You are on page 1of 227

[12/4/2023, 2:39 AM] AsmaBaffa: 🏫 TANTIRIYA 🏫

A GIDAN YARI

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA
GARE KI
AIDA MAMAN TASNIM

1-5

INA GODIYA GA ALLAH DA YA BANI IKON FARA SABON LITTAFIN NAN

INA MIKO GAISUWA DA JINJINA GA MASOYA MASU BIBIYAR NOVELS DINA INA MUKU ADDUA ALLAH
YA AMSA MUKU BUKATUNKU BAKI DAYA DA WANDA NA SANI DA WANDA MA BAN SAN SU BA.

Page naki ne
MRS CHIEF

*👭GARKUWAR MATA👭*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya
mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce,
kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan
kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da
surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿
🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da
matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai
dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki
yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane
irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba
su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta
humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza
da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in
abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu
shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano
amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna
bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai
kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi
kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN
K'ARIN BAYANI
08089965176
07084653262

BISMILLAH

GA MASU AUDIO..BAN YARDA A JUYA MIN NOVEL ZUWA AUDIO BA.

Gidane me kyau Dan madaidaici da shi na rufin asiri haka gidan yake a unguwa
wacce take ta masu rufin asiri daidai gwargwado,gidan dauke yake da dakuna hudu sai
Palo da toilet a tsakar gida guda biyu ko Ina siminti ne Palo da toilet ne kawai da
tiles, gidan dai babu makusa Dake cikin birnin Kano, wani matashi ne kyakyawan
gaske da shi, fari amma haskensa ba can ba a kalla zai Kai 31yrs,dauke da sallama
ya shigo gidan hannunsa rike da Yar yarinya wacce zata Kai 3yrs itama yarinya
kyakyawa wacce ke kama da matashin me suna Mohsin.

Yaran gidan ne suka Masa sannu da zuwa Yaya Mohsin,murmushi yayi ya amsa,Hidaya
ce tazo ta rike Masa hannu suka shiga palon gidan,bayan sun gaisar da shi yace Umma
fa? Hidaya Ido ta runtse sabo da kunya tana danne dariyarta tace Yaya wai ta tafi
shako warin gardi kasan cikin da Umma ta samu ita me son wari ne,ban gane ba Mohsin
ya tambaya,Hidaya ta sake fashewa da dariya tace kaga Yaya Umma tayi tayi akan
lallai Abba sai ya daina wanka sabo da ta samu warin hammatarsa ta shaka Yana sata
nutsuwa amma yaki sam sai yayi wanka, bata Jin warin shine take ficewa wajen masu
aikin gini ta Dan sinsino sai ta dawo,wlh munyi munyi amma taki dainawa gashi Aunty
Naila tana gidan yari, itace dama zata iya taka mata birki, Mohsin shi kanshi
mamaki yake yi wai duk cikin da Ummansu ta samu ne yasa ko yaushe ita dai ta shaki
warin gardi shine dai dai, suna zancen sai suka ji Muryar Umma tayi sallama ta
shugo sanye cikin doguwar riga bubu me Fadi ta silk material ta yafa mayafin sai
cikinta kato a gaba, sai wani annuri take yi da nishadi.

Palon ta shugo ta zauna tana furta wash Alhmdllh dadi ya ratsani amma gardin
nan kazami ne na gaske malam na shaki irin Wanda nake so,Mohsin ya Kalli
mahaifiyarsu yace Yanzu Umma da aurenki da mijinki amma kije shakar wani warin
gardi duk da ciki ne ya jawo ai bai dace ba, Kubra wacce suke kira da Umma tace
ahhh kaga laifina? Ubanku tsaftar tsiya gare shi nayi nayi ya fasa wanka na kwana
uku yaki yarda ai kuwa dole na fice Inda zan samu kwanciyar hankali,tunda nake fita
sai yau nayi dace na shaki irin Wanda nake so tun da ya daga hammatarsa mallam sai
naji wata nutsuwa,Umma tana labarin har wani lumshe Ido takeyi tana cewa wlh wani
ni'ima da salama sai wani ratsani take,duk damuwar da nake ciki ta garkame Naila a
gidan yari sai naji ta yaye yau bacci harda munshari,idan Kuma Bakin ciki kake min
to ka daina wanka da aske hammata kazo na dinga shakar warin naka,Mohsin ya yatsina
fuska yace Allah ya kiyaye min,Umma tace Ina Hanan matar taka? Mohsin yace tana Nan
lafiya.

Uhmm wannan matar taka marowaciya ita ko irin kyautar nan da ake yiwa surukai a
dan siye suruka bata yi,sisinta banci ba me za ayi da mace irin Hanan,Mohsin yace
haba Umma duk irin girmamakin da take yi ai shi ake so...kafin ya rufe Baki Umma
tace a'a ai babban girma shine Yan kyaututtuka a zamanin Nan waye yake yayin wani
girmamawa ai kawai ace ungo shine girma

Canja zancen Mohsin yayi yace Umma yaushe zamu je ziyarar Naila Kinga ta kusa
sati daya a gidan yari ya kamata muje,Umma tace ba Wanda zai je mata da wuri ita
tasan me ta aikata dama Naila a rashin jinta nasan zata aikata sabo da haka kar
Wanda yaje sai ta gane kurenta,Mohsin yace haba Umma haka ma fa Abba yace bazai je
ba ko su Hidaya duk babu Wanda zaije mata,sharri aka mata ni ban yarda Naila zata
iya kisan Kai ba,nace babu Wanda zai je duk Wanda yaje ko ban sani ba ban yafe muku
ba,Naila da tuntuni take da samari na kirki masu kudi Inda zamu huta wannan
solobuyon uban naku dolo ne ba abinda ya iya, nace ta zabi daya ta aura taki ai
gashi nan yanzu garin shegen kinibibi da taurin kanta ya ja mata,ni na haifi Naila
amma kowa yasan halinta bata ji ga taurin Kai,gaba daya Dana sanin kaita wajen
ubana nake,ya gama kashe min yarinya,idan na tuna Alhaji Ibrahim da yake son auren
Naila amma ta koreshi mutumi me kudi taki yarda da shi idan na tuna abin nan sai
naji Naila ta sire min....Umma ta saki kuka yiiiii.....tace raina baci yake,cikin
masifa tana zaro Idanuwa nace sabo da haka ba Wanda zai je mata.

Yarinyar Nan sabo da rashin gaskiya ta fita da atamfa a jikinta suka tafi ashe
aski taje aka mata tayi shigar Maza kawai Dan ta siyar da magani,gashi Nan taje
gidan yari bangaren Maza a matsayin namiji Dandaudu yanzu so kuke muje a tona mata
asiri cewar macece? Billahillazi idan suka gano duk sai kotu taci kwal uban mu
Mohsin Yana mamakin halin Ummansu yace amma Umma da taje Abuja Inda kaddarar ta
fada mata ba kece kika ce taje ba tunda Abuja ne zata samo kudi,Sai nace taje ta
shiga matsalar me gida? Kaga karka dameni wallahi zan dura Maka ashar tashi ka ja
yarka ku bar min gida,Mohsin mikewa yayi Yana gyara Karin gugan shaddarsa milk ya
dauki Amal yarsa ya sabata a kafada ya bar gidan ransa a bace.

Direct Inda babansa yake aikin gadin petrol din turawa da suke aikin kwalta da
shi,can ya nufa da yamma likis,Babansu irin dolayen Nan Wanda haka Allah ke
hallitarsu, wasu gasu nan ne dai,Mutane suna zuwa satar petir din shi yasa suka
zuba masu gadi,yau abokan aikin nasa basu zo ba sai dare shi dama da safe yake nasa
zuwa yamma,Yan iskan gari ganinsa wani dolo sai suka Masa wayo suka samo aron jaki
harda Mangala a Saman jakin sai kace a kauye suka zubo gallon 50ltr guda biyu suka
taho Abban su Naila yana can Yana dolancinsa ya wani kwanta a Jikin bishiya ya saki
baki har suka zo suka saka tiyo suka ja petir din sai da suka cika jarkokinsu sun
Dora tsaf a Saman jakin kenan ya farka,daga nesan ya musu magana Kai lafiya
barayine? Matasan barayin petir suka ce a'a dama petir muka kawowa turawa ko zasu
siya, da masifa ya dinga korasu da hannaye Yana ku tafi ba'a so ba'a so baza su
siya ba shegu sarakan son kudi sabo da a siya da araha ku tafi,suka juya da jakin
da jarkokinsu cike da petir din da aka sashi gadi,Mohsin yaga duk abinda ya faru
Yana Saman lifan dinsa da yarsa Amal a gabansa shi kanshi wannan abin na Abbansu ya
bashi dariya matuka mutane sun saci petir Yana kwance Kuma sun Masa wayo kiri kiri
ya kore su da kansu,barayin suma suna barin wajen suka tsaya suka dinga sheka
dariya kamar ba gobe gashi motar tank ce ta petir bare a gane an sata.

Mohsin nan ya karaso wajen Abban nasa sannan ya sauka daga kan machine
din,Abban nasu ya kalle shi yace Mohsin idan na kalleku sai naga kamar ba ni na
haife ku ba kyawawan yara Yan gayu ga nutsuwa kar dai ace na yabi kaina amma na iya
tarbiyya,dariya Mohsin yayi yace Abba Kaine mana kana gani muna kama ma,Abba yace
a'a yanda nake kamar birin da ake wasa da shi ta ya muka yi kama gaku dogaye charas
da ku amma ni kana gani kafata ma kamar fatar Kura,Mohsin Yana ta dariya ya gaida
Abban nasa yace Abba wai baza aje wajen Naila bane?

Fuska Abban ya bata sabo da Umma ta zuga shi, yace babu me zuwa yanzu sai Nan
gaba,Mohsin yace a gidan yari fa take Abba,ah idan sun kulleta su jefa mukullin a
rijiya Dan tani kar ta fito a kulle ta har kwatagwan, uban waye yace ta Maida kanta
namiji shedar bata da gaskiya ,Mohsin shuru yayi kawai ya juya zai tafi kenan sai
ya tsinci Muryar Abba yace zo ka bani Dari biyar ni,Juyowa yayi tare da zaro dubu
daya ya mika Masa ya juya ya tafi,Abba dai kwanciya yayi ya koma baccinsa yace
barayi ku kuka sani Kuma, ato idan kuka sata Allah Yana kallon ku ni dai nayi iya
yina, ya lumshe Ido sai bacci

Mohsin gidansa ya koma duk ya damu Yana shiga Dan gidansa me kyau madaidaici
yasha tiles ko Ina,ga matarsa Hanan me tsafta da ita ko Ina Kal Kal Yana
kamshi,sanye take cikin kana Nan kaya ta matse ta tsuke gata da kyan diri Yar gayu
ce ta gaske,Yana shugowa Palo ta mike ta rungume shi hannayensa yasa tare da
zagayeta tsam a jikinsa Yana shakar kamshinta,fuskarsa ta karewa kallon tana Masa
wani kallon so a hankali cikin salo ta furta waye ya taba min mijina,Amal ce ta
kwalla ihu tana ture Hanan tana taba mata Daddynta,dariya suka yi Hanan tace Sorry
Amal ta matsa gefe Amal ta koma wajen Daddy dinta ta makale,zama suka yi sannan
yace kinyi min zobon kuwa? Fuska ta yatsina tace kayi hakuri na gaji ne shi yasa,Ya
danji haushinta sabo da bai taba cewa tayi Masa Abu tayi ba sai idan itace taga
dama, shuru yayi kawai.

Cikin gidan yari dake garin Kano,lungu da Sako ake tafiya da ita an tasa
keyarta gaba sanye cikin Kayan dake jikinta Wanda aka kamata dasu wato wandon jean
blue na Maza gashi barmeme katon gaske,sai riga me dogon hannu da wata rigar jean
din a sama itama me dogon hannu komai na Maza ne a jikinta har takalmi,sai hula da
ta saka irin ta Yan acaba a kanta, sai ka rantse da Allah dan kyakyawan saurayi
ne,sai dai ace Yana kalar mace amma ba me tabbatarwa macece.

Ko nononta ba'a Gani ta sa wani yankin kyalle ta dame kirjinta tasa seletape ta
zagayo tun daga bayanta har zuwa gaban kirjinta ta manne breast dinta da fatarta
dam sannan ta sa vest ta Dora riga ta sake Dora wata rigar me nauyi ta jean da ta
tafi da ita.
Suna tafiya amma taki sauri wani jibgegen namiji ne wanda yake Ma'aikaci ne a
gidan yarin kana ganinsa kaga rashin mutunci zalla tsawa ya dakawa yarinyar
matashiyar burdurwa tunaninsa namiji ne yace sauri mana.
Allah ya taimaketa basu ce ta cire kayanta ba sannan basu mata komai ba har aka
gama case din tare da yanke mata hukunci,Allah ya amshi adduar Naila basu ganeta
ba,dama tsoronta kenan shi yasa kullum a addua take kar a gano macece ita.

Naila ta fara wani uwar tafiyar kamar Dandaudu tana wani yanga tana doro tana
kwambo ta sake rage saurin tafiyar tata tana wani gadara tana ciccije lips,wata
mahaukaciyar tsawa Ma'aikacin yayi yace zan sassaba Maka kamanni shege
criminal,Naila ko a jikinta tana jin mutumin yana cewa an kaika aiki gidan me kudi
ka kashe uban gidan naka kayi asara,gashi hukuncin daurin rai da rai ba fita, ka
godewa Allah ma duk bangaren masu daurin rai da rai suna shanawa, yana ta
masifarsa.

Ko a jikin budurwar sai juyowa ma tayi fuskarta dauke da murmushi sabo da


tsananin kyawun wannan budurwa shi kanshi Ma'aikacin kasa kyafta idonsa yayi yana
kallonsa,Budurwar ta kalleshi tayi Muryar Maza tare da furta da Allah akwai Yan
Daudau Irina? Ni Dandaudu ne,harka ce ta Takashi akeyinta,ni idan ba Takashi bazan
iya rayuwa ba,ni yanzu ma breziyya nake nema haba sai kace muna Maza ne, kirji wani
rashanene haka sabo da Allah, Dan kana gidan yari sai a Maida ka akuya sabo da
Allah Kalli fa ni Abu ba kyan zubi ba sai kace an dura ruwa a bakar Leda ba a gane
farkonsa da karshensa yanzu kafin na fice daga gidan nan ai sunyi muguwar faduwa
sun zube a kasa ku taimaka min karku rage min farashi gandroba kuke ko me,karku
ganmu Maza ku raina mu ni dai na koma mace tun da dadewa ehe, ku shigar damu wajen
gomnati a samo mana brazeyya available mu Yan Daudu,kar a barmu suyi zubar gado
gashi Allah ya kawo mu rayuwa cikin gardawa, wallahi Wanda ya taba ni ban yafe ba
ehe.

Har ga Allah Ma'aikacin ya zaci Dandaudun gaske ne,yace Kai ya sunanka? Naila
tayi fari irin Dandaudu tare da furta Tantiriya nake idan ya Maka wahala zaka iya
cewa Terror, sunan da aka yanka min rago Kuma Jamilu

Ma'aikacin sai yanzu ya daina kallon Dandaudun kawai ya kwashe shi da Mari,
Naila ta dafe kumatu da sauri ta saki Kara tace ya shige ni wlh Allah ya Isa Idan
na yafe Maka Kabila nake,Idan na yafe Maka kace ba Sunana Jamilu ba kace ba Yar
Nigeria bace ni,Ma'aikacin kamar Allah ya aiko shi ya samu budurwa ya fara jibgarta
tunaninsa Dandaudu ne amma abinda ya bashi mamaki laushi jikinsa,sai yayi tunanin
ko Dan yaro ne,tsayawa yayi ya daina dukan ya shiga kallon hannayensa yanda yaji
Laushi,sai da ya gaji sannan ya jata a kasa kiiiii.... ya jefata cikin wani daki
Wanda yake cike makil da maza ridi ridi ba masaka tsinke, can gefe Naila ta
koma,cikin Mazan wani Baki wuluk idanuwansa jajir dasu me suna Mula yace Kai ya
sunanka,Naila ta tayi karairaya tare da furta Jamilu, Nickname Dina Kuma
Tantiriya,lokacin Ina soya doya a Tafa bakin tasha na samu suna Tantiriya

Wani a ciki shima DanIndo shine yazo tare da make bakin nata yace rufe mana
baki ko yanzu na yaga Maka baki gida biyu uban me ka yi aka kawo ka nan Dandaudun
banza? Nan bangaren ko wanne ka gani Yan hukuncin daurin rai da rai ne, Naila tace
sharri aka min na kisan Kai,DanIndo yaja tsaki yace sharri ai gwara ma da kashewa
kayi shine ka yi jarumta amma sharri aka Maka, ko ba komai sharrin yayi irinsa muke
so,Amma wallahi da ace bashi kaci aka kawo ka nan babu ruwanmu da yaro ne,ba
ruwanmu da Daudunka da sai na kusa kashe ka a gidan nan amma tunda harka ce ta kisa
wannan shine dai dai, da Allah zai sa ka fita da na maka hanya an baka bindigar
aiki,ka Ganni nan Hirer killer ne ni nan.

DanIndo ya sake dukan kirji yace billahillazi gidan yari da ka gani a wajena ya
zamar min kamar gidan gado Kuma muna da yawa irinmu dan uban babanka Jamilu,Naila
ta saki baki tana kallon ikon Allah,DanIndo har Yara ne da shi a gidan yarin sai
abinda yace suke yi,group group ne kowacce kungiya suna da leader wanda yafi kowa
iya shege da Yara a karkashinsa yana bautar da su,a gidan yarin suka hadu kawai
Idan anfi karfinka shike nan sai dai ka zauna a kasan wasu Wanda suke bangaren Yan
daurin rai da rai kenan.

Naila kuwa tunda aka kawota taga wasu a ciki suna ta fitowa da Maka makan
wayoyi ko wanne da tasa suna harkokinsu,suna da freedom zasu iya siyen abinda suke
so suci ko su Sha, har su sigari abubuwa da dama duk bangaren daurin rai da rai ana
barinsu suna yi,sannan kullum akwai ranar kidan koroso za ayi rawa a cashe ta
koroso,akwai ranar da Yan Solo ke zuwa suyi musu wasanni a cashe,duk wani wasanni
suna yinsa,ga sana'ar hannu,ga musulmai dole suje makarantar addini Data boko,
bangaren mata ma daban na masu ciki daban,duniya guda ce,amma duk Wanda su masu
daurin rai da rai ne to sunfi kowa more rayuwa a ciki sabo da su an San har abada
ba fitowa,sabo da nishadinsu aka tanadar musu abubuwan nishadi,haka lokacin maulidi
ma ba a barinsu a baya.

Naila tana ta Shan kallon Yan iska iya Yan iska,a ranta tace dole na zama tsagera
Tantiriya,a Nan sunana na daji Tantiriya zai min amfani,bangaren daurin rai da rai
ko ma'aikatan ciki basa shiga wajen sai da dalili sabo da zasu iya kashe wasu iya
Kaci dai hukunci daya ne dai Wanda suke ciki daurin rai da rai tunda yanzu in ance
Wanda ya kashe a kashe shi to fa ba a kashewar, gomnati bata sa hannu, a haka ma
masu kwakwaran hanya da kudi ake fitar dasu ba a sani ba.

Tantiriya dai ganin an dameta da kallo suna nema su ganeta sai daki ta canja
na wasu malamai ne Wanda kaddara ta fada musu, su biyar ne a dakin shi yasa ta koma
can taga suna da tsoron Allah baza suyi mata komai ba,Bata son cudanya da mazan.
malaman ban sai kallon Naila suke tunaninsu Namiji ne Dandaudu,Sallama tayi da
Muryar data canja ta dole ta Maza amma duk da haka sai aji kamar ta mata, Malaman
Nan tana shugowa duk wanda ya Kalli Jamilu Terror sai yaji gabansa ya Fadi sai yaji
Yana wani son Dandaudun,gaba dayansu,basu sake shiga wani hali sai da Naila tayi
magana, babban malamin cikinsu a kalla zai Kai 50yrs a hankali ya hadiyi yawu wani
tsoro ya kamashi sai istingifari yake Yana furta a ransa Allah na tuba na kamu da
son Dandaudu Allah ka kubutar dani,shima Malam Jilani Yana kallon Jamilu Terror sai
kuwa yaga ya saki murmushi,wani narkewa yayi a zaune wani matsananciyar kaunar
Dandaudun yaji lokaci guda,Malam Usama kuwa har baya son ya kyafta Ido da kallon
Yaron Dandaudun,Naila kuwa dariya take a ranta a fili kuwa ta maze,wani gadon
karfensu ta ja gefe can karshen bango ta Kai bed din ta kwanta a abinta.

Babban malamin Sharu ne ya Kalli Dan uwansa Malam Usama ya rada Masa kasa kasa
tare da dafe saitin zuciyarsa yace Akaramakalla kana jin wani masifa data ke neman
fada min kamar ni da tilawata izu sittin naji me kalar Dandaudun can ya birgeni
namiji ne fa,Ina kallonsa naji zuciyata ta hau bugawa wani kaunarsa ta kamani yaro
namiji Dan uwana kamar Dan cikina ni malam,ku sani a addua Dan Allah,Usama ma kasa
kasa yace nima Dan ubanka haka naji gaba daya sai naji ya tafi da imanin....da
sauri ya danne bakinsa da tafin hannunsa, yace wannan jarabawa ce Allah zai mana mu
halkanta mu dukufa da addua,Naila ce suka hada Ido da Malam Jilani ta saki wani
murmushi,Jilani kirjinsa ya dafe ya fado cikin su Malam Sharu shima Murya kasa kasa
yace yayi min murmushi wlh sai naji sonsa ni dai na shiga uku barin dakin nan
zanyi,shima Alaramma Garzali Yana satar kallon Naila Yana dauke Kai,Naila ta daga
Masa gira daya tare da kashe Masa ido,Zuciyarsa ce ta fara bugawa da sauri
Kafafunta ya kalla sak irin na mata ya bude baki,abinka da an Dade ba a hadu da
mace ba ji yayi kamar ya rungume Jamilu Terror, ai tashi yayi ya fice daga dakin
Yana salati a ransa,shi kadai uban zufa ya hada

Yace Ina zan sa kaina yau naji Ina son Namiji,a daren malam Jilani yace saukar
Qur'ani ya zama dole, a daren haduwa sukayi kowa ya bude Qur'ani kwana suka yi suna
addua Allah ya cire musu son Da namiji Jamilu,Naila tana ta baccinta gefe daya ita
hankali kwance ta samu dakin malamai ba ruwanta,su kuwa suna ta surfa addua akan
Allah ya tsare su da Jamilu.

Washe gari da safe mazan gidan yarin masu uban yawan masifa Yan matasa
dattijai,tsofaffi duk gasu nan iya kallonka da munana da masu kyau duk gasu nan,duk
kalan laifinka akwai ubanka a ciki ko wanne da bangarensu, bangaren mata daban na
maza daban,haka ranar ziyara sai an gama da maza sannan a bude mata ba Wanda ke
haduwa da wani tsakanin mata da maza,gashi Sabo da lalacewar ta kasar mu dakuna
sunyi kadan,toilet,komai babu na kirki,haka uniform ma babu sai wata riga da ake
bawa Maza lokacin ziyara,sai sutura kayan gida amma basu wuce kala uku ko hudu,haka
bangaren matan yawanci basu da bra,wasu Kuma suna da ita,wacce tafi wata karfi ma
zata kwacewa wata ko an kawo mata daga gida,Naila dai itace mace daya kwal a
bangaren Maza Wanda babu Wanda yasan Hakan har Ma'aikatan kaf a namiji ne Kuma ana
zargin Dandaudu ne,Naila bata da ko bokiti ,gashi wai a gidan Yari zata yi gayu.

Yanda take nunawa Dandaudu ne kawai, tana zaune a cikin dakin Malaman tace akwai
ruwan zafi? Ya Sheikh bana tsarki da ruwan sanyi sabo da na koma mace ni, na hana
kaina amfani da ruwan Sanyi,tana magana tana zuba uban karairaya wai dole Dandaudu
ne,gaba daya malaman Nan suka saki baki suna kallon Jamilu duk ya tafi da
Imaninsu,cikin rada da tsoro Malam Sharu yace addua bata karbu ba mu sake dukufa
wlh, Mallam Garzali ya a hankali ya saci kallon Jamilu sai kuwa suka hada Ido,fari
tayi Masa,da sauri ya yayiwa Sharu magana kasa kasa yana yi min fari wallahi,kansa
ya sadda kasa duk ya rasa Inda zai sa kansa.

Naila ce ta shiga aika musu da fari tare da dage musu gira,Kasa karatun suka
yi,Kamar ruwa ya cinye su ba Wanda yayi motsi,sai zuwa mazan bangaren nasu keyi
suna kallonta ana labarin an kawo kyakyawan Dandaudu Dan matashin yaro,kowa yazo
sai ya tafi da kaunar Dandaudu Jamilu a ransa sabo da kyau da farin jini irin na
Naila,Naila taga suna ta zuwa kallonta ita bata sani ba,tace bayin Allah ruwan zafi
nake tambaya zanyi tsarki mu yanda muka koma mata ai mata sai da ruwan zafi harda
yin tafi da hannu Irin na Yan Daudu,suka dinga tuntsira mata dariya ganin namiji
matashi me kuruciya ta karfi ya koma mace, a dakin malaman ba Wanda ya bata amsa
karshe ma kowa Uzurinsa ya fita,Naila tashi tayi tana tafiya tare da zuba
hannayenta a aljihun bujen wandonta ta fito

Ko Ina mutane ne lungu da Sako ba masaka tsinke,Naila tace ashe duniya ce guda
a gidan Yari,tana zuwa taga uban layin botikai da fanteku harda languna tun na
zamanin da,tana zuwa ta dauki botikin wani na roba an cika shi da ruwa ta dauke ta
Kara gaba, da tambaya ta samu taga Toilets gasu nan ko wanne ta leka duk an lalata
su wasu Kuma Kashi ko Ina dama maza ba tsafta ba wasu,Naila ta rasa inda zata shiga
dole sai da ta wanke toilet din sama sama sannan tayi wankan ba sabulu ta, ta daure
kirjinta tam tam da yankin Atamfa ta Maida kayanta ta shirya tsaf sannan ta fito ta
Maida botikin,wasu shahararrun kartai suka taso zasu yi mata duka Allah ya kawo
DanIndo wanda kowa tsoronsa yake a gidan mugu ne na karshe,yana kallon mazan yasan
yaran Goje ne,yace me Jamilu ya muku? suka ce ruwa muka ebowa Goje tun safe muke
layi kafin muje mu dawo ya dauke yayi wanka,Naila tace ku fadawa Goje din Dan
babansa na dauka kayan gomnati ne muna da hakki,dariya wasu suka dinga yi da kyar
DanIndo ya kwaci Naila yace ku bari zai zuba masa,wani ya gama buga ruwansa Sabo da
zalunci Dan Indo ya dauke ya zuba a bokitin Goje yace kuje,Ya Kalli Jamilu Terror
wato Naila kenan yace jeka ka bugawa yaron can wani ruwan

Naila tace bazan buga ba,wani gigitaccen Mari Dan Indo ya hada mata kumatu biyu
sai gani akayi Jamilu tuni ya fara buga ruwan tana kuka sai da ta cika botikin
sannan Dan Indo yace ware daga nan.

Dan Indo bai taba jin fata me laushin ta Jamilu Dandaudu ba,ya tsaya sai kallon
tafin hannunsa yakeyi shima Yana mamaki,Sam ba fatar namiji bace da shi.

Naila tana sakkowa sai ga wani Ma'aikaci ya tari Naila yace kai waye da za a hana
Hawa Saman tuka tuka kazo ka hau, uban waye ya aikeka? Naila da taurin Kai take
kamar ba ita ke cin duka ba,ta Kalli Ma'aikacin ta nuna kanta da yatsa tace nice
Tantiriya Jamilu ko a garinmu haka sunana yake kaina akwai kwari ba a cina da
yaki,ma'aikacin ya Kalli Naila an zagaye su ana kallo,yace Zaka ga Tantiriya munga
Iyayenka a taurin Kai ma sunyi laushi a nan gidan bare Kai da ka Maida kanka
Dandaudu gafalalle, Naila tace banda ni cikakken Tantiri ne ni Ina kallon ku Ina
Maida kaina namiji,Kai Ma'aikaci kayi a hankali zan iya tsille ma takashi ato, su
kansu ma'aikatan tsoro suke ji,juyawa yayi zai tafi, Naila tace nayi marking dinka
sai na sa maka guba,sai na farke Maka takashi,Dani kake zance,ma'aikatan sun Saba
da tsagerancin Yan bangaren daurin rai da rai tunda suna gani shine karshen
hukuncin,dole ya tafi.

Naila ta fashe da kukan karya tace Allah ka Saka min ni Jamilu Ina ganin rayuwa
Yar Takashin ma ban samu ba tunda nazo naki yin farin jini,ana ta kyalkyala
dariya,tace Mummy data yi sanadin zuwana gidan nan ya Allah kasa Danta ya mata
dukan tsiya watarana.

Akwai Yan Daudu da yawa a gidan Yari da Kuma Yan luwadi wasu ma a gidan suka
lalace sabo da rashin mace a kusa, tunda suka ga Jamilu Tantiriya gaba daya sai
hadiyar yawu suke gashi kyakyawan gaske komai irin na mace gaba dayansu sai kaunar
Naila,har da Wanda ke ciki masu hanu da shuni sai suka fara neman gindin zama wajen
Tantiriya Jamilu,Naila a ranta sai dariya take shekawa su sun zaci namiji ne kowa
ya kaimu da sonta har Wanda ba Yan luwadi ba.

Rafeeq zaune yake gaban Mahaifiyarsa Mima wacce ke faman kallonsa tana bin
Aljihunsa da kallo tana zaro idanuwa tana kallo tace banga Aljihun ya dago ba? Na
shiga uku kar dai ace haka kazo hannu yana dukan cinya, Rafeeq ba tare da ya sake
cewa komai ba ya jefa hannunsa a aljihu Kudi ya zaro Wanda sun kusa dubu hamsim ya
Mika mata,jiki na rawa kamar yau ta fara ganin kudi kamar ba a gidan kudi take
ba ,Allah ya maka Albarka wannan waje naka na Shawarma Allah ya karo customers

Sam baka yi kalar me Shawarma ba wlh yaro kamar Dan gidan Salman Khan kalar kudi
amma ficika babu,Yan mata sai rububi aljihu ba komai wannan kusan dubu hamsim din
wata nawa kayi kana Tarawa? Rafeeq wani takaici ne yake kamashi a duk sanda Yazo
gidan iyayensa,mikewa yayi yana Shan kamshi fuskar nan a murtuke da kyar ya iya
bude Dan bakinsa yace na wuce ni yana cewa haka ya fice daga daga katafaren Palon
Mima din Wanda ya gaji da tsaruwa, compound ya fito motoci ne gasu nan iri iri a
gidan masu tsadar gaske gidan ko Ina sojoji ne ke tsaronsa kana gani kasan na
babban Soja ne gidan..

Gate aka wangale Khalid babban Da a gidan ya shugo da motarsa lafiyayya,yana


yin parking ya fito cikin kakin sojojinsa ya zuba kyau ya nufi wajen Rafeeq dake
hanyar fita,Rafeeq Kai dai baza ka canja hali ba wlh kana ganina na shugo zaka tafi
ai ka tsaya mu gaisa ko,Rafeeq juyowa yayi da kyar da shegen Iyayinsa ya mikawa
Khalid hannu suka gaisa kana gani kasan Yan uwa ne na jini ba karya suna kama sai
dai Rafeeq yafi Khalid kyau na gaske,sannan yafi gayu Dan gayu ne shi sumarsa ma
askin Yan duniya aka mata,suna gaisawa ya juya yayi tafiyarsa ya bar Khalid a tsaye
da mamaki yace yaron nan fa takamarsa ta fara yawa nema yake ya Koma kamar Spark,
tsaki yaja ya wuce abinsa.

Shawarma Joint me kyau da shi Wanda ke dauke da katuwar wata rumfa an zuba
kujeru da table masu kyau na Passion Wanda Idan mutum na bukatar zama yaci a wajen
zai zauna,haka daga ciki ma akwai katon daki ya gaji da alatu Shima ciki kujeru ne
da table na Yan gayu na cin abinci ga masu son zama cikin sirri,daga kofar wajen
kuma ga hotunan abinda ake siyarwa nan shawarma,burger,chips and chicken da kayan
sha Kuma, aikinsa yake yana ajiye Dan littafin Menu karami Wanda ke rubuce da iya
abinda ake siyarwa yana bin ko wanne table yana ajiyewa da sauri,sabo da yana da
lecture 4 to 5,a hankali wata mota me kyau tayi parking a gabansa da sauri ya barwa
yaransa aikin ya koma ciki ya shirya cikin kana nan kaya masu kyan gaske ba karya
yayi kyau ya fito rataye da jakarsa ya shiga gaban mota,ko kula abokin nasa baiyi
ba,a hankali Abokin yace Rafeeq halina da Kai yanga sai kace masifa magana ma ta
gagara wlh har mamaki nake da ake zuwa joint dinka siyen Shawarma Kai da Spark
halinku baiyi ba,Spark ma ya fika rainin hankali duk da Yayanmu ne amma shi kake bi
wlh Dan wulakanci ne turai ta kwance Masa Kai,mutum kullum ba Rahma ga shegiyar
yanga kamar Dan gomna ga bala'i Kuma a gidan ma Spark ba Soja bane kaima haka amma
kunfi sojojin ma,kaima ka koyi halinsa sabo da kuna gadara da kyau ko me oho, ka
kyale spark yayi ya fika indai kyau ne,gashi da kudi shi idan yayi ba matsala tunda
ya fika komai, shi dai Rafeeq ko kala bai ce ba wayarsa ya zaro Samsung yaci gaba
da dannawa abinsa,a hankali cikin muryarsa me Dadi ya furta next month zanje
Kano,me zaka yi? Ban taba zuwa ba yaron da akace yazo aiki ko ziyara ko me ya sawa
Daddy guba an Yanke masa daurin rai da rai,yace kasan lokacin Makaranta sun Kai mu
Egyft branch dinsu,so ban San yaron ba ban ma taba ganinsa ba,Islam Abokin Rafeeq
yace Kai mene naka a ciki? dama Yan aikin nan Yan iska ne zasu iya gashi ance
Dandaudu ne ma,Rafeeq yace Yaya Spark ne zai aikeni can wai yana da ja sabo da
yasan Mummy dinsa yasan Halinta,yasan Kuma halin da suke ciki da mijinta Daddy, to
me zaka masa Dandaudu na tsani Dandaudu? yace zanje ne nayi masa Yan tambayoyi ance
sunansa Naila Hashim naji gidan Jamilu,Islam yace alright amma da mota zaka je?
Kasan bani da mota muje ka rakani kawai,Allah ya kaimu no wahala,shi Spark din
bazai bamu kudi ba? Yama bamu fa Yana accnt,tun daga haka Islam ne kadai yake
labarinsa Rafeeq bai iya magana ba.

Naila tana gidan Yari kwananta biyar taga zalunci iri iri,ma'aikatan ma Idan
kayi laifi zasu iya maka duk muguntar da suka ga dama iyakaci Idan ta asibiti ce a
kaika asibitin gidan kason,ga wahalar ruwa,sai mutum yayi sati baiyi wanka ba sabo
da kasar tamu ba ci gaba,kazanta kadai ya Isa ka kwashi cuta,komai yayi karanci a
ciki,ga mutane masu laifi sunyi yawa ba wajen Saka mutane tunda Wanda ya saci akuya
ma kaishi ake gidan Yari,a masu kudinmu Babu Wanda zai Kai musu agaji ya gyara musu
tuka tuka ko toilet da dakin kwana musamman gomnati wannan hakkinta ne,musamman
bangaren maza yafi Muni da kazanta za a hada mutum biyu a sarka daya a daure su ko
Ina zasu je tare Idan daya zaiyi Kashi ko fitsari dole agaban daya zaiyi ko
mene,Hakan yasa da yawa sun zama Yan gay suna Neman Yan uwansu maza haka matan ma
da yawa Neman junansu suke maimakon a samu gyaran Halin sai Kuma a lalace a
ciki,harkar daba da rashin gaskiya wasu duk a ciki suke koyowa,rashin kunya,taurin
Kai da fitsara iri iri duk koyo akeyi a cikin gidan gyaran hali,Naila tana zaune a
jikin wata bishiya sunci aiki sun koshi tun safe suke noma a can wani bangare suna
gyara ciyawa,sun hada uban zufa,Basu samu Salama ba sai da suka yi nisa,duk
haskenta tayi Dan duhu , jikinsu furu furu,Dan Indo ne ya zauna kusa da ita su ko a
jikinsu har kiba ma wasu keyi a ciki,Naila bata San sanda hawaye ya fara zubo mata
ba.

Dan Indo ya kalli Jamilu yayi dariya sosai yace ashe dai Jamilu Tantiriya Kai
karamin dan iska ne? Da kace baka ji kai Tantiriya ne, Naila tana share hawayenta
tace kana gani a haka zan kare rayuwata a wannan masifar wallahi sharri aka min ban
aikata niyyar ko kisa ba,DanIndo yace da ka adana kalamanka ba maganin da zan
Maka,kawai abinda zan fada Maka tunda baka da karfi sai taurin Kai ka kiyaye yiwa
mutane nan rashin kunya,wlh watarana Idan suka gaji zasu karairaya ka su
watsar,kayi biyayya,mun fika iskanci,Kai iskancinka na Daudu ne Amma tunda kaga
muna musu biyayya to kawai kayi, kana gani dai a gabanka suka sa karfe suka cirewa
Hamisu farcen babban yatsa Kuma ko a jikinsu, Naila ta goge hawayenta ba tare da
tace komai ba,kafin ta rufe Ido a cikinsu aka zabi shugabanni suna sasu aiki Wanda
ya kamata na tsafta da gyaran wajen kamar a makaranta,mazan sun dawo da tsawa da
duka sun kora kowanne aiki,Amma Naila kin tashi tayi suka zaneta kuwa Amma ko gezau
da uban taurin Kai take,Inda taci Sa'a duka gidan kaunarta suke haka kawai basu San
ba gender dinsu daya ba.

Indo ce ta kwala mata Kira da Tantiriya dake yanzu kowa haka yake Kiran Naila
da Jamilu Tantiriya domin ita ta radawa kanta sunan gata gata da farin jini Allah
ya bata kowa Yana sonta suna daga mata kafa sosai amma bata da kunya ga taurin
Kai,ta matsu iyayenta su kawo mata ziyara ko zata samu kayan canjawa da Dan kudin
siyen abubuwa,a haka sai da taga dama sannan ta mike ta shiga cikin Yan gidan suka
ci gaba da aikinsu amma sun rasa dalili Bata son cudanya da Maza sai ta ware kanta
gefe,sannan namiji Bata bari ya riketa sai idan Bata sani ba,Hakan ya tabbatarwa da
kowa ta shahara a harkar Daudu.

Naila tana noma ta Kalli wani Dan saurayi matashi kamar sa'anta ne amma ya fita
girma da komai namiji da mace ba daya bane ko a halitta, suna Shiri dashi Amjad,
tace Amjad ban taba ganin mace ba tunda nazo gashi har na kusa sati,oh ashe kallon
mata ma Rahma ne,dariya Amjad yayi yace wlh ai in ba a Yan uwanki mace ta zo Miki
ziyara ba baza kiga mace ba,Kai da kake Dandaudu Ina ruwanka da mata,Tantiriya tace
to ai munfi Jin dadin rayuwa cikin mata sune muke kama, Allah sai dai irinku Maza
haba shi yasa naga maza suna ta Neman junansu.

Ni a dangina ma bamu da mazaje Samari sai wani Dan banzan kanina me tafiyar tolo
tolo sai uwata sai ubana, Wanda zai iya zuwar min Yaya Mohsin ne,kaga Ina da
saurayi Kuma nasan zaizo, Amjad Baki ya tabe tace Dan uwanka ne fa namiji,Jamilu
yace kamar ka sani yanda nake son Gambo beauty sai baza ayi ba ta furta da sugar
Yan Daudu,Amjad ya sheke da dariya yace kunyi asara wlh.

Amjad ya sake cewa hala kai Hariji ne ne ko kana sex tun a gida? Yo mu yai muna
layin gidan Kashi cewar Naila.

Naila a ranta tace a gidan Nan nasan ma cuta ta kamani ta ciwon sanyi sabo da
kazanta wlh har kaikayi nake ji a gabana tabbas na kamu da ciwon sanyi.

Wani shahararren Dandaudu ne da ake kira da Skoler yazo wajen Tantiriya Yana
rangwada yace Kawas ya kamata na fada miki kiyi taka tsantsan da toilet mu mata
muna kamuwa da ciwon sanyi in kinji gaba na kaikayi sai kiyi magana zasu kaiki
asibiti a baki magani ahayye ya tallafe kirji ya zaci da gaske Naila Jamilu ce,suna
ta hirarsu har kusan dare sannan suka hau layin karben abincin dare abincin Dan
kadan gashi ba Dadi,masu kudi suna ta siyen abinda suke so,a hakan ma Idan wani
yafi karfinka ya samu ya masgeka ua kwace ya hade du ya cinye.

Naila tana layi aka zubo mata Miya da Katon sandararren tuwon masara,ta Kalli
abincin ta bata fuska tace Kai masu girki kuji tsoron Allah Miya kamar yawun kaza
haka gomnati tace kuyi? Wani Ma'aikacin cikin fursunonin yazo zai kwade Tantiriya
Naila da duka sai yaji ya wani shiga ransa sai ya koma yayi mukus ya juya, amma
Naila harda tana Allah ya Isa wlh ma'aikatan har sun gaji da Halin Jamilu
Tantiriya duk abinda akace kar yayi sai yayi, duk mugunta iri iri Amma bata jin
magana,rashin kunyar ta da taurin kanta kullum karuwa yake sabo da basa taba
dukanta kowa jinta yake a rai tunaninsu ma namiji ne.

Washe gari da yamma yau ta samu tayi wanka Dan Indo ne Ara mata sabulu ta fito
gabanta Yana ta mata kaikayi cutar sanyi ta kamata,ta rasa Inda zata sa kanta gashi
ba abin ta fada ba a gano ta,Dama kayan Dan Ido ta Ara ta barma a jikinta a wanke
suke,ta wanke nata tas ta shanya su,kayanta suna bushewa ta koma toilet ta shirya
ta Saka abinta, yau fes take sai kaikayin da gabanta ke mata na hauka cikin dakinsu
ta shiga Wanda yake da malamai a ciki,gado ma Babu na kirki wasu duk a kasa suke
kwanciya ko shimfida babu a masu kwanciya a gado har Tantiriya Jamilu,,ta Ari
bargon malam Sharu tace bani da lafiya bani aro ta kwanta ta lullube jikinta da shi
a ciki ta samu ta tattale kafa ta hau sosa gabanta ba ji ba gani,a hankali kasa
kasa tana cewa a bani cokali wannan susar sai da cokali.

Naila tana susarta tace yau Bado Yana cin ubansa da Susa,a fili Ashe ta furta
Dariya su Malam suka yi sun zaci iskancin Yan Daudu ne kawai,Malam Jilani yace mene
Bado? Naila tace gaban mata, ku baku ga yayi kama da Bado ba? Bado wannan Abar da
take fitowa a cikin ruwa,Idan baku San Bado ba kuje kuyi bincike,malamai sai kunya
ta lullube su,Malam Sharu yace Dan Allah ka koma cikin Yan uwanka Dandaudu Bai
kamata kazo cikinmu ba muna malamai.

Rafeeq gida ya shugo cikin takunsa na yana kamshi yayi Sallama a gidan
ShimaA wannan gidan da gani kaga gidan me hanu da shuni gidane na gasken gaske
komai na more rayuwa akwai duk da gidan da iyayen Rafeeq suke yafi kyau sosai Amma
wannan ma ba baya ba,ga motoci nan hadaddu masu tsada daban daban,Rafeeq yana shiga
katafaren Palon gidan wata matashiya ce baza ta wuce 50yrs ba da kuruciyarta
kyakyawa son kowa kin Wanda ya rasa ga kyan Kira da diri,tana ganin Rafeeq ta saki
murmushi tare da amsa sallamarsa,kallonta yayi ya zauna a hankali yace Aunty barka
da hutawa,Wacce ya Kira da tace Dana ya aiki ya Kuma school kana garin shine sai
yau zaka zo min? Sai da ya dauki lokaci sannan yace kiyi hakuri Aunty Exam muke yi
ne,kin San indai lafiya ai zanzo ko? tace na sani to ya school? normal Aunty,bari
na kawo maka abinci,me kika dafa ne? Hmmm zai wuce tuwo ne da kyar fa ma ya bari
nayi tuwon, kasan komai dai yau ma ko kudin cefane bai bayar ba,ayi mutum kamar
talaka Wanda bai gaji arziki ba,Hawaye ne ya zubo mata tace Ina so ko Yaya ne ya so
ni ya kyautata min amma Hakan ya gagara sai ma kuntata min da yake kana gani dai,
Aunty wai waye naji ance an kaishi prison akan gidan su Spark? Hankalin Aunty ya
dawo kan Rafeeq, tace wani Dandaudu ne marar Imani ya kashe shi,daga kawoshi gidan
mutane,Aunty ta kwashe labari ta fadawa Rafeeq,Rafeeq yace Allah ya kyauta shi kam
a ransa bai yarda ba Sam, yana da ja akan kisan domin yasan tsakanin Mummy da
Mijinta irin zaman da suke, tace sunansa ma wai Jamilu Hashim.

Rafeeq yace hmm kawai sannan yace kina da kudi kuwa? tace da kyar ma na samu na
siyan kayan Miya Sweetheart, Rafeeq ya mike tare da zaro kudi dubu goma yace kiyi
hakuri da wannan kin San Yan Makaranta,ta Mika hannu Zata karba kenan me gidan ya
shugo sanye cikin wata peach shadda Yar gaske yana sheki yana kamshi Shima ba wani
babba bane,Rafeeq yace Sannu da zuwa wani kallon banza yayiwa Rafeeq yana daure
fuska yace bana hanaka bata kudi ba,iyalina ko naka bana son shishigi,wato kana
nuna min ban iya ruko ba ko?to baza ta karba ba jeka da kudinka,kafa dameni Karka
bari na hanaka zuwa gidan nan,Ina daga maka kafa baka gani, Rafeeq kudinsa ya karba
ya Kalli Aunty a sace suka hada Ido ya faki Ido ya tura mata kudin a kasan kujera
tana kallo ya ajiye ya fice abinsa,Wanda ta Kira da Abban Na'eem da Na'eema ya fara
yayyafa mata ruwan masifa yace wlh ki kiyayeni Rumaisa Ruma ki kiyaye ni banza
shashasha,wato tona min asiri kike sabo da kin raini Rafeeq gani kike kamar ke kika
haife shi karki manta Dan Yar uwarki ne,Yar uwar taki ma da bata son kike shiga
sabgar danta in Banda masifa ma kina juya bakya haihuwa ki hakura da rike Dan wani
mana yaja tsaki,tace kayi hakuri abincin fa? Bana ci ya juya ya wuce part dinsa
fuuuuuu dama ya Riga yaci nama me rai da lafiya a wani joint me tsada a koshe yake
abinsa.

Su Naila ana gobe ranar ziyara dukkansu murna suke musamman Wanda Suke da
tabbaci za a zo musu daga gida,ita kuwa Naila bata murna domin Iyayenta Basu yarda
da ita ba shi yasa suka ce ba ita ba su Kuma babu Wanda zaizo wajenta ko an kaita
can,tasan halin Ummanta ,Amma haka suke ta tsafta suna gyara jikinsu kar azo a
gansu cikin kazanta,Naila tana Kallonsu ta zuba tagumi a inda ta idar da Sallar
la'asar Sallar ma a boye take yinta,a haka ma da ya ta shugo da Karamin mayafin a
cikin wandonta a boye,duk Allah ya tsallakar da ita ba a kamata ba,Addua take Allah
ya rufa mata asiri kar a tarfa ta,sai ta bari an fita makaranta take buya tana yi
ba nutsuwa sabo da tsoro, kullum itace karshen fita school tace ya Allah karka bari
a kamani ko a ganta da mayafi kowa yasan iskancin Yandaudu sunyi Imanin baza a kawo
musu Mace gidan ba shi yasa duk suka amince Dandaudu ne,Allah yasa ma basu kamata
ba har yanzu,kullum addua take kar a kamata har ta fice a gidan,kullum cikin
faduwar gaba take.

Wani Wanda ake kira da Skoler Dandaudu baki har kunne ya samu Dandaudu me kyau
kamar mace,wajen Naila ya karaso Yana rangwada ya furta budurwata ke wai baza kiyi
wankin ba? Ai ko sabulu sai na Ara Miki ki wanke kayanki, ga wando da t-shirt Dina
ki Saka,Naila tace ni ai ba Wanda zaizo min wa nake da shi Babana da Ummata sunce
baza su zo min ba,nafi sa rai ma da Yaya Mohsin amma nasan halin Ummanmu ko zan
mutu baza su kawo min ziyara ba,Dandaudu Skoler yace iyyee ke ki bari Dan Manzo, ai
shike nan amma baki sani ba ko sun huce, kinyi fa sati daya da zuwa nan Jamilu ki
samu dai kiyi tsafta ga farcenki nan sunyi Zako Zako haba Jamilu ta ,gashinka buzu
buzu,ga kaya sunyi dirty gashi kina fama da susar Bado abin ai yayi yawa,sai yanzu
Naila ta tuna hannunta na gabanta da sauri ta cire,Skoler yace ahhh karki ji
kunyata ai daya muke nima macece irinka sosa abinki kafin Nan gaba ki aminta Dani
na dinga lashe pole din naka,Ahhh ranar akwai harka ahayye chass Chass heyyyyy
nanaye, fito dan Allah Jamilu Baby mu wuce.
Hannun Naila ya rike ta fisge da sauri,ya saki da mamaki yace ahhhh wannan laushi
kamar auduka, billahillazi kinji za ayi bantan bala'i Dani a kanki Yar uwa,I love
you Jamilu,Dan Allah ni dai Jamila zan dinga kiranki please

Naila ta Kalli Skoler tana hawayen karya gwanin ban tausayi tace nifa ba a sani
sannan ba a hanani Iyayena ma hakuri suke Dani shi yasa ma da akace na kashe wani
suka yarda kije kawai zanyi tunani akan soyayyar, Skoler yayi tafi tare da bugar
cinya Yana fari yace shike nan Ina jira tawan ,Naila tace ba gwara ma na mutu na
huta ba,gwara kazantar cuta ta kashe ni, zuciyata ta buga kawai na huta,ba na Jin
magana ni yawwa ba a sani sannan ba a hanani,Suna jinsu kowa ya rabu da su,Shi kuwa
Skoler ya dage lallashin budurwarsa yake Jamilu,tana ta shagwaba ,gajiya yayi ya
zaro dubu daya yace ungo Baby je ki Sha lemon kwalaba ki sanyaya makoshinki,Naila
taji wani dadi ta karbe tace thanks ,yace wow yimin fari Jamilu na,Naila tayi Masa
fari da Ido,Kirji Skoler ya dafe yana karairaya yace zan suma bar ni haka, shi a
dole ya samu budurwa namiji irinsa Dandaudu.

Washe gari bayan mata an gama zuwa ziyararsu sannan aka bude maza suma aka dinga
zuwa musu suna ta murna yau sun samu abincin gida suna ta ci amma banda Naila ko
kare bai zo wajenta ba ko ma fitowa bata yi ba sabo da sai Wanda aka zo wajensu
suke fita,kusan kowanne anzo masa suka dinga dawowa da sabulai da omo,rezo,shaver
da tarkace daban daban amma banda Naila me kaya kala Daya,ana koya musu Karatun
addini Dana boko a ciki,ga sana'ar hannu iri iri,Itadai Naila sakar hannu ake koya
mata a ciki da Saka kayan sanyi,Sai filin wasa Idan sunyi niyya,Naila ranar wasa
tana can daki bata zuwa,duk sanda ta tuna iyayenta da Yan gidansu Kuma taci kuka ta
koshi,hankalinta bai sake tashi ba sai da ziyara tazo taga kusan kowanne kato anzo
masa banda ita,a Hakan ma su Dan lIndo da Yan Daudu ne suke taimakonta da sabulu da
omo gashi wani satin zata fara period ta rasa Ina zata samu pad duk da sanyi ya
kamata bata San ko zaizo ba ko bazai zo ba oho.

Dare na yayi sauro kamar zai cinyesu sauraye ne na hauka kamar yayi gomnati bata
dauki mataki ba Yana zubawa mutane cuta,Naila sai Susa take ga cizon sauro gashi
yanzu duk tunani da bakin ciki ya hanata ma yin tsaftar ba sosai ba,gashi ba wuta
ma bare su samu suga haske ba kullum ake kunna musu inji ba,cikin duhun daren
kowanne a kwance yake, kasa kasa take jin maza Yan gay suna numfashi suna ihunsu na
Dadi ga wasu Kuma suna biyawa kansu da kansu bukata,Ko wanne daki haka suke yi Idan
dare yayi,Yan Iskan karshe sai kalaman banza sukeyi suna ihu da Nishin Dadi,duk
sanda Naila taji Hakan hankalinta tashi yake taji a duniya bata bukatar komai face
Namiji,macece me bukata amma yau dake ciwon sanyin nata yayi nisa bata ji sosai ba
ta mike sum sum ta koma dakin malamai Inda yafi mata mutunci, su na kirki ne basu
aikata alfasha baccinta tayi a can.

Kafin sati biyu farcenta sunyi mugun Zako Zako duk ta fita a hayyacinta ta rame
tayi duhu duk haskenta amma sai da ya ragu,ana gobe Ziyara Rafeeq da abokinsa Islam
a Kano suka kwana a hotel kowanne da dakinsa,washe gari da safe bayan sunci
lafiyayyen Kari ,Islam ya fito shirye cikin hadaddiyar Shaddarsa me kyau sea blue
Dinkin Yan gayu na Yan zamani yana kamshi ya Saka hula kalar kayan yayi knocking
dakin Rafeeq yayi yana tsaye yana fesa turaruka shi sanye yake cikin kana nan kaya
masu mugun kyau na Yan gayu Riga me dogon hannu me tafe da hula bata da nauyi Sam
sannan ya sauke hular a bayansa,da wandonsa fari cif cif shi ya tsuke, gashinsa ya
gyara bai wani sharce ba sabo da an wani murmude sumar ne gata da yawa an kwashe
bayan keyar duka ba gashi sai kadan,gefe da gafe ma an kwashe anyi wani irin gyara
wajen yayi shape sosai daga tsakiya zuwa gaba sai tarin sumar me shegen tsayi an
murmurdeta a tsaitsaye gyaran fuskar ya fito ras gashi da sajensa me kyau kadan sai
gemunsa dan chass da shi Wanda ya kawata farar fuskarsa,abunka da me kyau gashi
yana da Dan haskensa baza ace Masa baki ko wankan tarwada ba Kuma hasken ba me yawa
ba,mutum gashi da cikar zati da kyan sura kana ganinsa kasan zai wahala ace ba ruwa
biyu bane, yana bulbula kamshi ya fito,Islam ya Mika masa hannu suka tafa irin na
Yan zamani yace let's go mun makara fa,suka fito a tare zuwa cikin motar Islam
wacce ta sha wanka ta hadu suka saki kidan zamani tare da Jan motar, Rafeeq ke
driving, da tambaya sannan suna duba location a waya map a haka suka Isa gidan
yarin,Dan cin hanci Islam ya Mikawa masu tsaron gidan aka bude musu ana girmamasu
aka basu shedar shiga ciki, suka yi parking sannan Wanda suka bawa cin hancin suka
tambaya ya shiga da su har inda ake ganin Yan gidan yarin maza da aka zowa
ziyara,suna ta fitowa gasu nan iri iri dattijai da Yan matasa ba kalar da Babu,Suna
shiga suka fadi sunan Jamilu,Rafeeq yace Jamilu Hashim,akwai wani Ma'aikaci nan
yake ya gane yace wani me kama da mata ko,ya bada Umarni aje Azo mata da Tantiriya
Jamilu,Nan take Rafeeq da Islam suka Kalli juna mamaki ya kamasu,su gashi basu San
waye bama Jamilu Tantiriya bare su tabbatar,gashi gidan yarin duk Wanda aka zowa
ziyara a gaban kowa za ayi hira a gaban masu tsaro da sauran da ake zuwarwa ziyara
suma suna ta hirar su ana jin na kowa.

Naila tana zaune ita kadai a dakinsu tayi tagumi aka zo akace Kai Jamilu fito
Yan uwanka sunzo,ihu ta saki da murna tace nasan Yaya Mohsin ne,ni sanan Abba ma
zai hakura ai nasan Umma ma dole zata huce,gaskiya Iyayena suna so na,gashi banyi
tsafta ba haka ta fito tana uban sauri itama baki har kunne zata ga Umma,har ta
fito inda ake ganin mutane Naila ta shiga zare Ido bata ga kowa nata Wanda ta sani
ba,Amma kallo ya dauke mata Ido tace wai yaushe rabon da na ga mota kunga yau na
hango motoci ta window,Mika tayi da hamma tace Allah mun gode maka da ka halicci
Nasara ka Bawa bature ikon kera mota, ashe Kallonsu ma Rahma ne amma da kullum sai
Maza kartai nake ta kallo Yan banza sai kayan wari,yau maza Kun shiga uku a
wajena,ta fara zare Ido tana washe baki tace ga maza Yan gayu ba masu wari ba
yau,maza mutanenmu,ana jinta ana ta dariya a wajen Banda masu tsaro duk dariyarsu
sai dai suna gazawa suna danneta suke yi wai ba raini.

Kai baka ga Wanda ke jiranka bane wannan yaron baka ji wlh,Rafeeq Yana zaune
yana ta danna waya ko kallon Naila baiyi ba Yana dai jin surutun kamar mace kamar
namiji bai sani ba ko shine sai da Islam yace gashi fa yazo,sai lokacin Rafeeq ya
dago a hankali ya Kalli Naila ya ganshi yaro ne ma matashi,da riga da wando manya
na maza kayan dukun dukun wandon ma ya dan yage,Islam yasan Rafeeq bata musu
lokaci zaiyi kawai shi yasa yayi magana yace kaine Jamilu?

Tace ae nine Tantiriya Jamilu mana,wajenka muka zo,ta dawo benchin da suke zaune
ta zauna a gefen Rafeeq,kamar an tsira masa Allura haka ya tashi tsam ya tsaya a
tsaye,cikin masu tsaron ne sunga kalar kudi harda sake mikawa Rafeeq kujera ta
daban ya zauna shi daya tare da harde kafa Daya kan daya kamar yana Palon ubansa,ko
kallon Naila baiyi ba,Islam ne yayi magana yace kaine Jamilu Hashim ko? tace ae a
sanyaye ganin kyamar da Rafeeq ya mata,yace kaine ka je Abuja ka kashe me gidan
ko? Naila tace aka yi min sharri dai sannan ni Kuma ina da gata na ba aiki naje
ba,labarin Zaka bamu Muji ko zamu iya wani abu akai,sai lokacin Rafeeq ya dago yana
kallonta sabo ya gane labarin nata karya ne ko gaskiya ne,mamaki ya kamashi ganinta
kamar mace haka.

Amma kafin ta fara labarin wani kaikayin ciwon sanyinta ya hada ta gaba daya ta
rasa inda zata Saka kanta gashi so take ta Sosa gashi maza ne a wajen sannan tana
tsoro kar a kamata, a ranta tace Kai uban wa na ajiye wai in Sosa abina,a ranta
tace ai da kunya Kuma a gaban maza,Zullo tayi tana daga zaune tare da Jan yaji
shiiiiiiiii.......kafarta ta dora kan daya tana mutsu mutsu,taji kaikayi ba sauki
dai ta mike tsaye ta sake komawa ta zauna tana so ta Sosa, duk sai kallonta akeyi
banda Rafeeq da Islam ba kikawai har ma'aikatan, Naila tace gashi ba a komawa ciki
a dawo Kai wannan rashin yanci da yawa yake Susa ma ba dama mutum yayi.

Bakinta ta toshe da sauri ashe maganar a fili ta furta,tunawa tayi a cikin gidan
kaso su Kam Babu kunya ba shayi,Islam waya ya daga ya mike ya matsa gefe,ganin
Islam ya tashi ta saci kallon Rafeeq tunaninta baya kallonta ta saci kallon mutane
taga kowa harkarsa yake

Baki ta tamke kamar me tsotsar alawa tasa hannu a gabanta Saman wando ta haka ta
Sosa kadan ta sake satar kallon Rafeeq da mutane ta sake sosawa da karfi,harda
lumshe ido taji Kam Salama sai ta manta ma taci gaba da susarta,Rafeeq yana ta
kallonta dariya ta cika masa ciki a ransa yace yaron nan bashi da lafiya,dagowa
yayi da sauri ta cire hannunta,cikin muryarsa me kasa kasa da gadarar gaske yace
me kake sosawa?
Kai mene haka kaikayi?a wajen neman mazan ka kwasowa kanka? ya tambaya, ko kunya
ya daga masa Kai a hankali yace ance sanyi ne ya kamani Dan Allah baka taho da Dan
wani karfe ba? Wani mugun kallo ya mata Wanda ba Shiri tayi mukus tana tsiri tsiri
da Ido

A hankali yace sabo da kana da infection sai ka dinga Susa a gaban kowa baza ka
iya hakuri ba,Naila tace a'a wlh bani da shi ya jumbo Yana kaikayi ace bazan Sosa
ba kasan kuwa bala'in da nake ji,Kuna da asibiti kaje mana shuru tayi yace karka
bata min lokaci ka bamu labarinka,lokacin Islam ya dawo Shima ya zauna yana
Sauraren labarin Jamilu,tiryan tiryan ta basu labarinta kaf amma suma binne su tayi
ta barsu a namiji ce ita Kuma sun yarda.

Wace Naila

WANNAN LITTAFIN SADAUKARWA NE GA


AIDA MAMAN TASNIM

FREE PAGE

WANNAN NOVEL NAIRA 300 NE

Account number
0175487861
Asmau Garba Muhammad
Gtbank

KATIN MTN
08061929616

'YAN NIGER GA NUMBER


+22790795939

Kar a manta da Sharhi fans please.

Ina godiya gare ku masu godiya da masu addua

AsmaBaffa
[12/4/2023, 2:39 AM] AsmaBaffa: 🏫 TANTIRIYA🏫
A GIDAN YARI

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA
GARE KI
AIDA MAMAN TASNIM

6-10

Page naki ne
AUTARESS

Follow this link to join my WhatsApp group:


https://chat.whatsapp.com/LAizQA6PofSLoFhQ7XeaQx

Ina kuke masu burin suga sun kawata gadajensu da hadaddun bedsheets? Ko Kuma
blankets kike nema? Masu aurar da yara ko kannai da ke kanki uwargida indai kitchen
utensils kike bukata
To kukanki yazo karshe.kuyi joining group din R&U exclusive kitchen and more
Ku more wa idanun ku da kayan kitchen Yan yayi na gayu da zannuwan gado na kowanne
kasa Zaki samu acikin farashi Mai sauki
Kuma Maza Bata barku abaya ba idan Kuna bukatar a hada muku lefe nagani na fada na
amarya Kona uwargida wato na fadar kishiya duk Zata hadamuku acikin kwanciyar
hankali.idan ma akwatunan kawai kuke bukata duk inkuka tuntubi Rumaisa zaku ganewa
idanuwanku
Tana Kano state Kuma Tana tura Kaya kowanne state afadin nageria harma da kasashen
da muke makwagtaka dasu
Zaku iya tuntubarta ta wannan number
07034559202

NAILA HASHIM asalin sunanta, Hashimu Dolo asalin Fulani ne dake zaune a
yankin Jos,yawan fada tsakanin arna da musulmai ya shafi Fulanin yankin Jos Inda
ake musu asarar dabbobi da rayuka,wannan yasa Iyayen Hashimu suka tashi suka shiga
Minna Inda Daji ne sosai ko Yan Fulani kafin ka samu gidan wani sai ka Sha
wahala,a hankali suka dinga karuwa a dajin,ko wanne bafillace yazo ya samu wajen
zama har suka hada ruga guda da matansu da yaransu.

Tunda mahaifin Hashimu suka dawo wannan daji da matarsa basu taba haihuwa ba
tsawon rayuwa,suna ta neman magani Ido rufe,sune gidan wannan malami sune can har
Allah yasa mahaifiyar Hashim katsam ta samu juna biyu ,suka haifi dansu
Hashimu,amma tunda aka haife shi halittarsa take kamar irin gaula gaula haka,irin
dolaye kullum bakinsa na dalalar da yawu,tunda ya taso komai na duniya bai iya ba a
haka ya girma har ya zama saurayi ya samu ilimin addini sama sama amma dalalar da
yawu sai da ya girma sannan ya daina da kyar,Yana da tsafta sosai.

Hashimu lokacin da ya isa aure, neman aure ma kasawa yayi, idan aka samo Masa
budurwa tofa sai kunya sai ya gudu ma ya kauracewa gari kullum Yana cikin
gonaki,karshe da Mahaifinsa ya gaji sai ya samu abokinsa Sagiru Wanda yake da
budurwar yarinya kwaya daya tal Kubra,sai ya nemawa Hashimu aurenta ya Masa gini
aka Masa aure,ba Wanda ya zaci wai Hashimu zai iya tsinanawa mace wani Abu amma
watanni uku aka ga matarsa da ciki kowa yayi mamaki a dolancin Hashimu ga matarsa
da ciki

Matasa suka tasa Hashimu gaba da tsokana ana cewa matar Hashimu ta samu ciki,Ashe
Hashimu yasan hanya,mata ma sai gulmar suke a gidan biki suna cewa oh ikon Allah
wannan waje ko mahaukaci Yana gane shi wai matar Hashimu Dolo da ciki,lokacin
Iyayensa wasu Yan bindiga suka harbesu a hanyarsu ta dawowa daga Jos sunje
ziyara,tunda Hashimu ya rasa iyaye sai ya siyar da shanunsa kaf ya tafi birnin kano
ya siyi gida a can suka zauna da matarsa Kubra ba uwar sana'ar da yake har suka
cinye kudin shanun tas,gadonsa duk ya siyar suka cinye kudin a ciki,ya koma sai dai
mutanen unguwa su dinga taimaka musu.

Wahala data ishi Kubra sai iyayenta suka siyar da sa aka bata jari kawai ta fara
sana'ar siyar da kayan Miya a gida sannan ta shiga makarantar yaki da
jahilci,macece kyakyawa ajin farko fara tas,shi Kuma Dolo Hashimu Yana da Dan duhu
amma kadan amma kyakyawa ne sai idonsa tsulun tsulun a ciki Kuma duk dolancine ya
Maida shi haka,ita dai Kubra jajirtacciyar macece mace me kamar Maza ga zafin
nema,a haka tana karatun Nan bayan ta haifi danta na farko Mohsin kyakyawa fari
amma ba can ba sai kyau Kam akwai shi ba karya,tana yin arba'in ta biya waec da
Neco ta zana jarabawarta,Kuma data fito tayi kyau sosai.

Lokacin ba wahalar samun school da wuri ta samu college a nan tayi NCE kamar
wasa kawai sabo da taga mijinta mutum mutumi ne,lokacin Kuma ta haifo yarta ta biyu
sankaceciyar gaske kyakyawa ajin karshen karshe fara karkar da ita tsakanin Naila
da Mohsin ya Kai Shekara goma,ranar Suna taci Naila.

Bayan Naila ta cika Shekara Uku a duniya Maman Kubra ta rasu sai babanta Affa ya
auri wata matar Sahura me kirki,gasu basu da yara dama yarsu daya Kubra,Affa ya
damu ya nace sai an bashi Naila,har ga Allah Kubra Bata so ba amma kawai Hashimu
Dolo yace dauketa mana ku tafi na baka ita halak malak,ba dama Kubra ta Hana tunda
Ubanta ne.

Affa ya tafi da Naila can Daji rugarsu,Mohsin yayi bakin ciki Yar kanwarsa sun
Shaku duk Inda zasu je tare, Naila a ruga ta taso cikin sangarta da gata sai abinda
take so,Bata San babu ba Sam,Bata San wahala ba,sai dai an sata a Islamiyya da
boko,babu makaranta a dajin amma sabo da gata Affa kullum shi ke kaita makaranta a
kekensa can a garin tsalle Wanda basu da nisa da garin kuma babban gari ne, sai ya
kaita kuma ya dakko ta da kansa a keke,ga makarantar private ce,Naila Allah yayi
mata basira da hazaka har ta gama primary ta shiga secondary tana Jin turanci
sosai,ga wani bature yazo rugarsu yawon bude Ido a garin yake zaune Naila ta zama
kawarsa kullum shi ke koya mata turanci har ta kusa gama Secondary dinta sannan
baturen ya koma kasarsa.

Naila kaf kauyen babu me kyawunya sannan babu macen data kaita shekaru a budurwa
duk da wuri ake aurar dasu,Naila har cewa suke ta tsufa ba miji sai boko,duk garin
babu me taurin kanta da rashin ji,tana zuwa kiwo,tana zuwa Rafi,tana Hawa sama,duk
wani Abu da akeyi a kauyen itace ta daya indai ba makaranta sai ta yi, sai rashin
jin masifa a gari,Sam a kauyen karatunta baya mata amfani, amma bata da karfi,ita
kullum sai dai a bita sai dai ta Mulki mutane ba dai a mulketa ba haka Allah yayita
da son Mulki,duk Inda ta shiga sai ta zama shugaba, sannan tafi Jin fulatanci akan
Hausa duk da tana Jin hausar Kuma tana yi,har tallan fura take yi idan babu school.

Tare da mazan dajin suke yawo da wasa,yara kanana gasu Nan sai jahilci yasa ba
abinda basa aikatawa,suna caca,suna shaye shaye gashi suna neman mata,sai kani ya
nemi matar wa,Yaya ya nemi matar kaninsa, haka uba ya nemi matar dansa,Da ya nemi
matar uba,gashi Nan jahilci iri iri sana'arsu ce a garin, duk karatun da Naila keyi
Inda kasan bata San A ba duk iskancin da akeyi a garin tana ciki, banda bin Maza su
dama mazan garin basa bin budurwa sai dai matan aure suke Zinar su,budurwa ta
Sha,manya da yara ba maganar iskanci da batsa da basa yi.

Affa shahararren me Bada maganin karfin Maza da maganin matan da basa haihuwa a
kauyen,daga gari gari ma zuwa ake wajensa,duk Wanda gabansa baya aiki,ko baya
biyawa iyalinsa bukata to azo wajensa Yana da magani sadidan,dai daikune zasu zo
basu dace ba.

Shi yasa da yaga Naila jajirtacciya ce sai ya koya mata komai ba abinda bata sani
ba na maganin sirrrin komai ta sani,watarana itace take sallamar mutane idan sunzo
sai yace ta gansu ta basu magani, Kubra wato Umman su Naila Bata ji dadin koyawa
Naila wannan Bada maganin ba na karfin Maza ai lalata ya macene a matsayin Naila
yarinya budurwa amma ba yanda zata yi,Mohsin ma bai so ba amma shi Baban Naila Dolo
ba ruwansa shi ai anyi dai dai cewa ma yake ai gwara ta koyi sana'a.

Umma da su Mohsin
Da kannen Naila Hidaya,Aslam,da Zarah idan suka je garin Naila ko ta kansu bata bi
kamar ba Yan uwanta ba,ita bata so ma suzo tunda taji suna cewa zasu dauketa a
maidata birni ganin ta kangare da yawa shi kanshi Affan tafi karfinsa bai isa da
ita ba shi yasa ya amince su dauketa din.
Naila fuskarta me Dan Fadi ce me dauke da hanci dan cas baiyi tsayi can ba Kuma
ba gajere ba normal hanci ne da ita me masifar kyau,idanuwanta Dara Dara masu
kyau,gata da gashi amma irin na Fulani yawanci ja ne ba Baki wuluk ba gashinta jaja
dashi kamar na akuya duhun nasa kadan ne ba baki wuluk ba,gata da saje, doguwa ce
me Dan kauri ba ramammiya ba Kuma ba me kiba ba,tana da masifar kyan diri gata fara
da ita.

Mohsin kuwa School of Nursing yayi Kuma ya samu aiki a Aminu Kano,yayi gidansa me
kyau na matasa masu rufin asiri ya auri budurwarsa da suka Dade suna soyayya Hanan
kenan Yar gidan Dankoli,Yar talakawa ce futuk a birnin,bayan ya nutsu Yana aiki
Yana Dan zuwa kasuwar kwari Yana business na shadda, a haka ya samu ya canjawa
iyayensa gida me Dan kyau ya sake gyara musu shi sosai, kayan abinci duk wata shine
ke kawowa a gidan,haka kannensa shi da Kubra ke daukan nauyin komai nasu har
makaranta,shima Hashimu mutanen unguwa suna ta Masa fada ya samu sana'a,cikin ikon
Allah an kawo turawa suna aikin wani gidan ruwa da titin kwalta sai suka ebi masu
gadin man petir dinsu na aiki sabo da yanda mutane ke sace musu,cikinsu harda
Hashimu shine ya daina zaman banza ya samu gadi.

Ranar da Naila ta fara bin Yan caca a garin,mata da Maza suke haduwa sai su
raba dare suna caca amma bai wuce a sa Dari biyu Dari biyar baya wuce haka,tunda
Affa ya ganta a ciki ransa ya Baci,ya nemi waya ya kira yarsa yace azo a tafi da
Naila abin ya fara yawa.

lokacin ta zana jarabawa sun gama Neco,Naila macece me son gwaninta,tana so


tayi abinda babu Wanda ya taba yinsa,ranar da Naila ta shirya saka Gagarumar caca a
garin wacce babu irinta sai ta sanar ta sa Budurcinta a caca ana gayyatar kowa duk
Wanda yaci ga Naila kyauta zai bare a leda,Kuma a ranta karya takeyi kawai tayi ne
Dan ta Bata musu lokaci ta gudu, har shela tasa aka yi a garin, matasan,dattijai
kusan kowa dake kauyen Sai da ya shiga cikin cacar har Wanda basa caca, tana so
tayi abinda wani baita yi ba,ranar Kuma aka yi da yamma an fara caca Naila ta rike
sandar kiwonta ta wani coge a jiki a gefe tana kallo,ana ta buga caca sai aka samu
wani Dattijo Malam Ya'u ya lashe gasa, Naila tana ganin haka ta sheke da dariya
tace karya nake dama nima caca nayi muku,kowa yace Bata isa ba.
Malam Ya'u da ya lashe gasa ya gigice yace karya ne wlh sai an bani
hakkina,Naila ta arce da gudun tsiya da Sandarta

Ana haka kawai sai ga Mohsin yazo a machine dinsa lifan sabo dal yayi parking a
gabanta,tana ganinsa bata San ma daukanta yazo yi ba tuni ya karbo kayanta a wajen
Affa ya karaso wajen hanyar Inda suke cacarsu,Malam Ya'u yace wlh zamu hadu duk
Inda na ganki sai na nemi hakkina, Mohsin kiranta yayi ta taho tana son Mohsin
sosai,sai yace sabon machine na siya hau na danaki kiji,zata hau baya yace gaba
zaki hau fa,dole ta hau gabansa,tace Yaya Dana ni naji dadi kayi sauri, ya sata a
gabansa yasan a baya zata iya dirga ta fece bata Jin magana tana Hawa kawai sai
gani tayi an hau babban kwalta sai birni,tayi kuka tayi ihu ta kira Affa yafi dubu
amma sai da ya kawota birni dama bata taba zuwa ba tunda aka kaita can,Malam Ya'u
yace wlh ko za a Shekara dubu indai Ina raye idona idon Tantiriya sai na karbi
hakkina.

Sanda tazo sun Sha wahala da ita da kuka da zagi da masifa sai ta koma
kauye,gashi Anki yarda har ta hakura ta saki ranta,daga zuwanta ta samu samari amma
duk ta kore su wai lallai sai sunyi bleaching sun koma farare.

Umma Kubra tana da Kawa Hajiya Tagwadas a layinsu,sai watarana Tagwadas tazo
tace tunda Naila ta Dan kusa wata guda a gida ta bata aronta zata rakata Abuja
gidan Yan uwanta su gaisa, masu kudi ne,daga can ma watakil Naila ta samo miji,ai
dama Kubra sai murna taji masu kudi tace ba komai zata rakaki,Naila tunda taji wai
zata yi rakiya Abuja har sati biyu tace baza taje ba,Mohsin ma yace gaskiya a'a
amma Ummansu Kubra ta nace ita zata tsine musu idan Naila bata je ba,dole Mohsin ya
hakura yace Naila taje,shine Naila ta shirya yau zasu tafi,Umma ta shiga kwalawa
kira

Umma....Umma....yawu cike a bakin wacce aka kira da Umma ta fito tace Naila
tafiyar ce ne? Naila tace ae Umma daga kauye sai Abuja tunda daga can zamu wuce
kince na biya na gaisar da Affa ko? Ai gwara ki bi Hajiya Tagwadas kije Abujar Nan
wallahi wannan dolon uban naku ba komai yake tsinanawa ba shima sai dai a
bashi,Naila tace Dan Allah Umma ki daina yiwa Abba haka bai dace ba Kuma a gaban mu
haba wannan fa yawa kike Umma.

Umma share Naila tayi taci gaba da magana idan kinje Abuja ki bude idonki ki
gano hanyar samun kudi ko kanwarki ma Hidaya kizo ki jata karki biyewa babban
yayanku Mohsin da shegiyar bokon nan marar amfani,Ina boko Taga amfani a kasar Nan
ka gama duk karatunka mutumin da ko primary Bai je ba bakauye sune masu kudin kazo
wai kana neman aiki a karkashinsa sabo....yawun da ya sake cika mata baki ta zubar
tace jeki Allah ya tsare ki kyale su Mohsin kuje kauye ku gaida ubana ki wuce can
garin kudi Abuja garin Alhazawa,Naila kyakyawar gaske ajin farko tayi dariya tace
maganin da Affa ya koya min shi zan Kara koyowa gaskiya naje da sana'ata
Abuja,tunda a nan Yaya Mohsin ya hanani Bada magani,Umma tace ni kaina bana son
wannan sana'ar Ina mace Ina siyar da maganin karfin Maza,Naila tace sai ni wlh
burina kenan na dinga gyarawa mata mazajensu Ina fixing din wacce ta samu matsala
in ta kama ma na kalla,Harara Umma ta balla mata tace haka na muku tarbiyya ki zama
me class ai gwara in kinje can ki dinga gayu kina samo alhazawa masu kudi kina cin
kudinsu,Baki Naila ta tabe tace nidai gwara na samu halak dina tallan maganin
karfin Maza tunda Ina da nasibi Akai kina ganin awwalu matarsa bata taba haihuwa ba
amma da na bashi maganina ya warke yanzu yaransa biyu a kauye.

Sannan nan tsohon Nan Tafida abokin Affa da zai Kara amarya ni na tsumashi ki
duba tsufansa amma sai da na Masa garanbawul ya Mike,ga wannan Dan lukutin Alhaji
shehu,Allah ya rabamu da Maza Yan lukutaye Dan Ina Jin kunyarki ne Umma da na Baki
labari,Umma wacce ta zubawa Naila Ido baki bude tace ke fa halina Dake bakya Jin
magana ba Wanda ya isa dake ba Wanda yake saki ko ya hanaki haba Naila ba
mutuncinki bane ki daina biyewa Affa sabo da kin taso a hannunsa, kina daji baki
san me ake ciki ba yanzu an waye mata aji ne dasu gaki kyakyawa,lalacewar da kika
yi yasa na kwato ki daga can rugar Fulanin,Affana ya lalataki da ya koya miki irin
sana'arsa bakya gani shi namiji ne,Naila p-cap dinta ta gyara tare da turo baki
gaba tace wallahi ni nafi son kauye bana son birnin nan Kun fiye takura ta furta
tana karkada handkerchief a hannunta, ta duka tare da goge takalminta Snickers
black me kyau na zamani Wanda Mohsin ya siya mata,wando ne a jikinta pencil baki
sai rigarta shirt me dogon hannu tsayin rigar ya Kai gwiwarta gata me Fadi da ace
bata da kyau da mugun Muni zata yi amma Dake fara ce kyakyawar gaske ga diri me
kyau sai tayi kyau sosai ta zama wata Yar gayu,gashin dai gashi nan a cukurkude
bata son a taje mata gashi Kuma baza ta taje ba gashi irin na Fulani jaja ba baki
ba sai tsayi da santsi.

Kudin mota Umma ta mika mata tace gashi tashi kije ku tafi ta kawo kudin mota
ta mika mata,Naila ta karba ta irga taga dubu bakwai ta Kalli Umma tace me nake
gani haka in this situation? Dubu bakwai Ina zata kaini inje kauye Kuma naje Abuja
duk a dubu bakwai,dama kin san baki da kudi kika ce na bita Abuja ni bazan je ba
wallahi Allah na fasa,yanzu ko maleji ai sai ki hau,Ihu Naila ta kwala tace ni
kamata Yar gayu a maleji Allah ya kiyaye,Umma kin san fa ni ban san babu ba ato duk
abinda nake so Affa yi min yake wallahi sai abinda naga dama,nace muku idan baza ku
iya dani ba ku maidani wajensa for God sake makaranta ce nayi Kuma nafi su Hidaya
iya turanci ma tunda turanci ku kunce shine Ilimi,nifa bazan iya daku ba yawwa.

Mohsin ne ya shigo yaci wankan kana nan kaya,yace ke Kuma wa kike dagawa Murya?
Umma? Oh na San baki da tarbiyya dama tunda Affa ya kaiki kauye nasan jahila zaki
dawo mahaifiyar taki kike fadawa magana anyhow? Naila kwalar rigarta ta gyara tace
ni nace a bada ni,gaskiya na fada taya zata turani Abuja da 7k a rayuwar
yanzu,hasali ma abinda take nuna min nayi ba me kyau bane,wai na tara samari nayi
amfani da kyau na naci kudinsu me Hakan yake nufi? Nayi karuwanci,Umma ce ta buga
tsalle tare da toshewa Naila baki kar aji wai,Mohsin da mamaki ya Kalli Umma yace
hakane? Ina...Ina Umma ta fara tace karanta mata nake akan ta zama me aji,amma
kanaji fa tallan maganin karfin Maza zata yi,Naila baki ta cuno tace sana'ar Dana
iya kenan ko kai Yaya idan Hanan bata gamsuwa ba matsala zan iya baka magani in ta
kama ma na kallet.., Mari ya zubawa Naila kafin ta rufe baki yace kina hauka ne ni
sa'anki ne? Banza Yar kauye jahila,Naila murmushi tayi tace saiwowi ne Yaya, Umma
tace na shiga uku ni Kubra,na yarda shi yasa a kauye suke ce mata Tantiriya
Naila,ai na cancanci sunan Umma bana Jin magana wlh kuyi hankali Dani tarbiyyata
sai an shirya na lalace kunyi sake,ni da kaina watarana Ina zama in ta tunanin
kaina da kaina nace ke Naila kanki babban ne cewar Naila.

Ni kuwa zanga Wanda zan aura a duniya,ya shiga uku duk Wanda ya aureni ya auri
alakakai babu zancen soyayya ni ban iya ba,mene soyayya ban santa ba zaici ubansa
mijina Alqur'an.

Yanzu dai kin fasa zuwa in kina so naje ki karo kudi ba maganar maleji ban san
shi ba. To kawo kudin a ajiye idan kudi sun cika sai ki tafi,Murmushi Naila tayi
tana goge takalminta tace wannan ai saidai naci tsire dasu sunzo kenan ai ni kudi
basu taba shiga hannuna sun fita wlh bazan bayar ba dama na dade banci nama
ba,kullum daga shinkafa da wake Mai da yaji,sai tuwo sai dafaduka shike nan nake ci
a gidan Nan.

A wajen Affa kuwa kullum sai ya yanka mana zabi munci abinmu ,dagani sai matarsa
Iya tsohuwa mu uku abinmu,ni bana farin ciki da samun kanwa irinki a rayuwa cewar
Mohsin ya ja tsaki ya fice ,Naila tace tsaya Yaya mu tafi gidanka mana,Allah ya
kiyaye na daukeki a haka a machine dina ki canja kaya na mutunci,Naila tace jeka
zanzo da kaina ka cewa Hanan ta min faten wake masu gidan zasu zo,Dake ke kika Gina
min gidan ko,Kinga ni bana farin ciki da zuwanki kowa ya tafi Islamiyya Banda
ke,Islamiyya zanje yanzu da girmana sai kace sabon tuba ko wata yarinya ni yanzu
karatun Islamiyya ai bazan iya ba Ko Kai Mohsin wlh sai na kureka a karatun
addini,nifa bana ji ne kawai yawwa duk Inda naje sai na buwayi kowa Kun dakkowa
kanku,in kana jin tsiya to nice,Umma juyawa tayi kawai daki tana tunani ita Ina
zata samu Wiwi ta shaki warinta sabo da ta samu kwanciyar hankali,yau Dan cikinta
warin Wiwi yake so.

Abba ne yayi sallama sanye cikin wata jallabiya fara tasha wanki,Yana shugowa
Naila tace sannu da zuwa Abba Dan sawalwali,dariya Abba yayi ba shiri yace Naila
bakya rabo da shiririta,Naila tace Allah Abba da Kai me kudi ne Kuma jajirtacce da
mata rububinka zasu yi,Abba harda shafa kasumbarsa wacce ta Sha gyara Yana wani
murmushi Yana Jin dadi Naila tana yabonsa a ransa yace Yar cikina ma Taga kyawuna
bare Yan mata,Me kake tunani ne Abba ta furta tana goge shegen takalminta,Cikin
kasa da Murya Abban su Naila yace shi yasa kullum idan na fito sai naga su Harira
suna ta kallona na rasa dalili ashe so na suke yi sunga kyau na, gaskiya naga
fa'idar Tsafta,rannan haka Lami me abinci a bakin tasha ta dinga kallo na,da Debora
me siyar da Amala, haka zaki ga ana ta rububina musamman mata abin nan Yana daure
min Kai,Naila saura kadan dariya ta kwace mata karya ta shirgawa Abba dan yaji
dadi,a fili ta maze tace Abba dole yau mu fita na rakaka wajen manyan yara ka kyale
su Debora,Abba yace shike nan watakil ma shine silar samun Wata attajira ta aure ni
Kinga ni na huta Kuma wallahi ke zan fara kaiwa Aikin hajji na kaiki Dubai daga Nan
na siya miki shirgegiyar mota,Naila tace yawwa Abba ta samo Maka aiki me kyau
ma,fuska ya bata harda shagwaba yace a'a bana son aiki ni nafi so ni kawai ta dinga
bani kudi Ina hutawa,Naila irin shagwabar da Abba yayi itace tasa itama ta shagwabe
fuska tana kallonsa dariya tana cinta a rai tasan Abbansu baya son neman na kansa
ko kadan ko ya samu aikin baya yi sai ya dinga sakaki har sai an kore shi,a Hakan
Ummansu don tana koyarwa a secondary ne itace ke daukan nauyinsu sai Mohsin da yake
Nurse a asibitin Aminu Kano shima Yana bajinta a gidan basa Shan wahalar komai suna
da rufin asiri.

Naila radio ta kunna lokacin ana shiri da fulatanci dake ita tafi Jin ma
fulatanci akan Hausa,tana ji suna hira da Abbansu,Umma kuwa takaicin Naila ya
kamata da take zuga Abbansu akan Yana da kyau mata suna kallonsa zata jawo ya mata
kishiya gajiya tayi da jinsu ta fito a fusace tace wallahi idan Baki daina zancen
mata na kallonsa ba sai na tsine miki Yar banza marar tarbiyya banza Yar
kauye,Naila tana bakin cikin da Yan uwa da iyaye suke kiranta da Yar kauye bayan
su suka kaita kauyen riko aka bawa kakanta ita sannan tana ganin tafi kowa wayewa
da iya wanka amma ana ce mata Yar kauye Jahila bayan ta fisu ilimin addini,idan
turanci ne tana jinsa kamar ruwa sabo da tana da brain,tunda suke ce mata Yar kauye
take ta kokarin gyarawa lallai sai ta zama Yar birni,Naila tace yaushe ne ake cika
a zama cikakken Dan birni? Umma da sauri tace Shekara arba'in,Baki Naila ta bude
tace lokacin na tsufa, birni bazan zama Yarka ba, sai nayi shekaru arba'in zan koma
Yar birni to na fasa,tsaki Umma ta ja tace da Abba tashi Kai Kuma muje ka zauna
kana zance da wata shashasha muje ka yanka min kubewar Miya ,sum sum ya Mike ya
bita ciki Yana cewa akwai feraye kabewa ne a fere miki ko miyar kubewar dai zaki
yi? Da gadara tace ae,yace to ki kawo sai a yanka miki,Umma wani tsaki ta ja tace
sai anjima.

Su Hidaya ne suka dawo daga school Naila ta kalle su tace Yan makarantar
bokoko,Hidaya tace Aunty Sannu,Naila tace karki sake kirana da wata Aunty munafuka
so kike na tsufa da wuri,Umma ce ta sake fitowa tace ki kyale mun yayana kar ki
takura min yara ai ya kamata ke cikin samarinki ma ki fitar a aurar dake,Naila tace
wai Khalil Dan Yana zuwa wajena? Umma ai Baki ne wuluk wallahi ya bari sai na samu
kudi na siya Masa man bleaching ya koma fari,Ina son fararen Maza sabo da haka dole
ya koma fari in Yana so na idan business Dina ya kankama zan dinga siya Masa man
bleaching Ina maintaining color dinsa na yarda,tsaki Umma tayi ta koma ciki tace
girkin uban waye zai miki?Naila tace kin san wlh ni ban ma taba shiga kitchen ba
Allah na tuba to Ina dakko kwano amma ban da shi ko ruwan zafi ban taba dafawa ba
kawai abinda na sani shine a bani na ci, yaran naki su dafa miki tunda ni bakya
sani a yaranki ta mike ta ficewarta.

Tana fita suka hadu da saurayinta Khaleel Baki ne wuluk amma Yana da kyau,
Magana ya mata Naila,tsayawa tayi ba tare data juyo ba tace nace kaje ka koma
fari,ga man bleaching Nan ka samu ka dinga shafawa,ni namiji farinsa ko na Mai ne
Ina sonsa,Khalil yace Allah ya tsareni sai kace mace ko wani Dandaudu,Naila tace to
karka sake kulani matukar baka fara bleaching ba, tayi tafiyarta gidan Hanan ta
nufa wato gidan yayansu Mohsin, gidan da nisa tsakaninsu amma haka ta taka a kafa
har gidan, kowa ya ganta a mutanen Kano ya zaci ba musulma bace irin aranan Fulani
ne,shi yasa sai dai a kalleta ace gaskiya arniyar nan ta hadu Inama musulma
ce,tunda taji haka suke fada,duk Inda ta wuce sai tace salamu Alaykum,wasu suce
irin Yan Fulanin Daji ne da basa sallah, ga shegiyar Sanda ta kiwon shanu kullum a
sakale a kafada har wani Mai ake shafawa sandar tana kyalli.

Da sandarta a wuya tayi sallama ta shiga gidan Mohsin suna zaune da matarsa
Hanan a kujera doguwar suna kallo a plasma tv,Yar su Amal tana daki a kwance tana
bacci,Naila tana shugowa ta tsaya a kofar palon tayi gyaran Murya Ehem Ehem na
shugo?

Mohsin yace yanzu sai da kika zo dan masifa,Naila ta shiga a hankali,yace ki


fitar min Yar iskar sandar nan taki sai kace namiji

Naila ta jingine sandar a kofar dakin daga ciki sannan taje ta zauna tace Mohsin
ta Sha Mai idan na barta a waje kura zata yi akan kura ta shafi sandar can gwara ni
kura ta haye jikina.

Hanan matar Mohsin ta Kalli Naila kawai ta wani watsar ita a rayuwa bata son
dangin miji, tafi so daga ita sai mijinta Kuma tana bakin ciki Taga mijinta yayiwa
danginsa alheri ko iyayensa bata kauna tafi so kawai daga ita sai danginta,Naila ko
ta Hanan bata yi ba,Mohsin ya kalleta yace baki gaishe da Hanan ba

Naila da maganarta ta yan fulani tace ni Shanda na zo ta min ko shannu da zuwa ne?
Ni ban taba zuwa gidanka ta min kallon Rahma ba Kuma ai kana gani, duk iskancin da
mace kewa dangin miji to wlh mijin ke bada kofa,da ya jajirce akan Yan uwansa ba
wata kafura data isa ta wani wulakanta Masa Yan uwa,amma ita su Umma ma bata kauna
taga ka taimake su ko sun zo Nan,wlh duk Wanda baiga darajar iyayena ba nima bazan
ga darajar sa da iyayensa ba,aikin banza aikin wofi mata an taimaka an auro ki,ki
Kalli yayana kyakyawa kamar Dan India ke kuwa kamar Yar yare hanci kamar hannun
kuturu ,Allah ne ya miki halittarki amma iskancinki yasa aka fada miki ki sani baki
da kyau ehe maleji muke yi dake..

Aradu duk da a Daji na girma na fiki iya soyayya ni tunda naga Yaya Mohsin kafin
yayi aure yafi kiba nasan baya Jin dadin auratayya,wlh sai mun miki kishiya ta
kwace shi,kullum Yaya cikin gayu da kamshi ke kuwa wankan ma Baki iya ba Yar
shagwabar ma da ake yiwa miji Yaya sai dai ya gani a gidan abokansa,wlh kika sawa
yayan cuta Hallare dinsa ya daina motsi sai na kaiki Kara, Mohsin bai Jin fulfulden
da Naila ke ji bai San mene Hallere ba fulatancinta da babanci Dana wasu yankin
hasali ma su basu San komai da fulatancin ba ko wanne iri.

Mohsin yace Zanci ubanki mene Hallere? Naila ta cuno baki tace pole dinka I
mean,your Jumbo,ai Mohsin ya Mike a fusace Naila ma ta mike ta fada bedroom ta sa
key,yace zaki fito ne wlh yau sai na miki dukan tsiya a gidan nan sa'anki ne ni.

Hanan tace Abban Amal kana gani ta shigar min bedroom ai bai dace ba,Mohsin itama
ya zuba mata harara yace ke danginki uban waye baya shiga dakinmu har kawaye kaisu
kike idan zakuyi gulma,rannan kaninki Khalifa namiji katon gardi ya isa aure na
ganshi a ciki Kuna Hira,ni da gida na sannan Dan kanwata ta shiga shine zaki ce ta
shigar miki bedroom sannu me daki, duk abinda kike yiwa Yan uwana Ina kallonki
kyaleki nake yi,me yasa kuke haka a rayuwa miji baya wulakanta muku dangi da iyaye
amma ku burunku wasunku da yawa ku wulakanta nasa haka ake rayuwa wannan ai jahilci
ne da kauyenci,yarinya ta shugo sai da na fara kallon fuskarki kina wani yi mata
kallon banza kina harararta taya zata gaishe ki tunda kin zubar da girmanki,babu
kawo mata ko ruwa, su shiga kitchen kice zasu lalata miki kaya,Hidaya ba bautar da
bata miki ba sanda kina laulayi da kika haihu haka ta dawo gidan nan komai itace
take miki amma karshe yanzu in tazo kallon arziki baki mata sabo da ke baki san
arziki ba,shame on you.

Hanan kuka ta fashe da shi da karfi Wanda sai da ta tashi Amal daga bacci tace
makira annamimiya tazo gidan Nan ta hadani fada da mijina shegiyar Yar kauye,Yar
daji munafuka gantalalliya, look karki sake kiran kanwata da gantalalliya shegiya
cewar Mohsin,
Na zage ta shegiya gantalalliya Yar kauye munafuk....kafin ta rufe baki taji
Mari ta ko Ina,sautin kukanta Hanan ta Kara da ihu.

Naila dake daki tana ji dariya take tana tsalle akan gadon Mohsin tace nice
wakiliyarka shedan basai kazo ba jeka abinka je kayi soyayya da matarka Iblis na
karbi aikin a hannuna,ka bar min wuka da nama,auren Nan zan raba shi karka damu
shedan, kasan ni ba irinku bace iska kullum bazai yuwu Ina nan ba wannan nacin naku
bazan iya ba Iblis Allah ya sake la'antarka amma daga yau na kulla zuwa gidan nan
ko yaushe Ina tayaka aiki karka damu,kana ganin nazo kawai kayi tafiyarka wani
uzurin.

Sai da ta gama surutunta ta dawo bakin kofa tace gidan Yayanmu ne gidanmu ne ehe
ba a isa a hanamu shakatawa ba Yar gidan Sule dan koli, Mohsin yace ke nake jira
kema ki fito wlh tun kafin na balle kofar nan, Naila tace yo ni nace babanta ya
dinga siyar da kayan koli, anan zan kwana yau sai dai ku koma dakin baki gashi Yar
katifa ce a dakin Yar gidan Sule dan koli ba a mata kayan arziki ba,shegen gadon da
suka kawo na zamanin baya na karfe me spring sai kace gadon gwauraye.

Mohsin yaja kwafa Naila taki bude kofa,Hanan ta gama kukanta har tayi shuru Dan
kanta ta zauna sunci gaba da kallonsu ba Wanda ke kula wani,har magriba tayi Mohsin
yaje masallaci ya dawo Naila bata bude kofar ba,bayan yayi Sallar Isha ya
dawo,Hanan taki yin girki shi Kuma baya cin tazarce,yasan dama indai suka yi fada
to gaba zata fara sai ta kwashe wata biyu tana gaba da shi, shi yasa da ya tashi
dawowa ya taho da take away dinsa Kuma iya nasa shi kadai harda ruwan roba da lemo.

Abincin ya bude har da cinyar kaza guda biyu manya manya,Me fushi Hanan ta
dakko ragowar girkin rana jullof din shinkafa wacce ta sandare da kyar take
turawa,Mohsin ya baje a Saman Center carpet Yana ci,Hanan sai satar kallonsa take
yi tana kallon kwanon fried rice dinsa ta Sha hadi, tana ta kallon abincin, ta zaci
hankalinsa baya kai ta zura hannu a hankali zata zari cinyar kazar,ji kake tassss
ya make hannunta,hannun ta janye tare da galla Masa
harara taci gaba da cin daskararren abincinta,ta sake mika hannu ta zari lemonsa
da sauri ta kafa Baki tana kurba kafin ta hadiye ya Mike ya matse bakinta sai da ta
zubo shi waje ta karfin tsiya sannan ya kwace abinsa ya Mike gaba daya ya canja
kujerar zama ya cinye abinsa tas har kashin sai da ya rumurmushe,wanka yake so yayi
har 9pm Naila taki bude kofar ta fito bacci yake ji.

Ita kuwa Hanan har ta mike taje tayi kwanciyarta a daya dakin me dauke da
katifa,yasan yanzu hakkinsa haihata haihata shike nan, yace to shike nan Kuma Yar
karuwar da nake samu da dan tagomashi ta tafi da abinta taje da tsiyarta.

Kofar ya Mike ya bubbuga yace Yar kanwata Naila,Naila dake ta faman fesa Masa
turare a jiki tace na'am da karfi,yace dan bude min wanka zanyi na kwanta bacci
nake ji,Naila ta karaso bakin kofar tana murmushi tasan dama tunda taji ya kwantar
da Kai to da dalili,tace haka kawai na bude ka zaneni aradu bani budewa,yace na
fasa na huce,tace anya Yaya to rantse, yace wallah kinji na rantse haba My sweet
sis, budewa tayi, ya waro idanu ganin yanda ta canjawa furniture din dakin wajen
zama ta gyara bed ta dame shi yayi masifar kyau,yace ai ko Dan wannan gyaran bazan
zaneki ba.

Ina kika samu tsintsiya da mopper? Naila tace naga matarka kazama a daki ta barsu
sabo da kazanta da ganda tayi aiki da safe ta barsu a daki,kaga a toilet na ebo
ruwa a famfo na zuba Omo duk a toilet na gani Kalli yanda yayi kyau ko uwarta Abu
me man kuli baza ta iya irin aikin nan nawa ba,bakinta ya bige taji zafi,yace bana
son rashin iya maganarki ki dinga zagin mutane kina ambatar sunan iyayenta kina
zagi,Bai dace ba matar yayanki ce yanda zaki min biyayya haka zaki mata to nima ba
biyayyar kike min ba bare ita,ki daina kinji ko ba tarbiyya bace wannan sannan
wannan shigar da kike shi yasa ake ce miki Yar kauye bana Jin dadi in ana miki
haka,nace muje na kaiki Saloon a gyara miki gashin kinki yarda,Umma tace ki tsaya
ta taje miki kinki kowa yace ki bari a gyara miki kinki ji sai dai ki wanke shi a
cukurkude babu sharcewa ba komai da ya bushe a haka zaki tufke abinki, Naila tace
zafi Yaya ni bazan yarda ba wallahi akan a taje min gashina gwara a maidani
kauye,ai sai da nace baza ku iya rike ni ba ka wani je ka dakko ni a dole ni wlh
bana son birnin nan,gwara Ina kauye da yanzu nayi ashar tafi million amma anan ba
dama sai da dalili ake ashar haba rayuwa tayi tsanani ba freedom ba kolabo,ni
wallahi na gaji,sau daya ne aka taba cinye ni a caca badan na tafi da wasu kayan ba
da zigidir za a min sabo da suturar da take jikina na saka a caca.

Mohsin Allah birni ba dadi ba kolabo iskancin banza suke yi na karya suke yi
iskancin,Allah wallahi saura kadan Yaya na sa budurcina a caca,Mohsin ya saki
salati da sallalami yace ke wai da gaske kike? Ni Ina wasa ne wlh da gaske nake yi
Maka a dajinmu mata da Maza caca suke yi har matan aure, ranar da nace na sa
budurcina a caca ranar kazo ka dakkoni,samari sunyi ca kowa ya shiga cacar ko zai
dace harda dattijai sun shiga cacar kawai kuka zo daukana shi yasa samarin kauyen
suka ce duk ranar daka koma wallahi sai kasha ruwan sanduna tunda ka cuce su,Kai ka
sanni kuwa kowa respecting Dina yake a garin babu kamata,ga iya wankan gayu,ga kyau
gani chass Umma ta haifi yarinya,babu me taurin kaina duk garin shi yasa aka sa min
tantiriya amma ni ba yar iska bace fa,banyi komai ba kalau nake Yaya fess nake ba
abinda ya faru da budurcina.

Mohsin sai da ya gama sauraronta sabo da idan ko yaro ne yazo da shirme ka


saurara maybe akwai abin dauka ko na gyara sai a dauki mataki,yace ai bamu San haka
kika lalace ba Naila,Naila tace ai na wuce haka ma,mu da muke zama a cinyar Maza
watarana ma Affa ne ya min duka yace idan na sake sai ya yanka ni,shine ban Kuma
ba,Mohsin ya saki salati yace Allah ya hadaki da mijin da zaici ubanki yayi
maganinki Naila,dariya ta sheke da shi tace sai dai naci nasa uban Yaya,idan ba duk
Wanda ya aureni ya auri masifa da kudinsa ba Allah ya konani,Mohsin yace Baki hadu
da Wanda ya fiki bane,dole kizo ki buwaye mu ashe kin lalace da yawa

Naila tace ba karamar lalacewa ba Yaya Dan Allah yasa ma na tsaida Sallah wata daya
da suka wuce,Mohsin ya sake bude Baki yace dama bakya sallah duk shekarunki har Sha
Tara 19yrs to 20yrs? Naila tace wallahi sai bana Allah ya nufa,ai azumi ma sai
shekarar Nan data wuce na tsayar da shi amma duk na karya nake yi sai na buya na
Sha ruwa da Koko,watarana Kuma idan naje kiwo sai mu kafa baki a nonon saniya
direct musha mu koshi.

Dan Allah full stop zo ki tafi gida goma tayi,a kauye ma sai na Kai 12 na dare a
waje muna wasa bare Nan birni fitila ko Ina gari kamar rana,to naji ke duk turancin
da kika iya a Ina kika koya? Makaranta mana,na yarda ai kina da brain,bature ne
yazo dajinmu yawon bude Ido Ina zuwa makaranta,sai watarana zan baka labari,yanzu
ka kaini gida Yaya,bacci nake ji na fada miki ki shiga napep,to kuwa sai dai na
kwana,tsaki yaja yace jeki Palo bari nayi wanka nazo,Palo ta dawo ta zauna tana
kallo har yayi wanka ya fito cikin 3qurt fari da t-shirt brown,yace muje mana kina
ta kallona kamar baki sanni ba.

Naila tace, kayi kyau Yaya Ina ma ba Umma ce ta haifeka ba,gaskiya Umma Bata
kyauta ba ta cuceni data haifo ka Kuma ta haifo ni ai sai ta tsaya idan ta haifeka
ma ba laifi sai ta bari ni a haifeni a wani gidan can sai mu hadu sai muyi aurenmu
ko ya kace,ai haihuwa ta mana illa kawai yanzu sabo da Allah sai a haife mu a gida
daya the same father and mother haba haba,ai da ba gida daya bane ni nasan ma da
Kai zan hadu dole in aureka, da anga 'Ya'ya wai wai zuky, dariya ce ta kwacewa
Mohsin sabo da suna masifar kama da Naila duk gidan sunfi kama kowa ya gansu basai
ance Yan uwa na jini bane.

Dariya ya dinga yi sosai tana kallonsa tana murmushi Yana dariya yace taso mu
tafi ya riko hannunta, ta mike ta dauki sandarta da bata mantawa da ita,shi ya
manta ma da shegiyar sandar yasan wannan sandar baza ta kwatu ba,ya bata rai yace
ajiye sandar nan,haushi taji tace idan baza ka kaini ba ni zan tafi a kafa,ba yanda
ya iya haka ya fitar da machine dinsa lifan.

Tace ban iya hawa machine ta gaba ba mu zaman dare muke a kaikaice muke Hawa,
Yaya sai an dorani,ko Affa dorani yake yi,tayi tayi ta kasa hawa sai faman juye
juye takeyi da kyar dai ta hau ta juya Masa baya maimakon ta Kalli gaba sai ta
Kalli baya ma'ana sun hada baya da baya,ga sanda sakale a wuyansa, Mohsin yace
wallahi idan kika fado ba ruwana Dan iskanci kinyi kusan wata guda a birni kina
kallo yanda ake Hawa machine sai ki juya baya zaki fado kinji na rantse"

Naila tace to Yaya kaifa yayana nane na jini yanzu idan na juyo Enndu(Boobs)
Dina suka taba jikin ka fa,mu mun iya hawa machine a haka,yace ke kika san Enndu
shashasha, yaja machine dinsa suka Kara gaba ana ta kallo ta zauna daram amma dole
ta rike machine din ta Dafe da hannaye biyu sanda Kuma ta tsakiyarsu a kwance.

Tana ganin me tsire Yana yawon dashi a Kai a bude tace Mohsin tsaya na siyi
tsire,da karfi tayiwa me tsire magana Kai me tsire da zafinsa? Mohsin yace wannan
abin ya gama Shan iska duk kwayoyin cuta sun hau Kai,tace mu haka muke siya a can
kauye idan munje kasuwa,ta sake cewa da me tsire kaga ya hanani siya Kuma Ina
so,kowa Yana jinta duk na gefen titi tana cewa ya hanani siyen tsire Kuma Ina so,
sai dariya ake musu ga hanyar gefen tasha ne,Mohsin Yana ji yace nan ba haka bane
to ba a wannan shirmen, sai da ya karasa waje me kyau Wanda nasu a cikin glass yake
yace na nawa zaki siya? Tace na dari biyu

Uban wa zai baki nama a dari biyu,sauka tayi shima ya sauka ya siya mata na dubu
daya,ya siyi na dubu biyu yace gashi nan ba yawa wannan nasu Umma ne da yaran,tace
to mun gode ta sake juyawa zata hau machine irin dazu,Mohsin yace wallahi kika hau
da baya sai dai na barki a nan,dole ta juya gaba ta shako wuyansa sannan ta hau ta
rirrike shi Kam a haka ya kaita har gida,yace to shiga Kinga ma basu rufe gida ba
da alama ke ake jira ta sauka

Tace Yaya? Ya amsa da Naam,tace ka dinga yiwa Umma fada ta tsaneni su Hidaya
take so kullum suyi tace min Yar kauye jahila,Wani furucin da Umma take yi wallahi
tambade yaranta take bata sani ba,kanaji wai naje Abuja na samu masu kudi na dinga
cin kudinsu ai wannan jefa yarinya ne a hanyar banza,ni da nayi haka ai gwara na
bada kaina a caca, nace sana'a zanyi taki yarda yanzu sabo da Allah wa na sani a
Abuja da za ace nabi wata Hajiya Tagwadas,Kai daga Jin sunan kasan ba na kirki bane
wai Tagwadas,Kuma idan nace bazan je ba ta dinga zage zage da lafazi marasa
dadi,gaskiya kayi mata magana ato ana shiga hakkina a gidan nan,gashi nan sai
ramewa nakeyi kullum,Mohsin yaga yanda take uwar kiba da kyau amma tace ramewa
take.

Mohsin murmushi yayi yace ashe dai kina da hankali Kanwata,Ina da shi mana amma
Kai kadai nake nunawa hankalina a wajen kowa ni bani da hankali ato Kuma bance ka
fadawa kowa ni Ina da hankali ba,abin sirri ne,dariya Mohsin yayi ya mika mata
hannu yace give me five, ta mika Masa hannu suka tafa,yace idan ta takura kije
kawai amma ki nutsu ai tace rako zaki yi just 2weeks zaku dawo ko ai ba matsala
idan ta takura kije, shike nan ta furta tace sai da safe,idan ka koma kar ka kula
Yar banzar matar Nan taka ko kaji sha'awarta ka makale kafada kace a'a,idan yaki
hakura ka fada min zan baka magani shike nan sai kayi wata baka ji kana son mace
ba, Baki Mohsin ya tabe,tace ka daina rainawa da gaske nake nazo dasu ni nake da
sirrin,lakani ne Dani I can fix you, gwasaleta yayi yace oummm ke dalla rufe min
baki,jeki good night ta shiga ciki ta rufe gidan gaba daya .

Ashe Abbansu Yana waje bai shugo ba,


Naila tana shiga ta same su masu Assignment duk suna ta yi wasu suna kallo,Umma
zaginta tayi tace Dan iskanci sai ki tafi waje ki Dade haka har dare ki zauna baza
ki dawo ba,sabo da ni ban isa ba ubanku dolo ne,ni Kun rainani banza
bagidajiya,Naila tace amma ai na fada miki na tafi gidan Yaya,shine zaki Kai dare
haka sabo da hauka irin taku ta Yan kauye, Naila baki bude take kallon Umman tasu,
ledarsu ta mika musu tace gashi inji Yaya,da sauri Umma ta fisge ledar tace miko
min waccen ta hannunki

Ai nawa ne wannan shi ya siya min daban,to Baki isa kinci ke kadai ba,Naila ga
taurin Kai tace wlh bazan baki ba ai nawa ne ai ga naku na baku,kune bakin nama ni
a can ci muke mu koshi sai ya ishe mu kullum,Naila kika sake fada min magana baza
ki samu albarkata ba,da sauri Naila ta bude baki,tace wai ku me kuke yi haka ne
komai akayi sai ku dinga furta munanan kalamai akan yaranku wani abinda da iyaye
basa ganewa duk Baki ne,amma ni kikewa su Hidaya me yasa ba a musu wai? Ko sabo da
ba a nan na girma ba,karku bari nayi fushi wlh Ina da taurin Kai duk duniya babu me
sakko Dani,ai samun lafiyarki Naila kiyi aure ko ki bi Hajiya Tagwadas Abuja kiyi
kwana biyu kiyi samari ki dawo masu kudi nake so yawwa.

Naila tace ai bance miki bazan je ba amma ni ana matsa min zan fasa Kuma babu
me sani,ai kuwa da na tsine miki,Su Hidaya suna jinsu, Hidaya irin mugayen nan ne
da basa magana sai bakar zuciya da hassadar tsiya,amma a haka sai ka rantse tafi
kowa hali me kyau,tunda taga Naila ta fita kyau da komai shike nan take Dan Jin
haushi amma ba sosai ba.

Naila tana cin Dan tsirenta Umma tasa hannu ta kwashe guda hudu ta karawa
Hidaya biyu ta bawa Zara daya sai Aslam ta bashi shima suna ci,Naila zuciya tayi ta
tura musu tsirenta tace ku hada ku cinye na koshi,suka dauke kuwa.

Sai lokacin ta lura ba Abbansu ta shiga nemansa tace Umma wai Abba fa? Shi
yasan Inda yake cewar Umma ta share zancen,
Naila ta mike zata bude kofa tace idan kika bude wallahi sai ranki ya baci,Umma
a waje zai kwana fa,ya kwana a bola ma mece matsalarki uwar shishigi cewar Umma.

Tsabar dolonci irin na Abban su Naila da yazo yaga an rufe gida bai iya kiran kowa
a waya ba,har yayi niyyar bubbuga musu kofa ya Kai hannu kenan sai ya fasa yace
bazan tashe ku ba haka kawai,uhm uhm Ina Sam sai ya juya ya koma masallaci ya
kwanta a ciki,a Nan yayi bacci idan ya farka ya tashi yayi Ibada ya koma bacci a
haka ya kwana,bayan anyi Sallar asuba ma bacci ya koma a masallacin,yace bazan
shiga hakkin su ba suyi baccinku, sai 10am ya fito ya nufi gidan.

Lokacin su Hidaya duk sun tafi makaranta sai Naila sai Umma,Naila ta tasa
kokonta a gaba da ta Saba da dashi kullum ita bata Shan shayi kullum sai ta siyo
Koko da kosai, Bata ga Abba ya dawo gida ba sai ta kasa Sha ta zauna tayi
tagumi,Umma kuwa ko a jikinta wanke wanke take yi a Jikin pampo tana faman zubar da
yawu, 10:11am Abba ya shugo gidan dauke da Sallama,Naila tace ahhh.... Alhmdllh
Abba Sannu da zuwa Ina ka tafi ne?

Ita kuwa Kubra Umman tasu ko kulashi Bata yi ba sabo da bashi da kudi gashi
baya iya komai,shi ba a fada da shi,yace Naila a masallaci na kwana nazo naga Kun
rufe kofa kar na tashe ku Kuna bacci shi yasa na kwana masallaci,Yanzu ma nasan Kun
tashi shi yasa nazo gidan,Tausayin Abbanta ya kama Naila matuka

Tace Abba kana zuwa ka dinga bugawa komai dare Kai da gidanka,tsaki Kubra ta ja
tace gidan Mohsin dai ai shi ya siyi filin ya gina mana da ai a wani wulakantaccen
gida muke ,wannan me zai iya tsinanawa kansa bare wani ta ja tsaki taci gaba da
wanke wankenta karshe ma ta gaji tace na gaji ka gama kazo ka karasa wanke
wanken,da sauri Abba yace to,Naila ta fara hawayen Tausayin Abbansu tace haba Umma
haba Umma ni zanyi a madadinsa,Abba bai iya cewa komai ba,.

Naila tace sai kiyi ta cewa Abba bai iya komai ba bayan gashi ya haife mu ai
kuwa ya tsinana miki,tunda gashi ma yanzu wani cikin ne Dake na Abba ai kuwa shike
tsinana abubuwa, Naila ta mike ta riko hannun Abba ta kaishi Palo ya zauna a kujera
tace Abba kaima Dan birni ne shayin? Yace ae Ina da ulcer bana Shan Koko,Naila ta
mike ta shige kitchen ta hado Masa tea ta fito,Umma ta mike tana harararta tace dan
ubanki mu gani

Ta sa cokali ta juya shayin tace madarar da kika gambaza Masa a ciki shi yake
siya mana ko kece? Ai Yaya Mohsin ke siya dansa ne Kuma ai kuwa kayansa ne cewar
Naila
Ae to naji bread din da kika dakko na ubanki ne? Ko kina sana'a ne Umma naga dai
Mohsin shi ke bada kudin sabo da haka Abba Yana da Iko da shi,kwafa Umma ta ja haka
Naila ta kaiwa Abba,shi Kuma ba zuciya ya fara Shan abinsa, Naila juck din kokonta
daga kwat kwat kwat sai da kusa shanyewa ta huta ta sake yin kwat kwat kwat, sanye
take cikin dan gajeren wandonta buje da shi ba kyan kama da vest a jikinta wai
kayan baccinta ne tun a dajinsu, gashinta buzu buzu a cukurkude

A haka Mohsin ya isketa ya Sha wankan shadda fara ya zuba kyau Yana ta kamshi
ya shugo,Umma ya fara gaisarwa har kasa,kamar wani sarki ne yazo haka Umma take
murna sabo da shike daukan nauyinsu komai da komai, Cikin Palon ya shiga Naila ta
kalle shi sama da kasa ta juya ta Kalli Abbansu ta tabe Baki ta zurawa Abban ido.
Abba yace lafiya Naila? Naila tace me yasa kuka haifo wannan a Nan gidan ne muka
zama Yaya da kani,ai kunyi hadama sai ku barshi a haife shi a wani gidan mu hadu
can muyi aure,har Umma dake waje sai da tayi dariya,tace wannan kwai sakara, Mohsin
Yana dariya yace sannu Naila,hannu ta mika Masa suka gaisa harda dunkule hannu ta
mika Masa shima ya dunkule nasa ya mika suka hade yanda gayu suke gaisawa.
Naila tace kayi kyau Yaya.

Abuja birnin tarayya Zaune yake a katafaren palonsa Saman kujera ta alfarma da
files a gabansa Yana ta rubuce rubuce ga laptop a gefe Yana dubawa,babu Sallama
Asmau ta fado palon tare da furta hey Baby,ko kallonta baiyi ba bai ma San iskar
data ajiyeta ba,kamar ba mutum take yiwa magana ba,gefensa tazo ta zauna, wata uwar
tsawa ya buga mata wacce ba shiri ta mike tsaye zumbur, ba tare da ya kalleta ba
yace waye yace ki shigo min gida har Palo ba sallama ba komai, zata yi magana kenan
cikin tsawa yace get out.

Asmau ta Sha Abaya me tsada tayi kyau itama kyakyawa ce wankan tarwada taci
make up,tace karfa ka manta Spark an mana baiko aure zamuyi,kwana nan zamu zama
miji da mata,tunda Mummy ni ta zaba Maka a matsayin mata amma sai ka dinga
wulakanta ni,ko da yake ai kowa ma Kai wulakantashi kake yi, Mima ma baka kyaleta
ba bare wasu Kai kawai wacce ta raineka itace mutum a wajenka, ko wacce mace an
kawo Maka kaki aurenta gashi Nan har ka Kai 31yrs baka yi aure ba ga kannenka nan
su suke Shirin yin aure, anya kuwa kalau kake baka da wata cuta ko aljana ta aure
ka,Kai duk wankan da mace zata yi bata birgeka duk kyawunta ko kallon mata baka
yi,ai kuwa ni nasan Aljana ce ta aureka ma.

Waya ya dauka fuskarsa kyakyawa a murtuke ya kira securities suka shugo mutum
biyu yace ku dauki wannan abin kuyi waje da shi karku sake na sake ganinta a gidana
,sorry sir suka furta suka dauki Asmau tana ihu da karaji tana tsine tsine suka
jefo ta waje, dama bata shigo da motar ba haka ta shiga motarta sai gidan Mummy
wacce ta raini Ashraf Spark.

Spark kuwa wata ajiyar zuciya ya sauke yace an maidani yaro,matar aure ma ace
sai an zabar min a rayuwa ni bani da yanci,me yasa ni ake takura min ne,ba laifi na
bane,nayi soyayya da yawa,nayi Yan mata daban daban baza su irgu ba at the end zan
gano kudi na suke so ko kyawun da Allah ya min bani ba, sabo da haka soyayya ban
Kara yi har abada aure na hakura bazan yi ba dama ban taba yinsa ba.

Kwanciya yayi a Saman 3str ya baje kafarsa daya tana kasa daya Kuma tana Saman
kujera,kansa ya dafe yana kallon sama ya Lula tunanin duniya.
Babban Amininsa ne ya shugo Kuma cousin brother dinsa Kamal,Sallama yayi ba tare
da ya kalle shi ba ya amsa Masa, Kamal ya kare Masa kallo sanye yake cikin
jallabiya coffee color me tsadar gaske kawai shining take tana sheki, hannu Kamal
ya mika Masa suka gaisa sannan Kamal ya tambaya Spark how far?

Ashraf Wanda aka fi sani da Spark Sam Ashraf asalin sunansa ya buya kowa da
spark yake kiransa har iyayensa,sabo da kalar idanuwansa da kwayar idonsa suke
kamar blue kamar baki Kuma irin kalar na wasu turawan, yace I'm good bro,Kamal yayi
dariya yace dan wulakanci shine ka Kori Asmau? Kafin ya rufe Baki Spark ya furta
mind your Business,ya ja tsaki ya Mike,shi dama bashi da mutunci baya ragawa kowa
duk abinda yaga dama kawai zai yabawa mutum a haka ma Dan Kamal ne shi yasa ya raga
Masa,mikewa yayi a fusace ya tattara tarkacensa ya bi steps zai haura sama

Kamal ya sheke da dariya yace an dai yi baiko ya zakayi rana za a saka Dan
ubanka,Spark Yana bin steps yace sai dai a daura da ubanka,Ubana? Yeah you heard me
clearly a daura da Ubanka, Kamal yaji haushi amma ya zaiyi da Dan uwansa abokinsa
Kuma yasan halinsa ba wata rayuwa yayi a kasar Nan ba sosai shi yasa yake wasu
abubuwan ba tunani,bashi da mutunci ko na kobo,Kamal kwafa ya ja tare da mikewa zai
tafi sai ya tsinci Muryar Spark yace kazo upstairs,Yana fadan haka ya juya,Kamal
kamar bazai je ba dai sai ya hakura ya haura sama, Saman lafiyayyen bed dinsa na
alfarma suka zauna,kawai spark Yana daukan wayarsa yaga sakuna suna ta shugowa ta
WhatsApp,budewa yayi sai yaga Asmau ce ta turo Masa pics dinta sun fi ashirin Nan
take yayi cilli da wayar ya kwadata da kasa tayi kwatsa kwatsa, yace zan iya kashe
yarinyar nan,can you Imagine,Kamal ya rude ya zaci wani Abu ne babba yace me
tayi,pics ta tura min sunfi 1million shegiyar yarinya mayya,to taga handsome ba
dole ta rude ba cewar Kamal.

A dinga sharhi pls bana son godiyar nan da stickers ni Kam 😅

BOOK 1

Free pages

300 ne ga me bukata

Accnt no
0175487861
Asmau Garba Muhammad
Gtbank

Katin MTN
08061929616

Yan Niger ku nemi


+227 90 79 59 39

AsmaBaffa
[12/4/2023, 1:28 PM] AsmaBaffa: 🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN TARI

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA
GAREKI
AIDA MAMAN TASNIM

11-15
Page naki ne
BESTYNBEELAT

Follow this link to join my WhatsApp group:


https://chat.whatsapp.com/J0ZFfbvon6ZGASEYAwZX5s
*Ina mata yan gayu yan kwalisa*
*Ina iyayen da suke so yaron su sufito fes*
*Albishirin ku kuzo gidan sauki da rahusa anan za a share hawayan ku*
*Munada kaya masu inganci nagarta gakuma sauki kayan mu sune kamar hak*
*Atampa*
*Les*
*Abaya*
*Sleep dress*
*Shoes*
*Mayafi*
*Hand bag*
*Misk*
* ETC*

MASU AUDIO BAN AMINCE A JUYA MIN NOVEL BA IZINI BA PLEASE.

Hannu Spark ya mikawa Kamal yace bani wayarka ya mika Masa ya danna wasu
numbers yace a kawo Masa sabuwar wata waya wacce taci uwar iphone a tsada da
komai,ba ko Ina ma aka San da irin wayoyin ba,a wani kwali take kamar kwalin
turare,ba a dade ba aka kawo Masa ya cire layikansa ya Maida cikin sabuwar wayarsa
ya mikawa Kamal yace jefa a Dustbin,Kamal yace kana raina min hankali wlh, ai bata
wani fashe da yawa ba sabo da almubazzaranci sai a jefa a shara a siyar da ita kayi
sadaka da kudin ai yafi,harara ya aikawa Kamal yace ance banda kudin sadaka dalla
ka bawa me so bana bukata, Kamal yace an gama ni Ina so tsaf zan gyarawa budurwa
ta,idan na bata har ihu zata yi, Spark yayi dariya tare da furta Dan gargajiya ne
Kai ai,suka fara hira da surutunsu na abokai a haka Kamal Yana hakuri sosai,Spark
yace wai wani ne ya kawo min aiki kaji kudin kuwa ya raina min hankali, Kamal ya
kwashe da dariya,Spark baya dariya shi a rayuwa sai tayi bala'in kamawa kullum a
Shirin masifa da rashin mutunci yake, yace ai wlh gwara na zauna kullum nayi ta
danna ashar,Kamal ya saki dariya yace wannan Dan rainin hankali ne,Spark yace Allah
yasa banyi signing ba Kuma kasan company ne,better cewar Kamal haka suka ta hirarsu
ta abokai.

Washe gari Monday sai 11am Mummy ta kirashi a waya bai daga ba sai lokacin da ya
tashi a bacci, yayi wanka ya shirya tsaf cikin kana Nan kayansa na kirki Yan gaske
kana ganinsa kasan ba pure Dan Nigeria bane,ya fito ya Sha kyau Yana kamshi tare da
taku cikin kasaita ,da gudu Securities suka bude Masa bayan motar da suka ga ya
nufa wata bakar mota,Yana shiga bayan motar shi kadai sai driver,Wata motar
securities dinsa suka shiga suka wuce,a hankali yace gidan Mummy,Driver yace okay
Sir, Yana hakimce a bayan mota Yana kallon gefen titi karaf ya hango wata budurwa
tasha gayu tana tafiya wata tsohuwa tukuf da kyar take tafiya tazo wucewa da
abincinta a kwano tana tsaye tana ci,jiri ya kwasheta tayi sauri ta rike budurwar,
a haka hannayenta da manja ta shafawa matar manja a Jikin kayanta, budurwa ta saki
wawan ihu ta juyo tare da shararawa Tsohuwar Mari ta hankadeta ta Fadi da abincin
nata,Nan take Spark yace da driver kayi parking a wajen waccen matan,driver yayi
sauri ya tsaya a hankali ya karaso saitinsu sannan yayi parking,Spark ko gama
parking ba ayi ba ya bude mota ya fito, nan take budurwar data juya baya taji an
fisgota da mugun karfi sai da gwiwarta taje kasa,ta mike zumbur kawai taji Mari ta
ko Ina kamar ba mutum bane yake marinta ta zaci Tsohuwar data mara Aljana ce itace
ta rikide haka ta dawo namiji saurayi kyakyawa,kyawunsa data Gani ta tabbatar sai
aljani,tace iya Dan Allah ki yafe min,Iya kiyi hakuri,sai kace ubanta cikin sojojin
da suke tsaronsa ya karbi bulalarsu da suke tafkar mutum da ita ya samu budurwar
Nan ya zaneta tas duk sai da ya fasa mata jiki har fuskarta kafin kace me
kamanninta sun canja mutane sun taru a wajen ana kallo,su tunaninsu ma kanwarsa ce
sabo da yanda ya zaneta,yace mahaukanta jahilai kawai tsohuwa dan ta rikeki zata
fadi mummuna irinki ma har wani yanga zakiyi,wahala tasa budurwar ta kwashe
takalmanta a hannu ta zura da gudun tsiya tana kuka har tayi gaba sai ta dawo tayi
reverse ta juya sai hanyar gidansu Inda ta fito.

Tsaki yaja ya juya ya Kalli Tsohuwar dake yashe a kasa tana ciwon kafa da kyar
take tafiya,zuwa yayi ya dagata yace Iya tashi,ku ma tsofaffin nan bakwa ji wasu
duk Kuna da gata sai ku fito titi Kuna wulakanta kanku,Tsohuwar tace Dan nan Allah
Maka albarka na gode wannan ba yinka bane yin Allah ne,shi ya turoka ka rama min,
na tabaka da Alheri wajen Dana nazo tunda ya taho cirani yau Shekara biyu kenan bai
dawo ba babu aike ba waya,ya manta Dani uwarsa,shine abokinsa ya taho Dani wajensa
ka ganshi can ma shine ya bani abincin nawa Allah ya Masa albarka, Spark yace Uhm
tsallakawa zakiyi wajensa? tace ae Dan Albarka,kawai Spark ya dauketa kamar ya
dauki tsinke ya tsallakar da ita,ya zaro kudade sababbi Yan dubu dubu Bai ma irga
ba ya bata,ya juya abinsa,tana Masa godiya ko waigowa baiyi ba ya koma mota suka
Kara gaba.

Gidan Mummy ya nufa ya isa gidan cikin takunsa na mazaje masu ji da


kansu,gidane na alfarma me tsari Wanda ba kowa sai masu gadi mutum biyu,Yana
parking masu gadin suna gaishe shi ko kula su baiyi ba ya dai mika musu hannu kala
bai ce ba ya wuce abinsa,Wani Babban mutum ne ya fito Wanda yasha wankan shadda da
alama me gidan ne zai fita shima, Clashing suka yi da Ashraf Spark kenan Nan ma bai
kulashi ba shima Alhajin bai kula Spark ba kowa ya wuce abinsa ba Wanda ya nuna
alamar yaga wani,direct part din Mummy ya nufa,har yayi nisa yaga bai dace ba sai
ya juya ya samu me gidan Yana bude mota yace Ina Kwana Daddy,Ko kulashi dattijon
baiyi ba,shima sai juya abinsa ya tafi wajen Mummy, sallama yayi a katafaren
palonta ya shiga Wanda kamshi ke tashi ta ko Ina,tana Dining cikin shiga ta alfarma
cikin Less me tsada white and Golden,Ransa a hade ya isa wajenta yace good
morning...kanta ta dago a hankali ta kare Masa kallo sannan ta hade rai itama

Ta mike tsaye tace bari na mike Kafi ganin tsayi na sai ka raina min hankali da
kyau, wato sabo da wulakanci shine jiya kayiwa Asmau korar kare ka sani aure ba
fashi gwara ma ka so ta, wallahi ka kiyaye ni karka ga wai ubanka babban Soja
ne,kaima ka fara aikin soja kayi resine ba abinda ya dameni,ni na raineka
Mahaifiyarka kawai haifarka tayi baka isa ka min iskanci ba,Dan karamin bakinsa ya
tsuke yace Ohhh Mummy kin san bana sonta, ki daina jawowa Ina bata miki rai a
kanta,ni fa ba yaro bane babba ne,Ina aiki Ina da kudi ku daina rainani komai kice
sai yanda kika tsara zanyi bazai yuwu ba fa Ina fada miki kar kuyi Kuskuren daura
auren nan wlh zan iya sakinta a wajen nan take,zaku ji kunya ki daina turota gidana
haba ai ba tsari ba class mace tana bin namiji har gidansa Kuma gida ni kadai a
ciki,duk ranar da ta sake zuwa sai na mata tsirara sannan zan jefota waje idan baku
yarda ba ta sake zuwa ku gani, Kai ya girgiza kamar Wanda ya Sha kwaya yace nayi
warning naku a daina takura min bana so a kiyaye, ya juya ya fice abinsa ba tare da
ya saurari me zata ce ba.

Mummy ta zauna jiki a sanyaye tace innalillahi na cuci kaina Dana dinga barin
yaron nan a kasar waje gashi nan yafi karfina ayi yaro duk ya gagari kowa ta zuba
uban tagumi.
Shi kuwa gogan gidan Mima ya nufa wacce itace ta haife shi,gidan ko Ina sojoji
ne birjik sabo da Babansa Babban Soja ne,sannan yayansa da kannensa ma mazan Sojoji
ne, Yana shiga ya iske kannensa mata da Maza har da matan duk da kayan sojoji a
jikinsu suna ta faman rawa a Palo sabo da tabara,Yana shiga suka kashe kidan sabo
da sun san rashin mutuncinsa ba Wanda ya bari, part din Mima ya shiga tana bedroom
tana shiryawa mijinta kayan tafiya zai bar kasar, sallama yayi ya shiga itama a
tsaye yace morning Sweety

Murmushi tayi tace ka tashi lafiya? Ni fa bana son gaisuwa yanzu da ba lafiya
nake ba ai bazanzo ba,to zauna mana ,bashi ya kawo ni ba,ki fadawa Kanwarki tunda
ke yayarta ce ta daina matsa min bana son Asmau ki fada mata Ina ganin girmanta
tunda ita kuka bawa rukona kawai an bata ni kyauta duk ta matsa min,bana so a fada
mata.

Kai Dana ne dama? ai ni sanda na mallaka mata Kai har abada na bata ni ba ruwana
da safgarku, ku kuka sani kunfi kusa ai,kar ka sake kawo min karar uwarka, Kai da
Rafeeq me yasa bakwa son a zauna lafiya ne,ga Rafeeq Kuma ma ko Yan Nan gidan bai
saurara sai yaga dama daga shi sai Islam abokinsa to ya fika ta wani bangaren shi
Yana yiwa wacce ta rike shi biyayya baida kamarta,amma banda Kai you are so
stubborn.

To kuwa an kusa sawa na fara neman mata nima indai za a aura min Asmau neman
mata zan fara,Yar uwarka ce fa cewar Mima,yace Yar uwar me ni Ina ruwana da wasu
Yan uwa,tace toooo zagi ya matso kaina,juyawa yayi ya fice abinsa ko bangaren
mahaifinsa bai saurara ba ma yasan ba zama yake ba,duk Yan gidan basa gaisuwa daga
Hey shike nan,ba Wanda ke safgar wani sai da dalili,ko sun hadu baza ka gane Yan
uwa bane sai dai a kamanni,shi kuwa Spark bai ma fiye kama da su ba,kamar ba Dan
kasa ba haka yake kamar a wata kasar aka haife shi can Jinin nasara,ga tsirfa wani
irin murdadden mutum ne.

Bayan sati daya Spark yayi shiri ya bar kasar ya tafi Germany,ba wanda ya
fadawa sai dai aga baya nan kawai, Kamal kadai ya fadawa,Indai suka ga shuru bai zo
ba to baya kasar kowa yasan wannan amma indai Yana gari dole sai yaje ko fada anyi
da shi.

Naila dai Umma ta sata gaba sai tabi Hajiya Tagwadas zuwa Abuja haka Mohsin
yace tayi hakuri taje tunda sati biyu ne kawai zata yi,waya Yar karama keypad ya
siya mata da layi rike wayarta na farko a duniya kenan ya koya mata yanda ake
amfani da ita,ta hada kayanta a Yar jaka da Umma ta Bata.

Yau zasu tafi da wuri ta shirya taje har dakin Abban su ta same shi Yana Shirin
fita aikin gadinsa da ya Saba tace Abba zan tafi ayi mana addua,yaran yanzu ana
musu addua ma ya muka kare kana dai gani yanda dole sai mun lalace bare ace ba a yi
min addua ai lalacewar Abba sai tafi haka,ni kaina tsoron kaina nake yi,Abba in
kana jin Yar hau to nice sabo da haka a surfa min addua ta cire mayafinta tace dafa
Abba sa min albarka.

Abba yace to.. to ya dafa kanta yanda tace ya furta Naila Allah ya tsare,iya
albarkar kenan?ta tambaya, ya zazzaro idanuwansa Wanda suke kamar yayi zawo na
shekaru yace a dai dinga kula,abi duniya a sannu,a Dinka taka duniya a
hankali,yawwa na gama shike nan jeki cewar Abba, Naila bata gane hausar ba tace to
Abba sai ta fito tana sanda tana tafiya kamar barauniya zata saci kayan wani.

Lokacin Mohsin ya shugo gidan ya iske abinda Naila keyi tana faman sanda yace ke
Kuma mene haka? tace Abba ne yace nabi duniya a sannu na takata a hankali,dariya ta
kama Mohsin ya dinga sheka dariya yace to Yar kauye ba haka yake nufi ba fada ya
miki fa lokacin ya ganar da Naila me ake nufi,ta dinga dariya da maganarta ta yan
Fulani tace aradu ni kwai wawiya bani da Kai sai na daukan kaya ai Affa shi baya
min haka sai dai ya dinga washe min Baki.

Tace Abba kuwa harda zazzaro Ido duk akan zai sa min addua ya Ilahi wlh sai naga
kamar Wanda ya Shekara a gadon asibiti yana jinya,gaskiya Umma tayi babban Jihadi
data iya auren Abbanmu kan uba wlh da nice gwara na tafi yawon ta zubar, Mohsin
yayi dariya kamar ba gobe,Naila tace Allah Yaya kirjin Abba kamar na fara,baki ta
toshe da hannunta tana dariya a hankali tace a haka wai shine bargon Umma ai yasin
ko quarter din Umma bazai rufe ba,ya Umma take yi da Sanyi? Allah ya bani kudi na
siyo mata bargo babba na gaske karta dogara da kirjin Abba,ta sake rufe bakinta da
tafin hannu tana dariya Kallon Mohsin ta yi tace Yaya da alama Kun shirya da
matarka ko?

Rada ya mata a kunne yace ae maganin gargajiya za a bani,dariya tayi tace bana
murna kishi nake yi da hassada me yasa kuka Jone? Ai tunda naga ka shugo kana yaye
mana hakora nasan jiya an rufe kofa,baki ya make mata, tace nidai kishi nake ta
fada tana harararsa.

Mohsin yace baki tambayi Amal yarki ba yau,Naila tace wai Kai Yaya Nan murna kake
yi kayi abin kunya ya fito fili? Ban gane ba ya furta,tace abinda kayiwa Hanan
matarka ta samu ciki ta haifo Amal ai rashin kunya kuka yi a daki sannan aka samu
cikin gashi ta haihu kaga kowa yasan me kuka yi abin kunya ya fito fili,Mohsin
dariya yayi yace ke kika sani ni dai na haifi 'yata, kallonsa Naila tayi tace uhmm
kaji da shi, nifa shi yasa Sam ba sosai nake kiranka da Yaya Mohsin ba tunda ka
haifi Amal nasan kaima A ne kana rufe kofa,Mohsin gashinsa me yawa ya shafa.

Hidaya yau ba school su hudun suna gida,tana ta aikin gida Hidaya komai ba
abinda bata iya ba a rayuwa na aikin gida,ita kuwa Naila ko wanke wanke komai sai
dai ayi mata.

Mohsin ne yaja Naila gefe yace ai dai gidan Yan uwanta zaki raka kawar Umma ko?
Naila tace ae haka tace shine fa Umma tace masu kudi ne gidan suna da Maza wai na
bude Ido na kalle su ko zanyi saurayi,wai yaran dangi ne gida gida duk dangi
ne,Mohsin yace kina Jin wahala ko baza ki iya ba ko da matsala ki gudo gida kinji
ko ki kirani a waya kinji ko? Tace ae naji Yaya,I will miss you,ka kular min da
kanka,Jikin Nan natural a adana shi,zan tsananta bincike ko Kai ba Dan Abba da
Umma bane ya kamata ayi bincike,zai wahala ma ba musaya aka yi musu a asibiti
ba,Dariya suka yi Mohsin yace a gida aka haife ni ba a asibiti ba kinga dansu ne
ma, kiyi hakuri ki samu wani yarinya, Nooo... rayuwa sai dai Yaya ta furta tana
dariya,wasan su kenan tun Umma tana kulasu yanzu zuba musu Ido take yi.

Hajiya Tagwadas ce ta shigo da uwar akwati anci uban gogoro kamar Yar yorubawa
tace yawwa ke 'yata fito mu wuce me napep zai kaimu tasha,Umma tace to kuje Naila
Allah ya tsare,Naila tace ke Umma Tagwadas daukar min jakata ai ke zan raka unguwar
bazanyi wahala ba, ni sandata kawai zan dauka waye yace kice na rakaki shike nan
jakar ma sai na dauka ,Naila dai da kyar aka lallabata ta saka riga da skert na
atamfa sabuwar da aka Dinka mata,tayi mata masifar kyau,ai suna ficewa daga gidan
ta ja skert dinta sama ya dawo wajen gwiwa duk kaurinta a waje ana kallo,Tagwadas
tasan taurin kan Naila yanzu sai tace ta fasa zuwa, ita da take so a can ta samu me
kudi yace Yana son Naila cikin Yan uwan nasu shike nan ta samu hanyar shigar su
burinta kenan shi yasa ta zuga Umman Naila tace zasu samo kudi da miji na gari me
Naira.

Suna cikin Napep Tagwadas tace gidan da zamu je basu taba haihuwa ba,Kuma ance
matsalar a mijin ne,Naila ta zaro ido tace to ga shawara ta samun kudi Umma
Tagwadas,tace Ina jinki Naila,me zai Hana muje ayi min askin Maza me kyau ayi min
Daadaa, nayi shigar Maza kawai na koma namiji sai na basu magani ko zasu dace Kinga
idan suka dace mun zama masu kudi musamman ke da kika yi hanyar magani,idan naje a
mace baza suyi Amanna da maganin ba
Hajiya Tagwadas tace wannan maganar taki ta kama hankalina muje kawai shagon
aski akwai gidan kawata a can layin sai mu siyo kaya a gwanjo na Maza ki shirya
tsaf, Naila taji dadi sai suka wuce shagon aski, Naila ta zauna tace ayi mata askin
zaratan samari masu ji da kansu ta zabi wani kala Daadaa,aka rage gashin kuwa tare
da kwashe gefe da gefe aka tura gashin ya koma baki wuluk sannan aka yi mata Daadaa
a wajen gashin me yawa, ba karamin kyau tayi ba, suna fitowa suka wuce Kasuwar
Kofar Wambai Gwanjo suka siya na Maza kala biyu manya manya kayan masu Fadi,gidan
Kawar Tagwadas suka je a can Naila ta fara shirinta, ta samu Bandage ta tube
rigarta ba bra ta nade kirjinta tana zagayowa dashi ta gadon bayanta ta manne
breast dinta da fatar jikinta ta sake mannewa da seletape,kirjinta ya dame daf
kamar bata da Breast sannan ta saka kayan mazan barma barma,sai ga Naila ta fito a
Dan matashin saurayi me kama da mace.

Naila tana fitowa Hajiya Tagwadas ta tafa mata tana dariya,Naila tace daga yau
Sunana Jamilu,karki manta fa Jamilu nake,tafiya suka yi sai tasha.
Naila har suka karasa tasha bata yiwa Hajiya Tagwadas magana ba ko sau daya,ta
fito daga Napep tana wulwula sandarta tana wasa da ita da gani ta kware da wasa da
Sanda salo salo take wulwula sandar,kafin kace me duk ta ja Yan kallo an taru ana
kallonta ana ta dariya, zaton kowa Namiji ne, sai da ta gaji ta daina lokacin sun
samu motarsu me kyau aka sa musu kayansu suka shiga mota sandarta akace ta kawo a
sata a bayan mota tace aradu ban badawa,ai sai naji kamar nayi wata mummunar
mantuwa bada ni ba.

Ana fara tafiya Naila tayi bacci har akaje bata San anje ba sai da zasu sauka
aka tashe ta,sai ta tuna ashe fa Abuja zasu,Hajiya Tagwadas tuni ta sauka ta fito
musu da kayansu,sannan Naila ta fita itama tace garin kamshi iri iri uhmmmm,sai
munje gidan ma zaki gani tun bama gidan sojojin ba,Naila tace uhmm yanzu mene next?
Taxi suka shiga ta kaisu katafariyar unguwar gidan Mummy ta nufa direct sabo da
sunfi dasawa ta dan fi saukin Kai,Hajiya Tagwadas tana buga gate me gadi ya leko ya
ganta ya Santa Nan take ya bude kofa Yana washe baki,Suka shiga suka ce ah sabon
Dan aiki aka kawo mana ne suna kallon Naila Jamilu.

Naila tace wuce nan yaro ni da nake da shanu nafi karfin aikatau,shuru suka yi,
Tagwadas tiryan tiryan ta kaisu har palon Hajiya suna shiga suka sameta zaune a
kujera ta kafa tulun shisha a palon tana faman zuka tana feso hayakin waje, Naila
ta zaro ido tare da furta kaga dattijuyar banza, ke Inna kiji tsoron Allah tsofai
tsofai ai idan lokacinka ya wuce to ya wuce,ko kara'i kike yi ne? Hajiya Tagwadas
ce tace Kai Jamilu dalla rufe mana baki,Mummy ko ta tasu bata yi ba bata San ma
Allah yayi mutane ba a wajen a haka itace me saukin Kai.

Tagwadas ta Fadi a gabanta tare da mika gaisuwa kamar taga sarauniya tace ranki
ya Dade ajiyar Dana na kawo miki Dan kawata ce ki dan bashi dakin zama ya zauna
kafin naje na dawo,Naila ta bude baki mamaki ya kamata,zata yi magana Tagwadas tace
karka ce komai Jamilu zamu raba gari,Mummy tana ta bulbulawa huhunta shisha tace
okay fine barshi kije,tace godiya nake uwar dakina,kudi a zube a gefen Mummy ta
irgo wasu ta mikawa Tagwadas tace ya mutan kauye? Tagwadas ta furta Naje kauyen
waccen satin kuwa suka ce a gaishe ku,hannu ta daga mata tace ya isa tashi ki
tafi,ko kallon Naila bata yi ba,Naila tana kallo Tagwadas tace Kai Jamilu ka zauna
a nan zanje na dawo,Naila ta tabe baki tace to tare da cakewa a Jikin sandarta tayi
wata tsaiwa akan sandarta yanda Fulani ke yi,Mummy Yan aiki ta kira tace gashi Nan
ku kaishi masauki ku bashi abinci ya koshi a nuna masa komai,Naila dai tana kallon
ikon Allah.

Me aikin ce tace muje ko part din maza ta nuna mata, sannan ta kawo mata
abinci ta nuna mata toilet a cikin dakin sannan ta fice,Naila taci ta koshi tayi
wanka ta kulle kofar da key sannan ta canja kayanta na mata doguwar riga marar
nauyi ta material tare da saka hijab ta gabatar sallolin da ake binta tayi addua,
bayan tayi Sallar Isha ta kwanta bacci dake dare yayi.
Bata farka ba sai washe gari da safe bayan tayi Sallar asuba take ta koma bacci
tana sharara uban bacci har 11am sannan yunwa ta tasheta,wanka tayi ta sake nannade
kirjinta ta manne da Seletape ta Maida kayanta na Maza Wanda ta zo dasu a jikinta,
kayan matan Kuma cikin Inda ake ajiye kaya a dakin sip Nan ta bude ta boye su a
ciki sabo da kar a kamata sai ta bar kayan mazan kala daya kacal da magungunanta na
siyarwa na gargajiya duk suna cikin Jakarta,ta nufi part din Mummy,tazo shiga kenan
taji suna ta fada da mijinta.

Mijinta Alhaji Aliyu yace wallahi aure babu fashi sai nayi shi,ni Kuma baka isa
ka Kara aure ba sai dai idan bana raye ko baka raye,Kai zan iya kisan Kai,zan iya
kashe ka na kashe kaina wlh,indai ka Kara auren Nan sai kaga ba dai dai ba zaka San
wa ka aura,ba a abinda kika isa kiyi karamar Yar iska,tace to mu zuba mu gani waye
zaiyi kasa,yace mu zuba ya fito a fusace ya kusa yaci karo da Naila tace cikin
Muryar maza Sannu kayi hakuri,Ina kwana? Hannu kawai ya daga mata ya wuce abinsa
dake gidan ko Maza ma free to enter ne.

Palon ta shiga da sallama ta samu Mummy ta zube a kasa tare da Kifa kanta a
Saman kujera tana rusa uban kuka,Naila tace akan kishiyar wlh kin bada mata ai ko
ni Jamilu da ace macece ni to bazan yi haka ba,baki hadu ba,Mummy kishi na cinta ta
manta ma yaro ne Jamilu sai tace baza ka gane ba,wlh wlh tunda na aure shi bai fi a
irga ba muke saduwar aure bashi da lafiya gabansa baya aiki sosai gashi ban taba
haihuwa ba duk nayi hakuri dashi na zauna a haka shine zai min kishiya,Naila kamar
babba tace share hawayenki Waraka tazo miki Allah ne ya kawo miki magani har gida
Inshaallah daga yau sai kince Hallare ta isheki,Dan Nan mene Hallare? Naila tace
Abar da kike kuka a kanta.

Naila taci ga yanzu ni Kinganni sabo da sanin kan aikina ba kalar da ban sani
ba,ke me ya kaiki auren gajere?,irin tasu fa shape din kubewa garesu,kin san okro?
Kubewar Miya Banda me kahon barewa,kin san a kubewa ma akwai doguwa to ba kalar
doguwar ba, Yar gujub din itace irin ta mijinki,Ina ganinsa nasan tasa ba pole
bace,ni fa muna hada Ido da namiji to tsirara nake ganinsa, harda tafa hannu tace
duk wani Dan uwana namiji zigidir nake ganinsa,Mummy tace wallahi Dan nan ta
megidana haka take kubewa sak,ah na fada miki ai muna yin clashing dashi na hango
shi tumbir Zigidir, Mummy tace Allah da baiwa yake,Naila tace a daji na girma ni a
Nan fagen na kware,ai gado nayi a wajen kakana tun na goma Sha biyar baya da suka
shude sana'arsu ce,ba wanda yayi gado a kaf dangin mu sai ni nan Jamilu,Ina bada
magani idan ta kama ma dole sai na gani to sai na ganta nayi mata aiki da kaina da
hannuna,Hajiya ta saki baki tana kallon Jamilu,Naila tace ae fa idan ta kama to sai
kalleta,ta nuna idonta da hannu tace akwai wani sirri a idona Ina kallonta lalurar
dake wajen zata fito sabo da taga abinda ta gani a cikin idona.

Tace kina so na baki maganin ki yarda da Allah,bani zan warkar dashi ba Allah
ne amma idan ya zama Sila sai Kiga kin dace,Mummy tace kawo na gani,akan sana'ata
kice sai na kawo kin gani ma,in kina so sadaka zan baki in bakya so ki bar min
abina wannan maganin da kin san aikinsa da ko million nace siya zaki yi.

Fita Naila tayi ta bude Jakarta ta kwaso su gasu nan a kulle a leda Dan mitsil
mitsil gari ne green da wani red,ta kawowa Mummy tace gashi wannan kala biyu ne,Dan
girki zaki Masa shi kadai dai dai cikinsa ki juye Masa ki tabbatar ya cinye tas
shike nan daga lokacin ki tafi bedroom ranar kika yi wasa sai an kaiki asibiti an
miki dinki,Mummy dai badan ta yarda ba ta karba,Naila tace to ai kunyi fada ta ya
zai ci girkinki yau? tace kiransa zanyi na bashi hakuri,kina tunanin Hakan zai sa
ya yarda Dake ai zaiyi tunanin da wata a kasa wai ya kike hakane kin fa haife ni
duk da ni namiji ne amma baki da wayo,Mummy ta Kalli Naila da sauri wannan gatsali
da yaron yake yi sai kace danta Spark babu mutunci a harkar su.

Naila tace ki jira shi ya sakko da kansa sannan ki Dan bashi hakuri sama sama
sannan ki sa Masa amma da wuri haka ai sai ya raina ki,nifa da ace ni macece ba Dan
iskan namijin da zanwa biyayya ni mamaki ma kuke bani da kuke nacewa mutum
haba,Mummy ta saki Baki tace ikon Allah kai nifa na haifi yayanka ma ko yayarka ta
biyu bare kai,ka kula kana gidana Ina taimaka maka da abinci kana fada min magana
ba ladabi,Naila ta kalleta tace bani maganina na bar miki gidanki ni haka nake Ina
da kirki Ina da zafi, kaina da kwari idan na birkice hmmm.

Mummy sama ta haura abinta Naila ta baje a kujera kamar gidan ubanta harda kiran
Yan aiki,wata tazo a ciki tace zubo min abinci ki hado da hantar kifi, Yar aiki
tace babu hantar kifi,tace to hantar kaza fa? Babu itama,zabo? Babu hantar
zabo?,Naila tace shima comon zabon abin banza? tace ae,tace to ta Dan maraki? Akace
babu,tace ta rago fa? Yar aiki tace sai ta Sa gaskiya,Naila tace uhm uhm bana cin
Naman Sa sabo da ai cin Amana nayi shanu dabbobinmu kawai sabo da cin Amana naci
namansu Bada ni ba,Yar aiki tace sai kace me bautar saniya, a'a daga India nake
Naila ta furta da Muryar maza,Uhmm me zan kawo yanzu? Nasan ma babu Koko kawo min
abinda kuka dafa banda shayi.

Naila dai tana gida har kwana uku suna shiri da Mummy sabo da maganin da Naila ta
bata,Kuma mijinta ya fara sakkowa sun ma kusa shiryawa gaba daya shi yasa yau Mummy
zata Masa girki da magani,taci gyaran jiki sosai za a angwance,yau wankan data
dauka ma na musamman ne, Naila tana kallonta sai shanawa take a gidan masu hanu da
shuni har yanzu Kuma bata ga wani namiji yazo gidan ba basu je gidan sojojin ba,ta
dai kira Mohsin ta fada Masa komai normal.

Mummy Dan faten wake da doya tayima Alhajinta yaji kifi,Yana son kifi iya
cikinsa yanda Naila tace haka tayi,part dinsa ta nufa ta Kai Masa yace zo Halima,ta
koma zata zauna ya jawota jikinsa yace Hali dubu tawa ko kefa ai gwara da kika
hakura nayi auren mene aciki kece fa ta gaban goshi,wallahi ba wacce zan so sama da
ke a duniya,Mummy tace uhm ta kakalo murmushin dole tayi dai tace ci abincinka ko
na baka a baki,yace da zan fi son Hakan,ta dauki spoon ta fara bashi a hankali Yana
ci,har ya kusa cinyewa bai sani ba sabo da dadi sai da ya cinye tas sannan ya Sha
ruwa sosai,har zai kwanta yace naji na gaji ne sai ya dauki carbinsa Yana tasbihi
ya kwanta a Saman bed dinsa,Mummy ta kwashe kwanikanta tas ta fice ta wanke Kal ta
Adana sannan ta koma wajen me gidanta,carbin ta samu ya jefosa kasa tana zuwa ta
daga hannunsa taji ya saki alamar ya mutu rai yayi halinsa, murmushi ta saki tace
akan kamin kishiya wallahi gwara ka sheka can Kai ka isa mutumin banza butulu,Kuma
dole group na company naku su ajiye million goma in Sha bushasha ta,Hannu ta Dora a
Kai da kururuwa ta fito tana ihu tana bako ya kashe min miji,Magani ya bani na
karfin Maza ashe guba ya bani Mummy ta zunduma waje ta tara mutane ta kirawo
makwafta,ta hau kiraye kiraye na Yan uwa da abokan arziki sannan ta kira police
suka dungumo gidan, gida ya cika makil,Har Hajiya Tagwadas ta kira a waya ta taho
hankali tashe domin ita har ga Allah burinta ta samu shiga a cikin masu kudin
danginsu ta dinga samun kudade shi yasa ta kawo Naila ko zata Saba da su ta samu
saurayi a cikin Yan gidan tunda suna yawan zuwa gidan sannan tasan watarana Mummy
zata iya tafiya da ita cikin dangi kuma sai suka canja su gwada maganin ko Mummy
zata dace mijinta ya warke ta haihu.

Naila bata gane batu ba,sai da Mummy ta shaketa tare da kifa mata Mari tana
jijjigata tana cewa matsiyaci ashe maganin kisa ka bani ka kashe min mijina ta
dinga zabgawa Naila Mari, Naila zuciya ta ciyota ta dauki sandarta ta bugawa Mummy
iya karfinta a kanta Nan ma Mummy da sharri ta sulale ta fara suman karya farrrr
farrr, Naila ta jefar da sandar ta haye ruwan cikin Mummy ta dinga rama marinta
mummy duk ta shanye Marin nan wai bata sani ba suma take, Naila ta daga hannaye
sama tace a tafi dani da hujja Allah shine shaidata,wacce Bata San alkhairi ba
butulu.

Da ace baki saka Masa guba ba maganin Dana baki kika saka Masa wallahi da
aurenki ya daidaita maybe ma ke da kishiya shike nan watakil ma ki haihu kinwa
kanki, ta ciro takalminta ta bugawa Mummy a Baki baki ya fashe amma duk Mummy wai
suma take bata sani ba bayan tana Jin komai.
Mutane kafin kace me gida ya cika dam ko Ina manya Maza da mata,ga dangi ta ko
Ina suna ta parking motoci ta bangaren mata da Maza,da kyar aka banbare Naila daga
kan Mummy, kuka ta saki taje ta shaki Hajiya Tagwadas tace Allah ya isa
d...da ...da .kika...kawo ni Nan...duk kafin kace me sojoji ta ko Ina a gidan
matasan samari hadaddu suna ta dira dangi, a tsakiya aka saka Naila duk an zagayeta
ana kallonta mutane har sun firfito da waya,ba Wanda ya gane macece,Misam ne ya
Dana bindiga yace wallahi duk Wanda ya daukar mana hoto sai na harbe shi,ai kowa a
tsorace yayi kasa da waya wasu ma jiki na rawa suka kashe wayar,Mummy dai tana can
mata suna ta yayyafa mata ruwa da ta farfado tace wayyo mijina sai tayi farrrrr
luuuuu da Ido sai suman karya, suna ta fama sai da kyar ganin za a gane ta sannan
ta farfado gaba daya ta kurma uban ihu ta fado cikin mutane da gudu ta isa Inda
Naila take ta Kai hanu zata shaki Naila,lokacin Naila zuciya taci karfinta hannunta
ta rike gam iya karfinta ta lankwasawa Mummy yatsu,Kara da Ihu Mummy ta tsala tace
a dake ka a hanaka kuka ga Mari ga tsinka jaka, ta sake Kai daya hannun Naila kamar
Dan biri tayi tsale ta dane Mummy ta shake Mummy,Misam a ransa yace tunda yaron can
yake fada haka yana da kamshin gaskiya ya kamata ayi bincike me tsanani.

Mummy ta kwace kanta da kyar tace namiji ya rungumeni Kuna kallo wayyo...namiji
ya rungumeni fasiki ne, Naila hawaye baya tsayawa a kumatunta Taga dai Maza manya
sun shiga part din Alhaji Aliyu ana Masa sutura, da kanta ta taka gaban police da
suka shigo ta mika musu hannayenta biyu tace cikin turanci ku tafi dani muje nasan
Allah zai fitar Dani,sai lokacin kowa yayi mamakin Jin turancinsa ba kowa ne ma ya
iya irin nasa ba Dan kuwa Naila ta iya turanci ba karya.

Yan sanda suka sa mata sarka a hannu ta shige mota da sauri domin kallon da ake
mata gwara ta shiga motar taji sauki tsoro take ji kar a gano macece ce shine
damuwarta kawai, suka ce ai kuwa duk mutanen Dake gidan abin ya faru sai an tafi
dasu har Mummy, Tagwadas itama kuka take domin itace ta jawa Naila wannan masifar
haka ta daka tsalle tace nima a tafi dani,sai masu gadi suma an tafi dasu,Mummy
tana an kashe min masoyi ta shiga motar Yan sanda aka tafi dasu,sai Yan uwa a gidan
suna zaman makoki aka Masa sutura aka kaishi makwancinsa aka ci gaba da zaman
makoki,wayoyin Ashraf Spark sunki samuwa dama haka yake yi ya tafi waje bazai kira
kowa ba,da yawa ko number dinsa ta Nigeria wasu basu da ita,ko ka kira ma sai yaga
dama zai dauka.

Sai Kamal aka sanarwa ya sanar Masa,yace shima Bai kirashi ba,Daddy yace to
idan ya nemeka ka fada Masa tunda shi bashi da hankali,Dake da yawansu sojoji ne
wasun su duk basu wani ji abin sosai ba sun Saba ganin mutuwa da kisa da cases
daban daban.
Bayan kwana uku ana bincike amma Naila baza ta fita ba Sam, gaba dayansu case
din kotu aka mika su,amma Mummy sai da tayi kutun kutun aka Maida karar can kotun
Kano sai kudi take kashewa lallai ayi sauri a yanke hukunci kar bincike yayi
tsanani a ganota.

Sanda aka sanarwa da su Mohsin me ke faruwa hankalinsu ya tashi matuka ba


kamar Mohsin da suke shiri da Naila,yafi kowa shiga wani hali sai Abbansu shima ya
damu sosai,Umma kuwa bala'i ta hau yi tace Yar iskar yarinya ce bata Jin
magana,taurin Kai da ketare maganata shi ya jefa Naila a wannan halin,nayi Imani ko
kaffara bazan yi ba kin Jin maganata da Naila ke yi shi ya jawo mata sai da nace
kar ta siyar da maganin Nan bana so Bada yawu na ba,amma jarabar taurin Kai da
jahilci da hauka shine ya ja mata ai gashi Nan hukuncin kisa za a yanke mata Allah
yasa ba ita kadai na Haifa ba,nayi nayi tayi aure gata da masoya taki ji ai gashi
Nan,Kuma wallahi babu Mai zuwa Kai mata ziyara a nan gidan sai taji jiki a gidan
yari.

Abba yace koma mene ke kika jawo ke kika turata,to na turata baza kaje ko kotun
ba wallahi,ance an kawo shariar Kano to baza kaje ba,nima baza ni ba Kai duk gidan
Nan,Hidaya tace Haba Umma ke kika haifeta fa Dan Allah kiyi hakuri sharri aka mata
wlh baza ta iya kashe wani ba,shima kaninsu yace wallahi sister baza tayi ba ni dai
Ina tausayinta,kanwarsu ta karshe itama tace nima haka bana bayan Umma.

Umma da bala'i tace to naga Wanda zaije kotu ko an yanke hukunci naga me zuwa
ziyara gidan yari,Hidaya tace nidai ance soyayyar Uwa da yaranta daban ne amma ke
Umma taki ba haka bane, Umma jaka ta dauka ta fice an rasa Ina take zuwa tunda
cikin ya Dan Kara girma Umma kullum sai ta fita ta dawo ko ina take zuwa oho Kuma
idan zata dawo sai a ganta da fara'a ashe warin gardi take shakowa ko warin taba
sigari.

Mohsin Kam baya iya bacci sabo da halin da Naila ke ciki kullum a cikin damuwa
yake,gashi su ba masu kudi bane sai rufin asiri,ita Kuma Hanan matarsa ta takura
Masa ita baya mata soyayya baya kulawa da ita sai tunanin kanwarsa,bashi da lokacin
fada da ita sai dai addua da yake faman yi Allah ya fitar da Naila.

Gashi Umma ta Hana kowa zuwa kotu har sai da Alkali ya bukaci ganin iyayen Naila
sannan ala dole yau za ayi zama na biyu a kotu shine Umma,Abba da Mohsin suka
halarci kotu,ana jiransu ana cewa zasu shugo aka yi yuuuu dangin Mummy da na mamaci
mijin Mummy suka zuba musu Ido,ga sojoji a kotu da kaki duk a layin Mummy suke tun
a Nan Mohsin a ransa yace Nailansa baza ta kubuta ba dole tayi prison,sai dai ko
nan gaba Allah yayi ikonsa.

Naila tana tsaye a cikin Inda Wanda ake tambaya ke tsaiwa ta Kalli Umma suka
hada Ido,Umma kuka ya taho mata tayi sauri ta dauke kanta sabo da uwa ai dole uwa
ce,Abba kuwa tuni Yana ta sharbar kukansa dama kadan yake jira,Mohsin ne ya Kalli
Naila tana Nan da riga da wandonta na Maza,suka ga ta koma namiji ko hular babu a
kanta an cire a Inda take tsare, dama Tagwadas ta fada musu komai tace su rufa mata
asiri kar kotu ta sake ganowa macece tayi shigar Maza Naila baza ta tsira ba za ace
lallai tayi kisan me yasa tayi shigar Maza.

Naila Mohsin ta kalla idonta ya ciko da kwalla ta shanye kukanta sai hannu ta
dagawa Mohsin tana murmushin karfin hali, an hana magana ba dalili amma sai ji aka
yi tace Yaya Sandata itace gadonka tana gidan munafukar nan wacce ta min
sharri,magana alkali yayi ko kulashi bata yi ba tace Yaya ka tabbatar ka dakko
sandar nan tana dakin da aka bani ka rike ka dinga tunawa dani kafin na dawo,Abba
ka daina kuka zan dawo fa Inshaallah verysoon ana yanke daurin rai da rai Banda ni
ban aikata ba Allah zai fitar dani ko Bada sanadin kowa ba,ka rubuta ka ajiye kamar
na fito,ku daina wani damuwa ni jajirtaccen namiji ne, zuciyata da karfinta zan iya
da gidan yari ko sojoji ne a ciki fitowa zanyi bare wasu gandrobobi,Ni Jamilu na
fada muku ko ta Yaya sai na fito Dan bakin ciki sai dai ya mutu ta Kalli alkali ta
karasa da gwalo tana Masa gwalo .

Naila tana ta masifa a kotu ko alkali shuru yayi Yana kallo wani abin ma dariya
Jamilu yake bashi sai ya ganshi kamar mace in yana wani abin,ta Kalli su Misam da
sauran matasan kyawawa kamar su suka yi kansu ga kudi,tace kartan banza kartan wofi
kunyi kunyi kyawun banza banza,sojanku bai da amfani tunda baku da CCTV, baku iya
kama me laifi a family dinku kunyi asara,Kuma wallahi idan na fito a kanku zan dira
duk sai na fanshe wahalata ta gidan yari,haka kawai ko uwata bana yiwa aiki zaku
sani bautar iska a gidan yari,ta Nuna Mummy tace kanki kika cuta,naji ana ta zancen
wani Dan iskan danki a nan wai Ashraf ku fada Masa sakona kafin na fito ya saurari
zuwana gare shi har ta kansa zan bi,gwara da naji kinfi sonsa zaku ga tsiya,Naila
bata San Spark ake cewa Ashraf ba,bata ji sunce Spark ba gashi baya kasar ma amma
ta dauki Karan tsana ta dora Masa tace a kansa zata huce.

Mutane suna ta kunshe dariyarsu,Alkali kuwa sai da ya Dara a wajen,Sabo da ba


wata hujja Naila bata da hujja yaso ya kubutar da Jamilu amma rashin hujja shine
sannan yaji kudi ta wajen Mummy ta antaya Masa kudade, Kuma ba kotu ce ta musulunci
ba bare yace suyi rantsuwa.
Lauyan Mummy daga ya tambayi Naila Abu sai tace ae hakane nayi, in ta gaji da
tambayoyi tace na gaji ni ku yanke min hukunci na tafi na huta anbi an isheni, Duk
da haka ba a yanke hukunci ba sai da Alkali ya dake sharia yace sai an sai an sake
zurfafa bincike,Nan ma Mummy ta saki kudi ta karkashin kasa.

A zama na uku binciken gawar tun kafin a binne


Gawar da aka auna an tabbatar guba Alhaji yaci ya mutu,sannan an dakko jakar Naila
an kawo kotu an tattara maganin gargajiyarta an Kai an auna suma suna dauke da
sinadarin guba Kuma irin wacce Alhaji yaci ya mutu,Mummy sai murna take tasan kulla
kullar da tayi,babu yanda za ayi da Naila dole hukunci ya hau kanta,ita ta matsu ma
a yanke mata hukunci ta huta da tsareta da akeyi cikin Wanda ake zargi sannan tsoro
take ji kar a gano ita din macece, dole Alkali ya yanke mata daurinta na rai da rai
a gidan yari yace kamar yanda ka furta in kana da gaskiya Allah zai fitar Da kai
kayi lafazi me kyau kana da tauhidi Jamilu.

Naila tace oho Kuma dai nidai bazan ga mutuncinka ba tunda ka kare sharia da
wuri ba wani bincike,a wannan na karshen Mohsin ne yazo kotu kawai shi kadai,baiyi
kuka ba,Naila ta kalle shi tace karka yi min Kuka ni ai zaka dinga zuwa ziyara, ni
Namiji ne me dauriya, Ma'aikatan ne suka tasa keyar Naila wato Jamilu gaba,Zasu
wuce ta gefen Mohsin ta dafa shi tace sai kazo ziyara ranar akwai shoki wlh, Yaya
ba komai karka damu....karka damu Yaya.....zan rike kaina, a haka aka wuce da ita
Jikin kowa a sanyaye,babu Wanda baiji Tausayin Jamilu ba,Shariar Sam da ganin
yanda aka yita kasan alkalai da lauyoyi sun Sha kudi,kowa Yana da kokonton ba
Jamilu ne ya aikata ba da alamar tambaya kawai babu mafita ne,ga Mummy ta iya kulla
kullar tsiya.

Mohsin ya fito zai hau lifan dinsa Yana goge kwallarsa da handkerchief Misam
ya dafa shi ya tsaya,hannu ya mika Masa suka gaisa,yace karku damu ku bari danta ya
dawo ya iya kwatowa mutane hakkinsu Yana da tausayi na tabbatar da Yana kasar
wannan abin bazai faru ba baza a kulle Jamilu ba, Mohsin yace kaddara ce ba
damuwa,bani number Dinka sabo da duk halin da ake ciki gaba zaka ji,Mohsin ya bashi
number suka yi Exchange sannan kowa ya tafi,su suka bi jirgi suka koma Abuja,Mohsin
yayi gida.

Yana shiga gida ya iske Umma tana ta kuka a Palo tana cewa duk rashin Jin
Naila ne ya jawo gashi Nan nasan ma an yanke mata hukunci,Mohsin yace ai kuwa sai
dai ayi mata addua,wlh ba Wanda zaije mata ziyara da wuri tunda taurin Kaine da ita
taurin kanta ya ja mata,Abba Yana zaune ya zuba tagumi Yan gida sunyi jugum jugum
ana ta zuwa musu jaje,Matar Mohsin tana zaune a gidan da yarta ko a jikinta ita a
ranta ma Allah ya Kara takeyi ta tsani Naila,Hajiya Tagwadas itama tana gidan wajen
Umma harda zazzabi tace jarabar kwadayi na ne ya kaini, gashi ta hannuna abin ya
biyo wayyo ni Tagwadas Ina zan sa kaina,Mohsin ficewa yayi kawai ya tafi gida.

Spark bai San komai ba sai da yau Allah yasa ya kira Kamal,Kamal ya haushi da
bala'i yace wallahi abinda kake yi ba tsari bai dace ba,sai ka bar me kake yi ka
dawo Nigeria Mijin Mummy Dinka ya rasu,kamar saukar tsawa haka Spark yaji maganar,
yace me ya same shi? sai da cuta ake mutuwa magana baza ta yuwu a waya ba malam
kawai ka dawo kasar sai kaji komai.

Spark kashe wayarsa yayi ya kira Mummy tana kallo taki dagawa tayi fushi da
shi,kiran duniya taki dagawa,Mima ya kira duk suka ki dagawa,kowa ya kira a family
bazai daga ba,sabo da ya batawa mutane rai,a ranar da yamma ya tattara ya sauka a
Nigeria, Kamal yaje ya dakko shi a Airport suna tafiya Yana bashi labarin komai
tiryan tiryan har ya gama Jin komai da ya faru,yace wannan yaron karya mummy ta
masa,ai shi yasa aka so kana gari time din cewar Kamal.

Spark ya furta yanzu Yaron life in prison? Wlh baka ganshi ba son kowa kin
Wanda ya rasa kyau dai a wajensa har da na siyarwa wlh kamar mace mace,tsaki Spark
yaja yace ana zancen hankali sai ka kawo shirme, bari zanbi a hankali Inshaallah
wannan yaron bazai yi life in prison ba,idan Mummy ce ta aikata gwara ita tayi
zaman gidan yarin.
Naji mutuwar nan sabo da mijin Mummy shi yace na daina Masa magana,na biye Masa
sai watarana kawai nake Masa sannu amma baya amsa min ban so Hakan ba bro gashi ya
wuce,ban kyauta ba,Kamal yace shi yasa aka ce a dinga hakuri da rayuwar duniya
yanzu gashi nan ai ya mutu,idan ance ka canja hali Kai a'a.

Ya isheka Kamal a cikin zafin mutuwa nake karka dameni cewar Spark,mutumin nan
sai na bi Masa hakkinsa,Allah sarki rayuwa,Kamal yace watarana mutuwar kanmu zata
zo,a fusace Spark yace kanka dai Banda ni,yaushe nazo duniyar ni yaro Dani,Kamal ya
dinga dariya yace ake dauke jariri ma karewar rashin dadewa a duniya,Ashraf yace to
na ebo shekaru da yawa inshaallah
A haka suka karasa gidan Mummy.

Labarin abinda ya faru kenan Naila ta tsinci kanta a gidan Yari bangaren Maza.

Ci gaban labari.

Free page

Masu bukatar siya 300

0175487861
Asmau Garba Muhammad Gtbank

Katin MTN
08061929616

Yan Niger ga number ku nemi wannan


+227 90 79 59 39

Sharhi please

AsmaBaffa
[12/5/2023, 2:05 PM] AsmaBaffa: 🏫 TANTIRIYA🏫
A GIDAN YARI

16-20

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA
GARE KI
AIDA MAMAN TASNIM

Page naku ne
Najida Aliyu Bicca
Mhiz Awwal

*👭GARKUWAR MATA👭*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya
mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce,
kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan
kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da
surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿
🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da
matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai
dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki
yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane
irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba
su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta
humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza
da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in
abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu
shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano
amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna
bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai
kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi
kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN
K'ARIN BAYANI
08089965176
07084653262
Yau ma akwai kidan koroso da rawa kusan kullum sai an musu kidan koroso
da rawa a gidan yari amma iya bangaren masu daurin rai da rai watarana harda Yan
solo ana kawo musu domin nishadinsu,wani lokacin Kuma akwai ranar Yan drama suma
suna zuwa ciki bangaren Yan life in prison a musu sabo da nishadi,yau ranar koroso
ce za ayi da yamma har zuwa magriba.

Ko wanne yazo Inda Tantiriya Naila yau tazo tayi kallo itace bakuwa, Naila
tace ba kidane a gabana ba in fita daga gidan nan shine target dina,duk kansu Jin
Jamilu suke a shashasha,Dan Indo Yana Shan sigari yace idan ka fita kayi magana na
baka babban aiki wlh,kaje a baka bindiga banza ka zauna ana maka sharri a banza
kayi na gaske akwai binda Dan kutmar...kai Allah, Naila dariya tayi tace Allah ya
tsare ni da kisan Kai tana maganar Yan Daudu harda shanye hannu, tace ni Jamilu duk
wani iya shege Dani ake farashi,ai mune wakilan shedan ehehehayye...Dan Indo
zuciyarsa ta buga wani birge shi Jamilu Dandaudu yayi,haka kawai yaji Yana masifar
kaunar Jamilu,a ransa yace Ina ma mace ne Jamilu,ko ace ni Dan neman Maza ne da na
kwashi harka a wajen Jamilu.

A hankali ya faki idon Naila Tantiriya ya rike damtsenta tare da jawowa,yaji


wani laushin masifa ya wani jawo shi talau,ashar ya dura tare da ja da baya ya dafe
kirji Yana kallon Jamilu yace amma Kai tun a cikin uwarka dama Dandaudu ne?, Naila
ta tsuke baki tare da furta tunda na fado duniya ni dama babarmu tace kukana da
nake yi maimakon aji Inya Inya sai aji Ina cewa Zaniiiiii....Zaniii....idan na
shide sai aji kukan ya canja sauti Dan.....Dankwaaaaaa......liiiii....DanIndo ya
kwashe da dariya, Muler Dake gefensu Yana Jin hirarsu Yana ta dariya yace Kai
Jamilu amma uwarka ta haifo Dan iska,Naila tayi fari da Ido tare da shanye hannu
tana tsuke baki ta wani lashi labbanta sannan tace ya ranka ka daina gatsa sunana
kamar kana gatsar rake ka kirani da Jamilu Tantiriya haka nake,sai ta dauki mintuna
kafin tayi magana sai ta tsaya ta gama karairaya da wani lankwashewa sannan take
magana.

Wani me suna Farau Farau shine ya Kalli T.k ya Masa rada yace nifa tunda aka
kawo yaron can Jamilu wlh na fada matsananciyar kaunarsa ni ba me neman Maza ba
abin nan Yana damuna,Tk yace abinda zan fada Maka ka rigani kenan wlh abin Yana
damuna,kusan duk mutanen gidan Nan kaunar Jamilu suke anya ba asirin farin jini ne
da shi ba kuwa,Cikin rada Farau Farau yace kaga kaga kalli Yana murmushi Kalli...
Dan Allah baiyi kama da mace ba? Tk yace a macen ma full option,ance jikinsa laushi
kamar me,muje mu taba Muji,Muler da Tk suka taso da niyyar taba hannun Jamilu su
ji,sai kuwa Dan Indo yaji wani uban kishi ya make hannun Muler yace wlh kana taba
Jamilu sai na rushe Maka hakora,sun san DanIndo sai suka koma Inda suka taso,Naila
a ranta taji dadi Sam DanIndo ya tsaya mata ba Wanda ke kawo mata wasan shirme sabo
da suna ganin abokin Dan Indo ne.

Naila ta juya ta Kalli Dan Indo tace Ina baka labari abokina,yace Ina jinka,ai
Ina fada Maka ni idan nazo waje shedan ya kan bace yace oga tazo har gisuwa yake
kawo min ida na shirga wata tsiyar,badan gidan yari ba da yanzu na kashe auren Yaya
na, amma kisan Kai bada ni ba,Dan Indo ya furta mene a cikin kisa ai kawai Wanda
yayi akuya kawai ka caccaka Masa wuka,ai ni billahillazi da me zarto nake amfani
cewar wani me suna Baballe da ya tsomo musu baki, shi da yake babban Dattijo ne
ma,ya kunna sigari yace maganin shege sai Dan Banza Tantiriya Jamilu,ai karka sake
a kawo ma raini ko a gidanku ne,Naila tana Jin halin kowa iri iri.

Tunda tazo gidan yari Dan ragowar tsoronta ya gudu, Uban Dawa yana wajen yace
ni ka san daga Ina tsiyata ta fara? Maza nakewa fyade,in ketawa Namiji haddinsa ba
komai bane duk girman gardi nayi niyyar lashe Masa Timber karya yake ko ubansa
waye,Baki suka hada suka yi wata shaharriyar shewa da ihu harda,suna da masifar
yawa a wajen sun hada uwar daba,wani da ake kira da Goje yace ke Tantiriya wanne
tsiya kika yi a kasar Nan ta alfahari? Wacce kai da kanka Jamilu idan ka tuna kake
jinjinawa kanka? Naila tace Ni Jamilu nine wanda na saka Budurcina a caca tun
farkon fara Daudu nawohoho suka furta kamar Wanda suke shuka abin arziki haka suke
hirarsu,

Fitsara da rashin mutunci a cikinsu ba a magana,akwai Yan iskan da su tsirara


ma sukeyi watarana a ciki uban kowa ya gansu,duk wani sabon me laifi da aka kawo
shi gidan yari Wala mace ko namiji tofa kowa sai yaji labarin an kawo sabo, sai
Kuma an San waye,duk iskancin mutum akwai Wanda ya ninka shi sau dari a ciki,suna
zaune Naila taja DanIndo da Goje wanda suka fi mutunci tace kwana nan zan bace a
gidan nan,Goje yace ta wacce hanya Tantiriya? Naila tace ta bangaren Mata zan koma
nayi shigar mata,dariya suka saki,tace wlh da gaske nake,ta bangaren Mata Anfi
samun damar guduwa idan ta kama,daga part din Mata sai bayan Daji Kunga kuwa sai
fecewa,Goje yace ai kuwa kana haurawa zaki karairaye, ka Kalli uban katangar
gidan,tunaninka katangar banza ce,a banza zaka ga kartai sun kasa tserewa, gashi
yanzu an Kara kwalabe da wayoyin shocking kana tabawa sai mutuwa,Naila tace bazan
yarda daku ba,to munji yanzu ta ya zaka shiga bangaren matan har ka zauna ba a
ganeka ba,Bari zaku gani bari yayana yazo zai kawo min kayan Mata ku gani.

Bikin Spark an saka rana an saka bikin a kurkusa, babu bata lokaci Mummy ta
matsa Masa ba yanda ya iya,sai masifa yake yi,yau gidan su Asmau yaje har gaban
iyayenta ya musu warning yace idan kuka aura min yarku ba ruwana da Yar uwa ce zan
iya kashe ta nine ajalinta gwara ma ku janye ato ba abinda zai hadani da ita ya
fada ne Dan ya tsorata su a fasa auren,yaci gaba da furta me zanci da yarku bana
sonta ko dole ne ana so dole ne Dan kawai Kuna Yan uwana sai ku takura min.

Baban Asmau kuwa masifar son 'ya'ya ne da shi,sai abinda yaransa suka ga dama
shi suke yi ba a yiwa yaransa fada bare ace ba a sonsu,shi indai kana son yaronsa
to ka gama da shi,tunda ya fuskanci Spark baya kaunar yarsa shike nan ya tsani
Spark yake mugun Jin haushinsa,sabo da yaga iyakarsa shi yasa ya dage ayi aurensa
da yarsa ko tsawa idan yayi yarsa ya sa a ransa sai ya daure shi,sai yayi amfani da
mukaminsa da hanya da kudinsa yaga karshen Spark a duniya, Suna jin Spark ya gama
masifarsa ya fice ya bar gidan tare da shiga motocinsa suka bar gidan,Baban Asmau
yace ni Kuma bari naga karyarsa bari a dawo da bikin nan da sati daya idan ya isa
ya mata ko tsawa ya gani ni Kuma ba rangwame wallahi sai ya kare rayuwarsa a gidan
yari Kuma bazan ma barshi a gidan yarin Abuja ba kar ma suje suyi cin hanci,l,Lagos
zansa a batar da shi,ni dama bana son yaron nan tunda ya taba kwace min wata
Kwangila da gomnati ta bani.

Kawai Baban Asmau sabo da shima babban Soja ne sai yace a dawo da bikin sati
daya,Spark sai labari yaji wai an dawo da bikinsa sati daya,a fusace ya tafi gidan
Mummy, shi yayi driving shi daya yana shiga ya samu Mummy a palonta tana takaba
amma Dan masifa sai tayi bikin kamar ba me takaba ba har lallenta take yi, ya
durkusa a kasa a gabanta,haka kawai ya fashe da kukan karya,yana hawaye yace wlh
bana sonta Dan Allah karku aura min ita,bazan iya rayuwa da ita ba,ni bata min
ba,Mummy ko kissing nata bazan iya ba bakinta ya min girma sai ta hadiye min bakina
Kinga nawa Mummy ya turowa Mummy karamin bakinsa,yace ki tuna na Asmau kamar kofar
ShopRite ya sake fashewa da kukan karya tare da Dora kansa a cinyar Mummy,a boye
Kuma Dariya yake, Dariya Mummy tayi ta rike hannayen Spark tace yau Spark da
hawaye akan mace,yace wlh bana son ganinta ko a hanya bare ace zan aureta,ni Spark
ace za a min auren dole wlh bazan shiga gidan ba ko an kaita gidana.

Mummy tace ka makara ka koyi sonta wlh yau saura kwana shida zaka ganta a
gidanka,mikewa yayi Yana cika Yana batsewa hakarsa bata cimma ruwa ba,sai ya koma
spark dinsa ya daure fuska Yana kunkuni ya fice cikin fushi dama kukan karya yayi
ko za a tausaya Masa sai gashi ba nasara.

Spark Yana ta bincikensa akan Case din Naila ya zaiyi ya fitar da Jamilu a
gidan yari ga matsalar aurensa,kamar wasa biki yazo ranar Friday za a daura Kuma a
ranar za a Kai amarya ba wani biki za ayi ba sabo da Mummy tana takaba,Spark har ya
hakura ma yace Allah yasa haka shine Mafi alkhairi ya zaiyi.
Ana gobe daurin aure tare suke da Kamal suna Hira, Spark yace na kyale yarinyar
Nan sabo da son da take min,taci darajar Sona da take yi amma fa bazan ko hada room
da ita ba wlh har ta gaji tace na sake ta shine kawai adalcin da zan iya,ni zan
hada jiki ne da wacce zuciyata ke so wacce ta kwanta min a rai wacce bana
kyankyami, Kamal zamuga wace Yar sa'ar Nan Yar gidan waye idan Kuma Asmau ce zata
sace zuciyar to,Spark yace hmmm ya Kalli Kamal yace zaka Gani inshaallah,ai Asmau
bazan taba sonta ba,ni ba abinda ta min kawai Allah bai sa min ko digon sonta
ba,hasali ma a duniya ba wacce na tsana irinta.

Asmau kuwa Banda murna ba abinda takeyi,itakam shagali take matukar zata zauna
gida daya da spark to rayuwa ta mata dadi ko da bazai kulata.
Washe gari Friday daurin auren Spark dukkan Yan uwa da abokan arziki sun hallara
har abokinsa Kamal duk sun dauki wanka amma ba ango yace bazai je ba wlh,mahaifinsa
da Mima mahaifiyarsu sunyi iya yinsu yaki zuwa,haka aka daura aure ba ango,shi Yana
Office ma aikinsa yake ya kashe waya kar ma ayi Masa Allah sanya Alkhairi,haushi
yake ji in akace Allah sanya Alkhairi, zuwa Yamma aka Kai Masa Amarya sai kace
dole,amarya anci gayu an hade,har aka watse ango bai zo ba,shuru shuru haka Amarya
ta mike tayi alwala tare da gabatar da sallah sannan tayi Shirin bacci ta kwanta
abinta,Nawwar a ranar a Office dinsa ya kwana ma bai je gidan ba.

Asmau kuwa bayan ta kwanta bacci, sai da safe dangin Amarya suka zo zasu mata
sallama zasu tafi garinsu amma sallamar duniya a palon ba a bude ba,har suka gaji
tare da shiga ciki suka zauna a Palo nan ma shuru shuru,suka fara duba bedroom
dinta sai kuwa suka hangota a kwance ta Kalli sama idonta a kafe,da sauri suka isa
kanta suna tabata shuru har ta sandare ta kame, Dake akwai dattijai a ciki suka
tabbatar ta rasu,wuyanta ga shatin igiya Nan da alama igiya aka sa tare da shake
mata wuya har ta mutu,sai kuka da kuka suna cewa dama angon yace sai ya kasheta to
kuwa da gaske ya kasheta shike nan sai bige bigen waya azo ango ya kashe Amarya ya
gudu baya gidan ma.

Hankalin kowa ya sake tashi a family gaba daya,iyayen Spark kowa suka tattaro
sai katafaren gidan Spark, Kamal ma da gudu yazo gidan,iyayen Asmau kuka suke suna
cewa wallahi baza mu yarda ba,mahaifiyar Asmau ta fada kan gawa tana kuka tace
Asmau...Asmau na....wayyo ya kashe min Yata bai San zafin haihuwa ba, Mummy da gudu
ta shugo gidan tana wallahi Dana bazai yi kisa ba ban yarda ba karya ne sharri ne
ta Fadi a kasa tana kururuwa,Mummy a duniya tana son spark ko uwar data haife shi
baza ta fada mata son Spark ba,kamar ranta haka yake,tace wallahi da nasan haka
zaku ce bazan daure gindin Spark ya auri Asmau ba.

Mutane ba Wanda ya yarda da Mummy duba da halin Spark da Kuma furucinsa Kuma an
San baya karya shi yasa har iyayensa na gaskiya suka yarda, Baban spark shima Soja
ne ya Kalli Baban Asmau yace kuyi bincike ku dauki mataki akan Ashraf ya girbi
abinda ya shuka,Mima uwa to fa uwa ce amma Mummy ta fita son Spark itama tace idan
an tabbatar shine a hukunta shi, sai kuka take tana cewa tabbas yara haihuwarsu
jarabawa ce,mu iyaye muna ganin jarabawa akan yaran da muka haifa, Rafeeq zuwa yayi
shima Yana ta al'ajabi amma bai yarda Spark zaiyi haka ba sabo da yasan halin
Spark.

Baban Asmau dama kadan yake jira yasa aka Kai gawa asibiti duk wani gwaje gwaje
anyiwa gawa amma komai normal bata ci wata guba ba da wire ko igiya aka shaketa har
ta mutu,Spark aka shiga nema lungu da sako babu Wanda yayi zaton Yana Office,sai da
Yan sanda suka dangana da Building dinsa,gashi Baban Asmau ya musu alkawarin
mahaukatan kudade na mamaki shi yasa suka dage.

Suna shiga ciki ko Ina a bude yake sabo da ma'aikatansa duk sun zo aiki,har Office
dinsa suka shiga sai kallon tsaruwar office din suke,akwai Palo a ciki suka karasa
a Nan suka same shi Yana ta bacci hankalinsa kwance kasancewar jiya baiyi bacci da
wuri ba Yana ta aiki.
Tashinsa suka yi sun san da kudi shi yasa ba raini suka tashe shi,a hankali ya
bude idonsa ya kallesu da uban yawa a kansa sun zagaye shi,kallonsu ya sake yi yace
lafiya? daya daga ciki yace matarka Asmau....kafin ya rufe Baki Spark yace Allah
yasa ta mutu na huta da mayya,me ya faru? Sheda ta Kuma tabbata sai suka fito da
sarka tare da furta You are under arrest, ana tuhumarka da kashe matarka,Idanuwa
Spark ya zaro yace kisa Kuma ni? Yaushe ma na kwana a gidan? Mamaki ya
kamashi,Asmau ce ta mutu? Su dai yanda suka ce zai raina musu hankali ne kawai suka
sakala Masa sarka a hannaye yace ba sai Kun sa min sarka ba zan iya binku normal
cire min chain,ba musu suka cire Masa.

Spark yana furta innalillahi wa innailayhirrajun yaci gaba da cewa ko a lahira


Allah karka hadani da Asmau, ya Allah ka gafartawa Asmau ka yafe mata,Allah ka
gafarta mata irin shiga hakkina da tayi ta aure ni bada izinina ba l,Allah na yafe
mata ka yafe mata,kansa ya jinjina yace uhhmmmm su Asmau an matsa min lamba Allah
ya yafe miki,Sadakin ma sai da Papa ya biya min,Allah ya miki Rahma uhmm rabo
to..dama ance rabo Yana kisa,sai da nace a hakura rabon wata ne aka ki ji, Yana
magana ya tattara documents dinsa da kudadensa da duk wani Abu nasa me amfani ya
fito dasu tare da Yan sandan motocinsu sunfi biyar suna ta jiniya.
Manager dinsa ya mikawa yace ka kaiwa Mummy kace ta ajiye min ba Mima ba Mummy
nace,yace angama sir,ya shiga mota yaransa masu aiki a karkashinsa suna kallo Yan
sanda suka tafi dashi.

Yana can aka sallaci Asmau tare da kaita makwanci,Yana motar Yan sanda ya Kalli
Inspector guda yace iceko takaba bata hau kaina ba? sabo da tsabar ya raina musu
hankali,Kuma wulakanci Spark ne,Yana da kudi to ba uwar da suka iya Masa,dama duk
jaraba akan talaka take karewa, Spark sai kallon raini yake musu,suna ta Shan
wulakanci iri iri.

Inspector yace Kai nifa Inspector ne,Spark yace no Inspectataatatatataaaa,yaja


wani tsaki Kuma ba uwar da suka iya yi,shuru ya musu fuskar nana hade, har suka
kaishi tare da tsare shi,ko tambaya suka Masa baya basu amsa a mutunce,shine ya
Kara basu haushi sosai.
Duk wasu bincike an fara yinsu akan Spark amma ba hujja shi ya kashe Asmau,Baban
Asmau kudi yake dannawa Yan sanda akan a Masa duka to shima Spark Yana da kudi
Kamal Yana kawo kudi dole basa iya dukansa ko farcensa basa iya tabawa gashi
tsagera Yana da kwarjini,Inda Allah ya saukaka ma da wuri Baban Asmau ya Kai Kara
kotu ta can Lagos,ana ta faman bincike yaga zasu bata Masa lokaci ya Maida karar
Kaduna,Nan ma yaga Spark ya fishi hanya ana ta daga sharia gashi ma za a bada
bailing Spark,tsoro yaji kar ya cale kasar waje,yasa aka sake tsare shi sosai aka
Maida case kotun dake Kano state.

Yayi hakane Dan ma kar Ashraf ya bada cin hanci a sake shi,duka dangi ma sai
labari suka ji ai an Maida shi kano.
Wani mugun azzalumin Alkali ya samu sannan da lauyoyi azzalumai, Spark Yana
tsare ba dama yayi katabus,Mummy duk kulla kullarta Baban Asmau ya fita gashi
babban Soja ga kudi kamar yayi, gashi namiji ya fita basira,iyayen Spark da
danginsa sunki shiga cikin case din sabo da spark ba Wanda ya kyale shi yasa suka
kyale shi.

Suna ji suna gani aka Masa sharrin kisa ta karfi tare da yanke Masa daurin rai
da rai shima a gidan yari.
Spark yaga masifa ana kawo shi ciki gidan yari Naila ce ta fara ganinshi tace
wow, sai data tsaya ta kare Masa kallo Yana wani gadara da kyar yake tafiya fuskar
nan a hade ba mutunci dama ya lafiyar Kura bare tayi zawo, sai kallonsa akeyi sabo
da kyansa da gadararsa ana ganinsa an San Dan gidan wani kusa ne a kasar, Naila ce
ta fito tana tafiyar Yan daudunta tabi bayansa tana kiransa tace wannan zaka dace
da Daudu,ni Kam nayi budurwa,ta fara kiransa da Asabe....Asabe....ko Tabawa ce ne?
Tabawa...ahhh Ashe ba tsohuwa bace sannu ko sunanki Kamariyya? Jin Muryar mace
sosai yayi mamaki ya juyo ba shiri,gashin kawai ya kalla yace a ransa Ashe Dan
daudu ne,Naila ce ta katse Masa tunaninsa da cewa Kaiiii gaskiya kina kama da Lady
Gaga, jar Uba I love you, shike nan ga suna na Yan gayu Iklima ai yafi?,ni sunana
Dahara,wani takaici ya kama Spark,Sam shi ya tsani mutum dandaudu wani tsanar mutum
yake yi,ga wannan gaba daya suffar mata gare shi, Naila kuwa ta jera dashi taci
gaba da cewa,Sunana Dahara sunan ya samo asali ne tun Ina karama Allah ya sa min
yin tsarki,kullum ni dai na dauki buta nayi in tsarki shine aka canja min Suna
Dahara, Kuma fa Ummata sanda tana da cikina ance Bata iya rike fitsarinta shine
kullum ta dauki buta shine ana haifo ni nima kullum da buta a hannuna dole aka gaji
Dani aka sa min Dahara.

Look ni ba wani abu nake so ba,kawai abokina zaka zama sabo da ba karamin girma
bane a ganni tare da Kai,kawai ma ace Ina Dating naka ai ni na zama kadara, duk
Inda ya sa kafa Naila tana biye da shi,mutanen gidan sai daga mata hannu akeyi a
matsayin Dandaudu ne kowa sai yace su Jamilu Terror anyi sabon kamu, Naila tace
harka ce ta Uhmm humhum,hankalinta ta Maida wajen Spark tace to shike nan da
sunanka zan na kiranka, ya sunan naka? Ko kulata baiyi ba, ganin Dandaudu y matso
kusa da shi hannu yasa ya ture Jamilu,ai Naila rikicif sai gata wanwar a kasa,
lebenta na kasa ya fashe kadan,Mamaki ya kama Spark namiji guda daga Dan ture shi
yayi wannan uban faduwar haka,Bai San macece ba,a ransa yace wannan ya gama kashe
kansa ya zama macen gaske,wait tsayawa yayi Yana tunani da yasa hannu a jikinsa
yaji Laushi haka,wani sabon mamakin ya dira a zuciyarsa,kallon jamilu a kasa Yana
goge bakinsa, haka ya wuce bangarensa na masu kudi wajensu daban dakinsa shi kadai
harda tv da fridge harda kujeru sai dai rayuwa kawai a waje daya musamman ga namiji
akwai wahala.

Naila tashi tayi da kyar ta goge jikinta tana dingishi ta koma dakin su
Alaramma Jilani,samunsu tayi suna Hira ai suna Ganinta ta shiga gaba daya suka jawo
Qur'anansu kowa ya bude ba shiri,dariya suke Bata.

Gefen bed ta zauna Malam Garzali ya dago Kai ya saci kallonta ai kuwa karaf suka
hada Ido Naila ta kashe Masa ido daya,da sauri ya duka karatunta Yana yiwa sauran
magana kasa kasa yace kaiiiiiii wallahi Ido yake kashe min Kuma ya birge ni,Malam
Garzali shima yace nima haka zuciyata

Naila Hanata akayi shiga indai ba da izinin me kudin ba to ba Wanda zai shigar
musu sai da izini,shima ba kwana ba idan da kwana to Wanda ya shiga shima sai an
biya Masa kudinsa daban,yini ma sai an biyawa mutum zai yini a wajen,bangaren masu
kudin ma shi ba wani me kyau can ba kawai Dan akwai kujeru da fridge ga toilet ko
Ina tiles sannan har wanki ma da guga yi musu akeyi zasu iya dauka a cikin Yan
gidan yarin suna biyan mutum hakkinsa Yana musu.
Spark da wayarsa da komai amma ya canja layika gaba daya sai in shi ya Maka
magana sannan kasan shine,in banda Kamal da Rafeeq da ya nema ba Wanda ya nema sai
Mummy dinsa me kaunarsa itama ya kirata amma sauran ba Wanda ya kira sabo da duk
sun yarda zai iya kisan Kai.

Spark bakin ciki ya taru ya Masa yawa ya rasa Inda zai sa kansa,Naila kuwa
tsabar bala'i sai da ta bada cin hanci aka barta ta shiga dakin Spark,tace wato ita
duniya dai ko Ina me kudi yake akwai banbanci a lahira ne kawai kowa zaici kwal
ubansa Kai daya muke, ranar ba wani me kudi,palon ba kowa bedroom ta shiga a zaune
ta hango shi ya hada Kai da gwiwa Yana hawaye shi daya.

Naila tana shiga a hankali take sanda,ya ganta tun shigowarta,a ransa yace
wannan Dandaudun ko maye shege tsinanne,Naila da karfin hali zama tayi a gefen
gadon nasa, cikin Muryar Maza mazanta da take amfani da ita tace Allah sarki hakuri
zakayi kaddara ce,wallahi ka saki ranka idan sharri aka Maka zaka fita
watarana,Allah zaka fadawa kawai,gidan yari idan ka saki ranka akwai dadi ma itama
wata rayuwa ce ta musamman Kuma zaka yi nishadi,ka kwantar da hankalinka ka saki
ransa idan sharri aka Maka uban Wanda ya Maka sharri yaci... dan me..Kai Dan
kut...nace durun....kai...duk bata karasa zaginba idan ta dakko sai ta saki ta kama
wani.

Ka tsaya kana kuntatawa kanka kana namiji aradu ka fito a dama da Kai,karka bari
kanka ya kulle,gidan yarin bata rago bace aradun Allah,gidan Maza malam anan zaka
tabbatar da namiji ne kai, anjima kadan yau za ayi gala rawar solo ka fito kayi
nishadi karfe biyar za a fara har dare, Spark a ransa yace iyyeee a gidan yarin?
Bai San a fili ya furta ba,Naila tayi dariya tace ai har koroso kullum sai anyi da
wasanni kala kala kazo muje na nuna Maka komai ka huta da bacin rai, tunawa yayi da
Dandaudu yake magana sai ya bata ransa ya daure fuska,Naila tace wasa nake Maka ni
ba Dan daudu bane kawai Ina kama da mata ne shine Yan gidan yarin Nan suke fada min
haka,amma wlh ni ba Dan Daudu bane sunana na gaskiya Jamilu,Spark ya Kalli Jamilu
wato Naila sosai,murmushi ta saki a ransa salati ya saki kawai yayi shuru shi Kam
wannan mata Maza ne gaskiya bai yarda ba sai dai Matamaza.

Tashi tayi ta fice,tana fita ta koma wajen su Goje har hudu tayi taje tayi
sallah a boye malaman dakinsu jam'i baya wuce su,suna fita take yin tata kafin su
dawo, suna mamaki Bata zuwa jam'i iya wuya a daki take sallarta,wanka tayi a toilet
din ta shirya tsaf ba Wanda ya taba ganin jikinta,kaya ta canja suma sai masu kauri
burma burma na Maza,harda shafa turaren da Scoler ya bata sai wajen da ake musu
wasan Solo lokaci zuwa lokaci,Yan solo sunzo harda Yan film an kafa kida an fara
cashewa kowa ya zauna ana kallo wasu suna ihu suna liki,sai ga Spark kamar ba a
gidan yari ba ya Sha kana Nan kaya sai shining yake dake sabon zuwa ne gashi
kyakyawan gaske fari,ga kyan sura da diri,ga kwarjini da cikar haiba,Jamilu
abokinsa ya fara dubawa a wajen can ya hango Naila zaune a gefe daya bata shiga
gwamitsin kartai,kujera ta nuna Masa a gefenta,wasu munafukai harda gulma dama
tunda naga kalar guy Nan nasan shima Yana harkar Daudu,Terror an samu Dan uwa,Spark
hannu ya mikawa Naila yayi sallama,Naila ta kalle shi kawai ta basar ta share,Yan
Solo suna cashewa wata Yar bariki har da zuwa zata rungume Spark Naila tace ke
dalla matsa na saka miki guba ki shaka ki mutu bar Nan Dan uwarki tana zaro ido ta
koma Yar Zara,tana zare Ido tana magana ta Maza ta Yan Zara,amma duk da haka mace
sak.

A hankali Spark ya dago Kai ya Kalli Naila,dariya ta kusa kama shi,a ransa yace
ikon Allah namiji ta karfi sai ya koma mace to naga Dan ubansa ta ya zai canja
Banana dinsa,ai sai ya yanketa kawai idan ya isa,shi kadai Yana tunani sai ga
scoler yazo Yana rangwada yace da Naila Tantiriya ta? Jamilu Naila ya kalle shi
yace Na'am my love Ina ka shige ne Ina ta missing naka.

Dandaudu Scoler yace ahayyeeeee Yana tafi yace Dan ma har yanzu kinki yarda kiji
dumin jikina,Naila tana shagwaba tace ai karka damu Darling tana so tayi
kuka,Scoler ya dafe kirji yace na shige su ni Yar Nan karka bari hawayenki ya zubo
tawan mene ne? Jamilu Yana rangwada yayi fari sannan yace ba Kaine ba sabo da Allah
haka ake saurayin kaki zuwa zance bare ko kudin zance ka bayar gashi Dan liki ma
bani da kudin yi,Scoler yace Dan Allah daina fada jiya aka turo min kudi ungo yasa
hannu a aljihu ya zaro Yan Dari bibiyu na dubu biyu ya mikawa Naila,badan yau
Saturday ba Alqur'an sai na rungume ka cewar Naila,amma anyi rashin sa'a yau cikar
shekarar kakata ta wajen uwa goma Sha biyar da mutuwa,ranar bakin ciki ce sai nan
gaba.

Scoler yace kiyi hakuri amma gaskiya kakarki ta cuceni data mutu ranar asabar ai
sai ta bari zuwa lahadi Sunday yanzu je kiyi liki,Yan wasan kwaikwayo suna ta uwar
rawa a fili, Naila ta mike tace zaku ci ubanku sisi bazan lika muku ba,caca zanyi
muku,ta wuce ciki filin rawar,Dj harda fadar sunanta ana ta cewa Jamilu Tantiriya
Allah ya tsare mana Kai,Naila ita da kanta dariya ta kamata ta dinga dariya,mazan
Nan sai kallonta suke ana ta son Jamilu sai kuskus ake yi.

Naila ta zaro Dari biyu tayi mata rikon tsauri ta tsaya kusa da budurwar me
tikar rawar tace a duwawu zan lika miki taje ta manna Dari biyu a duwawun budurwar
Nan,da karfi tace aradu ciko ne ciko jama'a,Kuma ta rike kudinta Kam sai ta manna
sai ta zare kudinta Yana makale a hannunta, mc Yana ta zugata Dan ta lika tace na
ki wayon wlh ficikata baza tayi ciwon Kai ba akan me duwawun ciko ba, ana kallo ta
fice tana cewa ciko ne wlh kar Wanda ya lika sisi gwara muci tsire ciko take
mirgudawa,na taba maimakon naji wajen Yana karkarwa sai naji yayi dubush baya motsi
kar kuyi asarar kudinku,suna ta dariya Yan gidan yari,amma sai da wasu suka lika
kudin sosai,Scoler ya Maida kudinsa aljihu ya fasa likin yace asararru

Ba'a wasa da Yan daurin rai da rai ko sun kasheka to fa su hukunci daya dai
gashi Nan shi yasa budurwar Yar film sum sum ta koma wajen rawarta bata ce kala ba
duk tijarar da Naila tayi mata,kamar ba gidan yari ba yanda ake likin kudi ana zuba
naira Banda Spark bare Jamilu Naila da ba gatan kirki shi yasa yaki lika
sisi,Scoler ne yazo yace me yasa wai Baki yi likin ba? Allah ya hana likawa irin
wannan masu yada badalar kudi haka Malam Jilani suka ce Kuma na dauki
wa'azinsu,Scoler yace munafukan malamai Allah yasa kar su kashe Maka zuciya ka
daina Daudu,Naila tace a'a wannan ko Sudais ko shureim na Makkah ne suka zo bazan
daina ba Daudu yanzu na fara,Scoler yaji dadi yace yawwa ko Mufti Menk ne karki
dauki wa'azin,Naila tace hauka nake Daudu for life.

Spark Yana jinsu ko harkarsu bai shiga ba.


Tunda Spark ya zauna baiyi Magana ba daka kallo sai danna waya har ya gaji ya
mike zai tafi abinsa Naila bata kulashi ba itama,sai da ya tafi tace Dan iyayi wai
shi me kudi dan ya samu ma Ina kulashi sai nayi maganinka.
Tashi tayi ta koma dakinsu Inda kasa kasa tana jiyo surutun mata dakin wasu a Jikin
dakinsu yake,Naila ta Dora kanta a Jikin bango tace da karfi Ina son daya a
cikinku,Mata ta bangarensu sukaji magana,wata a ciki ana ce mata Beauty tace Ina
sonka nima sunana Beauty.

Kasa kasa Naila taji tayi tsalle tana murna,tace Inama da kofa da na Kalli
fuskarki,sunana Beauty aka bawa Naila amsa mata sai shewa suke a dakin,Naila tace
mashaallah zamu dinga zance ta Nan sunana Jamilu me zamani,Beauty tace daga Jin
Muryarka ka hadu,Naila tace da zaki Ganni sai kin dalalar da yawu na hadu,Wata a
ciki tace nima Ina sonka,Naila tace duk ku taho Ina sonku ni na mamajo ne ko wacce
zan iya da ita,ya aka ji da rashin da namiji a kusa? Beauty da karfi tace muna fama
wlh duk gamu taron balagaggu,Naila tana dariya itama da karfi tace iceko bakwa
warin balaga? Malam Garzali suna dakin suna jinsu su tunda suke ma basu taba Jin
Muryar mata ba sai yau,Kunya duk ta kamasu manya dasu gasu malamai Jamilu duk ya
takura musu,ga kaunarsa duk ta kamasu sun rasa sukuni,Beauty tace Kana da waya?
Naila tace me kika ce? Banji ba,kana da waya? Naila tace Allah sarki maraya ne
ni,Beauty Yar gidan me kudin gaske ce itama kaddara ta kawota tace karka damu zaka
yi waya me tsada zansa Daddy ya kawo amma sai munci gaba da soyayya Naila a ranta
tace dole na dage naci kudin Beauty, Su Malam Jilani suna jinta sun kasa karatunsu
da suke faman yi,Beauty tace da dare zamuyi free call ta jikin bangon nan,Naila
tace karki damu sai anjima bye.

Ta Kalli Malam Jilani tace ku malamai ba a morarku sai dai ku Mori mutum wato
tunda nazo Kun San maraya ne ni amma ko sisinku ba a ci haka aka koyar daku a
Islamiyya,Malam Sharu ya zaro Dari biyar yace ita kenan gareni ungo Dan Allah ka
canja wani dakin Jamilu,Naila tace tab Ina nan so kuke ayi min fyade,Malam Garzali
a hankali yace mun shiga uku mu dai.

Umma ita kadai ce a gidan yara suna Islamiyya da yamma lis sai Abba yayi
sallama ya dawo a gajiye Yana Nishi ya zauna Saman kujera,tace Kai Kuma lafiya?
yace yau Nasha aiki jarkar Mai biyar na dauka a wajen aiki duba min kaina na fara
sanko ko? Umma ta watsa Masa harara tace yanzu sabo da lalacewa akan ka dauki
jarkar mai biyar shine abin gajiya haka har wani sanko zai fito Maka,Abba yace ke
kinji nauyi ni gaskiya idan haka zan dinga yi zan bar aikin Nan bazan iya ba,Umma
ce ta fashe da kuka,da sauri ya kalleta da Dan cikinta a gaba sanye take cikin riga
da zani na atamfa,yace lafiya taki magana sai kuka take yi,yace haba Kubra menene?
ta sake fashewa da kuka,Abba duk ya rude Yana tambaya menene? Sai da kyar tace Dan
cikina nane yace a dauke shi,Abba ya bude Baki yace ta Ina yayi maganar? ya akayi
ni banji ba, through placenta ya fada min uwa ce kawai ke gane yaren danta,Abba ya
kalleta yace yanzu Kubra na gaji amma baza ki tausaya min ba,taya zan dauki jaririn
Dake ciki? tace ai idan ka daukeni to ka dauke shi,Kubra gata me kiba Abba Dan
tsurut haka ya Mike ya yunkura Yana Nishi ya dauke ta da kyar suka tsaya a
tsaye,tace kaji wai a zaga da shi yace,Kubra nauyi ne Dake wlh kamar buhun sugar
kiyi hakuri kuka ta fara ya fara zagawa da ita a hankali da kyar Yana Nishi,sai da
taga ya Sha bakar wahala sannan tace yace a cinyarka zai zauna shi,Abba ya ajiyeta
da sauri Yana Nishi kamar me,ya zauna ta zauna a cinyarsa yayi zuru da Ido ransa a
bace sai da taga yara zasu dawo sannan tace to danwake zaka yi min yau yace shi zai
ci,Abba ya kalleta kawai ya Mike ya shige daki tare da kulle kofar ya sa key shi
bazai iya cewa bazai yi mata ba tunda ya Saba Yana yi mata watarana.

Mummy tunda aka kama Spark hankalinta fa ya tashi matuka kuka ba dare ba
rana,duk ta rame ta lalace burinta taje taga Danta,sai lokacin ta tuna da Jamilu fa
Yana can shima ta dalilinta,share zancen tayi duk da suna waya da Spark amma Sam
hankalinta baya jikinta, Mima Kam abin a ranta yake dukanta Wanda ba Wanda ya gane
Hakan sai dai a ganta duk ta fige ta rame,Daddyn su Spark shi kansa abin Yana
damunsa amma ba yanda zaiyi.

Mima tana dakinsa ya kalleta a hankali Sam bata hayyacinta duk ta


rame,tambayarta yayi yace meke damunki ne ko tunanin Spark ne? Mima murmushin
karfin hali tayi tace a'a...idonta ya ciko da kwalla sai kuka bata San sanda ta
fashe da kuka ba,Daddy ya kalleta cikin shigarsa na kayan manyan sojoji Yana Shirin
fita,yace sai hakuri fa kaddara ce sai dai addua.

Rafeeq ne ya shugo ya same su a haka da sauri Mima ta goge hawayenta ta nuna ba


komai shima Rafeeq duk da yaji zancen su bai nuna yaji ba,gaishe su yayi kawai
sannan Mima tace ya school din? yace Alhmdllh,Kuna waya da Spark kuwa? yace dazu ma
munyi waya da shi ai shi baya cikin wahala part dinsa ma daban,Mima tace yayi kyau
na kira shi yaki dagawa ai,dole yaki dagawa ni banga laifinsa ba Yana da gaskiya,Ku
Baku bari anyi bincike ba Kun kasa tsaya masa Wanda Kun San gaskiya bazai aikata ba
amma kuka goyawa iyayen Asmau baya an bata Masa suna sabo da Yan uwantaka,dama
Aunty ce ta aiko ni tace ki bata sakon na Kai mata,Mima tace to tana wani bata rai
ta dakko sakon ta mika Masa a leda tace yaya kudin baka kawo ajiyar ba, fuska ya
daure yace na bawa Aunty ya juya tare da ficewa abinsa.

Mohsin zaune yake Saman Sallaya Yana addua cikin tsakiyar dare Naila yake ta
yiwa addua,Hanan ta farka tace wai har yanzu adduar ce kazo ka kwanta karka kashe
kanka akan wata,ko kallonta baiyi ba,haushi ya kamata tace wannan Naila din kwai
tsinanniya ta Hana mijina sakewa,a fili tace yau kwana nawa kaki kazo ka sauke min
hakkina Kuma kasan Ina bukatar namiji a kusa,bai ko saurareta ba,ta ja tsaki tace
wlh bazan yarda ba sai na kaika Kara wajen iyayenka kazo ka min abinda nake bukata,
mikewa yayi ya bar mata dakin ya dawo Palo,tashi tayi tace wlh baka isa ba akan Yar
iskar kanwarka ka wulakantani tazo Yana sallah ya tada sallah ta fado gabansa, ai
kuwa ya Kifa mata Mari ya makar da ita gefe ta Fadi can gefe wanwar, sallarsa ya
tayar, sabo da ta hanashi sallah ta dinga kururuwa amma bai fasa sallarsa ba har ta
gaji.

Washe gari da safe ta riga shi tashi sai gidan su Mohsin Yana bacci Bai San ma
ta tafi ba,tana zuwa ta samu Umma suna karyawa da yara yau ba school, tunda Umma ta
ganta tasan ba lafiya ba,dama ta tsani Hanan bata mata kyauta kadan take jira,Abba
kuwa Yana zaune abinsa ya gama karyawa Hidaya tana aikin gida yara suna wasansu.

Hanan ta gaishe da su Umma tare da fashewa da kuka,Umma tace in kin gama kukan
Kya Fadi abinda ya kawo ki,ai ni kukanki farin cikin ganinsa nake yi Hanan Maza ci
gaba wlh Inda kisan Ina kallon film din India sabo da nishadi,Hanan sai ta daina
kuka Jin furucin Umma ta daure tace karar Mohsin na kawo,Abba ya mike zai tafi
wajen aiki yace ki fadawa matar gidan gata Nan ta isa komai ya fice abinsa ya
barsu,Hanan tace Umma Mohsin Yana zaluntata kawai hakuri nake zama da shi,Umma tace
da ubanki zakiyi idan ba hakuri ba kowa hakuri yake ai nima da kika ganni me wari
nake nema ban samu ba haka na hakura sannu shafaffiya da Mai, Hanan tace ai nawa
yafi na kowa domin baya biya min hakki na kullum sai Sallah cikin dare,idan cikin
dare yayi shuru Yana yiwa Naila Addua Kuma ko kema ai naga ba haka mijinki ke miki
ba, Umma salati ta saki tace laaaaa wayyo sannu ai ni macece ta kwarai ni haka nake
Masa irinki mahaukaciya shi yasa kika Ganni Ina shanawa sai abinda nace to na cika
mace,ke fa? zaki min iskanci idan ke surukar zamani ce nima itace dai dai nake
dake,marowaciya ko Dan kwai baki taba dafowa kince a kawowa Tsohuwar Mohsin taci
ba,bare Dan sabulun wanka da wanki,kije ki tambayi tarihina a kauye kiji har saniya
na taba bawa surukata kyauta Dan kawai na samu shiga,ke kuwa ko cinyar kaza daga ke
sai danginki, Kun takurawa Dana sannan dare ma bazai huta ba ubanki zai miki cikin
daren?

Duk fitsararki na haifi Wanda suka fiki ke idan da Naila tana Nan kin isa ma
kizo har gida ki fada min kice wai mijina ba haka yake min ba,in Haifa miki yaro ki
aura kizo Kuma ki ci min mutunci Yar matsiyata,Hanan tace to wallahi idan na fada
halaka shi ya ja ai Ina ganin Maza gasu nan,Umma ta daga hannu sama tace ya Allah
ka fito min da 'yata Naila tazo taci ubanki har gida, wayar Umma ce tayi ringing ta
daga sai taji Muryar Naila,ta manta haushin Naila take ji sabo da Hanan taci
mutuncinta, tace Naila ce wai? Naila tace ae Umma itace Jamilu ba,yawwa a dinga
gyarawa sabo da tsaro ko kice Tantiriya is better Umma,ya gida ya kowa Ina Yar
bakin ciki Hidaya? duk kowa lafiya Naila,iceko kina lafiya? tace to gashi nan dai a
fadawa Yaya my love ya kirani da wannan number din,Umma tace to ga matarsa ma tazo
ta kawo kararsa,Naila tace ki fada mata na saketa saki uku Umma ta kwashe kayanta
na saketa,tana jinki ma ai na sa a handsfree,Naila tace yawwa ai da Allah yasa Ina
Nan da tuni na kashe auren Yaya, Umma tace wai baya biya mata hakkinta,Naila tace
ai da nasan gidan yari zanje da kafin na tafi zan bawa Yaya magani na kwantar da
Hallare wanwar a kasa bata sake motsi sai ya sake aure na tashe ta,Umma dariya ta
kamata da kunya sosai amma bata yi dariya ba kunya ta hanata dariya ga suruka na Ji
ga Naila yarta,share zancen tayi tace idan ya shugo zai kira,Naila tace to a gaida
su Aslam da Hidaya Yar bakin ciki da Zarah,sannan a cewa Darling ya kirani,Umma
tace to sai munzo ziyara.

Naila tace ko baku zo ba ma I can survive, Allah Yana kula da halittarsa, tururuwa
ma Allah na kula da a barsa bare Dan Adam, Tausayin Naila ya kama Umma sosai harda
kwalla ta datse wayar da sauri tasan magana Naila ta fada mata da suka ki zuwa
mata.

Hanan tuni tayi waje ta fice ta tafi gidansu tana kuka tace Mohsin da iyayensa
ne suka ci mutuncinta, Mamanta tayi mata nasiha aka maidata gidan Mijin,Mohsin baya
gidan bai san ma ta koma ba,Yana dawowa daga wajen aiki ya ganta a gidan tana
girki,ransa a bace yace yanda kika tafi ki tattara ki koma gidan naku ai Umma ta
kirani a waya ta fada min karata kika Kai musu sannan kika wuce gidanku sai ki koma
gidan naku Kuma karki sake ki daukar min 'yata,Wani takaici ya kama Hanan tace ai
dai muna da gidan ko,sabo da kaje gidanku an zugaka shine zaka dawo ka raina min
hankali dadin abin dai ubana Yana da gida,Mohsin yace kije dai ku kwana da yara su
tsula miki fitsarin kwance a jikinki,lokacin da nake zuwa zance gidanku in kika
fito mayafinki zarnin fitsari yake ko kina tunanin ban gane ba to hanci na ya jiye
min shuru nake miki kawai Ina dauke kaina gefe,Hanan zuciyarta har suya take sabo
da bacin Rai,bedroom ta shige ta dakko mayafinta ta saka tana tsaki tace gidan naku
ai ba fin namu yayi ba,ubana na ma yafi naku,naku sai yanda tsohuwa tayi da shi,ta
juya zata tafi ya fisgota yace me kika ce? taji tsoro amma duk da haka tace na fada
gwara ubana...ai kuwa Mohsin ya hau jibgarta tana ihu har makwafta sai da suka
shugo,da kyar aka lallaba Mohsin ya kyaleta amma mayya Hanan ta San ta kan
Mohsin,sai tace bazan tafi ba ai nayi wanki gashi Nan a Saman igiya yanzu zan
kwashe zan tafi.

Mutane kowa ya watse sai wata dattijuwa Mohsin yana cewa Baba sakinta
zanyi,Tsohuwar tana cewa kayiwa Allah Dan girman Allah ko Dan darajar yarku karka
saketa,bazan zauna da ita ba Baba,Baba tace karka ce haka Dan nan,Hanan ta koma
bedroom ta cire kayanta ta fito da daura kirji ta shiga toilet ta fito ta sake
komawa,ta fito karo na uku ta shiga kitchen sai ta sauke zaninta a iya kugunta ba
bra ba riga daga samanta sintir sai kayan uban nonuwa suna ragaje ragaje ta fito a
haka ta wuce su tana girgiza ta shige Palo ta sake fito tana girgiza kirji tana
cewa duk abinda mutum yake ji nima Ina ji,Baba tsohuwa tana ta dariya a ranta tasan
iskancin Hanan tasan dalilinta,Mohsin sai kace tsohon maye duk Inda Hanan tayi sai
kallo Yana mika wuya Yana Cewa Baba zan sake ta fa? Iya tace a'a kayi hakuri,Hanan
ta fito tana waka ahayee dawo dawayya....tana girgiza....Mohsin yace to Baba ance
rayuwa sai da hakuri musamman ga ma'aurata ko? Baba tasan batun tace ae yi hakuri
kaji,yace to na hakura yanzu tunda dai nima na zageta shike nan 1-1 idan ta sake
sai ta bar gidan nan,Baba tace ae Hakan yayi ayi hakuri ya wuce ,yace sabo da ke
Baba Ina ganin mutuncinki na hakura,Baba ta bar gida tana ta dariya.

Hanan kuwa Kwata kwata yini tayi tana zagade a gidan tana wake wake taki saka
riga a haka tayi wanka ta saka Dan skert ba ko riga ba bra ta sake fitowa kamar
karuwa,a Palo ta zauna tana girgiza tana wake wake,Mohsin Yana ta kallonta kamar
maye hankalinsa ya gama tashi matuka,Amal dama tana gidan su Hanan,Tashi Hanan tayi
tana murguda duwawu tana tafiya ta shige daki ta fito daga ita sai pant ta zauna
suna facing juna da Mohsin ta baje kafafu tana tauna chewgum tace zama daram,Mohsin
a nutse yace dama ai kece kika jawo ni ai bance karki zauna daram ba,idan aka yi
hakuri duniyar nawa take eyeee, rayuwa dole sai anyi hakuri da juna ki daina taba
min iyaye wallahi akan iyaye na ba abinda bazan yi ba,Hanan tace ni ai ka zagi nawa
taya bazan rama ba daga na nemi hakkina sai kuyi min taron dangi, Mohsin yanzu Kam
dama a matse yake yace indai akan pleasure stick ne ake wannan tashin hankali gata
nan,ai ita ba bakuwar zafi bace,Hanan taji dadi ya sakko tace to yanzu naji zance
nima ka yafe min mu tafi Downstairs, yace sai kinje kin bawa Umma hakuri,tace zanje
ai ba komai,yace to suka yi cikin bedroom.

Sharhi please fans

Book 1
Free page

Accnt no
0175487861
Asmau Garba Muhammad
Gtbank

Katin MTN
08061929616

Yan Niger
+22790795939

AsmaBaffa
[12/6/2023, 5:18 PM] AsmaBaffa: 🏫 TANTIRIYA🏫
A GIDAN YARI

21-25

Official
By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE
GARE KI
AIDA MAMAN TASNIM

PAGE NAKU NE

Hauwa S Zaria
Binta Umar Abbale
Ashanty

MASU AUDIO BAN YARDA A JUYA MIN NOVEL BA,BADA IZINI NA BA.

*_Albishir! Albishir!! Albishir!!!_*


*_Jama'ar Annabi inayi muku Albishir da cewa nakawo muku wannan shahararre Kuma
ingantaccen gida, gidan da suka darje suka rairaye suke kawo Muku kayiyyaki masu
dankaren kyau da Kuma inganci abisa farashi dai dai da Aljihun ku_*
*_Hajiyata, kanwata, Aunty na, kinaso kisamu kaya Wadanda ba kamarasu? Kayanda
idan kika shirya kika fito kizama abin kallo a wurin Yan uwanki?_*
*_dama wadanda zasu ganki ahanya?_*
*_sbd yadda Zaki fita daban da saura?_*
*_Kinaso Idan kikayi shiri arinka tambayanki a ina kika saye wannan kayan?_*
*_Zakije gidan biki ko gidan suna Amma kina tunanin kayan dazaki saka saboda kiyi
fita ta Alfarma ta kece raini?_*

```ARZUQLANA GALLERY```

*_sunkawo muku duk Wani abu Wanda zakuna bukata kama daga:_*
```Laces
Atampha
Shadda
Abayas
Materials
Gyale
Takalma
Jaka
Kayan Kitchen
Bangles n jewelries```
*And many more*

```GIDAN KYAU, GIDAN QUALITY, GIDAN SAUKI, GIDAN KWALISA, DA ADO```

*_Wani abin sedai kunbiyomu zaku Gani da idanunku_*

*_sunayin kasuwancinsu bisa gaskia da Amana, ba cuta ba cutarwa_*

*_koda bakida kudin Siya Muna gayyatarki dan ki tallata kema kisamu naki_*
*_Yar uwa kasance a gidan, da abaki labari gwanda ki bayar_*
https://chat.whatsapp.com/FRJAnQZXm0t7rAroZWlMnQ

Mohsin tsoro yake yi kar ya saki matarsa yazo Kuma sha'awa tayi Masa yawa
ba Inda zai rage zafi tunda ya Saba da mace shi yasa, bayan sun Sha love sunyi
wanka Mohsin cikin yard dinsa milk ya cakare Yana shining ya fito tare da Hawa
lifan din Ya nufi gidan Umma.
Yana yin sallama a gidan ya samu Umma a kitchen tana Jin shuguwarsa ta fashe da
kuka harda hawaye sosai,duk su Hidaya sai da Umma ta basu mamaki Hira sukeyi amma
daga Jin sallamar Mohsin ta fashe da kuka.

Mohsin ne ya karasa Inda take a kitchen ya leka ya samu tana kuka,hankalinsa ya


tashi yace Umma lafiya? Umma tana shesheka tace zagin da Hanan ta yi min wallahi
bazan yafe mata ba,yarinya tazo har gida ta ci min mutunci Kuma su Hidaya basu iya
rama min ba Wanda nasan da Naila na Nan ba a isa anyi min haka ba, in haifi Dana
azo a fini Iko da shi wulakanci har kaina,ga zafin haihuwa da nakuda sannan nazo na
hadu da zafin suruka,ni a haihuwarka ma ban Sha wahalar nakuda ba amma wlh abinda
Hanan take min yafi zafin nakudarka zafi.

Mohsin yace kiyi hakuri Umma zata zo ta Baki hakuri,da masifa Umma tace ka
dauki mataki ne? Mohsin sai karya yayi yace ai cewa nayi ban yarda ba taci duka sai
da makwafta suka raba abin sannan na kira iyayenta na fada musu shine suka kirani
tare da ita a gabana suka mata fata fata suka ce Kuma na saketa har na dauki
takarda da biro zan fara rubuta shine ta Fadi a kasa tana cewa ta tuba Kuma zata zo
ta bada hakuri, Umma tace to Ina jiranta tazo ta sameni wallahi sai na sake ramawa
fada bai kare ba,Mohsin yace to Umma wai ya zuwa wajen Naila? tace ai naga amfanin
Naila wannan satin aje mata ziyara tare zamu tafi da Kai da Abbanku ma,Mohsin farin
ciki ya kama shi yace Allah ya kaimu Alhmdllh,zanga Naila ta,Umma tayi dariya tace
hankali ya kwanta ko? Yace kwarai kuwa ai nama za a siyo har farfesu za ayi
mata,Umma tace da kuwa ka kyauta,Abba ne ya shugo Yana masifa yace ni wannan aikin
barinsa zanyi Allah ya kawo min wani bazan iya ba.

Mohsin ya gaida shi,Abba yace aikin nan barinsa zanyi rana ta isheni bazan iya
ba,Umma baki ta tabe taci gaba da aikinta,Mohsin yace to wacce zaka yi? Wacce zan
zauna a cikin rumfa cikin inuwa,kana da jarin? Ina naga wani jari ai Kaine zaka
bani gwara na dinga siyar da kayan Miya,zaka iya zuwa ka saro? Abba yace ae zan iya
a bani jari,Mohsin yace to an gama amma Dani za aje a saro kayan,yace ae muje tare
amma wannan aiki su canja wani a madadina,Umma dai kawai girkinta take yi har
Mohsin ya bar gidan bata ce kala ba,duk yanda ta Kai da juya Abba to Banda bangaren
aikinsa baya tantakwaruwa akan wannan aikin.

Bayan kwana biyu Mohsin yaje ya samu ma'akatan yace Abbansa ya bar aiki su nemi
wani,baturen cikin harshen turanci yace me aka yi Masa? Mohsin yace shima bai sani
ba ya canja aiki ne,sai lokacin wani baki bahaushe shima gadin yake yi amma nasu
sai yamma yace au yanzu Hashimu akan turancin Nan ya bar aiki? Mohsin yace wanne
turanci? mutumin ya furta ai tunda masu duba aiki suka zo turawa suka dinga yi Masa
turanci,suna ta turanci shi bai iya ba shine yace bazai iya aikin nan ba azo ana
zagin addininsa bai sani ba,wai bazai taba yiwa yahudawa aiki ba,ba hakurin da bamu
bashi ba yace sun Masa wulakanci cikin turanci anci mutuncinsa,Mohsin yayi dariya
sosai ya gane so kawai Abba yake ya daina aikin,haka dai yace musu ya canja aikin
yi,a ranar aka yiwa Abba rumfa a kofar gidansa.

Washe gari Mohsin ya dauki Abba suka tafi Inda ake saro kayan Miya,aka saro
Masa tumatir,attaruhu,tattasai,Alayyahu,kabewa,albasa,green beans,da duk wani kayan
lambu yazo ya shirya abinsa a rumfa Saman table,ga abin zamansa ya zauna yace yanzu
nasan Ina sana'a.
Abba ya fara sana'a ana ta layin siye sabo da layin nasu babu masu kayan da yake
siyarwa wasu a ciki,matsalar daya idan mata suka zo siyayya ko matan aure ne sai
yayi ta turguza musu kayan miyar,yayi ta zubawa a leda ba ji ba gani,idan namiji ne
yazo sai ya millira Masa tsadar masifa.

Naila dare yayi kaikayin Infection ya dameta amma haka take Dan mazewa ta cire
katuwar rigarta data Dora a Saman katuwar t-shirts me dogon hannu me kauri, Maganar
Su Beauty taji tana cewa Hello.....ta jikin bango,Naila dariya tayi tace na koma
Yar Yahoo Malam Gaza, Malamai ana ta zuwa daukan karatun littafan daban daban a
wajensu suna ta karatunsu amma Naila ta mike ta koma Jikin bangon Dake hade da su
Beauty tace Hello Beauty na? tana Jin matan suna cewa wallahi ya amsa yayi magana
Beauty kizo saurayinki yayi magana,Beauty ta matso sosai da karfi tace ya kake? I'm
good, Beauty tace naji kamar Dan Fulani,wai Dan Allah Dan Fulani ne Kai naji hausar
ne sai a slow, Naila yaren fulatanci tayi,Beauty ta furta Kaiiii a'a daina ni bana
Jin fulatancin nan,Naila tace to ya gidan yari ya bangarenku yake? Beauty tace wlh
ba dadi ai bangaren mata yafi dadi muna iya shegen mu San ranmu matan harda shewa
yeeeed,Naila tace muma nan muna namu iya shegen dai dai gwargwado,tab Kai Nan kaji
kuwa abinda akeyi,Naila tace ke duk iskancinku fa baza ku fada mana ba,gamu Nan da
su Malam Sharu da su Jilani duk Yan iska ne mu ,Malam Sharu ya dago da sauri ya
Kalli Jamilu zuciyarsa ta wani buga yanda yau akwai haske gashi ta cire rigar Saman
ya kafe Naila da Ido Yana fada a ransa yace ji Jikin ma irin na mace,Malam
Gargazali ya Kalli Malam Sharu yaga yanda yake ta faman kallon Jamilu

Sai yaji wani kishin Jamilu a ransa Sam baya kauna a dinga kallonsa sabo da
son da yake Masa,Shi kuwa Malam Jilani Yana dorawa wasu Dake gidan yarin karatu
amma ya kasa sabo da Muryar Jamilu Dake dukan dodon kunnensa kasa karatun yayi yace
Dan Allah kuyi min uzuri sai gobe karatu kaina ciwo yake,Daliban nasu suka ce ba
matsala suka tafi.

Kwanciya kowannen su yayi Yana saurarar Muryar Jamilu a dakin kowa da abinda ke
damunsa na son Jamilu a ransa, Jamilu kuwa bai San ma me suke yi ba yaji an daina
karatun,suna ta hirarsu Naila tace Kai ku wai Kuna kwana da wando? Malam Sharu ya
Kalli Malam Jilani suka hada Ido tare da girgiza Kai,suna Jin su Beauty harda guda
kamar zasu Kai amarya wata a ciki tace wannan sai dai a tambayi Yan dakin su Karima
sune Yan kungiyar kwana ba wando mu nan harda Pampers muke like mazaunanmu,Naila
tace amma baku more rayuwa ba ai idan Kuna so ku Shana kuji dadin bacci ku dinga
kwana da wando,Beauty tana dariya tace ka bani kunya wlh rannan wata tayi Hakan
kyankyaso ya dinga bin wajen,Malam Sharu riga yasa tare da toshe kunnuwansa,Jilani
yasa hannu ya toshe nasa,Malam Garzali kuwa kunnuwa ya bude shi wannan hira dadinta
yake ji

Malam Garzali yace da sauran mazan wallahi ta tuna min da matata Sayyada,Malam
Sharu yace hmmm tunda aka kawo Jamilu nake tuna Mariyata yau rabona da iyalina
Shekara nawa ana daukan hakki a gidan yari,ya dace a dinga hada aure a gidan
yari,Malam Jilani yace kamar ka shiga raina ya Akii da an fito mana da matan gidan
yarin kowa ya zabi dai dai shi a daura mana aure, su Jamilu suke hirar amma su
Malam Sharu sun fisu Jin dadin hirar kamar kar a daina,bayan sunyi sallama Malam
Garzali yace har Kun gama hirar? Jamilu yace ae,a'a ka sake kiransu mana kuyi yaran
suna da kaifin hankali,Jamilu ya dinga dariya yace wato Kam ni Jamilu aji tsorona
ni da kaina Ina kiyayar kaina,Budurwarku ce ko tawa ni na gaji da Jin Muryarta
to,Malam Jilani yace ai kuwa kayi dace Jamilu yarinyar akwai zakin Murya sai kace
matata Suwaiba,Naila dariya take a boye tana ta zurma malamai suna sakin zance
cikin kamewa.

Bangaren Spark kuwa Yana bangarensa shi kadai,duk ya damu ya rasa Inda zai sa
kansa ba abokin hira ba abin yi,abinci ma ya rasa me siyo Masa tunda ya shanye
yogurt da juice dinsa sai biscuits su yake iya ci kawai tunda yazo gidan,wata
matsananciyar yunwa yake ji,ga uban zafi AC dinma ta daina yi,kallo tun yanayi har
ya gaji,gashi sai samu Dan aikin da ya Masa ba bare ya samu dan abokin hira,tsaki
yaja ya Mike ya fito hannunsa dauke da Dan karamin mifici Yana fifita, takaici na
cinsa a ransa yace dama ni nasan Asmau babu alheri a kanta,a jikina naji dama sai
ta jaja min masifa,ko tana raye Allah ne yasan masifar da zan fada amma gashi da ta
tashi mutuwa ma sai da ta tafi da rayuwa ta a haka ma Allah ya taimakeni ban kwana
a gidan ba ai da sai an hada Dani an kashe shike nan ta ja min amma duk da haka
gashi dai ta mutu ni Kuma hukuncin daurin rai da rai badan Ina addua ba shike nan
nima hukuncin kisa za a yanke min.

Beauty ce ta sake kwalawa Jamilu kira tana ta Hira ga Naila kaikayi ya isheta
tace da Beauty Ina zuwa zanje na karbo sako zan dawo karki bacci sweetheart,tace to
Ina jiranka wlh hira da Kai dadi akwai nishadi,Naila tace Allah sarki ai Ungozoman
din data wanke ni me fara'a ce tana min wanka bakin Nan a washe gata da katon baki
tana magana tana tintsira dariya shi yasa na taso da abin dariya da Surutu bakina
baya shuru,ta fito zata buya tayi susarta tana fitowa wani bangaren duk duhu tana
sauri tana bi lungu da sako duk yawanci mutane suna daki wasu suna waje suna Shan
iska, Inda bishiyoyi suke ta nufa sauri take kawai ta buya tayi susarta kawai tayi
karo da mutum karon da tayi da shi sai da ta Fadi har kasa sabo da macece ita ba
karfi.
Spark ne ya haska wayarsa yaga Jamilu yace Kai wai baka da karfi ne duk ka kashe
zuciyarka ji yanda kazo ka bige ni Ina zaka je haka, Naila tsayawa tayi tana
kallonsa,yace Kai wai baka sanni bane mene haka nifa ba Dandaudu bane bana son
wannan kallon,Naila mikewa zata yi ta kasa kafarta ta gurde,tace Dan Allah Dan
taimaka min na kasa tashi wannan kafar zaka danna min ta koma dai dai ta murde.

Spark wani haushi ya kama shi amma yace ni ban iya ba,Naila tace shi yasa ba a
son mutum fari kalarka da yawa sabo da irin wannan baku da tausayi ,oh tunaninka
tausayinka zanji? Ae mana baka da Imani abin yayi yawa ka rage,hmmm kawai yace Ina
zan samu abinci? Naila tace dare yayi ai kasan nan ba freedom ba a yin abinda aka
ga dama, Dan Allah ka tafi ni sauri nake budurwa nayi,Namiji? Spark ya tambaya,tace
Kai nifa bana harkar takashi yawwa macece sunanta Beauty, a waya? a bangaren mata
mana akanta zan iya fasa bango na kalleta,wannan ginin zaki iya fasawa? Naila tace
wai me yasa ba a hada aure a gidan yari ne,ai da sai masu daurin rai da rai a dinga
hadasu aure, uhm Spark ya furta kawai ya juya ya tafi abinsa Yana kamshi sosai,
Naila susarta tayi sosai ta dawo dakinsu.

Malam Garzali yayi bacci cikin bacci ya fara mafarkin Jamilu suna zuba love
Kuma a mace Jamilu yazo Masa ya Sha mafarkin dadi sun zuba love,cike da nishadi ya
tashi da asuba ya Kalli Inda Jamilu ke kwanciya can karshen katon dakin Yana ta
baccinsa hankali kwance yace ya Ilahi wannan ba mace bane kuwa dole nayi Istihara
ko Allah zai nuna min gaskiya.

Washe gari yau ranar ziyara ce,yau Kuma Su Umma zasu zo wajen Naila,anyi girke
girke masu rai da lafiya,Mohsin,Umma da Abba suka zo mata,Ana bude Maza Wanda aka
zowa ana ta kiransu duk sun fito kamar me,Naila ba zato taji ance Jamilu yazo,tace
nasan wannan Yan iskan ne zasu zo Wanda suka zo waccen karon tana fushi tana cika
tana batsewa ta nufo wajen,Spark ta Gani shima an kira shi Yana waya ya fito sanye
cikin 3qtr da tshirts arsh color sababbi yayi kyau sai kamshi yake Yana shining
dake shi wajensu special ne,yana waya ya Kalli Jamilu ya canja kaya kanana girman
kayan da yake sawa ne yake bashi dariya,amma yau ganin Jamilu yayi Yana ta fushi ba
nishadi ba murna,haka ta fito ai sai ta hango Mohsin a tsaye Umma da Abba suna
zaune ga kaya Nan a ledoji, ihun murna tayi ta fito da gudu tazo ta fada Jikin
Mohsin tana murna tana dariya tace wow sai dariya Kuma tare da hawaye a fuskarta,
Mohsin kankameta yayi Spark Yana satar kallonsu fuskar nan ba Rahma,.

Naila wajen Umma ta koma ta fada cinyarta tana murna,sai Abba ta mika Masa
hannu ya riketa,shi ta fara durkusawa ta gaida shi ya amsa Yana murna Naila bata
taba durkusa musu ba sai yau,Umma tace oh Nail....Naila da sauri tace Jamilu Karki
manta cikin rada, Umma ya ta iya haka tayi shuru bata ce Jamilu ba bata ce Kuma
Naila ba,Naila tace yawwa Umma ka Fadi Alkhairi ko kayi shuru,ya gida ya kowa da
kowa ya su Hidaya shugabar masu hankali ta Kano state? Umma tace Hidaya din? Ai
haka take nunawa ta fini hankali ita wayayya me hankali,Abba ya aikin? Abba yace
Alhmdllh gashi nan kuwa naga ke har kiba ma kike yi,Naila ta sake gyara musu take
yi Jamilu ku daina mantawa ta fada kasa kasa,Mohsin yace Hanan tace a gaishe ki,Hmm
ka dai ari bakinta,bana amsawa indai itace,Mohsin yayi dariya yace ki yafe mata,wlh
bazan yafe mata ba ni fa kawai ka fara neman aure,au kin fasa binciken a kaina ai
sai ki bari a bincika ko canja ni akayi a asibiti muyi auren,Naila ta tuntsire da
dariya tace lokacin ban waye ba yanzu na waye ato,Mohsin yace a Hakan? baka ga
alama ba? Ni Gani nayi kin sake zama wata tsagera Yar kunyar ma da kike yi ta
Fulani yanzu babu naga duk uban mazan Nan harkarki kike yi,Naila tace Dan ma baka
San tsiyar da nake shukawa ba Yaya,Na zama Yar Yahoo fa wata nayiwa Yahoo zata siya
min waya ta zaci namiji ne muke ta soyayya ta jikin bango,Suka yi dariya Umma tace
Allah ya shiryaki,Suna hirar kuwa sai gashi an sake zuwa neman Jamilu
Tantiriya,tace gani, Baban Beauty ne yace a Baki, Naila ta karbi ledar ta bude
wayace hadaddiya Samsung sabuwa dal a kwali,harda kudi dubu goma a envelope, Naila
tace Baban Babyna ya bani Yaya,Mohsin ya boye dariyarsa shi Kam Naila tafi
karfinsa,duka Maza da matan ubansu suke ciki a wajen Naila, su Malam Garzali ne
suka fito suma anzo wa kowa cikinsu,harda zuwa su gaisar da Iyayen Jamilu kowanne
wai su a dole masu Aboki,.

Dan Indo shima yazo ya gaida su Umma,Scoler da Goje ma suka zo suka kwashi
gaisuwa,Scoler Yana wata karairaya ya Kalli Mohsin yace da alama wannan shine yayan
namu,Naila tace shine Darling dina nane,Scoler yace ah wallahi shar Darling Mohsin
barka da isowa na Dade Ina so mu gaisa da babban Yaya ashe zaka zo yau Darling,sabo
da Allah bakwa kyauta mana ba kunki zuwar mana ziyara,to yanzun ma Kun kyauta ai
idan zaku tafi zan yi mi'ara koma baya inzo muyi sallama yayi girgiza Yana shanye
hannu yayi gaba.

Umma ta rike baki tace yau Ina kallon ikon Allah, Mohsin kuwa Spark yake kallo
sai yaga kamar ya sanshi, Umma sai yanzu ta kula da Spark tace Kai waccen fa kaiii
amma waccen Dan me kudi ne wannan irin kyau haka ko ziyara ya zowa wani ne? Naila
tace ai abokina nane shi aka zowa Ziyara,Yana zaune tare da Kamal da Sadeeq kaninsa
sai Naila taga kamar gulmarta suke yi.

Lokacin Kamal yake cewa ka tambayi kuwa Jamilu Hashim din ai Yana ciki
shima,Saddiq ya nuna Naila yace gashi can ma wlh wannan amma ni mamaki nake ace
namiji ne,Kamal yace namiji ne mana ai akwai masu kama da mata, Spark yace dama wai
shine Jamilun da Mummy ta daure? Kamal yace shine kuwa ka taimaka Masa Dan
Allah,Spark baki ya tabe yace waccen ai shahararren Dan duniya ne wlh ban taba
ganin Tantiri irinsa ba,Saddiq yayi dariya yace muma da muka je kotu mun Sha kallo
wallahi a gaban mutane da alkali ya dinga tijara,baka gani ma'aikatan gidan ma sun
sallama Masa.

Spark yace Jamilu yafi karfina ta ya zan taimaka Masa duk gidan nan ba Wanda ya
kaishi suna baka gani ba sai zuwa gaida iyayensa akeyi ba,ka dai daure cewar
Kamal,Saddiq yace nima wlh Yana birgeni ba a taba namijin da nagani yake birgeni ba
irinsa, Naila tana gani tace waccen gulma ta suke,Mai gulma Dan wuta ta furta yanda
zasu ji ta,tace duk mai gulma ba shi ba Rahmar Allah

Spark ya kalleta suka hada Ido ambola ya mata,ya zageta da hannu,Naila tace
niiii ...ta nuna kanta ya daga mata Kai, Kai ta jinjina tana murmushi tace zaka
shugo ne,Kamal yayi dariya yace kaji yace zaka shugo,Spark yace baida karfi ko
kadan bigeni yayi rannan fa ya Fadi a kasa,suka yi dariya.
Naila kuwa abincin aka ce a bude a gani sabo da tsaro kowa ya kawo abinci sai ya
dandana kafin na gidan yarin ya ci,Umma duk ta dandana,Sannan Naila tace yau akwai
party wlh ta zaro yankan nama daya kato ta lunkuma a bakinta tana ci tana kallon
ma'aikatan nasu tace Dan bakin ciki sai dai ya mutu wlh Allah,nama munfi bayin
gomnati ci,muna bautar Allah suna bautar Gomnati,Umma tace kiyi shuru Dan Allah mu
fita lafiya..suna haka sai ga Hanan tazo itama tsabar sa Ido wai taga yanda Naila
ta rame tayi dukun dukun tayi duhu sai kuwa ta hangota Shar da ita,a haka ta karaso
tana Jin haushi.

Karasowa tayi tana Bata rai su Umma kawai ta gaisar ta Kalli Naila tace Yaya
wahalar gidan yarin? Naila tace hmm wahala tana wajen Wanda suke cikinta ni Kinga
wahala a jikina ne?rayuwa kenan cewar Hanan,Naila tace yo dama life haka take mana
cikin biyu zaka yi Daya ko kaji jiki ko kaji dadi,ke ba gashi ba ai son ranki ki
auri me kudi to ga Yaya Nan dai sai rufin asiri kina kallo matan masu kudi suna
shanawa ke kuwa fa? Kina son daura atamfa super ba hali sai dai chigambi karama
Naila ta furta tana kallon atamface chigambi a Jikin Hanan,taci gaba da cewa to
Kinga rayuwa haka take kina cin shinkafa da wake wata tana cin Shinkafa da Miya har
da nama da kayan lambu,Umma tace gaskiya ne ke kika ja ma kanki Kuma wlh bazan
hanata ba.

Hanan baki ta tabe,Naila ta sake dakko nama tasa a baki tare da girgiza Kai
tace wash....dadi my Enemies are crying,har mafarkin kukan makiyana nayi jiya na
hango su suna ta kuka ashe yau abin zai faru hhhhh tayi dariya tace ahhhh Makiyana
suna fama,Yaya ya kamata fa ka hanzarta ka Nemo mace ka Kara aure mun gaji da
shinkafa da ake ta ci kamata yayi a nemo taliya da Miya, Umma tace to ya isa haka
ai kin rama duk tsiya wajenki ta zo,Naila tace sa Ido dai tazo taga ya na koma Kuma
taga ba haka ba,mutum ba a shiga harkarsa ya dinga takurawa wani shi yasa tuntuni
nace na saketa ni,wlh Bata gabana Sam na gama da shafinta a haka ma darajar Darling
take ci,Inama ace Yaya ba Dan uwana bane ta dole zan shiga gidan wlh muyi kishi ni
bana so ma a saketa sai nasa tayi zaman bakin ciki a haka zata kare rayuwarta.

Abba Yana jinsu yace Naila ba a hanaki ki ji ko bakiji me Umma tace ba, nayi
shuru to naga bakin Umma shine yayi sanadin zuwana Nan gidan,sai da tace kar na
siyar da magani bada yawunta ba amma naki jin maganar uwata sai gashi na fado gidan
yari Dan Allah ku yafe min daga yau sai abinda kuka ce zanyi ba ruwana,Hanan mikewa
tayi taja tsaki ta fice tayi tafiyarta gida,Mohsin yaji haushin tsakin da Hanan
tayi a gaban iyayensa bayan itace da tsokana hasali ma bata fada Masa zata zo
ba,ransa ya baci matuka abinda take Masa duk Inda taga dama sai ta fita ba tare
data fada Masa ba.

Hirarsu suka ci gaba da yi Naila tace Abba ya kasuwa ashe an koma kasuwa,yace
kasuwa Alhmdllh Ina can Ina ta yin araha,ai kowa araha nake Masa, Naila dariya ta
kamata wai Yana can Yana ta Araha,Naila tace Abba kace duk masu abincin siyarwan
nan na layin...kafin ta karasa yace duk a wajena suke siyen kayan Miya,zawarawa da
matan aure harda Yan mata layi suke min ni kuwa inyi ta musu araha,Umma ta kalle
shi tare da galla Masa harara,tace kamar Wanda yayi abin arziki bayan duk dakko
kayan Miya sai an cika Masa kudin jarin ya karye,Naila tayi dariya tace Abba Debora
me yin Sakwara itama nan take zuwa? Yace ae rannan ma kyauta na bata,Harira kuwa me
shinkafa da Miya jiya tace min tunda ta fara siyan kayan miya wajena miyarta
yawanta ya karu, tace riba take ci sosai shi yasa kullum a wajena take siya,Mohsin
yayi dariya a boye Dan kuwa Su Harira sune suke cutar Abbansu Yana basu da yawa
watarana ma shi yasa idan Yana free sai yaje ya zauna a wajen sannan ake cin Riba
ko a tura Hidaya ta zauna ta siyar shi Kuma ya koma gida ya kwanta abinsa ko ya
taya Umma girki.

Naila tace Inama Ina Nan Abba yanda kake son hutun Nan na karba na dinga siyar
Maka kaje ka kwanta ka huta kawai tunda burinka kenan,Abba yace da kuwa na zama Dan
Madara,Umma tayi dariya tace a ranta yazo dai ya dameni ba uwar da ya iya sai
jaraba shi dai yaji dadi a rayuwarsa.

Suna surutunsu Naila tace ma'aikata ga nama Bismillah Kunga month yayi nisa ba
albashi bare a ci a gida,yanzu da za aje shaguna duk list din Yan bashi idan aka
dakko ma'aikatan gomnati ne a ciki,dariya suke yi kawai, sabo da suma ma'aikatan
wasu duk lallaba Yan gidan yarin suke suna wasa da wasu,Wanda yayi rashin mutunci
idan ya sake mutum Yana gidan yari zai bada umarni a bishi har gida a kashe shi,shi
yasa sai da taka tsantsan, dariya suke yi indai Jamilu yazo waje sun ga ta kansu da
bakaken magana.

Spark ya gama da su Kamal zasu tafi yace Mummy yaushe zata zo? Wai sai ta gama
takaba tukun, yace Alright my regard to her ace na gode,suka tafi shi Kuma ya taho
zai wuce ciki Naila ta riko rigarsa ya tsaya tare da Juyowa tace abokina ga iyayena
da yayana My love,duk wulakancinsa sai tayi mamaki ganin ya rusuna ya gaida da Umma
sosai,Ya gaida Abba da mutuntuwa sosai harda kakalo murmushi,Sannan ya mikawa
Mohsin hannu yace sannu da zuwa Yaya,Mohsin zasu yi sa'anni da Spark suka
gaisa,yace kaima kaddara ta fada Maka to Allah ya kubutar da ku,yace Ameen da ledar
take away a hannunsa,muma lokaci yayi tafiya zamuyi an fara Maida mutane ciki,Spark
yace yeah ai matan ciki za a fito dasu suma,Naila tace ai naso ganin Beauty amma ba
dama, Spark ya faki Ido ya gallawa Jamilu harara.

Mohsin yace to Jamilu ku shiga ciki zamu wuce,Naila ta mike tare da daukan
ledojinta, tace a gaida su Aslam da Hidaya,tayiwa Mohsin rada ka tabbatar yau baka
bawa Yar iskar matakar ka ba Hallare,Kaine baka da garanti a rayuwa ayi mutum ba
hakuri,wlh idan na fito sai na kashe Hallare ta daina komai kowa ya huta,dariya
yayi yace munje wajen Kaka Affa,mun fada Masa halin da kike ciki Yana ta kuka
wlh,Har maganin gargajiya ya bani shi yasa yanzu Hanan bata so nace ta tafi
gidansu,Baki Naila ta rufe da hannu tana dariya tace Yaya kaima ka zama
Tantiri,Umma tace Dan Allah Kai muje sai za a tafi zaku fara kus kus, Naila tace
Umma ya bin kangon wajen masu gini? Umma tace na daina yanzu bana so na koma neman
warin taba sigari,Abba yace Dan Allah muje sun fa daga mana kafa Kalli yanda ake
Maida wasu ciki.

Sallama suka yi Naila ta tafi ciki tuni Spark yayi nisa har jiri yake yi na
yunwa gashi daga nesa su Kamal suke basu taho Masa da abinci me nauyi ba,Yana
komawa ciki ya tsaya Yana jiran Jamilu,Naila ta shugo da kayanta Niki Niki,wai wayo
zai mata yace Jamilu zo muje part Dina muyi ciyayye kasan akwai Lada cin abinci da
Yan uwa,ana so ko makwafta da abokai ka dinga fitowa da abinci kuna ci tare.
Naila tace Allah sarki ai shi yasa mutanen da suka fimu zumunci da kaunar juna
to za a hadu a ci abinci tare muje,yayi mata wayo dake macece.

Spark yace a ransa Kai Jamilu ba wayo, suka shiga bangarensa sai da izininsa
aka barta ta shiga ciki, palonsa suka zauna ta bude ledarta ta duba har kayan Maza
an kawo mata harda pad a ciki a boye an sassaka a ljihun kayan pieces yanda baza a
gani ba,tace ai sai Yaya Mohsin, harda hular Sanyi da hula p-cap yanda zata dinga
rufe gashinta, da wani mayafin kamar na Maza tasan na sallah ne, ta samu kayan sawa
har kala biyu ga vest ta mata me kalar ta Maza,haka boxers da panties dinta duk a
boye Wanda mace na iya sawa haka namiji na iya sawa tasan aikin Mohsin ne.

Shi kuwa Spark Yana Ganinta ko ta kan kayan Bai bi ba kawai abincin yake so a
bude yaci me gishiri da Maggi, Naila Jamilu ta bude abincinta na farko farfesun
Naman rago Yana kamshi,Ga wata fried rice taji hadi,harda hadin salat daban da
soyayyar kaza,gefe ga tuwon shinkafa miyar egusi, harda dambun nama da yawa
daban,sai chinchin da meat pie, ga hadadden zobo Umma tayi da sanyinsa,Jamilu yace
Kai gidan yari yayi ta wani bangaren,da a gidane yaushe za a kawo min wannan, da
spoon na roba guda uku an zubo mata.

Spark sai kace abincinsa ya dauki Spoon yayi Bismillah ya ja kwanon Fried rice
ya fara ci,yaji dadi yace mamanku Jamilu ta iya girki,Jamilu ma yasa spoon yace
kaifa mamanku? yace tab Yan aiki suke girki ta manta yanda akeyi ba dadi nata,
dariya ta kama Naila ta dinga kyalkyala dariya, Spark ya kalleta yaci gaba da cin
abincinsa ba tare da ya kalleta ba yace Jamilu kasan kana kama da mace kuwa? Naila
tace haka ake cewa ya na iya da halittar Allah,tunda nazo gidan Nan nake kallon
kirjinka ko zanga Nono amma babu,Jamilu yace wato Ido kake sa min, fuska ya hade
yayi shuru Yana cin abincinsa sai da ya cika cikinsa dam,tunda yazo gidan yarin sai
yau ya koshi yaji dadin jikinsa, duk ya cinye shinkafar Naila kadan taci ya cinye
mata,tuwon ta jawo zata ci ya kwace yace sai dare za a ci wannan, Jamilu ya tsaya
Yana kallon ikon Allah yace ni da abincina zan fasa ciyayyen wlh kaji mutum,Yace
baka isa ba sai mun dinga ciyayya daga yau Kaci abincina naci naka ya tura mata
ledarsa yace gashi Nan cinye wannan ai dama ba aci nawa ba.

Naila ta bude ledarsa Taga tarin snacks da su yogurt,fresh milk da tarkace


daban daban, ta zabi cake kato da yogurt taci ta koshi sannan tace kawo abincin na
tafi da shi akwai Yan dakin mu,yace baza a basu ba kawai sai su cinye mana suma ai
anzo musu Kai Jamilu bana son wannan Imanin naka,idan mutum ya fiye Imani baya iya
taimakon wasu,Naila dariya ta kamata tace to kawo Naman a basu,yace ka basu
farfesun mana mu sai mu ajiye soyayyen ko ya kace,Naila tace to Hakan yayi ta dauki
farfesun da wasu cakes din da su lemuka Wanda aka kawowa Spark ta tafi da su
dakinsu tana cewa sai dare zanzo muci tuwon yace to sai kazo,ka samo min Dan aiki a
part dinku zai na min wanki da guga da shara zan dinga biyansa.

Naila tace gani aikin me nake ni indai zaka biyani zanyi,a ransa yaji Tausayin
Jamilu Ashe shine Mummy dinsa ta yima sharri,amma bazan nuna nasan shi bane,wannan
dalilin ne ma yasa har ya gaida iyayen Jamilu,baida burin yasa Jamilu aiki ya dinga
wanke Masa kaya da shara a fili yace muguntar tayi yawa gashi ya yarda naci
abincinsa wannan Jamilun akwai kirki,wai har Yan dakinsu zai bawa namansa, kwanciya
yayi a Saman bed dinsa Yana ta sake saken rayuwarsa.

Naila kuwa tana zuwa dakinsu ta iske malaman sun hadu suna ta cin abincin da
aka kawo musu duk cikinsu babu me binci da nama,daga shinkafa dafaduka sai shinkafa
da wake,sai shinkafa da Miya da kifi sai Dan lemon su fanta,Jamilu Yana shiga suka
ce Bismillah Malam Jamilu,Naila tace a'a kune malamai Kun taba ji nayi wa'azi a
gidan Nan? Ba karantarwa ce ta kawoni ba kaddara ce wlh ba Wanda zan koyawa karatu
ko na iya,Malam Sharu yace a daina biyewa rudun duniya Jamilu ka shigo makarantar
mu, Naila tayi dariya sosai tace zan shugo,Naman ta ajiye musu tace gashi ta zube
musu snacks da lemuka tace ga naku,suka yi ta mamaki Dan a jarabar Jamilu basuyi
zaton zai kyauta ba,suka dauki yanka daya daya,Jamilu yace naku ne fa ku cinye wlh
du ana tare taya zan cinye abu ni kadai,Malam sai murna da godiya yace Allahu
Akbar.

Naila kuwa Beauty ta kwalawa kira akace ta tafi wanka tace idan tazo kuce yau
bazan samu Daman Hira da ita ba naga sakon waya na gode,suka ce to za a fada
mata,Malam Sharu yace Kai ni wannan Jamilu adduar ma taki Masa aiki Inda kasan
shedan,Dan Indo ne ya shigo yace Jamilu Terror taho taho ga abinci, Naila ta mike
ta bishi suka tafi,Scoler ya tare su a hanya yace Habibty na ajiye Maka Kazarka
soyayya ce,Naila tace Rasssss dani Ina zuwa zanzo na karba,Sai da taje Wajen su Dan
Indo da Goje ta karbo rabonta tace sai dare zata ci amma tana zuwa ta bawa su Malam
Sharu sai murna suke yi,taje ta karbo kazar Scoler a soye ta sake kawowa su Malam
Sharu,ana ta Bata abubuwa sai ta duba duk Wanda baida gata a gidan yarin ko ba a zo
Masa ziyara ba sai taje ta bashi,har wasu take Gani tace wane baka bani nawa ba,sai
an bata sai tazo ta nemi yaku bayi a ciki ta basu,Jamilu ya sake suna sai
mutuncinsa ake gani,bayan tayi wanka da dare kaikayin gaba ya isheta tace gobe
asibiti zanje inshaallah, ta shirya cikin sabon kayan da aka kawo mata suma manya
falka falkan gaske, ta gyara tarkacen kayanta,suna fita Sallar Isha tayi sallarta
da addua Allah ya rufa mata asiri kar a gano ta sannan Allah ya fitar da ita, yanda
take sallarta idan sun fita jam'i haka tayi abarta,Allah kuma Yana ta rufa mata
asiri har yau ba a kamata da mayafi tana sallah ba a haka ma sai ta nemi lungu a
cikin dakin take yin sallah.

Malamai suna dawowa suka zauna zasu fara karatu yau sunci nama harda fara addua
kafin a fara karatu suka ce yaron nan Jamilu idan sharri aka Masa Allah ka fitar da
shi,Allah ka shiryi Jamilu,Allah Dan darajarka ka kubutar da Jamilu daga gidan
nan,ka Kara daukaka shi suna cewa Ameen Ameen, Bismillah da Ayatulkhursiyyu,Naila
dariya ta kamata ta danne ta zauna a kasa ta daga hannu sama itama tana cewa
Ameen,Allah Gani ni Jamilu Allah kana kallona,Mummy ka tarwatsata,Mummy data min
Sharri Allah ka tattaro bala'in duniya Dana lahira ka danna acan cikin Mummy, Allah
kasa kullum cikinta ya kumbura,ka sata zawo,komai taci ciki ya kumbura,Ya Allah da
zawo,da kashin jini,da amai da gudawa colera,ciwon zuciya, ciwon kafa,ya Allah da
ciwon Kai,Dana mara,ciwon Sanyi irin naw,,,,tunawa tayi zata tona kanta tace Allah
karka bari ta auru,Allah kasa tayi kwantai,ba ita ba samun bazawari,Allah Danta
Ashraf da take ji dashi Allah kasa ayi Masa sharri irin nawa ya fado gidan
Nan,Allah ka hadani da Ashraf Dan Mummy a Nan gidan yari,Allah basai na fita ba
Allah a Nan gidan,Allah ka bani ikon cin ubansa,kar naji tsoro,kar ya min kwar
jini,naci ubansa daidai yanda ya kamata.

Su Malam Sharu suna addua sai suka tsaya kallon adduar Jamilu suna dariya Yana
gama adduar suka ga ya mike yace na tafi wajen abokina mutumin kirki Ashe Yana da
kirki duk gidan Nan babu me kirkinsa idan Kun ganshi ku dinga girmamashi wlh ga
kudi ga kyau ga kirki iya kirki yau da shi muka samu ladar ciyayya ma yaci abincina
naci nasa,Malam Garzali yaji wani mahaukacin kishi yace kaga Jamilu ka rabu da
yaran masu kudi ka fiye rawar Kai ka kula ka tsare mutuncinka ato Ina baka shawara
kar a Maka wayo kana yaro a lalataka Jamilu,Jamilu kayiwa kanka fada tam shike nan.
Naila tace a'a mutumin kirki ne wannan duk gidan Nan nafi kaunarsa,Wanda nake
jira Allah ya hadani da shi Dan Mummy ne wallahi bala'i da masifa har sai na aro ta
Ummata,rashin mutunci da tuggu kuwa shima sai na Nemo Kari sai na kusa halaka shi
da sharrina,Malam Sharu yace wannan yaro Ashraf ya shiga uku har na fara tausayinsa
mu kanmu da ba abinda ya hadamu ka buwaye mu bare shi,Naila ta fice abinta harda
shafa turarenta sabo da Spark dan gayu ne.

Yana dawowa daga masallaci ya samu Jamilu ya shugo,yace Kai naci Dan tuwonka
Yana Nan shine harda zuwa da wuri,Naila tace Ina laifi Dana jira akayi Sallah ma ko
tuwonka ne? an kawo Maka ne daga gidanku? Spark uban isa da gadara yanzu kirki
anjima rashin mutunci,yace gashi can dauki abinka,ya furta da gadara da kyar yake
magana yana bata rai,Naila taji haushi tace koshi kayi shi yasa ka fada min haka
taje ta dauki abincinta ta tattara da nasa gaba daya tayi waje,ya fito da sauri ya
fisgota, shi mantawa yake Jamilu baida karfi,Naila sai gata ta zube a kasa har
gwiwarta ta fashe,yace sorry, da sauri ya daga Jamilu yaji shi shafal ba
nauyi,jikinsa wani shegen laushi haka,tsoro ya kama Spark yaja baya Yana kallon
Jamilu,yace anya Jamilu bazan Maka tsirara ba kuwa na gani namiji ne ko mace,please
muje ka tube wandonka,ni ba gay bane ba abinda zanji kawai so nake na
tabbatar,Naila tace au ta haka ka bullo fyade zaka min dama ance yaran masu kudi
Yan iska ne to duk gidan yarin Nan sai na fada musu Kai Gay ne,Spark ya zaro ido
yace na janye maganata karka bata min Suna Ina respecting din kaina da kaina.

Naila tace to karka sake ce min haka yace never, muje zaka ci abincin? yace ni
da zaka bar min abincin ma nafi son haka,Naila tace to muyi musaya Kaci nawa naci
naka,yace good,ta koma ta shige ciki ya shiga shima Yana jinjina anya Jamilu ba
mace bane,Haka yayi shuru ya zauna Yana kallon News,Naila ta dauki nasa snacks tana
ci abinta cikin Jin dadi,shi kuwa baya cin tuwo ma a gida amma gidan yari tasa wai
shine ke yin wayo akan a bar Masa tuwo,tsaki yaja yace akan tuwo da shinkafa duk
mutuncina ya zube wai yau ni Spark nace wa wani katon zindiki sorry akan tuwo,bazan
yafewa kaina ba yaja tuwon Yana fushi Yana cika Yana batsewa haka ya fara cinye
tuwonsa Yana Santi,yace uhm Poor Umma da iya girki,maganarce ta fito fili Allah
yasa Naila bata ji ba da ya gane kurensa akan iyayenta bata wasa.

Naila tace ance ku masu kudi Kun San juna watarana Kuna haduwa a wajen da sai
me kudi ke zuwa,idan a Abuja kake Dan Allah kasan wani Ashraf babarsa dai wacce ta
Raine shi Mummy ake ce mata duk family dinsu sojoji ne yawanci,ance ai shegen
Ashraf din nata ya fara aikin soja ya bar aikin ya koma business sabo da shi bakin
Dan iska ne,ance ai matsiyacin ya tara kudi,naji danginsu kowa sai yace Ashraf,baka
sanshi ba? Tunda Spark yake bai taba dariya irin ta yau ba,ya dinga dariya a ransa
yace Allah ya taimakeni ban fadawa Jamilu ni bane Alhmdllh da Ashraf ya sanni,Allah
yasa bai San nasan shi Mummy tayiwa sharri ba,Naila ta tsaya tana kallonsa Yana ta
dariya

Tace ka sanshi dan iskan algungumin? Spark yace ai abokina nane, Alhmdllh ta
mikawa Spark hannu tace mu gaisa ya mika hannu suka gaisa yaji wani shegen shock
duk jikinsa ya dauki vibration,itama Naila haka taji da sauri ya janye hannunsa
yayi wani Sanyi itama haka,tunawa yayi namiji ne da sauri ya girgiza kansa ya dawo
daidai,tace zaka min hanyar ganinsa idan Allah yasa na fita daga Nan gidan, Kai
wannan dan nata sai na Masa akuya,wlh sai na huce a kansa Dan iska
matsiyaci,mutumin banza Allah yasa ya talauce ga mijinta ya mutu ta rasa ko suturar
sawa inshaallah sai na taimaka Masa da shi da ita,jahilan banza jahilan wofi, Spark
yaji ana ta Masa mummunar addua shi ba da laifi ba yace Kai Jamilu addua akewa
mutum kace Allah ya shirya Ashraf.

Naila tace wlh bazan ce ba sai dai na tsine Masa na sake tambade Masa albarka
mutumin banza wa ya sani ma ko a turai din Mata yake bibiya Yana can Yana sheka
iskanci da mata,shi baiyi aure yayi ibadar Allah ba ya zama Dan kwararo shine turai
shine kudu Lagos wajen mata,Dan Bariki, Mayen mata,Ashraf yayi dariya kamar cikinsa
zai ciwo yace wait Jamilu kazafi fa kake Masa ba wani kazafi ai mun sani yaran masu
kudi me suka sani in banda lalata mata Yana can ya zama Dan aci kullum sai kace
Ronaldo kullum aci kwallo haka ya Maida mata,zai gane kurensa Ina Nan Ina addua
Allah ya hadani da shi sai na kwankwatse Masa Hallare, Spark yayi dariya kamar ba
gobe,Naila tace wallahi tun a waya zaka hadani da shi na fara rage zafi da zagi na
fara rage hanya kafin mu hadu,Ba fa shi ya maka laifi ba Jamilu,Naila tace nima ai
ba Ummata ce tayiwa mummy laifi ba ta kare akan Dan Umma to nima akan Danta zan
kare.....

Gidan Baban Asmau tuni sunyi hakuri suna ta uzurinsu an daure Spark,Amma Maman
Asmau wato marikiyarta itakam Yar uwar Maman su Spark ce itama kanwarsu ce,abin
Yana damunta bata ji dadin kulle Spark ba ai shima danta ne,a dalilin haka gashi
Mima ta daina shiga harkarta bare Mummy kamar ba Yan uwa ba gaba suke da ita,Kanwar
Asmau wace ake kira da Safna itama zata kai 26yrs ta gama degree har aiki tanayi a
asibiti,itace kadai tafi kowa damuwa a gidan ta shiga wani hali,tunda aka kashe
Asmau take ta faman ramewa tana damuwa sosai watarana ma sai ta kulle daki tayi ta
faman kuka,kowa yasan yanda suka Shaku da Asmau kamar me kullum suna tare dakinsu
daya,har addua ake mata sabo da yanda ta fice a hayyacinta,aikin ma ta daina zuwa
ba irin lallabata da ba ayi ba taki hakuri,ta samu babansu tace wlh Abbu Spark
bazai kashe Asmau ba,kawai furuci yayi a dai dai kaddara ta fada Masa,Dan Allah
kasa a sake shi idan yaso tunda ana so lallai sai an hadin zumunci ni me zai Hana
na maye gurbin Asmau ko da ace baya so na nima zanyi hakuri na zauna dashi sabo da
na cikawa Asmau Yar uwata burinta,Ni a maye gurbin Asmau Dani,Abbu ya Kifa mata
Mari ya sake Kifa mata Mari yayi ball da ita yace har abada bani ba hada alaka da
Spark Kuma bazai taba fitowa ba,mahaukaciya wacce Bata kishin Yar uwarta Dabba
wacce bata San me take ba get out,ta mike Zumbur ta fice tana sharbar kuka tace
Allah kaga niyyata ta alkhairi ce amma Abbu yaki ta fada dakin Mahaifiyarsu Tana
kuka Mama kinga Abbu ne akan nace ya saki Spark ni a maye gurbin Asmau dani shine
ya mareni ya min duka, Mama tace maganinki kenan ai na hanaki zancen,nifa so nake
na taimaki Spark a fitar dashi,Mama tace duk da bani na haifi Asmau ba wlh ko ba a
kulle Spark ba bazai aureki ba kema,wannan yaron bashi da ta Ido shi yasa nake baya
baya da shi,kina dai gani Yan uwana sun san Asmau bani na haifeta ba amma gaba suke
dani,abin ya kwabe da yawa kiyi hakuri.

Sharhi Dan Allah

Free page
Accnt no
0175487861

Katin MTN
08061929616

Yan Niger
+22790795939

AsmaBaffa
[12/8/2023, 6:56 PM] AsmaBaffa: 🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

26-30

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE
GARE KI
AIDA MAMAN TASNIM

Page naki ne
YAR LELEN ROYAL STAR

MASU AUDIO BAN YARDA A JUYA MIN NOVEL ZUWA AUDIO BA IZINI BA

*_Albishir! Albishir!! Albishir!!!_*


*_Jama'ar Annabi inayi muku Albishir da cewa nakawo muku wannan shahararre Kuma
ingantaccen gida, gidan da suka darje suka rairaye suke kawo Muku kayiyyaki masu
dankaren kyau da Kuma inganci abisa farashi dai dai da Aljihun ku_*
*_Hajiyata, kanwata, Aunty na, kinaso kisamu kaya Wadanda ba kamarasu? Kayanda
idan kika shirya kika fito kizama abin kallo a wurin Yan uwanki?_*
*_dama wadanda zasu ganki ahanya?_*
*_sbd yadda Zaki fita daban da saura?_*
*_Kinaso Idan kikayi shiri arinka tambayanki a ina kika saye wannan kayan?_*
*_Zakije gidan biki ko gidan suna Amma kina tunanin kayan dazaki saka saboda kiyi
fita ta Alfarma ta kece raini?_*

```ARZUQLANA GALLERY```
*_sunkawo muku duk Wani abu Wanda zakuna bukata kama daga:_*
```Laces
Atampha
Shadda
Abayas
Materials
Gyale
Takalma
Jaka
Kayan Kitchen
Bangles n jewelries```
*And many more*

```GIDAN KYAU, GIDAN QUALITY, GIDAN SAUKI, GIDAN KWALISA, DA ADO```

*_Wani abin sedai kunbiyomu zaku Gani da idanunku_*

*_sunayin kasuwancinsu bisa gaskia da Amana, ba cuta ba cutarwa_*

*_koda bakida kudin Siya Muna gayyatarki dan ki tallata kema kisamu naki_*

*_Yar uwa kasance a gidan, da abaki labari gwanda ki bayar_*


https://chat.whatsapp.com/FRJAnQZXm0t7rAroZWlMnQ

Spark suna zaune Yana faman Jin me Jamilu ke fada Yana ta Shan zagi a wajen
Jamilu shi da Mummy, katseta yayi yace yanzu ka samo min me aikin? Naila tace gani
wai zanyi indai zaka biyani,Kai ba karfi ba kace zaka yi,Ae zanyi haka Ina so,yace
ba damuwa,Naila tace bari na tafi dare zaiyi,ka zauna a nan mana zan biya Maka
kudin kwana mu zauna tare nima na huta zaman shuru,Naila tace a'a tafiya zanyi,Baki
ya tabe tare da furta alright you can go,Naila tace aha sai da safe,ko kula Jamilu
baiyi ba ya mike Yana taku dai dai ya shige bedroom dinsa,Naila ta juya ta fice.

Tana fita taga kartai sun hargitsa gidan suna ta fada ana kokarin rabasu,tsoro
taji ta juyo da gudu tana haki ta shiga dukan kofar Spark kamar zata balleta domin
shi ya sa key,wanka yake yi amma ihun Jamilu yaji Yana cewa abude wayyo,da sauri ya
daura towel Dan guntu jikinsa duk kumfa ya bude kofar,ta fado ciki tana haki zata
yi kuka tace fada akeyi saura kadan jifan dutse ya fasa min Ido,murmushi ya saki
tare da furta shine Kuma abin kuka ko kunya baka ji sai kace mace yaja tsaki tare
shigewa toilet abinsa,sai bayan ya gama wankansa sannan ya fito,jikinsa Naila ta
saci kallonsa a ranta ta furta wow idonta ta dauke a kansa kar ya kamata taga bai
son kallo, gashinsa yake gogewa da Karamin towel,Naila sai faman kallonsa take ta
saki baki,kamar wata wawiya, Juyowa ya sake yi da sauri tayi kasa da kanta ta koma
kallon kafafunsa masu kyau farare sanye cikin takalma slifas, gashinsa ya busar ya
fara taje shi,Naila taga duk su lotion dinsa masu tsada da sauri ta Kalli skin
dinta ita, tace shi yasa ni bana shining Dan hasken nawa ma sai guduwa yake,wai ni
ya haka ne ai kuwa bai isa ba wlh duk da ya fini haske sai na kamo shi.

Juyowa yayi haka kawai yaji shi Sam a mace yake kallon Jamilu ya rasa dalili
magana yayi a gadarance yace koma Palo zan shirya,Jamilu yayi murmushi Yana kallon
Spark yace Ina namiji me zan gani a jikinka,ni ko towel dinka ka cire ba ruwana ba
abinda zan Gani abinda kake dashi nima Ina da shi, Spark yace Allah? tace sosai
fa,yace to a Kalli juna wallahi na yarda ka tube wandonka ni ma zan cire towel din,
Naila a ranta tace wannan fa ya uzura min tsakani da Allah kar ya gane ni,a fili
tace sai kace wasu yara,wato na ganeka so kake yi muyi wasan bayan murfin kofa na
yara to bazan yi ba na girma ni,idan mace kake bukata ka San ya zaka yi ka samu
wata ta bude Maka Garejinta ka shiga amma ni namiji ne,me yasa kuke zargin macece
ni ta ya zan shugo Nan ba a gane ba Kuma,to a wajen Yan sanda ma daga ni sai
gajeren wando da singlet,Inama kasan Mummy da nace ka tambayeta kaji ai ita ta
ganni a haka,Spark yace na yarda to ka fiye surutu Kuma ka daina kallona.

Naila da sauri ta dauke kanta amma ta manta ta sake sakin baki tana kallon
kyakyawar surar Spark, ta wani bude baki ta sake shi,a haka ya fara shafa mai Yana
Juyowa again ya kama Jamilu,da sauri Naila ta mike zumbur tace na tafi,ko magana
baiyi ba Yana jinta ta bude kofa ta fice, a tsorace take tafiya tana addua a
bakinta har ta fada dakinsu Inda ta samu malaman sun fara bacci ma,tace an gaji da
tilawar kenan,tazo ta kwanta tare da jawo sabuwar wayarta ta kunna tana Gani ta
hadu a fili tace wannan tafi karfina kyan wayar Nan Yaya Mohsin wlh shine Dan gayu
ni Ina gidan yari wa zan birge da waya Ina cikin wahala ai gara na rike Yar
karamata burin kwaila, ta jona abarta a charge ta cika full sannan ta zare ta Maida
cikin kwalin ta ajiye tace sai sunzo ziyara na bashi ita.

Bangaren mata a gidan yari Beauty kwance take a Saman gadonta tana ta faman
tunanin Jamilu tana matukar kaunar Jamilu,Surarsa take kissimawa a ranta kawai ta
hango Jamilu wani kyakyawan matashi hadadde me dauke da faffadan kirji, damatsansa
wasu manya alamar Yana Gym,murmushi ta saki cike da shauki ta juya a Saman bed din
tare da rungume wata teddy dinta da Maminsu ta kawo mata, ta sake juyawa tayi mika
tare da sake kankame pillow tace wato Allah haka yake ikonsa idan yaga dama ba Inda
bazai hadaka da mijinka ba,gashi nan shima sharri aka Masa kamar yanda nima haka
bari Daddyna ya fitar dani wlh sai na fitar da Jamilu ko arzikin Daddy zai kare
muje muyi auren mu,wayyoooo jamiluna ta fara Shure Shure a Saman pillow tace yanda
nake Allah ya bani kyau na ba laifi, gani da haske na, chass dani,nasan sai na
birge Jamiluna.
Sake hango damatsan Jamilu tayi a ranta Yana taku ingarman namiji take ta
hangowa,wani irin zaratan Maza,ranar haka Beauty ta kwana tana faman nazari akan
Jamilu masoyinta, Garzali kuwa a daren har Istihara yayi ko zai samu a nuna masa a
mafarkin ko Jamilu mace ne amma sai ya hango Jamilu da katon Hajiya Babba,a firgice
ya farka Yana neman tsari da wannan mafarkin shi Kam,yace inshaallah ba haka bane
idan kuwa hakane to Jamilu mata Maza ne,haka ya koma ya kwanta.

Washe gari da asuba Naila suna tafiya masallaci tayi sauri ta tashi tare da
yin alwala tayi sallarta tayi addua sosai Allah ya rufa mata asiri kar a
ganeta,tace naga makiya sun fara sa Ido a kaina,tana cire Hijab din Malam Sharu
Yana shugowa saura kadan ya kamata Allah ya kiyaye amma yaga kamar ta zare abu daga
kanta, gashi da sauran duhu da sauri ta daga bargonta ta jefa a kasa ya kunna haske
da sauri yaga ba komai ya kalleta sosai Naila ta daga hannu haka tana addua,Malam
Sharu yace wai Kai Jamilu wanne addini kake yi? ayi mutum baya zuwa jam'i,Naila
tace ban yarda da limamin ba bazan taba bin kowa sallah ba a gidan Nan duk babu na
gari bare a bishi sallah,kowa shegen kansa ne mummunan Abu ya aikata aka kawo shi
akan me zanbi mutum sallah, bazan bi kowa ba,ban yarda da Imanin kowa ba a gidan
Nan, tawa Sallar nake yi.

Malam Sharu yace Allah ya shiryeka ka gane jam'i ba abin wasa bane,Naila tace
Ameen shi yasa ni ka ganni PHD ne dani wajen minding business dina,kaga shi yasa
akace babu kyau shiga abinda ba ruwanka kasan irin hujja ta ne? Ina da hujja me
tsauri amma mutane baku San wane mutum ba ko me yake Shirin yi sai ku dinga shiga
lamarinsa,ko ka manta hadisin ne Yana daga kyan musulunci ka bar abinda ba
ruwanka,to mu a arewa yanzu kowa nunawa yake yafi kowa ilimi,hankali,da wayewa,kowa
yayi addininsa Malam Sharu nima addina nake yi ba ruwanku.

Malam Sharu yace mu dai gaskiya ce sai mun fada ko za a sa kanmu gabas a fille
sai mun jawo aya da hadisin idan mutum bai dauka ba ruwansa,Naila tayi murmushi
Allah ya bada sa'a, Kuma Ina tabbatar muku watarana sai kunji kunya,Kun sa min
Ido,Kun San dalilina a dakin nan? Yace sai ka fada,Naila tace wani Assignment nake
amsawa Ina gamawa zaku ga dalilin,Allah ya kaimu Jamilu cewar Malam Sharu.
Baccinta ta koma ta barsu sai wurin 11 ta tashi ko makarantar gidan yari Naila
bata taba zuwa ba amma Spark shi Kuma Yana zuwa duka boko da ta addini,sai da tayi
wanka ta shirya duk a cikin toilet sannanta fito da kayan data cire,tace ga zafi ga
manyan kaya Ina fama wlh,ta wuce bangaren Spark masu tsaron wajen suka ce ya tafi
makaranta,Naila ta dinga mamaki ta nufi makarantar, tun kafin ta karasa ta hango
gashin kansa Yana sheki,dariya ta kamata tace dole kanwar naki shegiya wuya ta sake
shekewa da dariya,Juyowa Spark yayi kenan ya hango Jamilu a window Yana ta faman
Masa dariya,suna hada Ido tace ajeboooo.....ajeboota an koma yaki da jahilci sai
dariya....dariya ma ta bawa Spark yace yaron nan ya takura min a rayuwa.

Ball taje ta karbo tace ba wata makaranta da zanyi wai shi irin yasan darajar
ilimi to ai ba Wanda ya isa ya min dole sabo da haka ni ball zanyi,harda daga Masa
ball din ya gani,tayi gaba filin wasan sai da yamma yawanci ake yin ball ita kadai
a fili tana ta wasanta da ball bata iya komai ba,Spark ko gama lecture bai bari
anyi ba ya fito ya taho wajen Jamilu,a hankali yake tafiya ana wani gayu ana
basarwa hannu daya a aljihu anci kana nan kaya tracksuits ne a jikinsa rigar me
hula a baya, bakake da ratsin fari,kafarsa sanye da Sneakers,Naila tace shegu kudi
ko a Ina suke basa buya wa zai ce shi a gidan yari yake,ji yanda ma duk Yan
bangaren da suke a VIP din nan sai kyau suke da kiba to zasu ci abinda suke so
gashi basu fita ko Ina uhmm.

Karasowa yayi Inda Jamilu ke ball dinsa shi kadai,hannayensa duka ya zuba a
aljihu yace saka muyi,Jamilu ya jefa ball suka fara Yana ta zubawa Jamilu yanka da
oc ta ko Ina bai iya komai ba,sai dariya take tana so ta kwace ball din sai faman
yanke Jamilu yake hannayensa ma a aljihu sai yanzu ya cire hannayen,Naila sai taro
shi takeyi kar ya wuce da ball ya cinyeta, zuwa tayi tasa kafa a Jikin tasa kafar
zata kwace kwallon ai sai ta Fadi tim a kasa,Jamilu ba karfi ko na anini,dariya
yayi yace ka dinga sakin jiki haka wai ko yaro ne indai namiji ne ai Yana da karfi
duk da Kai yaro ne,Naila sai tayi halin matan na son girma tace wlh a'a da kadan ka
girmeni tab, Spark ya kalleta yace anya Jamilu anya kuwa,Mene? ta furta tana
dariya, zo na taba kirjinka Jamilu,Naila ta hade rai tace idan gay kake yi ka Fadi
gaskiya malam, kyale zancen yayi yace a ransa sai na taba kirjin Jamilu dole wlh,
suka ci gaba da ball dinsu, Naila sai faduwa take ana zuba mata yanka, taci sa'a ta
kwaci ball amma Bata yi komai ba ya kwace tace wlh ban yarda ba ya kamata a kawo
rapefree,yace to a samo.

Goje ne yazo wucewa Naila tace Goje yawwa tsaya ka zama alkalin wasannan idan
anyi mugunta ka busa please,Goje ba usur ba komai yace ai na Saba da fito wajen
kiran karena sanda Ina gida ku fara,suka fara har su Naila suka samu Yan kallo a
wajen da yawa suka tsaya suna kallon Jamilu domin shike kawo su wajen, Spark Dan
girman Kai ne baya harkar kowa.

Goje ya shiga da gajeren wandonsa da singleti ya saka kwallo a tsakiya sannan


yayi fito da baki yace ku fara,Spark ya cillawa Naila ball ta fara tafiya yazo ya
kwace Yana rabarta ta zube a kasa ta Fadi wai ya bigeta,alkalin wasa ya busa fiiit
aka mikawa Naila ball ta buga wai an bugata da kasa, ta bugo kwallo Spark yaje ya
kwace ta bishi zata kwace ya dinga yanketa Yana wasan kura da Naila Jamilu a filin,
ta gaji ta manta ta rungumo kugunsa ta rike shi Kam Kam tana haki, Spark kamar
gunki haka yayi poster ga Goje Yana ta busa anyi rike amma basa jinsa sai faman
fito yake bakinsa har ya gaji,Yana zuwa ya dagawa Naila hannu yace an baki red
card, sai lokacin suka dawo hayyacinsu ta sake shi da sauri tana dariya cikin hakki
tace to kana gani zai kashe ni da gudu,Red card aka baki ki fita.

Akwai Wanda suke kira da Muler ya shugo yace shi suyi da Spark yace to,suka fara
ball da Spark da Muler,Muler mugun kwaro ne a ball har ya fi ma Spark iyawa,Naila
tana waje tsaiwa ta gagareta ma sabo da gajiya sai zama tayi a kujerar Yan kallo
tana hutawa, mazan suna ta zuwa karshe ma shiga suka yi da yawa aka raba kwallo,
harda Spark ko wanne gida da Goal keeper, suna ta yi Naila tana ta kallo tana
nishadinta ganin yanda Spark yake kokari a ciki,ya iya ball sosai,sai da suka
kwashe kusan 2hrs sannan Spark ya fito a gajiye ya barsu suna yi wani ya shiga a
madadinsa,Naila da su Scoler Yan Daudu sun taru suna ta kallo su a dole mata
ne,Scoler yace Ina zan iya hada jiki da Maza su balla ni Ina zaune cikin rufin
asiri,wani labaran yace Kai Jamilu ka Mori saurayi Kalli yanda yake tafiya Inama
nice,Naila tace gata sunanta Spark ai Yar budurwar tayi tsaya ma kuga ta karaso,
Scoler harda fifita da hannunsa yace Dan Allah ya jikin Spark din Yana sparking
kuwa ahhhh ahayye ke Kam Jamilu kin caba ga farin jini ,ni dai gaskiya kinci amanta
,Jamilu ya Kalli Scoler yace ai kasan so shi tsuntsu ne tashi yake daga kan wannan
ya koma kan wannan,Labaran ya furta ai ni bana bakin ciki Kun dace tunda ban sameka
ba Jamilu to uban kowa ya rasa,Tantiriya ta mike tace mun tafi Shan shayi ni da
Baby Spark,Spark ya jita ya daure fuska ya tsani Dandaudu a duniya,ta bi bayan
Spark suka tafi,Spark shi tunda ta rungumo kugunsa abinda yake ji a jikinsa game da
Jamilu ya tashi hankalinsa, Sam tunani yake sosai akan abin Nan, me yasa wai ko ya
suka hada jiki sai yaji shock,tsaki ya ja yana tafiya ya juyo ya Kalli Jamilu yace
a Ina ake soya kwai? Jamilu yace kawo a siyo Maka,kudi ya zaro dubu daya yace guda
biyu za a soya sai tea,Ina da bread,Naila tace to ni uku za a soya min Kai biyu tea
cup biyu,yace karka sake ka kawo min a bude,Jamilu yace an gama ta juya ta tafi
tace banza ta Fadi,ta tafi wajen masu siyen tea Maza ne dankam suna ta Shan tea,
can ta iske DanIndo tace ya man how far,Yace a dey woo da wata katuwar
muryarsa,flask Dinka dayan nan zaka bani,Dan Indo ya kurbe ragowar shayinsa yace
let's go, suka tafi taje ta karbo shi, sabo Dan karami da shi me kyau,Dan Indo shi
Yan dabarsu da basu fada gidan yari ba suke kawo Masa duk abinda yake so,yanzu zai
sa a gama da mutum Yana daga gidan yari,Kuma manya har kiransa suke Yana gidan yari
Yana bawa yaransa na gida umarni ana zaluntar bayin Allah, su kashe duk Wanda suka
ga dama,kullum cikin Kwangila yake iri iri da shugo da miyagun kwayoyi, Naila Allah
ya dorata a kansa,Yana ji da ita,yayi yayi ta bashi dama yasa a kwato mata hakkinta
taki tace sai ta fita tukun, ta karba ta sake dauraye flask din sannan ta siyo
shayin ya Sha hadi sosai,aka soya musu kwai ita uku shi Kuma biyu, harda siyo wata
butter ta leda ta karasa kashe kudin duka.

Tana dawowa ta shiga sai taga wannan karon ba a hanata shiga ba,samunsa tayi
yayi wanka ya canja kaya,ya Kalli Jamilu yace kayi wanka,Jamilu bai San tarko ya
hada Masa ba so yake ya ganshi ko ba namiji bane,sai ta shiga toilet dinsa tsaf da
ita,ta saka key sannan ta tube tayi wanka,Bata zo da seletape da bandage ba bare ta
mamme boobs dinta sai ta tsallake boobs din tayi,bata zubawa bandage din ruwa ba
kar ya lalace ya cire tunda tayi wanka da safe,kayanta ta karkade ta mayar ta
shirya sosai ta fito,Yana jira yaga ya fito daure da towel sai yaga ya fito da
shirinsa yanda ya shiga sai dai ga alama yayi wankan,yace ga lotion dina ka tube
kayan ka shafa mai,yace a'a zafi bana shafa mai ni da zafi, Spark yace hmmm a ransa
yace zan Tara a gaba dole da sai na ganka Jamilu,a fili Kuma ya jawo flask yaga ta
hado da wani Dan cup Wanda kana Sha zaka jefar, na take away ne in mutum na so ana
basu idan ka siya tea.

Ya zuba tea din ya Dandana yace not bad amma a dakko Madara a Kara wannan
gidan rayuwa cikinsa sai da Madara,Naila ta dakko peak da aka kawo Masa aka rasa da
me za a fasa sai wajen me shayi ta koma aka fasa mata ta dawo suka sake tsulawa a
shayinsu itama ta zuba Nata,ta dakko bread kamar nata me dadi ta saka kwai a
tsakiya tana yaga tana kora ruwan tea,kallonta yayi shima ya fara cin nasa,tace wai
mu Maza me yasa muke da Yaudara ne? Spark yace Gender dinmu ce haka,ta cika baki da
kwai da bread tace uhmmm? Yace yeah,tace kune dai masu Yaudara, ai da ganinka zaka
yi Yaudara ba kadan ba Spark,mata nawa ka cinyewa Bado? dariya yayi ba shiri yace
da ace nasan mata ai ta Katanga zan dinga haurawa part din Mata na zama kwarto a
gidan Nan,dariya tayi ta sake kurbar tea tace nufinka Kai virgin ne? original ma
kuwa,Naila tace kaji tsoron Allah fa,yace da gaske ai ni da ace nasan mace to
Beauty zaka bani kawai naje can, yanzu sai ka haura? Ina nan zan sa a kawo min ita
ba Wanda ya sani ma.

Naila tace lallai da kuwa kaga namijin kishi,ya Yagi bread and egg Yana cin nasa
a wani gayence yace egg din ma ba dadi,tace to kawo ta dauke ledar kwai tare da
furta do you think i will beg you to eat? So you can't beg me to eat?ya tambaya,
tace yeah,Spark yace ai naga baka da Imani ko kadan ya kwace ledar Kwansa yaci gaba
da ci har suka gama ya wanke hannunsa da sabulu tare da kuskure bakinsa,Jamilu ma
haka,yace sai me aikin nawa,Jamilu yace gani,yace Start to ya koma kujera ya kwanta
Yana kallo Yana danna wayarsa

Naila sai da ta fita ta samo tsintsiya ta siyo harda mopper duk gasu Nan ana
siyarwa,ya bata kudi again ta siyo bokiti dasu plate da spoon da duk wasu tarkace
na bukata amma sai shegiyar tsada dake a gidan yari ne, tazo ta fara shara Yana
binta da kallo komai irin na mace, shi kansa daurewa yake yi gaba daya bai taba
ganin namiji haka ba ko mata Maza ne kuwa,Jamilu Yana ta aikinsa sai da ya gyara ko
Ina neat har toilet ya wanke Kal Kal,Naila a ranta tace ko a gida bana aiki Ashe
dai na iya gashi Ina bautar kato,naki yiwa uwata da ubana nazo Ina yi a banza.

Tana gamawa ta tattaro kayansa kala hudu duk ya cire ta shiga toilet taci
ubansu da wanki sabo da tasan tsaftarsa da iyayi amma duk da haka ta fito zata
shanya yace kawo na gani,ya duba kayan kafar wando da su aljihu ya kare musu kallo
yace basu fita ba a sake,Naila ta gaji Dan ma kana nan kaya ne haka ta koma ta sake
wankewa,ta fito yace Jamilu da ka Dan sake wankewa Banga sunyi haske sosai ba,Naila
tace ni baiwarka ce wlh bazan sake ba ta fice ta shanya ta leko tace idan kaga dama
ka saka idan baka dama ba ka barshi ta juya tayi ficewarta, Spark ya jinjina Kai
yace ba komai gidan yari ce ta jawo min shi yasa yake ganin ni sa'ansa ne yaron da
baifi na dauke shi ya zama cleaner dina ba,rayuwa kenan, shi Spark a dole anci Masa
mutunci,yace kwana nan zan daina dariya ya daina ganin hakorina,ya dinga jinjina
maganar yanda Jamilu ya wani zazzaro Masa Ido Yana Masa fitsara,ya nuna kansa yace
niii...hmmmm ba komai.

Beauty tun jiya take so taji Muryar Jamilu amma shuru,duk ta damu kanta ga
number waya ta bashi yaki kira,Naila kuwa Yar kwakwurar wayarta ta sa ta kira
Beauty Wanda ita ta zaci wayar da tasa babanta ya bawa Jamilu ne,bayan sun gaisa
tace to ya kaji wayar? Jamilu yace wani dadi idan Ina shafa Saman screen sai naji
suwal suwal gaskiya wayar ta hadu na zama babban yaro,kinji yanda nake Jin muryarki
kuwa clear wani so smooth,sai naji zuciyata tace aaa...aff idan muryarki ta daki
dodon kunnena, Beauty harda dariyar farin ciki tace daga Jin muryarka my love nasan
Kaci kaji jiya anzo Maka da kaji ko daga gida? Naila tace harda ragadada, Beauty
tace sai watarana zan baka labarina, Tantiriya tace karki damu nima zan Baki nawa,
to ya soyayyata? Beauty tace tana kashe Murya da yanga ta furta tana nan mana sai
karuwa ma da take kullum, percentage nawa? ta kusa cikewa 100, Tantiriya tace har
naji dadi kin san Ina sonki da yawa,Gashi baki taba ganina ba,Beauty tace duk a
suffar da na ganka zan iya aurenka ko kuturu ne, Tantiriya tace da yatsuna ma
kwantar da hankalinki,in kika ganni zaki ji dadi fa,Beauty tace muyi Whatsapp mana
sai naga pics dinka,Naila Ido ta zaro tace yanzu Ina da wani uzuri ki bari zan miki
magana,Beauty ta furta angama ogana my man.

Watace tazo wajen Beauty ana kiranta da chikar gayu, yarinya ce matashiya
domin su Naila sun girmeta baza ta wuce 18yrs ba, ita ba fara ba Kuma baza ace baka
bace amma tana da kyau matukar gaske,dumimi da ita da gudu ta shigo ta daki Beauty
a gadon baya ta fice da gudu,Beauty bayan ta kashe wayarta ta mike ta biyo Chikar
gayu da gudu,wata dattijuwa ce me kudin gaske wacce ita ba a block din Yan daurin
rai da rai take ba,shekaru biyar aka yanke mata saura baifi wata biyu ba wa'adinta
ya cika ta bar gidan gaba daya,Itama a VIP take me kudin gaske ce ita Chikar gayu
ce Yar aikinta ta zama kamar yarta,Bata Jin magana tsokana ce da ita tun Yan gidan
suna dukanta har sun daina ma.
Dattijuwar me suna Hajiya Kaltume itace ta rike Beauty tace dan Allah kyale min
yarinya bakya ganin ita yarinya ce kin bata shekaru biyu haba Beauty tamu,Beauty
tace wlh Dan Ina ganin girmanki ne Hajiya ba komai na kyaleta,tace na gode Queen of
Beauties,Beauty taji dadi tace Allah Hajiya na Kai queen? tace ae mana,Zan iya
birge mijina? Hajiya tace sosai ma ai bazai iya Kara miki kishiya ba,tace sunansa
Jamilu,Hajiya tace Nice name,Ina sonsa Yana Sona,jiya ma da ban ji muryarsa ba sai
da nayi kuka,Hajiya ta zaro ido tace kibi soyayya a hankali Yar Nan,Beauty tace ni
wlh bazan bita a hankali ba akan Jamilu sai dai a mutu,Hajiya tayi dariyar manya
tace uhm uhm fa Beauty kar muzo muga ana tsinewa Jamilu muga ana rusa kuka,Beauty
tayi dariya tace Allah ya tsareni da zagin Jamilu har abada,wallahi da zanga
malamai ma sai nasa sun mana addua Allah ya Kara mana dankon soyayya da Jamilu.

Hajiya tace lallai kinyi nisa baki San iskancin soyayya ba idan ta tashi
maganinki,Beauty tace ki mana addua kawai Hajiya amma idan Allah yasa muka fita
daga gidan yari zamuyi aure Jamilu zaiga soyayya a karuwata zan shiga gidan mijina
ba kunya ba komai sai abinda Jamilu ke so,Hajiya tace Allah ya nuna mana tace
Ameen,kina Jin labarin nayi aure idan kika ganni Hajiya kawai ki kirani da Karuwa,
ai zansa Daddyna ya bibiyar min hakkin Jamilu shima sharri aka Masa, Daddyna me
kudi ne Kuma Kinga Yana da kafa gashi Senator ne har sau uku yayi senator yayi
minister na tsaro da wasu mukamai duk ya rike,Hajiya tace mashaallah,Beauty tace
Babana Yana da Dabban kudi,wani jahilin kudi ne dashi,Hajiya mutuniyar kirki tace
mashaallah Allah ya Ida nufi.

Ameen cewar Beauty,Chikar gayu ce tazo ta wuce da littafanta zata je


Islamiyya,Beauty tace zan kamaki a school ne yanzu zanzo nima,Chikar gayu tace wooo
ta zaro harshe ta Kara gaba,Bangaren mata ma haka yake gasu nan ba kalar da babu
manya da yara,ga Yan iska Nan tatattun gaske da Wanda kaddara ta kawo su,iya shege
kala kala wani bangaren ma kida suke ji a Bluetooth speaker suna ta faman tikar
rawa ta fitsara,duk a nan su Beauty suma suka sake wayewa idonsu ya bude suka zama
basu da kunya basa shayin uban kowa.

Makaranta Beauty taje ta samu Yan mata suna girgiza wai ana gasar girgiza Boobs
aga wace tafi iyawa sai shewa suke a class,Malama bata shugo ba a Islamiyya suke
wannan iskancin,Chikar gayu da nata ko girman kirki babu amma tafi kowa zakewa
kamar zata cire Kafadunta, Beauty tana zuwa ta ajiye Jakarta ta shiga ciki tace ga
rawar Jamilu,haka zan na masa a Palo idan munyi aure,guda suka saki da shewa ana
dariya,Chikar gayu tace saura luwaluwai muga wace gwana anji Beauty ta lashe gasar,
Nan ma suka fara har malama tazo suna ta fama sai da ta musu magana sannan suka San
tazo ma.

Abban su Mohsin Yana bencinsa a zaune Yana ciniki sai ga wata bazawara ana ce
mata Zainab Kai zaka rantse Bata taba aure ba ta dau wankan yan birni tana taku dai
dai,tunda ta taho yake kallonta sai kace Dan iska, Zainab tana zuwa yace Zainabu
Abu me tagwayen suna Allah ya kawo miji na gari ko da kuwa nine,Zainab tayi dariya
dama har gulmarsa suke a layin yanda yake Mayen mata ba uwar da ya iya sai son
mata,tace kayan Miya za a bani,Abba Yana washe baki yace kice yau dadi za a ci naga
gidanku kunfi dafa shinkafa da wake,Zainab a ranta tace kaji mutum marar mutunci ya
fada min magana a wayance,a fili tace ae a zuba min na Dari biyar, ai kuwa ya dinga
antaya mata kayan Miya Yana kallonta ba ledar yake kallo bama Zainab din yake kallo
Yana ta faman zubawa ya bata yafi na dubu daya,hannunsa sai rawa yake karrrrr
karrrr, Zainab ta karbe kayan Miya,yace cucumber fa ga salat ai girkin zaifi dadin
ci,tace kudina sun Kare,hannu na rawa yace ai sai a baki ko kyauta ne zo ki karba
haba kamarki ai sai da kayan lambu, ya dakko hannu na rawa zai zuba a leda sai ga
Umma ashe tana labe tana kallonsa ta cikin gida ta fito fit....

Tana masifa tace to namamajo ke zo Dan uban uwarki ta fisgo Zainab ta juye kayan
miyar tana masifa tace Yan iska barayin banza,wallahi Allah na kallonku a haka ku
bude Baki Kuna zagin gomnati barayi barayi bayan duk gaku nan barayine kowa ya samu
dama sai sata Yar iska me hanci kamar gurji,zaki ci cucumber ai hancinki ne
cucumber din,wato Kinga banza ta Fadi,Umma ta gyara mayafinta ta zuba mata na dari
biyar dinta, tace ungo jeki idan kin fasa Kuma a baki kudinki ki tafi wani
wajen,Zainab karba tayi sum sum ta wuce tana cewa nifa ba ni nace ya bani
ba,wallahi zan jawoki na miki mugun duka na karyaki na karya banza,Zainab ta tafi
kawai,Abba ya sadda Kai kasa Yayi mukus,Umma ta Harare shi tace Kai Kuma la'anarka
a mata take ko? baka da aiki sai son mata,a haka kamar Dolo ashe wayonka a mata
yake, hannun Abba taja suka shiga cikin gida,duk masifar Umma bata yiwa Abba a
gaban mutane sai dai watarana a gaban yaransa take cin ubansa,tace haba Hashimu ai
dama ni tunda aka kaini gidanka a matsayin amarya naga kasan hanya fes kabita babu
gargada nace da wata a kasa,watana biyu a gidanka na samu ciki ana zuwa ganin
amarya na fara amai ashe har ka jefa kwallo daya,to billahillazi baza ka ebo min
cuta ba,baza ka jona min kanjamau ba,idan aure zaka yi kayi kawai ni ban hanaka ba,
Allah ne yace ku Kara,tunda mace daya ta Maka kadan ka Kara yafi min kwanciyar
hakali.

Abba anyi mukus da kyar yace ni ba aure zan Kara ba,Umma tace na fahimceka fa
Hashimu mace daya ta Maka kadan,Ina da lalura watarana baka iya hakuri....Hidaya
ce ta shugo gidan da markade ta dakko ta tsaya Jin me su Umma suke,Umma tace bar
nan Dan kutmar....ta dura mata ashar, ba shiri ta ajiye markaden ta fice runfar
Abba taci gaba da sallamar mutane.

Umma tace abinda kake yi yaranka kake zubarwa da mutunci a unguwa sai gulmarka
akeyi Kai ko kunya baka ji,na baka dama idan kaga wacce tayi Maka ka fada min Danka
zai Maka auren duk abinda ake kashewa zai kashe Maka bazan hanashi yayi komai ba,
ai Kai ubansa ne mahaifi,ni bani da bakin kishin da za ace na haukace akansa,Ina
sonka dole zanyi kishi ba macen dake son kishiya a duniya amma ni da wannan halin
naka gwara ka Kara auren tunda ai da a baya ba ruwanka da mata ko kulasu baka
yi,yanzu kuwa ka gaza hakuri,Abba Yana kallon Umma har ta gama kamar zaiyi kuka
yace Allah na gode Maka daka bani mace ta gari, na gode ya rungume Umma yace kin
yarda nayi auren? Alhmdllh yau ku rufe gida a masallaci zan kwana Ina Sallar dare.

Umma a nan ta saki baki dama fada tayi bai Kai zuci ba ta zaci bazai iya ba zaiji
tsoronta, tace wallahi karya nake ban yarda ba Hashimu,baza ka Kara aure ba na
isheka ni kadai,
Hashimu yace maganar farko ita sarki yake karba wallahi an karba,ni baki isheni
ba,ga kullum masifa masifa kice bana miki komai,kiji tsoron Allah Umman Mohsin ni
aurena zanyi,Umma salati ta saki tace na shiga uku Hashimu daga wasa wallahi ni
wasa nake,Kuma indai akan masifa ne na daina yi Maka daga yau zan gyara
Halayena,Hashimu yace ki gyara din ai Yana da kyau auren ma ai sunna ce me
kyau,Umma sai kuka sosai,Hashimu yace kiyi hakuri kici gaba da neman warin sigari
kina shaka kafin ki samu lafiya,Umma ta saki kururuwa tace wallahi Hashimu butulu
ne Kai,Hashimu yayi mukus kamar Dan Dolo ya fice abinsa wajen sana'a,daga ranar
Kuma ya daina kallon mata shi a dole aure zaiyi bayan ko bazawarar babu ma,duk
arahar kayan miyar ya daina wai zai samu dahir mene zai dinga batawa kansa lokaci
Yana kallon banzaye a waje.

Harira tazo wajen zata Masa wayo Abba ko kallonta baiyi ba,Harira tace Hashimu
Allah bar mana Kai,yace ko kiyi addua ko kar kiyi idan Allah yaga dama zai barni
mana,Kuma watarana dole zan mutu,na nawa zaki siya ya furta ba mutunci,Harira tace
ta dubu uku,Hashimu ya millira mata uwar tsada ta dinga mamaki haka ta bar wajen ba
fuska,Umma Kuma kwana biyu sai kuka sai bacin rai,gashi shuru Mohsin bai zo ba,yau
Allah ya kawo shi da yamma,Yana zuwa Umma ta mike daga Inda take zaune tana gyara
wake tace muje ciki,Shi dai Mohsin ya ganta duk ba sukuni tayi yagai yagai da
ita,yace Umma lafiya dai? Umma tace hmm Dan nan Abbanku dai aure zai kara,Mohsin
Dake namiji ne ko a jikinsa Maza ba ruwansu da kishiya,yace Umma shine duk kika
damu haka na zaci wani abin ne ma,wacce zai aura? Umma tace shi yasan wacece ni dai
yace har yanzu bai samu ba tukun amma tunda ya furta ai sai ya samota,to Umma a
kanki zata zauna tazo ta zauna mana halin Abba ma kadai ya koreta.

Umma tace baza ka gane ba Mohsin wata macen da niyyar sharri take shugowa burin
Matan yanzu idan an auro su kawai su Kori uwar gida ko su jefa mutum a masifa,wata
bin malamai tazo ta hanamu sukuni wata babu mutunci a harkarta,wani auren idan anyi
ya zama sanadin fitarka daga gidan miji kenan shi yasa kaga bama son kishiya,Kuma
dai kishi halak ne,Mohsin yace to kiyi hakuri inshaallah ba abinda zai faru Allah
yasa haka shine Mafi alkhairi,Umma tace hmmm dama nasan baza ku goya min baya
ba,Mohsin yace Umma gwara tun wuri mu hadu a samowa Abba ta kirki wacce zaku zauna
lafiya shike nan kawai,Umma tace a'a bana son ta kirki nafi son wacce zata buwaye
shi ya saketa,Mohsin yace tab kin san Abba ba wani iya saki da zaiyi Umma nidai ga
shawara nan,tazo a samo Yar banza tayi ta gana miki azaba Kuma ya kasa sakinta ai
gwara ta kirki,Umma tace to shike nan,Mohsin yace a makwaftana akwai wata Fatima
mijinta ne ya mutu yaranta biyar amma duk suna can Kaduna dangin ubansu sun karbe
yaran ita kadai ce,tana da kirki da hankali a hadasu da Abba kawai,Umma tace babu
wata ta kirki a kishiya Malam kawai kace ka hada baki da ubanka Kun munafunceni ta
saki kuka.

Mohsin yace kefa kika shawarce ni ban san zancen ba wlh,tashi ka bani
waje,Mohsin ya Mike cikin shigarsa ta kana nan kaya masu kyau yayi kyau ya
fice,babu me kallon Mohsin yace Yana da aure ma,Yana fita Abba ya tare shi yace
Mohsin kaji zan Kara aure ko? Mohsin yace ae yanda yaga Abbansa Yana ta murna ka
rantse an kawo amaryar ma,sai yaji tausayinsa yace Abba wace matar? Yace ku nake
jira dama mu taru muyi shawara a samo min ta kirki,Mohsin sai da yayi
kwalla,Abbansu Yana bashi tausayi matuka,yace to Abba ni na samo Maka Umma ta Santa
ma a makwafta na take, sunanta Fatima,Abba yace Fatima bintu,Batoola,Mohsin sai da
yayi murmushi,yace to ai da bazai raka ubansa zance ba,zanzo da abokina Malam
Isa,sai ka nuna mana gidan,to gobe kuzo da yamma zan sanar mata,yace to Allah ya
muku Albarka,Allah ya tsareka,Allah yasa ka a Aljanna Firdausi,ubangiji ya tsare
min Kai da dukkan yarana, Allah ya fito min da Nailanka,Sai lokacin Mohsin ya washe
baki anyiwa Naila Addua.

Abba yace Allah ya tsareka a duk Inda kake Allah ya doraka akan makiyanka,ya
tsareka duk wani sharrin masu sharri,Allah ya azurta min Kai,ka shahara kayi suna a
duniya Suna na kirki bana sharri ba,Mohsin yace Ameen ko ba komai ta wannan
bangaren Abba yafi Umma bai taba yiwa dansa baki ko ya Fadi wata mummunar kalma
akan yaransa, bai taba ba,Kuma indai kayi abin kirki yaji dadi sai yayi ta surfa
Maka addua ,shi fada da nasiha ne bai iya ba Sam,iya jaraba Kuma ba'a fada da shi
ko me zaka yi Masa,sai dai idan ka bashi haushi ya kauracewa mutum Kuma bazai gaba
da Kai ba,kowa ya sanshi Yana da baiwar da ba kowa ke da irinta ba,amma wasu basu
fahimta dolancin nasa kawai suke hangowa sun manta da cewa Allah baya halittar dolo
kowa ka gani da baiwarsa.

Tantiriya yau da dare babu abinci bata je wajen Spark ba,tana can wajen su Dan
Indo tana Jin hirarsu da suke duk hirarsu babu ta kirki sai ta shuka tsiya da Kuma
zuga wasu suna so su koyawa wasu wani mummunan ta'addancin, layin su Dan Indo kowa
ka gansu da shi to ya gawurta a kisan Kai,ko kidnapping da fashi da makami etc, su
kuwa Yan Daudu suma a bariki suka yi kisan Kai aka daure su, Dakinsu ta dawo ta
samu ana ta daukan karatu,zuwa tayi tare da gyara p-cap dinta ta zauna a gaban su
Malam Sharu tace nazo daukan karatun, Alhmdllh Alhmdllh Alhmdllh suka shiga
furtawa,Malam Jilani yace addua ta karbu Allah ya shirya Terror Allahu Akbar,haba
ai gwara kayi Ilimi ka rage iskanci.

Suka fara bude Qur'ani Naila tace daga baqara zan fara tilawa,ta nutsu tayi
Bismillah ta fara rera karatunta,duk cikinsu babu me iya karatun Jamilu ma,duk wani
harafi sai da ta bashi hakkinsa tana da basira ba kadan ba,duk suka tsaya suna Jin
Jamilu mamaki ya kamasu,abin ya daure musu Kai,gashi Kuma Muryar mata,Kuma Muryar
dama Dan Fulani suke ji,kowa yazo daukan karatu sai ya zauna Jin karatun Jamilu.

Spark Yana can ya gaji da jiran Jamilu Yana so yazo ya siyo Masa abinci amma
shuru,tsaki yaja ya fito sanye da 3qtr blue da riga armless fara hannayensa cikin
aljihunsa Yana tafiya Yana taku dai dai,da tambaya ya karaso dakinsu tun daga nesa
yake Jin kamar Muryar Jamilu Yana rera karatun Qur'ani me dadin gaske, ciki ya
shugo dauke da sallama,Jamilu Yana Jin Muryar Spark yace sadakallahul azim na gama,
Muryata tsaraici ce babu kyau haramun ne ehe tayi yanda Yan Daudu ke yi, Malam
Sharu suka dinga mamaki, Malam Sharu ya mika mata Hadisai yace Malam Jamilu
Bismillah,Naila tace sauri nake yi kasan fa nice Tantiriya budurwata tazo amma bari
nayi kadan,ta karanta ta fassara yanda kowa zai gane,ta karbi wani shima tayi daga
Nan tace Babyna yazo fa zamu tafi mu caskale.

Ido suka zaro, Malam Garzali ya furta an gama karatu Kuma anci gaba da Daudu
shiriya har yanzu bata zo,tace ku daina yankewa mutum hukunci kawai nayi karatun ne
Dan kusan ni ba jahili bane Ina da ilimi kawai a yanda na tsinci kaina to bazan yi
aiki da shi ba tukunna sai nan gaba,Malam Jilani yace Subhannallahi Allah ya
shiryeka wallahi mutuwa Bata jira,Naila tace ni kuwa nasan da haka tunda ko a
makwaftanmu anyi mutuwa,an harbi mutum da bindiga ya mutu a gabana a kauye, kaga
kuwa nasan zata zo Kaina watarana,Spark yace Inshaallah ba yanzu ba uhm uhm Yana
karkada yatsa,shi dai Spark baya son Mutuwa sai da ya bawa mutane dariya,Malam
Jilani yace kaga Dan banzan yaro Kafi so a barku kuyi ta sheke aya,wallahi kuji
tsoron Allah ku daina neman juna namiji da namiji tirrr, Jamilu ya furta amma Allah
yasan gaskiya watakil ma na fiku a wajen Allah.

Malam Jamilu a dawo lafiya cewar Malam Sharu,Naila tace yau darajata ta sake
karuwa na sake samo sabon suna,Malam,Dandaudu,Dahara,Jamilu, Terror, Tantiriya,ga
Kuma Yar Yahoo har naci waya da dubu goma,duk ni kadai,Juyowa tayi bayan ta mike
tsaye ta Kalli Spark suka hada Ido, Ido daya ta kashe Masa,da sauri ya dauke Kai
tare da shugowa dakin gaba daya ya mika musu hannu suka gaisa,gadonta ya hango ya
gane na Jamilu ne tunda yaga kayansa a Kai,Let's go ta furta tare da ficewa
waje,Bin bayan Jamilu yayi,Malam Sharu yace Allah ya shiryeku ku gane gaskiya,duk
tunaninsa neman juna suke.

Spark yace yunwa nake ji dama,Jamilu yace sai kace na haifeka wai, kawo kudi a
siyo Maka,Dan aiki nane Kai fa albashi zan biya cewar Spark, Jamilu ya karbi kudi
suka tafi tare har wajen abincin ma, sai hakuri duk bai yarda da tsaftarsu ba amma
yunwa bata da hankali,a wajen ya tsaya,Jamilu ya tafi siyo Masa shi Kuma ya kira
Kamal yace wai baka fadawa masu kawo min abincin ba? Yace na fada musu gobe zasu
dinga kawowa,wasu masu reception dake Kano Spark ya biya kudi kullum za a kawo masa
abinci da rana shike nan.

Jamilu Yana siyowa suka taho suna surutu tana bashi labarin abinda ya faru
tsakaninsa da Mummy har aka kawo shi gidan yari sai dai ya boye bai ce shi mace
bane,suna shiga palonsa ya zauna taga ya linke kayan sawarsa,Abincin ya fara ci
yace Kai baza Kaci ba? Jamilu yace na koshi yau naci wajen su Goje,Yana cin abinsa
yace zan karawa Yan gidan nan tuka tuka guda biyu biyu both bangaren mata da
Maza,sannan zan sa ayi musu Solar ta ruwa kowanne bangare naga babu ruwa suna Shan
wahala,Zan fitar da masu kana nan laifi zan biya musu kudin tarar da suka kasa
biya,sannan zan karawa Mata toilet block guda zanyi,suma mazan haka,sai wasu
abubuwan da suka lalace duk zan biya a gyara,ya ka gani? Naila taji ya wani
birgeta, tace amma zaka yi aikin Allah wlh mashaallah Allah ya biyaka da
Aljanna,yace Ameen Allah nayi tawasli da shi Allah ka bayyana gaskiya na bar gidan
nan,Naila Jamilu yace Ameen Ameen tare dani,yace see you a matsayinka na wa? Dariya
tayi tace a matsayina na dan aikin me aikin Allah, ko baka so na fita? yace ba
laifi in ka fita Ina murna,Jamilu yace baka kaunata bari na tafi,Spark yace ka
zauna a nan mana ka dawo nan da zama,ka dinga tayani hira,Naila ta zaro ido tace
a'a zan dai dinga zuwa ko yaushe,bai matsa ba yace okay fine,so yake Jamilu ya
shagala ya samu ya lalube shi ya tabbatar namiji ne shi yasa yace ya dawo wajensa
da zama,a ransa yace koma yane dai yazo watarana zai shagala yayi bacci wlh sai na
cire Masa wando ko na taba kirjinsa naji ban yarda da wannan Jamilun ba.

Yana cin abinci Yana hada uban zufa,Naila ta dauki Dan karamin mificinsa na roba
ta durkusa a gabansa kamar me daukan karatu ta fara Masa fifita,Yana cin abincinsa
harda lumshe Ido
Ayi hakuri na makara yau bana gida ne

Sharhi please

Free page

Account no
0175487861
Asmau Garba Muhammad Gtbank

Katin MTN
08061929616

Yan Niger
+22790795939

https://chat.whatsapp.com/FRJAnQZXm0t7rAroZWlMnQ

AsmaBaffa
[12/8/2023, 6:57 PM] AsmaBaffa: https://chat.whatsapp.com/Lro2cmYgE0588BKELFJhbf

🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

31-35

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM

Page naku ne
BABY AK
ZAINAB USMAN
MOMY FARUK
FM

Follow this link to join my WhatsApp group:


https://chat.whatsapp.com/Lro2cmYgE0588BKELFJhbf
Assalamu alaikum matan kwarai munkawomuku magungunan mata masu kyauda inganci
munada maganin sanyi original muna hadin 3ster hajiyata kizamo star agurin oga
hajiyata karkimanta shima ogan akwainashi muna nan asokoto muna aikawa kowane gari
harma damokotan kasashenmu babu inda bama kai kaya ⭐⭐⭐3 Alkhairice garemu yan
uwamata
Gamai bukatar lambar kira gata 09039320715 sai munjiku siyannagari maidakudi gida
3⭐⭐⭐alkhairice

Naila tana ta Masa fifita har ya gama cin abincin sannan ta ajiye mificin,ba
wani da yawa yaci ba tace har ka koshi? ae ya furta mata Yana Shan ruwan roba,dayar
kujerar taje ta kwanta tana kallo,kawai sai bacci ya dauke ta,har dare yayi 12am
tana bacci,yaje ya tsaya a kanta Yana karewa surarta kallo,ya kafeta da mayun
idanuwansa, a hankali ya lallaba ya zare hular dake kanta wannan karon ta sake
canja Daadaa din dake kanta ta gyara gashin haka, ya kalleta ya sake kallonta da
yatsa ya nunata Yana magana kasa kasa yace yanzu wannan ace namiji ne wai,ikon
Allah komai zai iya faruwa,idan kyau ne ai nima Ina da kyau ya akayi ban zama haka
ba,shara ma yanayi wani da karairaya fiyas fiyas ya gwada yanda yake sharar, Naila
ce ta juya baya tare da gyara kwanciyarta bata San me yake ba,ya shiga karewa
bayanta kallo yace gashi nan yana da duwawu gashi nan da shape sosai,a hankali ya
dan ja wandon na Jamilu ya damewa Jamilu duwawu,da sauri ya tsorata ya ja baya yace
see ass ahhhh karya kake Jamilu mace ne Kai,duwawu ga tudu nan kamar kabarin me
tatsine ace namiji ne.

Yace bari naji da laushi a hankali yasa hannu ya latsa kadan,ya sake mamaki
yace wannan bazan yarda ba sai dai Jamila karya ne ace Jamilu wlh Jamila ce,yace
saura na tabbatar bari na taba nonon yakai hannu a hankali cikin sanda,caraf yaji
Jamilu ya rike hannunsa, tashi Naila tayi tana rike da hannun Spark sai kuwa ta
daure fuska ta mike zata tafi,yace kasan karfe nawa kuwa da nisa fa zuwa
bangarenku,Naila tace gwara na tafi haka,shi yasa wlh bana son shiga harkar mutum
dama burinka kenan ta mike ta jawo takalmanta ta saka sannan ta bude kofa tana
fitowa tace Alhmdllh wai da yau ya kamani da naga ta kaina.

Washe gari da safe Naila asibiti taje ta samu likitocin,an bude mata file da
komai sannan taje ganin Likita,tana shiga Office dinsa ta zauna,yace me ke tafe
dakai? Jamilu yace kasan Likita ni Dandaudu ne,Likita yace naga alama ai,Naila tace
to cutar sanyi na dauka garin harkar mu ta kafta harka,kaikayin Pole nake yi,Likita
yace mene Pole Kuma? Tace Ma'ana power bank,Arrow,the siga,long Jumbo,ko baka gane
ba Ina nufin Timber, Likita yace na fahimta da kuraje? Naila tace masu ruwa ma
kuwa,murmushi likinta yayi ya rubutawa Jamilu magunguna yace wannan a nan pharmacy
zaka shiga ka karba,sannan zaka zo kullum akwai Allura har ta tsawon kwana
biyar,Naila tsoro ya kamata bata son Allura amma haka ta daure.

Likita ya hada Allura ya cika sirinji taf yace juya,Jamilu yace babu me rike
ni oh ni Dahara Tantiriya na shige su za a tsira min tsinken bature,ayi min a
hannu,Doctor yace bana Allura a hannu ni,Jamilu yace wayyo zafi Yana yarfe hannu
tun ba a fara allurar ba,da kyar ya juya duwawun ya bude kadan,Likita ya Masa
allurar kamar wacce za a yanka haka take kwailo,liliya wajen tayi ta fice da
sauri,Likitan tana fita ya tallafe habarsa da hannayensa yace anya kuwa wannan
namiji ne,Kai idan kazo gidan yari zaka ga abin mamaki a rayuwa.

Naila tana fitowa sai yarfe hannu takeyi tana dingisa kafa tana tafiya akan
anyi mata Allura, pharmacy ta shiga ta karbi magunguna masu uban yawa ko wanne da
yanda zata Sha,dakinsu ta dawo ta ballo magungunan duk ta dinga Sha da daya da daya
har ta gama sannan ta kwanta a gadonta,bayan wasu lokaci magunguna suka fara aiki
Kaikayi ya karu sosai,ga Kuma side effect na magani duk ya rikita mata jiki,Malaman
suka Kalli Jamilu tare da tambaya lafiya? Jamilu yace zazzabi nake shine naje
asibiti aka rubuta min magunguna,suka dinga yi Masa sannu,haka ta kwanta ta lullube
jikinta har kanta tayi bacci.

Beauty ce ta dinga kiran wayar Jamilu amma ba a daga ba, gajiya tayi tazo tayi
magana ta jikin bangon,Malam Jilani yace bashi da lafiya Jamilun naku zazzabi yake,
Beauty tace to ayi Masa sannu Allah ya bashi lafiya Dan Allah idan ya tashi ya
kirani,suka ce za a fada Masa.
Naila taci bacci sai dare ta tashi a baccin suna fita Sallar Isha tasan suna
dadewa tayi sauri ta rama sallolin da ake binta,ta koma ta kwanta tana kwanciya
malaman suna shugowa tare da Spark suka shugo , a kwance yaga Jamilu da magani a
gefe a leda, a gefen gadon ya zauna yace ya jiki? Jamilu murmushi ya saki yace da
sauki,dama baka da lafiya? Jamilu yace ai kawai ganina kuke yi amma bani da lafiya
mazantaka ce kawai nake nunawa,kasan mu mazajen kwarai ne akwai juriya, Spark yace
hmmm ya bude ledar maganin ya karanta yace zazzabi Kuma naga Antibiotics,Naila tace
basir dina ne ya tashi inji Likita,Spark yace Allah ya Ara min rana Jamilu Allah ya
bani sa'a a kanka ya furta kasa kasa yanda ba Wanda zaiji, Dariya Naila tayi ta sa
hannu ta jawoshi sosai tana daga kwance ta rada Masa zaka ji kunya kuwa abinda kake
zargi ba shi bane, hannu ya Kai yace ka tsaya naji kirjin ma ya isa, ya Kai hannu
Jamilu ya bige hannun.

Su Malam Jilani sunyi kasake suna kallo,Sharu yace dakin nan idan muka yi wasa
fa muna barin badala irin wannan to za a daina karbar adduar mu,Allah zaiyi fushi
damu,muna kallo namiji da namiji suna soyayya Kalli yanda suke magana,Malam Garzali
ne ya rufe baki da sauri yace wlh ya tabawa Jamilu fuska,a lokacin Kuma Spark ne ya
shafa habar Jamilu yace babu alamun gemu Jamilu fa har yanzu,Jamilu yace ka takura
min wlh zan daina kulaka, Spark yace na daina inshaallah daga yau, Naila taji dadi
abinta tana murna.

Bayan kwana biyar Naila ta warke sosai Kuma tana ci gaba da maganin Infection
dinta a lokacin Kuma ta fara period,Allah yasa da pad dinta ta dinga abinta ba
Wanda ya sani ba Wanda ya gane ta, Kuma suna waya da Beauty sosai da Yan gidansu
musamman Mohsin gashi suna ta Shirin sake zuwar mata Ziyara,Spark kuwa anzo masa
yafi sau biyar ma su Kamal, ga Abinci yanzu kawo Masa akeyi kullum na dare Dana
rana daga eatery, ranar Ziyara Mohsin da Umma tare da Hidaya ne suka zo ba
Abba,Naila ranar Baki har kunne,wannan karon ba a zowa Spark ba sabo da shi har
sanda ba ranar Ziyara ba duk Wanda yake son Gani Yana ganinsa musamman da babban
shugaban gidan yari yaji Spark ya fitar da kwangilar aikin da za ayi musu na gyara
gidan yari kowa murna suke ma'aikatan sosai suke girmamashi sai abinda yake so ake
Masa.
Naila Kuma ganin ya sa mata ido sai ta rage shige Masa idan taje aikinta zata yi
Masa kawai ta gama ta fito,Spark bai Jin dadin Hakan Jamilu Yana sa shi nishadi sai
ya daina sa idon ma.

Da wayar Samsung a kwali ta fita wajen su Mohsin tana zuwa tace Yaya wayar Nan
zata Kai nawa? Mohsin ya karba ya duba yace ai wayar manya ce wajen dubu Dari biyu
ce,tace taka ta hannunka nawa ce? yace dubu tamanin tace to bani taka na baka
wannan,Mohsin yace Kai sis ni da zan siya miki ke zaki bani, tace to mene a ciki
kaji Yaya amma karka sake wlh ka Bawa Hanan ko pics idan tayi ban yafe ba, Umma
tayi dariya tace Kai ke fa halina dake ruko, Amal kawai za a dauka itama Dan kawai
'yata ce shi yasa amma da tunda ta hada jini da Hanan baza a dauke ta ba, yarinya
tayi kama damu taki duk tayi kama da uwarta hanci kamar tulu,Mohsin yace bana son
sharri Amal dince me hanci kamar tulu,Spark ne ya fito, kawai Naila taga ma'aikatan
sai wani girmamashi suke yi kamar wani me Mulki.

Ta kalle su tace mu wato anga talakawa ne shi yasa ba a kaunar mu,idan baka da
kudi shike nan sai duniya tabi ta tsaneka,wallahi abinda kuke bakwa kyautawa a
kasar nan, talaka shine abin tausayi amma Banda ku,ni da nazo munafunci na kuka
dinga yi amma yanzu Kunga me kudi har cewa kuke barka da fitowa ranka ya Dade ana
wani matsa Masa hanya ni waye yayi min sannu da zuwa,wani Ma'aikaci yayi dariya
yace to Kai ai Kafi kowa ma farin jini tunda ka fito mutane suke Maka magana,wani
yace Jamilu,wani yace Terror,wasu suce Tantiriya,yanzu naga malamai sun wuce sun
kiraka da Malam Kuma,ga Yan Daudu suna cewa Dahara,to mu me zamu ce Kuma,Naila tace
uhm ku dai Kunga kudi,Spark kudi ya zaro ya rarrabawa ma'aikatan wajen har na bakin
gate sunzo sun karba,Naila ta kalle shi tace neman suna ne badan Allah bane,Spark
ya juyo ya kalleta ya mata gwalo,dariya tayi tace wlh nima sai ka bani,takowa yayi
yazo ya gaida Umma sosai harda surunawa ya mikawa Mohsin hannu suka gaisa, Hidaya
sai kallonsa take kamar mayya,Naila duk sai taji haushi ta harari Hidaya tace ni
ban san ma me yasa aka zo dake ba Hidaya, ki ta kallon mutane da anyi magana kice
kin waye ke Yar birni.

Hidaya ce ta Kalli Naila ta harareta taci gaba da kallon Spark, Naila ta dauki
tsinke ta nuna idon Hidaya da shi kamar zata zokale mata ido,Hidaya ta janye idonta
da sauri,Spark ma bai San me suke yi ba Yana can Yana magana da Mohsin,Naila ta
mike tace Yaya Mohsin bani wayar mana,ya zaro wayar tasa Yana zaune Yana kokarin
cire layinkansa Naila ta rungumo kafadunsa tare da Dora kanta a Kafadar Mohsin tace
Sweetheart,yace matsa Dan Allah,Naila tace sai na Dana nima yanda Hanan ke yi,Spark
baki ya tsuke ya Kalli Naila wani haushin Jamilu yaji kamar ya shake shi, fuska ya
daure sosai kamar an aiko Masa da mutuwa ya juya tare da Jan tsaki ya bar wajen ya
koma ciki.

Bayan su Mohsin sun tafi ta dawo ciki da abincin da suka kawo mata da
tarkace,bangaren Spark ta nufa direct a Palo ta same shi zaune yayi shuru Yana
tunani fuskar nan ba Rahma,Ledojin ta ajiye tana murmushi tace sun tafi
abokina,Spark yayi banza da Jamilu,Naila tace ga abincin yace bana ci bazan ci
ba,tace Okay fine ta zauna a wata kujerar, lemo ya dauko Wanda nasa ne Yana Sha
Yana cin biscuits,tana kallonsa kawai cin abinsa yake Yana Shan lemon yaki kulata,
tashi tayi ta fisge robar lemon ta zari biscuits din ta gudu can wata kusurwa a
dakin tana Sha,Yaji haushi yace Oh bani lemona bana son irin wannan,yaje ya tsaya a
bayanta sosai zai kwace,ta sake kurba ya rirrke Jamilu ta baya yace bani Ohhh I
don't like this yaja tsaki,Jamilu ta tirje a Jikin kujera tana Sha,ya manta ma ba
mace bane ya rungumo jimilu cikinsa ya riketa sosai ya kwace lemonsa,amma me sai
yaji Hallare ta mike lemon ya saki a kasa ya koma kujera ya fada Saman kujera Yana
salati a ransa, Yana cewa na shiga uku ni ko addua zanje ayi min ne,na rasa gane me
nake ji game da Jamilu,why? Sai ya bawa kansa amsa kabarin me tatsinensa ne ya taba
min jiki shine na mike haka,Oh God wannan fa ya wuce kabarin me tatsine ma ya koma
Jakin babangida, Naila bata San me yake tunani ba ta zauna a gefen kafarsa tace na
dai Sha nima,ka tashi Dan Allah muci abincin ko sai dare ko na bayar?

Yanzu sabo da ana kawo maka abinci me dadi shine kake min gani gani,idonsa ya
dago ya zuba su a kan Jamilu gaba daya ya koma wani ja harda kwalla a ciki,Naila
tace wai zazzabi kake yi ne? idonka yayi ja fa,Spark Bai iya cewa komai ba gashi
idan yace Jamilu ya fada Masa gaskiya sai masifa,shuru yayi ya Dan kokarta ya dawo
hayyacinsa ya mike zaune ya jawo abincin yace muci,ya firfito dasu abinci masu rai
da lafiya,suka zauna a kasa tare suna ci suna satar kallon juna,kowa da abinda yake
tunani a ransa.

Hanan kuwa abinda Naila tayi mata waccen ziyarar taji haushi ta dauki alwashin
sai taje gidan yari ta tonawa Naila asiri ba tare da kowa ya sani ba,shiryawa tayi
ta wuce gidan Umma sabo da Mohsin ya damu lallai sai taje ta gaida Umma da
Abba,tana shiri sai ga Mohsin ya shugo yace ga Abba Nan da abokinsa zasu zo ki fasa
zuwa yau gobe sai kije,Hanan wani takaici ya kamata tace ai kasan dai nace zan biya
gidanmu Kanwata tana zazzabi zan duba ta,yace nace baza kije ba Abba zaizo kanwarki
tafi Ubana nane? Hanan mayafin ta cire tana kunkuni tana furta duk an bi an takura
min sabo da Ina da aure ta zauna a Palo tana fushi.
Abba ne yayi Sallama ya shugo tare da abokinsa Isa,Hanan ta wani bata rai ta
amsa,sai Mohsin ne yace su shugo Palo,bayan sun shugo sun zauna da kyar Hanan tace
Ina yini,Abba yace lafiya Lau ya gidan? tace Alhmdllh ta mike ta shige daki ta
barsu a Nan tare da Mohsin bata ko sake lekowa ba,Mohsin ya bita bedroom yace ki
fito ki kawo musu lemo da ruwa da abinci, dama basu ci abinci ba suka fito to ni
abincin yau kadan nayi me yasa baka ce na dafa da su ba,Mohsin yace wai Ina zuwa
ubanki ne ya kawo min abincin ne ko kuwa? Ubana guda zaki wa wannan wulakancin?
Kuka ta saki harda kururuwa,Abba suka ji kukanta yace Kai Mohsin lafiya?

Ya fito Yana cewa wannan yarinyar bata da mutunci wallahi nayi danasanin
aurenta,Abba yace a'a indai akan mu ne mu tafiya ma zamuyi muje ka raka mu gidan su
Fatiman shike nan mu babu matsala ma ka kyaleta, su Abba suka mike Malam Isa yace
ka rabu da ita Dan Allah Mata sai hakuri,Mohsin ransa in yayi dubu to ya Baci,haka
yaje ya kira musu Fatima tace su shiga,shi Kuma Mohsin ya koma gidansa Yana zuwa ko
magana baiyi ba ya dakko biro da takarda ya rubuta mata saki daya ya jefa mata Inda
take kwance yace gashi Nan kije daga dubiyar ki zamanki a gidanku na sakeki saki
daya.

Sai ta mike zumbur Kuma sai kuka tana yanzu ni ka saka Mohsin yaja tsaki ya
fice abinsa tana kuka Wiwi ta dauki Amal ta shirya kayanta tace yanzu a gidanmu
wajen kwana ma aiki ne,taja Amal tana kuka ta fice,kowa ta gani a hanya sai tace
mijina nane ya sake ni ba abinda na Masa,duk Yan layin Nan sai da suka taya Mohsin
murna ya rabu da Hanan bata da hankali ko kadan Bata San mutunci ba,gashi duk ta
fesa a layin an saketa bata San Allah ya Kara ake mata ba,a gefen titi suka hadu da
Mohsin ya tsaya da machine yace bani Yata, ta duka ta dauki Amal tace bazan bayarba
wallahi shege dan iska ehoooo jama'a ga barawon yara, mutane suka taru sosai,Mohsin
ya gyara machine dinsa yazo zai fisge yarsa taja yaja suna ta Jan Amal kamar zasu
tsinka ta,har Hanan tayi nasara ta fisge yarta,wani Dattijo yace kaga Mohsin
kyaleta taje ka dakkota cikin ruwan Sanyi,Hanan ta ajiye Amal a gefen titi tace
dalla tsallaka muje tana ji da masifa ko titin Bata kalla ba yarinya ita Kuma ba
hankali sai ta tafi da gudu saura kadan mota ta maketa Allah yayi da kwananta
Mohsin ya fisgota suka Fadi gefe can,yarinyar da shi sai da suka kuje a kafa,Hanan
tasan tayi laifi sai ta shige Napep da sauri ta gudu tana cewa wlh sai na huce akan
Naila,wacce Kafi kauna sai na jawo muku matsala gaba dayanku.

Abba ko da yaje zance Fatima tana kallonsa Bai iya cewa komai ba tunda suka je
yayi shuru,itakam zata Kai 40yrs Yar gayu ce ba laifi sai dai tana da wani hali
Wanda sai Wanda ya zauna da ita zai gane hakan,ta Kalli Hashimu tace baka ce komai
ba Kai?yace to me zance ai gwara mutum ya dinga kamewa,sai kace Kaine macen? yace
ba a nan take ba Batoola namiji ne ni na gaske,ni ba a gane ni namiji ne a haka sai
kin shugo gidana tukun zan baki mamaki,Fatima ta zaro ido tace to Allah ya
kaimu,Malam Isa sai zuba zance yake,sai da suka gama zasu tafi Abba ya Kalli Fatima
yace Batoola babu wani anko a kasa da zakiyi? Ko Baki da bikin wata Kawa ko Yan uwa
ai sai ayi miki ankon,Malam Isa Yana ta faman dukan Hashimu a kafa a boye zai bata
tsari amma Hashimu ko a jikinsa yace ki fada kar kiji kunyata zan miki ankon.

Batoola banza ta Fadi tayi karya tace bani da wani biki sai na wata Yar yayata
ankon ma ba Mai tsada bane dubu goma ce atamfar,Abba yace kacal karki damu zan ba
Mohsin gobe zai kawo miki,ya zaro dubu biyu yace ungo wannan kici kifi,ko bakya
Dora kifi a shinkafa? Batoola tace ai da dadi ne? Abba ya gyara zama yace musamman
a shinkafa dafaduka idan ta dakko dahuwa a tukunya tana wannan chaf chaf chaf din a
tukunya sai ki bare kifinki ki zare Masa kaya,karki dugurguza shi a haka a hankali
zaki zare kayar,

Gefe Kuma ga shinkafarki a tukunya Saman wuta tana chaf chaf chaf ta dakko dahuwa
sai ki bude ki zuba kifin ki juya a hankali ki rufe ki barta turiri kawai ya
wadatar idan kika sauke kika fara tsallake haba ai Kuma shike nan.
Batoola ta dinga dariya Abba yace ki gwada ki gani Ina dafawa matata idan
shagwabarta ta motsa, kin san Kubra akwai Mulki bani da kamar Kubra duk duniya uwar
yayana ba,duk wacce na aura sai ta yiwa Kubra biyayya zata zauna lafiya,Isa ya sake
zungurar Hashimu akan yayi shuru amma Hashimu sai surutu an samu budurwa,Malam Isa
sai cewa yayi su tashi su tafi suka mata sallama suka wuce,Batoola tace yo ai ni
dama Wanda zan juya nake nema wannan sullutu ne sai dai Uwar gidansa Yana sonta da
yawa dole na shiga da shirina wlh dole na kwace shi,Batoola bata San Umma da Mohsin
ke yin komai a gidan ba, Abba baya tsinana komai amma har taci alwashinta.

Washe gari Umma da Abba suka ji Mohsin ya saki matarsa,Umma murna tayi amma
Abba ba Wanda ya sani yaje da kansa gidan su Hanan ya dawo da ita gidan
Mohsin,Mohsin Yana Shan shayi a Palo shi da Amal sai ganin Hanan yayi tare da
Abba,yace Abba mene ne haka Dan Allah,gidanku Mohsin rufe min baki,na dawo da ita
wlh tun wuri ka maidata dakinta idan ba haka ba zamu samu matsala da Kai kaji na
fada Maka,komai ai hakuri akeyi,mu da ace bama hakuri zan zauna da uwarku ne,Bai
bar gidan ba sai da ya tabbatar ya Maida Hanan sannan ya tafi,Hanan da Mohsin daga
Nan Kuma suka dora gaba ba Wanda ke kula wani sai da dalili.

Bayan kwanaki Aikin da Spark ya kawo gidan yari ya kankama sosai ana ta aiki
ba tsayawa,sannan kullum sai an zabi masu kananan laifi ya biya kudi an fitar da
su,Jamilu ya buwayi kowa akan abokinsa ne ai yake aikin ruwa sai yaga dama zai saki
wa mutane ruwan,cikin kankanin lokaci aka kusa gama ayyukan cikin Yan satikai, sai
yabawa Spark akeyi,bangaren mata ma masu kananan laifi yasa aka fitar ciki harda
Chikar Gayu domin rabonta ne ya rantse shekaru sunfi goma aka yanke mata amma aka
zabo da ita,Chikar gayu sai kuka take tana murna Kuma tace wannan Spark din da ya
fitar dani Allah ya biya shi da Aljanna,tabi kowa daki daki tana basu hakuri a yafe
mata abinda tayiwa mutane,karshe wajen Beauty taje suna ta kuka suna Murna Beauty
tace idan na fito Chikar gayu har gidanku zanzo,Chikar gayu tace shike nan yau za a
girgiza kirji babu ni a Islamiyya,Dan Allah Beauty ki hada da nawa kiyi,Beauty tace
Inshaallah chikar gayu duk abinda akeyi zan dinga hadawa da nawa da naki Ina yi,
iskancina zan rubanya ya koma ninki biyu harda naki,Chikar gayu tace na gode zamu
dinga waya ai daku dukkan ku,Sannan Dan Allah yau idan na tafi inji labari me dadi
Ina so naji cewar lallai duwaiwai sunyi Injury,Beauty tace kamar da kasa yau zan
cika alkawari,Chikar gayu tace duk gidan Nan Dake na yarda nasan ba karamar
Tantiriya bac.

,Beauty tace haka nake nice nan yo ai mu duk wani iskanci a jininmu yake,a gidan
Nan fa muka goge,Chikar gayu tace wayyo Wanda basa gidan yari sun shiga uku Gani
nan na fito yau za a kwanto kura,Ina zuwa unguwar mu Me unguwar layinmu zan samu na
shararawa Mari,Beauty tace harda sa hannunsa a shugowarki Nan karki ragawa uwar da
ta haife shi ma,Chika tace harda kakarsa, ahaf a gidan yari fa na balaga,anan na
fara irgen dangi,na fara period, Beauty ta mika mata hannu suka tafa sannan ta
tambayi Chikar gayu tace wai Chikar Gayu da zaki fara Irgen dangin naki da wa kika
fara irgawa? Chikar gayu tace shegen kaya kanin Babana da shi na fara nace Saminu
number one sai na bangare daya ya fito bul,na zaci kurji ne yasin,suka saki
shewa,tace na biyu sai me mitsitsi Ido kanwar babata Hasiya baturiya Ina irgata
nace Hasiya sai Wanda ya fito sai ya koma,Hasiya ba sa'a amma Ina irga Kakata Dake
ta Sha Madara ta gaji sai suka fito duka karo na biyu amma daya yafi Daya,nace baza
ta sabu ba,na sake irgo kakana na wajen uba tsohon ance akwai kyauta duk da ya mutu
abinka da jininsa sai ga dayan ya daidaita,daga Nan Kuma na fara irga kannena da
sauran su Mariya,Zainab,furdausi, Mubarak, Ismail har dai suka wuce irgen
dangi,yanzu Kuma Saurayi suke ta kira nace Dan ubanku miji dai, dariya duka matan
keyi suna da mugun yawa matasa Yan mata.

Rayuwa babu ke Chikar gayu Lami ce,ai Inshaallah duk zaku fito Ina Nan zamuna
waya yau a gadon bayan uwata zan kwana,Ma'aikaciyar ce tazo tace Chikar Gayu to
fito an tattaro wasu duk masu kana nan laifi,Chikar gayu tace Banga Azima me kwana
ba wando ba Dan Allah idan tazo duk da munyi sallama ku fada mata yau ta kwanta ba
wando har da nawa ta hada ta kwanta, Sukace zata ji,Beauty sai kuka take tana
tausayawa kansu su har yanzu ba labari,Hajiya Kaltume ta rako Chikar gayu tana
murna domin itama ta kusa fita bata damu ba,Beauty sun rako su Chikar gayu har iya
Inda suke da iyakar zuwa,Chikar gayu tana zuwa bakin kofa ta kwaso shoki tace sai
na dawo naga waye Spark din nan na Masa godiya,bani da gata an daureni a laifin da
ba nawa ba, Allah ya zama gatana na, shekaruna hudu a gidan yari, tana fitowa waje
wajen masu aiki ta daga hannaye sama tace Alhmdllh na shaki iskar yanci.

Aka basu takardu suka yi signing sannan sauran duk suka fito suna Murna suna
sauri Yan uwansu suna jiransu a bakin gate za a dauke su,amma Chikar Gayu ba Wanda
ta fadawa wai mamaki zata bayar, ta ratso cikin ma'aikatan tana kwambo tana wani
bubbudawa sai kace Soja tana gadara tace ko za a Maida ni ne eiyeee? ba wani shege
da ya isa Allah ya fitar dani waye ya isa, E choke you? Ta tambayi wani Ma'aikaci
yace akan me? tace ba Wanda ya isa,sai data tsaya ta kwaso shoki yafi a irga ta
cashe ba kida tayi kida da baki ta taka rawa sosai tayi fitsararta suna
kallonta,duk wani Dan iska suna kallonsa basa kula mutum,Rafeeq ne yayi parking da
mota ya fito yazo wajen Spark tun a mota yaga an fitar da wasu Chikar gayu ta taho
zata fice waje,da Gandroba a bayanta zaiyi waje da ita amma tana wani mamar mamar
da duwawu a haka take tafiya,shi Kuma Rafeeq a motar kida yake ji me duka yace ah
yarinya Kya yi rawa wannan masifar gida ka fito ai kayi abinda yafi rawa sai ya
karo mata vol ya bude motar ya fito, Chikar gayu ta gama iskancinta ta Kalli Rafeeq
ta Harare shi tace Kai dalla matsa da motarka zan wuce hanya tayi min kadan
yau,tazo gaban masu gadi tace a bude min gate wajen shigowar mota,hanya yau ta min
kadan,sun Sha kunu tace ko za a Maida ni ne? tabi ta kofar da mutane ke wucewa tace
to nace tayi min kadan na kasa wucewa, basu kulata,sai da ta gama iya shegenta ta
fice,tana fitowa tace wai wai ta Ina zan gane hanyar gidanmu ma haka ta shiga napep
tace Me Napep fara zaga Kano Dani kafin ka kaini tasha na shiga motar Kaduna garin
Gomna gidan ubana,yace a zaga Kano? tace da uwar kudina Kai karka min akuya.

Spark ne ya fito Rafeeq yace yanzu naga wata Yar iskar yarinya Yaya an saketa
wannan Yar ta gama kangarewa kaga yanda take girgiza tab,Spark yayi dariya yace
nima Jamilu Yana ciki ya buwayeni,kasan matsalar namiji ne wlh sonshi nake? Rafeeq
ya bude baki,Spark yace hmm bala'in ma da nake gudu idan yazo ko Hira muke yi sai
na mike kamar me, Kuma Karin bayani idan banganshi ba bana iya bacci,Rafeeq yace
again dai? yace baza ka gane ba Kuma idan ya rike hannuna dadi nake ji,Kai komai
yayi birgeni yake wallahi, idan na ganshi da wani sai kishi kamar zan mutu sabo da
kishi,Kai ko 'ya mace ban taba sonta haka ba a rayuwa,gashi kullum so nake na
kaurace Masa ko zan samu sauki amma bazan iya ba akansa zan iya batawa da kowa,Kuma
bana gudun abin kunya,Rafeeq yace Ina girman naka yaya? Kai da kake respecting
kanka? Jamilu ya ruguza komai,Kai In Kai Maka karshen zanci sai abinda jamilu yace
shi nake yi yanzu,idan yace yi kaza haka zanyi, Yaya Ina masifar taka? Ta gudu babu
girman Kai babu duk Jamilu ya sauke min shi, Kai ni yanzu ma na sake fahimtar
rayuwa na nutsu,yanzu idan na fito kowa zaiga na nutsu masifar da take afka min
tayi yawa.

Yanzu Rafeeq yayanka zai zama Dandaudu me son namiji Dan uwansa Ina tsoro kar
na mutu a kaini yankin annabi Lut, Rafeeq yace Allah ya tsare inshaallah zamuyi ta
addua Allah ya rabaka da Jamilu, Jamilu ya zama annoba,Spark yace ku samu malamai
ku basu sadaka a tayani da addua Jamilu nake so namiji,da zai aure ni murna
zanyi,yanda zan biya Sadakinsa ko mace Bata isa takai Jamilu tsada ba a
wajena,Rafeeq abin yafi karfinsa ya bude baki,yace Yaya ka daina fadar haka yace
gani kuke wasa nake abin Nan wlh bro bana wasa bane da gaske nake son Jamilu Kuma
tsakani da Allah amma Jamilu Sam yaki ya yarda Dani Ina sonsa Idan yazo ma na fada
Masa sai ya dinga dariya wai wasa ne.
Rafeeq yace abin Nan sai an dage da addua fa, Spark yace shine mafita,wata
hirar suka shiga sun gama ya karbi sakonsa ya koma ciki Rafeeq ya tafi.

Spark Yana komawa ciki ya fara dingishin karya yana furta wash,da Jamilu suka
hadu zata tafi kallon ball a filin wasa,tana ganin Spark taji wani Sanyi a ranta ta
karaso Inda yake tace me ya sameka? Yace daga asibiti nake kafata ce take ciwo
Likita yace naje ayi mata ruwan zafi sannan a mata tausa,Jamilu ya rude yace muje
bari na karbo ruwan zafi,Spark yaji dadi yace Ina jira kazo ka tafi dani,Naila ta
fyalla da gudu taje ta karbo ruwan zafi a cup tazo ta rike hannun Spark tace muje
sannu,Yana dingisawa tana cewa sannu, suna zuwa Palo ta zaunar da shi a Palo Saman
kujera tasa karamin towel dinsa a ruwan zafin sannan ta zauna a kasa sosai taja
kafar tare da dorata a cinyarta, ta Dan dage kafar wandon,farar kafarsa tana
shining ta bayyana,tace Nan? Yana wani numfarfashi yace ae nan wash zafi,wayyo
zafi,Naila ta Kalli fuskarsa yanda yake yatsina tace Dan Allah kayi shuru haka haba
sai kace ka samu Badon mace kana ta wani ihu wai Kai ajebo, dariya ya boye ba
shiri, tace Allah ai Kaine ka bari ka adana ihunka sai kayi amarya sai kayi abinka
ko Mimanka da Daddynku bazai hanaka ba,Spark yace Allah? Naila tace ai birgesu ma
zakayi suce ashe dansu gwarzo ne, yace to Allah ya kaimu tace Ameen.

Dama baiso ya tafi yawo yafi so suyi ta zama tare, haka ta Kai har dare a
wajensa tana faman jinya ya hana Jamilu sukuni da wayyo wayyo kafa,dare yayi yace
bazai tafi ba,Naila Allah yasa tana period Bata sallah period dinta na biyu kenan a
gidan yari, zai kwanta ya damu Jamilu muje mu kwanta,Jamilu Ido ya raina fata,yace
Ni zan kwana a Palo, Spark yace dalla bro wai mene haka muna abokai me zai faru ne
wai, Naila tana gudu kar ya ganeta haka ta bishi bedroom, ya kwanta a gefe
daya,Naila sai zare Ido take yi tana faman zaga gadon tana Jin tsoro tana addua a
ranta tace Allah ka kawo min mafita kwanciya da namiji a gado daya babu aure taya
zan iya,ta dinga zaga gadon,Spark tashi yayi ya sawa kofar key,Naila kamar zata yi
kuka,yace nifa nafi son wajen su Malam Jilani yau Ina da daukan karatu, yace Jamilu
wai mene haka sai kace mace wai,Naila da sauri tace ka daina ce min mace tam ta
lallaba ta hau can gefe karshen gadon tana furta wayyooo a hankali yanda bazai ji
ba, ta kwanta dai tayi shuru tana karanta wasikar Jaki,Shima Spark Yana kwance ya
wani baje daga shi sai gajeren wando,Naila kasa kallonsa tayi da kyar take iya
hadiyar yawu,yawun bakinta ma ya kafe,Spark Yana kallon Jamilu duk abinda yake yi,
ranar Naila kasa bacci tayi,idan Spark ya farka zai lalubeta yaji sai yaga idonta a
bude tarrr sai ya koma ya kwanta,

Sai 3am yayi tunanin tayi bacci ya tashi a hankali zai duba ya taba yaji sai
Muryar Jamilu yaji yace kaima ka kasa baccin ne? Da sauri ya koma ya kwanta Yana
Jin haushi yaki bacci,ranar a haka suka kwana ba Wanda ya runtsa.
Washe gari ta riga shi tashi baccinsa yayi lokacin ita Kuma ta gyara ko Ina fes
ta siyo musu tea ta gama kawo komai,ya fito shirye yayi wankansa cikin jallabiya
fara me tsada, Naila taga wani kiba yake karawa da kyau sabo da baya fita ko Ina,
tace mu karya nima wanka zanyi ka Ara min kayanka na saka wai duk Dan ta fitar da
shi daga zargin da yake mata,yace to da sauri wai irin zai kalli jikin Jamilu,
tunaninsa jikinta zai nuna a kayansa,sai lokacin tace Good morning,yace whats Good
about the morning? Yaja tea dinsa suna Sha,tace ya naga kafa har ta warke? Ya manta
ma jiya yace kafa na ciwo,yace Ina tashi naji ta warke.

Sai da suka karya sannan Naila ta shiga toilet dinsa yau ma bata wanke wajen
boobs dinta ba ta bar mannewar da tayi bayan ta gama ta shirya ta fito da kayan
jikinta,yace kace na ara Maka kaya? Jamilu yace barshi kawai na fasa, Spark tun
Yana so ya gane ma har ya gaji ya hakura.

Maman su Asmau ce ta zauna tare da yarta kanwar Asmau a daki suna kuskus tace
Kinga wallahi ki rabu da zancen Spark din Nan idan ba so kike Daddy dinku ya gano
Ina da sa hannu a kashe Asmau ba,Kinga ki rufa min asiri,nayi zaton Yar uwata ce
zata ce a bawa Spark ya aura sai kawai tace Asmau sabo da Asmau tafi ki nunawa a
fili tana son Spark,Yar kishiya ce fa Asmau, hauka nake na yarda wata banza can ta
auri Spark yaro me kudi da arziki gaki Yar da na Haifa Dan uwanki wata banza can
sabo da na riketa a dinga cewa ta zama kamar Yar uwa,wlh karki sake a gane, kin san
million biyu na bayar aka kashe Asmau,Kanwar Asmau tace ni wlh Ina son Spark idan
ba a fito da shi na aureshi ba nima mutuwa zanyi,ni Ina ruwana ni nace kisa a kashe
Asmau ai gwara kiyi kokari ma a hana auren amma kisa aka kashe ta ni Ina ruwana
kawai ki San yanda za ayi a fito da Spark na aure shi duk duniya Nafi kowa son
Spark ato idan ba haka ba na tona miki asiri.
Daddyn su Asmau ne ya fado dakin yace ba sai kin tona mata asiri ba naji da
kunne na,amma ku dai jininku kunyi asara,Kuma ba Yan arziki bane ku,uwarku tayi
asarar haihuwa, Nan take hawaye ya zubo Masa yace Kun sa na kama yaro, na bata Masa
suna ba hakkinsa,to ki sani zan fito da shi Nan da 3days ke Kuma zaki koma
prison,ya durkushe a kasa Yana kuka Wiwi Yana furta wannan wacce irin masifa ce
wannan,wannan mene haka,Mama sai diririce ta fara cewa tsaya Kaji yanda akayi,ka
bari kaji mana,Nan take ya kira Yan sanda suka tafi da Mama ya fada musu komai
Wanda sune suka kama Spark,yace a hada da kanwar Asmau a tafi da ita a Kai case din
kotu zasu fi bayani da kyau,ya dauki waya ya kira dukkan manyan Spark yace gaskiya
ta bayyana amma suje kotu zasu ga ko waye ya kashe Asmau,ba Wanda yasan waye ana
dai ta jiran ranar zuwa kotu domin a ga waye yayi hakan.

Jamilu yau ya fito Yana kallon ball,wani ne ya bugo ball sosai tazo ta daki
cikin Jamilu,Nan take ya Fadi kasa a sume hancinsa Yana jini,aka yi kan Jamilu babu
bata lokaci Goje Yana wajen ya dauki Jamilu yaji ba nauyi shafal Yana mamaki ya
wuce da shi asibiti,Spark bai sani ba sai Goje ne yace budurwarka fa ya sume yana
asibiti,ko gama ji baiyi ba ya nufin asibitin,ya samu Likita Yana kan Jamilu Yana
cewa yaki farfadowa Ina ta kokarin dai,Spark yazo kan Jamilu, Doctor yace bari naje
Office na dakko kayan gwaji zan kirawo wasu doctors din, yi kokari ka cire Masa
riga yafi Shan iska,Jamilu Yana sume bai sani ba,Spark ya cire uban rigar daya
jibga, sai wata t-shirt a ciki itama ya daga zai cire sai yaga vest ta mata,da
sauri ya janye rigar sama gaba daya sai yaga nonuwa an damesu da seletape da
bandage,da sauri ya mayar ya rufe rigar,ya kama wandon Jamilu jean ya zuge zip din
ya Buda yaga pant da pad alamar period take,ya sake jawo pad din yace har Jinin sai
na tabbatar ya kalla,ya Kalli gaban Naila,yace Alhmdllh gashi nan kuwa,bari na
Kalli kadan sai yayi sauri ya gyara mata komai ya zuge ya gyara komai Yana uwar
murna yace wallahi wallahi na fada wannan mace ne, karya ne ace namiji ne
haka,farin ciki ya isheshi ya sake kallon Naila,a hankali ya duka ya Dora bakinsa a
Saman nata yayi kissing dinta,hayyacinta ta dawo a lokacin ta bude Ido Taga Spark
bakinsa cikin nata Ido ta zaro ta hankade shi, yace sorry Jamilu kaki farfadowa ne
shine nayi Maka na baki ko zaka farka

Mikewa tayi zaune sai ga Likita ya dawo,Yace Alhmdllh ai ya farka ma,shike nan
buguwa ce yaje ya huta a bashi ruwa ya Sha,Spark yace to ya rike hannun Naila Yana
wani Jin nishadi a ransa bai nuna ya gane mace bane ya barshi a Jamilunsa, fitowa
suka yi Jamilu yace kaje ka rama min ball din daya buga min na suma na fada
Maka,Sorry by mistake ne ai cewar Spark Yana dariya ya rungumo kafadar Jamilu,Naila
ta kwace kanta da sauri tace na fada Maka nifa ba Dan Gay bane,murmushi ya saki ya
sake zuwa ya rungume Jamilu ta baya,Naila ta sa kafa ta take Masa kafa ya saki ihu
ya saketa ba shiri,ganin yaji zafi da yawa tace Sorry taho ta mika Masa hannu,yace
Jamilu ka fiye mugunta, fari tayi da Ido,ya saki dariya yace Jamilu Terror Dan
duniya , Naila tayi dariya tace Fadi ka Kara harda tallafo kirji tace da ace Ina da
boobs Dana girgiza,to mu Maza sai aka mana Hallare,Spark yace ya zamuyi Jamilu sai
hakuri gashi ba mata a nan.

Naila tace kwana nan ni Jamilu zan fara kwartanci a gidan nan domin zan fara
haura katangar mata,Spark yace shima yayi mata ta Yan Daudu yace ke kike da Beauty
harda yin girgiza,Bata San shi murna yake ya gano macece ba,Naila ta dinga dariyar
girgizar da yayi,tace wlh kaima gidan yari ya fara bataka, hannu ya shanye yayi
fari da Ido yace ai dama ni can tsohon dan duniya ne, tataccen dan Bariki ne,kin
taba ganin an kawo salihi gidan yari ai duk mune Yan iska, Naila ta dinga dariya
harda rike ciki, Spark ya shafa sumarsa Yana kallonta tana faman dariya,wasu
bangaren suka nufa Wanda Maza ne sun hada daba suna Jin kidan Yan tauri abinsu ana
ta faman danna ashariya, Spark yayi kalar yanda Goje keyi,irin Yan tauri yanda suke
yiwa kansu kirari, a kusa da mazan masu Jin kidan ya fara vibration yace kutmar
dumadu tsumina ya tashi ku bani hakuri....Jamilu ya saki dariya yace sai kayi Kaine
Spark......

Spark yace Kayyasa Kai sai ni Dan gidan Ahmad Maleek na kasar Jordan,Jamilu
yace ai Maleek din na kasar Jordan kakane a wajenka,yace wuya a kasar Jordan
billahillazi,Jamilu yace Kayyasa chau chau fada musu Dan ubansu, kowa ya ja dakai
zai Kai kasa,madalla da haihuwarka me Golden Eye, Wuya a gidan yari, dariya ce ta
kama Spark ya matsa gefe ya ja Jamilu yasan Jamilu Tantiriya babu ta Ido sai ta
fishi zakewa a cikin kartai,yanzu burinsa bai wace ya zaiyi ya hana Jamilu shiga
cikin Maza ba a daina kalle Masa ita,ga Jamilu bata San yasan mace bace sannan bata
ji,mafita daya ce ya fitar da ita daga gidan yari ko nawa zai kashe a duniya.

Sharhi pls

BOOK 1

Free page

Accnt no
0175487861
Asmau Garba Muhammad Gtbank

Katin MTN
08061929616

Follow this link to join my WhatsApp group:


https://chat.whatsapp.com/Lro2cmYgE0588BKELFJhbf
Assalamu alaikum matan kwarai munkawomuku magungunan mata masu kyauda inganci
munada maganin sanyi original muna hadin 3ster hajiyata kizamo star agurin oga
hajiyata karkimanta shima ogan akwainashi muna nan asokoto muna aikawa kowane gari
harma damokotan kasashenmu babu inda bama kai kaya ⭐⭐⭐3 Alkhairice garemu yan
uwamata
Gamai bukatar lambar kira gata 09039320715 sai munjiku siyannagari maidakudi gida
3⭐⭐⭐alkhairice

AsmaBaffa
[12/10/2023, 12:19 PM] AsmaBaffa: https://chat.whatsapp.com/FRJAnQZXm0t7rAroZWlMnQ

https://chat.whatsapp.co ~~ m/FRJAnQZXm0t7rAroZWlMnQ

🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

36-40

Official

By
AsmaBaffa
SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM

Page naku ne

Ummeetah Muhammad
Babyn Baby
Baby Ak
Nice Gal
Hauwancy

FANCY HONEY kawata Amarya Allah sanya Alkhairi,Allah ya Bada zaman lafiya,Allah ya
kawo kazantar daki😀

MASU AUDIO DAN ALLAH BAN YARDA A JUYA MIN NOVEL ZUWA AUDIO BA

Beauty waya ta kira Daddy dinsu tace Dan Allah Daddy a hada Case dina da case
din Jamilu shima a fitar da shi,Daddy yace tab Beauty wannan wacce irin soyayya ce
baki San mutum ba bai sanki ba ai dai Kya bari tukunna ki fara fita idan kika fita
sai ayi maganar Jamilu,Beauty tace to shike nan Daddy,yace Beauty kin kusa fita
inshaallah komai ya kusa kammaluwa kudi sunyi aiki,Allah ya rabamu da
talauci,talauci baida amfani ko kadan,Beauty tace a'a Daddy shima Yana da wani
amfanin ta wani bangaren fa,yanzu wani watakil idan aka bashi kudi neman mata zai
dinga yi, kuma Allah yana so yaje Aljanna sai ya hanashi ai kaga talauci yayi
rana,wani caca zaiyi in yana da kudi,wani Gay,wani Kuma dai yabi hanyar banza ya
koma dan wuta to Allah Yana son mutum,ai sai ya barshi da talauci a sa talauci ya
Masa dauri da ankwa,Daddy yace uhm yau Beauty tana wa'azi ikon Allah gidan yari
tayi rana,yau Beauty ce take min wa'azi na fada ta fada kai duniya,Dariya Beauty
tayi tace Islamiyya ce kawai ta ratsani Daddy Kuma ban gama shiryuwa ba fa a
haka,Daddy yace ah ni wannan gidan yari Alhmdllh ko iya haka ma naji dadi,Beauty
tace hmm Dan baka San ta'asar da muke bane Daddy,yace to Allah ya Kara
shiryaki,Beauty tace Ameen,suka gama hirarsu sannan ya kashe waya.

Yau Spark rike Naila yayi ya hanata tafiya,tace ni wlh bazan kwana a nan
ba,Spark yace to ya kake so Jamilu? Naila ta fara shgwaba bata San ma tana yi ba
harda doka kafafu ni....ni.....ni.....sai dai nima ka biya min VIP Dina ta furta
tana turo Dan bakinta gaba,Spark gaba daya yaji tsigar jikinsa ta tashi ya daure
tare da basarwa yace Iyye Jamilu Daudu haka tayi nisa Kuma?,Sai lokacin Naila ta
tuna da me tayi,Dariya tayi ta mika Masa hannu suka tafa irin yanda abokai keyi
tace shege abokina ka gane Ina fa sani nayi just ayi raha kasan ni akwai wasa,Spark
ya kalleta kawai yasan wayancewa tayi a ransa yace amma yarinyar da tsaurin Ido
take wai Shege fa tace min ta rainani fa,idan na aureta waye shugaban Kuma,nayi
mata uzuri ai duk tayi ne dan ta kare kanta.

Suna daga tsaye ya turata Saman kujera ta fada Kai a zaune shima ya zauna a
daya kujerar yace Jamilu in tambayeka mana? Naila tace Ina jinka, ka taba yin
budurwa? Naila tace Kai ba daya ba ma ai ni da a baya kwallon mayaudari ne,yace ba
wasa ba fa nake yi,Naila tace na taba yi baza su irgu ba tun daga kauye nayi
budurwoyi na dawo birni harda su Khalida,wai saurayinta Khalil take nufi Wanda tace
sai yayi bleaching, tace Khalida kyakyawa ce sai dai baka ce ni nafison mace fara
nayi nayi ta fara bleaching taki ni kuwa nace to tayi asara naki kula ta,ta nace
min Kuma Allah yasa kaddara ta jefo ni,Kai harda yaran masu kudi,ya fahimci zancen
yasan gaskiya ta fada sai dai ta juya abin ta maida shi saurayin mace shi Kam ya
gama gane kan Naila.
Tunani ya tafi to waye Khalida Kuma sunan idan za a juya zuwa namiji yace ohh
Khalid,yace a ransa yarinyar nan tana da basira, Spark yace doguwa ce Khalida din?
Kishi ne ya kamashi gaba daya haushin Khalid yake ji,Naila tace doguwa ce fa
kyakyawa na fada Maka saura kadan ma Umma su bani ita,Amma ya bata zo miki visiting
ba? tace dama ai na fada mata kar ta sake zuwa Inda nake sai ta koma fara,Spark
yace sai wa? tace sai hajiyoyi sai na kauye, Naila tace baka fada min ya aka yi ka
tsinci kanka a gidan yari ba nima kaga na fada Maka dalilin zuwana gidan yari.
Spark duk labarin da ya Bata gaskiya ya fada amma bai nuna mata cewar shine
Ashraf ba,kawai iya aurensa da Asmau ya fada mata,sai sunan iyayensa da kanne da
yayye, suke nan ya fada, bata gane komai ba tunda ba saninsu tayi ba.

A daren Kuma Mima sai kiran Spark take a waya ta fada Masa an gano gaskiya
kwana nan zai fito sai murna suke Allah sarki Uwa da Mummy sunfi kowa murna,shi dai
yaga suna ta uban kiransa duk Wanda basu taba kiransa ba sai kiransa suke,yace
watana yafi uku a gidan yari ba Wanda ya kirani sai Mummy,Kamal da Rafeeq yanzu
Kuma har su Papa kirana suke yi,harda kannena kawai yaki dagawa,Naila tace ka daga
mana ko alkhairi ne tun dazu wayarka take Ringing,ai bude wayar yayi ya cire
layinkansa dama jiya ya saka su,sabon da ba Wanda yasan number sai Mummy,Rafeeq da
Kamal layin ya Maida.

Yasan Naila bata sallah amma sai yace banga kayi Sallah ba Jamilu,ni Sam ban
taba ganin Sallarka ba,Naila tace ai ni ba kullum nake sallah ba,yanzu banji Ina so
nayi bane shi yasa,Spark yace to ba matsala Allah ya shiryeka tace Ameen,da ya
takura sai Jamilu ya kwana a part dinsa sai yace bari naje na dakko abu zan
dawo,yace kayi alkawari? Yace ae,okay fine,Jamilu ya fice ya koma ya debo pad biyu
data safe data dare, ta dawo yace me ka dakko to? tace dama kayana na killace kar a
lalata min,yace to,tace bari nayi fitsari ta shiga toilet ta dade Yana jinta tana
ta faman wanki,sai da tazo Jikin Sink zata yi brush kawai taga Pad gida guda a
ajiye,tsoro ya kamata tace ai ban taba Ganinta a nan ba kaiii yau na shiga uku
Aljanu sunyi min ajiya,a guje ta dauro towel ta fito ta manta,shi ta tsorata shi ma
yanda ta fito da mugun gudu,sai ya mike ya rigata yin waje,tace Kai ka dawo zo ka
gani

Ya bita da kallo kuwa tun daga kafafu har sama,jikinsa ne ya mutu ganin
cinyoyin Jamilu lukuta lukuta na mata,tana jibga uban kaya, Jikin nata ma yafi
fuskar haske sosai, sharewa yayi kar ta gane Bai kalleta ba yace Jamilu lafiya?
tace Abu ne a cikin toilet din kazo ka gani,ta tararrabe fuska,Spark yace Kai kamar
ba namiji ba wai Yana satar kallonta ya bita ciki,yace mene? pad ta nuna masa da
yatsa yace mene wannan din Bready kika kawo mana Kuma toilet?,Naila a haukarta tayi
mamaki taji dadi Kuma da bai San ma mene ba,tace ban taba ganinsa ba sai yau,Spark
yace baka kula ba dai, ai ni na dade Ina ganinsa na zaci ma kaine ka kawo,Naila sai
ta fara rantse rantse duk ta zargi kanta tace wallahi Allah ba ni bane, kaji na
rantse Maka da zatin Allah bani bane sai kace mace me zanyi da wannan ni kuwa,itace
take magana amma ita yake kallo ya zuba mata mayun idanuwansa, yace to tun zuwa na
gidan Yari nake ganinsa a toilet din nan maybe wani ne ya kawo ya ajiye,Naila tace
okay na gane,yace idan kayi wankan Dan Allah karka sa kayan Nan sunyi nauyi da yawa
baka tunanin cuta ta kamaka ta skin,fita yayi ya barta yaje ya dakko mata jallabiya
yace ungo kasa kasa wannan, Naila ta karba tana ta zargin kanta tace wai me yasa
yanzu ya daina takurawa sai ya Kalli jikina ne,karfa ko ya gano, tace a'a ai da ya
gano ai bazai kirani da Jamilu ba,Kai Naila kema kinyi shirme kin fita da
towel ,Naila tace to ai ya Saba dani shi yasa ma Bai ko kalleni ba ai ya hakura ne
ya gama yarda namijine,dariya tayi harda tafi tace Ina Shege ni Jamilu
Tantiriya,tace yau zan sha iska, ta cire seletape din da bandage Wanda take
nannadowa tun daga gadon bayanta ta zagayo da shi, ta taho da wani daga dakinsu
amma yau bata sa ta manne nonuwan ba tace yau ku huta Kuma,tayi wanka ta gama
kenan,yayi mata knocking yace bude Dan Jamilu me zamani ga lotion ka shafa,Naila ta
bude kadan tare da miko hannunta waje,tsokanarta yayi ya rike hannun yace wa na
kama yau sai na kalleka Jamilu,Kara ta saki tana ja hannunta
Body lotion ya bata ta karba,yace Jamilu badai katon hannu ba,tace wallahi a'a
bani da katon hannu ni ta rufe kofar,tana dubawa sai taga ba irin nasa bane,ta zaro
ido ganin hoton mace a jiki ta bude kofar kadan ta jefo man waje tace ni Macece da
zaka bani man mata? kafa sa min Ido Spark tam, ta rufe kofarta garam ta shirya haka
aka sa vest me kauri da wando gajere na Maza ta zura Jallabiyya taga Boobs cako
cako a tsaye ana Gani,cirewa tayi tasa bandage dinta da Seletape tun daga gadon
baya take lafka uban mannewa ta gama ta Maida vest ta Dora jallabiya,Naila ita tayi
Imanin Spark bai ganta bai Kuma gane cewar mace bace

Ta fito ta ganshi a Palo a kwance ya fara bacci ma,tashinsa tayi tace kaje ka
hau gadonka ni a nan zan Kwana, Spark yace jeka Kai bed din ni zan kwana a
Nan,Naila tace ni wai wanne Imani ne yazo Maka ne Aboki Banga kana haka ba da,ka
fara acting daban,Kaje ka kwanta,kaga Jamilu ni bana son surutu idan Kuma dakin
naku zaka tafi ga kofa Nan, Naila tayi tunanin wani abin ke damunsa baya son
surutu, ta koma dakin tana murna tayi kwanciyarta ita kadai,tunda tazo gidan yari
sai yau ta Sha bacci na mamaki ta saki jiki,amma duk a dakin malamai ne bata baccin
kirki a tsorace take kar a kamata.

Yau kuwa har yaje sallah ya dawo bata tashi ba tana uban bacci,shima bai tashe
taba ya koma baccinsa a Palo sai 9am ya tashi yayi wanka duk tana bacci har ya
shirya cikin Jallabiya shima fara irin ta jikinta ya dauki Flask ya tafi siyo musu
tea mutumin da Jamilu ke siyo masa baya komai Jamilu ke yi amma yau ya dauki Flask
dinsa karami me kyau na Yan gayu yaje ya siyo komai,Chips ya siyo me shegiyar tsada
kamar me ya dawo, yaji karar ruwa alamar tana toilet tayi brush da wanka,ledar pad
din data gani jiya ta farke ta dauki biyu tace yau ranar rushing ce har biyu zan
saka ko ta waye ma sakawa zanyi,ta shirya abinta ,Yar kofar ta bude kadan ta zuro
hannunta tace Friend miko min bakar leda,Yana sani yace ba baka ya mika mata
fara,tace baka nake so,ya koma ya dakko ya mika mata ta karba ta rufe kofa ta daure
pad din data cire ta fito ta leka waje Yana kallonta ta jefa a Dustbin sannan ta
dawo,Jamilu yazo sanye da jallabiyarsa.

Gani tayi sunyi anko,shi kuwa gani yayi tayi mugun kyau,tashi tayi ta koma
toilet ta hada wayo sai ta leko tace innalillahi Spark zo ka gani,ya Mike ya leka
yaga an bude pad din an dauki wasu,yace ikon Allah,Jamilu yace mutanen boye ne suka
dauka wata aljanar ce ta dauka,Spark yace to a dauketa a jefar ya dauka zai jefar
ta kwace tace Ina ruwanka mutanen boye sunyi ajiyar su zaka jefar musu ka kyale
musu suyi amfani da abinsu, Spark dariya yayi yace to a barta Jamilu.

Suka fito Jamilu yace wai Kai ka siyo tea din? Kai ya daga kawai,tace uhmm
ajebo anji masifu a gidan yari an goge,Spark yace a dole nake Shan tea din nan na
gaji da shi gashi zazzabi ma nake ji,Jamilu ya kalle shi yace shi yasa jiya baka da
sukuni? Kai ya daga mata tare da furta tun wurin magrib,da kulawa Jamilu yace sannu
ko sauro ya isa ya sa mutum zazzabi a gidan nan, maybe Malaria ce,daurewa yayi Yana
Shan tea din amma kamar zaiyi amai,Yana gama Sha da sauri ya shiga toilet sai amai
ya dinga kwararawa, Naila da sauri ta tashi ta bishi ciki, ta tsaya a gefensa ya
gama tsaf tare da wanke bakinsa yayi flowshing sannan suka fito tana Masa sannu,
muje ka kwanta kasha paracetamol sai anjima muje asibiti, yace duba ledar can akwai
a ciki,ta duba ta dakko Masa wani me kyau ba irin na yaku bayi,ta ballo ta kawo
Masa ruwan da yake Sha na roba,hannu ya mika mata,tace bude bakin,ya bude ta zuba
masa da kanta guda biyu ya kora da ruwa,hannayenta ya rike Sanyi yake ji ya furta
Yana sake kankame hannayenta cikin nasa. wuyansa ta taba da bayan hannunta ta cire
hannunta tace wannan uban zafin jikin fa.

Ruwa ta ebo me dan dumi a bowl na roba ta saka towel din karami a ciki ta matse
kadan tace cire rigar a goge Jikin nan ko zaiyi Sanyi,Yace kana namiji gardi zaka
taba min jiki naki ya furta ,Yana lulluba da bargo a Saman bed din,Naila ta fisge
bargon tare da haurawa Saman bed din ,a zuciyar Spark dadi yake ji,a zahiri Kuma da
kyar ya yarda,ya cire rigarsa daga shi sai boxers,jikinsa me tsananin kyau Wanda ya
tafi da imanin Naila,shi kanshi wani farin ciki yake ji a ransa marar
misaltuwa,kansa ya dora a Saman pillow ya juya mata baya gaba daya,gashi da kwailo
baida juriya a cuta, ya dinga dishi uhmm...uhm...wash....Naila a hankali ta shiga
goge Masa jikinsa, Hallare tuni ta mike sai da ta gama bayan nasa tace juyo
gaba,Yana Jin kunya taga yanda ya mike,yace ai haka ma ya isa thanks,ka juyo in
zaka juyo,bargon ya ja ya rufe daga kugunsa sannan ya juyo,Naila jikinta har rawa
yake itakam bata taba ganin namiji haka ba,da sauri ta rufe idonta a haka take yi
Ido a rufe,shi kuwa Spark fuskarta yake kallo kawai kamar maye ya lashi lips dinsa
a hankali Yana wani kallonta ba ko kyaftawa kamar wani wawa, har ta gama Ido a
rufe,da sauri ta dauke Bowl din ta zubar da ruwan ta wanke towel din tare da
shanyawa kafin ta dawo yayi bacci ma.

Bangaren nasa ta gyara ta fice abinta ta koma dakinsu na malamai,tana shiga


suka ce wai yanzu Jamilu Ina kake zuwa ne? ga budurwarka ta ishemu da nemanka ta
jikin bango Beauty, Naila tace Ina wajen Budurwata ta number one a raina Spark muna
zuba love,kasan ni both side ce in buga da mata in buga da Maza,Malam Sharu yace
Muna addua Allah ya shiryeka Jamilu, gobe fa akwai maulidi muna gayyatarka
Jamilu,Jamilu yace wai dama watan ya tsaya ne? Suka ce ae baka ga ana ta yanka
shanu ba a gidan nan zamu ci dadi, kazo kaima a baka sura ka karanta,Jamilu yace
idan dai Yan Mandiri sunzo masu kida zan shiga na chashe sabo da haka ba wani gardi
da zaiji Muryata ni Jamilu Tantiriya,Malam Sharu yace Allah ya shiryeka Kai sai dai
sai abin shagala ka iya,Jamilu yace sosai ma kuwa ranar akwai dukan kirji inyi rawa
itace zata kaini,Malam Jilani ya furta Allah ya shiryeka ka daina harkar Daudu kana
bin Maza Yan uwanka, kaima idan kana so mu dan samu waje mu kebe malam,Malam Sharu
yace ai gwara mu mutu,Dariya Jamilu yayi harda shewa irin ta Yan Daudu.

Ranar maulidi tun yamma aka fara Maulidi a gidan, Naila bata je ba amma ana
saka Mandiri ta tafi wajen,Maza an samu rana sai shagali akeyi suna ta tikar
rawa,wurin Spark ta koma yaji sauki suka je asibiti aka bashi magunguna bayan an
tabbatar malaria ce, bai fi kwana uku ba ya warke,lokacin Beauty ma ana shirin
barin gidan yari domin Daddy dinta ya shiga ya fita shekarar ta biyar a gidan yari,
sai yanzu Allah yayi,shi yasa take ta neman Jamilunta ta fada Masa,amma bata same
shi ba sai yau,Jamilu Yana daga wayar yace tuba nake gimbiya sarautar mata,kaina
bisa wuya,Spark Yana zaune Yana jinta kawai shi bai so yaji Naila da wani ko wata,
fushi ya fara ya kwanta kawai Yana jinsu Beauty tace Allah fa yayi nima nan da
kwana uku zan fita an gama komai,Jamilu ya furta wow,tace murna nakeyi zanzo Maka
ziyara na ganka,Naila tace na miki murna Baby Allah ya samu a danshinku, Beauty
tace Ameen .

Naila a ranta tace ni yaushe zan fita ne? Kawai sai hankalinta ya tashi, Spark
kuma ana ta kiransa a waya a fada masa labari me dadi yaki dagawa gashi har an fara
zama a kotu,Mama zama daya ganin asirinta ya tonu kawai ta Fadi gaskiya bata Musa
ba,Yan uwanta da suke uwa daya uba daya da Kuma Wanda ma uba suka hada suna ta
jimami har kuka suke ta faman yi,ba kamar Mima da Mummy,Mummy harda refefe baki
tace kinyi asara Kaltume,me ke damun mu ne? Mu yanzu mata sabo da son zuciya mune
zaluntar yaran kishiya,shi yaro ma me yayi Maka,yaro Amana ne, uwarsa bata gida ko
ta mutu sai mata su zauna sabo da son Kai su dinga zaluntar yaran kishiya,wasu su
nakasa yaro ko yarinya,wasu Kuma suyi ta gana musu azaba wannan zalunci ne Kuma
Allah bazai bar mutum ba,wasu har da kisan Kai a kashe Dan kishiya,kishi hauka
ne,kishiyar ma da ta mutu amma baza a hakura ba sai kishin ya koma kan
yaranta,yanzu mene ribarki Kaltume dan kin kashe Yar kishiya sabo da ta auri Spark
wato yarki kike so ya aura sabo da yana da kudi,tirr da hali irin naki
Kaltume,ganin ke kika raineta har ta girma na zaci ta zama Yar uwa,na zaci mun zama
daya da Asmau,yarinya tana mutuntamu,Kai Kaltume kuma kin yarda Dan Yar uwarki uwa
daya uba daya yayi life in prison,to Allah ya Toni asirinki,Mummy ana ta kallonta a
mutuniyar arziki ana cewa gaskiya ne,su kuwa sauran magana ma ta gagara.

Kotu zaman ta dage zuwa sati biyu sannan ta nemi a kawo mata Spark tare da ci
gaba da tsare Mama, Mummy harda cewa alkali sati biyu yayi yawa Dan Allah a fito
min da Dana dama na gama takaba ni Kam Alhmdllh,alkali ya kalleta yace to da kika
gama takabar aurensa zaki yi kema? Dana ne fa yanlabai,yace ai naji kince kin gama
takaba a fito miki da shi,zata yi magana alkali ya dakatar da Mummy da ta damu kowa
a ciki da surutu.

Abba bayan ya dawo daga zance komai sai da ya kwashe ya fadawa Umma amma yaki
fada mata zai mata anko,Yana runfar kayan miyansa Mohsin yazo wajen,bayan ya gaisar
da Abba,Abba yace yau ba aiki ne? Yace ae,to madalla dama Batoola ce za ayi mata
anko suna da biki ka kawo dubu goma a Kai mata ko kakai mata da kanka,Mohsin yace
Abba kasan wata yayi nisa sannan kasuwar ma Bata tafiya yanzu ga me gidan nawa yayi
tafiya,Kuma ma daga zuwa sai ace za ayi mata anko har na dubu goma,zagina zaka yi
Mohsin? yace haba Abba ni na isa,to kaje ko rance ka samo ka kai mata kaji na fada
Maka, Mohsin ba yanda ya iya yace ni na jawa kaina dana hada shi da Fatima.

Naila ce ta kira Mohsin lokacin daya shiga gidan wajen Umma, Mohsin yace na
manta ban fada miki ba Abba fa zai kara aure sis,Naila tace na shiga uku kishiya
zai wa Umma? Kuma kuka yarda? ya za ayi da shi shi yasa muka yanke hukunci cewar a
samo me hankali a aura Masa kar ya kwaso mana jaraba,Naila tace Ina wani me hankali
a kishiya,yanzu ma zuwan farko har tace ayi mata anko na dubu goma Kuma yace ni zan
biya gashi ni yanzu ma dubu daya ma bani da ita cewar Mohsin,abincin gidana ya kare
na su Umman ma ya kare,Naila tace ku rike auren Nan Sweetheart sai Allah yayi na
fito ni nasan tuggun da zan hadawa Batoola da kanta ta fasa,sabo da Allah dame zamu
ji ana fama da shi da gida, zai Kuma karo mana wani masifar salon tana zuwa ta
haifo wasu yaran,Kai Yaya me yasa zaka yiwa Umma haka,duk da tana yiwa Abba masifa
amma ai tana kokari tun Kuna yara itace cinku da shanku ta Sha wahala kullum a
teaching Dan a rufawa Kai asiri amma kuce yayi wani aure da me za aji, magana ta
Allah a nan baka yi tunani ba,ni bana goyon baya wlh kuma ko an aurota na dawo sai
ta bar gidan nan kaji na rantse.

Mohsin yace gashi yanzu ashe kaina na nemowa aure ban sani ba,Naila tace yanzu
baka da Sisi Yaya? Yace ae sai kayan kyau da wanka? dariya yayi tace Allah gwara
ayoka mummuna a baka kudi,turo accnt number Yaya kaga kudin Daddy din Beauty ya
bani ban kashe ba Kuma na samu wasu a wajen Spark Yana yawan bani kudi,ko bai bani
bama sai nace ya bani rabona,yanzu sai da na Tara 50k,Banda kudin da su Dan Indo ke
bani duk Tarawa nake yi,yace ke da zan kawo miki ni zaki bawa kina gidan yari,Naila
tace Malam ka karba, ni I can survive macece ana so na a gidan Ina samu ba
laifi,mene amfaninsu idan ban baka ba,Mohsin yace to Naila ai naji kunya,idan zaka
karba ka karba ni da Kai akwai kunya ne Hallare ma ta kama ganin taka zanyi
tsaf,zanci ubanki Naila tam,dariya tayi tace ka turo accnt karka bata min lokaci,ba
a dade ba ya turo accnt,a cikin gidan yari suna da komai nasu sai taje Wajen masu
POS ta tura Masa 50k din cass sannan ta koma dakinsu na malamai.

Spark yayi baki su Kamal sunzo suna fada Masa labari me dadi,yayi farin ciki
matuka sai dai Kuma mummunan labarin Mummy suna fada Masa ta bude cin duniya da
tsinke har kana nan kaya take sawa ta tsuke kamar Yar arna ta fice,itace gidan Shan
shisha da Kuma yawo da kawayen banza suna cinye mata kudi,kullum suna gidanta sun
tare,gefe daya Kuma tunanin Jamilu yake ta ya zai bar gidan ya barta,yace ai ko an
yanke hukunci ni ba yanzu zan fito ba,Banga ta tafiya yanzu ba,su Kamal suka bude
baki,yace ae ni yanzu banyi niyyar fita ba yanzu dadin gidan nake ji nafi nishadi a
nan,Su Kamal haka suka koma gida da mummunan labarin cewar Spark yace Bai shirya
barin gidan yari ba shi yafi son can,an Kuma rasa dalili sai Rafeeq ne ya tuna yace
ai wlh a uzura Masa ya bar gidan ana yanke hukunci sabo da namiji yake so,kowa bai
gane ba Daddy yace kamar ya? Rafeeq yace Gay yake so ya fara wlh wani Dandaudu yake
kauna,yace ma shi zai aura,Mima zumbur ta mike tare da furta Yana hauka ne wlh dole
sai ya bar gidan nan ana yanke hukunci,Kun san dai halinsa baya Jin magana ku San
yanda zakuyi wlh ya bar gidan.

Chikar Gayu sai da aka dan yawata da ita taga gari,tace to kaini tasha aka
kaita tashar mota,motar Kaduna ta shiga har ta shiga ciki tace na fasa katsina
zanje yes Katsina zani na fara zuwa wajen Uwata tukun na dawo naje Kaduna din gwara
na fara cin uban me unguwar layinmu sannan naje gidan Ubana,fitowa tayi ta canja
tasha ta hau motar Katsina suka ware birnin katsina, bayan awanni ta sauka a motar
ta biya me napep yayi parking a kofar gidan me unguwar Layin,taci sa'a a waje ta
ganshi,a gabansa ta tsaya,ya zaci fatalwa ce ya ja da baya Yana salati harda faduwa
a kasa Yana Nuna Chikar Gayu da hannu, Chikar gayu tace nice ba Aljana bace Dan
gyatumin ubanka,ai dama nace zan fito sharrin daka kulla min to na fito,Mikewa
tsaye yayi yace karya kike gudowa kika yi Kuma sai na sake kiran police sun Maida
ke,shegiya Yar iska haihuwar kwararo.

Ubanka aka Haifa a kwaroro cewar chika,me unguwa ya jawo sandarsa wai zai
kwalawa Chikar gayu ya zaci a baya ne sanda tana karama, Chikar gayu taci kwalarsa
dama gashi wani Dan figigi ta yanka Masa Mari,Mutane suka taru a wajen ana labari
Chikar gayu ta dawo, Me unguwa ya dafe kumatunsa yace ni kika mara? tana rike da
kwalar me unguwan ta lakace Masa hanci tace an mareka,baka ga na girma ba to na
balaga dattijon banza, ta zaro Masa idanu tare da furta balaga ce ta jawo, na rika
na tatira na tumbatsa, tayi fatali da rawaninsa ta shake shi sosai,mutane suka taho
suna cewa dan Allah Chikar gayu sake shi kina mace a unguwar Nan kowa yasan ke
saliha ce,Chikar gayu tace duk Wanda ya rabamu Allah ya isa,kar Wanda ya sake ya
rabamu wlh duk Wanda ya rabamu iyalansa ma sun shiga uku,mutane suna ta mamaki,
wani a ciki yace Chikar gayu da a baya ko yatsa aka sa mata baza ta iya cizawa ba
ita dai barta da gayu.

Chikar Gayu tace to yanzu gartsa yatsan zanyi,mutum ya sa min yatsan a baki ya
Gani idan ban gartsa Masa cizo ba kafira nake, koma na fille yatsan,Kuma wallahi
fada bai mutu ba bari naje na huta zanzo har gida sai na hanaka Shan ruwa a layin
Nan,bari naje naga dangi zan dawo a Yar dabata zanzo,Me Unguwa yace sai na daure
ki,ta hankada shi tana haki tayi cikin gidan Me unguwa mata suna girkinsu a murhu
sai kawai Ganin Chikar gayu suka yi ta daki tukunyar tayi foli foli da ita abincin
Dake ciki ya juye a kasa,Mata da yara sai kowacce ta nufi dakinta ta rufe,Chikar
gayu ta duba kajin gidan gonar me Unguwa da yawa a katon cage Yana kiwo ta bude su
tare da Koro su waje tace duk ku fice Dan ubanku,sai Kaji suka yo waje tatatata
suka yo waje suna kuka kuyat... kuyat...kut..kutt..kut,ta kwance akuyoyin me unguwa
ta Koro su waje kofar gida suma,fitowa tayi ta ce zan dawo ne sai ka fada min
abinda na Maka kayi min sharri zan dawo ne,gashi Nan kullum tsiya tsiya da kai kana
cikin birni kana kiwon akuyoyi gidanka kamar na kauye, daga yanzu gaba ni da ku har
yarana da jikokina da iyali na,Me unguwa Yana dafe da kumatu Inda yasha Mari yace
sai naga bayanki,idan har Ina sallah to ni Kuma sai na nuna Maka banje gidan yari a
banza ba,gidan yarin da kayi sanadin shigata to Kai na shigarwa,idan ba Kai
asararre bane muna alaka da Kai ta jini amma Kaine munafuki ko,zaka ga tantirin
iskanci me maiko.
gidansu ta nufa ana ta cewa ga Chikar Gayu ta fito ga Chikar gayu.

Bayan kwana uku Beauty ma Allah yayi tayi sallama da kowa itama,ranar da
Beauty zata fita aka kawo wata budurwar,Beauty tace yanzu duk ba kuka kike ba sai
nan gaba zaki fada,ki saki ranki ki tsula tsiyarki Yar nan duk Nan mu da kika ganmu
tantirai ne,mu da kanmu mun san ta wani bangaren ba kyau bama ji gidan masu laifi
ai gidan tatirarrun Yan iska ne,budurwar ta Kalli Beauty kawai tana Jin wani
kunya,Beauty ta Dora hannu a Kai tare da furta Laaaaaaaa Kunga kunya take ji cewar
Beauty,su Azima suka ce da sauranta lallai,ke a Nan ba kunya Dan ubanki wallahi ki
warware ko kici duka a gidan nan ba a mana kunya yanzu kyaji jiki cewar Azima da
wata dattijuwa Yar duniya.

A ranar da yamma Beauty ta fita taje Wajen signing,ma'aikatan suna tayata


murna,Beauty baki yaki rufuwa kowa ta gani sai gaisuwa Ina Kwana,idan ya amsa ma
sai tace Dan Allah mu sake gaisawa Kuma gaisuwar da wani Shoky take kwasota ta duka
ta kwaso tace Ina Kwana ta watsawa mutum shokynta,dariya ta dinga basu, Daddynta da
kansa yazo daukanta suna ta murna ta shiga hadaddiyar mota suka tafi gida.
Naila bata San Spark shima Yana Shirin fita ba sunyi muguwar shakuwa kullum
suna tare, tare suke yin komai Kuma Bai nuna yasan ba mace bace, Ranar da za a tafi
dashi kotu ranar ya samu Naila a part dinsa tana zaune tana Shan lemo da cake,ya
fito cikin shirinsa ,a gefe ya zauna a kusa da ita yace Jamilu zanje kotu,gaskiya
ta bayyana akan sharrin da aka min

Naila zumbur ta mike tsaya tayi rau rau zata yi kuka,shima tsayen ya mike tare da
rike hannayenta biyu ya bata labarin me Mama tayi, ya fada mata halin da ake ciki a
nutse,ai Jamilu sai kuka sai kurruwa da burburwa,kasa ta sulale tayi zaman Yan bori
tana tumami a kasa wayyo Allah na shiga uku kowa sai ficewa yake Yana barina,Ina
zan sa kaina Beauty ta fita itama gashi kaima, hawaye rabe rabe a fuskarta sharkaf
tana kuka harda shidewa tana furta way way way way ihihihihi wayyo zuciyata ta dafe
kirjinta tana uban kuka,tausayi ta bawa Spark yace bance fa zan tafi na barka ba ka
daina kuka,ya tasheta tsaye ta mike da kyar tana tangadi kamar Yar giya,rungumeta
yayi a hankali a kirjinsa tana ta kuka Yana bubbuga bayanta a hankali,a nutse yasa
hannayensa masu taushi tare da tallafo fuskarta ya shiga goge mata hawayenta amma
wasu bulbulowa suke kawai, hannu biyu ta sa ta riko rigarsa gaban kirjinsa tayi
baya da kanta tana rasgas uban kuka, yace amma da nasan haza zaka min bazan fada
Maka ba,kayi shuru Jamilu,Naila tace sunana Naila ni ba namiji bane wlh, Spark ya
kalleta sosai yayi dariya yace ai na sani tuntuni, kawai kallonki nake,tana
shesheka ta furta yaushe ka sani a Ina? murmushi ya saki yace nasan kai mace ne ba
tun yanzu ba sunanki ne kawai ban sani ba,Ashe sunanki Naila nice name,Naila duk a
rude take tace na cire abinda nake daure kirjinta da shi taba kaji ni Macece,Spark
yace ni da na kalla wai with my two Kworo Kworo eye,kallo fa nayi ni Kinga gani ya
kori ji,ki bari na dawo zamuyi zancen,kici gaba da zama a jamilunki please kafin na
fitar Dake,ai kace baza ka tafi ba,idan ban tafi ba taya zan fitar dake to? Naila
ta sake fashewa da kuka,yace na fasa bazan tafi ba zan zauna,da kyar ya lallabata
tayi shuru,idonta yayi jajir har ya fita tana hawaye.

Spark bayan an kaishi kotu da matakan tsaro a motar gidan yarin,Mima ya fara
gani ya dauke kansa,Mummy ya gani wajenta ya tsaya ya gaisheta ta rungume shi tace
Dana I miss you,ya furta me too,Rafeeq ya mikawa Hannu suka tafa da Kamal shima
suka gaisa,bayan duk wani bincike kotu ta wanke Spark tas bashi da hannu a kisan
Asmau sannan Mama Kuma an yanke mata hukuncin daurin rai da rai,tana ta
kuka,yaranta suma sai kuka suke na bakin ciki,ana fitowa daga kotu wai Spark ya
bisu su tafi,Spark yayiwa Wanda suka zo dashi Yana da abubuwan yi a ciki akwai
kwangilar gyaran kofofi da zai musu shi lallai a Maida shi ciki sai ya gama zai
fito,Har kudi ya basu tun a mota,Su Mummy suna kallo Spark yabi motar gidan yari
suka koma ciki da shi, to da uwar kudinsa.

Naila tana palonsa ta zuba tagumi tana ta wani sabon hawayen Spark ya shugo
yace au kukan kike yi dama? Naila tana kuka tace nidai ka zauna karka tafi,Spark
yace Tantiriyata ke da na sanki da juriya,jajirtacciyar ce ke fa,kici gaba da
fitowarki a Jamilunki karki sake a gano har na samu ki fita please,Naila tace to
kawai yace ko ke fa,Baki murmushi ba? Harararsa tayi tana goge hawaye,da kafadarsa
ya Dan biki tata kafadar kadan,kansa ya dora a kafadarta yana karewa fuskarta
kallo,janye jikinta tayi da sauri ya koma zai kwanta a cinyarta ta mike ta canja
kujera,dariya yayi yace ki dakko hijab dinki ki daina boye boyen sallah,kamar an
dinke bakin Tantiriya,tunda Spark zai bar gidan shike nan Kuma ta rasa sukuni,Bata
kazar kazar da surutu ko wani Abu,Su kansu a gidan yarin ana mamakin Jamilu ya
daina walwala Sam,Yar dariyar da yake bawa mutane ya daina an rasa dalili,su Malam
Sharu har tambayar Jamilu suka yi wai meke damunka ne Jamilu? Yace ba komai
kawai,Su Dan Indo,Goje sunyi sunyi suji meke damun Terror Jamilu amma basu gano
komai ba.

Bayan kwana biyu kullum Spark aikin lallashinta yake amma Jamilu ya daina
walwala,yace idan baza ki dawo dai dai ba zan tafi wlh,Naila tace ai dama nasan
zaka tafi din mene to ka tafi mana Dan Allah Kafi ruwa gudu,Spark yayi dariya yace
shike nan, washe gari ranar Ziyara,ranar Beauty zata zo wajen Jamilu, Chikar gayu
zata zo taga waye Spark da ya mata hanyar fita, Yaya Mohsin da Umma sunzo yau su
biyu,Naila ta fito jikinsa a sanyaye, tana zuwa ta fada Jikin Mohsin ta dinga rusa
kuka,abinda ya bawa su Umma mamaki kenan,gaba daya sai ransu ya jagule,ba haka suka
San Naila ba, duk yanda akayi da matsala,Mohsin ya riketa Yana lallashinta,yace
menene Naila? Naila taci gaba da kukanta da kyar aka lallasheta,yau ma'aikatan ma
da take musu habaici sun samu lafiya shuru bata ko kulasu ba,Mohsin da Umma da wuri
suka tafi jiki a sanyaye wannan zuwan bai musu dadi ba Sam,halin da suka ga Naila
ya tashi hankalinsu matuka.
Suna tafiya aka sake kiran Naila tazo inji Beauty,Beauty ta dauki wani mugun
wanka na masu kudi,Leshi ne a jikinta me masifar tsada fari da
golden,mayafinta,jaka da takalmi duk golden kana Ganinta kasan ba karya Malam,Naila
ta fito da Maka Makan kayanta na Maza,Beauty ta zubawa Jamilu Ido tana mamaki tace
ai wannan bai fi mate Dina ba a ashe yaro ne amma gaskiya wannan kamarsu daya da
mace,amma ba komai tunda Ina son Jamilu yaran ma ai sunfi iya soyayya,da fara'a
Beauty ta karaso tana karkada mukullin motarta me tsada,Zama tayi tace Jamil harda
gyara sunan tana dariya,Jamilu Murya ya bude irin namiji sosai yayi murmushi, yace
Babyna barka da zuwa ,Beauty kauna ta ratsata ta mike tsaye tace yau gaisuwa me
kwaso shoki zan Maka tasa hannu biyu ta wani kwaso wawan shoki ta dago tana cewa
Ina Kwana,Naila ta saki dariya tace a gaisuwar ma harda me Shoky?

Beauty wayarta ce tayi kara ta daga waya tace Chika kin karaso? Chikar gayu tace
Ina gate yanzu zan shugo,Chikar gayu ce me napep ya sauketa ta Sha atamfarta riga
da skert sabuwa ta coka daurin ture kaga tsiya ga wani glass ta saka abinta ta Sha
kyau,tana zuwa suka rungume juna da Beauty,Chikar gayu ta ajiye Jakarta gefe tace
gaisuwa me albarka tace Shegiya Beauty ya gidan?Beauty tace lafiya Yaya me Unguwa?
tace tuni na gama Episode 1, Episode 2 zan shiga.

Beauty tace ga fa my man Jamilu na ta nuna Jamilu ,Chikar gayu ta Kalli Jamilu ya
dora p-cap dinsa yana tsaye yana bouncing yana bubbudawa irin namiji din nan
hannayensa biyu cikin aljihunsa, Chikar gayu ta Kalli Jamilu tace Beauty anya baki
cuci kanki ba kuwa,wannan me zai iya Idan anyi auren,Naila ita abinda ya dameta
shine tafiyar Spark da zai bar gidan bata su take yi ba ma shi yasa jinsu kawai
take,sunyi hira sama sosai Jamilu ya koma ciki,Chikar gayu tace wannan zubin
Dandaudu gare shi Kinga Beauty wlh ki kama namijin gaske wannan me zai iya,taba
Golden Globes ma gagararsa zaiyi,karki aure shi fa tun a daren farko aji
kunya,Kinga Beauty Ina jiye miki, Beauty tace ni Ina son abina haka gashi kyakyawa
haka.

Suna nan Spark ya fito duk suka bishi da kallo,taji ana gaishe shi ana kiransa da
Spark,Beauty tace Chika gashi can shine ya fitar Dake,Chikar gayu ta mike ta isa
Inda yake,bai san tazo ba yaji mace tace Yaya Spark, da mamaki yace to wace kuma a
Ina na samu Yaya a gidan Nan,ya juyo Chikar gayu tana murmushi tazo ta rusuna tace
Ina Kwana,yace lafiya Alhmdllh,nice wacce Ina cikin mutanen daka fitar masu kananan
laifi, Allah ne yasa aka zaba dani a Wanda zaka fitar,amma magana ta Allah laifina
ba karami bane amma ikon Allah ba yanda za ayi dani, dake ba hakkina haka aka fitar
dani a cikin masu kananan laifi,zuwa nayi dama na ganka nayi Maka godiya,naji ana
ta Spark Spark nace sai kace wayar cellular ashe kuwa gaka Mashaallah Dan chamai
dakai,Allah ya saka da Alkhairi,ubangiji yasa ka shiga Aljanna silar haka,Allah ya
baka mace ta gari,idan kuma kana da mace to Allah ya baka ikon Kara mata
kishiya,kasan mata biyu sunfi kullum ba hutu shine ka cika cikakken namiji,yau kana
nan wajen taliyarka da Miya,gobe ka koma wajen shinkafarka da wake,amma ace mace
daya kullum fa taliyar ce ai dole ka gaji, to dama godiya nazo yi na gode na gode
sosai,Spark tunda ta fara magana yake saurarenta amma tunda yaji tayi shekaru a
gidan yari yasan zata aikata ma abinda yafi haka, ta fitsare a gidan yari, yace ba
damuwa na gode nima,tace to ta juya wajen Beauty tace muje gidan naku to yau a nan
zan Kwana gobe sai Kaduna.

Ana gama da ziyarar Maza aka bude mata,su Chikar gayu an hadu ana ta caf cafkewa
suna iya shegensu,da mata kawayensu,Beauty motarta cike da tarkace na ci snacks ta
dinga rabawa mata Wanda suke tare,Wanda tasan talakawa ne futuk harda kudi dubu
biyu biyu ta bayar da yawa,Chikar gayu su ba masu kudi bane ama da ledarta ta
alawoyi da biscuits ta rarraba musu tana cewa ayi hakuri mu gidanmu ba harka,sanda
na koma gida ma shinkafar gidanmu ta kare da tuwon masara na fara karo,ayi hakuri
gidan mu ba harka mu Kam,ana ta dariya.

Ranar Monday Spark ya shirya barin gidan,Naila tana zaune yace a nan VIP zaki
zauna ke kadai kin jini ko? Naila tace ae,yace bana so ki dinga shiga mazan nan
idan ba dalili kinji,tace ae,yace karki bari a kalle min ke duk Wanda ya kalleki
ban yafe ba,tana jinsa yace zan dinga zuwa ko yaushe ba sai lokacin ziyara ba,ki
zauna zan fitar dake kinji,tace to tana share hawaye.

Yace ga kayana nan kiyi ta sawa komai zan dinga siyo miki kinji,Naila tace
t.....t..to ta fara kuka,Spark yaga kukan Naila bazai kare ba ya gama shiryawa ya
Mike ya kwashi wayoyinsa yace zan tafi to? Mikewa tayi hawaye shabe shabe a
fuskarta jikinsa ta fada ya rungumeta tana ta uban kuka,Dago fuskarta yayi a
hankali ya hade bakinsu waje daya a hankali yake aika mata da sako,kafarsu ce ta
gagara daukansu suka fada Saman kujera,Naila tana jikinsa ta janye kanta da
sauri,amma tana jikinsa,cike da shagwaba me hade da kuka tace baka..b...baka fada
min ta ya kasan ni Macece ba,murmushi yayi yace ranar da kika Sume ya bata labarin
komai,idonta ta rufe da wuri tana dukansa a kirji tace shine ka kallar min gareji
na,Ashe Kaine ka ajiye min pad,yace yes kinyi amfani da abarki Kuma kika ce mutanen
boye ne,dariya suka yi wayarsa tana ta ringing Rafeeq ne yake kiransa zasu tafi

Muje ki rakani, suka mike tare suka fito,dama Yan gidan duk sun san Spark an
gama case dinsa zai fita shi yaga dama ya zauna,Duk da haka sai da suka bi lungu da
sako yayi musu sallama suna ta tayashi murna,Naila sai hawaye take yi ta kasa rike
kukan nata har suka fito bakin gate zai fita ita zata dawo ciki,bai ko juyo ba
tunda yasan kuka take tayi, sai da taga ya kule ta juyo ta dawo ciki,sai data dawo
ta dinga kwarara kuka da ihu ta Fadi a kasa tana ta rusa kuka,mutane da yawa suka
zo kan Jamilu Dake rasgar kuka,Naila kamar ranta zai fita tana cewa da haihuwata
gwara barina,me yasa babu wajen karuwanci a gidan yari gwara na fada yawon ta zubar
,mene amfanina gwara a yanke min hukuncin kisa a harbe ni na huta,me yasa a gidan
yari babu Bariki,gwara na shiga yawon duniya na huta da wannan rayuwa,sai kowa ya
dinga ficewa ana barina nima ai ba hakkina aka kawo ni, kowa a gidan idan yazo sai
yaga Jamilu kuka yake tsakaninsa da Allah abinda basu taba gani ba,duk sai ya basu
tausayi sun gane shakuwar da sukayi da Spark ne,da kyar su Goje suka lallaba Jamilu
ya koma dakin su na malamai,yau Tantiriya bata bari sunyi karatu ba kwana tayi tana
uban kuka tana wayyo gwara zuciyata ta buga na huta,ni a yanke min hukuncin
kisa,Malamai suna ta kallon ikon Allah,Malam Sharu yace ba a son bawa ya dinga yiwa
kansa mugun fata ko da ace da wasa ne,Jamilu yace karku dameni zan sawa dakin nan
gobara iiiiiihihi an fitar da budurwata Baby Spark,Allah sarki yau babu
caskalewa,tsotsiyar da muka Saba babu wayyoooo....Malam Garzali ya zaro ido yace
gwara daya bar gidan nan,Malam Sharu yace ban yarda Spark wlh Yana harkar banza ba
iskancin Jamilu Terror ne kawai yake so ya bata Masa suna,ai kowa yasan Jamilu
tataccen Dan duniya ne a gidan nan ba ruwan Spark.

Jamilu kwanciya yayi yace tsotsiya yau babu me min tsotsiya ya tafi, ta sake
fashewa da kuka ta mike zaune da tsakar dare tana bubbuga bed tace yau ba Wanda ya
isa yayi bacci a dakin nan,Malam Garzali ku tashi,Malam Jilani Malam
Jilani,Sharu ....duk suka tashi tsakar dare taki bacci ta hana Yan daki
bacci,Malam Jilani yace Spark ya bar mana jaraba,sand ya dauke Jamilu har mun samu
lafiya yanzu ya dawo.

Spark tunda ya bar gidan hankalinsa ya tashi gaba daya zuciyarsa tana kan
Naila,Sallama yayiwa ma'aikatan duka ya rarraba musu kudi suna ta godiya suna
tayashi murna ya shiga mota,Rafeeq yace yau anyi sa'a ka fito yace hmm gangan
jikina tana prison wlh,Rafeeq yace hmm Allah ya kyauta, ana ta Shirin tarbar Spark
amma Spark direct katafaren gidansa ya wuce babu gidan Wanda yajema a ciki,Bai je
wajen Mami ba bare Mummy,dangi duk sunje Murna anyi girke girke an dau wanka amma
akace ai ya wuce gidansa ma,Mima tace zai aikata ai mai hali bai fasa halinsa,duk
Mummy ce ta lalata yaron nan.

Naila kuwa gari na wayewa tace baza ta sabu ba, fita daga gidan nan dole, Ina
Sam bazan iya rayuwa ba spark ba,ko dai na haura katanga na karairaye ko Kuma na
fita ta ko wacce hanya,gidan yari ya daina min dadi,ya sire min,fitowa tayi buguzun
buguzun sai wajen Dan Indo,ta kira Dan Indo ya fito suka kebe gefe,tace Dan Indo so
nake ka wuce min gaba,so nake ka daure min gindi a kasar nan ka hada da duwawuka
duk ka daure min tam,Dan Ido Yana busa sigari ya sheke da dariya,yace ka gaji kenan
Jamilu? Na fada maka aje aci uwar wacce ta maka sharri a gaban kowa ta tonawa kanta
asiri a fitar dakai kamar Inda aka fitar da Spark Kai kaki,Jamilu yace ba wannan ba
ka bar min wannan a hannuna amma a canja wata shawarar,Dan Indo yace to mafita daya
ce ranar Ziyara zamu tada fada idan mun fito su Goje zasu fasa taron
ma'aikatan,zansa yarana Dake min aiki a waje suzo bakin gate su tarwatsa masu
tsaro,Kai Kuma Jamilu ka tsaya kusa ana fara fadan karka ji tsoro kawai ka sheka da
gudu ka fice Wanda ya gudu ya gudu Kuma wlh a kasar Nan duk Wanda ya gudu daga
gidan yari to ya Sha ba'a komawa ayi bincike bare a shiga nemansu wanted kawai
kyale su akeyi Wanda kika ga an dawo da shi to tabbas sai idan wanine a unguwar
yaje ya fadawa hukuma a boye amma ba a zuwa neman mutum idan ka tsira ka tsira
kawai Jamilu,idan kana da makiya a layinku kawai ka yanka wajen Lagos ko Abuja idan
komai ya lafa sai ka dawo.

Jamilu yace Allah ya kaimu ranar Ziyara zan fada a gida kar azo min ranar yace
yawwa ka shirya kawai.
Tana murna ta koma part din VIP Inda Spark ya bar mata ya biya kudinta a nan
take sallarta da komai nata a nutse ba tsoro da fargaba,yau da dare ya kirata a
waya yaji ta daga da murna,yayi farin ciki matuka da yaji yanda ta saki jikinta ta
hakura da komai.
Dariya tayi haka kawai tace Spark,yace Na'am Jamilu Kafi wuta zafi,dariya ta
sake yi,yace ya gajiyar kukan to? ta fara shagwaba tace ni kayi sauri Allah
kazo,Spark ya murmusa Yana Jin wani farin ciki yace sai ranar Ziyara,ban yarda
ba,yace bazan samu damar zuwa ba wannan satin ma sabo da Ina gyara Office dina da
abubuwa dai alot,tace to shike nan Allah ya kaimu,suka ci gaba da hirarsu wai nan
duk a friend's suke har yanzu.

Wani ganganci Naila tayi kafin ranar Ziyara ta dinga rubutu me tsayi a papers
da yawan gaske ranar mutane sun shagala a wajen ziyara duk tabi daki dai ta ajiye
takardun,ko Ina,dakin su Malam Sharu ma ta ajiye musu basa dakin,ta fito duk wani
lungu ta dinga jefar da takardun ta kwaso komai nata na kaya ta kawo dakin su Malam
Sharu ta ajiye a tsakiyar dakin tayi waje wajen da ake zuwa ziyara duk an fito

Hanan ranar tazo domin tonawa Naila asiri a gaban kowa ta fadawa duniya ita
macece ba namiji bace,tunda taji su Umma baza suzo Ziyara ba shine tayi karya tace
zata je gidansu ashe gidan yari tazo domin tozarta Naila, Naila kuwa ta Kalli
DanIndo suka yi signa,bata kula da Hanan ba,Dan Indo ya baza yaransa a wajen ya
musu fito,Goje yazo ya fyalle Yar wuka ko Ina ya samo oho suka fara dure duren
ashar,

Sai suka fara dukan juna suka hargitsa wajen ziyara,Goje ya daka tsalle ya ballo
rashen bishiya,a wajen suma yaran Dan Indo da wasu Wanda akayi tsarin dasu suka yi
kan ma'aikata da duka da ashar kowa zaneshi suke a wajen har masu ziyara ciki harda
Hanan suka kamata kamar Allah ya aikosu da duka ta ko Ina bulala take karba,wani
Yana lafta mata ya fasa mata gefen Ido tayi waje da gudu tana faduwa tana
tashi,suna danna ashar suna fada a junansu ji kake rudududu kamar dawakai,suka nufi
gate,Naila ta kwarara ihu tayi bakin gate wajen ma'aikata,su Dan Indo da jifa da
manyan duwatsu,duk ma'aikatan da bindiga wasu amma tafi gaban ma su fara harbi su
kansu ta kansu suka yi,Dan Indo ya fisgo bindigar wani Ma'aikaci ya danata ya dinga
Harbin sama, harbin iska tas tas,kafin kace me har ma'aikatan sun watse,Naila tabi
kofar fita tana cewa dama macece ni yeeeeeeeeee ku matsa dan ubanku ta fice fit ta
Sha kwana gudu take ba ji ba gani,mutane da yawa Yan gidan yari aka fara tserewa an
samu mutane masu laifi daurarru sunfi mutum ashirin Wanda suka fece kafin su Dan
Indo su gudu can cikin gidan yari can dakunansu suna dariya,Su basu damu da guduwa
ba,ba abinda ya damesu sunfi son ma gidan yari domin ko sun fita sai an dawo dasu
sai sun sake laifi an dawo dasu,Kamar gidan gado haka suka Maida gidan.

Da kyar aka kawo sojoji da ma'aikata over suka daidaita gidan yarin ranar ba
ziyara ta kare Kuma,kowa ya gudu an fasa ziyara abinci ma duk Wanda suka zo dashi
sun kifar da abincin sunyi ta kansu,Wasu daga cikin Wanda basu tsere ba Dake kowa
yasan Jamilu sunji da kunnen su yana cewa yeeeee mace ne dama ni a suffar Maza
nazo.

Anan Kuma kowa a ciki aka dinga tsintar takardun Jamilu a ko Ina a gidan daki
daki kowa ya karanta sai takaici da bakin ciki da cizon yatsa.
Malam Sharu suna shugowa suka ga takarda da komatsan Jamilu suka dauka suka fara
karantawa kamar Haka

Ni Jamilu Terror Wanda aka fi sani da Tantiriya dama karya nake ba namiji bane
ni,sunana Naila,harda rubuta abinda ya faru da ita tun daga zuwanta Abuja har
shigowarta gidan yari, in short tayi bayani.
Idan baku yarda ba ku duba kayana na dakin su Malam Sharu,Malam Sharu ko gama
karantawa basu yi ba, da gudu suka bude kayan Naila,da Hijab suka fara cin
karo,suka dakko panties na mata suka dakko vest ta mata,sannan suka dakko seletape
da bandage,sai ga pad ma sun zaro,takardar suka Kara dubawa suka ci gaba da karatu

Wannan Selatape da shi nake manne albarkatun kirjina,sannan a karshe Panties


Dina na barwa malam Sharu gadon su halak malak ya dinga sawa domin tunani,Kun nuna
min kauna na gode na gode kwarai,shi yasa na nemi dakin Malamai na zauna sabo da na
tsira da budurcina.
Naku har kullum
Jamilu Tantiriya.

Ai Nan take labari ya cika gidan yari har bangaren mata sai da suka ji ankai
mace bangaren Maza a matsayin Namiji.
Dan Indo daya karanta takarda yatsa yasa a Baki ya kwarara ihu yace Inda nake
neman mace Ido rufe na samu na kwashi harka,Goje yace wlh da nasan macece ni zan
fara yi mata filla filla, kowa ya karanta takarda sai zage zage da bacin Rai,aka
cika dakin su Malam Sharu kamar ana ganin kayan lefe haka ake kallon kayan Naila
filla filla ana bakin ciki,Scoler yace da na sani ai ko nono na taba, ranar Maza
group group suka yi ana tuna abubuwan da Jamilu ya dinga yi na mata amma suka kasa
ganewa macece.
Wasu suka dinga zagin su Dan Indo da suka fitar da Jamilu a sadaka.

Wanda suka dinga tura min 500 na gode kwarai da gaske,Kun San novel Dina baya wuce
300 amma Kuna tura min 500
Na gode kwarai da gaske
Allah ya saka da Alkhairi.

Aci gaba da sharhi


Ina godiya.

1,2,and 3 za ayi Kuma 300 ne duka in ka siya sau daya shike nan

BOOK 1
FREE PAGE
Accnt no
0175487861

Katin MTN
08061929616

Yan Niger ga number da zaku tuntuba


+22790795939

AsmaBaffa
[12/11/2023, 9:27 PM] AsmaBaffa: 🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

41-45

END OF FREE PAGE

1,2,3 duka 300

Accnt no
0175487861
Asmau Garba Muhammad Gtbank

Katin MTN
08061929616

Yan Niger
+22790795939

OFFICIAL

BY
ASMABAFFA

SADAUKARWA GA
AIDA MAMAN TASNIM

Page naki me Maida book Dina audio jinjina


Gare ki Auntyna
HAUWA S ZAIRIA

MASU AUDIO BAN YARDA A JUYA MIN NOVEL ZUWA AUDIO BA


Dandaudu washer ne ya shugo da gudu cikin su Dan Indo da takardar Jamilu a
hannunsa yace me nake gani haka? Su Dan Indo sunyi jugum jugum,suka ce da gaske
ne,yace yanzu naje dakin su Malam Sharu na duba kayan Jamilu,ya daga pant din
Jamilu na mata yace na rabauta da wannan ni wlh Ina so tunda macece ta saka wannan
gwaurantaka da me tayi kama ashe wasu sun gudu harda su lukaku sun fece da
Babangida,da Imrana Dan fillo,Kai harda Bajahilci ya fece wlh,Dan Indo ya mike
zumbur Yana busa sigari yace amma Jamilu ya raina mana hankali amma ni nayi
sanadiyar fitarsa Kuma ni na dauki alkawari ni zan dawo da Jamilu gidan yari Kuma a
namijinsa dole Dan uwatas sai na Mori wahalata,Goje yace ka daina cewa Jamilu
sunansa Naila fa yace gashi a takarda a rubuce,Kai Dan uwarka muga takardar nan na
Kara karantawa Dan Indo ya sake karanta takarda yace karya ne wlh mu zaki wa
iskanci yarinya,mu fa Yan kasar Nan ne,karya ne wlh,yanzu kun gane kowa yayi shuru
da zancen nan kar ma'aikata suji,idan aka dawo da ita ba uwar da zasu mata bangaren
mata za'a maidata,amma idan na dawo da ita a namijinta haka za a maidota
cikinmu,Kai wlh ko ta Katanga sai na sa an wullo mana da ita

Nan take Dan Indo ya bugawa yaransa Dake waje waya Wanda yake basu aikin kisa
ko wani aiki yace kuna Ina? Suka ce mun dauki hanyar Kaduna,yace ku dawo baya ta
haihu ku koma a cikin yaran da suka bar gidan yari akwai wani me suffar mata
sunansa Jamilu Tantiriya zaku ganshi da riga da wando na Jean wasu Maka Maka wandon
kamar buhu sai a sakaka a ciki a daure,to ku bisu duk Inda kuka ganshi ku dawo
dashi,idan baku ganshi ba ku kirani zan Nemo address din gidansu duk Inda yake
sannan zaku ga gashinsa duk tara gashin namiji Dan uwatas bazai tara gashi irin na
Jamilu ba,sannan Daadaa ce a kansa,suka ce an gama oga suka yi youturn nan take
suka juyo.

Scoler ne ya taho Yana karairaya yace oh ku kuwa ku kyale yarinya karku keta
mata haddi wannan ba daidai bane tsakani da Allah,indai da so da Amana ai ruwa ba
zai ci gwani ba,sabo da Allah da Manzo anbi an ishi Yar uwa,yarinya ta fita,tunda
taimako kayi tsakani da Allah ku kyale Yan mata Dan Allah ta tafi da kayan nononta
can Spark ya samu na zuka, dama watakila ya Saba a nan anga wajen hutawa yarinya
taga me kudi ohh ke duniya ni naga kiyayya,yarinyar nan Jamilu kiri kiri taki
kaunata anga me kudi an manne Masa ah ahayyeeee wuuuuuuu Ashe tana karbar Hallare
inji Jamilu da fada tace Hallare,to Dan Ubansa wallahi ba ruwana da fadar Naila
Jamilunsa sak babu batun canja suna,
Shewa Scoler ya sake yi tare da dukan cinya yace Shegen kaya Spark ai tunda naga
Dan banzan dan Nan Yana wani shining Yana sheki Inda kasan da inji ake goge masa
fata kullum nace ba banza ba Ashe dai madarar Nido yake samu wajen Jamilu,yarinya
can fa ta tare wajensa inji washer daya Dan Daudun,ai dole Jamilu tayi kuka to an
Saba kullum da bankade between inji bature yace Between her leg ahayyeee chassss
Spark ansha gara.
Dan Indo yace shi yasa yarinyar nan bata taba shiga cikin gwamitsin Maza ba,ba
a ganin sallarta,Ashe tasan me take boyewa,yau shekarata uku rabona da mace ah dole
a dawo min da Jamilu karya ne wlh cewar Dan Indo ya mike Yana zaga wajen.

Goje yace har na hango kaina da Jamilu Ina ninkaya cikin bahar maliya,Yan Daudu
suka saki shewa, Inshaallah baza ku samu sa'a akan Yar uwa Jamilu ba,bi'izinillah
ta fita kenan wlh ah haka kawai kune kuka kera mata Between din? bafa ku bane,ita
kanta hattana kirjinta Breast din Nan gani tayi sun fito rana tsaka kwatsam ta Sha
jinyar abinta tun suna kurji har suka nuna yo sai ace za ayi mata Iko,Dan Indo Mari
ya zubawa Scoler,Scoler ya kurma ihu yace naga wuta naga wuta Yana fifita fuskarsa
da hannu yace washer zo mu bar wajen Yan mazan Nan kar su nakasa mutum, Kuma
dukkanku kwalelenku Jamilu ya fita kenan ba dawowa.

Naila kuwa tunda suka fita da wasu mutum ashirin da biyu kowa ya tarwatse ya
kama hanyarsa daban,Naila ita da Bajahilci suke sheka gudu,sabo da gudun tsira
Bajahilci baiji sanda Naila tace ita macece ba Sam,sai yace Jamilu biyo ni kawai
kasan ni Ba Jahilci sunana kaina baya kullewa muje karka je gida Kai popular ne wlh
duk Wanda ya zama popular a waje to da wuri ake ganewa, Naila tana hakki tana gudu
magana ta kasa sai daga Kai kawai,Dan bandage da aka daure kirji ma ya zame ya gudu
garin gudu, amma basu tsaya ba yace bafa mu tsira ba Jamilu za a iya biyo mu Kaga
Sha kwana ta wancen lungun ka san fa a wajen gari muke sosai ta barauniyar Hanya
zamu bi mu fada cikin gari idan muka bi direct hanyar mota za a iya kama mu.

Naila tasha kwana ga wani shegen katon gidan gona ana ginawa anyi Katanga da
tsayi Kuma,Bajahilci yace haurawa zamuyi fa Jamilu,Naila tana hakki ta tsaya da
kyar ta iya cewa bazan iya ba,Bajahilci yace bari na gani ko zan iya dagaka,ya kama
kaurin Naila ya dagata sosai hannayensa a kaurinta tayi tsayi sannan ta kama
Katanga tana Bajahilci matsa gaba gaba,ya matsa ta kama sosai ta haure ta dirga
kasa,lokacin taji karar fadawar wani abu kamar karfe daga jikinta,amma Bata kawo
komai ba,shima ya hauro yace Maza muje suka ci gaba da gudu yi suke ba ji ba gani
har magriba ta fara,lokacin su Kuma yaran Dan Indo da mota suke ta yawo ita Kuma
Naila Bajahilci ya hanata bin hanyar mota yace za a iya kama su.

Suna ta gudu har suka kusa isa titi,Bajahilci yace to Kaga nan ba a samun abin
hawa na haya yanzu ka iya Hawa bishiya? ai Naila dama ita tun a kauye ta kware a
rashin ji tace duk tsayin bishiya wlh kamar biri yace hau muje Jamilu,Naila ta kama
wata katuwar bishiya dalaf dalaf ta haye can sama, Bajahilci ma ya hau,Naila tace
kishirwa nake ji wlh,yace sai dai kuwa kayi hakuri,ni kaga daga nan tashar Lagos
zan wuce sai Lagos kafin a gannni Kuma tab Allah yasa bani da iyaye,Naila tace ni
gida zanyi yace wlh sai kayi a hankali Jamilu zasu iya bibiyarka har gida kayi suna
a gidan,ka boye kanka wlh karka bari ko a layinku a San ka gudo yanzu shigar dare
za muyi, Naila ta gaji ta kwanta a Saman reshen bishiya, ta kasa magana ma sabo da
gajiya da yunwa ga kishirwa ta dameta,Aminu ba Jahilci yace Ina wayarka Jamilu ka
cire layinka fa ka karya shi wlh Kai wayar ma kanta ka jefar da ita za a iya
tracking,Naila ta fara duba waya a jikinta tasan tabbas da waya ta fito a garin
gudu ta jefar da wayarta ma,tace ta Fadi a hanya wlh,wayyo Spark gashi ban rike
number ba dame zan kira shi na gama yarda da wayata a hannuna,ai ni wannan fitowar
da nayi bata da amfani,Bajahilci ko magana baiyi ba shi dai ya cire wayarsa ya
rabata da layikansa.
10pm na dare Bajahilci yace yawwa yanzu zamu iya tafiya sauka Jamilu,Naila
jikinta ya mutu murus ta gaji Kafadunta sun kumbura wani wajen ma taji ciwo,ta
sakko a hankali shima ya dirga suka ware sai gefen hanya yace kar mu tsaya shiga
Napep cire rigarki ta sama ki jefar, Naila ta cire ta jefar a kwalabati sai t-shirt
me dogon hannu yace yanzu kin koma arniya kin gane karki nuna kamar a gigice muke.

Naila tace to suna tafiya Tantiriya komai da ruwanka da sunzo wajen mutane sai
ta fara yiwa ba Jahilci yare tayi hauka ta hada da fillanci harda wani Chinese na
hauka duk yi take,Bajahilci sai ya basar kawai Yana irin murmushi Yana kallonta
Yana daga Kai irin Yana ganewa hira suke ai.

A haka suka kwashe kusan 3hrs sannan ya nemi Napep suka shiga,ya Kai Naila har
kofar gidan Mohsin sannan yace kana zuwa ka canja kaya karka bari a San ka gudo ni
na wuce Lagos,Naila tace na gode sosai,yace fara bugawa in aka bude sai na
tafi,kamar yasan macece,Naila tace wlh Kaci sunanka Bajahilci yace dole wlh....ta
dinga buga gida,sai da aka Dade Sannan Mohsin ya taso zai bude ga tsoro a
ransa,yace waye?Naila tace Hidaya ce tayi Muryar Hidaya ta make Murya,ai ya zaci ko
gidansu ne ba lafiya fit ya bude kofa ya fito,tace dalla da abin kisa ne shike nan
haka akeyi?,kafin ma ta juyo Bajahilci yasa me Napep yayi gaba sun wuce .
Naila tace Yaya gudowa fa nayi,Mohsin yace Subhannallahi Ina murna Ina haushi,
ya jawota cikin gida ya rufe kofa, yace Naila yanzu ya kenan zasu iya zuwa nemanki
ko mutanen unguwa yanzu in suka San mutum case din kisa ne a kansa zuwa suke su
fada a boye sai azo a sake kama mutum sabo da kar su zauna da makashi a
unguwa,Naila tace cikin rada yi a hankali kar munafuka Hanan taji,yace ai tana daki
a kwance ranga ranga kafarta hannunta daya ya kumbura sumtum kashinta ne ya tsage
na hannu,sannan idonta duka biyun sun fashe sun kumbura sum ko gani bata yi,me ya
sameka? Wai machine ne ya bugeta nidai nace karya ne ban yarda ba.

Yau fa da asuba zaki bar gidan nan dole Naila,Naila tace ai wlh sai naga
iyayena,yace ko kauye fa baza ki koma ba za a iya bibiyarki wlh can za ayi
tunaninki a can kar ma ki nufi can,Naila tace to Ina zani wa na sani? Wanda na sani
number dinsa tana wayata Kuma wayar ta Fadi, Naila tace yanzu dai a dakin can zan
zauna bana so matarka tasan Ina Nan kayi shuru yace to tace ruwa da abinci ta shige
wani dakin daban a tsakar gidan,ya shiga kitchen ya zubo mata abinci da ruwa taci
ta koshi ta Sha ruwa,ta kwanta tana hutawa,Nan take bacci ya kwasheta.

Da asuba ta riga kowa tashi taje tayi wanka sosai tayi alwala sannan ta nufi
dakin Mohsin,bata so Hanan tasan tana gidan tunda ta kasa kunne taji basa love tace
ahh Hallare tayi hakuri yau ba a abin,nasan asuba tayi lokacin fitinar Hallare ne
gwara naje na dakko kayan kafin Hallare tayi tsiya,taleka tare da tura kofar a
hankali,ta samu Mohsin Yana kwance can gefe Hanan tana gefe daya,Naila farin ciki
ya kamata a hankali yanda ba Wanda zai ji tace Alhmdllh Yaya Mohsin ya tsani
shegiya ai na zaci zan ganta a kirjinsa,Allah ya wargaza ku kamar yanda kuka yi
kwanciyar Nan Allah yasa igiyar auren ma tayi haka, ta lallaba ta tabi ta
gefe,Mohsin ta tabawa kafa ya farka,ya gane Naila ce,ya fice da sauri sabo da shima
yayi sallah ya makara,Naila ta bude sip din kayan Hanan a hankali,ta zaro riga da
skert na atamfa wacce take a wanke a goge sabuwa,ta duba layin mayafai Nan ma a
hankali ta zaro kalar atambar tana haskawa da Yar wayar Hanan din Kuma a kusa da
ita ta dauka,ta duba wajen takalma ta zabo me Dan rudu wani sabo shima silver kalar
mayafin,ta dauki jakar Hanan sabuwa wacce jakar takalmin ce ta hada abinta, ta bude
wayar Hanan ta zare layikanta ta zube mata a gefen pillow ta jefa wayar a jaka, a
kan Hanan ta tsaya tace sai kace Ubanta ne ya siya wayar ko Dan koli ne ya siyo ta
fada a hankali kasa kasa tace to na dauke ta yawwa na fada miki Kuma kinji sabo da
haka na fita hakkinki ki ta juya tayi gaba.

Har ta fice sai ta dawo tace in tafi banyi komai ba ai karya ne Hanan ce fa a
gidan,Glass ta hango na Hanan da take daukan wanka wani pink faskeke ta dauke shima
tace kolabo zan fara,yanzu na koma yar kolabo Kuma,sai ta haska kafar Hanan ta
ganta a kumbure suntum,ta haska idon kadan kamar an kawo wuta an dauke ta ganshi
tsabar kumburi ya manne ma da kasan idon,Hanan tayi dariya marar sauti harda rike
ciki duk ba sauti,tasa hannu ta latse idon Hanan,Hannan ta farka a tsorace tana
cewa wayyo idona wayyo Naila ta fisgi kafar me ciwo wacce ta kumbura ta ja da
karfi ta Murda ta saki ta fice fit, Hanan ta tashi tana ta dube dubenta shuru,ba
kowa tana ta kiran Mohsin shi Kam Yana sallah .

Naila fitowa tayi ta koma ta dakko katon hijab again tazo tayi Sallah sannan ta
surfa addua ta mike sanye da hijab,ta fito Mohsin ma Yana idarwa ko ta kan Hanan
baibi ba ya fitar da machine Naila taje ta hau suka bar gidan ta rufe fuskarta da
Hijab din,sai gidan Umma,Suna zuwa Abba ya dawo daga masallaci,yaga Naila mamaki ya
kamashi Naila tana sauka a machine ta durkusa a gaban Abba tace Ina Kwana Abba,da
mamaki Abba ya amsa da lafiya Naila tayi kasa da Kai wai tayi hankali a gidan yari,
tace mun same ku lafiya ya akaji da rashe rashe da bama nan,Abba Dolo yace ei wlh
nan rannan ko sati ba ayi ba Magajiya ta rasu,Magajiya Babar Sani Takwashe,na
manta ma Alhaji me kosan sadaka da watan Ramadan shima ai ya rasu,haka ladi me
abinci ma,Naila tace Allah yaji kansu,Abba ya su Debora,Abba yace suna Nan suna
fama da kallon Maza yanda kika sansu basu daina ba ni yanzu ma kullum sai na
karanta Hasbinallahu kafa Dari sabo da gubar da ke cikin idanuwansu Allah kareni
dasu gashi nan duk da haka ramewa nakeyi gubar idon su Debora ce kawai tayi min
yawa,Mohsin yace Abba ka rufa mata asiri muje Dan Allah gudowa fa tayi.

Abba ya saki salati yace gudowa? Duk tsaron Dake gidan yari kika iya gudowa
Naila, Gwara tun wuri ki koma ciki kafin su damke ki,wannan ai cin amanar kasa
ce,cin amanar hukuma ce, duk da naji dadin ganinki gwara ace su suka sallameki da
kansu, Mohsin yaga abin na Abba ya zarce saninsa yace Kinga muje ciki,Naila ta mike
zasu shiga Abba yace Allah ya tsare Naila amma Ina jiye miki,Umma kuwa da katon
cikinta Wanda ya girma suka sameta ta kafa wutar gas a hancinta tana Kona wata
takarda wacce take nannade da tabar Wiwi,tana shakar warin da sassafe,Mohsin yace
Umma Zafa tayiwa Dan cikinki Illa wallahi,to kawai sai na kashe kaina akansa? ku
rabu Dani,Naila ce ta shiga ta kwace wiwin ta take da kafa tace Yar kanwar mu ko
kanin mu zai iya zuwa da nakasa,Umma tace laaaa Naila ta rungume Naila tana murna
tace ta ya hakan ta faru,Naila tace irin tserewar,Umma tace tsugunu bata kare ba,ai
wucewa zanyi,zuwa nayi na ganku dama ,kina da wajen zuwa ne? Naila tace Inshaallah
akwai mafita ku dai kuyi min addua,Umma tace to shike nan Allah ya tsare a Kuma
tsare mutunci a kiyaye,Banda taurin Kai,Naila tace to ayi a bani shayi na Sha,Mummy
ta duba flask tace akwai ruwa,da sauri Naila ta hada tea ta shanye tace idan su
Hidaya sun tashi ku fada musu na fita daga gidan yari Umma,My love zan wuce ina da
number Dinka a kaina zaka jini Inshaallah,Mohsin yace to Ina jira,leda ta dauka
tare da zuba kayan data dakko na Hanan dalayin wayar Hidaya ta karba

Naila ta nufi kofa tace to sai kunji ni,Mohsin Tausayin Naila ya kamashi,da
sauri ta fice tana ficewa da hijab din Hanan har kasa ta tsaya a zaure tayi kuka
sosai ta goge hawayenta,sannan ta nufi titi da sauri ta shige Napep tana barin
layin yaran Dan Indo suna zuwa gidan su Naila,su Umma sai hani suka yi Yan daba sun
fado musu gida suna bincike,basu kula kowa ba Kuma ba Wanda ya kulasu suka gama
dube dubensu sannan suka fice suna duba wayarsu har gidan Mohsin suna zuwa sai
Hanan kawai,Naila a Napep ta saka layin Hidaya a wayar Hanan data dauka,ta zauna
tana tuna number Spark ko wacce ta kira sai dai taji wani ko wata ya dauka tayi
missing number a ciki ba daidai take hadawa ba,tsaki ta ja ta hada number Beauty ta
kira Allah ya taimaka wannan daidai ta hada bugu biyu aka dauka,Beauty cikin Muryar
bacci tace na'am waye? Naila tace Jamilu ne,na gudo daga gidan yari bani address na
gidanku,Zumbur Beauty ta mike tace ka bawa me napep din waya,Me Napep ya karba
Beauty ta Masa kwatance sosai sannan ya mikawa Naila wayarta,GRA ya shiga da ita
wata katafariyar unguwar,hadadden gida na mamaki a nan yayi parking yace ga gidan
Nan nasan ma me gidan ai yayi fice,Naila Hijab dinta ta cire ta dawo namijinta
sak,Beauty ta kira a waya tace muna kofar gidan,da sauri Beauty ta fito ta biya me
napep kudi ya tafi,Naila ta gyara p-cap tace muje ciki suka shige,bangaren Baki ta
Kai Jamilu ta bashi daki sannan ta koma wajen me aikinsu tace ta hada mata
lafiyayyen Kari.

Naila kuwa sai kallon gida take faman yi tace umm Aljannar duniya bari nayi
wanka,ta mike ta bude toilet da komai da komai a ciki ta sake wanka na musamman ta
wanke gashinta sosai ta fito,body lotion ta Gani a mudubi ta shafa tana kallon
kanta a mudubi tana taje gashin nata Wanda ta warware daadaa din dake kanta,ta
dinga duba tarkacen Dake mudubin harda mayukan gashi da Kuma powder da abubuwa
kayan Hanan ta saka a jikinta har sun so suyi mata kadan sabo da Naila ta fita kiba
ta cika kayan fam fam,ta zauna ta shafa powder harda saka maroon jambaki tayi kyau
kuwa sosai kuma tayi daurin ture kaga tsiya ta tsaya a mudubi tana kallon kanta
tace amma fa Allah yayi halitta haka nake dama....bayanta ta juya tace wai wai
gaskiya Alhmdllh better thing,Ashe haka Allah ya halicceni, Allah na gode Maka dole
in godewa Allah ahhh kalleni Naila,Jamilu, Tantiriya dariya tayi tana shafa
fuskarta a haka Beauty ta shugo ta isketa,wani wawan birki taci da tire a hannunta
tace me zan gani Jamilu?
Naila hankali kwance ta juyo ta bankaro mata kirji tace Kalli kirjina me kika
gani? Beauty tace nono,tace mashaallah to Allah ya albarkace ni da su gasu Nan
mashaallah,Kinga kina da su kema,bani bra na saka ma,Beauty tace dama Kai mace ne
Jamilu? Naila tace wlh haka Allah ya nufa ko na cire wando ki gani? Beauty da
mamaki tace ya akayi kika zauna a gidan Maza.

Ni mamakin ma da nake da ka iya kallo na ba kunya ba komai kace macece,wai


baki ji nauyi na ba? tsakani da Allah daukanki nayi da har zanji wani
nauyinki,Beauty murmushi tayi tana kallon Jamilu mace kyakyawa tace wai yanzu
yaudarata da kayi baki ji komai ba irin kunya? mene haka da suna Kunya? Menene
ma'anarta, Beauty a ranta tace wannan ta fini iya iskanci,a fili tace amma kinci
amanata,Kinga ki kawo min bra da abincin kawai,Beauty ta ajiye tire ta fice ranta
na suya ta dakko bra ta dawo sannan ta kawo abincin Naila ta kwashi girki sannan
ta cire rigarta ta saka bra ta Maida kayanta, ta shiga bawa Beauty tarihin
rayuwarta da shiga gidan yari har fitowarta yau,Beauty ta tausaya tace kin bani
tausayi Kuma na miki uzuri a abinda kike yi,yanzu ita Mummy din ya za ayi da ita?
Naila tace wata zan samu na turata a matsayin Yar aiki gidan asalin wacce ta haifi
Ashraf ni ta kansa zan fara,so nake shima ayi Masa sharrin kisa a kaishi
prison,tare zamu je Abujar ni Kuma gidan ogar zanje Mummy,wannan Dan nata sai na
sumar Masa da Hallare dinsa ta daina amfani zai ci ubansa,Beauty ta sheke da dariya
harda shewa tace baki San ma me zaki Masa ba,Naila tace abin ne yayi min yawa sai
dai naje Abuja tukun sai naji tarihinsu sai nasan ta Ina zan fara ramawa,Beauty
tace to a kira Chikar gayu mana kuje tare,fitsararriya ce bata tsoron uban kowa,
Naila tace nima shegiyar kaina ce fitsarriyarce,ke bani da mutunci,ni kadai ma na
ishi kowannensu amma duk da haka a kira Chikar Gayun Nan da kwana biyu mu wuce idan
zata yarda,amma ke zaki bamu tallafin kudi,Beauty tace babanmu Yana da gida acan da
masu aiki da masu gadi kawai ku zauna a nan ba mace a ciki a banza ake gyara
shi,kawai dai a samu kudi ayi miki dinki na manyan yara,sannan ya kamata ki koyi
mota a can akwai na Daddy na ki dinga ara idan ta kama,Naila tace godiya nake sabo
da ni kaina ban san me zanyi ba ma sai na je tukun,na fara Jin tsoron kaina Beauty
Ashraf bazai ga da kyau ba,to kije musu a me kudi,Kinga baza su taba ganeki a
shigar mata ba,sannan kina daukan wanka kinga kin canja salo kenan da an sanki a
namiji yanzu a mace zaki fito Kuma ki boye kanki kar a gane kece,Naila tace tab ai
Murya zan makale wlh ko Spark sai yayi da gaske zai gane ni,yanzu ni Kuma ya za ayi
dani yaudarar da kika min? Har kuka nayi a kanka Jamilu wlh Ina hangoka a namiji me
damatsa da faddan kirji, Kuma yanzu Daddy ya bani 2weeks cikin masoyana na fito da
wani,Naila tace to ba sai ki zaba ba,ai Banda Wanda nake so,kiyi hakuri ki jira
Kiga zabin Daddy idan bai miki ba ki fada min master planner ce ni sai an rushe
auren.

Beauty tace na yarda da ke wlh tunda kika shiga gidan Maza kika fito lafiya ba
kamarar Tantiriya bace ke,Naila tace ta can ciki ma kuwa,Chikar gayu suka kira nan
take ta dauka,Beauty tace aiki ya samu fa tawan,Chikar gayu tace kice na bar Kaduna
na taho Beauty tace ai nace zan zo,a'a tsakani da Allah dama na gaji kin san ni
dama ba wani mafadi ne dani ba zanzo kawai gobe turo min kudin mota,Beauty tace to
angama,Naila tace Shegiya me kudi gashi sai gudanar da abubuwa kike da kanki,kema
ai zaki kudin idan kika auri Spark,Naila tace wlh ai da na fara baje Masa ai shike
nan Kuma sai arziki dama tsohon tuzuru ne kadan yake jira Dan banzan da wani blue
blue eye ai yaron nan na gana Masa azaba a gidan Dan kande ,na dinga jona Masa
chaji sai kiga ya dauka Yana signa,Beauty ta sheke da dariya tace saurayin da kike
so ma kenan kina zaginsa,Naila tace ai Ina aurensa bakina kanin kafata,oh ashe
Spark soyayya kuka kulla,Naila tace bai fa ce Yana so na ba nima ban fada ba,Very
soon zaku furtawa juna ne,Allah yasa number dinsa nake so na Nemo wlh,ya gama yarda
shi zai fitar Dani giyar so na kwankwanda wannan fitowar da kika ga nayi ta ba a
hayyacina na fito na,ai duk cikin Mayen giyar so ne yasa nayi zuciya na fito.

Nan suka lalace suna Hira har dare sallah ce da cin abinci ke tashinsu,ana
idar da Sallah Naila tace anjima zaki kaini wani aiki wajen budurwar Abbanmu ita
zan cikawa aiki na kafin na bar Kano,Karfe nawa?10pm mu dawo 2am, Beauty ta zaro
ido tace kawai ki shirya karki tsorata, ni sai dazu ma na tuna gidan su Batoola
Ashe gidansu kusa da gidan Yaya Mohsin ne,anyway ma dai yau zan gama da auren Nan.

Beauty tace anya kuwa ba shedanu ne suka shiga jikinki ba duk ke kadai zaki
wannan aikin? ga gidan yari kin fito yanzu Abuja zaki je neman fansa,ga Budurwar
Abbanku gashi kince kina gamawa zaki dawo wajen matar Yayanki,Naila tace ki zuba
Ido ki gani,yanzu Jallabiyya zaki samo min fara,sai dai ta babanmu,dakko min aronta
Beauty ta dakko Jallabiyar Daddy dinsu,tace saura farin Chalk,a daren nan suka Nemo
abinsu komai da komai,Naila tace muje ki kaini yanzu zuwa 2am idan na fito na ganki
a kofar gidan kina jirana da mota,Beauty tace an gama.
Naila kayanta ta cire ta saka Jallabiyar Daddy, ta dauki garin chalk dinta a
leda da cumb,da wata color kamar jini tace muje,Beauty ta shiga mota ta ja suka
tafi abinsu sai ungunwar su Mohsin,suna zuwa Naila Hijab ta Kifa a kanta sannan ta
fita,gidan su Batoola a bude dama daga ita sai dattijuwar babarta a gidan sai wani
tsoho tukuf babanta Wanda baya gani ma sosai.
Naila kamar abin arziki ta shige gidan,Tsohuwar da tsohon suna daki,Batoola an
tafi gidan suna Naila ta shige dakin Batoola da yake a bude ta turo kofar kadan.

Wani ruwan color kamar jini ta yarfa a Jikin mudubin dakin Batoola kamar jini
yayi tsartuwa,ta samu dakin ta hargitsa kayan ciki tayi kaca kaca da kayan dakin
Batoola,sai 10pm taji Sallamar Batoola tana cewa Hajiya na dawo ni Kam na gaji sai
da safe bacci zanyi,Naila da sauri ta samu tarin kayan wanki ta shige ciki ta rufe
kanta ruf,Batoola tana shugowa tana wakarta.

Ta hau cire Kaya Naila ta leko da kanta kadan tana kallon Batoola,ita dai
Batoola da hasken waya ta haska dakinta ta tube har bra dinta,Naila tace ji nonon
shegiya sai kace kwababbiyar flour da za ayi meat pie irin an gama tabileta a
inji,a haka take so Abba yazo ya jawo mana asarar kudi,Abba idan zaka lallaba na
Umma ka hakuri da shi to,ni na kasa ganewa Maza kana da mace da yaranka kana wahala
wajen ci da su da kyar ake Sha amma wai ka tafi neman wata macen,nifa na kasa gane
muku Maza tsakani da Allah ahhh cewar Naila a ranta,tace shegiya ji cikinta duk da
gani ta zazzagar da yara duk yayi spring yayi wani dabbara dabbara ayi fatar cikin
bawa ta wani cuccure ba excesise ko wacce sai dai taci ta koshi ta kwanta,Dan motsa
jiki irin na ciki da akeyi Yana damewa ya danyi kyau matanmu mu basa yi.

Batoola kayan bacci ta saka ta fada Saman katifarta,Naila tace ashshaa dole
Allah ya bani sa'a a kanki shi yasa na samu damar shugowa Bata azkhar sai wake wake
katifar ma baza a karkade ba ko da shedanu a Kai kawai an fada Kai,ai kuwa zaki ga
shedanu yau,Batoola dai Bata San da kowa ba,wutar nepa aka kawo ta mike zata kashe
kwai kawai taga jini a Jikin mudubi sai lokacin ta kula da yanda aka hargitsa mata
dakin,tace menene haka jini,tsoro ne ya kamata tayi Maza ta kashe wutar ta kwanta
ta lulluba da bargo jikinta na rawa,ta tashi ma ta fice ta kasa sabo da tsoro,tana
haka bacci ya kwasheta wurin 2am lokacin gari yayi tsuuuu kowa yayi bacci an kulle
kofar gida da Naila a ciki,a hankali Naila ta fito daga Inda take boye,ta lallaba
ta zare key din dakin Batoola ta bude kofa ta fito Sadaf Sadaf taje ta bude kofar
gidan da aka kulle ta barshi a bude ta dawo garin chalk dinta ta shafe fuskarta da
shi ta cire Hijab dinta ta jefo shi tsakar gida da chalk din da wannan kalar Jinin.

Bulalar data shugo da ita ta daga ta tsulawa Batoola,a firgice Batoola ta bude
idonta taga dodo sak Aljani gashi gashin Naila ta tashe sama kamar kayar bushiya,ta
canja Muryar aljanu......tana zaro harshe kamar mayya tace bamuuuu... yardaaaaa....
kiyiiiiii....aureeee...baaaaa.....ko....zakiiiii ...aure.....to.oooooo......ki.....
auri wani.....mun....lamunce.....ta sake zabga mata bulalar taci gaba da
magana......amma.....Banda.....Hashimu
Dolo .......bazai....iyaaaaa....ciyar....daaaaa
ke.....ba...muuuuuu...Kuma....muna...kaunarki.....tunda aka haifi kakanki na
talatin.....muke.....tareee....dakuuu....bama....son...abinda....zai ..tabaaaaaa...
..mana ke....idan...Kuma...kinki ji....zamu...bawa.....sarki
jininki....ya....shanye....Naila ta nuna Jikin mudubi da yatsa...ta sake zaro
harshe waje kamar karya tace....waccen....Jinin...tsohon mijinki ne.....sabo ..da
ya Saba mana umarni muka aika shi lahira....sarki ..ya shanye
jininsa......ki....tabbatar kin fadawa.....Hashimu Dolo....kin fasa
aurensa....Kuma....kiyi gaggawar......fitar da miji cikin sati daya...kiyi wani
auren.....karki bari ni....na dawo ..na samu... Baki auri wani ba amma Banda
Hashimu Dolo ... yanzu zan tafi kasar Ethiopia mu asalinmu a can muke.....Hallaren
Hashimu baza tayi miki ba ....sai dai tsofaffi.....Naila tayi wata dariya
tace....karki bari na dawo baki da aure.....sai ta canja harshe ta koma fulatanci
tafi minti talatin tana fulatanci a kan Batoola,karshe cikin tsawa tace kwanta ki
lulluba ta sake tsula mata bulalar tace lulluba da bargo....wannan bulalar da muke
miki.... ta karban dubu goman Hashimu Dolo ce.....da kika ce zaki anko......Bama
son karya.

Batoola ta hada zufa sharkaf jikinta Yana uban bari ko wacce addua tazo bakinta
karantawa take tace bazan aure shi ba wlh dama Ina da wani Usman nafi sonsa
ma,Naila tayi haushin kare wan... wan ...mun sani... ba sai kin... bamu labari
ba ...sannan tayi fulatanci tace zan... koma suffata ta aljanu..... Wacce Allah ya
halicceni da ita kina kallona zaki mutu.....zaki mutu...

Batoola magana ma ta kasa ta rufe kanta cikin bargo jiki na bari karrrrr
karrrrr, Naila fit ta fice ta kwashe Hijab dinta da tarkacenta da tazo da su har
bulalar ta tafi da ita ta fice da gudun gaske lokacin Kuma yaran Dan Indo suka sake
zuwa bincike suma cikin dare Neman Jamilu suna fara buga gidan Naila ta fito daga
gidan su Batoola da uban gudu kamar zata tashi sama ga fuskarta duk chalk fari tas
ga gashinta buuuuu.....ga farin kaya,ai suma yaran Dan Indo sai gudu suka rasa ta
Inda ma zasu shiga motar tasu, jiki na bari suka bude kamar zasu ballata suka
shige,Driver hannu na mazari ya kasa saka key dinma Yana hakki Yana karkarwa Yana
cewa wlh bazan sake zuwa unguwar nan ba ko me Dan Indo zaiyi sai dai yayi,wani
aciki yace ka ja mota dalla Aljanu ne suke wasan buya buya yau a..,driver ya fisgi
mota suka fita a million,sai da suka yi nisa wani a ciki yace tunda nake ban taba
ganin aljani Ido da Ido ba sai yau,Kai kaga wani gudu wannan gudun ya wuce na
mutum.

Bangaren Naila tana bi ta lungun da tace Beauty tazo ai kuwa tana zuwa Beauty
tana jiranta a mota,Naila ta bude kofar gaba ta fada tace muje na gama da wannan
case din, Beauty sai dariya take Naila ta yayyafa ruwa a hijab din ta goge chalk
din tare da yafa mayafu, Beauty tana sharara gudu sai ga yaran Dan Indo suma a
kwalta kamar zasu tashi sama sun wuce a million wani yuuuuut.....Beauty itama ta
Kara take gudun motarta tace ko barayi ne suka biyo su wannan gwara muyi ta
kanmu,Naila tace naga wasu fa kamar suna dukan kofar gidan Mohsin dina ko su ne oho
dake a hargitse nake shi yasa,suna komawa gida sai bacci kawai.

Batoola kuwa sai da Naila ta Dade da barin gidan sannan ta mike a hankali ta
fice fit daga dakin ta fada dakin su Tsohuwa tana cewa aljanu aljanu...zasu
kasheni....Dattijon suka tashi suka dinga zazzagawa Batoola fada suna cewa ai kece
Azkhar yayi miki karanci ke dai wake wake kawai,ance ki gyara halinki kinki ai
gashi nan,ke dai sai waka babu Azkhar da addua sallah ma sai anyi yaki Dake kullum
kece hada sallolin hudu a lokaci daya,ai gashi nan,Tsohon ya shiga tofawa Batoola
Ayatulkhursiyyu Yana cewa bakya karanta Ayatulkhursiyyu shi yasa,Batoola tace wlh
da na ga Aljan din na karanta yafi sau dubu amma ko gezau,wai fada min suke fa kar
na sake na auri Hashimu Dolo,wallahi na fasa zan auri Usman din yafi min na hakura
da son sai na juya miji,ga dubu gomansa ta anko da dansa ya kawo a Maida Masa
abarsa,babu ni ba Hashimu Dolo har abada,aljanuna basa kaunarsa Sam sunce ina
aurensa zasu kashe ni wai sune suka kashe tsohon mijina,Dattijon yace wanne irin
rashin tsoron Allah ne Batoola ai aljanu ma Allah ne ya halicce su idan Allah ya
kaddara sun isa su Hana ne, Batoola da sauri tace nidai nice me auren Kuma ni zan
zauna sabo da haka wlh na fasa,ga bulala Aljanin ya dinga zuba min kamar da karfe
yake dukana na hakura indai Hashimu dolo ne,sunce kar na wuce 1weeks banyi aure
ba,ai Usman ma mutumin kirki ne Kuma Yana da aikin yi duk da matansa biyu ace ya
turo,zan fada Masa in ya shirya nan da sati sati,Dattijon yace ai dama na fada miki
Hashimu ya miki tsufa kika ce ke Wanda zaki juya kike nema ai gashi Nan,sai ki
fadawa Usman din ya turo,ranar Batoola tare da iyayenta ta kwana daki daya.

Da sassafe Batoola ta fito ta nufi gidan Mohsin da dubu gomansa a hannu tayi
sallama,Hanan ta danji sauki tana kwance a Palo amma da kyar take gani,Batoola ta
shiga ta samu Mohsin Yana hada tea,yace ah Aunty Batoola sannu da zuwa,gaisawa suka
yi ta mika Masa 10k din tace gashi ka mayarwa Abbanku ka fada Masa na fitar da miji
yayi hakuri na fasa ni dai bazan aure shi ba,Mohsin yace a ransa ko dai Naila ta
cika aikin ne,sai ya hau dariya a ransa yace Alhmdllh haka kawai zan sake dakkowa
kaina masifa ai sai Naila Allah ya tsare min ke,a fili kuwa yace ba damuwa zan fada
Masa amma ki rike kudin an bar miki,Batoola da sauri tana karkada Kai tace a'a la
a'a ku rike abinku ta ajiye a Saman kujera ta fice,Hanan ta tabe baki a ranta tace
Umma an shiga malamai,ai baza su taba yarda a aureta ba,naji haushi wlh hmmm har
naje mun gama hada baki da Batoola yanda za a ganawa Umma azaba a gidan miji ta
zama ita da hoto daya amma jarabar shegiyar ta fada malamai zata haukata Batoola
Allah yasa Abba ya gano wata,Mohsin ne ya katse mata tunaninta yace kina ganin
Batoola har ta tafi ko gaisawa bakuyi ba Kuma naga kwana nan Kun zama kawaye,Hanan
a ranta tace dama kawancen namu na yanda za gallazawa uwarku ne idan ta kama ma a
saketa kamar yanda nima tasa aka sakeni ashe ta tafi kauye wajen Ubanta ya hada
asiri ansa Batoola ta dole ta fasa ba komai bari a samo wata,Mohsin Yana kallonta
kamar tana magana a ranta bai dai ce komai ba ya kwashe 10k ya zuba a aljihunsa.

Naila ce ta kira shi ya tashi tsam ya fice daga gidan ya koma kofar gida sabo
da Hanan kar taji sirrinsu, kashewa yayi ya kirata back,tace Yaya my love ,yace
Na'am ya a Ina kike ne? Naila tace wajen Baby Beauty ta gane gaskiya yanzu tasan ni
Macece mun zama kawaye Ina gidansu,Mohsin yace Abu yayi kyau,tace ai na gama aiki
jiya a kan Batoola,Mohsin yayi dariya son ransa yace har 10k din ta dawo da ita
dazu wai ta tsaida wani ba dai Abba ba,Naila ta sheke da dariya ta dinga bawa
Mohsin Labari yanda ta aikata komai,yace in kina Abu kamar ba Yar gidan Hashimu
Dolo ba,Naila tace Dolo ya haifi me basira ai Alhmdllh,suna ta hira tace saura
Abuja kafin na dawo kanka nayi waje da Hanan,matar tawa ni ban saketa ba ki sakar
min mata,Naila tace Kai Yaya baka da zuciya wlh akan Jin dadin Hallare sai ka zauna
ana Maka anyhow,wlh bazan yarda ba sai na dauki mataki ni,yace to ai zan gani ya
kashe wayarsa.

Ranar Kuma Beauty ta fara koyawa Naila mota,Naila da naci ance an gama na yau
ta taho amma ta rike mota tace jeki ni zan kawo motar gida,Beauty tace tab kika
fasa min mota Daddy sai yaci ubana idan ya dawo,tun safe suna filin har dare sannan
Naila ta bari aka dawo gida,suna zuwa Chikar gayu tace sai nan da sati zata zo an
hanata fitowa yanzu.
Naila tana gidan su Beauty ga Daddy baya Nan a nan take cin karenta babu
babbaka tana aikin koyon mota ba ji ba gani,Kuma Beauty ta zuba karya ta karbi kudi
wajen Daddy dubu dari da hamsim aka samu Dan kaya masu kyau aka siyawa Naila kala
biyar,Leshi,biyu,shadda biyu da atamfa,sai takalma da jaka kala uku,harda su agogo
da glass na sawa a fuska na Yan gayu, Naila tace akwai tsiya a Abuja,Sati daya
Chikar gayu tayi karya a gida tace aiki ta samu a Abuja zata je ta a mata
screening,ana ta murna a gidansu sabo da suna cikin talauci ko za a samu su
farfado daga talaucin.
Kawai iyaye sabo da talauci hauka ne ba bincike ba komai suka barta ta taho ita
kadai gidan su Beauty, ranar Kuma Naila suka karbo dinkunanta,Chikar gayu tayi
mamaki ganin me kama da Jamilu mace,Sai da Beauty ta bata labari,Chikar gayu ta
dinga shekawa Beauty dariya tace dama na fada miki kika ki yarda,harda kukan
soyayya ai gashi Nan,Beauty tace kawai ta bani tausayi da naji labarinta shi yasa
na dage zan taimaketa,Naila tana wajen tace a'a a'a ni ba a taimakona ke kiyayi
Tantiriya wlh a gidan Maza fa na zauna Dan kin bada Gundunmowa shine zaki ce zaki
ce taimakona kike,bara nazo ko maula? shawara kika kawo fa,Chikar gayu tana
kallonsu tace to yanzu Munji magana ta wuce a fada min aikina, Beauty tace wallahi
Naila kin Allah gareta amma ba komai,Naila tace wannan fa yiwa kaine kika sani ni
me zan miki gaba,Chikar gayu tace ku bani aiki na naji please,Beauty labarin Naila
ta kwashe ta bata da Kuma aikinta gidan Mima zata je a matsayin Yar aiki kawai ta
dakko sirrinsu taji labarinsu shike nan aikin?

Naila tace Wanda ya miki iskanci ki koya Masa hankali ki tabbatar Yan gidan idan
basu da tarbiyya to ki koya musu ita kin gane ai,Chikar gayu tace anzo Inda nafi
kwazo bawa duk wani marar tarbiyya to ya koma me tarbiyya zan basu tarbiyya.Naila
tace an gama zamu dinga waya kina can gidan ni Kuma Ina gidan su Beauty na Abuja
zan kula da bangaren Dan Mummy Ashraf kenan,zanci uwarsa daidai gwargwado sai na
hada Masa bomb,bala'i,tuggu da sharri na,Ke Kuma Beauty abinda ya kama na kudi
kawai ki dinga samo mana,Bafa kyauta ba yawwa bashi kike bani ki dinga rubutawa
Spark zai biyaki,ko a Ina idan bukatar kudi ta taso to kawai ki ranto min bashi na
dauka a wuyana Spark zai biya karki ji komai nasan dole zai kwakwulo gidanmu za a
bashi number ta shike nan zamu hadu a Abuja idan ta kama ma kiji an daura aure ko
irin na Yan India ne yanda suke zaga Abu ana mangale....
mangale....mangale....Kuma wlh bazan ce NAHI ba.

Chikar gayu tace ai wlh karki ce Nahi wlh ki aure shi kawai kuyi choreliye dinku
a turaka,Naila tace ai har chori merii sai mun yi,Beauty tace ku hada da Tere liye
Naila yafi dadi, Shewa suka yi.

Spark kuwa tunda ya koma gidansa yaki zuwa gidan kowa har Mummy din yaci gaba
da Uzurinsa,sai da yayi settling komai nasa a wajen aiki sannan yace ni dana daura
Shirin aure Ina naga ta zama,Jamilata tana jirana,zan ajiye sarakan bani bani
mata,amma Kuma Yana ta kiran number Naila ba dare ba rana shuru,wata Yar karamar
hauka ya fara da yaji yayi sati guda Yana kiranta tun wayar tana ringing har ta
daina,Bai San wayar Naila ta fada ramin bulo ba wajen haura katanga,har chaji ya
kare ta kashe kanta.
Spark yau gidan Mummy ya fara zuwa,Yana shiga Palo yaji kida na tashi ta tara
yaran mata kawaye suna ta Shan shisha a palon duk babu suturar arziki a
jikinsu,Mummy ta saka wani mini skert da Yar riga me siririn hannu gata tumbur sai
katon ciki,samanta sai kayan nono yayi dangangan daga kasa Kuma bata da kibar,Spark
Yana kallon Mummy a ransa yace Ashe haka mummy take da mummunar kama gaskiya Alhaji
Aliyu yayi hakuri wai wai samodara,a fili Kuma iya sallamarsa basu ji ba sai da ya
shiga ciki,Mummy wai ita wayayya ta fito da gudu subu.. subu.. My Son Oyoyo zata
rungume shi, Spark ya matsa da sauri ta rungumi iska,saura kadan matan Dake palon
su fashe da dariya sai boye dariyarsu suke yi,amma spark kallonsa suke kamar mayu
kowacce tana so ya kyasa,kamshinsa duk ya cika palon,Mummy hararar Spark tayi tace
baka da kirki wlh na tara friends a gidan Mima anyi girki dangi an cika amma kaki
zuwa haba Spark murna fa za a tayaka ka fita daga masifa,Spark dai Yana jinta yace
Ina yini ya kuke ai duk na ganku a kotu mun gaisa mene za a Tara min mutane sai
kowa yasan naje prison,au kaifa baka San arziki ba Spark murna fa za a tayaka,na
hutar daku kowa tace Allah ya tsare gaba amma sai an wani yi min girki da yunwa aka
ce muku na dawo?ni dai mun shiga uku da wannan yaro wlh wani auren za a Nemo ayi
Maka ko kayi hankali,ai Mima ta shaka dama tace wlh wannan karon da kanta zata samo
Maka matar aure,Spark yace tab.... ya juya yayi ficewarsa.

Gidan Mima driver ya kaishi Yana zuwa Papa da Mima suka sashi gaba da fada,Yan
uwa duk sunzo suna gaida shi Yaya Spark ya zo yau,Mima tace ka fitar da mace mun
gaji da iskancinka ka raina kowa ai gwara a samu me mana maganinka,Dan iskanci ace
wai namiji kake so a gidan yari wallahi bazan lamunci wannan ba,ko ka kawo matar
aure ko Kuma na zabo Maka Kuma wallahi idan kace baka so ban yafe Maka ba,Spark
keyarsa ya sosa,tace wato na Fadi karya ko? dama haka yake musu idan bazai iya Musa
abuba to Yana Sosa keya su sun san me yake nufi Bai amince ba,Papa yace to wallahi
ko kaki ko kaso idan nine ubanka sai na daura Maka aure da matar da zamu zaba Maka
ko a dangi ko a bare,zan Gani waye ya haifeka,marar mutunci ka Maida mu
shashashu,Spark ya Sosa keya again,Mima ta make Masa hannu,mikewa yayi zai tafi
Papa yace wlh zan iya sawa a Kai min Kai guard room sojoji su casa min Kai tunda
baka da mutunci,ko Kai ka kawo kanka duniya? Spark ya daga yatsa daya sama wai
Allah ne,Salati Mima ta saki,sai lokacin Spark yace kije Mima kiyiwa Mummy fada ta
zama Samodara wlh ba kyan gani Kinga kece yayarta kije ki fada mata gaskiya ta
gyara Halayenta sai kace basamudiya ni ban taba sanin haka take ba sai yau,Allah
dai yasa ba nononta na Sha ba,Mima tace uwarka ce dai Ina yayeka na bata Kai ta
raineka Kuma tafi kowa sonka,Spark ya makale kafada wai a'a,ajiyar zuciya ya sauke
yace ai tunda sai da aka yayeni ai da sauki, hararsa Papa yayi ya juya ya fice tare
da cewa sai wani Jikon.
Yana fita Mima tace nidai na shiga uku duk an rabani da yarana basa kaunata basa
Jin maganata duk sun kangare ba Wanda zan fadawa yaji tsakanin Spark,Rafeeq da
Misam, Papa yace ni nace ki rabawa Yan uwanki tunda kinyi dan Allah ki hakura ba
dadi irin haka kayi kyauta Kuma ka dawo kana zobe ladanka.

Spark dare da rana waya na hannunsa Yana gwada kira,gajiya yayi ya fara neman
number wasu na gidan Yari amma abin haushi ba number Wanda ya karba a gidan
yari,gashi abin haushin bai da number kowa na Yan uwan Naila,ya gama sakankancewa
shine Nan zai fitar da ita ai ga wayarta ta isa komai,shi yasa bai ma tsaya wani
sanin a wacce unguwa gidan su Naila suke ba,a fili ya furta zanje gidan yarin ai
wajenta da kaina naji lafiya,Dan wulakanci ko ta nemeni wato na tafi ta daina sona
ma ai shike nan ya mata kyau.
Ni Jamilu zata manta Dani ni Naila zata share.
Spark ya rasa Inda zai sa kansa ya rasa sukuni kwata kwata.

Naila kuwa ta Dan koyi mota amma hannu bai fada ba haka ta hakura tace Spark
yaki samuwa a waya duk number Dana hada wrong mu tafi gobe Abuja ko Allah zai
hadani dashi kafin naci uban Ashraf.
Spark shima yace gobe ya kamata na tafi Kano gidan yari kawai idan ma maidani za
ayi ciki gwara a Maida ni na sake sabon haka foundation a zuciyarta ya zanyi,Allah
yasa ba Foundation din Toka na gina ba.

Washe gari da wuri Beauty ta Kai su Naila tasha suka shiga motar Abuja,ita Kuma
ta koma gida,Spark Kuma da safe da wuri ya bi flight sai Kano Yana murna zaiga
Jamilunsa har nishadi yake yana wani latsa waya anci shegen wankan shadda sky tana
kyalli,gashin Nan yaci gyara,Naila kuwa a mota tana ta zazzagin Mummy tana fadawa
Chikar gayu halin Mummy, Chikar gayu tace Yar shegiya sai na kulla mata bakin
ciki.
Naila tace da shegen danta Ashraf ai gani nan zuwa na dinga bibiyar Mummy kenan
har sai na ganshi Dan ubansa.

Har akaje zagin Ashraf suke ta fama ita da Chikar gayu,suna sauka Naila tace
yawwa Mummy Allah ya dawo da Tantiriya iskanci salo salo shafi shafi sai naga
karshenki,yanzu a Yar wanka zan fito Yar masu kudi Yar kolabo,zaki ga tsiya,Jamilu
is back,Chikar gayu tace stoci sun sauka,eftoci sun sauka,Naila ta dauki jaka tayi
gaba Chikar gayu ta binta a baya tana mata wakar Star na cikin India
Singham....dararam...dararam...su da kansu suka yi dariya.

NA GAMA FREE PAGE

END OF FREE PAGE

300 ne 1,2 &3

Accnt no
0175487861
Asmau Garba Muhammad Gtbank

Katin MTN
08061929616

Yan Niger
+22790795939

Hey lovelies

Ke matar aure ce kuma kina neman business din dazakiyi daga gida da kuma baya
bukatan jari?
Kai dan makaranta ne kuma kana neman inda zaka ringa samun kudin kashewa?

Ko a'a ke kinada business dinki Amma kina neman wani side hustle haka da zai Kara
Miki extra source of income?

Ko kinada business idea da kikeson kifara Amma Babu jarin farawa?

Toh duk ku tarkato wannan training din, dan ga solution nan nasamo muku, kawai ki
danna wannan link din Dan Samun damar shiga group din

https://wa.link/49vn47

AsmaBaffa
[12/13/2023, 8:25 PM] AsmaBaffa: PAID GROUP

ACCNT NO
0175487861
ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK

KATIN MTN
08061929616

YAN NIGER
+22790795939

🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

BOOK 1

46-50

Official

By
AsmaBaffa

Sadaukarwa gare ki
AIDA MAMAN TASNIM

Page naku ne

Maman Afrah
Hajjafatty
Oummu Twins
Umu Afrah
My Num
Mom Twins
Ruky

Masu audio ban yarda a juya min novel zuwa audio ba Dan Allah.
Hey lovelies

Ke matar aure ce kuma kina neman business din dazakiyi daga gida da kuma baya
bukatan jari?

Kai dan makaranta ne kuma kana neman inda zaka ringa samun kudin kashewa?

Ko a'a ke kinada business dinki Amma kina neman wani side hustle haka da zai Kara
Miki extra source of income?

Ko kinada business idea da kikeson kifara Amma Babu jarin farawa?

Toh duk ku tarkato wannan training din, dan ga solution nan nasamo muku, kawai ki
danna wannan link din Dan Samun damar shiga group din

https://wa.link/49vn47

Direct gidan da Beauty ta basu address aka kaisu dake tayiwa masu gadi da kula
da gidan magana suna knocking aka bude musu suka shiga har ciki aka musu iso,gidane
na gaske part uku,ko Ina ya hadu sai kallo suke yi suka dauki daki daya su
biyu,Beauty me dafa abinci wata yare Sheyi ta kira tace taje gidan anyi baki zata
ci gaba da yin abinci,Sheyi sai gata nan da nan,Naila tace amma gidan nan ya hadu
gaskiya Beauty suna da kudi wai dankari,Chikar gayu tace Allah ya azurtamu Ameen.
Wanka Chikar gayu ta shiga tana fitowa Naila ma ta shiga tayi wanka suka fito
suka shirya cikin kaya masu sauki sauki,Sheyi tana ta girki sai kamshi ke
tashi,Naila tace Ina so na koyi girke girke na gargajiya dana zamani amma bani da
lokaci,yanzu idan Spark ya aure ni me zance da shi? Chikar gayu tace wlh tun wuri
ki koyi girki da zaman nan haka, me kike yi baki iya ba ai kuwa zaki ji kunya,Naila
tace ai yanzu na dinga dan lekawa kitchen wannan Sheyi din ta dinga koya min ko zan
iya.
Ai kuwa lokacin Naila ta shiga kitchen,tayiwa Sheyi magana da turanci Ashe
Sheyi ta iya Hausa ta gaske,Naila tace to maganar gaskiya Sheyi Nan da kika ganni
hotiho ce,ta gina bata shiga bace ni domin kuwa ba uwar dana iya na girki gashi na
samu mijin aure,ki taimaka Sheyi ki koya min su Amala irin taku da Sakwara,da miyar
Ugu yake ko ogu oho muku,Sheyi da Ogbono Soup me yauki da dandanon sabulu sabulu
haka,Sheyi tace Ogbno soup ce me dandanon Sabulun? Naila tace haka take mana
miyar,da banku,miyar Egusi da sauran su,Sheyi tace ba matsala zan koya miki
sosai,Naila tace na gode.
Kamar abin arziki Naila tace ke Yoruba ce? Sheyi tace ae kina Kashi a leda ai
ko? to gaskiya ki dinga tsaftacce muhallinki,Sheyi tace ai mun waye tuni wannan sai
na kauye,Naila tace haba ko ku fa amma ododuwa ku dinga tafka Kashi a leda ba tsari
ku canja hali wlh,abinda kuke yi bakwa kyautawa a kasar irin Nija Mama Africa uwar
Africa gaba daya,yanzu dai ki koya min girkinki iri iri,Sheyi tace karki damu
kyakyawa,Naila tace Allah me kika ce kyakyawa? Yes nah Sheyi ta sake tabbatarwa,Ya
kika ga saurayina zai yaba? Sheyi tace ai ko waye shi karya ne ace bai yaba ba,
Naila ta tsaya tana kallon girkin Sheyi tace Spark zan ci kudinka gani nan bisa
kansu Ina iyo, Naila ficewa tayi ta tafi zaga cikin gidan tana Shan kallon
haduwa,Chikar gayu ta Gani tayi waje ta fice,Naila tace halina da Chikar gayu
rashin daraja gidan ubanwa zata je,kafin ta rufe baki sai ga Chikar gayu ta
dawo,Naila tace Ina kika je? tace yawu naje na tofar wannan gidan ai yafi gaban a
tofar Masa da yawu ko a toilet,Naila tace ke anya kuwa a birni kika girma,duk kyan
gida Dan ubansa ki tofar da yawunki Inda kika ga dama amma banda gidan Spark,duk
shegen da ya tofar min da yawu ko na juna biyu ne bazai Kara zuwa gidana ba,Chikar
gayu ce tace zo muje mu Sha shayin Wiwi,Ido Naila ta zaro tace iskancina bana shaye
shaye bane,a gidan yarin kika koyi Sha? Chikar gayu tace ae wasu ne suke dafa mana
ta Katanga ake cillo mana da bushashen ganyen Wiwi muna dafa shayi,Naila tace baki
da hankali Chikar gayu,kina mace wannan ai na Maza ne,Dan Allah mu Sam me zaku
dinga kwaikwayo Kuna koya a rayuwa, Chikar gayu tace iyye ke wata ta kirki ce kin
gwamitsa da kartai ba gwara mu ba,Naila tace Chikar gayu ki kiyayeni aiki na
kawoki ki min in kin gama Spark zai biya kiyi abinda ya dace za a biyaki,Chikar
gayu tayi dariya tace cinikin biri a sama,dariya suka yi Naila ta furta gaskiya
beauty tsakani da Allah tana shanawa Bata da Yaya bata da kani,Chikar gayu tana ji
tace yo ai ni da babanta ma zai so ni duk katon cikinsa tarairayar kayana zanyi,
Naila ta sheke da dariya,Chikar gayu tace wlh tumbin Baban Beauty bala'i wai gashi
da cin tsiya yazo mana visiting watarana Kinga yanda yake cin abinci kamar wani zai
kwace kamar ba me kudi ba, inda kisan kura, Naila tace ni bama haka ba sai
hakoransa na tsakiya daya cire fafaroma, hakora dai suka fice yo ai ba daya bane
biyu ne ko uku ya Ilahi nace da kudinsa ya sa na roba mana,Zo Kiga Beauty yanda
take kuka tana ce Masa Daddy ni ka saka hakora wlh idan zaka ce s din nan dariya
kake bani,Naila tace ke Chikar gayu da munafunci,to Kuma mu ai kowa kallonsa muke
tsaf, ko zaren dinkin shaddar mutum ma sai mun kalla.

Palo suka koma ta zauna Chikar gayu taje ta dafa shayinta na Wiwi ta dawo da
abinta a cup,Naila tace shedan yau aiki zaibi ta kanka Chikar gayu kiyi Bismillah
kafin Kisha shayin Wiwi din nan tunda shedan komai za aci sai yazo ya tsoma baki,
Maza ki Masa bakin ciki kar ya Sha miki dadi,Chikar gayu tayi Bismillah ta fara
kurba tace ai da ta hayakin nake Sha bazan Bismillah ba zan fara zuka sabo da shima
shedan ya zooka ya shake a makoshi.

Chika tana zuka Naila ta kwace ta hankade keyar Chikar gayu tace ke a gidan yarin
har wiwi kika koyo sha? Da Allah ku dinga sanin abin kwaikwayo,mene wani Wiwi kina
mace dan Allah ki bari ki gama min aiki na lafiya idan yaso daga baya ai Kya Sha
abarki,taje ta zubar,Abinci suka ci sannan suka kwanta suna hutawa.
Zuwa dare Sheyi ta Dora girki ta kira Naila tazo ta koya Naila ta shugo
kitchen,tukunyar ta leka tace yawwa ai na gane wannan girkin miyar Egusi ce ko zamu
yi,yawwa Sheyi idan kika wanke namanki sai ki watsa a tukunya Yana tafarfasa Yana
zabalbala sai ki yanka albasa Sheyi ki barbada curry da Maggi,Maggi ki samu me
karfi yanda zai bada dandano,ki dakko manjanki idan ya daskare ma ba matsala duk
daya Sheyi.....Sheyi ce ta tadakatar da Naila tace ni nake koya miki ne ko ke kike
koya min? Naila tace kece mana ai practical nake,Sheyi tace ki tsaya ki koyi Abu
idan kinki ke zaki ji kunya a gidan miji,Naila tace Allah ba yasa ba bakinki ya
biki, yanzu na tsaya nuna min,Ehem haka zaki ce Yan mata,Sheyi ta shiga koyawa
Naila girki har suka gama tare Naila ta gane yanda zata yin miyar da tuwo ko
Sakwara ko Amala etc.

Chikar gayu tana Palo tana kallon tashar wakokin Nija,a haka Naila ta dawo ta
sameta ta zauna tare da yin shuru ta lumshe Ido tana Jin wakar tace na Lula tunanin
Spark gamu can mun fito daga mota mun shiga shopping mall Yana rike da hannuna,gamu
can na rakashi Office...muna soyewa a cikin Office,ya dannawa kofar key, yasa key
Chikar gayu,gamu can ya kaini awon ciki asibiti mum fito a hadaddiyar mota,ya tafi
dani aikin hajji,Gani ga ka'abah,daga can mun wuce America,laaaa snow.....na haihu
a can mace na samu,Chikar gayu tana kallonta ta rufe Ido wai tunani take yi,daga
Jin kida sai haihuwa Kuma,Naila tace baza ki gane ba,ni nasan me nake ji na rashin
Spark Ina zan ganshi?

Ranar haka suka kwana Naila tana zancen Spark Ina zata ganshi,washe gari bayan
sunyi Kari me kyau Chikar gayu ta dakko kayanta kodaddu jemammiyar atamfa riga da
zani dinkin me Fadi ta saka tayi daurin zani me Bakin almakashi gefe ya zobe baya a
dangale ta daura dankwali dan kanti, ta fito da kullin kayanta a leda viva ta
rungume a kasan hannunta,tace to matar Spark kira Hajiya Tagwadas,Naila tace ai sai
ta gane Kuma na fito a gidan yari.
Nari kiji ta jawo wayarta ta kira Mohsin ya daga tana jinsa suna fada da Hanan
ita magungunan basa yi ciwonta yaki warkewa ya maidata asibiti,Naila tace kaga
kyale wannan banzar ka kira Hajiya Tagwadas kawar Umma kace address din gidan Mima
kake so sun kiraka Abuja akan case Dina,Mohsin yace to ya kashe ya kira wayar
Hajiya Tagwadas,tace Dana Mohsin Allah ya Maka albarka Dana Mohsin,Kuma gashi har
yanzu naga Hanan taki ta sake haihuwa ko planning take ne?,Mohsin yace kaji gulma a
ransa,a fili yace uhm Allah ne bai kawo ba,to Mohsin ko aure zaka Kara? Mohsin yace
haka nace miki? a'a wai dama akwai wata ne da nake Maka sha'awarta a makwaftanmu
Iklima yarinya me hankali,bana sonta komai hankalinta Mohsin ya furta yace address
zaki bani please zanje Abuja an Gayyace ni akan case din Naila ance naje gidan
Mima,gidan Ahmad Maleek,Hajiya Tagwadas tace to bari na turo Maka a rubuce ai yafi
Mohsin Dan Albarka,yace Ina jira na gode.

Mintuna kadan ta tura Masa a rubuce shi Kuma yayiwa Naila forwarding,Nan take
ta mikawa Chikar gayu tare da kudi 3k tace ko me kika gani ki kirani,Kinga maganin
nan dana baki ki tabbatar idan kika ji Ashraf zaizo gidan to kisa Masa a abinci
yaci shike nan Hallare Kuma sai idan ni naga dama na tashe ta,Chikar gayu tace an
gama zanci uban kowa,Naila tace kiyi ba komai yi nane ni na saki a kotu harda wani
zuwa suna Jin sharia suna kallo aka daure ni,Allah ya tsare.

Chikar gayu ficewa tayi daga gidan ta shiga taxi tabi address har kofar gidan
Mima,aka sauketa taje tayi knocking,kofar aka bude ko Ina sojoji ne a gidan suna
muzurai suna zare Ido,Chikar gayu ko jikinta tace da Allah yanlabai Wajen Mima aka
turo ni,mutum daya ciki yace bari ayi mata magana aji, ya wuce ciki ya Samu Mima a
Palo ta hakimce,yaranta duk basa nan sai Misam da ya dawo jiya daga Barikin sojoji,
Yana zaune ya harde kafafuwa Yana kallo ba Wanda ke wa daya magana tsakanin Mima da
Misam,Misam wani karkada kafa yake irin Wanda Jin dadi ya ratsa shi, fuskar nan a
hade Yana ta fushi da alama fada suka yi da Mima,sojan ne ya shigo yace Ma kinyi
bakuwa daga kauye tace turota akayi,Mima ta yatsina fuska tace Kai masifa wai ba
anyi zakka ba an Kai, me suke nema Kuma?
Kai kasar Nan tamu akwai masu matacciyar zuciya,let her in,ya fita ya koma,Misam
yace Yan uwanku ne dai,au Kai banda Kai? Yace a'a Banda ni wlh na sansu ne,Kai fa
baka da mutunci kaima,shuru yayi sai ga sojan ya dawo tare da Chikar gayu,Chikar
Gayu tayi sallama tare da zubewa a gaban Mima ta kwashi gaisuwa,Mima ta amsa tana
wani cin magani

Meke tafe Dake waye ya turo ki? Chikar gayu wacce babu digon tsoro a fuskarta
tace Hajiya Tagwadas ce tace kina neman Yar aiki Dan Allah Hajiya kiwa Allah ki
bani ko me wanke kashin yara ce,ke ko naki ma zan iya wankewa,Da sauri Misam ya
rufe baki Yana dariya kasa kasa,sai dai ki wanke na uwarki cewar Mima,Chikar gayu
tace Allah ya huci zuciyarki tuba nake sarauniyar dattawan Abuja,Misam ya sake rike
dariyarsa da kyar Yana kulle bakinsa da hannu,mikewa yayi ya shiga kitchen ya saki
dariyarsa ya dinga dariya Mima tana jinsa taga abinda yake yi,sai da ya gama ya
maze ya fito harda daure fuska ya sake zama.

Mima tace zan daukeki kinci darajar mutanen kauyenmu suna da alheri, amma sai
dai ki shiga cikin masu girki,Chikar gayu tace na gode Allah ya Kara girma dama
Babana ya sa min albarka, shi yasa duk Inda naje ko badan Allah ba sai an amsheni
hannu bibiyu,Misam yayi sauri ya dauke Kai zaiyi dariya,Mima tace zan koreki wlh
wai wacce irin yarinya ce ne ke? Ko Yar kunya ta mutam kauye babu idonki a
soye,Chikar gayu tace sorry Mima Tsohuwar Yar Wiwi ce ni yanzu Allah ya shiryeni to
chajin ne bai gama sakina ba,karki damu na daina yanzu a hankali zata sakeni,shi
yasa na fito neman na kaina,Misam Yana ta dariya ya dauki magazine tare da kare
fuskarsa wai kar Mima ta ganshi,tasan me yake yi jaridar ta fisge ta kwala Masa a
jikinsa tace tashi ka tafi gidan uwarka, Chikar gayu tana zaune tana satar kallon
Misam wani kyakyawa da shi hadadden gaske sai kamshi yake, shi Kuma ko kallonta ma
baiyi ba,Chikar gayu tace Masa Ina Kwana? Yana kwano ya furta ba tare da ya ko
kalleta ba ya mike ya fice abinsa,Chikar gayu da sauri ta bude ledarta ta dakko
biro da Dan littafi ta shigar da sunan Misam ciki ma'ana ta rubuta a gaba tace
tarbiyya dole Kaine zaka fara karbanta.
Mima kallonta tayi tare da Jan tsaki ta mike tace kice a nuna miki wajen Yan
aiki ki koma can,Chikar gayu ta sake rubuta Mima a littafinta,Bata tashi a wajen ba
Yan gidan suna ta shugowa daya bayan daya ba Wanda ma ya kalleta,ita Kuma sai aikin
rubutu take.

Naila kuwa Beauty ta kira tace motarfa? tace bari a kira Daddy ya turo driver
ya dinga koya miki Kinga ai zaki San gari sannan ki fara zuba wanka.
Naila tace an gama,a ranar kuwa driver yazo ya fara zaga garin abuja da ita Yana
koya mata sosai,Naila sai murza kan mota akeyi kamar ta Ubanta,ko wanne namiji ta
gani sai ta kalle shi tace to ko Spark ne wancen oho.

Spark kuwa an taho zance wajen Jamilu,Yana sauka drop motar airport ya dauka
zuwa gidan yari,Yana zuwa ma'aikata suka dinga murna suna tarbarsa,suka gaisa tare
da tambaya oga ya akayi ne wajen wa kazo? Yace Jamilu Tantiriya nayi mantuwa ne a
hannunsa,ma'aikatan suka ce tab ai kuwa Jamilu baya gidan Nan ya gudu rannan baka
ga abinda ya faru a labarai ba ai yana daga cikin Wanda suka gudu,kuma mun samun
labarin ta gudu wlh an duba file dinta ko sama ko kasa an rasa shi so muke aje
gidansu a nemota amma abin ya fassakara,ga wani mummunan laifi data yi wai Ashe
Jamilu macece,haba ana fada nace biri yayi kama da mutum, dukkan ma'aikata mamaki
suke yi Jamilu ashe macece,Yan gidan yari Maza basa so a fada amma ta riga ta furta
da kanta sanda zata bar gidan yari a kunnen wasu ma'aikatan ta furta,yanzu baka San
kowa na Jamilu ba? Spark yace Innalillahi wa innailayhirrajun,sai da ya maimaita
sau uku yace yanzu Ina zanga Jamilu,na gama sanin nine nan zan taimaki Jamilu ya
fita,kash wannan taurin Kai da me yayi kama,sai kaje yanlabai ka ajiye mana number
Dinka idan an sameta sai mu kiraka,Spark ko magana baiyi ba ya Bada number ya basu
kudi yace duk Inda Jamilu yake a Nemo shi,suka ce ya zama dole ai kotu za a koma a
Nan za a bibiyi Inda dangi suke,Spark yasan Naila baza ta kamu ba Kuma baya fata a
sake kamata ma, jiki a sanyaye ya juya tare da shiga mota sai airport ransa a mugun
bace idonsa yayi ja sabo da bacin rai,Naila sai yau ta taba nata Masa rai a
rayuwa,a cikin jirgi sai huci yake shi kadai kowa ya kulashi sai masifa,yace wlh
dole sai na aureta ashe dama ba Sona take ba ohhhh ya ja tsaki tare da dafe Kai
haka ya dawo Abuja,gidansa ya wuce direct ya kulle kansa a daki Yana ta faman bakin
ciki wayoyinsa ma kashe su yayi gaba daya har tsawon kwana uku,Naila ita kanta
tunanin Spark take har ta kwashe kwana uku a Abuja Chikar gayu ana gidan Mima ta
rasa ma ta hanyar da zata yi maganinsa sabo da su basa ko bi ta kanta,Naila tana
kwance a gida,Chikar gayu ta kira waya tace ke naji wata a gidan yau tace Ashraf
zaizo,Naila tace yawwa ki shirya ki sa Masa tace angama,sai da aka gama girki tas
sai ta dawo kitchen din Mima ta buya,bata Dade ba spark ya shugo duk ya fita a
hayyacinsa,sama ya hau wiurin Mima,Yana shiga Mima tace ya na ganka haka kamar baka
da nutsuwa? Kamar baka samun bacci ma lafiya Spark? fuska a hade yace ni dama
tambaya ce ta kawoni,Mima tace to Dan Jarfa ko gaisuwar ma babu? Yace ni tambaya
nazo yi amma dai Ina Kwana? tace lfy Alhmdllh Ina jinka,yace da karfe nawa kika
haifeni? da rana,ko dare ko safe? Mima tace menene? Nifa kawai tambayarki nayi
please,Mima tace da safe na haifeka Kuma ranar juma'a yace to ya aka yi bani da
albarka an haifeni ranar juma'atu babbar rana da safe Bada duhun dare ba Kuma ace
ni komai nayi bazai tafi dai dai ba a soyayya,Mima ta kalleshi tace Allah ya
shiryeka,yace Ameen a haihuwata kuwa an samu alheri anya? Kuma kin samu kayan
barka?dariya Mima tayi tace to haihuwarka tafi ta kowa wallahi Nasha kyautar da har
na mutu bazan manta ba,Baki Spark ya tabe yace uhm bada zuciya daya suka bayar ba
to,duk yanda akayi cikin biyu akwai Daya ko dai an sa min kayan Haram a jikina ko
an ci Dani da Haram ko Kuma ba a yanka min ragon suna ba,idan kuwa anyi min hakika
an yanka rago to ragon Nan na sata ne aka siya ba a sani ba,wani ne ya sato ya
siyar muku a kasuwa aka yanka min,amma in ba haka ba taya za ayi Jimiluta ta gudu
ai na tabbatar tana Sona ta ya za ayi haka,gaskiya Ku bincika ko Kuma Papa gaskiya
ya manta baiyi addua ba a daren....Mima ce tace baka da hankali Spark,Ashe ta
tabbata namijin kake so da gaske oh ni dai na shiga uku da wannan jarabawar
rayuwa,Spark yace ai taki jarabawar kadan ce Mima idan aka hada da tawa ya furta a
sanyaye yace ku kunci duniyarku da tsinke mu kuwa har yanzu rako muka yo.
Kullum sai nayi zazzabin dare, Mima tace ba dole ba tunda kaki aure ai dole kayi
zazzabin dare abinda ma yafi zazzabi zaka yi tunda ba mace,Spark yace Kai Mima a
dinga sakayawa karki Ganni yaro nasan komai,tace uhm naga alama ai muje to wlh yau
sai Kaci abinci a gidan nan ko naci ubanka,yace uhm Mima a daina kalamai haka a
gaban yara,kawai Mima ta kalle shi yanda ya juya mata magana Kuma kamar ba shi ya
fada ba sai ya fuske abinsa,haka suka fito ta taso keyarsa gaba,tace Dan Allah kayi
sauri wannan uban gadarar taka ni bazan iya ba.

Chikar gayu ta kwalawa kira wai Chika...Chika...tana boye a kitchen tace gashi
Nan a dining ya fara dashi kafin na fito,a ranta tace Allah ka bani sa'a a kansa
yaci, ta zubo abinci me Dan ruwa ruwa ta zuba magani ta kawo dining ta koma kitchen
ta buya,Spark sai gashi sun fito da Mima tana cewa muje muje Kaci abinci wlh ko
naci mutuncinka,Spark ba yanda zaiyi yazo ya zauna Mima tace ga wani nan ma dauki
Kaci ai kana son dankalin turawa gashi Nan yasha hadi,Spark badan ya so ba yaja
plate gabansa ya fara antaya girki a cikinsa,yaji ya masa dadi ya cinye tas yace a
karo,Mima taji dadi ta kwalawa Chikar Gayu kira Chika fito ki karowa Dana abinci,
Chikar gayu a ranta tace sai kace wani yace dansa ne wai Danta,bari dai naje naga
uban waye Ashraf din ne, ta fito tazo gaban Mima,Spark ne ya dago a hankali ya
Kalli Chikar gayu itama ta kalle shi,yace ke ba kece ta prison ba? Tace ae nice ba
dai Kaine Ashraf ba? Spark yace nine mana Ashraf amma amfi sanina da Spark,Chikar
gayu nan take ta fara hada zufa tace a ranta Naila ta kashe Halleren mijinta ta
shiga uku,a gigice taje ta karo Masa ta same su Yana bawa Mimi labarin Chikar gayu
yanda ya fitar da ita,daga Nan sai taji tana kaunar Chikar gayu,a ranta tace dama
ita na aura Maka ba komai bari na tambayeta naji.

Chikar gayu Kuma da gudu ta fece daki ta kulle sannan ta kira Naila tana dagawa
tace aiki ya Baci.
Me ya faru ashe Ashraf shine Spark,Naila tace ban gane ba,wlh Ashraf din shine
Spark Wanda kika ce na sawa magani Kuma na saka ya cinye,kizo kofar gidan idan ya
fito ki ganshi da idonki,Naila tace gani Nan,motar su Beauty ta dauka hannunta ko
kwari baiyi ba haka taje har kofar gidan Mima,tana zuwa tayi parking a baya can ta
tsaya,sai ga Spark kuwa ya fito driver na jiranshi a waje da mota,gaba daya tunda
yaci abincin yake Jin Hallere dinsa tayi kwanciyar mutuwa,shi dai yasan a mike yazo
gidan Mima da abarsa managarciya ,haka dai ya shiga mota a gaban Naila,suna tafiya
Naila ta kira Chikar gayu tace fito Dan uwarki fito waje Ina jiranki.

Chikar gayu tace gani Nan ta fito,Naila ta fito daga mota tace Amma Chikar gayu
ke ba karamar matsiyaciya bace mutumin Nan Kinsan saurayinane zan aura kika kashe
min Hallare yanzu Bado shike nan bashi da Besty, wayyo na shiga uku,,Yar iska
mahaukaciya baki da hankali baza ki leko Kiga waye Ashraf ba sai ki sa Masa
magani,Chikar gayu tace ah haka fa kika umarceni dama duk marar hakuri da son
ramuwar gayya ai Yana tare da haka

Naila hannaye ta Dora a kai tace Ina mafita Hallare ta shiga jalala dole fa sai
na sake Masa magani wannan Kuma sai na ganta da idona,Chikar gayu tayi dariya tace
ah ai a dadinkinki ke da kanki zaki shafa mata maganin ko kuwa? tsaki Naila taja ta
shiga mota tana furta ta kwabe ba kanta na kashe kaina,sai ta fisgi mota kamar wata
gwana tana cewa na kan hanya ya matsa ko azumi sittin ya hau kaina yau.

Hawaye ta fara tun a mota tana Tausayin Spark dinta ta manta ma da shine fa
Ashraf,motar tasa tabi sosai Allah yasa ta hango su ya dauki hanyar gidan Mummy duk
da ba wani gane hanyoyi take ba sai da tambaya take iya zuwa waje,gida ta koma a
hanyar gidan ma sai data bata,tana komawa kaya ta canja ta zuba sabuwar shaddarta
me tsada a gurguje ta saka hular gashi me kyau dogon gashi ta daure da ribbon kamar
nata ya zubo kadan a gefen fuska ta shafa powder da jambaki pink dama shaddar pink
tayi kyau duguwar riga me aljihu ta Sha dinkin zamani ta dauki takalmi da jakarta
silver ta yafa mayafi ta fito tare da Maka glass dinta a fuska ba karamin kyau tayi
ba babu Wanda zaice Naila Jamilu ce zaka rantse Yar gidan wani ce,Mota ta shiga da
sauri tayi hanyar gidan Mummy ko zata ga Spark a can da kyar ta gane gidan, Parking
tayi a waje ta fito tare da yin knocking aka bude,suna Ganinta kamar Yar me kudi
sunga tazo Kuma da mota tana karkada key sai masu gadi suka bude mata ana cewa
sannu da zuwa Hajiya,Naila hannu kawai ta daga musu ta wuce ciki tana Izza tana
karkada key.

Palon Mummy ta wuce direct taji Muryar Spark Yana cewa Dan Allah ku kyaleni
naji da abinda ya dameni,budurwata ta bace na rasa Inda zan sa kaina amma ke da
Mima sai zancen wani aure kuke min idan so kuke na bar duniyar ba sai na mutu ba
kawai wannan wacce irin rayuwa ce,ko Dan halinku ma wlh a Hana mutum aure,ni nasan
halinku ne ke biniyata,Mummy tace nayi shuru tunda Kai sunna ce baka so ka
raya,yace sanda zan raya sunnar Kun ma sani ne ni ku rabu dani Dan Allah, wlh in na
gaji zan bar muku kasar,To ubanmu cewar Mummy.

Naila ce ta makale Murya ta koma ta Yan gayu masu yanga tayi sallama a
hankali,Mummy tace shugo ta zaci kawayenta ne sai taga wata Yar Gayun,Mummy tace
wannan ko Yar film ce ne sai naga kamar na Santa,gaskiya sai dai idan a film nake
Ganinta,Baki ta washe tace shugo mana Baby,Naila ta shiga tana kallon Spark da yaki
dago Kai ya kalleta kawai waya yake dannawa,ji take kamar ta fada kansa ta cinye
shi tayi missing dinsa matuka,wuri ta samu ta zauna,sannan tace Ina yini ta gaida
Mummy da ladabi,mummy ta amsa tana ta wani fara'a tace kamar na sanki a wani film,
Naila tace Ohhh Ashe kin gane ni tabbas nice cikin wani film YANKAN KAUNA ko? Mummy
tace wlh na manta sunan dai ni dai nasan tabbas na taba ganinki a film,Murmushi
Naila tayi kadan tace ae tabbas ai sunana Nasiba Yankan kauna Dake a film din nayi
tashe duk da cewa nayi films da yawa,Mummy tace ikon Allah kice duk su Alihu kin
sansu? Naila tace laaaa ai yau ma aikinsa zamu fita wani film dama location muke
nema me kyau to sai muka ga gidan Nan yayi mana to shi yasa nazo neman izini ko
kudi ne zamu biya,Mummy sarkin son wayayyu tace nooo ba sai Kun biya ba kuzo ku
fara idan ma zaku dinga kwana ba matsala,Naila tace watarana dai ni zan dinga zuwa
Ina Kwana kafin a fara film din sabo da na gaji da zama a hotel sai a dinga ganinka
kamar baka da mutunci da kima.

Mummy tace ba damuwa idan da wasu duk ku taho akwai abinci da komai baku da
matsala.Naila harda zamewa daga kujura tace mun gode Umma,Ai mummy ake ce min Umma
ai sai Yan gargajiya cewar Mummy,Naila tace gaskiya fa sai local mutane Ina yinki
uwar dakina,Spark Muryar ce take Masa gizo a kunne sai yaji kamar yasan
Muryar,kallon Naila yayi yaji kamar Jamilunsa wlh,amma ai Naila bata waye haka
ba,Yana ta kallonta a sace duk ta rufe fuska da gashi da glass ya kasa tantancewa
amma wlh kamar Jamilunsa,Mummy ce ta mike tsam tace Nasiba Yankan kauna bari na
kawo miki abin motsa baki,Mummy tana tashi Spark ya mike zai fita Naila ta kurawa
saitin Hallarensa Ido,kallonta yayi yaga ta kurawa jikinsa Ido,fuska ya daure kamar
bai taba dariya ba,yace ke lafiya? Ina Naila ai ta Lula kallon Hallare ya ta
koma,yace ke wai baki da hankali ne me kike kallo,Naila tana kallo tace wait sir,
are you out of your mind? are you normal? Naila tana kallo tana matsawa tace Sir
sorry Ina bada magani baka da lafiya,abarka bata aiki,Spark tsaki ya ja ya juya ya
fice Naila ta tsaya a palon tace yaki ya bari a gani amma ba komai dole sai na
ganta bari naga gidansa.

Ko Mummy bata jira ba ta jira ba ta fice ta shiga motar tabi bayan motar Spark
amma Ina motarsa ta bace mata gidan Mummy ta koma,tana shiga Mummy tace Ina kika
shiga ne? waccen Dan naki Aljanu sun aure shi bazai taba aure ba sai Kun tashi
tsaye Mummy tace ke Dan Allah wlh anyi anyi yayi aure yaki baya son ko wacce
mace,Naila tace sai an Masa maganin aljanu Kinga ni yae film ce amma Ina Bada
maganin aljanu,Mummy tace wlh indai zai warke ba matsala bani da burin da ya wuce
naga Spark Dina yayi aure,Naila tace dole sai na tare a gidansa idan ta kama har
kakana zan kawo ayi Masa magani,Mummy sun matsu Spark yayi aure suka ce ba komai
kawai zan Masa dole ma ya bari ayi Masa magani.

Naila a ranta tace oh na canja shigar Maza nazo Dan na samu shiga karshe na
fada prison,gashi yanzu a banza nazo a Yar gayu sun yarda dani Kuma,Mummy tace idan
zaki iya farawa to gobe ki ajiye film din nan Ali nuhu ya canja wata idan ya warke
kina da 1million,yanzu zan sa a miki kudi dubu dari biyar a accnt in kin gama
aikinki zan baki cikon kudin,Naila tace an gama yo film din banza na fada masa ya
nemi wata suyi rawarsu,gobe zanzo ki kaini gidan da kanki,Mummy tace ba
damuwa,Naila tace karfa ki Ganni da shiga me kyau wlh bani da wani kudi mu kin san
harkarmu ta celebrities haka muke da karya da fake life amma idan kika ga gidanmu
kare bazai shiga ba,Kinga Ina Hawa mota na gyara jiki na sa kaya masu kyau to da
cuta zata kamani shike nan sai dai aji ana neman taimako a gidan radio,Mummy tayi
dariya tace ai mun sani dama.

Naila ta gama ta fito tace yanzu ta spark nake tukun kafin na dawo kanki,wai
dama Ashraf shine Spark amma ba karamin munafuki bane Yana jina Ina nemansa Ashe
shine ya min banza sai ya gane kurensa tunda ya raina min hankali bazai taba gane
ni Naila bace sai na sake cin tudu biyu a soyayya,tunda ya Soni a Yar gidan yari to
yanzu Kuma zai Soni a Yar gayu.

Ashraf Kuma tunda ya fita yake tunanin wannan yarinyar yace anya kuwa wannan
bata da hadi Jamiluna,bari Allah ya hadamu idan da rabon na sake kallon Jamilu
timbir ai shike nan,zata gane kurenta duk gashin Nan sai na cire shi in na samu
dama ai nasan kalar boobs din nata da can wajen Garejin, ai nafi tantancewa idan na
sake gani,murmushi ya saki yace Allah ya sake hadamu wayo zan mata.

Yau kwana yayi da farin ciki da murna yaga me kama da Jamilunsa,Allah Allah
yake su sake haduwa,Naila ma tafiya tayi taji dadin ganinsa Kuma ta fahimci bai
ganeta ba,ga kudi zata samu nan take ta bugawa Chikar gayu waya tace ki bar gidan
Mima kice za a miki aure ki dawo gidan Mummy ki dinga hada mata tuggu kina gana
mata azaba,Chikar gayu ita kaunar Misam tuni ta kama ta ma, bata yin abinda akace
tayi iskancinta kawai take a gida,duk abinda akace tayi ba shi zata yi ba ta buwayi
kowa ta gallabe su,idan akace ta soya dankalin sai ta soya doya,in akace kosai sai
tayi yamballs,kowa yanzu tsoron sata dafa Masa Abu yake sabo da an San ba shi zata
kawo ba anyi anyi bata ji,Misam dinma bai san me take ba domin bai cika zuwa gidan
ba.

Chikar gayu tace ni bazan koma gidan wata ba na Saba da Nan gaskiya ni nayi
miji sabo da haka a gidan surukaina nake bazan zubar da damata ba,Na hadu da wani
cool guy,kije kiji da aikinki nima nawa nake yi, Naila tace ba komai wlh sai nazo
gidan na tona miki asiri,Chikar gayu tace ba komai nima Ina ji da nawa ai iya
shegen sabo da haka na gani Kuma na yaba,Kuma tunda na kulla Masa sai na aure shi
inshaallah,kin fasa basu tarbiyyar? ae na fasa idan na aure shi nafi bashi da
kyau ,Misam ne ya shugo gidan sanye da yard me tsada fari yayi kyau,Chikar gayu
wayar ta kashe ta kalle shi ya galla mata harara,tace an musulunta ashe yau anje
masallaci,ashe kana sallah ai ban sani ba,Rafeeq ne ya shugo Chikar gayu ta gane
shi sai yau ta ganshi a gidan tace ai da Gani ba tambaya kaga munafuki dama shima a
nan yake,kafin Rafeeq ya kalleta ta mike da gudu ta fada kitchen tana cewa
shinkafata zata Kone, ba girkin da take yi,lekowa tayi kadan suka yi Ido hudu da
Rafeeq Baki ya bude zaiyi magana ta hau rokonsa da hannu yayi shuru kar ya fada
tana nuna Masa yayi shuru da hannu,Baki ya tabe,Misam yace ke kawo mana abinci Yana
harararta.

Chikar gayu ta shige tana dube dube sai ga kyankyaso kato ya fito daga cikin
wani lungu, da sauri tasa tsinken tsintsiya ta tsire kyankyason ta dora a plate ta
rufe ta fito kamar abin arziki tace sannunku ta ajiye a gaban Misam tace gashi tana
yin kasa da Kai,Misam yunwa yake ji Yana bude plate yaga katon kyankyaso a soke a
Jikin tsinke,mikewa yayi Chikar gayu ta mike tare da kwashewa da gudu ya ya bita
suka yi waje da gudu,tsayawa yayi yace sai na harbeki idan na sake ganinki Yana
huci,ya dawo ya samu Rafeeq ma ya fice shi Yana jinjina rashin Jin Chikar gayu.

Yau cikin dare Umma ta fara nakuda,Abba dole ya farka daga bacci,Umma tace Ina
Jin haihuwa ce tashi ka daukeni na rasa Inda zan saka kaina,Abba yace da wannan
uban cikin kamar zai taba kasa ga kibarki ta ya zan iya kalleni fa sai kace kazar
mayu,Umma tace wayyo bayana ka daukeni Hashimu kaji na fada Maka,Hashimu yayi yayi
ya daga Umma ya kasa,Umma haushi yasa da ciwon nakuda ta mike zumbur ta dauki Abba
Dolo cak ta jefa shi a Saman bed tana masifa,Abba yace na zaci ma shillo shilloriya
zaki min ai da naji dadina,Wani takaici ya kama Umma tace ni mu tafi asibiti,Abba
yace yanzu karfe 1 na dare a fita yanzu,Kai dalla in zaka samo me napep ka
samo,Abba ya tashi ya fice ya bugawa makwafcinsu kofa yana da Napep ya fito yace
Hashimu lafiya? Wlh iyalina ce zata haihu take ta nakuda shine za a kaita
asibiti,makwafcin yace Allah sarki ai da ka iya tuki ma da na baka ka kaita
kawai,Abba yace ni da ko Keke ban iya ba bare machine ko wani Napep,tunda kake ka
taba ganina a kan Keke Ina tukawa, Ido makwafcin ya zaro yace Hashimu duk kiriniyar
Yaya Maza suna yara amma baka iya ko Keke ba,Hashimu yace ai ko kyauta ka bani mota
sai dai na siyar bazan iya tukawa ba.

Makwafcin key ya dakko yace muje amma Kai mace ma ta fika kwazo,Abba yace hmmm
rabani da tuke tuken nan bazan iya ba Allah na Gani ai sai na manta na taka birki a
matsayin totir ko naje na daga hand break din mota a tsakiyar titi,Makwafcin yace
amma ka cika lusari ,yace Kun Dade Baku fada min lusari ba ko Dolo dama ni nace
muku ba Dolo bane ni?,Shuru mutumin yayi yace ni Ina mamakin ma da Kubra take iya
rayuwa da wannan Hashimu,Hashimu ya shugo Palo yace to taso uwar biyu,taka a
sannu,Umma ta mike da kyar ta nuna masa kayan haihuwar data hada tace dauki muje
Dan Allah kayi sauri wayyo Allah marata faya ta fashe,Abba yace Allah yasa fafunga
ce ta fashe ba faya ba,ko kogi ne ya tsage kin isheni da kwailo, Allah yasa na kusa
Kara aure Batoola tana nan dai tana jira,Umma dakin su Hidaya ta leka tace ke
Hidaya,shuru,zafin ciwo yasa ta dirkawa Hidaya duka tace tashi ke mun tafi asibiti
kuyi min addua ki tashe su kuyi Nafeela da addua,Abba ya leko yace ku hada Dani,
Hidaya harda kuka tace Umma zan biku,Abba yace harkar bata yara bace ku zauna ni na
isa komai,Umma Mohsin ta kira bugu daya ya daga dama sabo da cikin Umma ya tsufa
shi Kam kullum a ready yake,Yana ganin kira ya daga,kasa magana tayi ta rike ciki
tace wash,Abba ya karbi wayar yace Mohsin Umma haihuwa ka taho asibiti Maza private
Kuma zaka biya,Mohsin yace to wanne? Abba yace asibitin Uba,Mohsin yace banji ba
me? Abba yace faya ta fashe faya sauri muke ya kashe wayar.

Umma ce zata ruko shi ya kwace da sauri tare da daka tsalle ya koma gefe yace
bazan manta yanda kika kusa kasheni ba a haihuwar Hidaya,muje Ina daga baya
baya,Umma ta shiga napep tana wash tana cijewa,Abba ya shiga gaba wai Dan kar ma ta
ruko shi taje ta shake shi,Umma ita kadai a baya tana ta Jin jiki,Mohsin zai fito
ya saka kaya Hanan tace wlh ba Inda zaka ta rike shi Yana Juyowa ya kwada mata Mari
ta sake shi ba shiri yaja tsaki ya fice abinsa ya hau machine ya dinga fyalla
wuta,Yana kiran Abba yaji Ina suka nufa Abba sai fada Masa yake Mohsin faya ce ta
fashe,Sai me napep dinne ya kwace wayar suka yi magana da Mohsin sannan suka wuce
private hospital,kafin suje ma Mohsin ya riga su zuwa har ya biya komai ana kawo
Umma Mohsin shi ya rike Umma ya shigar da uwarsa har ciki,ya kira Hanan yace ki
shirya zanzo na daukeki,tace ni bacci zanyi sanda na haihu ni waye yazo min,dama
nifa gaskiya wayata da aka sace min da kayan sawata Ina zarginka ko Kaine ka kwashe
ka kaiwa Hidaya,wayarsa ya kashe kawai ransa a bace,ya kira Hajiya Tagwadas kafin
ma yaje ya dakkota har tasa an kawota a Napep dinta da ake mata haya,Abba dake
asibitin private ne Yana ciki,ance ya fita yaki yace duk haihuwar matata tare muke
yi bazan fita ba.

Batoola kuwa an daura mata aure Abba bai ma sani ba shi kuwa Mohsin har daurin
aure yaje amma yaki fadawa Abba suka barshi Nan Yana jiran Batoola,sun hada baki
akan kar a fada masa Batoola tayi aure sai sanda ya koma zance yaji.
Ana ta jiran Umma ana mata addua Abba yana ciki tare da Hajiya Tagwadas tace Dan
Allah Hashimu ka fita ka bamu waje wai me zaka gani ne wannan masifa da me tayi
kama Kai ko kyankyammi baka yi? Abba yace gudan jinjina da Rabin raina Umman Mohsin
na fita na barta ai bazai yuwu ba Sam,haka aka kyaleshi,mata suna taimakawa Umma
ana kokarin fiddo da Baby Hashimu yace kar ku kashe min dana wlh karku soma.
Allah yasa dai Umma ta haifo yarta mace kyakyawa da ita kamar Yar Mohsin da
Naila suna kama,Hashimu bayan an goge jajirya katuwar gaske aka miko Masa yace
macece bazan Kalli tsaraicinta ba ku nadeta a zani,haba ai ba tsari na Kalli na uwa
na Kalli na 'ya, aka nadeta tare da Mikasa duk ya dame su a dakin,ya karba ya mata
adduoi sosai a kunne sannan ya taba kumatunta yace.. Yan... Yan.. Yan kin ganni
sunana Abba,Hashimu ne idan kin girma zaki ji inkiyata mummuna wacce baza ta miki
dadi ba Hashimu Dolo,Nurses sai dariya suke kamar me, Mohsin Abba ya kawowa Yar
Yana cewa kaga kanwarka ya ka ganta katuwa kamarku daya,uhm ansha warin gardawa a
ciki da Wiwi Allah sa kar ta samu cutar warin Kashi,irin wannan wari data shaka tun
tana ciki sai addua,Mohsin shi kansa Abba dariya yake bashi sai kace a kanta aka
fara haifar Masa yara,sai murna yake yace sai nayi sati guda ban siyar da kayan
Miya ba sai bayan suna,Mohsin yace Allah ya kaimu shima yayiwa kanwarsa addua
sannan yace ya Umman Abba? garau take da ba lafiya ba ai baza ka ganni a waje
ba,Mohsin a ransa yace ta wani fannin Uwata tayi dacen miji.

Naila washe gari da wuri taje gidan Mummy a taxi da katuwar akwatinta zata
koma gidan Spark da zama,Mummy tace gaskiya na yarda da gaske kike harkar nan,Mummy
ta shirya cikin kana nan kaya matsatsu ta yafa Dan guntun mayafi tace muje,Naila ta
zaro ido tana kallon Mummy a ranta tace tab,motar Mummy suka shiga,Mummy ta tuka
suka nufi gidan Spark, Yana bacci kasancewar ba aiki yau Sunday, har gidan Mummy ta
murza hancin motarta ciki, bayan tayi parking Naila tace nazo gidan mijina
gidana,tana kallon gidan tunda take bata taba ganin gidan da ya tsaru haka ba sai
yau a gidan spark,gidane Wanda an kashe Masa kudi iya kudi,ko da ya fito daga
prison sai da aka sake canja kusan komai na gidan, ga motocinsa Nan masu tsada iri
iri, duk Inda ake neman gida to gidan Spark ya Kai,Spark ne ya fito Jin mota ta
shugo Masa gida,Sanye yake da gajeren wando baki da Yar tshirts brown ba karamin
kyau yayi ba duk kuwa da cewa daga bacci ya tashi.

Naila ya kalla ta canja glass yau tasa brown ya mata kyau,sanye take cikin
atamfa riga da skert sun masifar mata kyau,ga gashin ya yarfo a fuskarta ta yafa
mayafi kawai ba dankwali a kanta mayafi ne a Saman kanta,Spark dariya yayi a ransa
yace haba yarinya sai dai kiwa wani basaja ba ni Spark ba,yace wannan karya ne
Naila ce yace ni da na zauna tare da ita mun kwana bed daya ma lokacin tana
Jamilunta,Bata gaji da wasan nan ba lallai yarinyar nan yarinyar nan da taurin
hanci take,Ashe da rabon zanyi kallo na biyu kenan,murmushi yayi a fili tare da
danne lip dinsa na kasa da hakoransa na sama,ya Bata rai yace wannan fa, good day
sir cewar Naila tana wani sirara Murya,kallonta yake sama da kasa murmushinsa ya
kasa boyuwa yace ashe dai Yar wanka ce ko Kuma basaja aka dawo yi min,Mummy tace
gata nan zata zauna da Kai zata dinga Maka girki,sabo da kana zama da yunwa ko ka
dinga yi da kanka Ina raye bai dace ba,shi tun da ya yaji zancen yasan da wata a
kasa Mummy ita tasan me Naila ta fada mata,Kuma shi yasan Naila dai zagin Ashraf
take zata dauki fansa kenan ya furta a ransa,wow wannan yarinya amma zan bari naga
ni me zata min ta dau fansar ita Kuma Mummy idan bata yi wasa ba kwana nan zata
shiga prison domin indai ya tabbata Naila ce wannan to wlh ko makawa babu fansa
tazo dauka,Mummy Taga Yar gayu ta yarda da ita Kai duniya,da wani bagidajene yazo
baza ma ta kula mutum ba,shi sai yanzu ma ya gano bakin zaren,yace lallai yaro yaro
ne Kuma mace mace ce tab,zanga ni ya za ayi dani.

Spark shi bai San tuni ma Naila ta kwantar Masa da Hallare ba yanzu ma magani
tazo ta Masa ba tare da ya sani ba shine dalilin zuwanta gidan, shi Kuma yace dole
nayi taka tsan tsan da Jamilu yanzu haka ma tunda ta gano nine Ashraf to ta daina
so na tabbas,amma bari na gani ya zama dole na kula da me zata yi sannan na dage da
addua Allah ya rabani da Sharrin Naila ta shiga bani tsoro,ashe da gaske take,
jikinsa ne yayi Sanyi sannan yaji haushin Naila matuka da tazo da niyyar cutar da
shi,yace amma ba komai ni Kuma wannan karon indai su Mima sun kawo min matar aure
ko wace zan aureta kawai,gaba daya Nan take ya canja kala idonsa ya canja wani
tsantsan bacin rai ne kwance a fuskarsa,yace maimakon ta hakura muyi aure
kash,juyawa yayi yace zata iya shugowa na amince ta zauna ya wuce kawai ya haura
sama.

Naila tasan kayanta ta hango bacin ransa tace hmm baya so shi wata ta rabe shi
Allah sarki abin kaunata shi Jamilunsa yake so,Mummy Nan take ta turawa Naila kudin
rabi a accnt tace ki kula da shi sosai ina so aljanun su fita kinji,Naila tace an
gama,ni daga Nan ma sana'a zan kama na daina harkar film,Mummy tace yanda kika gani
amma kin hadu da Jinin arziki zaki ci Naira ki more matukar Spark ya amince da
zabin mu yayi aura.

Naila tana shiga ciki a kasa ta zabi bedroom ta shiga ta ajiye kayanta tana ta
murna tace wayyo Allah dadi yau Gani a gidan Spark dina,shi Kuma Spark Yana sama ya
zauna a gefen bed yayi shuru kawai mamaki yake wai dama Naila ba sonsa take ba amma
ko da zata dau fansa a tunaninsa idan ta gano shine Spark zai ci darajar son da
take Masa,tagumi ya zuba hawaye zubo Masa a Saman kumatu,yasa handkerchief tare da
gogewa,kasa komai yayi wankan ma kasa yi yayi ya koma ya kwanta kawai,mikewa yayi
ya sake zama tare da hargitsa gashin kansa ya furzar da wata iska me huci,yace ni
na taba soyayya irin wannan haka tunda nake, akan mace har nayi hawaye.

Naila kuwa murna take kawai ta fito ta shiga zaga gidan tana Shan kallo sai da
ta gama kallon ko Ina sannan ta shiga kitchen Dan girkin data iya kadan ne Dan ma
ta koya a wajen Sheyi,Irish ta soya da kwai ta dafa tea ta zuba a flask ta kawo
dining tana jerawa,Spark ne ya fito fuskar nan murtuk,Naila tunaninta Bai ganeta
bane shi yasa,a hankali tace sannu sir,ga breakfast,Spark yayi zuciya a ransa yace
bari na ci idan ta kashe ni ita tayi asara,ya zauna a fusace a kujera tana murmushi
ta gyara glass dinta ta hada Masa tea tun daga yanda ta hada Masa tea yasan wlh
Naila ce duk abinda yake so ta sani gashi nan, Bismillah yayi tare da addoui yace a
ransa idan na mutu Allah na yafe mata sabo da son da nake mata,Allah ka zama
sheda,Naila dai taga Yana addua bata San me yace ba,tea din ya dauka ya fara Shan
abinsa zama tayi a kujera tabbacin ta Saba da shi gashi shi tsiyar so baya
buya,Naila a nutse ta dinga mika Masa slise bread din Yana karba,sai faman satar
kallon juna suke,shi dai baice mata kala ba,amma itace tace Sir abincin yayi? Ko
kulata baiyi ba wani haushi take bashi ma harara ya watsa mata tace a ranta bai
sanni ba Bai ganeni ba Allah sarki bai San Jamilunsa bace .

Mima kuwa ganin Chikar gayu bata ji amma Kuma ta shiga ranta sai tace wannan
itace daidai da Spark za yi maganinsa,sai ta kirata har dakinta,Chikar gayu ta zo
zata durkusa,Mima tace Chika ya sunanki na gaskiya ma kika ce? Suhaila,suna me
dadi,Ina so muyi wata magana tace to Ina jinki, zaki auri Dana? Chikar gayu ta zaci
Misam ne da sauri tace ae me zai hana ai kina da kirki Kuma tunda na shugo gidan
Nan nasan Ku mutanen kirki ne,a ranta Kuma tace karya nake ku ba mutanen kirki bane
Yan wulakanci in kuka ga talaka ne mutum, Mima tace Spark nake so ki aura,Chikar
gayu wani gumi ne ya keto mata tace a ranta ai Naila sai ta kashe ni Allah ya
tsareni da cin Amana,a fili tace a'a Mima kiyi hakuri wlh bazan iya ba dama wani ne
a ciki ba Spark ba,Spark ya haramta a gareni,ba Wacce zata ce baza ta so shi ba
amma Banda ni wlh kiyi hakuri a canja min wani,Mima tace to kuwa sai dai ki bar
gidan nan,Chikar gayu tace gari da yawa ai maye baya cin kansa,dama ni karya nake
miki baku da halin arziki yawwa in fada miki gaskiya Ina da gatana,karki ganni a
nan kice bani da gata,Mima tace to hada kayanki ki bar min gida,tace ko baki ce ba
dama,ta juya ta fice kayanta ta tattaro tayi wanka tun a gidan ta canja kayanta
masu kyau ba Wanda zai ganta ya rainta ta fito Palo tazo ta jefawa Mima Jakarta
tace gashi nan dama aro su nayi Dan Allah a kone su ko a kaiwa dangi a kauye.

Kuma bari kiji nafi karfin na muku bauta shi yasa kuka ga Ina muku rashin
mutunci iri iri yawwa, danki Kuma bazan aura ba a likawa wata mu bamu gaji cin
Amana ba yawwa,ta juya tana murguda duwaiwaka tace ayyiriri mamarrrrrrrrr......ta
wuce tana jijjiga jiki tana waka,Mima baki ta rike tace ashe da Karuwa muke zaune.
Chikar gayu tace Allah ya rabamu da zuriar masu kisan Kai mugun iri,ta juyo ta
Kalli Mima tace byeeeeee....
Tana fitowa Misam ya shugo Allah yayi shi da neman matan tsiya gashi mata suna
rububinsa sabo da shima ba karya,Chikar gayu ya Gani ta fito tana karkada jiki zata
fita,Bai taba kulata ba sai yau,yace Chik....da iyayi Juyowa tayi ya kalle shi Yana
birgeta a rayuwa yanzu Kam tasan yanda tayiwa uwarsa fitsara Ina zata bari ma suyi
alaka.

SANARWA

DAN ALLAH YAN PAID GROUP KU RIKE AMANA KARKU BAWA WASU KYAUTA.
ITA TA KASA SIYA KE KIN SIYA KIN BATA TA PRIVATE TASAN BA SIYA TAYI BA DOLE TA BAWA
WASU A HAKA ZASU TURA SHI GROUPS DA YAWA.

YAU DA ACE ITA KADAI ZATA KARANTA TA PRIVATE DA SAUKI SAI KU BAYAR A WATSA SHI A
GROUPS

WLH DA AYI WANNAN GWARA MUTUM BAI SIYA BA.


AKWAI CIWO GA WRITER DA WANDA SUKA SIYA.

AsmaBaffa
[12/14/2023, 8:24 PM] AsmaBaffa: PAID BOOK

Accnt no

0175487861
Asmau Garba Muhammad Gtbank

Katin MTN
08061929616

Yan Niger
+22790795939

🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

BOOK 1

51-55

Official

By
AsmaBaffa

Sadaukarwa gare ki
AIDA MAMAN TASNIM

Page naki ne
HASEENA AHMAD DAURA
Hey lovelies

Ke matar aure ce kuma kina neman business din dazakiyi daga gida da kuma baya
bukatan jari?

Kai dan makaranta ne kuma kana neman inda zaka ringa samun kudin kashewa?

Ko a'a ke kinada business dinki Amma kina neman wani side hustle haka da zai Kara
Miki extra source of income?

Ko kinada business idea da kikeson kifara Amma Babu jarin farawa?

Toh duk ku tarkato wannan training din, dan ga solution nan nasamo muku, kawai ki
danna wannan link din Dan Samun damar shiga group din

https://wa.link/49vn47

Chikar gayu tsoro taji yanda tayiwa uwarsa rashin kunya tab ai bai ma dace
ta so Danta ba tace ni bana zafafawa kaina amma dai bari mugani,karasawa tayi har
kusa da Misam ya zaci tsayawa zata yi sai ya ga ta daga Masa hannu wani ta wuce
tana rangwada ta bude gate ta fice abinta,horn yayi masu gadi suka sake bude Masa
gate ya fita da motarsa hadaddiya.

Chikar gayu tana tana tafiyarta a gefen hanya Yana tafiya a hankali Yana binta
Yana mata horn tunda ta juya ta ga shine bata ko kulashi ba taci gaba da tafiya
harda yin tafiyar nigogi tana dangale kafa Daya tare da basarwa tana bouncing,canja
wata tafiyar tayi ta Yan gayu tana yanga tana tana tafiya shi Kuma kamar maye Yana
binta a baya Yana kallonta Yana dariya, ganin Yana ta binta yaki hakura, ta kira
Naila bata daga ba sai da ta sake dagawa lokacin Naila suna dining spark Yana ta
Shan tea dinsa,kallonta Spark yayi ya danna tsaki kadan,Naila wayar ta daga tace
hello a hankali kasa kasa karta dame shi,Chikar gayu tace ke fa na gudo na kasa
hakuri wai babarsu na auri Spark dinki Dan Allah ke kinji marar mutuncin mata,Naila
tace ae gwara da kika gudu kin kyauta min Allah ya miki albarka amma da kin yarda
wlh da Kinga halin Tantiranci,Dariya Chikar gayu tayi tace,a'a Hallaren dinsa tayi
min kadan,Naila tace dama daidai nice ai,ah dama ai se ke, bani da kudi fa an
koreni ba ko kudin sallama,Naila tace akwai kudi a kasa zan tura miki 100k ki
turawa gidanku ko 70k ce wlh su rage radadi,a Ina kika samu kudin? Mum mana,Chikar
gayu tace ikon Allah ni kuwa na cuci kaina sai nayi rashin mutunci ko ficika ban
samu ba,a'a wannan rashin kunyar taki tayi karki dagawa kowa kafa amma a dinga
sanin ya kamata kwaila kinji,Chikar gayu tace nice kwailar? Ae mana baki ji
tarihinsu ba fa aikin banza kika yi dole fa ki koma gidan nan,ki kwantar da Kai pls
amma karki yarda da auren nan sai dai a canja miki wani.

Chikar gayu tace bazan koma ba ai da kunya kin san kuwa abinda nayi? Naila
tace to Kuma mu tsoron abin kunya muke, kawai nazo nan gidan Spark din,Naila tace
baki da hankali ki tafi gidan saurayinki Daddyn Beauty kafin a samo mafita,dariya
suka yi tace bari naje na hadu da Sheyi kawar ki,dariya Naila tayi tace ki turo
accnt ta kashe wayarta.

Naila tana ajiye wayarta Mohsin ya sake kira,ta daga tare da furta Darling Ina
Kwana,Spark ya kalleta ta kira wani da Darling,ji yayi ta furta laaa Yaya Umma ta
haihu? Innalillahi Ina tsoron wannan lamari yanzu ai da kunya haka zanyi aure Ina
haihuwa Umma tana haihuwa sabo da Allah ai da kunya,Ni na haihu Umma ma tazo sabo
da Allah,uwa da ciki ya da ciki shike nan mu da Umma kowa yasan muna kwalbewa da
miji,dariya ce ta kama Spark,yayi tari ya danne abarsa, to yanzu me ta haife? Mace
ta haifa cewar Mohsin Yana cewa mene abin kunya nima ai kwalbewar nake da Hanan,
kiyi sauri ki auren nan,Allah ya raya Yaya amma harga Allah Kai naso aure amma kazo
a yayana baka kyauta min ba wai sabo da Allah maimakon kazo a Dan gidan Malam Isa
sai ka fado a gidan Malam Hashimu Dolo,Mohsin yayi dariya yace ya zanyi nima haka
na ganni,kwalele Kuma,dariya tayi tace Yaya ya lafiyar Hallare?

Mohsin yace karki dameni kina Ina ne Abuja din? Naila ta saci kallon Spark suka
hada Ido tace ae Ina can,yace ki rike mutuncinki fa karki ga kamar baki da mafadi
wlh kina yin badaidai sai kinci ubanki nasan halinki,Kuma karki biyewa kawayen
banza,karki biyewa zuciya kizo kina aikin danasani,karki ji tausayina indai
matsalar kudi ce ki fada min, karki kasa fada min kice zaki ji tausayina ko nauyi
yayi min yawa kawai ki fada min,duk abinda kike so Ina nan,sannan ma kina Ina a
Abuja din ni fa hankalina ba a kwance yake ba,Naila tace Yaya ka kwantar da halinka
kamar kayi bako ya mutu, ba abinda zai faru inshaallah,Ina gidan su Beauty,yace to
kiyi zamanki a nan Banda samarin banza,Banda daukan fansar Nan kiyi hakuri Allah
zai saka miki,Naila a ranta tace nima ai Ina so na dawo gida na zauna a gaban
iyayena ya kamata a kai Mummy gidan yari na samu nayi free,a fili to tace kawai.

Tana kashewa ta turawa Chikar gayu 100k sannan ta kira Umma suka gaisa tayi mata
Allah raya tace Umma iceko lafiya kike? Umma tace sosai ma sai dai yaron nan Mohsin
nake tausayi wlh Kinga bashi da kudi gashi a tsakiyar wata,gashi shine zaiyi komai
a gidan nan abin Nan Yana damuna duk yaron bashi da sukuni ga gidansa ga gidanmu,ni
kudina na biyawa su Hidaya kudin term a haka ma bashi ake bina,Naila tace Umma Inda
naje Abuja na samu aikin yi har an fara biya na albashi ma sannan Baban Beauty ya
bamu kudi da yawa Umma kirki ne da shi,Umma tace Allah? Naila tace Allah a gidan
wasu attajirai sai shegen kudi,yaron gidan sunansa Ashraf dabban kudi ne da shi,
rabona nazo ci,Spark ya kalleta yayi dariya a ransa.

Ki fadawa Yaya zan tura Masa kudin,kema ki tura min naki na saka miki wani
abin,Umma tace mashaallah na daina zagin yarana daga yau Allah ya miki albarka naga
ranar haihuwa,ai kuwa haihuwa yanzu na fara,na dinga haihuwa kenan cewar Umma,Naila
tace dan Allah a'a ki hakura haka,yanzu idan nayi aure shike nan ana yi min ciki
kema ana miki Umma bazan ji dadi,sai kace akuyoyi,mijina ai sai yaga iyayena a
mutanen banza,Umma kowa aka ganshi da ciki an San me yayi Dan Allah Umma ki rufa
min asiri ko zaku yi abinku kuyi Allura,ni bazan hanaku kwalbewa ba,kinga ba wanda
yasan me kuke yi,Umma ki rufa min asiri Dan Allah nidai shike nan sai mijina yaji
uwata da ciki,abin kunyar da akeyi a boye ya fito fili.

Umma tace Allah ya shiryeki Naila na rasa ma me zance dake,yanzu na daina zagi
Allah ya shiryeni,to nidai kiyi Allura a tsayar da ita idan kunyi abinku ma ba
Wanda ya sani.
Dama Umma da son a bata kudi ko masifa Bata yiwa Naila ba,taji kudi sai dai tace
Allah ya shirya,Nan take ta tura, Naila ta tura mata 50k,ta turawa Mohsin 150k,ta
turawa Abba 20k a accnt din Mohsin tace ya bawa Abba,Mohsin yace aikin uban me kike
haka da zaki samu kudi? Naila tace ,Yaya wallahi ba cinikin Bado na nayi ba,ba
Wanda ya siya,abina yana Nan yayi kwantai Ina ta fama da shi an rasa me siya ya
aureni ma wlh,zuwa dare zan kiraka na Maka bayani,yace Ina jira baza mu taba kudi
ba sai kin mana gamsashen bayani,tace to sarkin tarbiyya wai Kai na kwarai,dariya
Mohsin yayi yace oh Naila case wannan fitsara yaushe zata daina ne ta kashe
wayar,Mohsin yace bari kiyi auren yarinya miji zai kashe bakinki.

Spark Yana jinta bai nuna yaji ba Yana latsa waya Yana kora tea dinsa,sai yanzu
yake sake jinjina Tantiranci Naila yace Umma guda take fadawa haka yo aini Alhmdllh
nayi dace,dama bana son mace wani Sumi Sumi nafi so me ji da balaga da iskanci Yar
Karuwa Karuwa haka yawwa tafi,dawowa tayi ta zauna tace ya naga baka cin chips din
ne? banza ya mata.

Ta kalle shi kawai ta hada nata ta ja plate din nasa gaba ya janye abinsa ya dawo
da shi gabansa ba tare da yace komai ba,Naila a ranta sai murna take tace yaji
dadin girkina wayyo,kasa rike murnarta tayi bata San ma ta saki murmushi ba da
sauri ta rufe bakinta da hannu ta mike tana rufe da bakinta kamar wacce zata yi
amai duk da ta rufe bakinta idonta da fuskarta ya nuna lallai dariya take yi,da
sauri ta nufi hanyar bedroom,tsawa ya mata kee....ta juyo da sauri yace wa kike wa
dariya,tace uhm uhm zuciyata ce take shi,ta shige bedroom da gudu.

Dariya ma ta bashi yace yarinya kamar Aljana,zama yayi tare da shafa cikinsa yace
har yanzu banji sign na wani ciwo ba bata sa komai ba maybe,ko sai a hankali zai ci
jikina cuta ta kamani,Ido ya zaro shi kadai yace mutuwa Allah ka taimakeni sai na
samu yarinyar nan nayi harkoki,Spark ango ahh ranar tab sai harkoki.

Naila wayarta ta manta a dining,daukan wayar yayi ya duba missed calls Wanda
tayi waya da shi yagani ta sa Darling,number din yayi sauri ya dauka ya shigar a
wayarsa sannan ya ajiye mata wayarta,sai da ya gama karyawa abinsa Naila tana
dakinta wata Yar aiki ta shugo tare da gaida spark ta fara gyara gidan,ba a gidan
take kwana ba kullum zuwa take tana gyara gidan Banda dakinsa.
Dakinsa Kuma da kansa yake zagewa ya gyara kullum ko da safe ko da yamma idan ya
dawo daga Office.

Kamal ne yayi Sallama ya shugo palon, Spark Yana zaune Saman wani Lilo da ake
sashi a palor can bangare daban me circle Yana ciki a zaune Yana danna waya lilon
Yana Lila shi kadan kadan,Kamal yace ya akayi suka gaisa yace please zo ka rakani
unguwa,da safen nan?
Suna haka Daddyn su Asmau ya shugo tare da yarsa kanwar Asmau wacce ake kira da
Wahida,Spark yayi mamakin ganinsu a gidansa,kallonsu yayi kawai,Mahaifin Asmau zuwa
yayi gaban Spark cike da nadama,Spark yace Ina Kwana,Bai zaci zai gaishe shi ba
yanda Spark yake ji da tsageranci,amsawa yayi yace dama zuwa muka yi mu baka hakuri
Dan Allah ka yafe min,Na yafe Maka cewar Spark,Daddy da mamaki yace haka da wuri?
Spark ya furta ai Dan Adam ajizi ne dukkan mu muna kuskure,share kawai ya wuce
Allah yaji kanta.

Wow Mahaifin Asmau ya furta yace ga kanwarta sunanta Wahida indai har kana
sonta zan baga ita,Wahida itama kyakyawa ce wankan tarwada,Shekeke Spark ya kalleta
bayan sunfi kusanci ma da Wahida,tace Ina Kwana Yaya Spark ,ya amsa,Daddy ku zauna
mana,kujera suka samu tare da zama,Naila ya kwalawa kira chef...fitowa tayi da
alamu ma bacci ta fara,yace anyi baki,Naila ta nufi kitchen ta shiryo kayan motsa
baki ta kawo musu sannan tace Ina Kwana ta gaida Daddy,ya amsa da fara'a, Wahida
kuwa wani haushin Naila taji sai harkarta take faman yi tana turo baki,itama Naila
Wahida take gallawa harara kamar idonta zai fado,yanda take hararsa yasa Spark a
ransa yace bala'i kar dai idon ya fado ki min asara,bedroom Naila zata koma yace
Zauna,Kamal shi kanshi kallon Naila yake ta faman yi Kamar ya Santa.

Waje ta samu ta zauna,tana kumburi,Spark yace zuba musu mana kin zauna kina
kallona,Naila ta Kalli Spark a ranta tace wayyo Bai San nice Jamilunsa ba ta mike
ta zubawa Daddy shi kadai,yace ki zubawa Wahida my wife to be,Wahida da sauri ta
dago kai sabo da ba zato abin yazo mata,Daddy farin ciki ya kama shi yace na gode
Dana Allah ya Maka albarka,Wahida sai wani murmushi take burinta ya cika.

Naila daurewa tayi ta zubawa Wahida lemon ta mika mata,Naila ta ajiye a wajen
ta mike da sauri fuskar nan kamar hadari,Spark yace mika mata a hannu mana kina
Bata mata lokaci,kallonsa Naila tayi idonta ya ciko da kwalla ta dage ta maidata
bata fito ba,ta mikawa Wahida ta rike,zata wuce Spark yace Zauna su gama ki
kwashe,dawowa tayi zata zauna yace on the floor ko bakya Jin turanci a kasa,Naila
ta koma kasa ta zauna a ranta tace idan Sanyi ya sake kamani ai Kai ka jiyo waye
zaiji dadin idan Kuma Sanyi ya min illa ka ragewa kanka dadi bado zaiyi Sanyi.

Suna Dan Sha Daddy ya umarci Wahida yace taso mu tafi,Spark ya mike Yana sani
ya dinga kallon Wahida shi a zahiri bata birge shi amma haka yake kallonta ala dole
Yana wani Jin dadi,Wahida kuwa a ranta murna take tana Jin tafi ko wacce mace a
duniya Spark sai wani kallonta yake kamar ta zuba ruwa a kasa ta Sha,Kamal Yana
kallon Spark Yana mamakin abinda yayi duk da bai gane Naila ba shima dai Yana
zargin ya Santa.

Har mota ya rakasu,Daddy yace Inshaallah zan kira Mima na gaya mata komai,Spark
yace ba damuwa,dawowa yayi ciki tare da Kamal suka haura sama,Naila tana kallonsa
sai lokacin ta mike da kyar jiki ba kwari ta shige bedroom tare da fadawa Saman
bed,tana tunani abin duniya ya isheta.

Kamal suna shiga ciki yace me yasa kayi haka ya zaka ce kana son Wahida,me zaka
yi da ita kasan a sanadin Asmau ubansu ba rashin mutuncin da bai Maka ba,Spark yace
tsaya Kaji ya zauna ya bawa Kamal labarin Naila kaf,Kamal yace Kuma itace Jamilun
da Mummy tayiwa sharri? Spark yace ae,Kai wai tunaninta tunda ta canja kamanni
bazan ganeta ba ashe na zama dakiki ma,Kamal ya dinga dariya yace sai yanzu na gane
zancen Ashe ba namiji kake so ba macece,kaga kuwa wannan idan su Mima suka ga Yar
kanwarsu ce dole su yarda aurenta zaka yi su baka ita,Spark ya furta ai Ina ganinsa
yazo da ita bani hakuri nasan me yake nufi wato naga kanwar ko zan sota ,Kuma in
suka bani ita aurenta zanyi ba ruwana, Naila sai ta gane kurenta a gidan Nan,gashin
kuma Kuma zanyi mata sai ta gaji da kanta tayi bayani.

Kamal yace to ni bana fata ka auri Wahida Ina taya Naila kishi,ai ita Bata damu
ba,in ba mace ba ma da gajeren tunani ai sai tazo min a Jamilunta muyi magana muyi
aurenmu mu wuce wajen,yanzu da aurena tayi tazo gidan Nan ai da tuni da Dana a
cikinta,Kamal yayi dariya yace duka duka yaushe tazo ko da kwana bata yi ba, dariya
Spark yayi yace Kuma ita tayi girki naci abina Ina ci Ina fushi,wlh kasan cin
abinci ana fushi abin dariya gare shi to kana tauna Abu Kuma kana fushi gwada ka
gani, Kamal ya gwada kuwa sai dariya,yace haka kayi Spark? yace ae mana.

Naila kuwa tana kwance tace wato ma budurwa yayi ai shike nan,Kuma bani tashin
Hallare wlh naga da uban da za ayi auren,bazan tashi Hallaren ba, sai 11am ta fito
tare da shiga kitchen ta Dora girki,fitowa tayi ta samu me gadi ta mika Masa kudi
tace kasuwa zan aikeka,yace to Hajiya ta Lissafa Masa abinda zai siyo mata ya karba
ya tafi ta koma kitchen tana yin tuwon shinkafarta,har a YouTube take sake kallon
miyar da zatayi,duk ta gigice ta hada zufa sabo da kawai tana tuwo,kafin ta gama ya
kawo mata sakon ta fito tsakar gida zata karba ta samu Spark da Kamal sun fito,tace
Ina yini dazu na manta wlh ban gaishe ka ba,Kamal ya amsa da fara'a Yana
kallonta,sanye take cikin doguwar rigar material black and maroon ta yafa siririn
mayafi a kanta,farar kafarta sanye da slifas me kyau,Kamal sai kallon bayanta yake
data juya,Spark yace bana son wulakanci wlh zaka daina zuwa gidan nan kazo har gida
kallonta ni bana so,ya Bata rai Kuma,Kamal yace alakoro na kalla,tsaki yaja yace na
fasa rakaka unguwar wlh,ya juya ciki abinsa,Kamal yace Allah ya shiryeka ya shiga
motarsa ya bar gidan,Naila tana kitchen ta bude fridge tana dubo kifi Spark ya
shugo ciki,fridge din ya nufa zai dakko abu bata San ma ya shugo ba,sai Jin mutum
tayi a bayanta kamar zai hau bayanta ta goyashi haka ya mata ya manne da ita yasa
hannu tare da bude kasa ya dakko lemon gongoni ya juya ya fice abinsa,ya wani
rungumeta sosai amma ya kama masifa matsala kina tare min hanya.

Sororo Naila tayi ta tsaya tana kallonsa jikinta sai rawa yake tace a hankali wayyo
dadi sai naji Ina marmari....marmari nake sai naji Ina so a taba Bazookas
dina....lekowa tayi a hankali a boye ta yanda bazai ji ba tace Spark wlh nice
Jamilunka, Spark Yana zaune a Palo yaga ta leko tana magana cikin rada shi baya Jin
me take cewa,dariya ta bashi ba shiri ya murmusa,Ido suka hada ta koma kitchen da
sauri.

Naila dai Spark ya bari da tsumar jiki, jikinta Yana ta faman rawa,tsumi ya
motsa ta Dade a tsaye kafin ta iya ci gaba da aikinta, tana gama tuwon a leda ta
kwashe ta shirya a flask sannan ta fara miyarta ta Ugu da gyada.
Fitowa tayi ta wuce shi a Palo ta shige bedroom tare da furta Bazookas na
jira,Bai gane mene Bazookas din ba,ta sake fitowa ta tsaya Jikin kujerarsa da yake
zaune tace a kawo abincin? Kai kawai ya daga mata,taje kuwa ta shirya Masa a dining
sannan ta wuce bedroom .

Daddyn Beauty ne yace ta shirya sun gama magana da mijin da ya zabo mata zaizo
yau ta ganshi idan yayi mata shike nan,tace Abba waye? Yace yarona ne duk abinda
ake neman a wajen namiji na gari to wannan yaron yayi,Yaronka Daddy? Ae yarona nane
a shagona Dake kwari yake zamar min,bashi da kudi amma inshaallah zan mallaka masa
komai ke sabo da ke ma zan iya bar Masa shagon nawa yaci gaba da juyawa,na yarda da
amanarsa,yaron kirki idan baki aure shi ba kinwa kanki,Beauty dai ba wata murna
haka ta shirya tayi kwalliya cikin dinkunanta data karbo sababbi ta saka shadda
blue black me kyau ta Sha dinkin straight skert da riga,zuwa Yamma 5pm me gadi ya
shugo yace Hajiya karama kinyi Bako,tace waye? Yace wanda Abbanku yace miki
zaizo,kaishi palon Baki kace gani Nan,yace angama ya fice.

After 5mnt ta nufi palon ta shiga da sallama matashin ya Sha wankan shadda arsh
yayi kyau iyakar kyau,Beauty wani farin ciki taji ganinsa matashi kyakyawa da alama
duk kuwa da bata ga fuskarsa ba,zama tayi a kujera suna facing juna,a hankali ya
dakata da danna wayar ya dago a nutse,gaban Beauty ne ya fadi,da mamaki tace Ina
yini? Ya amsa tace yasu Mama? Suna nan lafiya, wlh kana bala'in kama da wata
kawata Naila,Mohsin yace kin Santa ne? ae a prison muka hadu,ta fara bashi labarin
Naila yanda ta yaudareta a matsayin Jamilu,Mohsin murmushi yake yace oh kece Beauty
kika bata kudi da waya ko,tace ae nice wai Kai Dan uwanta ne please? tace dama
Kaine Mohsin din? yace ae nine,tace mashaallah,murmushi yayi,Beauty ta tsura Masa
Ido tace Allah me Iko kawai Naila haske ta fika kadan amma kamar da kuke ta baci,
Mohsin yace hakane,shi dai Nan take yaji Beauty ta shiga ransa bata da shegen iyayi
da girman Kai irin na Yan matan yanzu,mikewa tayi tace Ina zuwa taje ta kawo Masa
kayan ci da Sha,tace sai naga kamar mun dade sanin juna sabo da na Saba da Naila.

Mohsin ya kalleta sosai ta gama tafiya da Imaninsa,yace Daddy ya fada miki Ina
da aure Ina da mata da Yata daya zaki iya zama da kishiya? Beauty tace ai ni bana
tsoron kishiya ko wacece ita,tace ai a wajen miji ake nuna isa,a nan ake gasa,idan
ta saka mini skert ni da pant zan fito af mu a fada mana iya shege,mu muke da
sirrin kula da miji, Mohsin yayi dariya yace uhm uhm bana son kuri karki kije ta
miki kafa,Beauty tace za a gani tun yanzu ka fada mata ni bani da fada idan tazo da
sauki taga sauki idan tazo da iskanci na iyashi page by page zan dinga bude mata
nawa.

Dariya yayi yasan yarinta ce kawai,yace to wacce irin kulawa za a min? Beauty
ta danyi kasa da Kai ana rufe fuska a hankali tace sai nazo gidan bazan fada maka
ba yanzu karka manta hularka sabo da farin ciki, yace ke kin san me akeyi ne ma sai
dai na koya miki,girki kika sani da shara,Beauty tace me ka Mai dani yarinya ko
me?, Yace ai ke gidanki daban Daddy yace ya bani,tace no da Aunty zamu tare ai
gidanka ne ba nawa ba karka ga wai ubana ne ya baka kace wai nawa wlh ba nawa
bane,ba ruwana ban San alakarku ba, yanzu ya hada mu, kaga kuwa duk abinda ya Maka
badan ni bane,idan haka ne ma ka Maida ita Uwar gidanka can ni a gyara min Wanda
take ciki ai nasan gidan har kofar gidan na taba zuwa tare da Naila gidane me kyau
wlh.
Mohsin sai yaga hankalin Beauty sosai yaji ta Kara shiga ransa Kuma ta birge
shi matuka.

Kamar sun Saba haka suka dinga hira sosai sai wurin magriba yace zai tafi,sai
lokacin tace ban gaisheka sosai da ladabi ba, na manta,dariya suka yi yace a haka
za a kula da mijin? tace sai naga kamar Naila ce mun Saba hira,karki fada mata
kinji ki bari ta Sha mamaki,Beauty tace to shike nan ta rakoshi,ya hau machine
dinsa Wanda yasha wanki,ya wuce.

Beauty ta koma ciki tana ta murna tayi Miji itakam, Chikar gayu ta kira tana bata
labari,Chikar gayu tace inye yan mata an dace, Yayan Naila ne tab to ya kika
ganshi? Beauty tace haduwa za aci uban love,Allah ke? Chikar gayu ta tambaya,tace
hmm Yana da mata wai Ashe,Chikar gayu tace to mene Ubanta zamuci kawai idan tace
zata mana iskanci,Beauty tace ah zata karba matukar tace baza a zauna lafiya ba to
sunanta sakakkiya domin tabarar da zanyi a gidan nan ta baci shi yasa nake so a
hadamu gida Daya taga salon Yan gidan yari,kyankyasar gidan yari,Chikar gayu tace
ke dai bari har naji ma ni ta fita an sake ta,ai baza ta iya zama dake ba,Naila ta
bani labarinta tace Dan iskanci wai idan taga dama sai ta bude nono a tsakar gida
tana yawo haka,Beauty tace Ashe Mohsin zai Sha kallo nonuka hudu a tsakar gida yaga
ta kansa,rabu da ita ai sai mu bude masa hudu rigis,tana budewa zan bude nima Abu
kowa da nasa,Chikar gayu tace yawwa mu da muka iya girgiza shi,Ashe gasar Nan tamu
zata yi rana oh duniya kinji kishiya dai dai mu,suna dariya Beauty tace ai yanzu
shuru zanyi kamar saliha sai na shiga zata ga karuwanci kin san Allah dama ta
tanadi kudin mota domin ta kulla da yaji kenan,ita da yaji sun daura
kawance,iyayenta sai sun gaji da maidota gidan miji,Chikar gayu tace ki tabbatar an
hadaku gida Daya dama Naila tace bata da mutunci,idan ta miki kawai design her
face,Beauty tace yawwa mu baza mu cuceta ba sannan ba ruwanmu da ita amma tana fara
iskanci a hankali zan jawo Dictionary Dina na rashin mutunci chapter by chapter zan
dinga budewa a hankali Ina koya mata Ina koya mata a hankali sai ta haddace shi
tsab.
Chikar gayu tana dariya tace yawwa tawan ba wani shege,a nuna mata lallai fa
munje gidan yari mu ba irinsu bane da suka zauna a iya gida,shi yasa Naila take
birgeni,ai ba a Kai banza gidan yari cewar Beauty, taci gaba tace dama nifa yanzu
kadan nake jira abokin mutuwa nake nema,na Dade bamu fafata da wata ba,Chikar gayu
tace ke dai bari rashin fada da tashin hankali Yana damuna,na gaji da hakuri kowa
salihi a gari na rasa Tantirin da yazo daidai Dani,daga Naila sai ke sai ni haba
mun wani zama kawaye bama fada kullum sai mutunci a gaskiya mutuncin yayi yawa.

Gidan yari Washer ne Wanda ya Rabauta da pant din Tantiriya ya fito daga wanka
sanye da wandon Naila da tabarwa Malam Sharu a haka daga shi sai pant din Naila ya
fito Yana karairaya ya nufi dakin su Malam Sharu,suna karatu ya shiga tumbur sai
pant Yana karairaya yace Salam bayin Allah bakwa gajiya ne, kunfi kowa karatu amma
Yan banza ma sai ficewa suke daga gidan suna barinku bayin Allah,ku dinga sararawa
kanku Dan Allah,wlh ni tausayi ma kuke bani dan dadin duniyar nan bakwa ji,ya kuka
ganni?nayi kyau Dan Allah? Allah dai yayiwa Jamilu albarka kaji dadin da nake ji
kuwa,su Malam Sharu suka Kalli washer suka ce Allah ya shirya.

Yace Ameen Yana fari yace tunda nasa wandon Nan nake kawowa,kayi asara Malam
Sharu daba saka ba,yo yanzu Nike Nan a wanka,Ina sakashi kullum sai na jini a harka
wlh tallahi abin yayi,daga sashi nayi wanka ya Kai biyar,Scoler ne ya shugo ahhh
washer me zan gani gaskiya kinyi kyau ahhhh Dan Allah in ka gama dashi Ina son
kwance,Jamilu guda ta saka a bar so a bar kauna Ohhh ni yasu wai idan ka gama
wallahi Ina son kwance nima na kwashi tabarakina.

Washer yace akwai wani kamar a kayan nata duba ka dauka kaima kaji ,Scoler ya
sake bude kayan Naila Yana bincike ya dakko wani pink yace kalar ta birgeni irin
tamu,wlh sai naji wani rassss nima bari naje na chake,ya sake daga pant din yace
nida falmaran haba sabo da Allah wannan duwawun na Jamilu ai dole sai katon wando
oh,lallai sai kace bodin mota,juyawa sukayi tare da ficewa.

Suna fitowa suka hadu da Goje ya kallesu suka ce Goje Dawa Dawa uban Dawa, kaga
Scoler ma ya Rabauta,Goje yace shashashu ana neman wajen da kansa kun kare a abinda
ake sawa a wajen, Kuna hauka,au Baku hakura da Jamilu ba har yau? Goje yace never
wlh sai ta dawo gidan nan ai mun kafa mata kahon zuka,ita muke so,Kuma kullum a
cikin fafutukar nemanta muke sai mun samota yanzu ma mun sa anyi gabas ana
nemota,Dariya Scoler yayi tare da furta wata sabuwa inji Yan chacha Kun dorawa
kanku aiki,ke kiji Dan Allah washer wai sunyi gabas nemanta,Washer yace to Allah
yayi yamma da Naila su suyi gabas din.

Bangaren mata kuwa Mama data kashe Asmau Bata Saba da wahala ba amma a nan
gashi nan ta shiga wani hali,ta rasa Inda zata saka kanta,ga Yan matan ciki basu da
kunya,duk da Yan uwanta sun sa an maidata layin manya vip amma Ina sam,duk ta rame
tayi duhu,ga sauro Idan dare yayi haka zata fito tayi ta birgima tana susa ita ga
Yar Madara,akwai wata matashiya a ciki ta sa mata ido kullum da dare idan ta fito
ta ishesu da wayyo sauro ta kwanta tana ta malelekuwa a kasa sai yarinyar tazo tayi
ta Sosa mata jiki tana waka a Sosa...a Sosa..har wasu suma ko wacce tazo wucewa sai
ta Sa hannu ta yakushi Mama tace a Sosa sannan ta Kara gaba, ayi ta dariya,har suna
suka sa mata Mama Comedy, tunda taga haka ta daina wannan iskancin bata fitowa.

Umma kuwa tunda ta haihu yaranta idan suna gida suke yin komai,idan Kuma suna
makaranta Hashimu Dolo ke yi,yau ma da yamma ba kowa a gidan ana saura kwana biyu
suna,sai shi sai makwafta da suke ta shugowa,shugowa yayi wasu mata su biyu suna
zaune suna hira ya kira Umma da Yar Inna me kike so yanzu a dafa ruwan shayi ko
kuwa kunu zaki Sha? Umma tace a'a Abban Mohsin ruwan shayin dai kunun kanwar nan na
jiya daka dama min yayi zafi da yawa,yace haba Yar Inna yo ai sai ki fada nazo na
fifita miki,su dai mata Yan barka suna Shan kallo wasu ma sabo da Hashimu da Umma
suke zuwa gidan wai su a dole masoya, ita kuma Umma Dan ace ta mallake mijinta take
ta wani goyawa Hashimu baya,ba a dade ba Hashimu ya kawo flask na ruwan zafi ya
ajiye a gefen Yar Inna yace Yar Inna gashi,ya duko yace Yar Inna wanka fa yanzu
zakiyi a hada ruwan ko sai anjima?

Umma ta shagwabe tace ni sai anjima kar a dafa yanzu,Abba yace sorry sorry Allah
ya kaimu,ya fito ya zubo mata danwaken da yayi a plate ya kawo yace a kawo Maggi?
tace barshi haka,yazo ya dauki new Baby tare da shigewa bedroom da ita.

Matan da suke zaune suka ce wlh ke dai Kubra kinyi dace ki godewa Allah,irin
wannan mijin ba kowa ke samu ba,sai kace Jinin larabawa soyayya bata tsufa,Umma
tace to kana zamanka da mijinka lafiya ya kawo biyar ka kawo goma ba a San ya kuke
zamanku ba mutane a dinga cewa ka mallaki miji,dariya suka yi suka ce ai gaskiya ce
kin mallaka shi Kubra.

Abba yana jinsu suna zancen mallake miji,yace a'a na tuna da Batoola wlh aure
zan Kara fa Ashe, ya tuna ya fito ya mikawa Umma yarta yace riketa zanje wajen
Batoola ni wlh sai yanzu ma kuka tuna min zan Kara aure, dariya ta kama matan nan
amma ko ba komai Umma tana shanawa duk da dolancinsa,mutum zai Kara aure amma ya
manta ma,suka dinga dariya.

Mohsin kuwa sau uku Yana zuwa zance wajen Beauty ba Wanda ya fadawa,sun shaku
sosai da sosai,wani mugun kaunar juna suke kullum baya shiga gida da wuri sai yasha
soyayya a waya da ita,sai yanzu yake Jin kamar ma yanzu ya fara soyayya a duniya
Beauty ta tafi da Imaninsa,ko ta Hanan baya yi,kullum suna manne a waya da
Beauty,haka Idan Yana wajen aiki,Hanan dai Taga duk ya canja mata amma bata taba
Jin yayi waya da wata a gidansu ba,ta rasa gane kansa Sam sam,gashi da Yana yin
Sallar Isha yake dawowa yanzu ya daina,watarana kuma sai taga da yamma ya dau wanka
na gaske ya fice,shi Kuma Mohsin mamaki zai bata sai an kusa bikinsa da Beauty zai
fada mata,ganin haka Hanan ta fadawa babarta abinda Mohsin ke mata yanzu,tace zanje
gidan Malam sani na karbo miki rubutu kin san dangin Miji idan suka saka gaba to
sai sun ga bayanka.

Naila kwananta biyar a gidan Spark tunda yasan me ya hada mata sai ya daina
fushi kullum tayi girki yaci ya koshi ya fita idan ya dawo da ita yake tozali kamar
ya lasheta haka yake ji,yawan kallonta da Taga Yana yi sai Naila tace to ko Hallare
bata kwanta bane nifa mutumin nan tsoro yake bani, fitowa tayi sanye cikin atamfa
riga da skert tace bari na gwada na gani Hallaren bawan Allah Nan tana aiki ne ko
bata yi, Yana kwance a Palo tazo cikin damammen skert ta fara mopping wajen Kal Kal
dashi tace Sir zanyi mopping ta dawo gabansa,mikewa yayi zaune Yana chanja channel
tana gabansa ta duka tana mopping,Spark yace wayyo kabarin me tatsine,Naila tana yi
tana girgiza tana goge waje daya,Spark sai hadiyar yawu yake a hankali yace aure
taho Dan Allah,aure kana inane wai,duk ya wani rude, Naila ta matsa sannan ta juyo
tare da kurawa Hallaren Spark Ido a wando tace Kai Sir abarka....tana zaro ido,yace
what? Mikewa yayi tsaye,Naila tace Subhannallahi maganina baya aiki wlh ka ganta
Kai Kai Kai Inci nawa ce? Kallon Inda yaga Naila tana kallo yayi kunya ta kamashi
shi sai yanzu ya gane ma abin da take kallo,dariya ta bashi yace inchi tara ce,ko
kina so? Kai ta fara sosawa tace ae,a'a,ae,a'a.
Tsaki yaja ya wuce sama Naila ta bishi tace tsaya sir,a ranta tace Kai maganina
bayayi wlh,Sir tsaya mu gani.
Spark harda karawa da gudu yace ni wannan na rasa gane mata,dariya ya ba Naila
ta dinga dariya tace kan uba Zuru sunan wani gari.

Washe gari da yamma Taga yaci wankan da Bata taba ganin yayi ba,mamaki ya
kamata,sai ga Wahida taci gayu ta shugo,sorry Baby na ajiyeki kina jira,tace ba
komai my love muje, Spark yazo a gaban Naila ya rikewa Wahida hannu,Naila tayi
sauri tazo ta raba hannu ta fisge hannun Spark,idonta ya ciko da kwalla,tana Ina
Ina tace am...um....wallahi ...nice....nice...hannunsa ya kwace yace muje suka juya
zasu tafi ta jawo Spark da karfi,ya kalleta,tace zo muje kaji...hannunsa ya
fisge...gabansa ta tare da gudu ta tsaya,taki magana Kuma,gefe ya tureta zata Fadi
yayi Maza ya rike abarsa wai kar ya Fadi yace matsa ransa a bace,matsawa tayi tana
kallo suka fice,Naila tace bazan yi kuka ba ta daure dai bata yi kukan ba,amma zama
tayi ta kasa magana.

Sai dare ya dawo ta kulle shi a wajen Yana ta knocking tana Palo ta zauna ranta
a bace haka ta mike sanda taga dama sannan ta bude Masa ta koma a fusace ta
zauna,ya kalleta kawai yace Wahida tace a gaishe ki,ko kulashi Bata yi ba,ya sake
cewa tace kin iya girki,shuru tana fushi idonta ya ciko da hawaye,mikewa tayi
fuuuuu tayi cikin bedroom, dariya ya zauna ya dinga yi yace saura ki cire hular
gashin da kanki,ai kuwa kamar ya sani Naila sai gata ta fito ba hular gashi da
kanta a bude ba glass wai Dan ya ganeta,Spark ya nuna Sam bai gane wace ba,aransa
dariya yake kamar ba gobe,Naila ta zuciya tace gobe inshaallah zanje saloon a sake
yi min Daadaa zansa kana nan kayan Maza na gani ai dai dole ya gane Jamilu ce.

A dinga sharhi Dan Allah

Kuyi hakuri fa wlh


Uzuri ke rikeni Kuma Ina so na muku da yawa ne.

A rike Amana fans Dan Allah karku fitar badan halina ba Dan Allah.

AsmaBaffa
[12/16/2023, 8:05 PM] AsmaBaffa: PAID GROUP

Accnt no
0175487861
Asmau Garba Muhammad Gtbank

Katin MTN
08061929616

Yan Niger
+22790795939

🏫 TANTIRIYA🏫
A GIDAN YARI

BOOK 1
56-60

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM

Page naku ne
Mom Khalisat
Alhmdllh for everything
Aisha Umar
Ummu Maryam
Faeeza
Golden pretty
Hajia Baba Nunuwa
Maman Samha

Hey lovelies

Ke matar aure ce kuma kina neman business din dazakiyi daga gida da kuma baya
bukatan jari?

Kai dan makaranta ne kuma kana neman inda zaka ringa samun kudin kashewa?

Ko a'a ke kinada business dinki Amma kina neman wani side hustle haka da zai Kara
Miki extra source of income?

Ko kinada business idea da kikeson kifara Amma Babu jarin farawa?

Toh duk ku tarkato wannan training din, dan ga solution nan nasamo muku, kawai ki
danna wannan link din Dan Samun damar shiga group din

https://wa.link/49vn47

Sai da yayi wanka ya fito Yana zuba kamshi cikin kananan kaya marasa nauyi
wasu sky riga da dogo wando wasu milk,Naila tana zaune a Palo kallo takeyi abinta
yazo ya zauna ya Sha kyau,kallonsa ta sata ya mata kyau sosai tace Kai gaskiya
bazan bari Ina kallo a kwace shi ba mene ma amfanina wai ne Ina mace,har sai na
koma nayi Daadaa zai gane ni,amma dai nayi nayi kitso mana na Yan gayu kitso dai ai
Yana fito da aslin fuskar mutum,to ko kayansa zan saka,a'a me ya kaiki calaba
zanyi,tana ta tunani yayi magana ya Kai sau hudu bata ji ba,sai da yayi da Dan
karfi yace keeee Cheffff.....Juyowa tayi da sauri yace me kike tunani haka? Naila
tace Babana na tuna idonta ya ciko da hawaye ,wayarta ce tayi kara ta duba taga
Mummy,dagawa tayi tace Hello,Mummy tace Nasiba Yankan Kauna na samu labari me
dadi,bugawa nayi in miki godiya aikinki Yana kyau,kinji har ya samu mata yanzu ma
zancen aure akeyi wlh dangi ana ta murna Kuma gata Yar uwarsa,Naila wani bakin ciki
ya cikata ta daure tayi murmushin yake tace ai aiki Yana kyau a ranar kaka yazo da
kansa Alhmdllh,sabo da haka ana daurawa zaki ji Alert inshaallah,ke ni sabo da
murna ma ranar zan Kara miki kudi,ke sai dai ranar daurin aure tace na gode su Mima
duk zamu samu lokaci har gidanku zamuje godiya,tace Allah ya kaimu.

Tana kashe wayar ta zamo daga Saman kujera suuuuuuu ta dire gwiwoyinta a kasa
ta juya tare da kifa kanta a Saman kujera tana Dan danne hawayenta, Spark yace
lafiya? ba komai ta furta, yace to me kika dafa? Tuwo,yace wai Baki da wani girki
sai tuwo,ni bana cin tuwo ko yaushe,taya za ayi ta yiwa mutum tuwo a gida,kawai ma
Dan na taba zama a gidan yari ne amma ni a baya ma bana son ganin tuwo,kullum tuwo
miyar taushe,tuwo miyar kubewa,kuka,gyada etc oh can't realize that I'm tired of
eating tuwo? everyday tuwo,tuwo tuwo for God sake,bazan ci ba ni,Naila tace tayi
dadi miyar,yace komai dadi bazan ci ba,kiyi min Briyani rice,ko pilaf rice,Naila
tace Biryani Kai Dan India ne? Sannu sai ka bari kaje India Kaci a can ni in ba a
film ba Ina na taba Jin Biryani,sannan pilaf take ko me a bakinka na taba ji yau,ni
Yar gargajiya ce,yace to dafa min Indomie amma indai tuwo ne bazan ci ba.

Tashi Naila tayi ta shiga kitchen ta sake duba YouTube yanda ake dafa Indomie
ta Sha hadi,ta Dora Indomie ta dafa kwai kawai guda takwas,gefe ga Indomie tana
dafawa,harda yin jajjage,aka yanka albasa me lawashi,carrot,da green beans duk a
ciki,kafin ta kwashe ta bare dafaffen kwanta sannan ta juye Indomie a plate tare da
jera kawai guda uku a tsakiyar Indomie,ta dakko wani dogon green chilli ta wanke ta
saka shi a haka tsaye ta tsakiyar kawai ukun,ta wanke ganyen salat ba tare data
yanka ba shima aka jera su a bayan green chilli sai tayi Yar flower dinta a
tsakiyar girki,aka soka fork a gefen ta fito irin gwana tayi girki,Spark tunda ya
hango plate din daga nesa da ganye falaa ya dinga dariya a ransa a fili ya fuske,ta
kawo tace gashi.

Karba yayi yace professional cook ah'ah wannan girki haka,Nail tun kafin yaci
ta zuba masa Ido tana so yaci taji da dadi,Spark yayi spoon Daya yaji tayi dadi
yace best chef in the world,this Indomie sweet woooo ah'ah,Naila sai murna tace
style nayi tana wasa da yatsunta yace kin iya,kitchen ta koma ta koma, ta kwaso
kawai biyar a plate ta zauna tana cin abinta,yace to wannan girki irin na kasar
waje daga china kika koyo ne? Naila tace Allah ya kiyaye ai mu sai dai a
kwaikwayeni badai na kwaikwayi wani ba,Spark ya ciro ganyen salat Daya yace to
wannan ya ake Masa? Naila tace kamar ba Dan gayu ba gutsira zaka dinga yi,Spark ya
balli salat a ransa yace na koma cow yau, Kuma kace baiyi ba aji haushinka ya zanyi
so ne ya ja min ya cinye salat Yana cin Indomie,green Chili kuwa daukewa yayi ya
boye a kasan kujera kar tace bai ci ba salat sai ya cinye tas da Indomie,Naila ana
ta murna tace zan sake dagewa amma da ya kushe bazan yi ba.

Abba direct gidan Malam Isa ya tafi abokinsa akan suje zance wajen Batoola,
Malam Isa yace wannan mayaudariyar Kai baka San ma me tayi ba? to tayi aure tuni
yanzu idan da rabo to an samu.
Abba da mamaki yace Batoolar? Yace kwarai kuwa,Abba yace to shike na itace tayi
asarar samun miji Irina,amma Batoola ba karamar asarar miji tayi ba,har Ina cewa
kwana biyu idan na aureta zan huta da fadar sunan Kubra sai aji Ina cewa Batoola
amma kullum kiran sunan mace daya Kubra zo,Kubra yi kaza, Kubra kaza,amma idan na
Kara ai na huta da kiran sunan ko da na kwana biyu ne,Malam ya isa ya dinga dariya
yace dama Kai sabo da ka samun canjin kiran suna zaka Kara? Abba yace Allah ya Gani
da ace Batoola sunanta Kubra to ko sonta bazanyi ba,fadar sunan ya isheni haka
kullum babu ranar banza sai nace Kubra,amma Batoola ta cuceni da na tsaya na koya
mata yanda ake hada jullof da kifi yanzu wani zata je ta dinga dafawa,Malam Isa
dariyar abokinsa yake yace sunan Wanda ta aura Usman,Abba Yana ji to su karanta ita
da Dan Usmana,dama Kubra ta fita komai,ai Yar Inna itace mace dama Batoola har wata
macece,Yar Inna Inda kasan a hadisi aka rawaitota bata tsufa,sallama yayiwa Malam
Isa ya koma gida,Yana shiga gidan ya iske Umma ta fito daga wanka tana bawa
Jaririya nono,ya Kalli nonon yace Yar Inna ki dinga godewa Allah,Kalli Mohsin harda
matarsa da yarsa amma Kai ba Sha nonon ba,Kalli Naila dan Allah ta saki Hidaya ta
karba,itama ta bawa Aslam ga yanzu da Jaririya ta Kuma karba ai ke wlh macece,Umma
tace Kai ni yi min shuru yanzu fa kace aure zaka yi,Abba yace to na fasa nayi mata
fata fata nace kar ta sake kulani ni ke nake so,Umma tayi dariya Abba bai San Umma
tasan Batoola aure tayi ba

Umma tace Allah ka koreta? fata fata nayi mata me zanyi da wannan banza ma,da
ace na auri Batoola gwara na zauna kullum in ta goyaki,yanzu gobe suna ko Yan uwa
zasu cika gidan anjima to kar wacce ta hau min gadona yawwa idan ma zasu kwana to
su kwanta a kasa ni Kuma Ina Saman gadona,Umma tace ni wannan jarabar taka ta
isheni fa duk Sha'ani sai ka kunyata ni a mutane sai mata sun cika daki sai kazo ka
haye gadon Nan,ni da gidana ba me takura min.

Ana gobe suna Umma dinkunanta sun Kai kala shida,kayan jaririya kuwa kaf Mohsin
ya hada mata komai da komai,Abba kuwa ba uwar da iya,amma Mohsin a sirri ya siyo
katon rago yasa wani ya kira Abba kofar gida ya kawo Masa ragon,yace Mohsin ne yace
a kawo Maka,mutumin Mohsin ya kira a waya ya daga,yace ka bawa Abba wayar,aka bashi
waya Abba yace hello Dan Albarka,Mohsin yace Abba gashi Nan karka ce nine na siya
Maka idan ka Kai kace Kaine ka siyo kawai sabo da Umma ta daina rainaka ,Abba yace
Allah sarki Allah yayi Maka albarka na gode,Abba gidan yaja rago ya shiga da
shi,Aslam da Zarah suna Murna Abba ya siyo mana rago,Abba yace Mohsin ne ya siyo
amma yace kar nace shine ya siyo min kawai a barshi ni na siyo,kuce ni na
siyo,Aslam da Zarah Dake yara ne suka ce kuwa Abba Kaine ka siyo yeeeee,Umma tana
jinsu tace Allah ya kyauta.

Abba dakin me jego ya koma anyiwa Jaririya wanka ana gasa mata cibi ya karbeta
yaci gaba da gashin cibiyar da kansa,Umma dakinta taje tana shiryawa ya kawo mata
Jaririya lokacin tana shafa Humra,yace an samu lafiya harda shafa turare da kuwa
sai warin gardi gata bata nono Kubra,a gefen bed suka zauna Abba harda zugewa Umma
zip din riga ya wani wangale rigar, Umma tace dama duk sun cika har ciwo suke min
bata Sha da yawa,Abba harda taba nonon ya Kalli Umma yace da zafi? Umma tace
ae,yace muje na tatse shi kwarya a zubar, dariya Umma tayi tace sai kace wata
saniya kaima ka Sha ku hadu da Jaririyar ku shanye shi,Abba yace uwata ta dade da
yayeni wlh kice zaki dawo Dani jaririn dole,to ni wata 20 ma Ina Shan nonon
uwata,ba 18 aka yayeni ba,to naji dan Allah cewar Umma.

Yana suna mutanen kauye sunzo Yan Fulani dasu gaba daya,suna ta aikin suna,ga
makwafta sun shugo duk da Umma tace ba taro za ayi ba amma Abba yace wlh shi sai
anyi taro har da tirsasa Mohsin lallai ya bawa su Hidaya kudin Dj,haka aka dakko
Dj,washe gari suna Abba an Sha shadda ruwan Toka sai hada hada yakeyi,shi Mohsin ma
Abba dariya yake bashi sai kace wani ango kamar yau aka taba Masa haihuwa,
A layin har tsokanarta suke,ranar Kuma sai ga Spark yazo shi bai San ma suna suke
ba,a wata dalleliyar mota me tsadar gaske driver ya kawo shi,Mohsin ya kira a waya
yazo ya same shi,tunda ya saci wayar a wayar Naila Yana yawan kiran Mohsin,Spark
mota driver ya bude Masa ya fito a hankali cike da ji da mazanta ya tsaya a Jikin
mota kusa da gidan Abba,Yana kallo Hidaya ta jawo zugar kawayenta sai iyayi suke
sun dauki wanka suka wuce ta gabansa sai kallonsa suke,suna wani canja salon
tafiya,dariya suka ba Spark wacce tafi kowa iyayi ya kalla kamar bai kalleta ba
yaga mayafin ma a hannu ta rike kamar masu biki yace au suna fa akeyi,dama har
yanzu ana bikin suna,Dj ne ya saki sauti su Hidaya tun kafin su karasa suke uban
rawa,Hidaya tafi kowa zakewa,yace duk yanda akayi wannan kanwar Naila ce amma Naila
ta fita kyau,jikinsu ma Daya bane,Hidaya wata Yar firit ce Bata da kibika ko kadan
sai iyayin tsiya da giggiwa.

Mohsin ne ya karaso wajen da fa'a yace Ashe ka karaso Spark mota Mohsin ya bude
ya shiga shima Ashraf motar ya koma sannan ya mika Masa hannu suka gaisa,Hira suke
yi sosai sun Dade suna magana kafin daga nan yace ya kamata naga Umma na Mata
barka,Mohsin yace gidan ne akwai mata da yawa ban sani ba ko zaka iya shiga,yace
zan iya ni wacce Yar katuwa nake Jin kunya muje kawai,Mohsin yayi dariya sannan
suka wuce ta Inda ake Dj mata sai kallonsa suke suna yabawa,wasu har suna cewa Dan
waye wannan a kasar na,Spark dai har kofar gida,Mohsin ya shiga ciki tare da fadawa
Umma ai saurayin Naila ne yazo wannan Spark din na prison,Umma tace Innalillahi wa
innailayhirrajun Ashe saurayin Naila ne,gaskiya naji dadi Naila ta da saurayi
Allah me Iko,Daya dakin da ba kowa aka Kai Spark ya shiga,Umma taci gayu ta Sha
kyau dama gata fara tana zaune a kujera,Spark da sallama dauke a bakinsa ya shiga
dakin,Umma ta amsa tana kallonsa yanda ya sake mugun haske da kyau abin ba a cewa
komai,a kasa ya durkusa tare da gaida Umma ta amsa da fara'a sannan ya mata Allah
ya raya tare da karbar Yar yace ya sunanta? Umma tace Basma, mashaallah Allah ya
mata albarka,Bai Dade ba ya ajiyewa Umma 100k ya fice Umma tana ta godiya.

A kofar gida yaga Abba tare da su Hidaya da kawayensu suna cewa Allah Abba sai
ka Kara mana kudi,Dake shi Abba yanda yake tsokanar yaransa haka yake yi da kawayen
yayansa ma,shi yasa duk in suka zo Abba suke neme su,Hidaya tace Abba kudin
liki,Mohsin ne ya gasawa Hidaya harara tayi shuru,Abba ya ja gefe ya fada Masa waye
Spark,Abba anga suruki harda nutsuwa suka gaisa sosai sannan ya yayiwa Abba kyautar
ban girma ta kudade,Mohsin ma ya Sha kyauta.
Bayan suna Mohsin ya fadawa iyayensa game da auren da zai Kara ya musu bayanin
komai,Umma tayi guda tafi uku sabo da murna tace Ina goyon baya,yanzu da Malam Isa
da Yan uwan mahaifinku sai suke a Kai kudi a tsaida rana,Abba yace da ni naso na
fara kara auren Mohsin amma tunda ka riga ni Allah sanya Alkhairi.
Hanan kuwa ta rasa gane kan Mohsin sai faman Shan magani take da turare ba ji ba
gani amma shuru.

Bayan kwanaki Spark Washe gari Yana fita Office Naila taje saloon aka wanke mata
gashi tare da rangada mata kitso kanana sabo da fuskarta ta fito sosai,tana dawowa
gida ta samu Spark ya dawo Yana Palo a zaune.
Yace Ina kika je? Naila taji tsoronsa sosai tace saloon naje fa ka gani ta bude
kitson dama so take ya ganta,taje har gabansa ta Dora kanta a kusa dashi tace ka
gani ta dago fuskarta sosai tace nice nan fa,Spark yace na gani a ransa sai dariya
yake a fili ya nuna Sam bai ganeta ba.

Wahida itace tayi sallama tare da shugowa ta Sha wanka harda Yar wata jaka a
hannunta tana zuwa ta samu Spark a Palo Yana aiki a system Naila tana kallon film,
tace honey ya kk,Spark yace Alhmdllh,Mummy ce tayi sallama ta shugo tana murna yau
dai atamfa tasa tafi kyau ma,tana zuwa ta zauna tana fesa kamshi,Wahida tace tare
muke da Mummy,Naila kuwa Mummy ta gaisar sai Mummy ta mata wani banzan kallo Kuma
yau,ta juya tana amsa gaisuwar Spark,Naila ta kalla tace zo Ina son magana
Dake,Naila ta mike ta bita suka fita waje,tace yawwa fada miki zanyi ki tsaya iya
matsayinki karki shiga harkar spark my son aure zaiyi,maganin da aka saki shi
zakiyi naji Wahida tana fada mana kina mata kallon banza kina shigewa Spark,bazai
auri Yar film ba ki tsaya a iya film dinki,wallahi ba Yankan kauna ba ko girbin
kauna kike ba ruwanmu ato.

Naila tana gama ji ta ja tsaki ta juya Palo,Wahida sai wani zuba take,ta mike
ta shiga kitchen ta dakkowa Mummy lemo ta dakkowa kanta da Spark ta zauna suna
Sha,Spark Naila ya mikawa nasa ta karba ta balle tana Sha,wani takaici ya kama
Wahida,Amma bata hakura ba ta koma kusa da spark tana shakar kamshinsa ta fara mika
Masa lemon a baki,ya dinga Sha Yana satar kallon Naila,duk kitson da taje saloon
aka rangada mata wai bai gane ba,tana kallo Wahida tana bashi a baki Yana Sha,Mummy
sallama tayi Masa ta tafi,Naila idonta ya ciko ta mike da sauri ta shiga
kitchen,tana shiga sai kuka,tun tana yi a hankali sai ta fashe da kuka har wani
shidewa take, tana Jikin Sink ta Dade tana kuka taji shigowar mutum da sauri ta
fara kokarin goge hawayenta,Muryar Spark taji yace me kike yi ne,Muryarta tana rawa
alamar kuka take tace plate nake wankewa,are you crying? Da sauri ta juyo fuskarta
sharkaf da hawaye,kuka ne yaci karfinta ta fice da gudu daga kitchen din ta fada
dakinta,kamar me ciwon ciki haka ta rike ciki tare da dafe bango ta durkusa tana
tsafiya a haka da ruku'u tana rusa uban kuka ta fada Saman bed tana ta kuka,Wahida
ita tuni ma ta tafi tana murna ganin Naila tana kuka.

Spark ne ya bude kofar da sauri ya sameta a zaune tana sharbar kuka,yace


menene kike kuka haka? Me aka miki,Wahida tace....cikin masifa Naila ta dago tana
kallon Spark tace haka ka iya Wahida kaza, Wahida komai Wahida can't you see I'm in
love with you? Spark tsayawa yayi yace oh dama ba aikin ne ya kawoki ba sone
kenan,wallahi ina sonka ba zuwa nayi na cutar dakai ba,Jamilunka ce Naila ce nasan
ka ganeni yau ta mike tsaye tare da matsawa jikinsa sosai,saura kadan ya rungumeta
Dan ya danne zuciyarsa ne,yace to me yasa kika boye min baza ki zo min a Jamilunki
ba,zaki rufeni kina boye min abubuwa ta ya zan yarda dake shi yasa kawai na zabi
wata Kuma yanzu kin San dai anyi sa rana ma tuni sabo da a shirye nake ma gobe
friday za a daura aure wallahi kinji na rantse ba wasa nake ba aure za'a daura min
gobe inshaallah.

Tana tsaye tayi mutuwar tsaye ya fice ya Bata waje,ranar Naila kuka ta yini yi
ta kawana Bata iya ko lekowa ba,Kuma tace wlh bazan bar gidan ba na gani yanda za
ayi dani.

Washe gari Naila tana ganin kamar wasa sai Taji abokai ana ta dariya ana
tsokanar Spark sai murna yake ta leko ta kofa Taga ya fito Yana zuba kamshi da wata
uwar shadda me tsada da babbar riga farare ba kamarin kyau yayi ba,a bokansa Suna
cewa kayi sauri fa time ya kusa,Spark ya fito Yana washe baki suka fice,sai wurin
4pm sai gashi sun shugo da su Kamal,Naila tana kwance a kan gado tana ta faman
kallon pics din spark da bai San ta dauka bama,tana hawaye tana kuka,Spark harda
cewa yau sai nayiwa kaina guda wlh,abokai sai dariya suke,Yana cewa aure yazo na
kira shi ya amsa,Kamal yace muje reception din,suka Kuma ficewa da su Rafeeq,Mummy
tana gidan Mima ana ta shagali tace wai ni naji kamar ana cewa Kano akaje dauro
aure su da zasu je gidan Maman Wahida wai ya haka ne,Mima tace to Dan iskan yaro
komai har lefe Dana hada Masa kwashe abinsa yayi wai da kansa zai Kai Kuma ni naji
Maman Rafeeq tace itace ta Kai lefe,ni na rasa gane wannan kan aure amma koma mene
wlh da sanin Papan su Spark tunda ai danginsa ne suka Kai kudi da komai,ni gaskiya
auren Nan akwai wata a kasa Spark munafuntar mu yayi komai ya hana mu muyi daga
Ubansu sai Yan uwansa sai Kuma abokai ni wannan wanne irin yaro ne,Mummy tace ni
nayi mamaki ya hanani na tsoma bakina a harkar aurensa wani bikin arziki ne wai ace
sati daya jal har an saka rana an daura aure.

Wahida ce ta shugo palon da gudu tana rusa kuka wlh ba Dani aka daura ba,Daddy
yace da wata aka daura a Kano shima labari yaji,an zalunceni anci amanata an
yaudareni,Mummy tace ya tabbata, ta kira Spark a waya tace Kai kana Ina Dan uwarka?
Yace Ina airport ni da amaryata mun wuce Honey moon,Wayar Mummy ta katse tace
zai iya aikatawa bata San Spark Yana gari ba,tace ai Banga amfanin biki ba, uban
kowa ya watse ku tashi jama'a kowa ta tafi dakin mijinta tayi bautar Allah ango ya
tafi turai da amarya kowa ta hada shirginta biki ya kare.
Amma wannan ango anyi marar kunya cewar Maman Misam tace ah biki ya kare
Kam,Mima tace a fadawa masu girki su sauke tukunya.

Mummy sai bi take part part tana cewa biki ya kare kowa ta mike ta tafi gidan
mijinta a tashi a tafi, Mutanen kauyensu suka ce to Dan kawai ango ya tafi sai a
fasa biki haka akeyi,to abinci kuke so kuci ance an fasa kuje ku dafa a gidajenku
babu me ciyar daku yau.

Spark sai dare ya shugo gidan wanka yayi sannan ya shirya cikin kayan baccinsa
riga da wando sky ya fito yayi kyau,dakin Naila ya bude ya sameta tana ta faman
hada kayanta a akwati tana kuka zata bar gidan gobe da sassafe, hannayensa a aljihu
yace Ina zaki je Jamilu? ban sani ba tana hawaye,dariya yayi yace haba
kawata,tafiya zakiyi ki barni baza ki tsaya Kiga first night ba? Naila banza ta
Masa,rungumeta yayi ta baya,ta fara fisge fisge tace ka sakeni zan zageka
wallahi,sau nawa Kuma kika zageni ni,haba my wife,I'm sorry ya furta Yana kokarin
cire mata riga,mamaki ya Bata,ta kwace kanta da kyar, tana huci yace wlh yau sai na
taba Boobs, tsaki ta ja ya turata Saman bed ta fada Kai ya bita,tsalle ta buga ta
dire a kasa,tace wanne irin rashin Imani ne wannan kayi aure kazo zaka keta min
mutunci,Spark yace wlh gwara ma ki tsaya yaje ya sawa kofar key,Naila ta fashe da
kuka tace wlh bazan yafe Maka ba,Spark wayarsa ya zaro tare da kiran Mohsin yace
Yaya Mohsin gata tana ta kuka kayi mata magana,Wayar ya mika mata Naila ta karba
tace Hello Yaya,yace Na'am yace Naila kinci amanata Ashe dama a gidan namiji kika
je kika tare,yanzu idan ba mutumin kirki bane da tuni ya lalata miki rayuwa,wannan
takaicin wlh yasa da yazo ya fada mana komai da rayuwarku a gidan yari Umma ta
fusata tace lallai indai Yana so a daura aure Kawai,mu Kuma yau aka daura miki aure
da shi sai ki zauna da hujja tunda haka kika zaba,Kuma karki Kuma kirana daga
yau,Umma ma karki nemeta kije mun fita hakkinki mun daura muku aure,Naila ita Sam
Bata ma ta fushin da suke yi da ita,kawai mamaki da murna ne suka kamata amma a
zuciyarta,tace zanzo Yaya dole ka hakura wlh,Wayarsa ya kwace ya kashe,Naila tace
gidan zanje ka bude min kofa,Spark yace ai kinzo kenan tunda kika kawo kanki,fuska
ta bata sosai tare da furta ka bude min kofa nifa ba Yar iska bace,Spark a nutse
yace ni kuwa shine Dan iska ne ni.

Shuru tayi Masa ta tsaya a Jikin kofar,Amarya jimiluna zo ki kwanta ba abinda


zan miki am serious gobe har gida zan kaiki ma,Naila tace ban yarda ba kawai ka
cuceni bazan zo ba,wai baki yarda dani ba bana son taurin Kai wlh zan fasa kaiki
gidan na kulle ki a daki kin san halina,Baki ta turo gaba tare da makale kafada
tace kaje wajen abar kaunarka ku kwanta ,tashi yayi ya bude mata kofar yace jeki
Madam gobe idan kika ganni da Wahida karki damu mutane da kuka,tsoro Naila taji,ya
fice daga room din ya haura sama,Naila tunawa tayi da wahalida ta fito ta bishi da
sauri tana cewa gani mene ne?nifa Malam ka dameni ta furta tana shiga bedroom
din,kallonta ya shiga yi sanye cikin Kayan bacci wando dogo da Yar riga me gajeren
hannu pink da adon cartoon a jiki,yace me kike haka kamar yarinya Naila ta karasa
Jikin bed din ta zauna a gefen tace Gani,Yar tsuka yaja tare da furta idan zaka
kwanta ki kwanta ya furta fuskarsa ba wasa, haka Naila ta samu ta Dan kwanta badan
ranta ya so ba ta kwanta a gefe,murmushi ya saki me kayatarwa a ransa ya furta haba
ai gashi nayi maganinta na huta da raini,light ya kunna ya karo hasken yakwanta a
gaf da jikinta, tana jknsa tsoro ya cika mata zuciya,a hankali ya Dora hannunsa a
hips dinta,Naila Bata yi motsi ba tayi mutuwar tsaye sabo da tsoro cike da nutsuwa
ya dinga matso da hannun zuwa cikinta a hankali ya jawota tare da manta jikinsa.

Naila ji tayi Hallare a mike abinka da so baya iya barin mutun ya dauki wani
mataki,gaba daya haushin Spark take ji idan ta tuna Wahida,magana ya mata a kunne
yaji bakin na Naila ya mutu, shuru,yace kece Jamilu? Naila tace ban sani ba,dariya
yayi ta da maida hannunsa Saman cikinta Yana shafawa a hankali Yana wasa da
kyakyawar cibiyarta,jikinsa ne ya dauki rawa sosai itama Naila haka,hannayensa y
sake sawa a hankali ya janye rigar Naila sama wacce ba bra ba komai,rigarta take
kokarin gyarawa amma ya hana Hakan,kokawa suka fara sosai yace wait wait,Naila ta
juyo da kyar a jikinsa suna facin juna tace please Stop,bana so Allah,yace oh wai
karfi kike gwada min,jikinsa ya fisgota ta fado yasa hannaye tare da rungumeta a
jikinsa,wani kamshinsa me sata nutsuwa, Dan Allah ka bari, wai kin daina so na
nane? Oh ka ganeni? Murmushi ya saki Yana shafa gashinta ya furta tun ranar Dana
fara ganinki gidan Mummy nasan Jamiluna nane,amma shine kaje kake son wata? Da kika
zo gidana kince min kece ? Sannan why zaki boye min kanki? Kin sanni na sanki a
zaman da muka yi ya dace ki min haka? Me yasa ko mene da kika San nine baza ki fada
min ba,baki yarda dani ba,kin san zuwana gidanku nawa? Kin san ta ya ma aka yarda
na aureki,dama na fada miki ni ta dole ma sai na aureki idan nayi niyya sai idan
Allah baiyi ba,karki sake min irin wannan shirmen naku na mata da yarinta da
gajeren tunani,kinzo kina wani boye min fuska Kuma sai baza min duwawu kike a gida
badan Allah yasa ni ya Sheikh bane da tuni me kike tunani? Ina sonki kin sani zan
iya hakuri Dake ne? da na sani ma da kika zo tuni nayi sex dake Kinga gobe sai ki
sake zuwa gidana,kuka Naila ta saki tace wlh sai na tafi gidanmu,dama ai gobe zamu
tafi,bukatar maje Hajji Sallah yarinya tunda na aureki saura Wahida,idan na zauna
Allah ya tsine min bazan zauna da kai ba,ta karfi ya riketa yanda baza ta iya
kwacewa ba,rigarta ya cire mata gaba daya,ta gaji da kokawar ta hakura kawai.

Samanta ya koma tana kasa,hannayensa biyu yasa a hankali cikin salon da zai
hanata sukuni ya fara kissing wuyanta Yana shakar kamshin Naila me Sanyi,mukus kake
ji Naila ta kasa kukan da take ta daina,idonta ta lumshe,Naila a ranta tace karka
daina Kaci gaba,a hankali ya gangaro fuskarsa Yana kare mata kallo gashi ya kunna
light,cikin salo ya hade bakinsu waje daya,Naila tana zukewa amma ta gaza hakuri
tace haba Tantiriya kibi yarima Kisha kida kawai ke da kike ma Tantiriya shi da bai
amsa sunan bama ya fiki kwarewa,Naila ta fara Maida Masa martani kamar ta Saba,sai
sake makalkale Spark take,muryarsa na rawa yace da dadi? Naila tace babu dadi
Sam,baka da dadi ,murmushi ya saki,tace auren miji Dan duniya ai ai sai addua ci
gaba ya zanyi,dariya yayi kawai ya matsa gefe yana cewa a'a a barshi,tace to haka
nake so,wlh baki isa ba ya dawo tare da dorawa daga Inda ya tsaya,gangarowa yayi a
hankali har zuwa kirjinta,ganin manyan Boobs dinta jajir ya sake rudewa,a nutse
yake binta duk kuwa da rudewar da yayi,Naila tace duniya sabuwa a ranta.
Ganin zai wuce gona da iri Naila ta kwaci kanta da kyar,gaskiya ni na gaji ba
Wahida kake so ba, Spark yace akwai lokaci yarinya,baccin karya tayi,shi hakan ma
ya wadar da shi indai zasu kwana bed daya,a haka bacci ya kwashe Naila, shima daga
baya rungumeta yayi a jikinsa sai bacci.

Washe gari ya rigata tashi,Beb...Beb ya shiga tashi a hankali ta bude idonta


suna hada Ido yace tashi kiyi sallah zanje masallaci cikin Mayen bacci ta bude
bargon ta fito ta manta ba kaya a jikinta ga haske,Spark ne ya kalleta wani farin
ciki ya kamashi lallai shikam yayi dace wannan kirji a cike haka,ba zato taji kiss
a goshinta tare da furta I love you,Naila tace uhm ka ga dai nonuwa ai dole kace,
matsa ta tureshi daga jikinta tare da rufe jikinta da bargo,dariya yayi tare da
ficewa sanye cikin jallabiya,Sai da ya tafi Naila ta mike a haka daga ita sai pant
a haka ta shiga toilet da addua tace Kuma duk Dan iskan Aljanin da ya kalleni ban
yafe ba,tana wanka tana tunanin wai da gaske auren aka mata,irin son kudin Umma ta
tuna tace nasan Umma da son kudi wlh tsab zata Yarda,Shi dama Abba nasan ba abinda
zai ce

Tana fitowa bayan tayi brush da alwala Sallah tayi sannan da asubar ta dinga
zabgawa Chikar gayu waya,Chikar gayu da kyar ta daga cikin bacci,lfy Naila? Dalla
ki tashi Ina can Ina ta soyayya Baku sani ba,Chikar gayu tace Abi dai a hankali kar
ya cuceki,Naila tace kina Ina wai? Ina gidan Mummy taki,ta zama kawata na tare
acan,na je mata a matar me kudi makwafciya,Naila tace me gaskiya wannan Mummy din
tasono ce wlh Kuma ta yarda? Sosai ma ai dakikiya ce ke na yarda kanta da motsi
tsab zata iya kashe mijinta bata ganewa,karar tafiya Naila taji tace sai anjima zan
kiraki ya zanyi tun jiya yake latseni,Chikar gayu tace zai cuceki,Bata San Naila
aure ne da ita ba,Naila bata fada ba tace na zama yar duniya ni yanzu na muku nisa
ba abinda ban sani ba,jiya ba irin gaisuwar da bamuyi ba ni da Hallare,mun gaisa
mun Kuma gaisawa nace Hallare ban sanki ba tace kwana Nan zaki sanni nima zan
sanki,Chikar gayu watsakewa tayi tana dariya tace,Naila ki kiyayi Hallare Kinga
hmmm,Naila tace,Naila volume ta rage na Muryarta tace jiya tana gefena abata Yar
sumulmul,Chikar gayu tace ke kika Santa ni ba ruwana Ina Nan gidan Mummy sabo da
tsabar tabara fanta ma da Madara nake hata na Sha banza ta Fadi,Naila tace to ya
zata tona asirin kanta? Chikar gayu tace saura kadan zaki Sha labari,Chikar gayu
tace karki sake yaci lallai ya so Wahida ya daga miki hankali wlh ki rama,Naila
tace bazan iya ba zuciyata ta mutu yanzu tun daren jiya ba batun ramuwa bani da
sa'a a kan Spark gaskiya,ke ni na gaji da walagigi soyayya ta gama kassara min
rayuwa,gwara kullum Ina gefen Hallareta
Spark ne ya nufo bedroom tana Jin tafiyarsa ta kashe wayar ta fada Saman bed
tayi baccin karya.

Mohsin yau ma an Sha sabuwar shadda ana wajen Beauty zance Beauty ta kira
Mohsin 2+2,Mohsin yace mene 2+2? Naila tace sai nazo gidanka zan nuna Maka 2+2,a
ranta tace boobs 4 rigis amsar kenan ,a fili Kuma tace sai nazo yace Allah ya
kaimu.
Yaushe zaki je wajen Umma? tace jibi inshaallah zanje nayi barka yace to Allah
ya kaimu suna ta hira,bayan kwana uku da Kai kudin auren Beauty,yau ta shirya zata
je gaida Umma tayi mata barka,Umma anji Yar me kudi da sauri ta tasa keyar Hashimu
Dolo tace muna da bakuwa yau mu shiga kitchen,yace yau Me za ayi mata ne? kin san
wannan ba irin Yar gidan Dankoli bace Hanan marar kunya marar mutunci,Umma tace ai
dole wannan sai da nama babbar bakuwa,Abba yace ya ilahi bamuga ta zama ba ya figo
bowl ya fara gyara kayan Miya,Umma Kuma tana girkin ko kunyar yaransu basa yi domin
su yaran ma idan da sabo sun saba,tare da Abba suka gama girkin Nan tas,ba uwar da
Abba bai iya ba na aikin gida,shine yayiwa Jaririya wanka ya sa mata pampers da
kaya ya shiryata tsaf harda wani sa mata hula ta yara me adon ribbon a jiki,Umma
wanka tayi ya Bata Basma shima yaje yayi wanka ya canja yadinsa fari me kyau harda
sa hula suruka zata zo,su Hidaya suna dawowa Abba yace ayi Maza ayi wanka a shirya
yau big Aunty zata zo,suna Murna dukkansu suka yi wanka kowa yaci kwalliya da kaya
me kyau suka sake gyara gidan Yana ta kamshin turaren wuta.

5pm sai kuwa Beauty tayi parking da motarta wata fara ciki Kuma komai pink,ta
Sha farar shadda me tsada wani kamshi kawai take yi,harda Dora mayafi a kanta ta
rufe Rabin fuska wai kunya,ta shugo tayi sallama,Zarah tace ga Aunty tazo,Beauty
ana murmushi ana kasa kasa da Kai ta rike hannun Zarah suka shiga cikin palon tare.

Tayi sallama Abba harda yiwa Umma rada kinji kamshi Yar Inna,Umma ta fuske tana
cewa sannu da zuwa, Beauty irin ta kirki me hankali ta zube a kasa tare da gaida su
Umma suna amsawa,Su Hidaya suka gaisheta sannan Umma tace zauna mana a kujera sannu
da zuwa.

Beauty ta zauna tare da sanda Kai kasa magana ma kadan kadan takeyi,Hidaya tana
ta janta da Hira amma wai kunya ta hanata sakewa,Abba ficewa yayi gudun kar ya Fadi
wata magana suruka ta ganshi wani Dolo,ya fito da sauri yace bari na gudu daga
gidan kar bakina ya jawo min Suruka ma tasan na cancanci sunana Hashimu Dolo,yace
Hashimu yi ta kanka bar layin gaba daya,ai kuwa Abba sai ya bar ma layin gaba daya
ya fece.
Sai gab da magriba Beauty ta mikawa Umma kayan jaririya masu tsada harda atamfa
da Leshi masu tsada tace Umma zan tafi,Umma tace abincin ma kadan kika ci fa,Beauty
tace Umma naci fa da yawa tana murmushi ta fito Hidaya da Zarah suka rakota har
Aslam,ta basu dubu biyar tace gashi ku siya sweet,sai godiya suke suka amshe,Beauty
tana tafiya Abba ya bugo waya yace ta tafi? Umma tace ae sai gashi ya dawo
gidan,Umma tace yanzu nasan nayi suruka,Yanzu nasan Dana zaiyi aure,Abba yace gata
da kunya,Umma tace ai kunyar tayi yawa a nutse take.

Hanan ce ta shugo gidan hankalinta a tashe ko sallama babu tazo ta zauna tace
Umma Ina yini,ko amsawa Bata bari anyi ba,tace zuwa nayi naji waye yace bana kula
da mijina? ance magana daga Nan gidan ta fito?,Umma tace wato kureni kika zo kiyi
kenan to an fada ko kina kula da shi ne,tsakani da Allah ni an sa min Ido an hanani
sakewa a gidan mijina idan Banda mugayen mafarki ba abinda nake yi idan wani Abu
ake min a gaskiya a daina domin idan aka cutar Dani baza mu yarda ba domin nima
yace a wajen iyayena,Umma tace keee....Kutmar ...burar....Umma ta dinga zurawa
Hanan ashar sannan tace bafa tsoronki akeyi ba,abinda yasa kika ga bansa ya sakeki
ba Gani nayi ya macece ke kamar yanda nake mace,sannan baza ka raba yarinya da
gidan Ubanta ba kazo ka saketa ba, baka yiwa iyayenta adalci ba tunda sun sauka sun
baka yarsu,wannan dalilin yasa ban sa Mohsin ya sakeki ba,ke wlh a yau idan naga
dama sai ya miki saki uku gwara ki rufawa kanki asiri,Abba yace aure ma zai Kara
kowa ya huta,Kururuwa Hanan ta saki tace ai ke ba haka mijinki yake miki ba, ta
juya ta bar gidan tana kuka tana tozartasu a layin ita uwar miji ta hanata sukuni
da asiri.

Chikar gayu farko shiri tayi abinta ta sa kaya na mutunci masu kyau ta yafa
mayafi a kanta irin Yar matashiyar matar aure mayafin kato,gidan Mummy taje tayi
sallama a nutse,Mummy tana Palo ita Kadai tana kallo tana ci n popcorn,tunda Chikar
gayu ta shiga Mummy take kallon karfarta da suturar Dake Jikin Chikar gayu, tana
Gani a ranta tace ba laifi da Yar tsadarsu,tace shugo mana zauna,Chikar gayu ta
zauna tare da Furta Aunty Ina yini,Mummy ta amsa da fara'a tace dama makwafciya ce
ni Amarya ban Dade da zuwa layin ba nace bari na shugo mu dinga zumunci,Umma tasan
layinsu gidajen masu kudine tace wow ai kuwa kin kyauta na gode,ta sa me aiki ta
kawowa Chikar gayu kayan motsa baki Sannan tace wai Yan mata yanzu Ashe kin shugo
cikin shahada kema,Chikar gayu tace me fa? Aure mana ai aure babu dadi a cikinsa
mazan Nan basu da mutunci,Chikar gayu tace wlh Aunty kamar kin shiga raina ta matso
hawayen karya tace tun Ina Amarya kwata kwata watana biyar da aure amma wai akan
naki samun ciki shike Nan wai har zaiyi min kishiya,Mummy tace Laaaaaaaa ke tun da
wuri gaskiya Baki karki ba ni Ina ganin sai da na kwashe Shekara talatin da aure
mijina sannan yace zai min kishiya ai kuwa wlh nace ban yarda ba,ke yanzu mata
kwayar yancin su suke,Chikar gayu tace ai kuwa nima nace wlh bazan yarda ba ko ni
ko shi,daga aure akan kawai ban samu ciki ba,Mummy tace Dan banza watakil ma
mataccen Sperm ne dashi yake tiltila miki a jiki,karki sake zai shafa miki ciwon
mara,mata sun waye yanzu,kina ji ya matsa miki wlh kiba shege wuta ki bar Masa
gida,Chikar gayu tace idan na tafi Ina zanje? ko Nan gidan kizo ai ni Ina so inga
mace tana gasawa Maza Aya a hannu,Chikar gayu tace ai kuwa zai ga yanda ake tsiya.

Naila baccin karya tayi har yazo ya kwanta yace in zaki tashi ki tashi ni motsi
kika yi nasan me yake nufi,Naila tayi mukus yace wa yace kisa riga tunda kika ji na
dawo ai sai ki cire ko madam,wai dama Kai haka kake? Baza ki San haka nake ba sai
munje wajen Umma da Yaya Mohsin wlh,nifa gaba daya haushinki nake ji,ni zaki
canjawa kamanni,Kinsa zuciyata radadi,kin fito gidan yari amma ko ki nemeni sai ma
harkarki da kika shiga,kin san halin Dana shiga? to yanzu ai ka samu Wahida ba
shike nan ba,Kwafa yaja yace nine ma bani da zuciya Dana ke kulaki,to ya zaka yi
Dani tunda kana kwadayina,ni kaga naje wajen hallarenka ko na taba ta,dariya Spark
yayi yace wai Hallare.
9pm zamu tafi Kano a can zamu yini a can zan barki sai Nan da 2weeks za a dawo
min Dake inji Umma,Yana magana Yana shafa albarkatun kirjinta,Naila ko magana daga
an taba ta shike nan ta daina magana Kuma ta Lula wata duniyar.

A dinga sharhi aga posting

Masu Sharhi na gode

AsmaBaffa
[12/17/2023, 8:11 PM] AsmaBaffa: https://wa.link/49vn47

PAID GROUP ONLY

Accnt no
0175487861

Katin MTN
08061929616

Yan Niger
+22790795939

🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

BOOK 1

61-65

Official
By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM

Page naku ne

Meta force Business


Amina Maman Ibrahim
Shehuhassana
Hajjora Investment
Hajjafatty
Hasiya Muhammad

Hey lovelies

Ke matar aure ce kuma kina neman business din dazakiyi daga gida da kuma baya
bukatan jari?

Kai dan makaranta ne kuma kana neman inda zaka ringa samun kudin kashewa?

Ko a'a ke kinada business dinki Amma kina neman wani side hustle haka da zai Kara
Miki extra source of income?

Ko kinada business idea da kikeson kifara Amma Babu jarin farawa?

Toh duk ku tarkato wannan training din, dan ga solution nan nasamo muku, kawai ki
danna wannan link din Dan Samun damar shiga group din

https://wa.link/49vn47

Bacci su Naila suka koma,lokacin Chikar gayu taje da safe ta shugo palon
Mummy tace Aunty yau baza ki fita bane? Mummy Dake kitchen ta fito tace gaskiya ba
Inda zanje,Chikar gayu tace key din gidana zan Baki ajiya zan fita wurin aiki idan
na dawo na biyo na karba ta mikawa Mummy key ta Sha Abaya ta zuba kyau,Mummy ta
karba tana tambayarta ya tsohon guntun mijin naki? Chikar gayu tace wannan ai in
kina mutumin banza jarabar duniya to shi ai Alhaji Basiru mugun Dan duniya ne,Mummy
tace au me kudi ne? Chikar gayu tace jahilin me kudi ne Yana da mata amma ita a
kasar waje take rayuwa uwar gidansa, nice nake zaune a Nan Abuja,Mummy a ranta tace
anya bazan aure mijin yarinyar nan ba kuwa,gashi tace matarsa har a kasar waje take
rayuwa Kai bari na kokarta na raba yarinyar nan da gidan mijinta na huta ni na
shige ciki,na gaji namiji nake bukata,Mummy tace yaushe zanzo gidan naki Ina so na
kawo miki ziyara,Chikar gayu tace gobe ma Ina Nan kizo inshaallah tayiwa Mummy
kwatancen gidan Daddy din Beauty Inda take zaune,Mummy tace ai muna da Nisa ma ke
ai layinmu daban? Chikar gayu tace abinka da bakuwa ai na zaci duka street Daya
ne,Mummy tace a'a ba daya bane Dan kawai ke bakuwa ce a Abuja,na gode da kika wayar
min da Kai sai dai kinzo Allah ne ya hadamu shi yasa nazo Nan Ashe da rabon zaki
bani kyawawan shawara,Idan kina tare Dani bake ba takaicin da namiji,Chikar gayu
tace naga alama tana dariya ta mikawa Mummy hannu tace halina Dake kin San kan
tsiya suka tafa kamar sa'arta,sai bayan sun tafa Mummy tace kaga yarinya kamar
sa'ata.
Chika tace Ashe kuma sai naji danki yayi aure,Kun Sha biki Kuma lokacin bamu
hadu ba wlh ban sani ba sai jiya naji ana cewa angon ma Ashe wacce ya aura daban
naji ana ta labarin a gidan suna,Mummy tace Kai mutane da gulma suke yanzu wannan
labarin har gidan Naming ceremony? Chika tace sosai ai kunyi fice a duniya sabo da
Kuna da arziki,Mummy tace wlh fa ai arziki yayi,Chika ta sake cewa angon aka ce
baya ma gari ya koma kasar waje,Mummy kiri kiri taki yarda ayi gulmar Danta Spark
sabo da tana sonsa ita barta dai suyi shi da ita da Yan uwa amma bare bazai taba
Jin kansu ba iya nacinsa,Chikar gayu ta dinga soko zancen Spark Mummy taki yarda
ayi zancen sai ta waske,Sai da Chika tace naji ma ance Ashe ku ya rufe sabo da
karku dame shi Yana gidansa shi da matarsa yau naji a wajen kawar matar tace ai
sunje yayi fata fata da amarya sai da aka mata dinki sunje dubiya, Mummy tace to
Ina ruwansu mene na zuwa dubiyar in banda sa Ido shi yasa kawaye suke da matsala
Spark yaushe zai iya wani fatattaka mace mutumin da Bai taba yi ba yaushe ma yasan
mace,da ace kaninsa kika ce Misam wlh zan yarda domin shine me neman mata,
Chikar gayu kamar an watsa mata ruwan zafi haka taji tace a ranta dama Dan iska
ne kenan,tace ah nima ai ba wata ta gari bace sabo da haka Ina son kayana haka ni
zan saita Masa Hallarensa wato checking balance tunda Bata da saiti kowa ma bi yake
chab,Kasa hakura tayi tace na tafi Aunty ta fice..

Tana komawa gida Daya daga cikin me gadi Ana ce Masa Basiru Yana da kiba gashi
Dan babba haka suna shiri da Chikar gayu sabo da Tantiri ne shima akwai iya
shege,samunsa tayi tace zanyi bakuwa gobe kayi shiga me kyau a matsayin mijina
Kaine me gidan Nan,Basiru yace wato dai film zamuyi motocin nan duk nawa ne da
gidan? Chikar gayu tace ashe ka gane ta karanta Masa duk abinda zaiyi,Basiru yace
gaskiya ke me kaunata ce, ya sake cewa na gode ai ko da wasa aka ce kayi acting a
matsayin me gidan Nan to Wanda ya saka aikin Yana cikin me kaunarka,ace wannan
motoci da gidan Nan duk nawane a Kuma wasan kwaikwayo ai na gode Kuma na fito a
mijinki Haba Chika dadin ya min yawa tsakanina Dake sai addua,da ace cewa kika yi
na fito a talaka to wlh da bani ba ke nasan bakya kaunata ko da wasa akace ka fito
a talaka ai an cuceka,Chika tace Kai kuwa Basiru kamar an baka gidan kyauta irin
wannan murna wasan kwaikwayo fa zamuyi Kuma biyanka zanyi,da sauri yace bama sai
kin biya ba ni hakan ma na gode ai arziki ne ace ka fito a me kudi.

Dariya Chika tayi Dan Bata San manufar Basiru, ba shi tunanin Basiru ai har daki
zasu shiga su kwanta tare duk a matsayin film sabo da Basiru shima Yana Bariki Yana
bin mata irin garori masu Araha.
Chika ficewa tayi tana tunanin Ina zata San gidan su Misam ne taje da kanta Nan
ma ta buwaye shi,tace ai kuwa bari naje gaisar da Mima na bata hakuri duk da ni
bana Bada hakuri bari naje kafin na tafi bikin Beauty,amma zan samo address a wajen
waccen kwandon Mummy.

Mummy kuwa Chikar gayu tana fita ta kira Mima a waya tace Sister wai kinji Spark
Yana gari da amaryarsa suna cin duniya da tsinke,Mima tana ji tace amma yaron nan
ba a taba Dan rainin hankali ba irinsa, wlh fito mu tafi gidan yau zai ga ikon uwa
mahaifiya, Mummy tace muje da Wahida da Baban Wahida yafi ganin Bada wasa muka je
ba,a waya suka kira Wahida wacce take ta kuka tunda Spark yayi aure,Daddy sai zage
zage yake Yana cewa Asmau ta mutu ta sanadinsa yanzu zai kashe min dayar data rage
da bakin halinsa wannan yaro ba karamin Dan iska bane mayaudari,a nutse Mima ta
kira shi tace yazo suje can zata sa shi dole ya auri Wahida,Daddy yace sai kace
mace zan biye muku mu tafi sai kace wani sakarai da girmana da komai wannan aikin
ai sai ku,Wahida ta rushe da kuka tana rokon Daddy Dan Allah Dan Annabi Daddy muje
dan Allah,ba yanda zaiyi sabo da yarsa shi dama akwai biyewa abinda yaransa suke so
yace muje to ya zanyi akan farin cikinku zan iya zubar da mutuncina muje.

Shiryawa tayi ta fito shima ya fito cikin wani dinkin Leshi na Maza fari kamar
wani bayarabe,suka tafi lokacin ma Mima da Mummy suka yi parking a gidan Spark,su
Wahida ma da babanta haka yace wannan yaron ai sai an Masa Taron dangi shi kadai
iskancinsa yayi na mutum goma,Palo suka shiga ko Ina shuru kamar ba kowa,Mummy da
Mima ne kadai suka haura sama har bedroom din Spark Mima ta bankada kofar ba
tunanin komai ba hankali ba nazari,Mima tace kinyi ganganci sis in kika ganewa
idonki fa,Spark da Naila suna bacci makale da juna kan Naila Yana Saman kirjin
Spark suka ji an banko kofa da karfi sabo da suna bacci ma tsoro suka ji Naila ta
cikin bargon ta fada bayan Spark ta makale, daga kansu zuwa kafada a bude amma
jikinsu a rufe cikin bargo.

Mummy tace Innalillahi wayyo me nake gani haka kamar Nasiba Yankan kauna,Ashe
haka zaki min ashe a Nan zaki aiwatar da yankan kaunar taki,wait wlh wannan kamar
Jamilun da aka Kai prison duk da cewar sau Daya na ganshi a Police station cewar
Mima,Mummy tace sai dai suna kama amma original Jamilu Yana prison karki manta shi
namiji ne harda askinsa,Naila ce tace Beb ka gama yau round uku kayi kawai tun jiya
nake wankan janaba,babin Jima'i da muka gama jiya yayi dadi na haddace karatuna sai
dai biyawa kawai yanzu babin gusuli kake ta koya min jiya ,wal gusuli da wanka
Minajjanabati na daga janaba ai wannan babi yayi tunda muka gamako ta juyo ta Kalli
su Mummy ma Bata yi ba,Suka ki tafiya sun tsaya suna kallo,Mima tace amma ban taba
ganin Yar iska irinki ba to idan baki sani ba ni uwarsa ce mahaifiya,Naila kamar
Bata ji ba tace nidai Allah aci gaba ni kar ayi a cikin bargo muyi kana kallona
Ina kallonka please fito,ta fara kokarin cire bargon tace zo muyi tsotsiya,Mummy
suka tsaya sororo suna kallo,Naila taga sunki tafi ya sabo da dabbacin wasu iyayen,
tace to ya kaji nonon akwai milk, Mima ce ta fara fita daga dakin ganin Spark shi
kawai Naila yake kallo kamar Wanda aka asirce ya wani zama Dolo sai kallonta
yake,Mummy ma fita tayi ta dawo Palo suka zauna suka yi shuru ba wacce ta sake
magana,suna fita Spark yace Naila da Mima a ciki,Naila tace ai na sani ni wlh
bazan yarda da wannan ba Dan kawai na aureka a dinga shugo min daki haka ya kamata
ne,ni ban taba Raina wani ba ka sani sai dai idan mutum ya shugo gonata idan ya
shiga kuwa kasan bani da kunya badan da Mima bama wlh sai na bude bargon ta ganmu a
haka tunda haka suke so,Dan kawai uwa uwa ce wlh shi yasa na tsaya iya haka amma ni
ka sanni indai Tantiranci ne babu me fada min shi,ka fada musu gaskiya wannan ba
tsari a addini da alada ai Bai dace ba kawai Dan kana dansu shike nan Kuma Dan Kuna
da kudi sai kowa ace za a takashi,baza a hanani sakata na Wala ba a gidan
mijina,yawwa ka fada musu domin idan ta kama timbir zan na yawo sabo da an daura
aure boyo ya kare,idan Kuma suka ki ji ni kasanni ban San kunya ba,Dan ma a haka na
shiryu ne amma da tuni sunga hallarenka tunda basu gaji da Gani ba bayan duk
rainonka da suka yi sabo da Allah ka fada musu ni dai na fada Maka bazan yarda a
Dinka kallar min jiki ba,Spark tana magana shi Kuma bama yajin me take cewa ya
zauce gaba daya,bakinsa taji cikin nata,wuyansa ta shake kadan da wasa da hannu
daya wai ita gwana style take na kiss dariya suka yi a tare suna Maida numfashi
hancinsa Yana Saman nata sun hade fuska waje daya,Naila tace karo da karo sai rago
style kenan,Dariya yayi ba shiri ya janye fuskarsa yace yunwa nake ji,kaje wajensu
Kafin na shirya kar su jiraka,Iyayenka ne duk tsiya dole a girmamasu wallahi to ya
zanyi tun kana jariri suke faman wanke min Hallare idan kayi fitsari,gashi har ta
kawo yanzu ta shahara ta gawurta da taimakon su,yanzun ma da kaga nayi Yar fitsara
kawai yi nayi Dan kar su Kara maimaitawa wannan ai zubar da girma ne a matsayinsu
na iyaye ba tsari dole yaransu ma su daina Jin maganarsu haba, tashi yayi ya saka
kaya sannan ya fita zuwa Palo.

Yana fitowa Mima tace to tabbatace fitsararre marar mutunci,Wahida da


Daddunynta Spark ya kalla,Mummy tace ka kyauta Spark yanzu irin son da Wahida take
Maka amma ka yaudareta ka yaudare mu ka yaudari Ubanta mahaifi kaje ka auri wannan
Yar iskar Yar film me kama da Jamilu me maganin,ai tunda tayi kama da Jamilu to ba
Yar arziki bace,Mima tace kyale shi wallahi sai ka auri Wahida ko ka saki waccen
karuwar saki uku ka zabi Daya ko ka Kara aure ka auri Wahida ko ka saki karuwar
matar da ka aura, Spark hankali kwance yace Mima abinda nake so Dake ki daina
rantsuwa kar azumin kaffara ya kamaki kin San ba Wanda zanyi daga ciki,bazan saki
matata ba Kuma bazan auri Wahida ba,nifa ku daina cewa na yaudareta dama ni Allah
ya Gani wasa nayi mata ita da Daddy,wasa nayi sabo da nishadina,Kuma ma tsuntsu
biyu na jefa da dutse Daya,na farko dama munyi fada da Masoyiyata Ina so na Dan
horata ta dawo daidai,sannan na biyu Kuma dama ni Ina Jin Haushin Wahida sabo da
suna zuwa gidana ita da Daddynta ta yiwa budurwata kallon banza,ta hararar min
budurwa tun lokacin tana budurwata sabo da yanzu matata ce,Ina kallonta ta Harare
min matar da zan aura tazo ta ganta a nan,Beb Dina ma Bata Santa ba itama Bata
Santa ba to kawai sabo da ganin araharta sai a harareta haka kawai shi yasa nace
sai na rama mata,gashi Nan Kuma na rama mata,itama ta min laifi na Hora abata cikin
ruwan Sanyi ai shi yasa ma kuka ganni Ina Shan love.

Magana ta karshe ku daina zuwa Kuna shigar min daki Kai tsaye yanzu ba Gwauro
bane ni da iyalina kar kuzo kuga abinda ido bazai dauka ba,sannan ni kaina tsawa
bana iya yi mata tsoron abata nake ji matata tafi karfi na sallamamme ne ni,duk
abinda ta muku ba ruwana bazan iya daukan mataki a Kai ba sai abinda tace shi yasa
take juyani son ranta

Yanzu da kuka fado daki da Kun iske bamu gama bafa Ina tsakiyar harka ai Kunga
Kun jawa kanku,ashar Mima ta dura Masa tace Kai duk iskancin da kake ji da shi dai
dai nake da Kai Dan uwarka mu kake gayawa haka sabo da ana kyaleka,na fada Maka
auren Wahida ya zame Maka dole,in ba ma iskanci ba haka zaka ce wasa kake dama,
Spark yace ni gaskiya na fada na Gani wasa nake yi ni,Kuma ga Wahida ta fada idan
na taba zuwa zance gidansu, sannan ban taba fita da ita ko Ina ba itace take
zuwa,sau Daya ma na taba kiranta tazo zamu fita Kuma muna fita banyi Nisa ba nace
motar ta lalace dole ta shiga taxi ta koma gida,waya ma ita take kirana Kuma duk
sabo da Babyna nake yi Dan taji haushi Kuma mun shirya na aureta,babban Yaya ya
sani shine ya nemo min aure shi da Yan uwan Papa, Papa ma ya sani duk sunje daurin
aure da su aka daura.

Mima taji takaici tace to ni ba abinda ya dame mu wlh sai ka auri Wahida ko na
tsine Maka,Spark yace uhmmm ni dai wlh magana ta Allah bazan aure ta ba sai dai a
tsine min Kuma harda ke domin danki ne za ace ya watse ya lalace maybe ma na shiga
kidnapping na fara ta kanki,gwara ma ki sa min albarka kar nazo ko na koma bin mata
nazo wajen Mummy cikin dare Inda Bata da mijin Nan na afka mata Kunga tsinuwa tayi
aiki,Salati suka saki suna tafa hannu,Mummy tace Spark ni zaka afkawa harda hawaye
tana cewa wai dan daga raina dan cikina Dan yayata uwa daya uba daya zaice zai afka
min,Mima tace abin yaci tura lallai ka Kai karshe a iskanci,Spark yace idan aka
tsine min nace ai, Allah sai naje ta kanta Mummy zan fara in ta kamama na biyo ta
wajenki Mima,Mima tace na shiga uku bazan tsine Maka bama Allah ya kiyaye min,Spark
yace ato ana tsine min zan fara kidnapping duk Yan gidanmu sai na tsince su ko kudi
ko rai,Mummy tace harda ni? Kece ma ta biyu cewar Spark,ko na fada neman mata Dan
akuya zan koma kowa na samu ba kanwa babu Yaya.

Daddy Yana Jin haka yace da Wahida ke ki hakura wannan yaron bashi da mutunci
kina Jin iyayensa ma abinda yake fada musu ni na zare hannuna ya mike,Wahida kamar
mayya cewa take nidai Ina sonsa haka tabi Daddy tana rokonsa haka suka shiga mota
suka tafi gida.

Mima tace zaka San ni na haifeka Spark,Naila ce ta fito ta Sha wanka tazo gaban
su Mima ta durkusa tace Ina kwananku,Ruwan ashar kawai taji Mima tana ce mata
Karuwa kinwa Dana asiri ya haukace ba abinda baya fada mana wlh sai an sakeki zaki
ce na fada miki banza Yar talakawa Yar matsiyata,sai nasan waye ubanki,Naila banza
ta musu tace bari na kawo muku ruwa Dan Allah karku tafi ta mike ta shiga kitchen
ta kawo musu lemo da snacks ta ajiye a gabansu tare da tsiyaya musu ta mika musu.

Mummy ce ta karba ta watsawa Naila a jikinta tace kece bakuwar lemo ba a Saba
Sha a gida ba,ubanki ne ya siyo Karuwa Yar film,Mima ce tasa hannu zata Mari
Naila,Spark yayi Maza ya janye Naila,Naila murmushi tayi a ranta tace Inama ta
mareni wlh da yau baza tayi bacci ba,Naila ba abinda ya mata ciwo irin zagin da
suke mata suna zagin iyayenta,Spark yace kiyi hakuri kinji,tace ba komai rayuwa
ce,da uwarki ce cewar Mima,Kai Kuma kaga hasken fata ka makale sabo da kyau ai kyau
kabi kaji kunya duk kyan da Allah ya Maka,Kai kuwa Spark wlh baka da kirki
shashasha ne.
Naila ce tayi magana tace ba komai ai ko don darajar haifar min shi da kuka yi
gashi Kun Raine shi kuka dinga Masa tsarki Kuna wanke masa Hallare idan yayi
fitsari ko don wannan ai dole na girmamaku domin kuwa Kun wanke min Hallare sannan
lokacin da aka yi Masa kaciya taji Hallare taji ciwo amma kuka dinga bikinta Kuna
tsomata a ruwan zafi har da Zuba Dettol,har kaji kuka yanka Masa ta Yan
kaciya,Spark yace harda kosai aka dinga soya min,Allah? kaji ko duk Dan tayi
inganci har ta shahara ta kawo yanzu lafiya da ita, ko Dan wannan wlh iyayen miji
sunci a girmama su sosai,ko me zaku ce bazan ce komai ba tsakanina daku sai addua
cewar Naila, Spark bai ce komai ba har su Mima abin ya ishe su sai suka bar gidan.

Naila ta kalle shi tace me zaka ci? Kallonta yayi yaga ko damuwa bata nuna ba
yace kiyi hakuri,murmushi ta saki tace laaa ba komai ai iyayene daidai macen da
Bata fama da matsalar dangin Miji wlh amma sai dai na wata sunfi na wata amma duk
da haka wasu suna dace sai dai ba a rasa kananan maganganu nima Kuma a yanda ka
aureni ne babu yardar su ya jawo min,Baki San gidanmu ba ai idan suka sani ko suka
raina mutum to baza su yarda ba,musamman mummy itace ta raineni baza ta yarda ba
tafi son harka da masu kudi,Naila tace talaka bawan Allah dama da yawa wasu masu
kudin haka suke basa hada jininsu da talaka duk kyawun mace basu bari yaransu su
aureta indai basu da kudi,yace bari na shirya mu tafi Kano ki hada mana break sai
ki sake wanka sun bata miki jiki da lemo,Kitchen ta shiga shi Kuma ya haura sama.
Yau ma a YouTube ta Kalli girki ta hada musu yayi dadi kuwa suna karyawa ta
shiga wanka ta fito ta shirya cikin shadda pink wacce ya ganta da ita a jikinta
gidan Mummy farkon zuwanta Abuja,yace ke cire kisa Abaya doguwar rigar ta dame miki
duwawu za a kalleki,Naila taki yarda tace ai mayafin da girmansa,yace nifa ban
yarda,Naila ta fara fushi amma a lokacin ya duba online ya zabi Abaya me shegen
tsada,Naila tace ko ka siyo bazan sa ba kaje ka kaiwa Wahida.

Wai ke bakya manta Abu ne,Naila a ranta tace muje Kano din zaka ga iskanci kukan
da ka sani irin Kaci banza,a fili tace nifa ko ka siyo bazan saka ba,ni kike fadawa
haka? Naila tace ae,yace zan miki fata fata wlh naga kina kawo min raini sabo da
Kinga ba abinda na miki na kyaleki ko? Naila tace kayi mana Dan ragowar ciwon
Sanyina na gidan Yari ya kamaka gwara ma ka barni naje gida a Kara wanke ragowar,
Dariya Spark yayi yace ai dama idan mutum yayi aure ai ba ya rasa Sanyi tunda ku
mata kullum a cikinsa kuke,Naila tace kamar yanda kuke fama da Basir ba ku Maza
haka mata suke faman da Sanyi,ramawa kika yi kenan? Ae mana haka kawai kace wani
kullum a cikin Sanyi muke Kuma ai a Basir kuke,muje tunda baza ki Sa Abayar ba ana
so ki fito a matar me kudi Alhaji Ashraf Spark kina cewa ke a'a Yar kauye muje
haka, ya kira waya yace a ajiye Abayar zai karba gobe suka ce to.

Mayafin ta yafa da hand bag da kayanta na sawa duka gaba daya yace akwai
lefenki a can,Naila tace sai Nan gaba zan saka,yace muje ya daukar mata jakar tata
tare da rike mata hannu da daya hannun,Suna fitowa Driver ya bude musu gidan baya a
motar Naila ta Kalli Spark tace dole nayi yanga zaga ka bude min da kanka ni bazan
shiga budewar driver ba,Spark Yana murmushi ya zaga tare da bude mata ta shiga zai
rufe tace tsaya ka gyara min mayafina ka tabbatar bai fito ba,Spark Yana dariya ya
gyara mata tare da tambaya ranki ya Dade yayi?tace yi min kiss a goshi haka ake
soyayyar idan Wahida ce ai ka iya bude mata hakora.

Spark a ransa yace Allah sarki Bata San ma hararar da aka mata na rama mataba
duk da cewa tayi min laifi shi yasa itama na hukuntata,zagawa yayi ya shiga driver
ya kulle Masa kofar ya shiga suka ware Airport,Naila a motar ta kira Chikar ta fada
mata,chika tace nima Nan da lokaci kadan zan taho biki,bikin wa? Idan kinje Kano za
a fada miki,Naila ta kashe wayar ta kira Beauty tace Gani nan zuwa kano hmm tare
muke da Baby fa yau Kuma Naila sai cikin jirgi ku tayani murna Naila zata hau
jirgi,tace Chikar gayu ta fada min wai aure aka miki baki sani ba? Karyar Beauty ce
taji komai a wajen Mohsin na daurin auren Naila,Naila tace ae mana to abinka da
iyayen da suka Isa da yarsu ai na hakura zanyi biyayya,Beauty tace to ya tsinkar
fure Naila tayi kasa da Murya kamar me rada tace ai yafi karfin fure sai dai a
yayan ake tsinkewa sun nuna nunannu ne,Beauty tayi dariya tace nayi Shirin tarbar
babbar kanwata,Dan uwarki nice kanwar taki,Naila Bata San Beauty yayanta zata aura
ba har ta fara gyaran Amarya ma tana kashewa jiki kudi.

Naila kuwa har wani Shan kamshi take yiwa Spark sabo da zata tafi gida,tace
idan naje fa wasu suka ganni a gari aka Kai gulmata gidan yari suka dawo nema na?
Spark yace ba Wanda zaizo ai da nasan za a zo nemanki kema kin San bazan bari kije
ba,na riga na Bada kudi ko ankai gulmarki baza a maidaki ciki ba,ke ko kamaki aka
yi aka kaiki baza su maidaki ba,na riga na kashe case din,kin San fa Nigeria sai
idan baka da kudi.
Suna zuwa Airport Naila sai kallo akeyi Yana rike da hannunta suka shiga
jirgi,Naila sai murna akeyi a haka suka sauka a Kano,wani driver dinne yazo da
dalleliyar mota ya dauke su,har layin su Naila,Abba ta hango Yana siyar da kayan
moyarsa,Naila tace tsaya a nan na fara ganin Abbana,Spark yasa aka yi packing Naila
tace bude min kofa,ya fito ya bude mata ta fito ya rike mata handbag din suka
karasa wajen Abba a rumfa,Abba ya washe baki harda Waka yace ah,ah
a..yan..yan..yan..ya Naila ta,Dariya suka dinga yi ba kamar Spark da bai San
dolonci Abba ba, durkusawa Spark yayi tare da gaida Abba ya amsa yace Mijin
Nailata,Naila tazo zata rungume Abba amma Abba yaja baya yace Kubra ta isheni matsa
wannan ai raini ne uwarki nayi ke kina yi,Spark ya nuna yace kiwa naki kema gashi
nan,Spark ya boye dariyarsa shi dai,Naila tace Abba ana ta arahar kayan Miya? Abba
yace a'a na daina yanzu tsada nake ta yi cutar da mata suka dinga yi min nake
fanshewa duk sai na fanshe kudina, Batoola ta jawowa mata tunda ta gujeni yarinya
na gama koya mata salon girki yanzu nasan Usman dinta yaci kalarsa yafi sau
goma,tashi kuje ciki Kun zauna a waje,Naila ta mike zasu tafi cikin gidan Abba yace
Naila an Kara zama India,dariya suka yi suka tafi.

Mota suka shiga suka nufi gidan Allah yasa unguwar ba kowa yasan Naila ba sabo
da Bata Dade da zuwa daga kauye ba ta fada prison.
Gidansu suka nufa tare da tsayawa a kofar gidan sannan Spark ya daukar mata
kayan suka nufi cikin gidan,Khalil tsohon saurayin Naila ya kwala mata kira bai San
tayi aure ba baya gari,ya karasa kusa da Naila yace Naila duk irin son da nake miki
shine kika biyewa me mota sabo da yana da kudi.

Nan take Spark ya daure fuska ya fisgi hannun Naila suka yi ciki
suna yin sallama su Zarah suka dinga murna ga Aunty Umma ga Naila tazo,Hidaya kuwa
tana zaune tana gyara Salat ko wani murnar kirki babu, Naila tana ganinta tace Yar
bakin ciki an fara ne? Ki dinga addua kina da cutar hassada,Umma ce ta leko tace
bana son wulakanci ke daga zuwa ma,Dan me baza tayi murnar ganina ba sai ta zauna
tana aikinta,Idan zaki shugo ki shugo,Spark Yana gefe Yana ta kishi da bacin rai
namiji ya kula Masa mata, Umma tace shugo mana ai an zama daya ka zama Dan
gida,Spark ya shugo shima suka shiga Palo,Naila tace Umma harda canja kujeru
sababbi? Umma tace ai har waya na canja,Abba ne ya shugo gidan daga ji ana zancen
waya sai ya shugo palon yace Tecno ce me sunan mijinki Spark na biyar,Umma tace
Spark 5 ke Naila,Abba mikewa yayi yace bari a kawo ruwa.

Umma ganin suruki tace yanzu zan tashi,Abba yace Yar Inna bana son haka sai Kinga
suruki ki nuna ta Allah ce ke,ai hutawa kika Saba yar Inna, barshi ki huta ya fice
yaje ya siyo lemo da ruwan roba da kudin aljihunsa ya shugo,Hidaya tana kitchen ya
leka ya dakko plate Yana cewa na kashe kudi yau haka lemo ya tashi a kasar Nan? Wlh
Dan ba Kara bazan sake ba yau dinma karambani ne,ya zuba ya Kai har Palo,yace Kaine
Bako ka Sha, Spark bai fara Sha ba Abba yace kasha karka jawo min asarar kudina
abin duniya yayi tsada yanzu,Harara Umma ta zuba masa a boye yace. Bari na koma
bakin aiki na ya fice.

Naila tace Umma Ina Jaririyar? bacci take tana daki,Mohsin ne ya shugo palon
dauke da sallama,Naila harda ihu tace darling hannu ya mika mata suka tafa yace na
manta ma munyi fada,tace ai zamu shirya,gaisawa suka yi da Spark sannan suka fara
Hira,Umma taje ta karbi Hidaya ita Kuma taje ta gaida Spark ta zauna ana hirar da
ita,Naila tace Hidaya an fara kyau ga hanci Yana ta mikewa ashe zakiyi kyau,Hidaya
ta zumburi Baki ta mike ta fice ta shiga kitchen tace Umma kiyuwa Naila fada a
gaban bako sai disgani take,Ke Kuma ki dinga hakuri ke baki San wasa ba, Naila wasa
take miki ke bakya ganin yanda suke da Mohsin ne.

Spark kuwa Zarah ya dauka tare da dorata a cinyarsa Naila ta kalleshi ta Masa
inkiya da hannu tana hararsa wai ya sauketa,Murmushi ya saki ya mata banza,Mohsin
ne ya radawa Naila yace aure zanyi bikina ko sati biyu bai kai ba,Naila tace wayyo
dadi kasheni,yace sai Kinga ma amaryata zaki San nayi dace kin Santa fa,Naila tace
Allah? Yace kin San kuwa ya take? Naila tace ya kirjin nata yake tunda Kai a Nan
la'anarka take,Mohsin yayi dariya suna rada yace a tajamjam,Naila ta sheke da
dariya,tace na Maka murna ya bayan?yace wuhuhu ai tarago guda ne,Naila tace to dole
mu tashi a tsaye da gyaran Hallare,Mohsin yace ai tsumani zakiyi amma sai ta Saba
zan Sha maganin fa kar na wargaza mata Bado,Naila tace Kaka zaizo biki zan Masa
waya ya taho min da wasu nima har mijina zanwa saiti,Mohsin yace ke Naila har kin
San Abu,Naila tace uhm gobe dani za aje zance,ya zama dole mu tafi ki ganta da
kanki, Spark sai haushi yake ji Naila ta share shi tunda aka zo Kano take Masa
yanga,ganin kamar ransa ya baci sai ta dawo ta zauna kusa dashi,duk da haka shi dai
wai ta daina kula dashi sai complain yake mata.

Umma ce tazo suka yi ta Hira da shi sai bayan La'asar ya musu sallama bayan ya
bawa Umma kudi,ya fito Naila ta rako shi yace to Madam zan tafi duk Inda zaki je
sai kin fada min ko Nan da kofar gida ne,Naila tace to,yace sai me? tace ai ka sani
kaima kudin gyaran jiki Kuma zamu yi biki,yace zan sa miki a accnt,Pocket money fa?
Kudi ya zaro ya bata,tace na gode,saura wani ya miki magana ki tsaya kulashi, ya
shiga mota sannan ya sauke glass kasa yace I love you,tace Wahida fa? Harararta
yayi yace na gaji da zancen nan ya daga glass sama yace da driver suje Kawai suka
tafi,wani ne makwafcin su naila zaiwa Naila magana taji spark yace ki koma gida
fa,Ashe shi Yana ganin matashin yace driver ya tsaya,Naila gida ta koma kawai.

Tana komawa Umma sai murna take tace Alhmdllh kinyi miji Naila,Kwanciya Naila
tayi a Palo Umma tace fito girki da aikin gida ba shegen da zai miki,Sai kayan
gyaran jikinki na siyi wasu duk mun siya kadan za a karo sai Kuma na Skin Budurwar
Mohsin tace zaku dinga zuwa tare,Naila tace to ai dai a bari na huta.
Tun a jirgi Spark yake faman kiran Naila taki dagawa sai yanga take Masa,kiran
duniya sai ta Sa wayarta ma a silent,tace kaje ai ka kira Wahida sabo da ka raina
min wayo a gabana sabo da cin fuska wlh sai ka bani hakuri tukun ai ka maidani ba
mace ba ma.

A dinga sharhi pls nafi saurin typing

AsmaBaffa
[12/19/2023, 3:38 PM] AsmaBaffa: PAID GROUP ONLY

Accnt no
0175487861

Katin MTN
08061929616

Yan Niger
+22790795939

🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

BOOK 1

66-70
Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM

Page naku ne
Maryam Idris Kabir
Ummy Aysha
Lubabatu Mijinyawa
Mmn Nasree.
Momy FARUK
Oum Aariz
Aeesha
Rukayyarabiuadam123
Reina
Sadiya Muhammad
Hajjafatty

Hey lovelies

Ke matar aure ce kuma kina neman business din dazakiyi daga gida da kuma baya
bukatan jari?

Kai dan makaranta ne kuma kana neman inda zaka ringa samun kudin kashewa?

Ko a'a ke kinada business dinki Amma kina neman wani side hustle haka da zai Kara
Miki extra source of income?

Ko kinada business idea da kikeson kifara Amma Babu jarin farawa?

Toh duk ku tarkato wannan training din, dan ga solution nan nasamo muku, kawai ki
danna wannan link din Dan Samun damar shiga group din

https://wa.link/49vn47

Spark uzuri yayi mata


yasan taje gida Kuma maybe wayar tana jaka,Yana zuwa gida ya tura mata text
message cewar yaje gida lfy,Naila kamar bata gani ba,shuru shuru ba reply ya daure
har zuwa dare sannan ya sake kira sai da ya kira yafi sau biyar sannan Naila ta ga
a haka ji tayi tayi missing dinsa baza ta iya share shi ba.

Spark ko da ta daga baiyi complain ba,kawai ya mata uzuri ,Naila a ranta tace
wato ma baiji haushi ba bai damu ba,me kike yi? Bacci,amma naji ki fess? to bacci
nake ji ni ta furta ,hmm yaji kamar fushi take yi yace alright,Yana so suyi waya
yaji Muryarta gaba daya taki bada fuska shi ya rasa me yayi mata,kawai yace good
night ya datse wayarsa,ita kanta bata so ba.

Umma tana kusa da ita tace Ashe kuwa zaki koma gidan miji ba shiri wannan
iskancin ba a gidan nan ba,Yana miki magana kina wani share shi, sannu Naila karfa
ki manta Yar gidan Hashimu Dolo ce ba kowan kowa ba,a gidan nan baki isa ba wlh.

Spark kuwa Yana zaune ya tallafe fuskarsa Yana tunani,kwanciya yayi jiki ba karfi
yace Spark kwanta karka kashe kanka akan mace,Mace sai ta haukataka,duk yanda yaso
ya share amma ya kasa sai faman tunanin Naila yake,gidan gaba daya ba dadi bata
Nan.

Fitowa yayi sanye cikin Kayan baccinsa Silk olive color, a hankali ya nufi
kitchen ya dakko lemon gongoni ya zauna a Palo tare da kunna tv Yana kallon
American film a zahiri amma a ransa Naila yake tunanin gaba daya,zata susuta shi
gaba daya.

Naila ma tunanin Spark take yi a haka tayi bacci,sai asuba ta tashi bayan tayi
sallah tare da Azkhar ko bacci Bata koma ba ta fito ta shiga kitchen ta fara hada
musu break fast sabo da yara Yan makaranta,tana yi tana gyara gidan, kafin Yan
makaranta su gama shiri ta gama komai tana wanke wanke ma,Abba Yana dakinsa shi da
Umma ya mike ya leka ta window Yana ta kallon Naila tana aikinta,farin ciki ne ya
kama Abba,Umma ya kira yace Yar Inna taso Kiga yarki tayi hankali,Umma ta leka
itama tana washe baki tace shi yasa naji karar kwanika hannu ta daga sama tana cewa
Allah na gode Maka,Abba yace Alhmdllh ya mikawa Umma hannu suka tafa a hankali ba
tare da sauti ya fito ba, sabo da farin ciki da murna, Naila har masifa akewa yara
Dan iskanci ku shirya ku tafi makaranta sai Kun makara, ke zarah baza ki Sha shayi
ki tafi ba,Ke kuma Hidaya ki hadawa Aslam shayin mana sai Kun makara,Hidaya sanye
da Uniform ta hada musu shayin suka Sha tare da doya da kwai da Naila ta soya, Suka
karya sannan suka tafi makaranta,ta sake wanke kwanikan da suka Bata ta gyara wajen
da dakunansu duk ta gyara,Umma da Abba ma karyawa suka yi sannan Abba ya fice wajen
kayan miyarsa Yana mita Yana cewa ni wannan sana'ar ta isheni wlh kullum mutum sai
ya zauna a rumfa kayi ta zama a benchi, basir ma ya kamani,ni na gaji gwara a canja
min wata sana'ar.

Naila sai da ta gyara har dakin Abba sannan tayi wanka ta zauna ta karya ga
Spark Yana ta aikin kira bata daga ba sai da taji itama muryarsa take so ta ji
sannan ta kirashi back,yana dagawa again baiyi complain ba ko kadan uzuri ya sake
mata Naila Kuma so take lallai sai yaji haushi,Gashi bata iya Masa rashin
kunya,Yana Jin kalau take sai ya mata sallama abin Yana damun Spark sosai.

Haka ya shirya ya fita Office cikin wani yard me masifar tsada,Kai da ganinsa ba
sai an fada Maka ba Tan color,fuskar nan a hade ba fara'a yanda yake asalin Spark
kowa ya kulashi sai masifa,Aikin ma ya kasa tsaki ya ja ya shiga Mota zai
fita,manager yazo yace sir takardun nan zaka kawo,Spark yace karka dameni da wasu
takardu ya ja tsaki ya yace da driver muje, gidan Mummy yaje,ta ganshi ransa a bace
yau a spark dinsa yazo,tace kaga karka zo Inda nake bayan rashin mutuncin da kayi
mana a gidanka, Spark Ido ya lumshe yace Mummy Ina Kwana? Ban sani ba ta bashi
amsa.

Yace sorry Mummy daga nace zan afka miki shike nan sai ki dauki gaba dani ai
idan aka tsine min nake nufi,yanzu Spark sai ka iya afka min? Spark yace idan aka
tsine min ba mene bazan yi ba ai tsinuwa ce take aiki,yanzu sai ka aikata? Spark
yace me zai hana kuwa,Spark ko wani ka ganni dashi Ina harkar banza da shi ai sai
kayi min fada,yace Akan me? Kina Jin dadinki zan miki fada,ke da kika Raine ni Kuma
kawai sai na miki fada sabo da kina neman Maza ba ruwan Spark kiji dadinki ai ko
Mima ce ba abinda zance,iyakaci na dinga yawo da wandon karfe sabo da kar a biyo ta
kaina.

Allah ya shiryeka yace Ameen wai Mummy ku mata ya kuke ne? Sai a rasa gane
kanku sai kace masu Shan kwaya mata haka suke,Mummy tace an fara fada ne? dama
wannan marar kunyar ai tukunna nama sai ka saketa da hannunka,nifa ba laifin data
min kawai tambayarki nayi sabo da na San rirrin yanda zan zauna da abata
lafiya,Mummy tace lallai baka da kunya,ka gama yi mana rashin mutunci a kanta yanzu
kazo wai a fada Maka siririn mata, ta kasheka,share zancen yayi,tace ai baka Jin
kunya Kai ka gama zaginmu shine kazo yanzu kana wani tambayata sirrin mata ya muke.

Yau da yamma Mummy ta dauki wanka sosai ta shiga motarta tana Jin kida sosai
sai gidan Chikar gayu,tana zuwa ta hango gidan Malam wow tace Kai kai ya zama
wajibi na shugo gidan Nan a matsayin mata,Chikar gayu tayiwa waya ta fada mata a
bude gate,daya me gadin ne ya bude gate tayi parking sannan ta fito tana baza
kamshi, Basiru kuwa ya saka Yar shaddarsa ta sallah Yana zaune a Palo ya hakimce
Yana karkada kafa irin me kudin nan,Chika tace kayi fa aiki me kyau,yace za a ga
aiki ai ki kwantar da hankalinki,aiki sai ma mun shiga dakin bacci, Mummy ce ta
shugo Palo taga yaci kayan alatu sosai shugowa tayi ta zauna tare da furta wow ta
zauna,Basiru Yana karkada kafa Yana wata gadara da kyar yake magana,yace barka da
zuwa ya Kalli Chika yace my Watermelon Ashe yau bakuwa zakiyi Yana magana Yana
kallon Mummy,Mummy ma kallonsa tayi kawai Basiru ya kashe mata Ido daya tare da
daga mata gira,Mummy a ranta tace kaiii ya daga min girma murmushi ta saki,ya
kwalawa Sheyi kira kamar wajensa bakuwar tazo yace a kawowa babbar bakuwa kayan
motsa baki,Mikewa yayi harda zuwa ya rike hannun Chika Yana cewa Watermalone,Chika
a sace ta fisge hannunta tare da gasa Masa harara tana ce Masa Banda wannan.

Amma Ina Basiru a ransa yace tab ai wlh ba a isa ba na fito a miji Kuma ace bazan
taba komai ba an San hakane akace ayi film,Sama ya haura yace kizo Ina son ganinki
harda masifa irin me gidan Nan.

Ba yanda Chika ta iya ta bishi sama tace da Mummy Ina zuwa,suna zuwa Sama a
palon sama suka tsaya ya Bata rai yace wuce ciki,in wuce ciki in Maka uban me
sadaki ka biya? Film kika ce za ayi ai ana kwanciya a Saman bed,ai Hausa film muke
yi ba Nollywood ko American film ba cewar Chika,Basiru yace dama kin San ba
Nollywood zamu yi ba kika bata min lokaci to wlh Baki isa ba ni Nollywood film
zanyi sabo da haka wuce ciki muje.

Chika tace baka da hankali Basiru Hausa film muke yi na musulmai,Basiru yace ba
komai ai Hausa ma suna Waka da rawa a ciki sai munyi rawa da Waka tunda hakane Kuma
karki sa Bra kizo muyi girgiza,Chika tace ai ban taba sanin mahaukaci bane Kai sai
yau na fika iskanci wlh ta ja tsaki ta juyo wajen Mummy ta barshi tsaye,yace wlh
sai nayi Yaudara a film din sai na so kawar taki komai tsufanta.

Mummy ce tace wannan ne dama mijin naki? Chika tace ae,amma duk kudinsa yake
saka shadda me araha haka,to ai wasu masu kudi idan kudi yakai kudi ba sa saka kaya
masu tsada,Mummy tace wannan ma gara ne wlh karki sake ya dinga raina miki hankali
Yana zaginki ki rama ki zagi iyayensa,haka Mummy ta zauna tana faman zuga Chikar
gayu akan taci uban mijinta kar ta daga Masa kafa...

Chika harda hawayen karya tana fada mata yanda Basiru yake zaluntarta,Mummy tace
shi yasa fa wasu matan suke kashe mazajensu wlh ni bana ganin laifinsu ma,ba
ruwanka zaka huta ka shana kayi abinda kake so,Chika zama ta gyara tare da gyara
wayarta tace kice yanzu haka ake yi?Sosai ai mata sun daina zama yanzu,Ina ma zan
San Inda ake siyar da gubar Nan,Mummy tace zaki samu mana wata kawata tana siyarwa
a sirru,Naila tace idan na gaji zan kawo kudina,Mummy tunawa tayi karta jawowa
kanta sai tace ke naji yanzu bata siyarwa amma zan tambayar miki ko ta dawo tana
siyarwa.

Basiru Yana Jin zata tafi ya fice ya rigata zuwa Jikin motar,Chika Bata hanashi
ba,Mummy ya Gani tana Masa murmushi,yace bakuwar Alkhairi zaki tafi? Mummy tana
wani fari da Idanuwa tace ae sai na sake dawowa,wani zuwan ni zan kawota da
kaina,Mummy tace okay bari kaima na baka number ta ko gaisawa zamu dinga yi
watarana,Basiru jiki na rawa ya dakko kwakwurar wayarsa yace Af na manta babbar
wayata a bedroom,Kai ai wayarce babba sai ta dinga Maka nauyi a aljihu musamman
iphone nauyi ne da su,Mummy tayi murmushi tana karanta Masa number bayan ya shigar
tace ko Kai kadai ma zaka iya zuwa gidana ba kowa,yace kasurgumar bazawara ce ne
haka? Mummy tace wlh sakin Allah ce ba sakin mutum ba mijina mutuwa yayi kaga kuwa
ai sakin Allah ne,Basiru yace sorry sorry harda dafa Kafadar Mummy sorry Yana
girgizawa da hannu,Wayancewa tayi tace bari mana Alhaji Basiru kar matarka kanwata
ta Gani,yace ke rabu da ita hakuri nake dama da ita ba uwar da take min na
soyayya,Mummy ta furta wasu matan sai hakuri wlh basu iya kula da miji ba musamman
yaran Nan,Basiru yace habawa bari kedai Hajiya Ina Shan wahala a kasar Nan da
kudinka da komai mace ta zame Maka masifa ni sakinta ma zanyi,Mummy tace a'a ka dai
Kara hakuri ai gwara kayi mata kishiya tunda gidan kaga part part ne,Kin kawo
shawara na gode sai na kawota,Mummy ta shiga mota tana kissima irin kudin da zata
samu a hannun Alhaji Basiru.

Basiru ne ya dawo ciki yace Baby,Chika ta hade rai tace the End film ya kare,ko
kwanciya bamuyi ba zaki ce ya kare? Chika tace ya kare gashi Nan rubutu akeyi na
karshe dalla mallam kama gabanka bana son raini,tsayawa yayi zai sake magana Chika
ta jawo takalminta me tsini ba shiri ya fice.
Shirye shirye tayi itama na tafiya Kano,washe gari ta wajen Mummy ta biya ta
daki cikinta a haka ta samo address din Misam har Office dinsa tace bari na dawo
daga Kano nasan ta Inda zan bullo Masa.

Naila tunda taje Kano ake Bata magungunan gyara da kudinta Kuma tana siyan
wasu,Yau zasu je zance wajen budurwar Mohsin,Naila a waya ta kira Spark ya daga
Yana fushi sabo da Bata taba kiransa ba idan ya kira ma sai taga dama take dagawa
sannan idan ma ta daga baza tayi maganar kirki ba, daga gaisuwa shike nan,abin Yana
yiwa Spark ciwo matuka,sai da kiran ya katse sannan ya kirata back ta dauka,tace
Ina yini? Lfy Alhmdllh,dama unguwa zanje nace....sai kin dawo kawai ya kashe
wayarsa,hankalinta ne ya tashi amma ta danne ta shirya ta zabo atamfa cikin kayan
lefenta wata Indigo ta saka riga da skert kamar an aunata,tace wai Lefen Umma har
akwati Sha shida aka kawo? Umma tace gashi kin Gani ai sun kashe kudi,tace to ki
kwashi wasu mana a bawa su Hidaya da Zarah suma su Dinka,cikin shaddojin Kuma Abba
ya dauka,Yaya Mohsin da Aslam,Umma tace wa yace miki haka akeyi? Ai Dan kiyi Masa
kwalliya ya zuba miki,to ai dai ana kyauta ki zaba Hidaya da Zarah su zaba a bawa
my love Mohsin da Abba ki duba sunyi yawa fa,shike nan zan fada musu an gode.

Mohsin ne yazo yace fito mu tafi mana,Naila ta fito da Jakarta da mayafi duk
sababbi,Umma tace ki gyara mayafin Nan sosai bana son wannan iskancin na yaran
zamani mace me aure ba a banbanceta da budurwa bai dace ba, wasu mazan suna tare su
a hanya idan mace tayi shigar Kamala ba me tareta yace Yana so,amma yanzu mayafin
da wasu matan auren ke yafawa ko budurwa sai taji kunyar fita da shi, Naila an zama
matan aure cewar Hidaya tana kallonta,tace ai kuwa Hidaya baki ga sai Shining nake
ba? Hidaya tace na gani ai,Naila tace to Hallare ce ta jawo shi yasa kika ganni
haka,Hidaya kunya taji tace ke Aunty,Naila tace ah to Kuma baza a Fadi gaskiya ba
sai a zauna ana boye boye kamar me bin Maza,Mohsin ne yace Dan Allah muje ko kunya
bakya ji naga ranar da zaki hankali ki fara kunya Umma fa tana jinki sharewa
takeyi,Naila tace to ai ta San harkar itama gashi nan ta siyo min kayan gyara.

Suna fita taga mota me kyau Sabuwa wata zata Kai ta 2m,Naila tace motar wa ka
aro? yace ke baki sani ba to mijinki ne ya bawa Abba,Abba yace ya bar min ita nine
Dan zamani Allah ya tsare shi da tuki,da fa wai siyarwa zaiyi Umma tace wlh ba
Wanda zai siyar, Naila tace yayi kokari Spark gaskiya,nayi dacen miji,shi yasa nake
sonsa fa,Mohsin dariya yayi ya fara driving,yace Naila na fahimci Baki San Hallare
ba shi yasa kike wannan iskancin,wlh na Santa kaji Yaya to bari kaji na Santa sosai
sau nawa Ina kare mata kallo,Mohsin yace ai shike nan magana ta wuce,yanzu me zaki
siyawa Amaryar? Naila tace a siya mata turare mana,tace Yaya ya Hanan wai? Yau a
gidanka zan kwana,Yace kishi take Abba ya fada mata zanyi aure in kika ga haukar da
take ya Baci,Naila tace to ya nonon nata? Yace ai yanzu nake kallonsu kullum sai
anyi yawo ba riga tun Ina kallo a dadin Rai har sun sire min,yanzu ma ni haushinsu
nake ji,kullum Kuma sai an bude,Naila ta dinga dariya,tace duk duniya ban taba
ganin Dabba irin Hanan ba,da haka ake birge miji,Mohsin yace uhm ni yanzu na Amarya
nake Hange na gaji da nata Abu duk sun Sha iska sunyi Sanyi sun huce,Naila ta dinga
dariya tace yau dole na kwana a gidan,yace a satin Nan zamu tare a sabon gida kafin
ayi bikin.

Turarukan suka shiga Shopping mall zasu siya,Mohsin Zai biya kudin Naila tace
Ina auren me kudi zaka siyi Abu Ina wajen matsa ni taje ta biya kudin sai gidan su
Beauty,Naila taga har cikin gidan suka shiga, tace me zan gani wai? Wannan ai gidan
su Beauty ne,dariya Mohsin yayi yace itace amaryar Ashe babanta shine nake zama
Masa a shago,gashi ya bani gida sabo part biyu ba Nisa da daya gidan nawa ga Kuma
yace naci gaba da juya wannan shagon halak malak,Naila tace amma nayi murna,Ashe
Kai na dinga yiwa zance a gidan yari,yace wlh,Naila tace akwai tsiya Yaya Hanan da
amarya fa za a gwabzu,Mohsin yace wannan bata fada,yarinya shuru shuru saliha ga
iya soyayya ai Hanan sai dai ta zalunce ta.
Naila tayi dariya a ranta tace zaka ga Saliha ganin idonka.

Beauty ansha gayu cikin Abaya me tsada ta fito suka rungume da Naila tace amma
wlh Kun raina min wayo amma naji dadi ko ba komai na nadaki a madadina tunda ban
auri Yaya ba yayi Kuskuren zuwa a gidanmu, nasan zaki zama wakiliyata yawwa a adana
min shi,Beauty harda Jin kunya wai ita ta gari Naila tace duk fake ne nasan komai
yarinya,tafawa sukayi suna ta hira suka bar Mohsin a zaune shuru.

Ya gyaran Jikin? Beauty ta tambayi Naila,tace Inda kika min kwatancen na fara
zuwa tuni ma suna goge min skin sun bani su lotion da sauransu,sai harkar
kamshi,sai dare su Naila suka wuce gidan Mohsin.

Hanan tana Palo kawayenta sunzo sun zauna in banda tsinewa Mohsin da Maza baki
daya ba abinda sukeyi suna zugata, wallahi karki sake Amarya ta takaki ko shi ya
takaki,Hanan tace Ina zan yarda ai wlh tunda naji zancen nan shi da zaman lafiya
sai dai ya Gani a makwafta,masifa da bala'i ya dinga ganinsa kenan.wata a cikin
kawayen me hankali tace ni Kuma a shawara ki kwantar da hankalinki Kuskuren da kika
San kinayi ki gyara,sannan karki tayar Masa da hankali domin zai sake tsanarki ne
wlh,tun Yana sonki zai daina gaba daya,idan kuwa kika kwantar da hankalinki an San
akwai ciwo amma daurewa akeyi, mijinki na gari ne ki daure ki lallaba abinki shine
kadai zaki siyawa kanki mutunci.

Ko mutuwa zakiyi wallahi aure bazai fasa ba, Maza basa fasawa,idan kika daina
nuna Masa kishi sai yafi Jin kunyarki ,surukarsa zaki zama wlh Kuma zai dinga
tsoronki,duk abinda yake ciki akan auren sai kinji labarin ya fada miki,ke ko fada
suka yi sai ya fada miki,kece uwar gida amma mu muke Bada kanmu har a kawo wata
sama ta Kai tazo ta kwace mijin ko tayi sanadin mutuwar aurenka.....da masifa suka
hayayyako mata to sannu ustaziya mu zakiwa wa'azi to baza ta kwantar da Kai ba
salon a takata kenan Yar bakin ciki,kawar wacce a cikinsu ma itace karamar tace
shike nan Allah ya Bada sa'a,suka ce Ameen munafuka.

Naila ce tayi sallama kafin ta shugo a palon,da Sauri Hanan tace kanwarsa ce
karku kulata itace ta je gidan yari taje a suffar Maza ta shiga cikin kartai wacce
nake Baku labari ta hadu da me kudi ya dinga sex da ita sai da ya gama cinyeta tas
sannan ya biya cin hanci suka fito ta bishi Abuja can ta dinga karuwanci yanzu
karshe ya aureta Dake Yana da kudi tuni ya kashe case din taci banza, Kuma kisan
Kai tayi, wata tace to ki dinga taka tsantsan da ita kar kema ta aikaki
lahira,Hanan tace ai yayanta da iyayenta boyewa suke basa so asan zancen Kuma naji
labari,Naila ce ta shugo Kai tsaye suka yi shuru basu kulata ba itama Bata kulasu
ba ta zauna,tace Hanan? Tsaki Hanan ta ja tana harar Naila sabo da yayanta zai Kara
mata kishiya.

Murmushi Naila tayi tace tare muke da Yaya mun fitar da ankon bikinsa namu
zakiyi ko kuwa naku zaki fitar da kawayen naki? tun yanzu har Kun fara dannar
kirjin ne? Ai dai kwa bari bikin yazo,Hanan ta fara dure duren ashar kamar
mahaukaciya,duk uban da bai Kara min kishiya ba baya kaunar uwarsa da ubansa,Naila
tace ai shi yasa zamu Kara tunda muna kaunar uwarmu da uban namu,Amarya me dadin
tuwo da Miya gata da nonuwa lukwi lukwi Yaya idan yayi pillow dasu sai ya makara
gasu jajir abinsa,dama shi yasa akace a dinga sirkawa idan uwar gida baka ce sai a
Nemo fara,Mohsin ne ya shugo kawayen suka tashi sum sum suka bar gidan ita Kuma
Hanan kawai zage zage take yi ba ma'ana ba lissafi.

Mohsin yace Naila bana son tashin hankali kin sani ko,Hanan tace duk wani
matsiyaci dai dai nake dashi wallahi,duk tsiya kafin ayu daram akai kwandi,wallahi
ba Dan shegiyar da zan ragawa ko uban da ya haife ki ne,Naila tace Abba kenan?
Hanan tace ae,Naila tayi murmushi tace kin San dai me kayan Miya yafi Dan koli
nagarta ko?ko a jari ba daya bane,Hanan ta sake tunzura tana zagi,Naila tace biyu
da safe biyu da biyu da daddare, Amarya ce sai mun Kara sai dai ki mutu,Hallare
dole ayi sharing dinta,idan ya Baki ya bawa Amarya yawwa,ta yayana tafi karfin mace
daya lalura dole sai an raba muku ita,Hanan tace Inshaallah sai an miki kishiya in
Allah ya yarda,Naila tace kema da za a miki ke kika yi wasa da damarki,ni nawa na
isheshi tun Ina karama nake Shan madarar shanu akwai kayan aiki,ko baki ga jikina
bane? Mohsin ne yayi alwala zai tafi masallaci yace Naila bana so fa bakya ji ne
wai,Shuru tayi ta kyale Hanan tana ta kumfar Baki.

Naila alwala tayi ta dauki Sallaya, Hanan ta fisge tace ai ba Yayanki ne ya


siya ba ubana ya siya min,Naila tace Hanan karfa ki haukace sallah zanyi,tsaki
Hanan ta ja ta Maida sallayarta daki,Naila tace hmm kawai ta shimfida dankwalinta
tayi sallah a Kai..

Jakarta ta bude ta dakko mata wayarta data taba dauka sanda ta fito daga gidan
yari tace ga wayarki,ta zaro kayan sawar data dauka a wanke a goge tace gasu nan na
biyaki abinki kar na tafi lahira da nauyi,Hanan tace barauniyar banza,Naila Tashi
tayi ta shiga kitchen zata zuba abinci,Hanan ta shugo tana huci ta fisge plate
dinta,tace ubana ya siya min,kular abincin Naila ta jawo Hanan tace wlh akan kici
abincin Dana dafa gwara na zubar, ta kwada flask dinta da kasa sabo dashi, abincin
ya watse ,Naila tace ikon Allah haka abin yayi tsamari? ashe haukar kullum shahara
take.

Hanan kuwa tana huci ta chakumi wuyan Naila tana zage zage Naila ba karfi,kokawa
suka fara Hanan ta hankada Naila Jikin kofa Naila ta bige kafarta,kofa ta ji mata
rauni a kafa jini Yana zuba,turo Naila tayi waje tafado kasa,kafarta dayar ta gurde
ta kasa tashi,Naila tace wlh sai nayi sanadin barinki gidan Nan sai an sakeki,kin
jawa kanki,Kuma baza a sakeki ba sai kin Sha wahala a gidan Nan sannan a miki korar
kare shegiya, sai kin koma gidan ubanki,dama ai kin tsufa tsohuwar banza

Mohsin ne ya shugo ya samu Naila a kasa ta kasa tashi tana ta kuka kafarta daya
wajen yatsa Yana ta jini,Mohsin ya dagata da sauri yace sannu nace miki karki biye
mata bata da hankali, muje na Maida ke gida,Kinga abinda nake gudu ko,yace yanzu
idan na saketa ko na koreta mutane zagina zasu yi ace sabo da zan Kara aure
ne,Naila tace karka saketa wlh sai ta kunshi bacin rai,tana dingishi ta dauki
Jakarta da mayafi suka tafi,a chemist ya tsaya aka mata dressing suka koma gida.

Tana kuka tana Bada labari,Umma tace bar shegiya aure ne dai sai ya Kara,Abba
yace Naila kema da tsokana ai dole tayi kishi ko wacece, baki kyauta ba ai sai ki
kyaleta, Nan ga darasi a gidan nan nace zan Kara aure uwarku wacce hauka ce bata yi
ba,Umma tace yaushe nayi haka? Hashimu kaji tsoron Allah,to ai dama ita uwa tana so
ace Danta zaiyi aure musamman in basa shiri da uwar gidan Danta, amma idan akace
ita za ayiwa to Kuma sai tsiya,Allah ya kiyaye min nayi wannan haukar a kanka cewar
Umma.

Hashimu yace na nawa Kuma,a Hakan ana rainani a haka akayi kuka kina tsoro zan
dinga yiwa wata girki,Umma tace to ka karo matar yanzu,yace sai da kika ga nayi
kwantai zaki ce na Kara kowa ta gujeni,Batoolar ma ta gujeni, amma sanda Naje zance
ai ta iya baza kunne taji Ina koya mata girki,Umma tace au har girki ka koya mata?
Kaci Amanata,Abba yace Kinga ki gasawa Naila kafarta ni na riga nayi kwantai Kuma a
gari, ya zanyi Kubra dai kullum Kubra kamar masifa,dariya Umma tayi tace Allah ya
kyauta Maka Dan Yagana.

Abba yaji sabon Suna harda sosa keya Yana murmushi,yace Uhum Uhum Uhum...Allah
yaji kan Yagana ana lahira,Uhmm ko su Yagana kamanni sun canja oho, su Yagana an
mutu ana gulma,sun zaci ni Dolo ne sai su dinga gulmar mutane Ina jinsu ni kuwa in
nade tsab a kaina, sai naje na fadawa mutumin da suka yi gulmarsa nace Yagana tace
Maka kaza,Naila ta kwashe da dariya tana kuka tana dariya,Babar Hashimu ce guda
amma yake fadar haka,Umma tace Inshaallah tana Aljanna Allah zai yafe mata, Abba
yace Ina mata addua kullum Allah ya yafe mata amma har ta mutu tana zuwa wajen
malamai wai sai ta Kara haihuwa,nace Yagana nima da ya kuka sameni ki fawwalawa
Allah, amma Yagana taki ji,kullum baza suyi hirar duniya ba sai zancen wasu,ni Kuwa
Ina ji duk na kwashe naje na fadawa mutumin,Ina ta mata nasiha sai ta zazzageni,to
yanzu wa gari ya waya? Sai dai nayi mata addua idan Allah ya yafe mata shike
nan,idan Kuma bata dace ba yanzu walakiri ya sassaba mata kamanni,Umma tace Dan
Allah ka dinga fadar Alkhairi,Abba yace ni na sata tayi gulmar? yanzu haka da za a
dawo da Yagana duniya bazan ganeta ba tsabar dukan walakiri.
Naila sai dariya suke kamar ba gobe.

Naila tana hawaye Umma ta gasa mata kafa, Spark Yana ta kira,yau bugu daya
Dake shagwaba ce har ta daga tana kuka,yace menene? tace uwar gidan yayavce ta kusa
karyani,Spark yace amma dai baki karye ba ko? tace ae tana shesheka tana cewa
kafata jini take yi sai da aka kaini asibiti yanzu ma Likita yace gobe da sassafe
lallai na karya da hantar rago,Spark dariya yayi yace to ai ta kwana gidan sauki
indai zaki warke.
Tace Kuma yace da ice cream da daddare kullum sai na Sha,sai me? Spark ya
tambaya,tace da tsire me Laushi,yace wannan ciwon ai da sauki,yace wannan bata da
Imani gaskiya,Naila tace ai shegiya sai nayi sanadin sakinta wlh bazan yarda ba,an
fasa kawo Maka Amarya Nan da kwanaki kadan sai na dau fansa,Spark yace a'a please
Dan girman Allah a kawoki sai muzo tare mu dauki fansa,amma Ina wani kar a kawoki
ai bazai yuwu ba,Spark yace ki rabu da ita Allah zai saka miki,ai dama na ganta duk
wata ya muka kwana ce,duk ta zama wata Rasss da Kwassss,Naila tayi dariya tace ko
tayi kwalliya ma bata kyau,Spark yace ai shine Rasss da Kwass din tayi expire
kenan.

Yace ki rabu da ita a kawoki gidan mijinki yarinya Kisha madarar Nido inji
Scoler,dariya suka yi,Naila bata San Hallare ba Sam ta zaci wasa ne,tace Yama sunan
style din da akeyi? Spark yace suna da yawa fa akwai su
Snake in the monkey shadow, su Bend down,Naila tace na gane bend down dai kamar
zaka Koma shekarar 2001? Spark yace Ehem ashe kin gane, sun Dade suna hira kamar
zasu kwana a haka, yau Spark yasha nishadi da farin ciki da wuri ya Sha baccinsa me
dadi,Naila kuwa sai bayan sun gama ta tuna ai aji take ja fushi ma take yi da shi.

Shuru tayi Umma ta fito daga daki tace lafiya? Naila tace nidai soyayya tana
cutata Umma idan ya kira sai na manta komai na dinga farin ciki,Abba da yanzu ya
shugo ya tsinci zancen,yace ai haka so yake Naila ki tambayi Kubra,Kubra ya sanda
aka turani zance wajenki na dinga guduwa Ina Jin kunyarki,Umma tace Dan Allah daga
masallaci ka dawo ka tafi Palo a kawo Maka abinci,Naila tana ta boye dariyarta,tace
ko Dan Abba ai ka so zaman gidan nan wlh.

Su Naila ana ta gyaran jiki ba daga kafa ko Ina gyara yake Sha ita da
beauty,sunyi kyau sun Kara haske ko Ina suka gifta sai kamshi,Naila har wani kiba
ta danyi, Hanan taga biki ya taho ta haukace,Mohsin yayi mata lefe akwati uku
Amarya akwati shida amma tace bata so,ta fatalo akwatunan kofar gida sai kwashewa
yayi ya Maida su gida wajen Umma,Ya Bata kudi ko zata yi wani abu taki karba ta
watsa Masa abinsa,Baban Beauty shi ya zuba musu furniture amma kowacce da kalar
nata,Hanan sabo da kishi da tasan zata tare duk tasa almajirai suka fitar da kayan
ta kaisu ta siyar da na bangarenta ta dauke kudin kayan ta Kai gidansu ajiya,ta
kawo kwararrabarbun kayanta tsofaffin ta zuba a part dinta,gidane hadadde yasha
alatu part biyu ko wacce 3bedroom da Palo,ko Ina a tsakar gidan yaji flower da
interluck, ga motarsa shi Mohsin lafiya Lau abinsa,Chikar gayu anyi dinkuna sunyi
anko har Naila da sauran kawayen su Beauty Naila ita bata da kawaye a birni sai
kauye,Kuma sai da ta fadawa kaka a gayyato mata kawayenta na kauye,Kuma an basu
alawa zasu zo su hudu.

Ana gobe daurin aure ko wanne bangare an cika gida ana shiri har dinner Mohsin
zaiyi lafiyayya,Naila da iyayi harda kiran Spark lallai sai an kawo mata motar Hawa
sabo da zirga zirga,yo abinka da amarya ana zumudi sai gashi ansa wani ya kawo Mata
in ta gama amfani da ita za a zo a dauka.
Gobe ce ranar Dinner Hanan tace dole taje da kawayenta sai sunga tsiyar da za ayi
a can,Naila itace gidan Beauty itace gidansu,gata itace babba mace a gidan da ita
Umma ke shawarar komai,abinci ma duk an Bada kwangilar yi,tukunya ko digo baza a a
Dora ba a gidan sai dai a kawo a dire,Naila tace Umma Spark ni fried rice zan basu
kar a kawo min wani abinci idan ba ita ba ranar daurin aure zaizo,Kuma zaizo Dinner
ma gobe,Umma tace ai dai ranar daurin aure ai za bashi ko? Dinner ai akwai acan,ae
ranar daurin aure,Allah ya kaimu.

Abba an kawo goro da yawa da alawa na daurin aure,sai cewa yake ni ta Hanan nake
so a raba abata nata Dana danginta,ana rabawa cewa yake a fitarwa da Hanan fa nata
Dana Yan uwanta.
Spark shi duk burinsa yazo Kano ya sace Naila a rubibi su kwana a masaukinsa,har
Allah Allah yake gari ya waye ya tafi Kano.

A dinga sharhi fans


Masu Sharhi Ina godiya

AsmaBaffa
[12/20/2023, 12:35 PM] AsmaBaffa: Paid group only 300

Accnt no
0175487861
Asmau Garba Muhammad Gtbank

Katin MTN
08061929616

Yan Niger
+22790795939

🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

BOOK1

71-75

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM

PAGE NAKI NE
Baby Ak

Follow this link to join my WhatsApp group:


https://chat.whatsapp.com/LAizQA6PofSLoFhQ7XeaQx

Ina kuke masu burin suga sun kawata gadajensu da hadaddun bedsheets? Ko Kuma
blankets kike nema? Masu aurar da yara ko kannai da ke kanki uwargida indai kitchen
utensils kike bukata
To kukanki yazo karshe.kuyi joining group din R&U exclusive kitchen and more
Ku more wa idanun ku da kayan kitchen Yan yayi na gayu da zannuwan gado na kowanne
kasa Zaki samu acikin farashi Mai sauki
Kuma Maza Bata barku abaya ba idan Kuna bukatar a hada muku lefe nagani na fada na
amarya Kona uwargida wato na fadar kishiya duk Zata hadamuku acikin kwanciyar
hankali.idan ma akwatunan kawai kuke bukata duk inkuka tuntubi Rumaisa zaku ganewa
idanuwanku
Tana Kano state Kuma Tana tura Kaya kowanne state afadin nageria harma da kasashen
da muke makwagtaka dasu
Zaku iya tuntubarta ta wannan number
07034559202

Washe gari kuwa Spark ko fadawa Naila baiyi ba ya taho sabo da sai taga dama
take daga Masa waya,kawayenta na kauye sunzo da shigar Yan Fulaninsu gasu kyawawa
sai kalle kalle suke yi,Rayya, Jidda,Nafee,Dije su hudu Wanda gasu yara ma Naila ta
girme su duk an musu auren Fulani sun gudu daga gidan Mijin ma basa auren, yara
kanana duk an sake su sabo da ba a basu time sunyi zabin su ba, wasu ma auren
hadawa kawai akeyi yarinya ta dinga guje guje,karshe idan ta Saba da namiji tayi ta
sheke ayarta.

Naila duk ta kira me lalle tayi musu,kayanta ma sun musu yawa ta fisu kiba da
tsayi sai ta samo kayan Hidaya ta basu kala bibiyu,Hidaya tasan Naila zata
basababbi bata ko hana ba ,sannan Kuma ta siya musu anko an Dinka musu su hudun
tunda tun a waya tasan zasu zo,sai murna suke yi,ta siya musu Yan takalma haka masu
kyau flat da wata ke siyarwa a makwafta,tace ko wacce ta zabi Wanda ya mata har da
Yar jarkarsu Naila tayi musu kokari, dama sunyi kitsonsu gasu da gashi,tunda suka
zo basa Hausa da Naila fulatancinsu suke ta yi Naila an samu Yan uwa,Umma sai da ta
gaji tace Dan Allah kuyi Hausa ai sai ace gulma kuke ba dadi mutane na zaune Kun
juya harshe.

Naila an Sha lalle hannu da kafa ya zuba kyau,sanye take cikin vest me siririn
hannu da skert Dan kanti sun mata kyau abinka da me kyau gata Yar bulbul,gashi
yasha gyara ya koma baki ta dole,babu ko dankwali a kanta tana zaune ana karasawa
Rayya lalle tana cire mata na hannu.

Ta juya baya tana aikin cire lalle taji Mohsin ya shugo danginsu Yan Fulani
sai tsokanarsa suke yi ango ango, kado baya Jin fulatanci,Sallamar Spark Naila taji
ashe tare suke da Mohsin,Naila a hankali tace Kai ga mijina nan,Rayya tace wayyo
kunya ku miko Hijabi aradu a lullubeta,ango ne zai ganta tsirarar babu sutura,Dije
tace shike nan Tantiriya ta gama yawo aradun Allah wai Ina zaki je da abin kunya
hoodi jam,aradu ban iyawa cewar Nafee,Naila tace ni an fada muku kunyarsa nake
ji,ai dama ke baki Jin kunya ko kado haka ya ganki ya kyaleki Tantiriya,tunda Yan
kauyen suka zo ba Wanda ya kirata da Naila sai Tantiriya,Umma tayi tayi su daina
fada sunki ji.
Spark kuwa da ita ya fara tozali Yana ta kokonto ko ba ita bace ne irin wannan
chanji haka yayi yawa,ya sake kallonta a ransa yace Janare wannan haske da taka
Kara haka,gashinta ya kalla yasan itace sabo da askin da taba yi gefe da gefe da
aka kwashe Bai Kai tsakiya yawa ba.
Naila tana jinsa ma Bata juyo ba sai murmushi take ita kadai.

Umma suna daki da baki,saitin Inda Naila ke zaune ya yazo ya tsaya kamshinsa duk
ya mamaye gidan,Hannu yasa a wuyanta ta baya ya kama sosai kamar me shaketa ta baya
a hankali ya girgiza wuyan ya saki ya wuce abinsa,Dariya Naila tayi tace ai nasan
kazo Malam,Dije tace kunya ta kamani ta jawo hijab ta dukunkune kanta,Rayya tace
Ina zan sa kaina yau da abin kunya ku matsa na buya, Tantiriya tace kwayi Kwa gama
me za a fasa mutuwa ko hisabi? tamike taje ta wanke yatsunta da taba lalle, Umma
tana ta faman kiranta,ta tafi palon,Spark a cikin Yan kauyen Daji sai kallonsa
suke.

Masu wasa da Naila suka fara tsokanar Spark,Suna cewa wannan ma ai namu ne Kai
yaro wannan da Fulani yayi kama,Spark yace a'a yanzu ba a alfahari da ku,wato yanzu
a kasar Nan kowa ya tsani Fulani sabo da Bata gari sun watsa mu,Spark an daina
alfahari da Fulani yanzu bana ciki ni,Naila ce ta shugo suka koma kanta su
Tantiriya an dawo Yan birni iya shege ya kare sai dai kiyi a dakin mijinki,Naila
tace wlh bai kare ba kawai dan nayi aure sai ace tawa ta kare sai kace wacce ta
tsufa ni wlh shi yasa ma bana son auren ai su Yaya ne suka jawo min.

Mohsin yace kika jawowa kanki dai dama mene amfaninki,Ango Spark in banda
kallon Naila ba abinda yake,sabo da iskanci Kuma taga Yana kallonta ta fuske tana
surutu tana girgiza,Spark sai ya susuce,Umma sunga yayi shuru sun zaci kunya yake
ji,Umma tace ki kaishi Daya dakin ga key can,Naila ta dakko Key tace muje,Mohsin
yace dama gidana kuka kaishi ba mutane can,Naila tace a'a tasan halin Spark,yace
Hanan fa tana tsohon gidan har yanzu bata koma sabo ba ta dai kwashe kaya ko Ina
yanzu ba komai wai sai ranar da za a Kai amarya itama kawayenta zasu sake rakata
dakin miji,Spark yace ko Maza ne suka kaita ana farko,kara'i zatayi kenan ko
babanta ne ya kawota ne farkon aure yanzu take so kawaye su Kai ta,Mohsin yace
iskanci ne kawai ya fice.
Dakin Naila ta bude ba komai ciki sai katifa ta Sha gyara da bedsheet, Spark
yace Alhmdllh sa key,Naila tace ban gane ba.
Key din ya kalla yace bani key din idan wani ya shugo fa.

Wai me zaka yi? hanashi key tayi ta fice daga dakin tare da Maida key din wajen
Umma ta saka bra ta saka riga me dogon hannu sannan ta zuro hijab ta dawo dauke da
ruwa da lemo a tire,wai security kika saka kenan? Naila tace ba dole ba ka bari
mana a kawoni ko mene sai kayi,shike nan ba abinda zan taba? Naila tace ae,zaki zo
ne ai zan fanshe,komawa tayi ta kawo Masa sandwich da Samosa duk ita tayi abarta
Kuma sabo da shi tayi,Naila an dage da koyon girki sabo da a birge miji,ganin tana
so yaci, sai ce Masa take yi Kaci kaji,yace bazan ci komai ba sai kin koma kin cire
rigar Nan da kika saka,kina yi zan ci,Naila ana so aci girkinta,tace yaushe zan
koma cire riga a cikin mutane,cire a Nan yanda kika saka ki cire, sai na ci
abincin, ta cikin hijab ta cire ta zauna da vest dinta ko bra din ya ce ta cire.
Yace hijab fa a'a cire,Sai dai idan baza Kaci ba ta furta,fisgo hannunta yayi ta
fado Saman katifa.

Tsaya nifa ba abinda zan miki hugging naki kawai zanyi,rungumeta yayi a
jikinsa,tasa hannaye tayi hugging nasa back,Naila da anji Jikin Spark sai jikinta
ya mutu murus,abinka da shakuwa an Shaku,kasa katabus tayi sai ma sake kankame shi
da yi,a hankali ya dago fuskarta tare da tallafar fuskarta ya fara aika mata da
kiss,Naila Idanuwa ta lumshe tsayawa yayi Yana karewa fuskarta kallo Yana dariya
kasa kasa yace bude idon to,suna a rufe tace baza su budu ba yanzu, ci gaba yayi da
tsotse bakinta,tun tana Dan sharewa har ta kasa ta fara Maida Masa martani , tana
juya bakinta cikin nasa kamar zasu cinye juna,Spark yace kaga Yar gari,kin gama
wayewa,Naila taji kanta ya Kara girma an yabeta har da sake bada himma zata nuna
wayewar,Batasan Wato yake mata ba.

Juyata yayi tare da zaunar da ita tsakanin kafafunsa bayanta Yana Saman
kirjinta,A hankali yana shafa wuyanta har ya gangara tare da sa hannunsa ta cikin
vest Abu ko bra,Naila zama ta gyara tana Jin dadi,harda ajiyar zuciyar bata sake
magana ba sai dai tayi ta faman Sosa idonta, tana tsoro kar tayi Nishi sauti ya
fita, yace bata da kunya,yace Ko ba Tantiriya bace ne? Naji tayi mukus,Ido ta Sosa
tace itace mana,ya naji kinyi shuru ke da zanji kalamai na tashi,Naila tace nayi
hankali tare da dawo da hannayenta ta bayansa ta rike shi Kam,Spark yace au baza
kice komai? Haka kawai nayi ihu ka dinga min dariya daga baya, na daure abina,kiyi
abinki ni ba abinda zan miki Kinga a musulunci ba a so duk abinda kayiwa matarka
idan tayi ihu ta nuna taji dadi daga baya ka dawo kana mata dariya ko kana
tsokanarta to zata dinga Jin kunya ta daina shi yasa akace ba kyau,nima Kuma idan
nayi ihuna kika min dariya daga baya ba kyau,Naila tace ni dai wlh sai na Maka
dariya sai na tsokaneka,dariya suka yi.

Sandwich din ta dakko ta fara ci sai ta yi wayo wai tana cewa sandwich dadi,a
ranta tace karya nake Kaine me dadin bari na fake da dadin sandwich nake ji,Ido ta
lumshe tana taunawa tace dadi kashe ni wlh dadi,Spark ya ganeta shi dai yace ko dai
nine Sandwich din? Naila dariya tayi tace na rasa me yasa motsi nayi sai ka
gane,Spark shi Kam boobs yake aikin sarrafawa sai mutsu mutsu Naila take yi.
Ta bayanta ta miko Masa Samosa, kansa ya duko da shi saitin hannunta Yana
gutsira,Naila tace Kwalbewa duniya ce,kwanciya yayi ya dawo da ita samansa,Naila ta
Kalli Hallare harda dagawa Spark riga ta ganta kuwa a wando duk tana fitar da
ni'ima,Naila ta rufe da sauri tace Allah ya baki hakuri,Bai San ma ta daga masa
rigar ba,yace me? tace to Hallare ce take dalalar da yawu fa,ke fa? tace bado wai?
Tace ae me yake ciki? tace aradu Hawaye ne yake ta zubowa,Spark dariya yayi yace
Bado na hawaye,ya dauki lokaci Yana murzata sai da taga duk ya fara fita hayyacinsa
ta kwaci kanta da kyar tace a bari sai an kawo Amarya please,yace ni da nazo yau
daga dinner sai hotel zamu kwana, Naila tace Bada ni ba wlh haka kawai aje na samu
ribar Hotel,ni kwana nan gaba daya ban yarda da Kai ba,da a baya wani Dan Salihi da
Kai yanzu Ina abin naka kullum shahara yake.

Snacks dinsa ya zauna Yana ci yace ah yanzu an fara iya abubuwa,ai dagewa nayi
naga za a barni a baya kullum girki nake koya,yace good girl ga Indomie da bishiyar
salat ai kina kokari,kwana nan zaka yi tumbi,sun dade suna hira kafin yace zan wuce
hotel naje nayi baccina kafin lokacin dinner,tace to shike nan abincin fa? Kadan
Kaci,kafin na fito naci a gidane ai naci snacks dinki da yawa abincin ne ban ci da
yawa ba,mikewa yayi yace yau hannuna albarkar da take jikinsa tayi yawa,dariya tayi
yace you are so sweet,komai naki me kyau Allah ya miki baiwa,Naila tace Alhmdllh
bari na kira kawayena na kauye ku gaisa,yace alright ya koma tare da kwanciya a
katifar.

Fita Naila tayi bayan ta Maida hijab dinta tace Rayya tunda an gama lalle Kun
wanke ku zo zaku gaisa,Rayya tace wayyo ni Allah kunya,Dan birni haka,Dije ita
gwana tace ku fa baku waye ba aradu ku taho mana,suka tashi a kunyace suka shiga
dakin,Spark Yana kwance abinsa Saman katifa suka durkusa har kasa tare da gaida shi
Ina yini,yace lfy Yana fara'a a fuskarsa, Yana dariya a ransa kuma irin daurin da
suka coka goshi kwal,ya musu irin gaisuwar su,yace ya gida? Suka ce lafiya Lau mun
sameku lafiya? Spark yace lafiya Lau..lafiya Lau,ya manyan? Sukace lafiya kalau
kalau wallahi,ya sake cewa ya shanu ya masu gidan naku? Rayya tace nidai Dan
marakina Daya bashi da lafiya ciwon hanta ta kamashi,Spark yace to a yanka shi mana
a Sha dadi, suka ce kaiiiiii hodi jam suna dariya Rayya tace ai Affana sai ya kusa
kasheni,sanuwar fa wacce ta haifi Dan marakin gadonta nayi wajen kakana,Spark Yana
jinsu,Dije tace nidai tsakani da Allah mijina ya sake ni dukkan mu auren mu ya
mutu,gwara ma Nafee ita ta samu ciki ya zube mu kuwa shuru,Spark ya kallesu wannan
tsigi tsigin yaran ma me za a tsinta a jikinsu,Jidda tace mudai Allah ya kiyaye mu
musamman ni Iro Allah Bai bashi sa'ar iskanci Dani ba da tuni na boni la
lalashe ,Spark Yana ta dariya a ransa yace a ransa Iro anyi dakiki marar rabo,Rayya
tace kaga ni dai Ina son Sagiru na wlh amma iskancin Sagiru bazan iya ba nace ni da
Sagiru kaadii fau fau aradu,Spark yace uhm Sagiru ya cuci kansa, Rayya tace
Tantiriya ta dawo birni kowa a riga Yana ta kewarta.

Spark yace na manta ban tayaku jimami ba ya akaji da rashin Tantiriya? Suka ce
ohh Tantiriya ta barmu sai hakuri muke ta yi Allah yasa hannun na gari ta fada?
Spark yace na gari ne mana tunda gashi ta hadu da Tantirinta,dariya suka yi suna
Jin kunya suna rufe Baki suka ce to mun tafi,yace na gode ya mika musu kudi suka ki
karba sai Naila ce ta karbar musu.

Suna fita suka dinga labari wlh kirki ne da shi Ashe suna ta bawa Umma labari ai
har Hira suka yi dama Yana da magana,har wasa ya dinga yi mana wlh akwai kirki, a
farko mun zaci bashi da mutunci mun ga Yana gadara da takama Ashe shima Tantiri ne
a nutse yake magana baza kice shi ya fada ba,Spark fitowa yayi zai tafi Naila tazo
zata raka shi ya Dan matsa nesa da ita kadan yace kar ace bani da kunya a gidan
surukai,suna zuwa kofar gida yace koma gida,karki min make up lokacin dinner kuma
na tsani wannan kwalliyar da mata keyi,duk kyanta Bata birgeni Sam,kiyi da kanki
kawai ni bana son make up duk ta canjawa mutum kamanni,Naila tace to na huta nima.

Ana ta Shirin Dinner da yamma Chikar gayu itace babbar kawar Beauty an dauki
wanka kamar me,Amarya kuwa tana wajen make Up tare da wasu kawayen ta Sha farin
bride material me tsadar gaske an mata wata gown me kyan gaske ta zaratan amare,an
nada mata dauri da silver gogoro, takalmi Silver jaka ma haka,make up din tayi kyau
an dora mata mayafin amare a Kanta sharashara sai walwali take ta ko Ina,Ango Yasa
Shadda Yar ubansu Silver kalar takalmi da jakarta da gogoro.

Su Chika duk anci ankon Leshi me kyan gaske Blue and white,kawaye an Sha wanka
sunyi gayya kamar me, Yan mata tamfatsa tamfatsa sunzo duk kawayensu ne yawanci
daga gidan yari suka fito,Kamal ne zaizo shima sabo da abokinsa Spark ai kuwa
Rafeeq yace akwai dinner? akace ae yace ko banza na Kalli mata mu tafi
Kamaluddeen,Kamal yace Allah ya shiryeka Kai ba Dan iska ba sai son kallon mata?
Rafeeq yace ko banza ai na kashe kwarkwatar idona muje,Da yamma suka dira,Rafeeq
lokaci nayi yafi uban kowa saurin shiryawa yace Kano sai da shadda ya fito cikin
shadda me kyau wata ita ba milk ba ita Kuma ba ruwan kasa ba,suna dakin Spark shi
da Kamal,Kamal yace gaskiya kayi kyau Rafeeq Allah kawo babban rabo,yayi shuru
kamar Salihi,Mayen mata Misam ne Allah yayi ya kira wayar Rafeeq,kana Ina? Rafeeq
yace dinner Yan mata ne iya kallonka,Misam yace amma baku da mutunci shine ko ku
fada min ni shugaban mata guda,Ba komai ai gobe ma matan zasu taru ko? Rafeeq yace
ai ance akwai walima mata da Maza za ayi wa'azin zama da iyali lafiya,Misam yace
tab zanzo naji Ina jin wa'azi Ina zabar nawa ya nawa.

Ana ta tafiya wurin dinner dangin ango dana Amarya,Abba ya shugo gidan Yana
tarkata kan Yan mata danginsu ku fita ku tafi aje ayi rayuwa Allah ya sanya
Alkhairi,Wata babbar mace me suna Tani tace zanje nima nayi kallo, Abba yace Tani
gidan uban wa zaki? ki batawa yara show sunyi gayu aga irinki kamar wata Tsohuwar
mota hayis ba Inda zaki ai zubar da girma ne,Kubra ta cakare taci wani material an
mata make up,kyan da tayi ya Isa,Dake Kubra ce sai Abba yace Yar Inna an fito? Ko
ranar bikinmu baki kyau haka ba,idan an girma asan an girma,Kuma wallahi sai kika
yi kyau kamar kiyi ta zama a haka,ai da bazan sake fita wajen sana'a ba gwara
kullum na dinga kallonki.

Umma tace wai baza kaje bane? Abba yace a'a haka kawai naje na zubarwa da
yarana mutunci wlh tsab naji kida zan taka, Kinga ai girma ya Fadi kuje ku dai kawo
Basma nayi miki rainonta,tace madararta tana dakina Jikin bed,yace to ya karbi
Basma Umma ta fita ta tafi tare dasu Hajiya Tagwadas ansha gayu.

Naila ta Sha anko itama ta cakare ta zuba kyau kamar a saceta kawai Spark take
jira,ba a dade ba yazo a mota ana tuka shi ya hakimce a baya sai kace shine
angon,shadda sky ya saka shigen color din ankon da Naila ta saka,baya ta bude ta
shiga gefensa,Yana ta kallonta yace kinyi kyau sosai,Amarya da ango sun karasa
wajen Event suna waje ana ta musu ruwan pics sannan aka Bada sanarwa Amarya da
Ango zasu shugo,salon kida aka canja.
Amarya da Ango ana rakosu ana wata musu buzzer suka shiga tar da zauna,Rafeeq
tuni suna ciki shi da Kamal,Spark ne ya karaso tare da Naila rike da hannunta suka
nemi wuri tare da zama,ko wanne table da abinci da kayan Sha gasu Nan.
Babbar Kawa aka Kira Suhailat Chikar gayu,Chikar gayu ta fito wannan fili ana
nemanta,tun daga Jin sunan kowa ya baza Ido yaga wace Chikar gayu,Chikar gayu
mikewa tayi akayi harrrrr ana kallonta,ta isa gaban Mc ta karbi Speaker tace
Alhmdllh sabo da farin ciki a bani kidan Chika,aka saki sauti Chika tayi rawa iya
rawa kamar me ita kadai kwal ta iya chashewa,Naila ce taje da Dan takunta kadan
tana mata liki,Su Hanan ne suka shugo da kawayenta suna cin magani.

Naila ce ta radawa Chika maganganu sannan Chika tace a tsaya da kida zata Dan
Bada tarihin Amarya a takaice,Sai dariya Chika take bawa mutane domin rawar tata ma
ta iya shege ce,Speaker ta karba tace na tabbata kowa yana Jin Hausa a Nan sabo da
haka ba ruwan mu da turanci America ma uwata,aka yi dariya.

Tarihin Amarya ta bayar a takaice a nutse Kuma, aka tafa mata,sannan tace
Alhmdllh Alhmdllh nasan Amarya baki gaji siyar da dankunne da tozalin tsofaffi
ba,Baki gaji siyar da mazari da Alli ba wannan sai Dan koli,Naila tace gaskiya ne
wannan, sannan uwarta Bata kulla omo dan awo cewar Naila,bata da kanne ma bare ayi
mata fitsarin kwance a mayafi ko Ango ya taba Jin zarnin a Jikin Amarya sanda Yana
zuwa zance? Idan ya taba ji ya fada,Naila tace sai dai kamshi wlh,yeeeeee yan mata
suka saki shewa.

Hanan ranta ya baci ita da kawayenta masu zugata,tun a wajen ta fara kwalla,tace
ba Wanda yasan sirrina sai Naila,wallahi wallahi sai sun San sun min habaici,sai na
lakadawa Amarya duka bari a kawota a ranar a gaban mijin nata shege munafuki ai
shine ya Fadi sirrina.

Naila tace sabuwar Miya sabon tuwo,me za ayi da tsohon tuwo sai dai almajiri wlh
ko a jefa a bola,Chikar gayu tace Kainuwa dashen Allah Amarya Beauty an gaji arziki
gaba da baya, fara me farar aniya babu Mai ba sabulu natural daga Allah ce,hakora
reras ango ka dace,Naila tace da gani ba yunwa a jikinta Kai da Ganinta kasan ta
Sha Madara ta koshi tayi brush da Naman kaza,yayana yayi dace,yanzu nasan yayana ya
auri mace, na tabbata ango kayi dace domin ka samu mace ta gari wacce zaka samu
nutsuwa a cikin gidanka,wacce zata kula da Kai da danginka da duk wani Wanda ya
shafeka.

Duk kawayen su Chikar yawanci daga gidan yari suka fito babu na gari sai dai dai
kowa shegiyar kanta ce shi yasa basa Jin kunya ana fada zasu saki shewa,Chika tace
jama'a a gurguje bamu iya tashin hankali ba duk da cewa Kawata Nawwara wato Beauty
tana da abokiyar zama

Sabo da haka zan danyi nasiha ga Amarya,Beauty idan kika shiga ciki kika tashi
hankalin ango to kinci amanata ni babbar Kawa,ko da abokiyar zamanki ta tsokaneki
ki to ki nuna mata zaren ba kalar yadin bane, ki mata fatan shiriya idan Kuma anyi
rashin sa'a tana da motsi a kanta to karki sa kishi a ranki ki tsaya iyakar
iyawarki na ganin cewa an sadata da asibitin masu rangwamen hankali,Bamu ce idan an
tabaki ki kyale ba,a'a bamu gaji haka ba,ba ruwanki da tsokana amma ana cewa kule
kice chass amma a wajen me gida,yeeeeee ayiririri sai Chika lallai a nuna mata
gidan kaso ba karya ba cewar Yan matan,Chika cikin nutsuwa taci gaba yanzu kishin
fada da hauka jahilci ne da rashin sanin darajar Kai,a wajen me gida ake nuna
kishi, Idan ta bashi Sadine ki bashi sukumbiya,aka kwashe da dariya a wajen,Rafeeq
Yana dariya yace wannan yarinyar ban taba ganin Yar iska irinta ba,wai
Sukumbiya,Kamal yana ta dariya yace ai dole suyi Yan gidan yari ne fa kaf kawayen
maybe,waccen matar Spark din itace key na iskancin ita take musu rada.
Sabo da haka Amarya a zauna lafiya da miji,mudai Munji dadi da iyayenmu basu
gaji siyar da tozalin mata da Alli ba,Mun gode Jama'a Allah ya Maida kowa gidansa
lafiya ta mikawa MC waya,Hanan ta kumbura iya kumbura ta fusata,Mohsin ango Yana
jinsu ba yanda ya iya da su yaso dai ya hanasu amma sun shammace shi,Bai zaci haka
zasu yi ba,yace maganin Hanan kenan da ta taba Naila ita zata dinga sasu suna mata
rashin mutunci,bata San Naila ba,da ace bata kula Naila ba da lafiya za ayi bikin a
gama,Naila ta koma ta zauna kusa da Rafeeq tace baka gaishe ni ba Ina
Auntynka,Rafeeq yace ni kawar Nan taki badan Yar duniya bace da na sota ma,Chika?
Yace ae ita amma duk danginmu mu kare a Yan gidan yari fisabilillahi,Naila tace
gobe za a dakko malamar mu me yin wa'azi a gidan yari ta bangaren Mata,Matashiya ce
irinmu amma akwai ilimin addini da hankali wlh ga wa'azi da koya zamantakewar
aure,yanzu ku Dan masifa ma malamar me wa'azi yan gidan yari takewa wa'azi duk
malaman duniya,Naila tace gwara irin tamu,shekarata ashirin a gidan yari a can aka
haifeta yanzu an fitar da ita shekaru biyu da suka wuce Bata fi 22yrs ba wlh sai
baiwar wa'azi,Rafeeq yace Allah ya kaimu ai harda Maza maji wa'azin,su Chikar ne
suka gayyato mana malama Ikram,wlh indai kana son Chika zan Maka hanyarta,sai nayi
shawara cewar Rafeeq,Kamal yace Amarya ango Yana harararmu ki koma wajensa kishin
masifa ne da shi,Naila ta mike ta koma wajen Spark.

Anci an Sha anyi liki,su Hanan anyi kyau anci Leshi harda zuwa fili ta rike
hannayen Mohsin tana rawa duk cikin kishi,tana ta uban tikar rawa harda Karin
haushi take tikar rawar tana yi da sauri da sauri kamar mahaukaciya,duk ta
zauce,Mohsin yaga abin yayi yawa yace karfa ki sumar da kanki,kida slow music ki
dinga uban rawa haka kowa na kallonki a mahaukaciya,Hanan ko kulashi bata yi ba
kawai ta hada zufa tana haki tana tikar rawa a firgice harda dukawa,tana cewa uban
kowa ya Gani bana kishi,Ta fada da karfi kowa Yana ji, Spark ya dinga dariya yace
Kai jama'a Dan Allah ga kudi na dauki nauyi a Kai waccen asibitin mahaukata,Rass da
Kwass fa ta haukace Baby,Ni na taba ganin kishi haka.

Umma ce ta gaji taje ta fisgo Hannun Hanan ta fito da ita tace baki da hankali
ne,Allah ya isa duk munafukan surukan da suka zuga aka min kishiya ai munafunci
ne,surukai su dinga munafunci suna zuga dansu Yana aure sabo da an tsaneka wallahi
Allah ya isa,su an barsu sun zageni sun zagi iyayena sai ni yanzu sabo da Ina rawa
za'a hanani ta fisge hannunta ta fice daga wurin dinner din gaba daya sai gida.
Can ta iske da ginta tsirari tana zage zage tace wallahi sai nayiwa amaryar duka
za a kawota ne,sai na cinnawa gida wuta idan na tare,suma dangin sai wani bata
hakuri suke suna Kara zugata a nutse.

Bayan an gama Dinner Spark yayi hanyar Hotel da Naila ta fashe Masa da kuka
tace nice babba a gidanmu mace komai Dani ake shawara Idan Umma suka ji ni wlh
bazan je ba ka sauke ni,Spark yace ko Abba bazai ce min komai ba wlh Dan na daukeki
nifa ba abinda zan miki nayi alkawari sai an kawoki gidana,Naila tace aje wajen
Abban indai ya yarda zanje,Ta Manda Abba Dolo ne.
Suna zuwa suka same shi a kofar gidan Yana jiran Naila zai mata kaca kaca,dama
yace yau sai yayiwa Naila kaca kaca a gidan da fada, yace naji abinda kuka yiwa
Hanan a wajen party ke Naila ki kiyayeni ke Naila ki dinga saukakawa ranki ato
magana ta gaskiya, shike nan fadan wai ya gama,Spark yace Abba nima Kara na kawo,
akan nace ta rakani unguwa wai baza taje ba, Abba yace ke Naila ki kiyayi fushin
ubangiji,kibi mijinki sau da kafa da kika dawo gida mu me zaki yi mana? Banda ku
cika mu da surutu da kawaye,Naila tace Abba fa hotel yace hotel fa tana hawaye,Abba
yace Yar banza ni da Kubra zata kaini Hotel dinma ai San barka,so nake na samu kudi
nima na dauki Kubra muje picnic.

Spark kasa rike dariyarsa yayi,Naila tace Abba Umma fa sai ta sake haihuwa
wlh,Spark ya sake shekewa da dariya yace Dole dai a yara a samu DNA na gado ko Yaya
ne Naila itama doluwarce,Abba yace ki daina ja da ikon Allah,da ba a haihuwar za a
haifeku ne,gashi muna ta yawa a arewa sai cinye zabe muke na shugaban kasa,namu ne
suke ta mulki,Abba da suke cin zaben ai wuya muke Sha munfi kowa Shan wahala,Abba
yace ba abinda ya dameni da haihuwar Kubra,Allah in ya bamu muna so wani ma Yana
kuka yake bashi da yaro.

Naila ce ta tsorata Abba tace Yan hisba kame suke yi yanzu a hotel,Abba yace yo
Karuwa na dauka da za a kama mutum,jiya naji wa'azi ance a dinga fita da mace yawo
idan matarka ce,yanzu ance za a tafi dake kinki kina karyata malamai kamar marar
Ilimi,Abba kawayena su Rayya fa, in banda hirar shanu me suka iya,Naila yaja gefe
Yana mata kus Kus wai nasiha yace baki da hankali ke bakya koyi da uwarki,a gaban
suruki kike jayayya da ubanki wallahi watarana idan kuka yi fada zai miki gori
namiji ba Dan goyo bane,inja ki ja a gabansa Yana kallonki a marar tarbiyya,ki wuce
ki tafi idan Kuma baza ki je ba wallah baza ki kwana a gidana ba sai dai ki kwana a
waje ko ki tafi masallaci,Naila juyawa tayi tana fushi ta shiga mota,Spark da gulma
sai da ya tabbatar Naila sai ta je, yace Abba a hakura tunda bata so da an barta.

Abba yace a'a kuje kuje tafi da ita ai ba a biyewa mata haka suke da yanga ai
idan bata yi haka ba ai bata cika mace ba yaro,ai macen kenan,Spark yayi godiya
Yace Abba Allah ya Kara sutura,Abba yace Alhmdllh sutura Kam Ina da ita ma ta
isheni haka, Spark yayi dariya a ransa yace wlh Abba Ina ga bokaye ba mutum suka
sawa mamansa a ciki ba kawai aka haifo shi.

Naila mota ta shiga tana hawaye tace ko Kaka bamu gaisa ba da shi,Gani yayi
bilhakki take Masa kukan,yace ai ke dama ba a abin arziki Dake,yace driver juya ka
kaita gida kar ace satota nayi ,fushi yayi,Naila ta kalleshi kadan tayi shuru ya
Maidata gida,ko sallama bai mata ba yasa driver ya ja mota suka Kara gaba,Yana mota
sai cewa yake hmmm ya ja Kwafa yace yarinyar nan zata gane kurenta bari a kawota.

Naila bata samu Abba a waje ba tayi sauri ta shige dakin da suke zaune da su
Rayya,suma an dawo dasu daga wajen Dinner har sun kwanta,Naila ta shugo tare da
cire kayanta ta canja marasa nauyi ta sa Hijab ta wuce dakin da kaka yake tare da
wasu dattijan,Yace Naila,tace na'am Kaka,yace shugo Maza ki karbi sakonki,Shiga
tayi ya Bata magunguna yace ai duk kin San yanda ake amfani dasu,tace ae Kaka,yace
to zauna mana,wuri ta samu gefe ta zauna ya fara mata nasiha sosai,Naila tana ji
tana to.. to.. to.. ko Dan kuka babu,ya Dade Yana mata nasiha dattijan ma da suke
daki daya, suka tayashi sannan yace idan an kaiki watarana sai kuzo min ziyara ko?
Naila tace zamu zo Kaka,yace to gasu an dai kaya an nuna miki ko? Naila tace ae
Kaka na gode duk ance ango yayi komai sai da ka kawo min kayan kitchen masu kyau
harda tv plasma katuwa da fridge.

Yace ai sa na siyar muka tafi birni da goggo muka siyo miki na Yan birni,da ace ma
ango baiyi komai ba ai ni zan miki kayan dakin,goggonki ta baki naki magungunan ko?
Naila tace,yawwa wannan naki ne karki wasa dasu yanda tace ki Sha haka,Naila tace
to tayi musu sallama ta tafi dakinsu tayi kwanciyarta.

Washe gari karfe 11am ne daurin aure,wanka duk suka yi ko wacce taci gayu,Umma
Shadda ta saka maroon,Naila da kannensa duka shadda ce pink,Ango kuwa Fara ce Kal
ta Sha aiki,Abba yau yasha kyau kamar ba shi ba,Shadda Gezna Mohsin ya Dinka Masa
Arsh,gidan Amarya aka dunguma daurin aure, Baban Amarya yayi gayya masu kudi ne
kawai suke zuwa,11:30am aka daura auren Beauty Nawwara da Angonta Mohsin Hashim kan
sadaki dubu Hamsim.

Hanan tana Jin labarin tace ai bata yi tsada ba wlh,dubu Hamsim duk kudin Ubanta
Sadakin yarsa dubu Hamsim ai sai a saka mata million Daya Muji,kawayen Hanan da
danginta suka ce munje gidan surukanki wlh ana ta Shan lemuka mu lemo an kawo mana
kadan har ya kare,wlh karki yarda kije a karo mana namu ko da bala'i.

Hanan gidan ta tafi lokacin an dawo daga daurin aure ansha pics da Amarya Ango
yazo gida Yana ta dauka da Yan uwa,Abba ana yin pics ya fita sallamar masu zuwa
Masa Allah sanya Alkhairi,Hanan tasan babu me saurarenta sai Abba wajensa taje
sanye cikin Leshi taci takalmi da jaka,tayi kyau matuka,Abba Yana Ganinta yasan
matsala ce wajenta ya nufa kar ta kunyata shi a cikin mutane,tana zuwa ba gaisuwa
ba komai Abba lemo nazo a karo mana namu kadan aka bamu ni da kawayena sabo da ni
ba'a kaunata sai ta fashe da kuka.
Abba yace karki bata mana shagali ke wai bakya son zaman lafiya ne,Lemo carton
nawa aka Kai miki sabo da Allah,ai yayi mana kadan ni dama nasan an tsaneni ba a
kaunata,Mohsin ya daina so na yaga wacce ta fini kyau,Abba yace ai kema ba mummuna
bane ki kwantar da hankalinki Hanan bazai wulakantaki ba,karki ga Amarya ta fiku
kyau ki tsorata, duk mun San Amaryar nan tana da kyau amma kar wannan ya dameki,
Abba yace kin San Kubra baza ta Kara miki ba domin an baku da yawa, sabo da
korafinki fa abinci da lemo da ruwa da kaina na ebar miki nasa aka Kai miki,jama'ar
taki nawa ce? ko Kasuwar singa kika tara ne,Hanan tace ba komai to amma wlh sai an
Kara min ko na shiga ciki ayi wacce za ayi dani,kawai sabo da an rainani sai a
dinga nuna min kiri kiri ba a kaunata,Abba yace ko kinje Kubra baza ta Kara miki
ba,cikin gudunmuwarsa yace lemon duk carton daya nawa ne? tace dubu daya da wani
Abu da manya Kuma ya kusa dubu biyu,dubu biyar ya zaro ya mika mata yace gashi jeki
ku siya,kudin ta karbe ta juya ta tafi a Hakan ma korafi take yayi kadan.
Tana zuwa suka hau shewa da kawaye tace ai wallahi sai da aka bani kudina
chass, ai basu gaji da ganin tashin hankali ba wlh baza su huta ba indai nice har
sai an gaji an saki Amaryar.
Ganin Hanan da haka zata kori Amarya.

Spark kuwa ba zuciya akan Naila duk da yaji haushinta jiya amma Allah Allah
yake yazo ya ganta,gidan suka shiga tare da su Rafeeq suka gaida iyaye tare da yi
musu Allah sanya Alkhairi,Naila dai sai pics suke da Mohsin my love yau an zama
ango yau za a kawo Maka Amarya fa,Mohsin Yana dariya yace yau zan karbi sabon
kaya,ta dafa kafadarsa suna ta surutu,Spark ya kalleta yace da nine ai da tuni ta
fara korafi,Mohsin yace kema nan da 3days ai za a kaiki,Naila tace ae mana munyi
anko,tana ganin Spark tace takawarka Lafiya na Naila,anyi fushin anyi fushin zuciya
amma zuciyar ta kasa hakura da ni,ya zaka yi da Jamilu,dariya yayi ba shiri,da ya
shugo yace bazai kulata ba sai ya nuna mata fushi yake da ita amma gashi ta sashi
dariya a banza.

Rafeeq Yana ta kallo dama abinda ya kawo shi kenan,Su Dije suna ganin Rafeeq
sun zaci irin Spark ne,shima Spark din basu San sabo da Naila ya saurare su
ba,Kanin mijin Tantiriya ga kanin mijin Tantiriya, Rafeeq ya wani bata rai wai kar
wata ma ta so shi,ya tsani mace tace tana sonsa shi,Spark yace Kai kawayen mu ne na
kauye wlh karka Raina mana kawaye zan karbe jarin Dana baka,Rafeeq dariya yayi
kadan yace ai Kai yanzu Yaya sai an Maka uzuri,gaishe da su suka yi,Rafeeq ya Kalli
Rayya Dake ta kallonsu tace wannan shi dai Yana da da talatu ne fura,ta nuna
Rafeeq,Spark murmushi ya saki,to naga Yana ta wani yanga kamar mace,Rafeeq ya daure
fuska tam, Spark shi Naila ta dauke Masa hankali tazo tana Masa rada kayi kyau ko
Jin abinda Rayya kewa Rafeeq baya yi.

Rafeeq kuwa Naila ya tambaya yaushe za ayi walimar ne taku? Naila tace 3pm to
5pm sai a wuce Kai amarya,Kamal yace na taba Jin walima mata da Maza a hade,Rafeeq
yace haka tafi dadi.

Bayan sun tafi zuwa karfe uku Rafeeq harda canja Jallabiya da carbi a hannu na
tafiya walima,Spark ya dinga dariya yace ai Kai ka fi Angon ma,idan iskancin Nan
kake sha'awa kayi mana kaima,wannan masifar son mata haka Kuma kace Kai kar wacce
ta soka,Rafeeq yace ai ni Yaya nafi so na kallesu daga nesa sunfi birgeni,3pm
mutane suka cika a Inda aka kama za ayi wa'azi,Misam maye sai da yazo,Rafeeq ya
ganshi yace Misam kana birgeni Kai kawai mata kaji dadinka,baka da control ba
komai,zanci uwarka wlh sa'anka ne ni,kaima idan kana so ka fara mana sai son mata a
baki da Ido, Malama ce ta shugo.

Bata fi Naila ba Yar kyakyawa da ita me Dan haske amma ba can ba,ta Sha hijab
har kasa,idonta tar a kan kowa,Spark baki ya tabe yace wannan ce zata min wa'azi
naji Allah bazan batawa kaina time ba ya mike ya fice, dake a ciki bangaren mata
daban na Maza ma daban.
Matan su Naila duk an Sha Abaya,Maza yawanci da jallabiya,Amarya da Ango ana
zaune a high table anyi shigar larabawa ta Amarya da Ango.

Malama Speaker ta dauka suka hada Ido da Misam ya kashe mata Ido daya tayi sauri
ta dauke kanta dama shi da Rafeeq duk suna gaba gaba,Kuskure Malama ta sake yi na
kallon Misam ya daga mata gira tare da kashe mata Ido,ya radawa Rafeeq na samu Daya
yanzu Malama,Rafeeq yace cikin rada ga Chikar Gayu nan ta shugo,Misam ya basar sai
bayan Dan seconds ya kalleta,Chika ta kalle shi suka hada Ido gwalo ta Masa ta zaro
harshe,dariya yayi ya sake kallonta ta turo kirji gaba tayi girgiza kadan,dariya
yayi a boye yace ta sake yi wai,kanta ta dauke,yace Ina Amaryar Yaya Spark
ne? ,Rafeeq yace gata can mana ai wannan tafi karfin kanka sai dai Spark na sallama
mata,gata can a gaba Inda Chika take.

Malama ce tayi gyaran Murya tare da sallama,sannan ta bude da adduoi,Misam


Allahu Akbar ya furta sai da kowa yaji,Malama Ikhram ta gaji da iskanci su Misam
magana daya tayi sai sunyi Kabbara,sun gama Raina mata hankali,Misam tayiwa magana
siiiiii....siiiiii...hey ..hey....siiiiii,dagowa yayi daga danna wayar da yake suka
hada Ido, fito tayi Masa ta nuna kofa da bakinta wai ya fita,Malama da fito,ko
kulata baiyi ba yaci gaba da danna wayarsa,Mohsin ya radawa Amarya su Spark duk
gasu da Kamala kyawawan gaske gasu da aji sai iskanci fal ciki,Beauty tace naga
alama kuma kamar basu suke yi ba,sai su Fadi Abu su fuske,su Rafeeq basa saurarar
Malama waya suke dannawa amma ko ya tayi magana sai sunyi Kabbara Allahu Akbar.

Malama tana Jan Aya da hadisi tana wa'azinta sosai da sosai,ta Fadi mene ma
auren gaba daya,da sharudan Dake ciki,sannan ta dawo kan yanda ake zaman Aure,ake
tattalin me gida da kula da shi,tazo tana koyawa Amarya yanda ake tarairayar miji
dama duk irin malaman Nan fitsara sukeyi su fake da wa'azi,da Allah Amarya ayi
dinkunan zaman Palo Banda zuwa a dinga manne jiki a gidan miji,ki dinga saukaka
Masa yanda zai cire su cikin sauki,Rafeeq kasa kasa yace wannan fadakarwa ce me
kyau dole na dakko malamar Nan har Abuja ta koyawa su Mima rayuwa,akan kula da yara
da musu tarbiyya,Misam yace maulidi zamu ce zamu hada sai mu dakkota.

Chikar gayu tace wannan gaskiya ne ke Beauty kinji dai a saki a Palo su Sha
iska,Malama tace ashe Kuna ganewa Alhmdllh Alhmdllh,ba ruwanki da kishiya kiyi ta
kanki Amarya,me gida idan ya dawo yasha aiki ya gaji ya kamata ki tayashi cire
kaya,idan ya hada zufa ki tanaji handkerchief dinki me kamshi ki goge masa
gumi,sannan ki tarbe shi da ruwa me Sanyi,ko wani dan zobo haka me Sanyi,Maza suna
son girmamawa,karki zo ki wani tsaya Masa kerere kamar namiji,da karairaya da kissa
cike da girmamawa zaki bashi zobonki me Sanyi,idan ta kama ma ki bashi a baki,Maza
suna son kulawa,Rafeeq yace haka muke Malama musamman ni,Malama ta Harare shi.

Tace shimfidar aure Amarya, Chikar gayu tace a tafawa Malama anzo Inda muke jira
a bata darasi,Naila tace bari na bude kunne Malama nima Amarya ce anzo Inda muka fi
wayo,yeeeee suka saki shewa mata.

Kamal yace ni dai wajen Nan Ina da mutuncina bazan iya zama ba ya tashi ya
fice,Misam yace mu mun zubar da namu wlh sai naji komai,Maza matasa duk sun zuba
kunne,wani har cewa yake Malama mu ba a zo kan Maza ba,tace zanzo ne ku saurareni.
Sanda ta fara bayanin kwanciyar aure Mohsin kunya ce ta lullube shi,Rafeeq yace
ni dai na kamu da son Malama ta San harkar irinta nake so,Misam yace idan ka aureta
zaka Sha dadi ko Mai ta iya,yace musamman idan aka fada bedroom.

Naila kuwa cewa take an gode Malama Allah ya biya da Aljanna Munji mun dauka
zamu yi,Rafeeq yace Kai nima na tashi daga wajen Nan kar a rainani Chikar gayu sai
raini take kawo min,Misam yace dani za a kare sai an rufe addua da Dani,Rafeeq ma
ya tashi ya fece,Maza duk masu Yar kunya arcewa suka yi,Mohsin ya gaji shima badan
dole ba Ina zai zauna sai dai su Tantiriya irin wajen sune,da kyar ya daure aka
gama wa'azin Nan,Misam ana shafa addua yace har an gama gaskiya anyi sauri,Malama
ta gasa Masa harara.
Suna fitowa aka Maida Amarya gidan Ubanta dangi aka mata nasiha sosai Daddy ma
sai da yayi nasiha sosai,yace wlh idan naji watarana ko da wasa kin Masa gori na
bashi gida da jari ko wani Abu ko kika yiwa kishiya gori wallahi Beauty sai Kinga
fushina,na fada miki banza son gori a rayuwa,kayiwa mutum Abu tsakani da Allah mace
tazo tana yiwa miji gori shi yasa Maza basa son zama a gidan mace ko gidan Baban
mace,badan ke na bashi wani Abu ba,karki sake naji gori ko kiyuwa kishiya
gori,Beauty tace to ko kuka itama sabo da sun Saba da gidan yari akan aure Kuma
wanne kuka zasu yi,yayi mata fada Sosai sannan ya sata a mota da kansa,ga Yan uwa
da kawaye,Naila har da ita a Yan Kai amarya suna gefe suna yiwa Amarya rada,Beauty
tace karku damu fa ni kishiya Bata gabana,bana tsoron kishiya, gidan ta tarar sai
na bata littafina dictionary na duk wani iskanci sai ta haddace shi tsaf.

Hanan Kuma daga ita sai Yan uwanta a Palo suna zaune suna jiran Amarya,Hanan
tace a yau ana watsawa zan mata dukan tsiya wallahi,yau sai na daki banza,Kuma ba
uwar da zai iya yi min,ai nasan lagonsa ko me nayi Ina bude Masa Nono sai Kiga yayi
mukus,sabo da haka yau ma haka zanyi baza kuji komai ba,shi da nono ai Inda kisan
asiri.
Dariya suka yi da shewa,suna habaici habaice tun kafin Amarya tazo.

Naila suna mota tace babu fa wata Amana da zamu bawa Hanan,kawai a wuce da ita
part dinta,Chika tace Amanar Beauty ita ta isa ma mu Bata Amana har wani a fara Kai
mata Amarya ita din banza,Beauty tace muna zuwa ku wuce Dani part dina,kar muje ma
ta fada mana magana bazan iya kyaleta ba.
Suna zuwa manya dangi suka yi suka yi a fara Kai Amarya wajen uwargida a bata
Amana,Beauty tace ku nuna min hanyar bangarena akan a bata amanata gwara na Kai
kaina dakin miji wlh bazan yarda a bata Amana ta ba.

Su Naila suka ce muje ke suka tafi da Amarya bangarenta Wanda ya gaji da


haduwa,suna kaita,sai ga Hanan da sauri tace ko ba a kawota wajena ba zata fito ne
a banza na ganta,Dan ba a kawota ba sai me ko ance muku Ina son a bani amanarta,ko
an bani Amana sai na ci,Shewa kawayen Amarya suka saki da guda,Naila tace 2+2 ga
sabo ga tsoho wlh sai dai Yaya ya dauki sabo.

Amarya yau akwai harka a sakarwa Yaya jiki so nake da safe naga bakinsa kamar
gonar auduka a shayar dashi zumar da ai taba Sha ba,wata Maryam itama daga gidan
yari ta fito tace gobe Dan Allah Beauty idan munzo mu iske gadon nan a balle,karki
ji komai ko an balla Daddy a ranar zai iya siyi miki sabo.
Chikar gayu tace an taho da ruwan zafin ne kizo ki Kara gasa wajen Nan,yau akwai
Kwalbewa,Zaiji sabon ihu.

Hanan ba shiri ta bar dakin ta koma bangarenta tana huci,suna ta shewa sun cika
dakin Amarya, Dattijai sai barin dakin suka yi,ba a dade ba aka kwashe Yan kawo
Amarya kaf daga Naila sai Chikar gayu aka bari a gidan suna zuba iya shege.
Spark Naila ya kira yace sun wuce Abuja,tace ko sallama ai shike nan ka
kyauta,to ba yanga kike min ba,ai jibi za a kawoki ne yan mata Ina Nan Ina
jira,Hallare ce bana tsoronta ni,dariya yayi yace hmmmm Allah ya kaimu.

Bangaren Mummy kuwa ta samu Chikar gayu tayi tafiya sai soyayya suke zubawa da
Basiru har an fara maganar aure,Mummy tace ni Alhaji zaka iya dinga zuwa gidana ma
idan munyi auren nayi zamana a gidana,Basiru yace a'a a gidana zaki zauna
bangarenki daban na Suhailat daban,Mummy sai murna take yi tace daga Nan sai mu
wuce kasar waje,yace ba Inda bazan kaiki ba,Mummy farin ciki ya mamayeta.

Masu Sharhi Ina godiya


AsmaBaffa
[12/21/2023, 8:28 PM] AsmaBaffa: PAID GROUP 300

ACCNT NO
0175487861
ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK

YAN NIGER
+22790795939

🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

BOOK 1

76-80

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM

PAGE NAKU NE
Maryam Ta Ado
Aminatu Yusuf Bawale
Rahama Mamuda(mmn Hajiya)
Hafsatbala864
Sailuba Abdullahi Sani
Lubaba

*👭GARKUWAR MATA👭*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya
mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce,
kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan
kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da
surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿
🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da
matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai
dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki
yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane
irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba
su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta
humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza
da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in
abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu
shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano
amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna
bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai
kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi
kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN
K'ARIN BAYANI
08089965176
07084653262

Mummy Yan uwanta ta samu kaf ta tarasu ta sanar musu ta samu mijin aure,babban
mutum ne me Kamala Kuma yana da kudinsa,murna suka tayata, Dan uwansu Namiji a ciki
yace ai dama hakan yafi, zama ba miji ai bai kamace ki ba,shi yasa kike abinda kika
ga dama amma idan kina da miji ya zama security dinki,Mummy tace wlh dake babbane
ma yace turowa kawai zaiyi,Maman Rafeeq tace ai dai Kya bari ayi bincike ko,Mummy
tace Dan Allah Kinga ni bana son bakin ciki,ba ruwanki, da girmana da komai idan
ban sanshi nayi bincike ba waye zai min,ai bazawara irinmu mune kewa kanmu da kanmu
zabi,ni nasan shi ya sanni nasan asalinsa, Dan Jigawa ne Kuma Dan Fulani,Allah ya
tabbatar da Alkhairi suka ce mata tace Ameen,Yaya zai kawo kudi nan da kwana
uku,Allah ya kaimu ya furta.

Shi kuwa Basiru Chikar gayu ya Sanarwa tace Alhmdllh, Basiru Maza ka aureta,
Tantiriya zata tsumaka idan ta tare ka kwashi gara kawai,Basiru yace ai na tanadeta
Yar farar fatar nan tata sai ta koma ja sabo da dakuma da tumurmusa,Chika tace na
gayawa Beauty tace Babanta ana biki zai koma kasar waje bazai dawo ba sai bayan
wata hudu kaga lokacin inshaallah plan ya kare,yace Subhannallahi dadi kashe ni,
Ashe zuwanki Alkhairi ne,karka nuna kana son kudinta shegen wayon son kudi ne da
ita,Bata da kwakwalwa a komai amma akan kudi bata wasa,sannan remember ta taba
kashe mijinta,dole a gidan a saka CCTV a ko Ina ba tare da ta sani ba,sannan ka
kula fa sosai ,wannan karki samu damuwa tsab zan bi da ita,na fita iskanci,Chika
tace to sai na jika.

Spark Yana dawowa daga Kano Mummy tace yazo tana son ganinsa,a daren yaje sabo
da yanda ta fada kamar babban lamari ne.
Yana zuwa a bedroom ya sameta,yace Mummy ina yini ya gidan? Kallonsa tayi tace
lafiya lau my Son,zauna mana,zama yayi tana kallonsa tace Dana na kaina ni wani
kiba naga kana yi,ana ganinka anga nutsatse,Spark yace a tambayi nutsuwa a wajen me
mata,magidanci Irina,Murmushi tayi tace dama aure zanyi na samu miji, Spark ya
furta Allah ya sanya Alkhairi Dan Shila ne ya samu sugar Mummy ko kuwa Dattijo ne
ya hadu da daidai shi? Mummy tace Dan babba ne haka ya mallaki hankalinsa,matansa
biyu nice ta uku,Daya tana kasar waje daya kuma tana nan Abuja a gidansa, Spark
yace ya sunansa ne? Sai ayi miki bincike,karka min bincike bana son iyayi Dan
uwarka Kai aurenka ma ai ji akayi an daura sai ni da ka rainani,Spark yace nine zan
daura ai,Mummy tace sai kace bani da Dan uwa Allah ya kiyaye,aure a bakinka ma zai
dauru kuwa Inda kake mugun kwallon nan,ya sunansa wai? Mummy tace Alhaji Basiru
Kusa,Spark yace Allah ya kiyaye ba Lusari kafawa a katako bace, kaga tashi ka tafi
bana son rashin mutunci, abinci zaki bani bazan baka ba tunda baka da mutunci kaje
ka siya.
Yanzu Mummy akan Basiru Kusa? Ya kusa zama ubanka sai Kuma dole ka dinga
gaisheshi kana Masa biyayya,Spark mikewa yayi ya fice.

Naila suna zaune da Chikar gayu sun Kara gyarawa Amarya part dinta sai kamshi
yake,Chikar gayu tace ai ni yau Kuma gidan su Naila zan koma ranar da za a kaita
zamu wuce Abuja, Beauty tace ga kaza ta nan ta gidan Ango da aka kawo tunda an bawa
Yan kawo Amarya tasu ku dakko tawa ku cinye,Chika ta jawo kaza guda tace Naila sai
munje gida tace yawwa adana ta.
Ba a dade ba Ango ya shugo ya canja wata shaddar ruwan kwai an dosana hula a
gaban goshi Yana bulbula kamshi me dadi,shiga yayi har dakin Amarya, yace Naila
kuje abokina Yana waje zai Maida ku gida,Naila tace to Yaya a bita a sannu,zanci
ubanki wlh wai ni sa'anki ne? Kuje dan Allah an gode,Naila ce ta tsaya duba
mayafinta,Mohsin ya cilla mata mayafin yace dauki kuje,sai da safe,Naila sake
tsayawa tayi tace kamar nayi mantuwa naji a jikina,tsaki ya ja ya mike ya turata
waje ya rufe kofarsa,Chikar gayu tace ya matsu Kai masifa wannan bala'i haka,Maza
akan Bado duk su hana kansu sukuni.

Ango kuwa suna tafiya ko kofar gida basu Kai ba ya rungume Beauty,Yana murna
da,Beauty tace finally....Kara ta saki kadan yanda ya mata wata runguma kamar zai
fasa mata Kashi,sassautawa yayi yace Sallah,muyi sallah muyi bacci,Beauty ta kalle
shi kawai tace to Ina da Alwala ni,tace yawwa tashi tashi Emergency,Hijab ta saka
tabi bayansa suka yi Nafeela tare da adduoi sannan,ya jawo musu Naman a leda suka
ci suka Sha,Beauty ta shiga wanka,shi kuwa da zai taho gidan a lokacin yayi wanka
shi yasa bakinsa kawai ya wanke ya canja kayan bacci,wando gajere ko riga
babu,Beauty fitowa tayi daure da towel a jikinta,Ya bita da kallo kamar maye,kasa
hakura yayi ya mike ya isa Inda take zaune Jikin Mirror ta gama shafa turaruka tana
shafa lipsgloss, ta bayanta ya tsaya tare da dukawa ya rungumeta suna kallon kansu
a mudubi,murmushi suka saki a tare lokaci guda, a hankali ya rada mata bazan iya
jira ba,let's go to bed...muryarsa har rawa take.
Daukanta yayi cak ta rufe idonta tana dariya tare da furta kunyarka nake ji,Dan
Allah a kori kunyar nan bana sonta ni,sosai kunyarsa Beauty take ji,I love you Baby
ya furta tare da kwantar da ita a Saman bed,tayi flat ya zaune a tsakiyar bed din
gefenta,Ido ya kafa mata Yana karewa kyakyawar surarta kallo,hannaye tasa tare da
rufe fuskarta,a hankali jikinsa a mace ya cire hannayen da ta rufe fuskarta da shi.

Kirjinta ya nacewa da kallo ya gansu a cike fam,tun bai gani ba hankalinsa tuni
ya tashi,hannu ya Kai Beauty ta bige Masa hannun tana dariya,Fuska ya bata harda
shagwaba ya furta please,kwanciyarta ta gyara ta kishingida tare da yin pillow da
hannunta daya suna kallon juna cike da nishadi so da kauna,a hankali ya fara shafa
lips dinta,ya gangaro wuyanta zuwa kirjinta a hankali cikin salonsa ya warware
towel din,abinda yafi kauna suka bayyana,ai mikewa yayi zaune tare da furta
congratulations Mohsin, bari nayiwa kaina murna,dariya tayi tace mene? an bani mace
wacce nata na musamman ne ba masu zubewa ba, ai dole na fara taya kaina murna,
Allah na gode Maka

Idanuwansa har wani kankancewa suka yi sabo da jaraba,Beauty Shagwaba tayi tare
da yin yan girgiza,ba shiri Mohsin ya jawota jikinsa Yana rada mata zafafan
kalamai,Mohsin a hankali ya dago habarta da yatsa ya hade bakinsu waje daya ya
fara kissing dinta a nutse,Beauty sai kunya ake ji,Yana yin nisa ta fara biye
masa,tana Maida Masa martani,a hankali ba gaggawa ya fara latsa boobs dinta yanda
yaga dama,Beauty kunyar ce ta gudu taji dadi,dama ai dole irin wannan gyara dole a
kan gwiwa zasu zauna,Muryar Mohsin har rawa take, Da kyar yake iya magana,Hanan ce
ta zauna tana jira a kawo mata Amarya ayi musu Nisa ta samu kofar dukan Beauty sai
shuru,kasa jurewa tayi ta lallaba ta nufi bangaren Beauty tace wlh sai naji Uwar da
suke yi,Beauty taji kamar an bude kofar Palo,shi kuwa gogan ma bai ji ba Allah yasa
sun sa key a kofar bedroom.

Ta sake ji an Murda handle a ranta tace to ko wannan jakar ce ne tazo Jin


kwaf, kirjinta ta sake mikowa Mohsin ta bankaro su tace da karfi
wash....sweet.....ohh...MMohsin ya sake rudewa sai sambatu yake yi iri iri,Yana
biyewa Beauty, babu wacce nake so kamarki,sai yanzu nasan mene soyayya,Hanan tace
kaji munafuki laaaaaaaaa ta Dora hannunta a Kai tace mutumin da nima yace zai iya
bani duniyar Nan Baki daya kunji jama'a.

Baki ya Dora a Saman Boobs dinta Yana Sha Yana wasa da Daya,Beauty tana Jin dadi
tana dan ihunta na dadi,Sai kace maye sai lashe mata jiki yake zuwa cikinta,ya
gangara kasanta Bado,Beauty tace na sallama Maka gwarzon Maza ba wani shege,tana
Jin dadi sosai tana kukan dadi, Hanan ta Dora hannaye a Kai ita duk ba wannan ya
dameta ba tunda tasan dole dama Zasu yi,amma Irin Sambatun da Mohsin yake akan
Amarya yace shi yanzu baya son Jikin kowa sai na Beauty shine ya bata mamaki,Bata
rufe baki ba taji yace ko wacce mace namiji ce a kanki Beauty,Laaaaaaaaa Hanan ta
sake furtawa,ita kanta Beauty Bata zaci da zafi da yawa ba duk da taji mata a gidan
yari suna labarin.

Sai da Mohsin ya murzata son ransa sosai ta Kai karshe ta zauce shima haka, yace
ta Masa sucking,tace wlh yau bazan iya ba na susuce ka bari a second round tunda
zaka yi da asuba ko?.

Mohsin dariya yayi Dan yasan bata sani bane,a hankali ya fara kokarin
shigarta,tace dakata dakata ba haka akeyi ba wannan zafi a hankali ake tafiya,ya
kyaleta domin magana ta gagare shi,da zai fara shiga sai tace a tsaya,gyarata yayi
sosai Yana samanta ya mata rumfa ya yace bari a sake gwadawa tace me dadin zaka min
yace to,Yana farawa zai shiga ta fara a dakata tuni ma Bai ko saurareta ba yayi
ciki da kyar sai da tayi Kara.
Hanan tana Jin karar Beauty tace shike nan fam fam fam innalillahi taji
irinta,wlh Bata isa ba tunda taji irin abata aka Bata sai dai a bawa kowa tasa
yanka da wuka,Kuma wlh sai na mata duka, zata fito ne,ta ja Kwafa ta juya
bangarenta.

Beauty tun tana Dan daurewa tana kukan kadan tace wlh zafi na shiga uku zan
mutu,gashi Mohsin shi yasan mace ya Dan Dade da aure ya kware a fannin ya Saba Dan
jimawa kadan, Beauty kuka take Wiwi zan mutu zafi na rantse da Allah zafi
wash..wash...shike nan kwana na ya kare,uhm...uhm..uhm..jama'a zai kashe ni a
taimakeni jama'a,bige bige take da Shure Shure amma Mohsin ko gazau harda yakushi
duk ya Sha da cizo,ai bai San tana yi ba ma gashi yanda yake wasa da boobs dinta
kamar zai tsinke su sabo da baya hayyacinsa,Sambatu yake na gaske,ko saurarsa bata
yi,sai da ya more Amarya son ransa sannan ya samu nutsuwa,ko da yazo kawowa
kankameta yayi a jikinsa Yana Nishi da gurnani,muryarsa na rawa yace Abba nayi
gado...Beauty tace ya bar muku gado me wahala wlh, bazan sake yarda ba zaka
kasheni,Mohsin baya hankalinsa Nishi dadi kawai yake sai da ya gama tsaf sannan
Kuma ya koma kissing dinta a nutse Yana tsotse mata Baki,Yana shafa Na shanunta,Sai
da ya huta a haka sannan ya fito daga jikinta.

Kwanciya yayi a jikinta kamar shine me jinyar,sai da ya samu nutsuwa sannan yace
saura second round,Beauty ta goge hawayenta tace ka tafi wajen Hanan na bar mata
wlh indai hakane,dariya yayi sosai yace haka kike ce ko? Tace ae dama haka akeyi
abin wannan ai yaki ne guda ni wlh bazan sake yarda ba.
Haba Beautyna da asuba fa kika ce zan sake,na fasa wlh ni dai na fada Maka bana
so,shi yasa Yan uwa mata suke ta fada mana gaskiya amma muka ce ba haka bane.

I'm sorry Mohsin ya furta Yana lallashinta Yana riritata kamar kwai,a haka ya
lallabata suka yi wanka,da kanta tayi gashinta sannan suka fito,Shi ya tayata ta
shirya cikin Yar night gown dinta pink,komai ana gani,Mohsin kasa bacci yayi ya
zama Busy sabo da Nono,abin shi Kam ya tsumashi yake sabo da kyawunsu.
Har bacci ya kwasheta sannan yayi bacci,ita kuwa Hanan tana can maganar Mohsin
kawai take tunawa wai baya son kowa shi sai Amarya,Wato yanzu yasan yayi aure,amma
ban taba sanin namiji munafuki bane sai yau,tayi Kwafa ta kwanta tana gyarawa Amal
dinta kwanciya.

Washe gari da sassafe Spark ya tashi Naila a bacci da kira,cikin Muryar bacci
ta daga, yace ki tashi ki fara shiri gobe ne fa,na fara irga ko wanne second,shine
ka wani tasheni ance an daga sai next week,haba haba waye zai min haka ai kema kin
San baki isa ba, Naila dariya tayi tace nasan me kake wa wannan zumudin,yace wlh ai
zaki ciyu yarinya hmmmm ya ja Kwafa ,kunne ta toshe tace ba ruwana nidai da sassafe
ka ta tashe ni kana wannan barin zance ,kinyi sallah kuwa? Ae nayi mana da
asuba,alright kije ki yiwa Amarya da Ango girki kin San wannan KwarKwar din ba
abinda zata dafa musu gashi jiya an Sha aiki,Naila tace ai da wuri ya kore mu
Jiya,wai Yaya Ni zai kora akan Amarya,wai kuje an gode,Spark yace Uhmmm Kaji mazan
fama,kaji Mazan Kwarai,ai kai dama haka zakace ta kashe wayarta ta mike ta fita.

Kitchen ta shiga kuwa ta hadawa su Mohsin breakfast,Abba ne ya shugo yace wannan


soye soyen fa? tace na Amarya ne,yace to Ina na Hanan? Abba itafa ya dace tayi musu
amma nasan baza tayi ba shi yasa nayi musu,Abba yace ko Dan yarku Amal ai itama a
bata nata,duk kishin da take yi son Dan uwanku ne ya jawo, da tayi wannan haukar
ne? sai ayi mata uzuri tukun sai komai ya lafa.

Naila ta Kara soya wani ta zuba na Hanan itama,tana gamawa tayi wanka ta
shirya,Umma tace Ina zuwa? Gidan Yaya,ajiye a bawa Hidaya su kai,me zai kaiki
gidansu babba dake,Hidaya ce ta dauka tare da Aslam suka tafi can zasu Kai musu,sun
tafi amma sai ga Ango yayi Sallama a gidan ya Sha wankan wata sabuwar shaddar fil
Yana Shining,Naila ya Gani ta zura Masa Ido tana ta kallonsa sai faman dariya take
yi sai kace sabon kamu,fuska ya Bata ya Sha mur kar ma Taga Yana fara'a tace yayi
wani Abu ne shi yasa yake murna,Naila tace uhmm su Yaya da wuri haka ta tuntsire da
dariya,yace ke kika sani Kuma, ya wuce ciki tare da gaida su Umma,mutanen kauye su
tun jiya sun tafi ba kowa sai Yan gida sai Yan tsirari Wanda za a Kai Naila da su.

Abba ne ya Kalli Mohsin yace Ango kaima Lefen ka hadawa kanka ne haka? Mohsin
yayi dariya kawai,yace to ka tabbatar ka rage Wanda zaka sawa Hanan itama ayi mata
kwalliyarta,Mohsin yace to yasan akan Hanan sai suyi Fada da Abba cewa zaiyi Yana
zaluntarta,karka sake ka cuci Daya tunda kaga zaka iya auren mata biyu wlh baka isa
ba sai ka saukewa kowacce hakkinta,Kai kaga zaka iya sabo da haka dole ka daura
dammara,Umma tace to dadin abin dai Hanan dinma ba ganin mutuncinka take ba,ba
komai kanta tayiwa da ace ka zalunci mutum gwara shi ya zalunceka.

Mohsin da safe kafin ya tafi gida sai da yaje part din Hanan ya dubata amma
taki bude Masa kofa,direct tace baza a bude ba munafukin mata,tana ganin Mohsin ya
fita ta bude kofarta ta fito ta nufi part din Beauty.

A Palo ta samu Beauty da abincin da aka kawo a gefe, tana kwance tana kallon TV
duk da cewa bata Jin dadi sabo da jiya ta Sha wahala,tana ganin Hanan ta shugo ta
mike ta zauna da kyar,Hanan ta kalleta tana Harara ta ja tsaki tare da furta wlh
kice tak na miki dukan tsiya shegiya tsinanniya,Beauty murmushi ta saki tace kin
San iyayenki suna deceiving naki? wallahi babarki ta yaudareki ta cuceki sabo da
baki da tarbiyya,ba a baki training a gida ba,idan zugaki akeyi ya kamata ki gane
gaskiya,ba ruwana dake,bana shiga harkarki,haka kawai kizo ki matsamin daga kawo ni
jiya,Dan Allah ki bari Hallare ta tsirga min.

Ni banji haushinki bama da kikayi saurin aure min miji kika rigani Jin dadinsa
sai kece zaki ji haushina da nazo a ta biyu,ni duk haushinki da nake ji bai wuce
kin aure min mijina da wuri kin rigani ba,Kinga Madam sai dai kiyi hakuri fa dole
mijinki zan aura ya kike wani abu ne, ko wani kike so na aura?,bafa yanda zanyi ato
wallahi sai dai kiyi hakuri domin dole ma na aure shi gashi ma na aure shi,ni da
kika yi sauri kika aurar miji fa kafin nazo har kin haifi yarki.

Idan wai tunaninki zaki iya duka na wlh kinyi karya,na horu da aiki a gidan
yari, Ina da karfi Baki isa kin iya dukana ba sannan ni wlh Baki Kai ma matsayin da
zanyi fada dake ba na fiki ta ko Ina ba yanda zakiyi Dani,duk da Baby ya min Injury
a Bado jiya zan iya zagewa na chasaki,Baki San mu bama gudun abin kunya ba,banki mu
kashe layi ba yau ace an kawo Amarya jiya yau suna fada,na fiki hauka fa.

Bana shiga harkarki, kiyi rayuwarki nayi tawa,wlh bama ki da kunya mijina da zan
aura kinje kinyi sauri kin aure min mijina me waje tazo Kuma har kina da bakin
fada,abeg dalla Respect your self, ahh...ah.

Hanan mamaki ne ya kamata tace ni bance kin aure min miji ba sai ke lallai Baki
da kunya,dama Ina naga kunya ni,na miki kama da me kunya? Nufinki zaki dakeni kije
ki bude Masa wasu tarkacen nononki ya kalla ya kasa magana na karya wannan history
din yanzu wlh,Kina dashi Ina da shi Kalli nawa ma fresh dasu young Booby,Golden
Globes,Mohsin ne ya shugo gidan ya sake komawa bangaren Hanan kofar a bude Bata
Nan,part din Amarya yana taba handle din kofar Beauty tayi shuru ta koma ta
kwanta,Hanan bata dau haske ba ta fara zage zage.
Kin shugowa yayi ya labe a Kofa yana saurare.

Hanan tana bala'i Ko shi Mohsin din wlh nafi karfinsa bai isa ba wlh bare ke
banza a banza,Beauty tace yanzu Hanan ni zaki daka? Ae in dakeki in daki
banza,Hannu Beauty ta tafa da karfi kamar anyi Mari ta fashe da kuka wayyo Allah
kika mareni wayyo zata kashe ni,Mohsin ne ya daina sauraren fadan ya banko kofa an
taba Masa Amarya,Hanan ta tsaya sororo,ya fara bala'i wlh idan wani Abu ya samu
amaryata wlh sai nayi kararki,Ina daga miki kafa bakya gani,Hanan kuka ta saki tace
dama ka tsaneni wallahi gidan ubana zanje shege Dan iska kwarto,Beauty rungumeshi
tayi tana kukan shagwaba tace,kaga mulmula min tuwon duwawukana har da nan ta
dadawa duka,Mohsin yace sorry ya fara pressing din duwawun Beauty har lumshe Ido
yake,Hanan tace Allah Karuwa iyye au ta nan kika bullo ai nima duk Ina da su,sai ki
bari ranar kwananki kema ki bude Masa yanzu lokacina ne cewar Beauty.

Mohsin shi sai lallaba Amarya yake Yana Bata hakuri harda dora kansa a Saman
duwawun Beauty,Hanan tace me zai hana kayi an auro karuwa,Gwalo Beauty ta mata tace
Baby,zo muje na baka fresh milk,Bai kamata a gansu a waje ba Abu me daraja ai daga
ni sai Kai,yaushe zan bude su a tsakar gida kamar akuya,Mohsin ne ya Kalli Hanan
yace wai mene haka ne ki tafi bangarenki mana,wannan wacce irin rayuwa ce,bazan
tafi ba Azo a Jani ta karfi.

Mikewa yayi zai dauketa yayi waje da ita ya rufe kofa,Beauty ta rike shi tace
a'a wlh kwana na ne baza a rungumeta ba,nice da Kai baza ta shaki kamshinka ba,akan
haka gwara kayi second round idan ya so a Kai gawata asibit,taso ta mike ta jawo
shi tana karkada Masa kirji,Hanan ce ta rike masa dayan hannun tace ni kuma sai na
miki bakin ciki,Ta rungume Mohsin tana faman goga Masa kirji,Beauty tace Allah ya
isa kin shiga kwanana...

Mohsin ya fisge ya kwadawa Hanan Mari,ta Dafe kumatunta da sauri yace get
out,bana son dabbanci da jahilci,ka mareni? Yace wa ya kawoki bangarenta,kar Kiga
Ina kyaleki ki dauka Wawa ne ni,so kike ki sa min hawan jini,kishi hauka ne,kina
Abu kamar Jahila tun jiya kike zuwa wajen nan,Hanan tace zaka San ka mareni ba
laifinka bane laifin Nono da Karin duwawu,Beauty tace wlh nawa kindirmo ne naki
tsala,Ina bashi yasan da maiko ke kuwa man ciki ya kare an yade Mai babu,Kuka ta
saki ta fice taje ta tattara kayanta a katuwar akwati tace wlh gidanmu zan tafi,ta
bar Amal ita kadai yarinya tana cewa mum Ina zaki ko kulata bata yi ba,ta biyota da
gudu tana kuka tace wlh idan kika biyoni sai kin ci ubanki Mohsin da kakanninki
Hashimu Dolo da Kubra me idon mage,Yarinyar ta fashe da kuka tana ta birgima a
kasa,Hanan tace sai nayi yaji wlh bazan zauna ba,Amal tana kuka sosai tana cewa
Mummy muna da yaji a kitchen ai,ki dawo zan dakko miki yajin ni na ganshi,nice na
boye yajin, amma Hanan ta ficewarta ko Juyowa,ba gida ta wuce ba sai wajen Abba ta
tafi zata Kai Kara sannan ta wuce gidansu.

Mohsin kukan Amal yaji suka fito tare da Beauty,Beauty ce ta dauketa tace Ina
Mummy ki? Tana shesheka tace ta...ta ..tace...ta .tafi yin yaji,wai yaji zata
yi ..tayi ..yaji.. Kuma muna da yajin a kitchen wlh Daddy na rantse ni na boye shi
sabo da kar mutane su sace mana....taci gaba da kuka,Beauty tace sorry zata dawo fa
anjima,zaki Sha alawa? tace ae,to muje na baki, ki daina kuka Mummy zata
dawo,Mohsin yace kinci abinci? yarinyar tace a'a tace baza ta dafa ba Kuma su Aunty
Hidaya sun kawo ta hanani ci wai an saka asiri idan naci mutuwa zanyi.

Beauty wanka tayi mata,Mohsin yaje can ya kwaso mata kaya kala uku Yan kanti
masu kyau ta sa mata ta bata abincin da su Hidaya suka kawo taci sai ta bingire sai
bacci, Amal tana bacci Mohsin yaje yanda yarinyar take birgeni bata hana Daddy
sukuni saurin baccine da ita.

Beauty suna gama karyawa ta gyara bangarenta duk da tana Jin ciwo haka tayi
komai,shine yayi mata wanke wanke sannan taje ta kwanta ta fara baccin gajiya.

Hanan a rumfar kayan Miya ta samu Abba,da kuka ta karaso,Abba Yana ganin haka
ya buga banchinsa yace kooooootuuuuuu alkali ya Dake sauraren karar da za a shigar
yanzu yanzu sai bayan 25ga watan gobe,ya fito daga rumfar kawai ya shige gida,Yana
zuwa gida yace Aslam jeka rumfar Nan ka zauna, ya koma bedroom dinsa ya kwanta.

Umma ce ta shugo tace baka da lafiya ne? yace gajiya ce kawai,yanzu ka fita kace
gajiya yace to na gaji bazan zauna ba,tace ai shike nan ana Maka gata amma baka
so,ae bana so idan ana so a faranta min a canja min sana'a gaba daya na kusa fara
fitar baya sabo da Basir,nema kuke ku maidani me jego na dinga zama a ruwan zafi,

Hanan kuwa juyawa tayi tace ashe za'ayi yaki,wato shima Uban nasa an
zugasa,shine kotu ma, bari naje gidanmu, Abba kuwa kyale shi Umma tayi ta fita tana
cewa ke Suhailat kuzo ku gyara kayan Nan ku shirya komai gobe za a Kai Naila,Naila
tace na zaci sai jibi,sai kace mahaukatan iyaye wlh gobe za a kaiki inshaallah shi
yasa ma nace Matar Kaka kar ta tafi goggonki sannan kina gani Tani itama ta
bangaren Abba ance ta zauna gasu nan sune suke ta gyara gidan nan,Ga Rayya nan da
Dije Kinga mutum shida kenan,mijin naki yace jirgi, nace a'a sabo da kayanki ya
bamu mota uku da sassafe zaku tafi,sai an fara kaiki wajen Mummy wacce ta Raine shi
sannan Mima na fadawa su Tani komai,Naila rada tayiwa Chikar gayu tace Hallare ta
fara loading......ke ki shirya mu tafi wajen Beauty da yamma.

Da yamma kuwa suka shirya sai gidan Beauty,Lokacin Beauty sunyi sallah sun koma
bacci,Mohsin ya kankameta kamar maye, Sallama suka dinga yi shuru da abinci rana a
hannunsu,Mohsin ne yaji Muryar Naila tana Yaya My love mun dawo Allah kawo mu gari
ya waye rana tayi,Chikar gayu zama tayi a Palo tace Ina Nan zan bude idona naga
tafiyar Beauty ya ta koma,Mohsin ne ya fara fitowa,kana ganinsa kasan bacci
yake,sai da kuka dawo yau ma ai sai ku bari sai gobe,Naila tace akan me zamu bari
sai gobe baza muzo mu duba lafiyar kawar mu ba.

Harararsu yayi tare da komawa ciki,lokacin Beauty ta tashi sanye take cikin
doguwar riga marar nauyi blue and white, ta fito tana Murza Ido,Chika tana ta
kallonta tana waka agwagwa tana wanki kacar kacar Omo ya kare,Beauty tace wlh karya
kike yarinya ni Kinga na canja ne,Mohsin murmushi yayi ya koma bedroom tare da
shigewa toilet zaiyi wanka.

Naila tace uhm jiya Kuma an Sha zumar Yaya na? Beauty tace Kai wai ni yarinya
ce ne Kun dameni ni ai ban San ma haka yayan naki yake da hakuri ba sai jiya,yace
mu huta kawai watarana ayi,dariya suka yi Naila tace wallahi karya ne Ina da
ja,kedai kice ba zafi kawai yanda ake karya ba haka bane,Beauty tace laaaa ai duk
karya ce dadi ake ji,ki fada mana gaskiya Beauty,tace wai tsakaninmu akwai karya
ne,ana kaiki gobe karki ji komai duk karya ce ki sakarwa Spark jiki,Naila tace
Alhmdllh haba ko a Baki aka fadi harkar nan dadi gareta bare a zahiri ayi.
Chika tace zanyi sauri in samu nima in shiga daga ciki..
Abincin suka bude,Beauty tace an gaida kanwata,Naila tace Allah ya kiyaye
wlh,Mohsin ne ya fito zai fita,Beauty ta mike ta tare shi tace abinci baka ci komai
ba zaka fita,yace idan na dawo zanci,no ban yarda ka fita cikinka da yunwa ba,tana
magana da shagwaba tana wasa da wuyan rigarsa,Chikar gayu ce tayiwa Naila rada ahh
Bata ji wuya ba,ba zafi ba zafi Naila,kema karki ji tsoro,Naila tace hehehehe ni
zanji tsoron? ni da nafi Beauty karfin zuciya,Kuma ma shakuwar da muka yi da Spark
ai Mohsin basu yi da Beauty ba,tun muna gidan yari muke kiss har muka yi aure indai
zamu hadu sai mun kwalbe, ke ki kiyaye mu ai mun rage hanya mu tuni, Chika tace bai
taba fa taba miki bado ba,Naila tace kan uba ya taba rannan yaji hawayen Bado
Aradu,Chikar taci dariya tace halina Dake Naila har yanzu dajin Riga bata sake ki
ba Kinga sai fada min kike Beauty taki fada mana ita ita ,Naila tace mu Fulani bamu
iya Karya da boye boye ba, ato ya taba ne, da bai taba ba zan fada ne? Kuma naji
dadi ehe,wayayyu Yan birni a sa kaina gabas a yanka ni sabo da nace mijina ya taba
min Bado ai ba iskanci nayi ba Kuma ba gardi ne ya tabani ba mijinane.

Chikar gayu dariya ta dinga yi,itama Beauty sai da tayi Dariya,Mohsin fita yayi
yace zai dawo yasan fitsarar Naila ne,Beauty tace to anji me miji Spark,Naila tace
wlh Fadi ki Kara jikinsa duk dadi,hannunsa ma dadi ne,bakinsa sweet,kirjinsa
Sweet,Kamar yasan ana zancensa ya kira waya.

Fuska ta shagwabe kamar zata yi kuka tace helloooo...tana kumburo baki tace
Babyyyyyy.....Su Chikar suka kunshe dariyarsu,Spark Kuma wani dadi an ce Masa
Baby,yace tsumina ya tashi Hallare Inda kisan sabon Balaga,Naila ta sheke da
dariya,tace sorry ai gobe ne da wuri za a kawo ni,yace to kiyi kizo Kisha madarar
Nido,tace ya zama dole Mijina uban yayana,daga ni ba Kari ko? Spark yace bance ba
sai naga kamun ludayinki idan kina kula dani to kin Sha,amma idan kika gaza to Nima
ta Yaya Mohsin zanyi na Kara aurena nace kin zama Rass da Kwass,Naila tace over my
death body wlh, ba a isa ba sai na haukace akan Hallare,kasan kuwa Yanda na kafawa
Hallare kahon zuka? Ka kiyaye wlh zamuyi fada akan maganar Kishiya, Spark yace wasa
nake Ina zan iya kin riga kin gama Dani gaba daya, ya Golden globes Dina? Suna nan
sunce a gaishe ka wai hannunka suke so,sai gobe ai zasu sha wasa,Beauty a ranta
tace uhm zaki ci kwal ubanki gobe,zaki gane kurenki,ni kaina yanzu komai dauriya
nakeyi kawai amma ni nasan azabar da naji.

Sai yamma likis suka tafi gida,Mohsin ya dawo ya sake fita daga Amal sai
Beauty,Amarya ta Sha uban wanka kamar zata je Dinner ya shugo ya sameta suna kallon
Cartoon da Amal waccen an mata sabon gyaran gashi tayi kyau sosai,yace Amal wa ya
gyara miki gashin ne? tace Aunty ce tayi min tana dariya,yace gobe sai school na
saki a makaranta yau,gobe Monday zaki fara zuwa,ai dama kin isa fara school,Hanan
ce ta fado Palo tazo ta dauke yarta Amal,tace taso daga wajen matsiyaciyar
matarsa,baza a cutar min da yarinya a kashe min ita ba.

Mohsin zai mike Beauty ta rike hannunsa tace zauna yarta ce,ita ta haifeta bar
mata abarta watarana sai ka karbi abarka cikin salama idan Kuma ta dawo shike
nan,kayi hakuri kaji,karka tashi hankalinka Dan Allah,ni wlh ta daina bata min rai,
yanzu na gane bata da hankali gaba daya,ko Jahilci ya mata yawa tunda bata amfani
da iliminta Jahila ce, gemunsa dake kyalli ta shafa tana wasa dashi cike da kissa
tace karka damu zan iya da ita ni.

Thank you my wife ya furta,kansa ta Maida Saman kirjinta tace kwanta,Mohsin ya


zama Dan gata ji ya yake kamar yayi ihun murna dan farin ciki,a hankali kasa kasa
Yana wani narkewa yace karki barni kinji Wifey,please karki juya min baya idan kika
koma irin Hanan Mutuwa zanyi,baza ka mutu ba ta furta kasa kasa tana shafa Masa
tarin sumarsa me Laushi,tace abincin fa? Bana cin tazarce fa ni,tace ai yanzu Naila
ta aiko da wani tuwon shinkafa miyar gyada taji kifi Kuma tace kana so,Murmushi
yayi yace kanwata me so na,Yeah Kuna kaunar juna cewar Beauty, ji yake dama kar
Hanan ta dawo gidansa ta isheshi ta gallabe shi.
Ita kuwa Hanan ta dauki yarta Amal ta koma gidansu,uwarta tace karta koma yanzu
sai ana gobe zai dawo dakinta,zasu koma su karbo rubutu da turaren tsubbunsu,sai ta
tsumu da tsubbu tukun.

Yau Mohsin da kyar ya iya hakura ya bar Beauty ta huta,amma duk da haka ta Sha
latsa salo salo da tsotse tsotse.
Washe gari da asuba Spark ya dinga dannawa Naila kira motoci sunzo suna kofar
gida,Naila tace wlh su koma ko Sallar asuba ba ayi ba ace mota tazo, ai cewa akayi
11am,har 11am? Nidai gaskiya ana Wana ni yanda ake so, ana displani inji
bahaushe,Naila tace ka fada musu sai 11am yace ya zanyi ni dai Ina ganin hau,dariya
tayi ya kashe wayar ya kira masu motocin yace su tafi uzurinsu sai 11am Yana cewa
nace zan biya kudin jirgi sunki yarda Kai nidai na shiga uku.

10am sun gama shirinsu na Kai Amarya sai da suka jewa Beauty Sallama,Mohsin ya
dinga yiwa Naila nasiha sosai,taje ta rungume shi tana kyalkyala dariya tace mun
goge da duniya bama kukan munafunci mu irin na amare,ba ruwanmu Hallare zamu karba
tsab,dariya Mohsin yayi, Beauty ta jawota daga jikinsa tace daina taba min miji kin
girma fa,dariya suka yi,Chikar gayu tace saura Kus kus Dan Allah kuyi mu tafi gidan
yari zanje na Kai Invitation yau ranar da zan bawa Azima ta watsawa bangaren Maza
Dana mata Invitation dinki, Beauty bangaren Mata,Maza Kuma za a watsa musu na
Jamilu Naila sabo da su sake cizon yatsa.
Naila Mohsin ta ja gefe ta bashi maganinsa tace Yaya tana sabawa sai ka Dan
dinga zuba kadan a ruwa ko abinci kana ci.

Sai harka ba gajiya ba kawowa da wuri zaka ji dadinsa duk wani style sai
kayi,Inda kaga Yan Bf,Mohsin yace a'a sai kace Jaki,a Ina kika Kalli Bf din ne?
dariya Naila tayi tace ai gwana ce ni a kallo sanda Ina kauye, almajirai ne suke
turowa iri iri,sai muyi musu wayo mu Karba aro mu buya tare da su Rayya mu
ga...katseta yayi Yace Ai yanzu Allah ya shiryeki ko?tace sosai na shiryu Inda kaga
carbi, ,Karba yayi yace thanks Dear,karki sake kallo kinji,tace me zan kalla Kuma
gata mijina kullum in kwana da ita in tashi da ita, in Kalli ta uban wa ni
Tantiriya kowa yaje da Hallarensa billahillazi,ga fara can a gidan.
Mohsin yace kuje Dan Allah,Beauty tace sai tawan Ina sonki ranar gaskiya ko
agaban waye,Naila tace ke dai kici gaba da bawa Yaya Kindirmonsa na tafi ni,suka
fice abinsu .

Suna fitowa Chika taje gidan yari da wuri taga Azima ta bata katin ta
dawo,Lokacin Naila ta canja kaya wani Leshi dankarere blue black yaji hadadden
dinki na musamman kana Ganinta ba sai an fada ba kasan an kashe kudi a jikinta.duk
kayanta har lefe an shirya shi a mota Daya da dattijai biyu,mota Daya Kuma kawayen
Umma su uku ba Hajiya Tagwadas Naila ta hanata zuwa, kar a ganeta yanzu,Mota daya
ta Amarya da kawayenta Dije,Rayya,Chika,gaban mota Dije ce,Baya Rayya,Chikar da
Amarya,motoci ne masu tsada da kyau,tana mota Umma tazo tace Naila kinji fadan da
na miki ko? Naila ta washe baki tace ae.

Abba ne yazo shima yace Naila muna Nan muna aiko miki da addua kinji,kibi mijinki
sau da kafa tace Inshaallah Abba,komai yace kiyi kinji tace angama Abba,yace
danginsa abokansa da Yan uwansa kaf ke da duk Wanda ya shafi mijinki ki mutunta shi
ki girmamashi,sannan karki rowa, Banda rowa a hana dangin Miji abinci ko
abokai,kowa yazo gidanki ki tabbatar yaci ya koshi,kiyi koyi da uwarki Kubra amma
Banda masifarta.

A mazan yanzu ba Wanda zaki Masa masifar Ummanku ki zauna lafiya baki isa ba
komai son da yake miki,aure Kuma karki ce soyayyar nan da kuke yi a waje itace zaku
yi a cikin gida,da banbanci, ayi hakuri da sannan karki ga mijinki Yana da kudi ki
matsawa dukiyarsa lamba ke sai kinci dole na rabaki Naila,ki kula da mijinki ki
tattale shi Kinga dai matan yanzu gasu Nan ko Ina kullum cikin kallon Maza suke
suna kawo musu hari nima nan da kyar na Sha.

Sannan karki yarda ya kiraki shimfida kice a'a ko ki dinga Masa yanga ke gaki me
baiwa,akwai karuwai a waje,Naila Ashawo Kwando kwando gasu nan a Abuja,zaki gansu
bulbul duk kanjamau ce da su,karki bari Naila ya fada neman mata ko ba komai ya
dakko kanjamau Kinga kin cutu,muna kallo zaki rasu,wand bama fata muna miki addua
kinji.

Naila tace yawwa Abba haka nake so,in kinje danginsa ki bude Ido ki nutsu ki
karanci kowa ki iya zama da kowa kinji,Kuje Allah ya tsare Allah ya kaimu
lafiyaaaaa....Abba ya karasa da kuka Alhmdllh Allah ya cika min burina na aurar da
Yata mace lafiya ba cikin shege ba Dan shege,ba Wanda ya tsallaka min ita,ba abin
kunya,ga Mohsin ma Dana guda ya Kara aure, wannan abin murnane da alfahari a
wajena, wai yau ni Hashimu Dolo ne ya aurar da yarsa mace dansa Kuma ya Kara
aureeeee ......sai yayi cikin gida Yana kuka.
Har masu Kai Amarya da driver dariya suke kamar ba gobe.

Waye Spark ne?

Ayi hakuri bacci ne ya daukeni

A dinga sharhi pls

AsmaBaffa
[12/23/2023, 12:08 AM] AsmaBaffa: Paid group 300

Accnt no
0175487861
Asmau Garba Muhammad Gtbank

Yan Niger
+22790795939

🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

BOOK 1

81-85

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM

PAGE NAKU NE
Ummin Saddiq
Aunty Nurse Zaria
Uwar Batoola
*👭GARKUWAR MATA👭*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya
mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce,
kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan
kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da
surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿
🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da
matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai
dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki
yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane
irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba
su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta
humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza
da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in
abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu
shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano
amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna
bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai
kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi
kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN
K'ARIN BAYANI
08089965176
07084653262

Ashraf Ahmad Maleek, kakansu wato Maleek Dan asalin kasar Somalia ne,Matarsa
Zeenatu Yar asalin Nigeria ce Katsina state,Maleek hamshakin me kudi ne tun a
zamanin da,Zeenatu matarsa tun tana karama ta fara bin Maza,Wanda gidansu suna da
rufin asiri baza ace babu ce ta kaita ba.

Daga haka ta fara guduwa Bariki sai a nemeta a rasa, sai sanda taga dama take
dawowa gida,idan ta dawo zata zo da surutu masu tsada da kudi in tayi kwanaki kadan
ta koma,su biyu iyayenta suka Haifa yayarta ita ta gari ce Bata Dade da aure ba
Allah ya mata Rasuwa a ka bar Zeenatu wacce Bata Jin magana ko kadan,sai yawon
karuwanci ta sa a gaba,iyayenta sunyi kuka sun gaji sun mata addua sosai,a yawon
karuwancinta ta hadu da Maleek shima ya leka Bariki ya Maidata dadiron sa har
Soyayya ta kullum tsakanin su, suka tuba daga Bariki suka dawo gida aka daura musu
aure.

Bayan ya aureta ya dauketa zuwa kasar su can Somalia acan Kuma Allah ya bata
ciki ta haifo Danta namiji Uzairu, daga shi Bata sake haifar namiji ba sai mata,ta
Haifo yarta ta biyu Salamatu,Khudrah,Yusra,Lateefa,sai Allah yayi mijinta Maleek ya
saki Zeenatu.
Bayan ya saketa sai ya auri wata matar a can kasar sa ta haifar masa
Surayya,Rafeeqah,daga Nan sai matar tasa ta mutu, ya dawo Nigeria Abuja suka
daidaita aurensu,Zeenatu tace ita baza ta koma kasar Somalia ba,sabo da Yana sonta
ya tattaro yaransa suka dawo Nigeria gaba daya,sai da yaransu suka girma kaf suka
aurar dasu bayan kowanne da karatusa da sana'ar yinsa,duk yaransu sabo da kyawawa
ne babu wacce ta auri talaka a ciki ko wacce me kudi ta aura a garin Abuja.

Salamatu wacce aka fi sani da Mima itace ta fara aure,ta Auri matashin Soja me
ji da kudi Ahmad,Allah ya Bata haihuwa,haihuwarta ta farko Khalid ta Haifa wanda
shima Soja ne babba a yanzu a Lagos yafi zama tare da matarsa da yaransa hudu.
Na biyu ta haifo Nazeer lokacin anyiwa sauran Yan uwanta aure amma a cikinsu mutum
hudu basa haihuwa,taso ta haifi yara mata sabo da ta basu su kyauta su rike amma
Maza take Haifa,gajiya tayi ta hakura tana sake haifar Ashraf wato Spark kyakyawan
gaske ne na karshe, ita kanta tana sonsa amma haka ta hakura ganin Yar uwarta
Surayya ta damu da shi,kullum Ina Danta sabo da Spark kullum sai tazo gidan,kullum
tana siyo Masa abubuwa,Mima tana yaye shi ta kaiwa Surayya har gida tace gashi nan
ta bar mata tsakani da Allah har abada ya zama nata,babu ruwanta Kuma ko shiga
safgarsu baza tayi ba.

Surayya sai murna amma Sam mijinta Alhaji Aliyu baya son rike Dan wani
shi,kawai sai ya tsani Spark,tun Yana yaro har Spark yayi hankali yasan Mijin Mummy
baya kaunarsa,gashi Mummy ta shagwaba shi sabo da haka ma Yana gama secondary ta
dinga koya Masa business iri iri Kuma Allah ya taimake shi din,Makarantar Soja ta
sashi sai da yayi nisa yace bazai iya ba shi,a haka tana lallaba shi ya daure har
ya gama ya fito a Soja sak,ana turashi yaki wata kasar yayi resining dama ba so
yake ba ya bar aiki,dama shi ya gaji Yana so ya dinga tara sumarsa da shanawa duk
babu kullum aiki aiki duk yayi duhu zai lalace yace bazai iya ba,baza a canja Masa
halitta ba haka kawai akan fatararsa ta lalace gwara ya zauna da talauci.

Yo Mummy ta gama shagwaba shi baya Jin magana,gashi da mugun ra'ayi idan ya kafe
a Abu sai dai a kyale shi,ba a Masa dole shi,ya taso ba abinda yake nema ya rasa,
Alhaji Aliyu Kuma baya sonsa tun asali,zagi hantara duk Yana Masa har ma ya daina
jin haushi, Mummy kasar waje ta turashi yayi masters akan business,dama tun Yana
secondary take biya Masa kasar waje tana kaishi, Yana zuwa hutu can ya shakata har
ya girma kullum a tafiye tafiye yake kasa kasa baya rayuwa sosai a kasa Nigeria.

Gashi da Nasibi a rayuwa,tunda suka taso su ba musu fada duk abinda kayi daidai
ne,su kansu su Mummy iyayensu sunyi duniyanci kadan, daga baya suka tuba,basu basu
wata tarbiyyar kirki ba bare su bawa wani.

Spark kullum kudinsa na bunkasa ganin mijin Mummy ya tsane shi sai ya Gina
gidansa katafaren kawai ya koma can,Alhaji Aliyu da kansa yace Spark ya daina
kulashi sabo da bakin ciki yaga yaro ya girma a gabansa yazo ya fishi kudi.
Mummy suna yawan zuwa asibiti akan rashin haihuwa amma sai ace kalau suke
mijinta ne da matsala,sannan baya iya biya mata bukatarta,a haka ta hakura take
zaune da shi,ya Sha gwada nemo aure Mummy ce take ruwa da tsaki ta Hana auren ta
hanyar masifa da tijara .

Tunda taji ance ita kalau take kullum suna yin fada da Aliyu zata Masa gorin
haihuwa tace hakuri take alfarma take Masa,ga shegen son kudi duk family din su
Mummy haka suke su da sunga me arziki to shine nasu,sannan duk kusan kangararru ne
basu da kyawawan halaye na iyaye mata,shi yasa tunda mijinta Taga lallai aure zai
kara da gaske Taga ita bata haihu ba,ta ya za a kawo wata idan ta haihu ita shike
nan baza ta samu gado ba,akan gado taga gwara ta kasheshi.

Tana tunanin ya zatayi idan ta kashe shi ta tsira kar a gane itace sai katsam
Jamilu yazo me magani dabara ta fado mata ta aikata.
Bayan Mima ta bada Spark sai ta sake haifo namiji Misam ta dauke shi data yaye
shi sai ta bawa Dan uwanta Namiji Uzairu lokacin Dansa Daya a duniya tal wato
Kamal, ya dade da aure Kuma ,sai ta Kara Masa da Misam,bayan an bashi Misam sai
Kuma ya Kara aure duka matansa suka dinga haihuwa sai da suka haifar Masa yara
takwas Kamal shine babba shine Kuma mate din Spark,abokin Spark ne tare sukayi
school,amma a kasar waje Kamal shi Engineering ya karanta ya dawo Yana aikinsa Yana
samun kudi,ya Gina gidansa shima sannan Yana da budurwa har an kusa biki ma.

Misam shi matar Uzairu ce bata kaunarsa,idan mijinta baya gidan sai ta dinga
dukan sa tana zagin sa,idan mijinta na gidan ba Wanda take so kamar Misam a gaban
miji,Yaranta sune yara su take wa fada da tarbiyya,Misam ko me zaiyi baza ta yi
Masa fada ba, har ya taso ya girma ya fara yawon dare amma bata taba yi Masa
fada,tana kallo Uzairu Bai sani ba Idan ma taga zai gane sai ta boye ta kare zancen
kar ma ayi Masa fada ya shiryu,har Misam yayi nisa a neman mata sannan Kuma Kamal
ya gaji ya fadawa Abbansa Uzairu,Uzair hankalinsa ya tashi an bashi Amana.

Yaransa kaf gasu Nan a shirye amma na wata an bashi ya lalace a hannunsa sabo da
rashin kula,ya dawo lallai sai Misam ya shiryu Misam yace kayi sake Baba da baka
bibiyar Amanar ka, ka manta matarka azzaluma ce kawai ka barni a hannunta ba
ruwanka da bincika me ake min Ina ta nuna Maka ka gane kaki sai da na lalace, yanzu
bazan daina ba nasan mata nayi nisa,kullum ana bata min rai ba dole na tafi Inda
zanji dadi ba,Ba irin nasihar da bai yiwa Misam ba yaki ji,sai addua ya koma a
dalilin haka ya saki uwar gidansa gaba daya Kuma yaki dawo sa ita har gobe.
Kawaici irin na Mima Bata taba zancen ba tasan Kuma me Misam keyi, tana yi Masa
nasiha ma amma bata taba zancen ba a wajen wasu, ko da kuwa ace danginta ne, tunda
ta bayar ta Bada tsakani da Allah, babu bincike ya zama Danka duk da tana Jin ciwo
tasan ana zaluntar Misam a gidan amma ta hakura.

Bayan Misam duk sauran Yan uwan suna haihuwa su har su Babar Wahida,mace daya
ce Bata haihuwa itama, ita Kuma uba daya suka hada da su Mima, Yan ubanci yasa ta
hanata Dan ita,Ahmad Mijinta shine ya dauki Rafeeq da hannunsa ya bawa Yusra itama
yace ai babu dadi kin bawa Wanda kuke uwa daya uba daya kin Hana waccen Dan Kuna
yan Uba,Mima tace ni wlh banyi niyyar Bada Rafeeq ba duk yarana kyawawan ciki duk
na bayar dasu,yace kika Bada Spark ma wato ita waccen Dake Yar uwarki ce uwa daya
uba daya,me yasa yanzu zumunci ba ayi Dan Allah? ba kara ba komai, kowa Keke da
Keke wlh ni na bata Rafeeq ya dauke Rafeeq ana yaye shi ya bata kyauta.
Duk Wanda suke uwa daya uba daya da Mima sai da suka ji haushi.

Shike nan Mima ta tsaneta sosai sannan tayi mugun sawa Rafeeq Ido,ta takura Masa
har ya girma idan yaje gidan sai ta dinga tambayar shi me da me ake Maka? Kana cin
abinci? Bata dukanka? sabo da haka Rafeeq ya daina zuwa gidan ya tsane su gaba daya
har su Khalid ba ruwansa da kudinsu da kayansu,shi yafi son wacce ta raine shi,
akan a zageta gwara a zage shi,ba Wanda ya isa ya taba Masa wacce ta Raine shi,ita
Kuma Yusra mijinta akwai kudi amma ba wani sonta yake ba,aurenta yayi sabo da
sha'awa tana Masa biyayya iyakar iyawar ta amma baya Gani,ya tsaneta ma sai auri
saki ya iya, Dake shine baya haihuwar, gashi da mugun son kudi Yana da kudi amma
baya ciyar da iyali,kullum gidansa garau garau ake ci a haka ma da taimakon
Rafeeq,Yusra tana Shan wulakancin da namiji tayi tayi ya saketa yaki Kuma Bai fasa
wulakantata ba,duk abinda tayi Dan ta birge shi to fa bata birge shi, shi tsabar
mugunta ma baya so wani ya taimaka Masa a gidansa amma shi zaici me dadi a waje zai
sa suturar da yake so sannan zai hau motar da ya ga dama amma banda iyalinsa,Rafeeq
ganin haka ya fita shirginsa,Spark ne ya dauki nauyin karatun Rafeeq da komai
nasa,da kasar waje zai kaishi yace a'a ya barshi a Nan Nigeria sabo da Mama babu
Mai taimakon ta sai shi, Spark yace ya Fadi sana'ar da zai iya ya bashi jari,yace
ai shi joint za a bude Masa,anci dariya aka bude Masa Kato me kyau da ma'aikata da
komai shike nan ya zama Baban shawarma joint,ga school dinsa Yana zuwa private da
hostel dinsu sabo da tsakanin su da gida akwai nisa shi yasa.

Mummy Kuma tunda Taga Yana samun kudi Yana taimakon Yusrah mamansa wacce ta
Raine shi sai haushi ta sawa kudin Rafeeq Ido,sai ya tara kudinsa a accnt sai tace
lallai sai yazo ya bata kudi,ta dinga ta karbe kudin ta hanashi gaba ta hanashi
baya,ko yaushe a Dora jari Spark yake watarana Kuma Misam Yana bashi,Khalid ya siya
Masa mota amma ya siyar ya Dora jarinsa shike nan suka yi fada da Yan uwa Dan me
zai siyar da mota ya Dora jarin Shawarma,Sai ya daina kulasu du sai yaga dama, ya
fita harkar kayan su, ko an bashi baya karba tunda ana Masa gori a dinga sashi Yana
yin abinda baiga dama ba.

Mima kanta sai Kara ta kaiwa Spark ta Rafeeq ya daina kula su gashi gashi,ya
same shi ya Masa fada shine ya Dan sakko,amma idan ba Spark ba da Misam ba ruwansa
da sauran,shima tarbiyyar tasa da gyara sai dai bai Kai sauran lalacewar ba.

Bayan an bayar da Rafeeq Mima tace ta gama Bada yara a duniya, sai ta haifo
mace Kuma,a da matan taso ta raba sunfi dadin raino da tankwarawa,idan macece Bata
da matsalar Maza sai yanzu Kuma ta haifi Bisma wacce itama tayi aure da yaranta
biyu tana zaune a Uk,sai Badia itama tayi aure da yarta Daya a garin Bauchi,su ma
basu da wata tarbiyyar kowa harkar gabansa yake babu me yiwa wani fada,Wanda kake
shiri da shi to da shi kawai zaka yi zumunci.

Daga Nan Mima ta haifo Waleed,Atif,Arham duk makarantar sojoji sukeyi matasa
dasu,sai Kuma ta haifi mata biyu Anam,Zainab suma duk sun zama Yan mata haka marasa
tarbiyya ne,ga kudi ga sakaki na iyaye sai abinda suka ga dama,karatu Kuma da wuri
ake saka su shi yasa zaka gansu yara amma sunyi Nisa a karatu,Ina kaje boko Ina
zasu boko,Islamiyya a gidan ake musu sai sunga dama suke zuwa ma dake Islamiyya ce
amma boko ko basa so sai sunje.

Mace komai kankantar ta matukar me kudi ya fito to dole aure zasu mata karatu
tayi a gidan mijinta shi yasa su Badia ko secondary basu gama ba aka musu aure a
hannun mazajensu suka yi karatu.
Idan talakane Kuma sai suce yarsu karatu zata yi sabo da baza su bashi ba.
Duk sun lalata family dinsu sun tarwatsa kansu.

Ci gaban labari

Ana Kai Invitation prison Azima me kwana ba wando ta cika Umarni ta raba na
Beauty a gidan tace kowacce tayi addua da fatan Alkhairi tunda ba a samu zuwa ba,
suna ta tayata murna,Zagawa tayi ta katangar bangaren Maza wata a ciki ta dagata
sama ta watsa musu Iv ta ko wacce kusurwa ta bangaren mazan.
Dan Indo ya dawo daga cikin ball yaga IV da yawa ya dauka ya fara karantawa sabo
da IV din gidan yarin daban suka bayar da kudi aka buga musu ba irin na normal
mutane da aka raba bane,ya karanta yaga an saka
Iyalan General Ahmad Maleek
Na farin cikin gayyatar ku
Zuwa wajen daurin auren
Yayansu, Wanda an riga an daura shi tun 12Jul
Naila Hashim (Jamilu)
Da Angonta
Ashraf Ahmad Maleek(Spark)

Ku da baku samu damar halatta ba a tayamu da addua,yanzu haka an Kai Amarya dakin
mijinta idan da rabo ma an samu tuni.

Sabo da takaici Dan Indo ta hannunsa ya yayyaga,ya kurma ihu tare da furta Kai
Yan matan gidan yariiiiii.......kuzo nayi muku cikiiiii.....kun San yanda ake
cikiiiii .....Kafin kace me gidan yari bangaren Maza ya dauka Jamilu yayi aure,kowa
yazo Dan Indo yake nema.

Jamilu da yayi aure ba a kawo mana shi gidan yari ba mun more,Dan Indo yace ba
labari gashi wannan Spark din ubansa ma Soja ne duk iskancina ai bazan kawo matar
wani ba.
Scoler ne ya saki shewa ahayyeeee chass wa ya fada muku barno gabas take? Ai na
fada muku Terror yayi gabas kunyi Yamma wlh na gaba yayi gaba na baya sai labari
billahillazi,Jamilu tana can tana tsotsar madarar Nido,washer yace har milky me
bukunboti ma yanzu ta zuki abarta da tsinken zuka straw .

Malam Sharu kuwa suna Gani suka fara Alhmdllh Alhmdllh wato aihin Allah ya
karbi adduar mu ya shirya Jamilu da Spark,Allah ya Kara dankon kauna da soyayya har
mutuwa,Malam Garzali yace Astagafrillah wato sai naji darshin hassada a raina,
hassada ta darso a kirjina,naji Ina yiwa wannan yaro Spark Hassada da samun Jamilu
Tantiriya naji wannan ni'ima dama kaina ta fada,Allah ya shiryeka Dan uwa cewar
Malam Jilani.

Su Naila suna hanya Spark sai waya yake wa driver Wanda ya dakko Amarya da
kawayenta kayi fa tuki a hankali karka cuceni Mubarak,Wlh ka kashe min Amarya sai
ka mutu kaima, Mubarak Dan gidan yayan su Mima ne Uzairu,sauran biyu Kuma yayyen
Wahida ne,dukkansu cousins din spark ne ba yanda suka iya haka ya tattaro su dakko
Amarya.

Naila kuwa hirarsu kawai suke da su Rayya sai fulatanci suke,Chika kuwa Misam
ta dinga nemowa a social media ta ganshi kuwa a Instagram tayi following dinsa,tana
duba pics dinsa da videos dinsa gasu Nan latest,sai dai tana yawan ganinsa da Yan
mata,ana shigowa garin Abuja Naila ta fara murmushi harda rawa da kafadu anzo..
anzo... Mubarak yace Spark ya samu daidai shi wlh,Naila tace ai dama nace bazan
bacci ba idona kirrrrr sai anzo,Mubarak Yana dariya ya kira Spark a waya yace Ango
munzo muna Abuja amma gidan Mummy zamu fara kaita sun ce,Spark yace to kuje Gani
nan, Mubarak yace Kai Spark harka ta mata me zaka yi Kuma,Yace baka da hankali
Mubarak ance ma Amarya wasa ce ya ja tsaki ya kashe wayar.

Naila ya kira a waya yace Amaryata? Naila ta kama dariya tace nazo ai no more
damuwa,yace yeah mun daina fada ai Kuma,wani wuri suka yi parking,Dattijai mutan
kauye basu San haka ba a rayuwarsu sai yau,Motocin Spark ne guda hudu masu tsadar
gaske sababbi gal suka karaso wajen da su Amarya suke,Mota Daya Kamal ne da Rafeeq
sai wani Abokin Spark shima farook,Daya motar Kuma sojoji ne mutum uku Helux baka
me rufaffen baya tana Shining,Ango Yana cikin farar mota Yar ubansu an mata wata
uwar kwalliyar flowers kana gani kasan ta Amarya ce.

Gaba driver ne shima Soja ne ke tuka shi,kofa driver ya bude Masa ya fito,Ya
Sha wata Gezna kalar adon leshin Naila milk,yau ya sa hula a Saman tarin sumarsa
wacce ta Sha gyara,Sajensa da dan gemu yasha gyara sai sheki yake,Naila tace ga
nawan nan,Chika tace uhmm muna kallon sabon salo yau duk akan Amarya Allah ya bamu
itaku Naila,Rayya tace aradu dama ance duk Wanda yaje gidan yari Bada hakkinsa ba
sai ya daukaka.

Chika tace nima nan na hango tawa Daukakar Rayya,dole sai na auri kanin mijin
yarinyar nan Naila,baza ta sabu ba,ai ko Misam ya shirya ko Rafeeq cikinsu dole
wani ya Kara rage mugun iri idan ba haka ba na tambade,Dije tace ni kuwa Ja'e ma da
zai dawo to ni wlh da na gama tawa Daukakar aradu na Saba da Hallaren Ja'e,duk
kudin mutum,duk kyawun Da namiji ke ko da Larabawa za a tara min a jefa Ja'e
cikinsu to Ja'e zan zaba,Rayya tace yo me za ayi da mutum ba saniya sai motoci.

Spark ne ya tako cikin takunsa na Yan gayu ya bude bayan mota yaga Dije ce ya
Maida ya rufe yace shi yasa naga motar ta min duhu,dayan side din ya zaga ya bude
yace lantarki haba yanzu naga haske,dariya Naila tayi a hankali tace bari nayi
kunya tunda Amarya ce,Mayafinta ta lulluba a kanta fuskarta duk ta rufe sai ta
mayafin kawai take kallon mutum,Hand bag dinta ta dauka sannan ya riko hannunta ta
fito a hankali, Spark Yana tsotsar alawa a bakinsa Naila tace San min abinda kake
ci,ya ma manta shi Yana Shan abu,cirowa yayi da hannu ya sa mata a baki yace haba
in kayi aure shike nan baza a barka kayi kiba ba, komai Kaci sai matar ta ci,mata
ku dai zuciyar ku a mace take kullum a baku,Naila tace Dan Allah karka sa Amarya ta
dinga dariya ana ganinta,Su Goggo ana mota suna ta salati.

Goggo tace yau ni Ramatu naga abinda ya isheni ni 'yasu,rashin kunya kiri
kiri,wallahi Kin Gani Tani hannu ya rike mata,Tani tace yau ni Ina zan iya kallon
wannan fitsara,dole Kakan Naila yaji zancen nan cewar Goggo,Tani ta rafka salati
ganin Spark ya rungume Amarya suna dariya a Jikin mota,mayafinta ya daga ya shigar
da kansa shima,Goggo tace haka duniya ta koma? Shike nan duniya tazo karshe an kusa
tashin kiyama,ke Kinga Dan Allah mun bani Ramatu,ai muna kauye ta nan yajuju da
majiju zasu fara bullowa,Goggo tace na fadawa Naila idan ta fara ganinsu ta bugo
mana waya mu kimtsa,Me tuki dai yana ta dariyar su Goggo,bangaren su Dije ma sai
salati suke suna Jin kunya,Chika kuwa ficewa tayi da su Kamal suna ta daukan Amarya
da Ango pics da video iri iri,sai da suka gama sannan Spark ya sa Amarya a motarsa
ya shiga gefenta suka tafi gidan Mummy.

Mummy ya ta iya Danta ne ya fada mata zasu zo haka ta kira kawaye da wasu Yan
uwan suka je gidanta za a kawo musu Amarya,Mima kuwa duk dangin kusan suna gidanta
itama suna jiran Amarya,suna cewa wannan bikin arna kawai aka yi Amarya ya gama
kwashewa da ita sabo da iskanci yanzu ace za a kawo musu ita,Mima tace mu da muka
gansu akan gado ai magana ta kare Kuma,ni wlh tunda ake haihuwa ban taba ganin yaro
irin Spark ba, kace zaka Masa Baki yace zai afka Maka.

Maman Rafeeq tana ta dariya tace kar ki Masa baki wlh hukuncin Allah ne,Kuma
Dan kin gansu akan gado sai kice yayi wani Abu ba fa lallai bane zafi ya rage
maybe,Mima tace ai kune Yan zamani Kuma ba wasu manya bane Kun San ya matasan yanzu
suke,Maman Rafeeq tace sai addua wlh yaran yanzu,Lateefa tace ai Ubansa ne ya daure
Masa gindi shi yasa ko me yace sai ya hau ya zauna,duk yaran da basa gabansa yafi
kaunar su,da wuri yake musu Abu,ko Rafeeq Dan yaki karba ne amma ya damu,baya son
sana'ar Nan tasa wai Shawarma Joint kiji iskanci,wlh duk kudi ne yasa su yin
haka,basu da matsala ne shi yasa suke wannan iskancin cewar Kawar Mima.
Mima tace yanzu haka Amaryar da dan cikinta a gaba irin dai ta Christian,gata
tsagera idonta kar ni dai na shiga uku banyi dacen suruka ba cewar Mima tana zuba
tagumi.

Har gidan Mummy suka shiga tare da parking,Chikar gayu ita ta shiga motar kayan
Naila sun wuce gidan Amarya ita da me Jan motar.
Spark fitowa yayi ya budewa Naila tare da riketa ya fito da ita,Mummy suna leke
ta window Baki ta tabe tace kuzo kuga duk Yan kauye ne suka kawota amma dai sunga
kawayen Umma duk su Yan birni ne basu da mukusa,Oh ni na shiga uku ya kwaso min
matsafa yaran talauci,dama wata yar film ce Yar gidan masu kudi, Ni tunda tayi
yankan Kaunar ma wlh ban sake Ganinta ba,ita a Yan film din ma ba wata popular bace
domin tunda naji ita ya aura na shiga bincike Ina tambayar kawayena ko sun San wata
Nasiba Yankan kauna ba Wanda ya ganeta,wata tace maybe irin sababbin Nan ne Yan
giggiwa ba Wanda ya sansu sai karya,idan kin kure su baifi a Waka suke fitowa ba,ai
kyau ya bi da wanka,indai wanka ne basu da na biyu,Mummy tace ku gyara gasu Nan
dangin tsiya anzo za aci arziki.

Zama suka yi suka nutsu, Spark cikin mota ya koma ya zauna,Goggo tace tafi a
hankali Naila,cikin kawayen Umma daya sun rike hannunta sai zuba guda suke
ayiririri,Spark yaji guda har kunnensa yace yanzu nasan Amarya ta iso harda Kara
sauke glass yace bari naji da kyau.

Kida gaba daya motocin suka saki gaba daya iri daya wakar yan Nija,Rafeeq Yana
mota harda rawa a zaune,Yana cewa layi yazo kanmu,Mummy su kansu dariya suke tace
wannan yara namu anyi Yan iska, yanzu dan Amarya shine aka sa mana uban kida haka
duk sun hanamu Jin kunne, Dangin Amarya suka shiga da sallama ga katon carpet, a
nan suka zaunar da Amarya tana zuba kamshi,duk sauran mutanen dakin sun yaba da
Amarya amma Banda Mummy ta dai danne ne kawai sabo da Spark kar yazo ya mata
tijara,amma da sai ta jefar da magana,amma duk da haka sai da tace ai da baku
batawa kanku lokaci ba ma ya dauki abarsa ai mun ganta a gidan nasa tuni tasan har
gadon kwanansa.

Goggo tace yo ko ba komai ai tazo ta gaida iyayen Angon nata, ta ganku ku ganta
ai wata girmamawa ce daga wajen Iyayen Amarya Hajiya,Badan yace muzo ba ma baza mu
zo ba, sai mu wuce dakin mijinta kawai,idan badan zamani ba ma waye yake wani Yan
biye biye da Amarya har wajen uwar rainon Ango,wai bama uwar da ta haifi Dan ba,sai
zamani yanzu a fara wani biye biye da Amarya ana samu gantali a hanya,Mummy mukus
suka yi sunji Goggo ta Maida martani,Mummy taji ciwon maganar Goggo wai uwar raino
wato sabo da bata Haifa ba ake mata gori.

Kawar Mummy malamar makaranta ce itama tare suke koyarwa a primary school,tace
please arziki ya kawo mu ba wani abu ba,Amarya ce gata nan yarku ce dai,ba wani abu
ba, a bude taro da Addua,aka yi addua aka shafa Banda Mummy dake danna waya tana
chat da Basiru Kusan ta, wata ce a dangin Ango babbar mace tayiwa Amarya nasiha
sosai,tace Allah ya kade fitina kinji.

Naila ta fara kukan karya tana shesheka,su Goggo duk sun zaci da gaske kukan
take,harda cewa yi hakuri yar nan kowa da haka ta Saba,Tani tace 'ya mace ai 'yar
gidan wani ce, duk haka aka yi mana Naila aure sai hakuri,Goggo tana cewa rabuwa da
iyaye ba wasa ba,Allah sarki sabo da gidane da iyaye,ko Kaka 'yar Nan ta tuna ai
tayi kuka,Mummy ita dariya ma suka bata yarinyar da suka samu kwance a kirjin
mijinta wai yanzu itace take kuka, Mummy tace ai fa Amarya sai da kuka ai,Rayya ce
ta taba Naila tana girgiza kafadarta tace ki daina kuka kinji nima zaki sani kuka
shike nan mun rabu an raba mu,ta rungume Naila ta fara kukan gaske ita,Naila ta
kankame Rayya tana kukan karya,Goggo tace dole kuyi 'ya'yan nan,saurin kuka ne dani
karku sani nima Dan Allah.

Mummy baki ta saki tana mamaki tace a ranta amma yarinyar nan anyi Karuwa kaga
yar iskar yarinya,yau naga Bariki,lallai bariki iyawa ne wlh,Bariki ba sai an nemi
Mazan banza ba,a fili tace to Alhmdllh mun gode Allah ya bada zaman lafiya,sai a
kaita can gidan Mima din,suka yi godiya suka mike tuni matan dangin Ango suka rako
su da Abinci anyi wrapping dinsa a wasu paper masu kyalli na musamman,ruwan roba
da lemuka carton sunfi biyar, Mummy komai sai anyi karya,a bayan mota aka
zuba,Amarya kafin tazo Ango ya bude mata ta shugo, yana cikin mota bai fito ba
kidansu suke Sha kamar zasu tsaga gidan,Rayya ce ta rufewa Amarya murfin tana share
hawayenta na gaske ta shiga mota suka fita sai gidan Mima.

Kidan suka rage sai kadan kadan kowa suke ji a motocinsu,Naila mayafinta ta
janye kadan tace na Sha kukan karya kowa ya daka ta Tantiriya zai kashe kansa
watarana,Spark yace au Kuka kika yi? Naila tace na karya ba sai bani hakuri
akeyi,Rayya mahaukaciya wai kaji ta fara na gaske,Spark yayi dariya yace kin
birgeni keep it up,Naila taji dadi ya yaba a ranta tace ka shiga uku idan muka je
gida tunda kace naci gaba ai yau kwana zanyi Ina kuka sai na Kara birgeka.

Spark yace saura su Mima Kinga kunkan karya yasa kinyi zufa,driver karo
AC,driver ya karo AC yace to shafa wata powder kar aga Amarya da gumi kamar na wani
kwalbe,Naila powder ta sake shafawa sama sama ta gyara sosai harda gyara pink
jambakinta tace yayi? lekawa yayi yace yawwa,Mayafin ya gyara mata yace badan kayan
Nan suna da kyau ba da tuni sun yi dukun dukun a tafiyar motar nan,Naila tace na
gaji ma wlh baka ji kafata ba,Yace wannan karki damu da gajiya Hallare zata sauke
miki ita tsab,Naila tace sai kace wani magani da ake cewa Daga,tafi Daga ai.

Gidan Mima a cike yake da Yan uwa kaf Maza da mata sabo duk ba a San Amaryar
ba,kowa ya baza Ido zaiga Amaryar Spark,za dai muga karyar Spark a Ina ya
kare,Badia kanwarsu wacce itama tun daga Bauchi tazo har Abuja da yaranta kawai Dan
taga matar Spark wacece,dama idan mutum yayi fice a iya shege da tsirfa to kowa
zuba Masa Ido ake aga zabinsa.
Anam tace munzo bikin amma tsabar haushi Bai auri Wahida ba yasa duk muka koma,
ko gidansa bamu je ba bare mu ganta, Munji dai ance Yar aikinsa ce,Yar kauye ce
ma,tab yanzu haka ma mummuna ce,mazan Nan suna ta dariya suna jira su sha kallon
Amaryar Spark,taron na Mata ne amma duk sunki tafiya kamar mayu.
Harda sake kunna fitilun palon,duk ranar da take gari,wani Arham yace tunda naga
ko status Spark baiyi da ita ba nasan bata hadu ba, ai gudu yake kar ayi Masa
dariya,Dan Allah Mima kuce ta yini a Nan mu ganta sosai zuwa yamma sai a kaita
gidansa.

Mima tace ai dama yace anan zasu yini sai yamma za a kaita can,wai ko uban me
ake saka Masa a bed masu aiki basu gama hada gidan ba,Badia tace lallai Yaya duk
tsadar kayan gidansa? Mima tace ke kuwa zai kawo 'yar gold ya bazai canja komai
ba,ai gidan ya koma sabo wlh ya canja komai na gidan,Kuma in Kinga kayan da ya
canja sai kin rantse 'yar shugaban kasa ce zata tare a gidan.

Har kofofi duk an canja ke har su globes bai bari ba,ai naje gidan na Sha kallo,
nan kusa baza ki samu gida me kyau da aka kashewa kudi haka ba,ni mamaki ya bani
ma,mutumin da watarana budurwarsa ta Ghana ta yaudare shi, karshe ya gane kudinsa
ta ci kawai, yazo nan gabana yana cewa Mima I swear na gama love har abada bazan
Kara son wata ba, tana gwada yanda Spark ke magana,wai budurwarsa ta karshe Lilly?
Anam ta tambaya, Mima tace ita fa.

Spark ya Sha wahalar soyayya mata hudu ne suka yaudare shi, Kuma duk da haka
gaskiya Banga wacce yake so irin wannan da ya aura ba,cewar Mima,Yana sonta
sosai,idan ta kirashi jikinsa har rawa yake,amma waccen kuwa wlh ko sun kira sai
yaga dama yake dagawa,kiji Yana musu tsawa,sannan suna yaudararsa idan ya gane zaki
ga ya rabu dasu ba wahala Kuma zai ci gaba da rayuwarsa normal kamar komai bai faru
ba.

Wannan Naila kuwa akanta zai iya haukacewa na tsorata da Spark akan yarinyar
nan,sai yanda tayi da shi,mu da a gabanmu ya fada mana ni da uwarsa Mummy yace ya
zama Sallamamme,sai abinda tace,mu ja girman mu idan ba haka ba ko me tayi mana
bazai iya magana ba,shi yasa ba ruwana da gidansa,badan ma yace muje muga gyaran
gidan ba bazan je ba.
Badia tace to ko dai asiri suka masa kin San 'yan Fulani fa.

Karar motoci suka ji da Uban kida suna zuwa gidan suka saki sautinsu,Mima tace
ai Spark ne yayi aure sai abinda kuka gani Kuma,kannen Spark gaba daya kasa hakuri
suka yi suka fice Compound kallo,Spark yasan sa Ido suka fito yi,dariya yayi kawai
yace wai Dan uwanka ma a zamanin nan bayanka yake so ya Gani,nafi karfin ku yara
bazan fado kasa ba always Spark On top ne,Driver ne ya bude masa kofa ya fito ya
zaga ya budewa Amarya,Su Badia suna ta kallo tace Uhmmm kofar ma sai ya bude mata
sai kace Yar me kudi,Kansa ya zura cikin motar Yana yiwa Naila rada yace,behave
well nasan ke Oga ce,Naila kafa daya ta zuro,Kannen Spark harda leke suka hango
farar kafa ta Sha lalle me kyau,Anam tace to ai ba fara ce me kyau ba,bakake ma
akwai kyawawa wlh sunfi ma fararen kyau wasu,mu a fada mana haske duk danginmu ba
baki,Hannunta Spark ya riko ta fito,Kanta a lullube ,Arham yace ai dole dai a bude
mana fuskar, Spark Goggo ya mikawa Naila yace Amana,zuwa yamma za a dauke ta,Make
shi Goggo tayi tace to fitsararre mu Kuma ayi ya damu? Yana murmushi yace kwana
zakuyi mana kuga Abuja gobe a maidaku a jirgi,Goggo tace Dan nan ni bana son na
shiga jirgi matukar ba Makkah zanje ba,kawai Dan fitina da asarar kudi a iya
Nigeria zamu hau jirgi aradu baza muyi asara ba baza muyi Maka asarar kudi ba,Rayya
tace Goggo wlh sai dai ke a Maida ke a mota sai cutar mu kuke yi da tuni a jirgi
zamu zo mu koma,Yaya Spark a biya mana zamu hau mu,Spark ya tsaya a cikinsu sai
surutunsu suke suna dariya da nishadi.

Yan uwansa duk mamaki ya kamasu mutumin da baya dagawa kowa kafa wai shine tare
da Yan kauye suna wani hira da dariya,Badia tace su Spark an fado,Arham yace ni wlh
ya birgeni na koma fan din Amarya ma,irin wannan nake nema Ido rufe,Kuma ma ai a
kauye akwai Yan birni a birni ma akwai Yan kauye,idan Kuma kunce talakawa ne duk ba
da arziki aka haifi kowa ba sannan babu me mutuwa a binne shi da dukiya,Kuma yanzu
ta tashi daga Yar gidan talaka ta zama matar me kudi.

Ai kai Arham Dabba ne wa yake ta Kai cewar Badia,su Googo Naila ta rike tace muje
ciki,suka tafi ciki a hankali tare da Amarya suna ta guda har cikin palon,Mubarak
ne yace sai ka bamu kyautar mu da ka mana alkawari, Spark yace ai dai Kwa bari na
shiga dakin Amarya gobe na baku cikin nishadi,Suka ce ba damuwa barshi sai goben
maybe ma zaka fi bamu da yawa,yace wai nawa kuka ce ne? 50k muka ce,yace gobe Kuma
ai sai 100k sabo da Ina Ango na sak,suka ce a barshi sai goben,suka juya da mota
suka tafi har Spark din,Rafeeq kuwa Misam yake wa magana yace

Shi yasa na tsani Yan gidanmu wlh Sam basu da hankali,ji wannan sa Ido haka,Misam
yace Kai kake saurarar su ma,wannan Badiar tafi kowa Munafunci sai kace ba yan uwa
ba,Kai Ana dabbancin a gidan Nan wlh yanzu zasu saka baiwar Allah a gaba.
Rafeeq ya furta ai wannan daidai take dasu bana jinta Allah yasa idan suka fada
musu bakar magana su rama.

Suna shiga tafkeken palon sai kamshi da Sanyi kawai ke tashi,kullum gidan da kida
kamar yaran Arna,Palon ma kida suke ji a manyan Speakers sai da suka shiga sannan
aka rage kidan sosai amma yana tashi kasa kasa,Goggo tace bayin Allah a kashe mana
kida addua zamu yi,sai lokacin Anam ta kashe suka zauna da Amarya a Saman Carpet.

Naila Amarya anci gaba da kukan karya kasa kasa ta wani langabar da Kai anyi
kasa da shi tana wasa da zoben hannunta me tsada da Spark ya saka mata a mota,Mima
ma Jin Amarya tana kuka tace a ranta amma yarinyar nan muguwar criminal ce,Addua
aka yi sosai sannan Maman Rafeeq da tafi dama dama a ciki itace ta yiwa Amarya
nasiha,harda cewa Kinga dai shi dan dangi ne ato ki girmama masa yan uwa sannan
kema su girmama ki,ayi hakuri da juna, tunda kika ce kinji kin gani kina so dole
sai ayi hakuri,Mima tace ya zama dole kuwa,Goggo tace shine dai yaji ya gani yace
Yana so Kuma,yo mace ke auren namiji ko namiji ne ke auren mace? Sadaki ya biya
wuri na gugan wuri million guda sadaki sannan aka bashi,Yar masu shanu ce fa Wanda
suka gaji arzikin dabbobi,Mima kirji ta dafe tace what? Serious fa? Million Daya?
Goggo tace ai harda mota sabuwa gal tana can wajen Ubanta yayanta yana boris da
ita a cikin gari, yo a dauki wannan zizar a sadaka ne,kallon wannan kawai yayi ai
sai ya samu nutsuwa.

Kalleta fa baki ga kalarta bane?ai ba matar yara bace,ku godewa Allah ma da muka
baku da wuri ba sai da muka bari ya kwanta a gadon asibiti ba kawo ruwa kawo ciyawa
ana so ya farfado.

Dukkansu kallon kallo suka fara Goggo daga magana daya sai fadar magana take
musu iri iri,Tani tace Kunga mu ku bamu waje sallah zamu yi,Mima tace Anam nuna
musu yanda ake amfani da toilet din basu sani ba na sani,Goggo tace Kalli hakoran
mu dukkan mu hakoran Makkah ne a bakunan mu har Yan matan nan su Rayya duk munje
Makkah kasa me tsarki,har akwai wata toolet da bamu gani ba,ki tambaya kiji ko da
kike zuwa Makkah bakya haduwa da Yan Fulani duk mune ko Ina,wlh babu wani abinda
zaku yi bamu iya siya ba,a Daji kawai muke ne, ba rayuwa muka sa a gaba ba.
Mima tace da Haram ba,Goggo tace wlh yarinya ki kiyayeni ba a wasa da Fulani ba
a kawo mana raini sai na sa a batar dake duk kudinki,mukus suka yi ba wacce ta sake
ko tari sunji tsoro ko su Goggo suna daga cikin criminal basu sani ba,basu San
Goggo barazana tayi musu ba kawai.

Tani tace a kawo muku kayan arziki irin wannan iyayenta su yarda da danku suna
son Yar su amma suka dauka suka bashi ita Amana,mutum me daraja,yaro ya samu
yarinya duniya guda zai samu ya moreta, yayi mata ciki, ta haifa Masa yara amma ku
zauna Kuna fada mana magana,Baku da tsari Kai dan Allah ku canja tsarinku, ku canja
hali, Sam halin ku baiyi ba,baku yi ba,Kun sire min wlh,nononta kadai aka bashi ya
isheshi rayuwa bare a Kai ga lu'u lu'un,duk Yan dakin kunya suka ji Yan matan da
samari suka shiga boye dariyarsu,Maman Rafeeq tace Dan Allah kuyi hakuri haka,Tani
tace Allah to a dinga zaginmu a fakaice, yarinyar nan fa ba nonon jaka gareta ba
bana saniya bane na mutum ne,yau na tabbata bazai bari ta sake ba,Kuma kawai an
baku ita kwasha kwasha shine ake zagin mu,jarababben Dan naku ma da naci, in banda
kwarzaba me zaiyi yarinya Kun jawo mana asarar kudi sai mun dinga kawo mata magani
kar ya lalata ta,Lateefa tace to kuyi hakuri ku taso muje kuyi Alwala.

Maman Rafeeq Hannun Amarya ta rike taji Laushi tace a ranta ba abin kayi magana
ba ayi Maka cari,bari na fada a raina laushin nan kamar bata aikin wahala.
Toilet Lateefa ta kaisu cikin wani bedroom hadadde ta shimfida musu Sallaya
manya da yawa sannan ta fito suka bar musu dakin suka koma Palo suka fara gulmar
rashin mutuncin dangin Amarya,Mima tace Kinga Goggo nan kamar zata dake ni.

Anam tace Kuma da sai kuyi shuru, baku kyauta ba wlh ai ko ba komai suci
darajar Spark yanzu sai sunyi ta gulmar a can,Mima tace who cares? suna ta
gulma,Arham su mazan jira kawai suke a bude musu Amarya su ganta,Mima tace wannan
naci da yawa yake wai gidan Spark din ne Baku sani ba,ba sai kuje ku ganta ba a
can,wannan fa taron mata ne,Kun samu a gaba,amma sabo da basa Jin maganar iyayensu
kin tashi suka yi,funfurus suka yi a wajen sun zauna a kujeru wasu kuma a kasa.

Su Goggo Sallah suka kasaru ta azahar,Naila ma tayi harda wanke fuska da sabulu
tana idar da Sallah ta fara shafa powder tana gyarawa,tayi Yar make up dinta sama
sama tayi kyau sosai ta sake shafa turaruka har Jikin kayanta da mayafin sannan
Goggo tace ni wai ya naga idon ba alamar anyi kuka ne? Naila tace na rantse kuka na
dinga yi na gaske fa,Abbana na tuna ta sake kebe baki,Goggo tace to ya isa kinyi
kukanki,tace yanzu karki sake rufe fuska kyale shegu su ganki ai ba mummuna
bace,kawar Umma tace yawwa ta Dora mayafin a kanta ta bar fuskar a waje, suna zaune
sai ga Anam ta shugo musu da abinci ta ajiye,ta fice da sauri tace na ganta wallahi
ta hadu,Badia tace tayi dariya Kinga hakoranta? Anam tace a'a,to rufe mana baki
yanzu haka karyayyen hakori gareta,Badia ma ta dauki wani abincin ta shigar musu da
shi Dan ta ga Amarya,taci sa'a Naila na magana ta ganta taga hakora masu kyau
reras,sai ta fito tace na tabbatar ba karya.

Mima tace ahh Dan fa kyakyawa fa kyakyawa ce gaskiya, magana ta Allah tana da
kyau wlh ko ita zata yi kanta baza ta yi haka ba amma fa ba kyan hali bata da
kunya,Anam tace bari na sake Kai ruwan nan na ganta again,ta dauka kenan Arham ya
kwace wai shi zai Kai,Mima tace je kice su fito Palo zasu fi sakewa,amma ni kar su
bata mana dakin yara su fito ato.
Amma kin San masifarsu kice su fito zasu fi sake wa.

Anam ta shiga tace Amaryar mu ku fito Palo wai zaku fi sakewa,suka mike,kawar
Umma a ciki tace wlh su Goggo Kun kwato mana yanci sosai,gashi sai lallaba mu akeyi
ana Jin tsoron mu,Goggo tace ai ba a bari yanzu Kai ya kulle, ke kyaleni nan zuwa
na Makkah sau takwas, a waye nake karrr ba me daga min Kai,wacce shinkafa ce banci
a Makkah ba,wanne tayal (tiles)ne ban gani ba,su Tani wlh duk sun je yafi sau
uku,haka su Rayya duk an biya musu sun je,shi kanshi Hashimu Baban Naila tun Yana
saurayi mahaifinsa ya biya Masa yaje har sau biyu,Umman Naila kanta zuwanta biyu
Makkah.

Kawai mutum idan talaka ne sai a manta da yaje Makkah, Alhajin ma baza a dinga
fada Masa ba ko Hajiya,me kudi kuwa ko bai je Makkah ba kila ma Amurka yake tafiya
duk Shekara,ana tafiya Makkah Ibada shi idan ya hau jirgin Amurka zai ware amma sai
kiji ana Alhaji ya dawo ne,Anam tana jinsu tana dariya,Tani tace ai talaka shi
kullum sai an nuna Masa bakin ciki a rayuwa, Alhajin ma ko Hajiya bakin ciki ake
Masa sabo da bai iya Jin kida ba,bai iya saka damammen kaya ba Yana fitsara yana
badala,bai waye ba ake ganin talaka,me kudi ko jahili ne to wayayye ne ai ya waye.

Palo suka dawo Goggo ta Kalli su Arham tace Kai Ina abincin mu na uwar rainon
Ango? ni na shige su Maza sun tarar mana a Kai,duk Dan nono na da yayi saura sun
kalle min shi,dariya suka yi ba shiri har matan,ke Naila Dan ubanki ki dinga saka
hijab Kinga kallon da suke miki ko Ango Bai miki irinsa ba,ni dai Ina ganin bala'i
da masifa a gidan nan,zasu cinye Amaryar da Ido,kannen miji ne ku ba kyau
wlh,kallon ya fita daga na musulunci,wlh duk sai kunci ubanku idan baku bar palon
nan ba,Mikewa suka yi sabo da masifar Goggo badan sun gaji da kallon Amarya ba suka
fice, Arham ne ya kawo musu abincinsu na gidan Mummy saura kadan ya taka Goggo bai
kula ba,Goggo ta durma masa dundu,ya sunkuya Yana ajiye kayan,tace dan ubanka karya
ni zaka yi,tunda muka zo dama naga kana daga min gira Karuwa ce ni? da aure na da
komai,Arham Kara ya saki Yana Sosa bayansa ya fice Yana hararar Goggo.

Goggo tace wai a cikin ku wace uwar Angon ne? aka nuna mata Mima,tace shi yasa
take ta uban takama,Naila kuwa su Goggo suka yi suka yi taci abinci taki ci,sun
rasa dalili,Badia tace idan kunya kike ji ki koma bedroom kici,Naila kamar doluwa
wai ita a dole amarya me kunya, tace a'a yace kar naci sai an kaini can gidan,Goggo
ta tsaya da cin abincin tace Dan ubanki kashe kanki zakiyi? tun safe Baki ci komai
ba sai kinje gidansa,Naila a hankali ta furta ai munyi alkawari da shi ne, ni
bazan karya ba,Duk na dakin dariya suka yi,Anam tace tab lallai namiji zaki biyewa?
ai kuwa zai kaiki ya baro,wlh wayo zai miki kije ki danni kaza yayi maganinki,Naila
taki ci Kuma da gaske Spark shi yace ko zata ci taci kadan karta cika cinkinta ya
tanadar musu better.

Goggo ce ta sata gaba tace Dan ubanki muje daki mu zaki wa iskanci,ta kora Naila
dakin da suka yi sallah harda rufewa ta mika mata plate din fried rice da hadin
salat,ta kawo mata fruits,da ruwa da lemo,tace wlh idan baki ci ba sai naci ubanki
a dakin nan.

Naila tace ni za a sa na dinga bijirewa mijina tun yanzu,haka tana ci kamar zata
yi kuka sai da taci ta koshi dama yunwa take ji, Goggo ce ta bude Jakarta da wani
tsumi a roba tace shanye ragowar,Naila ta shanye tas tace karki sake ya ga wani
magin mata a wajenki,Naila tace ai na sani Goggo ai kawai ko me yaji daga Allah ne
natural ba Kari, Goggo tace yawwa yar gari,idan Kun Saba ma zaki ga Yana baki kudin
kina siya,wasu mazan Kuma da iyayi sai suce ni bana son shaye shayen Nan,ni kawai
ki zauna yanda Allah yayi ki,kina zama Kuma wangalewa zakiyi shike nan Kun dinga
fada kenan,karshe ko ya fara neman aure ko neman mata,sai an dage da gyara yanzu.

Banda Kuma na hauka ko me aka baki ki Sha ko a dinga baki abubuwa kina matsi
dasu ko wanne hauka karki karba zaki kashe kanki,Naila tace to an gama.
Kwanciyarta tayi a Saman gadon tace bacci nake ji,Goggo tace kiyi abinki domin
da dare baza kiyi ba 'yar nan.

Naila ta kwanta sai bacci kamar gidansu, Spark ne ya kira wayarta Goggo na
dakin ta dauki wayar tace kasa kasa bacci take,Spark yace okay,kar a tashe da wuri
gwara tayi abinta yanzