga amfanin karatun ba a guna amma ai naga
su Binta da zainab sunayi suma ?
Wanan matsalar su ne ni nawa matsalar na sani bata wani ba su ya shafa wanan
bani ba amma kai mugu ne ko ?
Zaki iya ba kan ki amsa idan kin so ko wani kalar nake ya bude min motar tare da
miko min ledojin dake bayan motar ina karba na fice ina fadin mugu kawai da karfi.
Girgiza kan shi yayi ya tayar da motar ya tafi sai da ya fara tafiyane tunanen
Nafisa ya zo mashi a rai yana tunanen ko ina taje dazun ya dawo bai samay ta a gida
ba.
Ya iso gidan ya shiga a falo ya samu su Hadiye zaine suna hira suna ciye ciye
gaishe suke da dawowa yace Nafisa ta dawo sukace bata dawo ba ya shige ya barsu a
gurin zaune.
Ya shiga ran shi a bace ya dubi lokaci yaga tara da wani abu na dare goma saura
kadan wanka ya shiga yana tunanen Nafisa a ranshi har ya fito ya kwanta shiru ba
Nafisa.
Ni na fado mashi a rai jarababu irin ku murmushi ya danyi yana rufe idon shi
kamshin turen oud dina yake tunowa daya shaka.
Ya lumshe idon shi tare da gyara kwanciyar shi yana lumshe ido yaji dadin
kasancewa mu a tare yau hiran da nake mai na buzaye ne ya dawo mashi a rai.
Ba abinda na raga daga halin da yasan Nafisa dashi zai iya cewa kila wani ya
fada min kadan daga cikin halinta daya fahinta.
Sai dai abinda ya tuno inda nace suna barin mazan su a gida su zo duniya su auri
wani mijin na daban sunayi suna zuwa ziyarar mazan nasu.
May wanan maganan yake nufi kodai shiyasa Nafisa take yawan ziyaran gida akai
akai bai sani ba da sauri ya kawar da wanan zancen kada zargi abinda bashi ba
yashiga zuciyar shi.
To wai ma ina Nafisa taje ne uban may tafitayi da tun safe har wanan lokacin bai
ta dawo ba yaja tsuki yace zan gwada ma Nafisa matsayin ta na mace a gidan nan.
Goma, sha daya shabiyu saura ya mike zubur hankali a tashe ya mike yana zura
riga a jikin shi ya sauko zuwa kasa komai na falon a kashe yake .
Su hadiye sun shige dakunan kwanan su kayan da sukaci abinci gurin babu kowa a
wurin tsuki yaja ya fita waje ya nufi gurin maigadi yana tambayan shi ko yaushe
nafisa tafita a gidan.
Maigadi yace rabon shi da ita tun shekarajiya da kawar ta tazo suka fita komawa
yayi ciki yana tunanen tun shekaran jiya da kenan Nafisa dama bata gidan tun
lokacin da shima yayi tafiya ko may ?
Kamar zai tayar dasu hadiye ya tambaye su sai kuma ya fasa ya koma ya kwanta
suna barin mazan su a gida su je wani guri su kara aure suna yi suna ziyarar su.
Abinda ya fado mashi a rai ke nan karfe daya agogon da ya kalla ya nuna mai da
sauri ya mike zaune biyu saura na dare yaji ana buga gidan maigadi ya bude kofa
motar ta shigo sai ganin nafisa yayi ta fito daga motar ta dan tsaya suna magana da
ta cikin motan.
Ta shigo gidan a gajiye take kafafuwan ta har sun dan kunbura saboda zaman motan
da tayi mai tsawo dakin su hadiye ta fara zuwa.
Ta samu suna barcin su hankali kwance ta ta da ita a cikin magagin barci tace
kin dawo da yare tace na dawo bata gane komai a guta ba ta juya zata shige tace
Alhaji ma ya dawo dazu da safe.
Dam taji gaban ta ya fadi da sauri ta fita zuwa dakinta ta kayan sihirin da ta
dawo take kokari boyewa a wardrobe din ta sai taga an kuna wutan dakin ta.
A fusace ta juyo sai ganin Abdulsamad tayi tsaye yana kallon ta da sauri ta kara
gare shi sai yayi saurin juyawa ya fice daga dakin .
Boye kayan ta karasa yi ta rufa mai baya ta murda kofan dakin a rufe taji shi
gam ta juya zuwa dakin ta ciki da fargaba da tsoro a ranta.
Washe gari ta samay alokacin ya gama shiri zai fita yana daura agogo a hannun
shi yana gani ta ya daure fuska tankar bai taba dariya ba a rayuwan shi.
Rudewa tayi tama rasa may ta fada mashi can dai tace Samad kayi hakkuri na san
ban kyauta ba na fita ba da sani ka ba.
Jakar laptop din shi ya dauka zai wuce ta zube kasa gaban shi tana fadi ka yafe
min gurin buki naje shine naka wanan lokacin ban dawo ba.
Nasan nayi laifi fita in dade baka nan amma kayi hakkuri haka ba zai sake faruwa
ba insha Allahu.
Yace don gani saunar na miji ki fita gida na kwana da kwanaki yanzu kizo kice
inyi hakkuri haka kai tsaye bayan kin gama yawon gantalin ki a can.
Kin kwaso kafan ki kin dawo min gida ki koma inda kika fito zai fi maki sauki na
baki minti awa daya ki fice a gidan nan da kowa naki.
Samad kayi hakkuri ka yafe min ba zan sake ba yace rufa min baki munafuka wace
bata san ciwon kan ta da darajan aure.
Ya sure jakkar shi ya fice a dakin da kyat ta iya mikewa tsaye daidai lokacin ya
dawo yana fadin fita min daga daki zan rufe abina ne .
Ta bishi da kallon mamaki a kofan tana tsaye ya rufo dakin shi karo na farko a
gidan abin ya mata zafi saidai cikin ranta tana fadin yi abin ka a hannu na zaka
dawo kwanan nan.
Ya fice ta bishi da kallo tare da juyawa ta wuce zuwa dakin ta tana mai jin
haushin shi.
Abdulsamad bai fada ma Nafisa zuwan mommy ba gidan sai cin karen su ba babbaka
suke ita da yan uwanta a gidan banza ta fadi masu kasa gasasa dama haka aladansu
yake yar su ta auri mai arziki dangi su kwaso a taru aci arzikin ta.
Mommy bata boye ma Anty Fati zancen tafiyan ta ba inda ta kirata ta fada mata da
bakin ta tare da cewa zatayi iya kokarin ta taga ta shirya tsakanin ta da mijin ta
kafin ta bar Abuja din.
Allah ya kiyaye hanya Fati tai mata tare da cewa mommy amma fa sai kin hada da
hakkuri don kun san Nafisa bata kaunar taga kowa ya rabi yaya Abdulsamad.
Abinda yakai ni shi zanyi idan tayi ba daidai ba dole ne in fada mata gaskiya
koda kuwa bata so dariya tayi don sanin halin Nafisa da tayi kamar yunwar cikin ta.
Tsaye yake tsakar falon inda yake umartan masu aikin da ya shigo dasu da su
gyara part din Fati yana masu kwatance yadda yake son gyaran.
Nafisa da ke barci a dakin ta Yanyala ta shiga mata da maganar cewa may ke
faruwa ne taga ana gyaran dayan part din da tace na uwar gidan ta ne.
Kamar ba cikine a jikin ta ba ta diro saman gadon ta fito inda masu aikin su nan
ta hausu da fada wayasa su aiki a gidan ta ba a fada mata ba.
Daga bayan ta ya bata amsa yana saukowa daga sama yace nine nan maigidan na basu
aiki suyi in biya su wani irin kallo mai kama da kai asuwa ta aika mashi.
Bai tsaya kulata ba sai kokarin shiga dakin da yake yi tasha gaban shi da sauri
ta tsare shi may kake nufi ne samad da wanan gyaran da akeyi ?
Yace abinda kika gani Nafisa shi nake nufi don gida nawa ne ba naki ba kamar
yadda kika fadi yanzu.
Nan hankalin ta ya tashi sai ta fara surutu ita may yake nufi da ita da zai mata
haka yace don yaga zata haihu zai dawo da fati da yaranta gidan shi.
Tace nasan dama kule kulen da ake shiryama ke nan kake yawan zuwa kaduna akai
akai yanzu dama ba so na yan uwanka keyi dani ba .
Shi dai bai mata magana ba don mazan dake gidan suna aiki ya fita batunta basu
raba hali a gaban su ba.
Hankali tashe ta kira madam tana fada mata abinda ke faruwa madam tace kika sani
ko watace zai dauko ya saka a dakin ba Fati ba ?
Nan hankalin ta ya kara tashi sosai tace Nafisa dam wanan tunanen baizo min ba
sai da kika tunatar dani haka yanzu.
Madam tace to zauna nan kina fada akan fati wata tazo ta shige dakin kina gani
saboda sakaci irin naki in zaki mike ki mike tun yaushe muka gama da wata fati can.
Wacce hudi daya mukai mata muka fitar da ita a gidan har diyan ta sai tarihin su
yanzu har kike tunanen ita zai mayar dakin ta.
Ke kasar ku fa zaki koma aiki kaifi sai Niger nan kusa kafin ma mu dawo aiki ya
kankama ko mu huta da ko wacece ma ke son muna kutse haka cikin ruwan sanyi.
Nafisa tace madam kin san ba zuwan ba kuma ba kudin nake jiwa ba don zan iya
saida da duk wani kaddara da nake da akan wanan aikin tunda yanzu na rasa gane kan
shi.
Matsala daya ne shine mutumin nawa yanzu kin san matsi yake min tun wanan tafiyan
da mukayi ondo ya kara burge min a gidan nan baya sake min har yanzu ga kuma
lalurar cikin nan dake jikina yanzu.
Madam tace ke dai kawai tawa ki nemi kudi in ma bai barki ba sai ni inje maki
manene amfanin zaman mu tare da ba zan iya maki komai ba.
Ai kawai ki daina damun kan ki mu za a gwadawa hanyar boka ko malam kuma ko
latsandan ne gaba da lahira indai ana zuwa zamuje shi.
Sai lokacin Nafisa tayi ajiyan zuciya taji dadi a ranta tana ganin aduniya bata
da kamar su madam dake tsaye a kan ta yanzu.
Tace uwar dakina Allah dai yaja muna nisan kwana tare ni nasan banda kamar ki a
duniyan nan yanzu.
Da wanan shawaran hankalin Nafisa ya kwanta nan ta shiga buga waya gida Niger ko
an samu wani bakon boka ko malami mai tashe a kasan.
Sai da ya ga komai ya kankama yadda yake so ya bar gidan bayan ya sallami
mutanen da sukai mashi aiki duk da yawan samari yan uwan Nafisa a gidan ba wanda
zaiyi bugun gaba dashi yayi mashi aiki alhalin biyansu yake duk wata dasunan aiki
suke mai a gida.
Bayan kwana biyu su mommy sun gama shirin su tsab ya tura Yusuf ya dauko su zuwa
garin Abujan mommy a gutin hajiya mama ta bar yaran ta tazo ita kadai sai iyan Bawa
da suka zo tare da wata yar mai masu shara budurwa don taimaka masu da wani abin.
Mommy sunyi waya da Ya Amina tana sallaman ta tace zata gidan Abdulsamad wanda
matar shi watan haihuwan ta ya kama zasu dan kwana biyu acan .
Ya Amina sai sulbul da baka tayi tace mommy ashe zaku hadu da Khadija na ke nan
mummy tace banda abinki khadija dake makaranta ina zan ganta ni ?
Sai dai idan sawa zanyi a dauko min ita ko akaini in gano maki lafiyan ta idan na
samu lokaci dariya kawai ta Amina tayi don ta san gidan su Abdulsamad basu san
komai ba a tsakanin mu dashi.
Tafiyan rana sukayi don haka sai da yamma lis suka shigo garin Abuja din direct
gidan shi suka nufa yana gida a lokacin don yana dakon zuwan su.
Nafisa wace ke falo tana shan iska ga yan uwanta a kewaye da ita kowa na shaanin
gaban shi sai sallaman su mommy da su iyan bawa suka ji .
Gaban tane ya fadi da ganin su mommy din gidan don bata taba zaton zuwan su ba
don a wautan Nafisa ta gama da kowa nashi yanzu babu mai marmarin zuwa inda yake.
Zuwan su mommy ba karamin faduwan gaba yasa ta ba sai take ganin ai zancen auren
da take zato ko dawowan Fati gidan gaskiya ne.
Shiya fito daga daki bayan sunyi waya da Yusuf ya sheda mai sun iso ya fito da
yar fara, a a fuskan shi yayin da ko kallo su mommy basu ishi Nafisa da yan uwanta
dake falon ba .
Shi da kanshiyayi masu iso dakin da zasu sauka din bayan dun gaisa sun mashi yaya
gida ya fito tare da Yusuf da ya shigo da kayan su ciki da taimakon wani saurayi.
Falon ya dawo inda suka samu Nafisa da yan uwanta sun juye harshe cikin yaren su
na buzanci suna maganan zuwan su.
Fuska a daure ya kalle ta yace Nafisa baki san mommy bane da gwago na iyan bawa
da baki tare su da zuwa ba ?
Tace a yatsune na san su mana ba matar mahaifin ka bane ita yace OK cikin wani
irin kallo har ya fara tafiya sai ya juyo yace tunda kin san ta kin san kuma matar
mahaifina ne baki iya taron su ba nima haka ban son in fita yanzu in dawo in samu
wa yan nan yan uwan naki a gidan nan yanzu.
Yana fadar haka ya juya ya fara tafiya tace wallahi baka isa ba don zuwan su
zakace yan uwana su bar maka gidan ka yanzu yace zaki san na isa idan yan sanda dun
shigo sun fitar min dasu.
Idan akwai abin da yan Niger sukaki jini shine dan kakin Nigeria don basu yi masu
da wasa idan sun farmake su.
Nan Yanyala ta fara magana tace haba Allaji ai bin baikai can ba daga dan wanan
magana har zaikai ka kira muna polizawa kawai dai jira muke su huta mu mika masu
gaisuwan mu.
Ya fice zuwa nemo ma su mommy abinda zasu ci a gidan don yasan ba zasu iya taba
cin abincin da suka dafa ba.
Bai dauki lokaci ba ya dawo dauke da ledoji iri na restaurant dauke abinci dasu
ruwa a ciki ya bayar aka shigo masu dashi har dakin.
Mommy ta idar da sallah sai ga yaron shi isyaka yana shigo da kayan ciki tare da
gaba tar masu da abincin.
Sunka ce har da dawai niya zuwa sayo abinci kuma nan dai iyan bawa ta kasa
hakkuri tace zainabu may kika fahinta ga wanan zaman ?
Murmushi mommy tayi tace ke dai iyan bawa ai ayi shani kawai wai ancuci na kauye
wanan matar bata da hali ko kadan.
Kin dai fara ganin makasudin zuwan mu garin nan ke nan don fitar shi kunyan
abokan shi nasan halin matar nan tashi dakilace na gani a fada.
Ba zamu sakar mata fuskan da zata kawo muna raini ko wulakanci ba don nasan tun
zuwan mu batayi farin ciki da ganin mu ba.
Sunci abinci sun huta sai ga Nafisa ta shigo tayi wanka ta saka sutura a jikin ta
yan uwan ta suna mara mata baya suka shigo dakin.
A falo suka samay su nan ta ja ta tsaya bata zauna ba tana fadin kunzo lafiya ya
hanya da mutanen gida ?
Mommy tace lafiya duk suna gaida ku yaya nauyi Allah ya rabaku lafiya tace amin
sauran suka shiga gaida su da yi masu ya hanya suka fice daga dakin ba wanda ya
zauna.
Shiko bayan ya mika sakon wuri na ya nufa kamar yadda ya saba zuwa man koda ya
kirani muna tare da maryam da zarah a dakina kiranshi ya shigo min.
Mutumin ki ne halan yazo maryam take tambayana nace cikin tabe baki shine ai kin
san bai tashi zuwa min sai wanan lokaci.
Maryam tace ai kuna daidai dashi in kin isa ki fadi a gaban shi yana da amsan
baki indai wanan yaya in love din kine.
Kai maryam kina da wuyan sha,ani wallahi na fada maki ba soyayya a tsakani na
dashi sai amin taka kawai na damuwa.
Zarah ta dago kai tace min wani guy kuke magana muje in gani idan ya min in saka
shi a layi mu shiga sha,ani dashi.
Zarah wai ke baki jin kunyan fadin fitsrane haka tace in banda abinki wake ta
wani wasa da so yanzu khadija bari kiyi wasa da daman ki yanzu yan jami,an nan suyi
maki wuf dashi.
Idan banda abinki an fada maki kowane yan matan jamia ke iya wuf dashi kai daya
zarah wanan ya wuce sanin ki wallahi.
Dariya tayi tace muje inga guy din nan dai da kuke wani zuzutawa haka dai
murmushi nayi kawai don ba zan so a ganni da ita ba.
Duk da ba wani shiga na yi ba amma suna ta yaba kyau da nayi wai na hadu zarah na
fadin ashe zaki zama yar hannu haka khadija.
Tare muka fito dasu sun zo su gaida shi tunda muka tunkare shi zarah ta tsunke da
ganin motar da yazo da ita tana fadin tun ban ga guy din ba wallahi nasan zai hadu
ko don motar nan da nagani how lucky you are da kika iya canko wanan zukeken guy
haka.
Mun iso yana ta faman ansa call a wayan shi sai da zarah ta kare mai kallo ta
dago bayan ya gama wayan suna gaida shi bai wani sake fuska ba ya amsa gaisuwan.
Tare da kawar da kanshi gefe daya zarah tace dama na sani sai irin wanan guy din
khadija wanan jan ajin naki yayi yawa wallahi har ta gama ta wuce bai yi magana ba
suna shiga maryam ta nufi dakin ta.
Maganar shi ta farko bayan wucewar su shine ina kika samo wanan kawar kuma ?
Nace a inda ka gan mu yanzu yace No ba girman ki bane da mutuncin ki yawo da
irin wayan nan nace kawatace fa tare mukazo karatu daga gida.
Na fada maki bana son in kara ganin ki tare da ita please na juyo ina kallon shi
ido cikin ido nace tana da aibu ne komay ?
Au ke baki ga aibu ta ba wanan bata da kamun kai ba girman ki bane yawo da ita
nace ka taba ganin mu a tare ne ko yanzu ma daurowa tayi ka gan mu da ita.
Har ya bude baki zaiyi magana sai kuma yayi shiru nima shirun nayi ba wanda yayi
magana daga cikin mu.
Can naji yace idan na fada maki wani abu zaki yarda dani ?
Zaki yarda gaskiya nake fadi.
Murmushi nayi nace idan maganar ta kama gaskiya mai zai hana nayarda tunda nasan
gaskiya ka fada.
Kin yarda dani khadija ?
Nace na yarda dakai mana yaya Abdul fati da mijin buzuwa ina fadi ina mashi
dariyan shakiyanci cikin gatse.
Shima murmishin ya dan yi wanda sai wanda ya sanshi zai iya fahintar hakan daga
gare shi yace kin san kamun kan ki yasa muke tare da ke har wanan lokacin.
Kasan ni ne da zaka wani ce ina da kamun kai bayan iyakar mu dan wanan
haduwan da muke yi.
Na tsinci muryan shi yana fadin niko na sanki khadija you are classic baby da na
taba haduwa da ita a rayuwana.
Katse shi nayi da fadin may ke faruwa daksi haka ne wai ke irin wanan magana
yanzu a kai na ko last zuwa da kayi haka ka dinga min wanan maganganun.
Ya girgiza min kai tare da fadin ba komai cikin lumshe idanuwa shi sai kuma ya
bude su ya sani gaba yana kallo na.
Shirun motar na kawar da fadin yau ba fita ke nan yace ina kike son muje nace
inda ka saba zuwa mana mu zaga gari kawai kana barnan man motar ka.
Haka kika dauki fitan namu dama nace hakane mana tunda ba wani guri muke zuwa ba.
Ke ce baki fahinci muhinmancin fitar namu ba kila amma ni yana da ma,ana masu
yawa a gare ni matuka khadija.
Don kasan cewan mu a tare you have change me now na fahinci su abubuwa da dama
da ban taba fuskantar su ba a baya.
Maganan gaskiya yau kin dawo min da farin ciki rayuwana har iyayyena sun zo gida
da sunan kwana biyu a wuri na.
Da sauri nace cikin murna wai da gaske kake yi yace kwarai kuwa deeda don yanzu
haka mommy da gwagona iyan bawa na gida maganan nan da muke yi dake.
Taya kike ganin bazan maki godiya a wanan kangin da nake ganin kin fitar dani
wanda a da nake dauka da shirmay irin naki na yara kike yi.
Sun kuyar da kai nayi kasa ina tunane hankalina yayi nisa bani jin abinda yake
fadi tsoro na daya ne kada mommy tasan ina tare dashi ta fasara haduwan mu a wata
manufa.
Ban sauri maganan shi ba na katse shi da fadin zan roke don Allah kada ka bari
mommy tasan kana zuwa inda nake don bansan da wani ido zan kallesu ba har hajiyan
ka.
Ya lura da irin rudewan da na shiga sai dai baice min komai ba ganin bai yi
magana ba yasa nace please yaya Abdulsamad ka boye wanan a matsayin siri a tsakanin
mu don Allah.
Kallo na yayi ya sauke murmushi yace saboda may kike son kada su san ina tare
dake nace dashi wayyo Allah kana son su dauke ni yar cin amana ne ko may ?
Cikin sanyi murya nace kasan su ba zasu gane mutunci ke tsakanin mu ba sai su
dauka muna tare da wani manufan da bashi ba.
Hakan kuma yana nufi na ci amanan su ke nan gama yadda suke son Fatin ka a gidan
yanzu kuma sai su gan mu tare yaya kake ganin zasu dauki abin.
Kai tsaye yace zasufi kowa farin cikin da hakan na sani tunda sun san ki sun san
halin ki zasu yi farin ciki da hakan.
Daga yau magana ya kare ba sauran wani abu a tsakanin mu tunda bukatar mu ya
biya ka shirya tsakanin ka da yan uwan ka.
Mamaki magana na ya bashi yace juyo yana kallo na sai can yace ai deal namu bai
kare ba tukun ko kin manta baki karasa aikin ki ba akan fati ?
Na amsa da fafin kwarai bamu kai nan ba cikin takaici nace wana kuma yanzu ya
rage gare ka sai kasan yadda ka shirya da matarka.
Ba wani sauran magana yanzu a tsakanin mu kuma na fada cikin tsiwa ya juyo da
kyau ya kalle ni yace don mommy tazo duk kike fadan wanan magana ko may.
No ba don tazo ba in ma don tazo din ne haka ne bana son su dauki abinda wani
fassarane kawai.
Ya zura min idon sa yana kallin yadda duk na rude yace a ranshi ashe karyan rashi
kunya nakeyi a da gashi yanzu daga jin mommy tazo duk na bi na birkice lokaci daya.
Motar tayi tsit kowa da abinda yake tunane a ran shi sai da ya shafa kan shi
naji yace relax deeda wace dake mommy zata san da wanan maganan dake tsakani mu
wai ?
Wata zuciyane ta bashi shawaran ya min wayau kawai don yadda na rikece din nan
daga jin mommy tazo zai iya sa komai ya faru idan ya biye min.
Kawar da zancen yayi da fadin zuwa nayi ki ban shawara yaya zan yi da Nafisa don
batai farin ciki da zuwan nasu ba yanzu haka.
Da sauri na dago kai na kalle shi da idona da suka sauya kala nace baka fada mata
zancen zuwan su bane dama , ?
Kai ya girgiza min yace ban fada mata zasu zo ba tunda ba itace ta aje ni ba yan
uwan ta dake zuwa ai ba fada min take yi ba itama.
Kada kaga laifinta a yanzu don kai kai sake har haka ya kasance tun farko saboda
tsoron ta da kake nuna kanayi da farko.
Ba tsoran ta nake yi ba deeda kaunane kawai na tsakanin miji da mata wanda ita ta
dauka tsoron tane yasa nake mata hakan.
Sai yanzun kasan da wanan yana iya faruwa ka manta a lokacin da take saka abu
kana mata shi koda kuwa baka son abin ?
Ya gyara zama yana fadin shine babban kuskure dana tabka a farko wanda nake
nadaman yi shi a yanzu haka.
Duk abinda zakayi ko zatayi kada ka bari rainin matarka yakai ga iyayyen ka don
ko zaka iya canza mata amma ba zamu iya canza iyayye ba.
Wai ke wake koya maki wanan hikimar haka nr ya tambaya cikin son in bashi amsa
nace baka son maganan ke nan.
Yace No idan ban so ai ba zan fada maki zuciyana na ba a yanzu don da zuwan su
abinda tayi masu yaci min rai sosai ba zan boye maki ba don yanzu ke ce abokiyar
shawarata shiyasa nazo maki da zancen.
Yaya zanyi khadija ina son in fita daga cikin dana shiga a bayane gida na yanzu
bana son su mommy su fahinci sakaci na a gida na.
Nace na yaushe kuma saidai kada a kara muma makwabta ku mun sanni balle su mommy
dake gidan tare ku.
Ina son mata na khadija shiyasa har haka ya faru da ni kallon shi nake cikin
mamakin kalamin shi na wai yana son matan shi da yace.
Shin shi wani iriin mutum ne wai nace nafisa dai kake so amma baka son fati kowa
ma yasan da hakan ?
Haka kuke tunane ya fadi cikin zafin zuciya amma ita ai tasan ina sonta halin ta
ne kawai baizo daya da nawa ba shine matsalan mu.
Kalon shi nake sororo kamar na samu tv da alama yarasa yaya zaiyi da damywar shi
ne ya tsinci kanshi cikin fada min sirin zuciyar a matsayi shi na mutum mai
shekaru kamar shi.
Tausayi ya bani don na fuskanci bayan Yusuf da suke tare baida wani wanda zai
fada ma zuciyan shi ya fahince shi shiyasa yazo gare ni.
Nace wallahi rayuwan ka na cikin hadari ya kamata ka koma ga Allah kayi abinda
Allah yace shine kawai mafita a gare ka.
Lokaci ya duba yace zai tafi lokacin sallah ya gabato zai dawo gobe tunda ba
school mu karasa tataunawa mukai sallama ya tafi ya barni cike da tausayi shi.
Shiko yana fita tun a falo ya fara ganin sauyin da gidan nashi ya samu da zuwan
su mommy din ga gida ya koma neat a lokaci daya a falo ya hango su hadiye suna
kuskus a cikin yare suna ganin shi suka shiga gaida shi.
Fuska a daure take amsa masu ya wuce part din su mommy din wanda anan fati da
take zaune da yaran ta ganin haka yasa ya tuna da abubuwa da dama na rayuwan su a
baya a gidan.
Kagin zuwa yanzu da komai ya hargitse mashi haka wanda kan shi yanzu ya dorawa
laifin kasancewar haka kamar yadda na fada mai.
Ya samu su mommy sun yi wanka suna karyawa a cikin tsanaki ya shigo da sallama
ya gaidasu tare da masu ya gajiyan hanya.
Mommy tace gajiya ai yabi lafiya don mun zama yan gari yanzu ko yace mommy duk ku
kukai wanan gyaran haka a gidan nan ?
Tace ba dole ba babangida gida ya koma kamar ba mata a cikin sa kasan mu mun
saba mijin mu baya son ganin kazanta ko kadan.
Iya bawa tace mai ni ina mamaki gida da mata haka ace bai samun gyaran da yadace
mace ta yi a gidan ta wanan matar taka akwai bakin son jiki ne da ita.
Ciki ai bai hana ka gyara muhalin ka sai dai dama idan gyaran bai damay ka ba can
amma yaushe ne mace kirki zata bar gidan ta haka ?
Mommy tace ga abin kari can a kitchen idan ta fito sai ta raba maku ka karya
kafin ka fita yace mommy zuba min zanci anan gurin ku don bata fito ba ko ina sauri
ne.
Anan ya zauna ya karya tare dasu yana mai jin dadi a ranshi yaushe rabon da ya
karya a gidan shi haka cikin dadin rai.
Bayan ya gama yayi masu sallama tare da tambayan ko akwai wani abinda suke bukata
a gidan ya sayo masu idan ya fita.
Mommy tace sai kayan kitchen din da taga sun soma lalacewa saboda rashin amfani
dasu da ba a yi akai akai yanzu dole a sayo wasu yaje matar shi tai mashi lissafi
don gudun su shiga mata hakkin ta.
Bai koma takan Nafisa ba ya fice gidan inda ya samu Sani driver yana jiran shi a
waje suka dauki hanyar zuwa office din su.
Barci nake a dakina tun dawowana class wayan shi ne ya tayar dani daga barcin da
nakeyi nayi mamakin kirana a wanan lokacin da yayi.
Bayan na karba mun gaisa ne yake tambayana idan maryam tana nan don Allah zai
aiko Sani driver shi mu taimaka mu sayo mai abin girki a gidan shi.
Da sauri nace mai kaga malam bafa zaman ka nake a garin nan ba da zaka dora min
nauyi irin haka a kaina ina matar ka kaje ka tura ta ta sayo ma mana .
Don Allah kiyi hakkuri ku taimaka min for today only naji nace na kalli maryam
dake barci nace yanzu yau friady muna hutawan mu ya dauko wahala ya dora muna kuma.
Ban sake komawa barci ba motsina ya tayar da maryam nan nake fada mata abinda ya
bukata da mu tace to may ye a hakan khadija ?
Ai taimako ne kin san matar shi ba wani wayewan kaine da ita ba kuma kin san
gata da ciki baki yanzu nace wanan ai ba excuse bane.
Son dorawa mutane wahala kawai yake yi don kada a zauna lafiya muna zaune kalau
zai dauko wahalan gidan shi ya dora muna.
Kin san may khadija nace aa cikin kada kaina tace walahi sai nake ganin wanan
Abduldin yana bukatan taimako a rayuwan shi.
Bai samu macen da ta dace da irin halin shi bane har yanzu yasa komai yanzu yake
bukatan taimakon ki ban san yaya zaiyi ba ranan da zaku rabu dashi tunda kince ba
soyayya bane a tsakanin ku.
Nace ai ke kin fi kowa sanin hakan shiya san yadda zaiyi don ni bashi ne a gabana
ba karatuna ne ya damay ni inga na kammala Allah yaban sa,a in samu aiki da wuri.
Duk da haka khadija akwai matsala ranan rabuwan ku kan inda ran mu zamu sha
kallo nace in babu sai abaku labari ai.
Tace labarin taimako ya juye ya zama soyayya haushi maganan ta yabani ban samu
bata amsa ba naso ta biye min kada muje ko ina ya karata can da halin shi shiya
sani.
Karfe uku bayan an fito sallah jumma,a sai ga malam sani driver yazo daukan mu
nan yaban kudin yace wai zamuyi waya dashi.
Muna hanya ya bugo min yana fada min duk wani abinda muka sani ana amfani dashi a
fannin girki har nama da kaji da sauran su mu sayo mommy ne ke bukata a gidan.
Kai dama duk wanan abin ba a saya a gidan ka may kuke ci a gidan silly girl ya
fada ya kashe wayan shi naja tsuki.
Mun shiga kasuwa maryam tayi kaca kaca da kudin komai mun hada sai yamma lis muka
baro cikin kasuwan inda ya fara sauke mu a hostel ya wuce bayan hilux din su acike
muka bashi sauran kudin shi ya kai mashi canji.
Wanka nayi tea kawai nasha da nai sallah muka samu wuri muka kwanta don gajiyan
da muka debo a kasuwan bamai taimaka wa wani a cikin mu duk a aikin sa kai da
mukayi.
Barci yana batun dauka na wayan shi ya shigo min jin murya na yasa yace har kin
fara barci ne ko may ?
Nace ba dole ba yau an samu wahalan da ba namu ba lada ba zunubi sai tarin gajiya
khadija ke wace irin yarinya ne wai da ba tsoron fadin magana a bakin ki ?
Yanzu dai ba wanan ba don may kuka ba sani ragowan kudin da ya rage yakawo min
kuma ya fada min komai baku sayo wa kan ku ba ku.
Saboda ba hakkin mu bane yasa muka bashi yakai ma kudin ka don Allah barni na
huta malam gara da kai kana da madafa.
Murmushi naji yayi yace ina dashi tunda ina da matar da zan runguma inji sanyi
ke ko sai dai ki kama filon ki ko ?
Kaidai ka sani nace mai sai da safe yace ba zaki tsaya nayi maku godiya ba zaki
kashe min waya ?nace ai ba don ka gode muna muka taimaka maka ba na kashe wayan
gaba daya.
A gidan shi ya iso da kayan akai ta shiga dasu ciki shi kanshi yayi mamakin yawan
kayan da muka sayo din ya kira Nafisa kafin ta sauko ya kira mommy da kanshi kan
tazo idan akwai abinda babu sai a sayo gobe.
Nafisa na zuwa mommy tana fitowa tare dashi yake tambayan ta ta duba ta gani
ranta a bace tace komai yayi sai mommy tace komai an sayo sayayya haka kamar na
mace.
Nafisa da ta juya zata tafine ta juyo da sauri ta kara kura ma kayan ido tana
kallo kayan da bata kalla ba da farko saboda idon ta ya rufe da masifa a lokacin.
Maganan mommy ne ya tsaya mata a rai da tace sayayya kamar mace tayi komai an
saya yadda ya kamata ta kira hadiye da yanyala wai su kawar da kayan wurin tana
daure fuska gata mai gida.
A daki ta samay shi zaune lokacin muna waya tace gurin ka nazo ya aje wayan da
na kashe yana kallon ta ta samu guri ta zauna da kyat.
Tausayi ta yaji ya dirka mai a zuciya tace may kake nufi da baka shawarce ni ba
ka sayo wanan kayan haka sai da kasayo abinka zaka kirani.
Yace saboda baki damu da asaya din bane yasa na sa a sayo min tace wace yar iska
ce ta sayo ma cikin kura mashi ido da son jin amsa daga gare shi.
Wanan ba matsalsn ki ba ne ke dai kiji da kanki ya fada mata yana kokarin mikewa
tsaye samad mai kake nufi dani ne wai ?
Da akayi may kuma yanzu tace ban fa gane inda ka dosa ba gaskiya da irin wanan
halin naka yace saboda baki son gaskiya ne yasa na canza nima.
Kana nufi nice mai laifi yanzu aike ma kin sani idan kina son mu shirya dake to
ki canzs ke ma yaushe rabon da na karya a gida na in ba yau ba da mommy tazo.
Dama nasan abinda ya kawo su ke nan ai hadin fada a tsakanin mu in bashi ba may
zai sa su kwaso kafan su suzo nan wai sai na haihu.
Yace saboda ina dan su kuma ni na bukaci haka a gare su tunda ke baki san komai
ba sai bakin yawo da lalaci kawai da kashin kudi.
Nice mai kashin kudi murushi yai mata yace ko yanzu ma nasan amsan kudin ne ya
kawo ki ai ba wani abu ba tunda baki damu da damuwa na ba.
Kaine dai ai naga kamar kana gudana yanzu nan dai suka shirya ranan ace tsakani
miji da mata sai Allah suka manta da komai a ransu.
Washe gari mommy ta sake hada masu break fast mai rai da lafiya tasa Aisha ta
gyara dining din aka jera kkmai a yadda ya dace ta aikawa su hadiye da nasu.
Tare suka sauko suka karya a tare sai hadiyan abincin take ba kunya ko wani nauyi
a tare da ita bayan sun gama ya fita zuwa wurin aiki.
Sai lokacin Nafisa ta kalle gefen dakin da su mommy ke ciki ta kira hadiya ta
rufe mata kofan kitchen da store din gidan gaba daya.
Da rana mommy ta turo Aisha ta gyara mata kitchen din sai ta samu gurin a rufe
ta koma ta fada ma mommy.
Mamaki ne ya kama mommy ta kira hajiya mama tana fada mata abinda Nafisa tayi
masu ita kuma mama ta kirashi inda take shiga ba nan take fita ba tace maza ya dawo
dasu gida tunda yasan gidan shu ba a hannun shi yake ba ya dauke su.
Hakkuri ya fara bata yace zai dauki mata hakan tace ya yake son yi idan Abban su
ya samu wanan baki labarin dama abinda yake ma gudu ke nan ya hana su zuwa tu
farko.
Hakkuri ya dinga bata har ta saurara mai tace tana jiran taji matakin da ya dauka
a gidan idan ba haka ba zata fada ma Abban su abinda ke faruwa kada yaji a gurin
wasu.
Yusuf yana zaune yana sauraren su yana kashe waya ya dago idon shi da suka kade
sukai ja yace wai may Nafisa take nufi da nine ?
Guri ta samu take wanan abin mana Yusuf ya bashi amsa yace in bashi ba rashin
mutuncin nata har yakai ga su mommy kuma yanzu.
Mommy ne zata rufewa dakin girki bata girka ta basu ba basu damu ba suna yi kowa
kuma yaci har zata rufe kada suci su kwana da yunwa komay ?
Tasan yadda Abba yake ji da iyalin shi kana zaton da ba mommy bace in anty amarya
ce Abban zata kira da kan shi ta fada mai kasan ko yau ba zata kwana gidan ka ba.
Wallahi idan zaka kara aure ka kara shine kawai mafita ga wanan shu,umar mace da
ka dauko wai mata bazata taba ganin darajan ka ba idan ba ta bude ido tagan ka da
wata mace ba a gidan.
Idan tana zama ta zauna in bata zama kuma ta kara gaba dama ba akirata ba kutse
ne da sa kai irin su ta kallamay kada dadin baki da komai ta aure ka.
Kai yace tare da bugun tabur din gaban shi ya mike cikin fushi Yusuf yace ina
zaka kuma yanzu ?
Gida yace cikin wani irin murya kamar mau zazzabi shima mikewa yayi ya bishi a
baya tare suka fita daga office din shiya jasu don Abdul din bai da karfin haka a
yanzu.
Suna tafiya yana dafe da kanshi ba tare da ya kalle shi ba Yusuf din yace ba
irin ku masu sanyin hali ne ya kamata ya auri irin Nafisa ba.
Sun fi daidai da irisu wa yanda zasu caja junan su a zauna lafiya amma ai dama
ita haka suke so su samu wanda suke juyawa son ran su.
Yanzu ai ta fara koya min iya magana ita da wanan yar matsalan khadijan din nasan
idan an auna ni za a samu VP dina ya hau wallahi Yusuf damay Nafisa take son inji
ne wai ?
Idan da sabo na saba izuwa yanzu haka kawai zai zo ya dauke ni a mota sai dai mu
zagaya gari ya dawo dani ya aje ya wuce makaranta.
Yau ma da yai kwana biyu bai zo inda nake ba komai na tafiya a guri na normal sai
dai zan iya cewa haduwa na dasu ya bude min wani sabon babi na rayuwane.
Duk da nake yarinya kuma mace ban yarda na fara hurda dasu ba sai da na karanci
rayuwan su nagane zama dasu ba yana nufin jefa ni a gurbataciyar rayuwa bane.
Yauma ina daki kwance ni kadai ina nazarin wani littafi don sabon da nayi da
yawan karatu sai dai ance sabo turken wawa ne don har na dan fara shiga damuwan
rashin ji daga gare shi kwana biyu.
Waya na da yai ringing na juya ina kallon mai kirana a lokacin ganin sunan shi a
screen din wayan yasa na dan sake murmushi sai da naja mai aji na dauki wayan.
Da sallama na fara magana ya amsa min yace kina hostel ko kina cikin makaranta ne
nace ina hostel yanzu fito ina waje yace ya kashe wayan shi.
Na shirya cikin wani dogon riga mai dan hannu shara shara riga yana dan matse
kadan daga saman shi kasan shi a bude.
Kai tsaye daga inda yake zaune a motar yana sana,an shi na hango shi cikin motar
ya mayar da hankalin shi sosai ga abinda yake yi.
Tun da ya dago kai ya hangoni tafe ya daina abinda yake yi ya tsura min idanuwan
shi masu kashe min jiki da zuciya haka ya sake min su tankar wanda ya samu tv har
na iso gare shi.
Daga waje na gaida shi kamar wanda baiji ni ba yayi sai bude min motar yayi da
alaman in shiga kai na daga na kalle shi carab muka hada ido dashi.
Nan nace dashi karatu nake fa yallabai ka kirani yanzu yace shiga mu tafi na
sani ai.
Tambayan shi nayi da ina zamu tafi tare da kashe shi da idanuwana dasu ke
rikitashi idan ya kalla.
Sayar dake zanyi yace murmushi nayi nace ai dako kayi babban kamu yau galleliyar
yarinya kamata ba karamin kudi zaka samu ba ko.
Nace yanzu ya kamata ace kana wurin aiki ka ko gida kana hutawa dan murmushi ya
sauke tare da fadin.
Bazan iya zama gida ba ne yanzu.
To ka koma office yanzu mana tunda lokacin aiki bai kare ba don nima karatu nake
yi yace don Allah ki shigo mu tafi kona fito na daukeki in sa a mota.
Nayi saurin nuna kaina nace ka dauke ni sai kace wata yar tsana ko matar ka can
da zaka dauke ni.
Don Allah shigo mu tafi kin sa mutane suna kallon mu na dan juya naga wasu yan
mata dake gefen mu sun kura muna ido.
Dole na bude motar na shiga ya tayar da motar muka bar gurin sai da mukai nisa ne
naji yace may yasa duka mata wani lokaci halin ku daya ne wai ?
Na bata fuska tare da dan kallon shi nace haba mijin buzuwa da alama yau baka
cikin dadin rai kake hango matsalan gidan ka ga kowa.
Kada ka danganta abinda ya hada ka da matar ka dani don bai shafeni ba ko kadan
yanzu ma banga abinda nayi da zaka fadi haka ba.
Yace nima ban san dalili kawai dai ina hango hakane gun ko wace mace kamar
halinku duk dayane wani lokaci.
Nace baka canka da kyau ba malam ai kaji ance mata suna suka tara .
Ya kalle ni ya girgiza kai yace bazan iya tabbatar da haka ba sai na gwada don
naga biyu halin su daya basu damu da damuwan mutum ba kansu kawai suka sani da son
abinduniya.
Wow i am impress dama haka ka dauki mata a ranka ashe ?
Yes sai dai ban sani ba ko kamar yadda kika fada inke din ta daban ce don na dan
ga alama haka.
Shiru mukayi duka a motar sai can yace cikin langabar da kai please khadija kiyi
hakkuri ki fahince ni don yanzu bani da zabi sai wanan tunanen.
But sai dai ban san may yasa ba nake yawan son in kasance a tare dake muna irin
wanan tafiya tare da shammatan junar mu.
What na fada cikin mamaki da rashin fahintar maganan shi tare da fadin me ye
maanar hakan a gare ka may yasa sai nice zaka ji dadin fada dani ranka yai maka
dadi.
Don haka kaje ka dauko ni a lokacin da nake a tsakiyan karatuna don kawai son
fitina kace wai kana son muyi ta shammatan juna kana jin dadi.
Murmushi yayi yana fadin bazaki gane ba ne khadija hakane kawai farin ciki na a
yanzu a take na daure fuska tare da fadin maidani inda ka dauko ni don Allah.
Haba mana khadija may kike fadi haka ke nan baki bukatan ganin farin ciki na ne
komay yanzu fa kika gama fadin mata suna suka tara da bakin nan naki.
Nace da ban dauka farin ciki kaka samu daga yin haka da nake maka ba ai na dauka
bacin rai nake sakaka.
Hummm yace sai ya juyo ya kalle ni yace to indai ina da wani matsayi a gare ki
yanzu dai ki zauna mu tafi.
Ba yadda na iya haka na koma na zauna tare da kawar da kaina gefe daya yace yanzu
na fara sanin ashe suna kuka tara.
Tunda gashi na roki alfarma a gurin ki kin yi min abu biyu ke nan na fahinta a
gare ki yanzu zaman mu tare da ke.
Nace wanan bata min lokaci na kawai kake son yi a banza bayan kasan ina da abinyi
a gaba na yanzu.
May yasa zan so bata maki lokacin ki haka bayan nafi kowa sanin amfanin abinda
kike yi yanzu.
Yanzun dai mubar wanan magana may kadauko ni yi a yanzu ne don Allah na tambaye
shi tare da kura mai ido ina son jin amsa na.
Wanan lokacin da wanan yanayin yafi min ko wani lokaci jin dadi a rayuwa na yanzu
matukar ina tare da ke khadija.
Kece mace ta farko da nafi jin natsuwa idan ina tare da ita khadija ya juyo ya
kalle ni tare da fadin kin san may yasa nace haka ?
Kai na girgiza mai cikin sanyin jiki alaman ban sani ba sai ya fada dai zan sani
daga gare shi.
Yayi murmushi ya kalleni yace kin san yadda zakisa zuciyar mutum ya sake ba tare
da an rabu cikin bacin rai ba khadija.
Ina jin dadin hakan da kike min ke ta daban ce da sauran matan zan iya yarda a
yanzu saboda wasu dalili da na kafa akan ki.
Wani dalili ne haka na tambaya da sauri tare da kallon shi yace baki taba rokona
wani abuba khadija alhali nasan kina da bukatan abubuwa da dama tunda kin san ina
da halin shi.
Na nuna kaina nace ni in rokeka kuma akan may zan roke ka bayan nasan rabo ne
idan rabona ya ratsa a kan ka zaka bani ko ban roka ba.
Good girl tafiya zatai dadi a tare dake kuwa tunda kin san haka she nayi saurin
fadin ashe kai marowaci ne ke nan ga mata ?
Ya dan lumshe ido yace ko daya wallahi na dai fi son inyi abinda ba sai an roke
ni bane sai dai ina haduwa da matan da basu da hakkuri ne khadija.
Ban san lokacin da baki na ya bude ba nace kana nufin har da anty Fati haka take
yaushe ma ta samu gurin roko a wurin ka kai ?
Ya na tukin shi hankali kwance ya murmusa yace kin ga yanzu ma kin fada da bakin
ki yaushe na kula ta balle ta samu tambaya na ?
Haka kowa ke gani khadija shiyasa manya sukace tsakanin miji da mata sai Allah
wanan abin na bar wa kaina sani kawai.
Daga ya mayar da kanshi ga titi yana ta tuki a hankali tare da shakan isakan dake
kadawa a lokacin may hade da kamshi kasa wanda ke nuna dama na son sauka a lokacin.
Ba wani guri mukaje ba sai yawata garin da mukayi kawai ya dawo dani hostel ya
aje ba tare da na tsaya ba na shige kai tsaye yaja motar shi ya tafi.
Ban san mun shaku da shi ba sai wanan karon ga jerabawa ya na gaba to muna ga
zancen zuci dake damuna haka ya dan sani rama kadan.
Karshe nabawa kaina shawaran abinda ka fisheni na watsar da komai na rugumi
karatu na gadangadan ina yi tare da share zancen su gaba daya a raina.
Ranan muna zaune da Maryam a dakin ta tsifar kaina na ke da ya kitso ya tsufa min
zan je in wanke kai na wayana yayi tsuwa na duba Yusuf ne a kan layin.
Nayi mamaki kwarai da ganin kiran shi a wanan lokacin na dauka da sallama tare da
gaida shi ya amsa yana fadin kanwa ta ina kika shige haka ?
Kai yaya Yusuf ina nan inda nafi karfi mana na bashi amsa yace ko dai mutumin
nawa ya boye muna ke ne ban sani ba ?
Wa ke nan kake magana nima na tambayeshi yace abokina mana kuma ogana a wurin
aiki nace wai mijin buzuwa kake magana ?
Dariya ya kyalkyale dashi yace kai khadija baki da dama wallahi har yanzu dai
mijin buzuwa aiko zaku kwasa dashi idan ya jiki.
Nace ina ruwa na dashi balle balle ya jini .
Yace ke ko keda ruwa dashi khadija yar mama amma dai baki da kirki Abdul din ne
zaki ce yau ina ruwan ki dashi da bakin ki kike fadin haka .
Tsuki naja na tabe baki kamar yana gani na a lokacin nace ni na fita batun shi
yanzu banda lokacin shi.
Yace subbahanallahi may yai zafi haka ne a tsakanin ku kuma keda mutumin naki
khadija ?
Mutumi na ko naka yaya na kai nifa ko wancan lokacin da nake kula shi albarkacin
ku ya samu a gare ni har na biye mashi amma ba don shi ba.
Kai haba yar mama bai dace ki fadi haka ba tsakanin ki dashi yanzu ai kunyi nisa
sosai bai kamata aji wanan maganan ba a bakin ki.
Taimako fa kikace zakiyi sai da abu ya kusa kai karshe zaki ce ba ruwan ki dashi
yanzu ai ko kece mai ruwa har da tsaki akan shi yanzu.
Mu dai bar wanan zancen nace dashi da sauri yace akan may zamu bari idan na
tambaye ki zaki fada min gaskiya ?
Nace akan may ke nan yace akan mutumin naki mana nace idan na sani may zai sa na
boye maka kuma ?
Yace Yaushe rabon da yazo gurin ki ko kuyi waya dashi when last kukayi koda waya
ne please kada ki boye min komai just feel free with me khadija?
Dan jin nayi sai can nace gaskiya mun kwana biyu dashi don ba zan iya tuna zuwan
shi gurina ba na karshe ko wayan shi a yanzu.
Yace abinda nake son ji ke nan daga bakin ki sai dai zan ari bakin aboki na inci
mashi albasa Abdulsamad yayi tafiya two weeks ago amma dai yanzu ya dawo.
Sai dai ko a yanzu da bukata nazo maki a kan shi don gaba daya khadija ba zan
boye maki ba Abdulsamad ya canza ga komai cikin yan kwana kin nan.
Gashi matar shi na shirin haihuwa watan ta ya tsaya tun last month sai dai har
yanzu bata haihu ba yana gida ko wani lokaci tunda ya dawo like da ita.
Katse shi nayi da fadin ni may ye nawa a cikin zancen nan kuma can su karata shi
da ita tunda shi ba tsayayyen namiji bane ko yaushe.
Namiji ne mana khadija ai shiyasa na kiraki don ki sheda mai cikin wanan wasan
da kuke yi don ya farga ga abinda yake yi din.
Ni tsoro na shine kada su mommy daya dauko gidan shi su fahinci susucewar shi a
kan wanan shuumar matar tashi sugane gazawan shi a gaban kowa.
Shiya sani mana tunda shi ke ji a jikin shi ba wani ba yayi saurin fadin a a
khadija ba haka zamu yi ba daurewa zakiyi mu fitar dashi daga wanan kangin don
Allah.
Ni haba yaya Yusuf ni may zan mai kuma shiya sani don Allah khadija dakata ki
saurare ni don Allah nace ina jin ka ai.
Zaki iya hakkuri ki daure ki kirashi a waya ki fada mai magana daya wanda zai
shi ya natsu ya dawo cikin hankalin shi yanzu don ke ce kawai mafitar da nake dashi
bayan Allah.
Ni kuma why sai nice mafita akan haka yace saboda ban taba ganin wani ko wata
dake fada mai magana yadda kike fada ba azauna lafiya kuma yai amfani da abin da
kika da mai a zauna lafiya.
Dan jin nayi ina tunane yace kada ki karaya khadija don nasan zaki iya ki
taimaka muna please wanan taimako ne indan kin yarda.
Yaya Yusuf wanan ya zama na karshe da zan ma wani alfarma akan wanan mutumin don
gaskiya baida niyar canza halin shi nake gani .
Khadija ba laifin shi bane shu,umar mace ya hadu da ita take juya shi yadda
take so nace har da halin shi a haka.
Kin yarda zaki taimaka muna ke nan nace naji zan gwada don Allah don kai amma da
ba haka ba babu abinda zai kara damuna da rayuwan shi.
Nagode kwarai da hakan da zaki min don wanan ne kadai hope din da nake dashi
yanzu akan wanan matar tashi.
Ina aje wayan maryam dake zaune ta kura min ido tana sauraren maganan da muke yi
din tace kai wasu maza suna haduwa da shu,uman mata wallahi.
Koda yake ba abin mamaki bane ga wanda yasan mazajen da ke auren irin yan yaren
buzaye zai san mazan ne a kasa matan suna sama.
Sai abinda sukace komai su mamaye na miji yazama nasu su raba shi kuma da kowa
nasa sai su da yan uwan su zasu dinga bushasha da shi da dukiyan shi.
Sai dai kima sam basu son auren mazan yaren su don irin bakar wahalan da suke
sha wurin su amma namu mazajen su ke kwadayin matan buzaye saboda bakar jaraban da
suka iya.
Yanzu dai kira shi muji yadda zaku kwashe a tsakanin ku don nasan akwai drama
nace ni wanan daure ni suke son yi maryam.
Ban san may yasa suke cewa wai sai nice zan iya masu haka ba bayan yana da kanne
mata da yan uwa da zasu iya.
Su iya may khadija ai abin sai da hikima ke fa ba yar uwan su bace kin ga yadda
kuke moved dashi kamar saurayi da budurwa ne.
Ke komai zaki iya fada mashi a zauna lafiya wani dan uwa idan yafa da sai inda
karfin shi ya kare ke ko sai ki fada mai a wasa bai dauki abin da zafi ba.
Wayan ta na karba ta hanyan yi mata karya wayana ba kudi a ciki tace ai bai san
layi na ba don haka ba lale bane ya dauki kiran .
Bari dai mu gwada mu gani idan bai dauka kiran har ya kusa karewa ya daga tare da
fadin hello nace dole zama da yan haure ya kowa ma wani akidar banza.
Wake magana please ya tambaya nace wata buzuwa ce ko kana son kari su zama biyu
a gidan ka murmushi yayi yace khadija nace ba ita bace.
Kina zaton muryan ki nan zai bace min ne nace marya na yana kama da na buzaye ne
?
Yace ai kamar ma ta baci baki ganin zubin ku daya dasu sai dai yaren da baki ji
nasu kai malam ni kiran ka nayi naji ko mommy ta koma ne?
Don nasan ba lale bane buzuwan gidan ka ta barsu su dade a gidan yace idan kina
son sani kije gidan ki duba mana.
Ban tashi ba ne da zanje yace ya kike nace ina nan yarda ka sanin a baya ke ba a
maganar girma da arziki dake ne ?
Nace banson don ba gaisuwa na kira ka muyi ba ko tambayana yaya ni yace ai kogi
ba ki dadi ba ko nace .
Wani kogin ke nan dai wani ko wani ruwa ne ya shige shi in ba nasa bane amansa
yake yi don haka ba gaisuwan ka nake nema ba.
Yace becareful nace a nan ko sai kaga mutum har mutum amma a gidan shi sai ka
rena mai wayo idan kaga abinda yake yi.
Ta yaya bakin haure har zasu shigo su samu mutum a gidan shi in ba samun wuri ba
suce sai abinda suke so zasu mai ni wallahi na dade da raina aya don tsakuwar ta.
Yau hausa kike ji ke nan nace daurowa ne hakan adai ji tsoron Allah kada mutum ya
zauna mace ta mayar dashi saniyar tatsan ta .
Ba mai ci sai ita da yan uwan ta kadai yace kina son wani abu ke nan nayi saurin
fadin haram wallahi adai ci lafiya.
Ga yan ketare nan suna taya ka ci idan ka wawuro su kuma sai su cafke ranan na
zuwa da zan maka irin ku kotu masu ba bakin haure makafa suyi yadda suke so da
dukiyar kasan mu.
Yace magana kike ji ke nan dai nace ba wani magana sai fadin gaskiyan da na saba
kulun idan naga anyi ba daidai ba.
Ya Abdul ace mutum baiwa kansa adalci kulun sai abinda mace ta dora shi a kai
yake bi yace wai may kike nufine don na rasa gane ida maganar ki ya doso har yanzu.
Mafalki nayi naga ka susuce kazama bawan mata sai goyon su kake yi a bayan ka ka
manta da kowa na naka sai masu jajayen kunne kasa a gaba.
Murmushi yayi yace ki fito fili kice kin yi kewa na kawai kin tsaya kina dora wa
wani laifi kuma ko na kulata ba mata na na kula ba na kula matar wani ne ?
Mata wai mata matar namu duka dai inji manya mata kan tana kaduna ka barota can
wanan ai ta bugi ne .
Khadija you are very stupid matar nawa kike aiban tawa a gaba na nace ko a idon
ka sai na fada don gaskiya ake fadi.
Namiji kamar mace baida say a gidan shi sai na mace macen ma abin kyamatar mu
gaskiya ka gyara halin ka sai anjima nayi saurin kashe wayan batare da najira amsan
da zai fada min ba.
Wanan yarinyar ta ci uban rainin wayo wallahi yace Yusuf da ke zaune gefen shi
yana murmushi yace khadija ce halan ?
Wa kasan zai min wanan idan ba ita ba ban san mayeatsalar ta da Nafisa ba ko da
yake su mata haka suke dama ko Nafisan da tasan da zancen khadijan Allah kadai
yasan iya boren da zatai min.
Kana zuwa gurin ta ke nan har yanzu ya danja tsuki yana fadin wallahi na dade ban
ganta ba tunkan naje Lesvegan rabo da na ji daga gare ta.
Yusuf yace ai gashi yau ta kiraka ita yace ta kirani taci min mutunci ba sai
nayi maganin yarinyar nan wallahi ta raina ni da yawa I don't know why take min
abinda taga dama haka ?
Kun fi kusa ai bani shiga tsakanin ku yanzu ai wani kallo yaiwa Yusuf din yace
tunda ka gama hadawa ba ai ka fadi haka yanzu ?
Au ni ma hada ke nan ashe wa ya manna min wanan chewing gun din idan ba kai ba
ina zaune kalau abina.
Amma ai tayi muna rana ba kadan ba kasan da hakan dai ?
Tsuki yaja yace ban san ya nakoma ba wallahi yar karamar yarinya ta shige min na
kasa yin komai akan hakan ?
Kun dai shige ma junan ku yanzun ne kuma kake neman maraba da ita ko why zaka so
ka rabu da khadija bayan kasan tana da amfani a gare ka ?
Amfani fa kace Yusuf yana kallon shi da idon shi da ya kafa mashi sai da Yusuf ya
rausaya kai yace kafini sanin haka malam.
Kada ka bari shedan ya rudeka kaiwa kan ka hasara zukekiyar yarinya kamar khadija
may kake fadi ne wai Yusuf ?
Kiran kawun shine ya katse masu magana da mamaki a fuskan shi ya furta kawu habu
yau lafiya kawu ya kirani haka ?
Ya dauka suka fara gaisawa da kawun nashi wan mahaifiyar shi cikin kunya da
nauyin kawun nashi yake amsa mai gaisuwan.
Don ya manta yaushe rabon shi daya kira shi ya gaida shi a matsayin shi na wan
mahaifiyar shi da take ji dashi a cikin yan uwanta.
Bayan sun gama gaisawa ne kawun nasa yace dama na kiraka ne idan da hali ina son
ka shigo kaduna a cikin wanan satin .
Da mamaki ya tambayi kawun nasa yace kawu lafiya ko yace a, a lafiya kalau sai
alheri akwai abinda nake son kayi ne idan kazo amma fa idan ba takura.
Haba kawu ba komai in sha Allahu satin nan zan shigo ranan jumma, a asabar zan
karaso zaria in gan ka kawun nashi yace nagode Allah yayi maku albarka ya kara
tsare muna ku.
Ya amsa da amin kawu na gode ya aje wayan yana mamakin maganan da kawun nashi ke
dashi akan shi Yusuf dake gefen shi ne ya tambaye shi ko lafiya.
Yana mai da kan shi bayan kujeran da yake zaune sama yake fadin wallahi ban san
abinda yasa yake nema na ba a yanzu.
Zamu tafi karshen satin nan don haka sai ka shirya muna tafiyan yadda ya kama sai
dai ban so tafiya yanzu ba a yadda Nafisa take haka haihuwa yau ko gobe.
Zamu iya zuwa muyi kwana daya idan hakane sai mu juyo idan ka gama ganawa da
kawun.
Yace hakan za ayi Allah ya kaimu lafiya gaba daya har ya manta da zancen wata
khadija ko don mantuwan da yake fama dashi a yanzu.
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu
kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama
sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana
magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci,
duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna
neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman
munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai
fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai
wayarku
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to
download it online
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography
including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490
its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted
biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not
blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we
are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day,
any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF
or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels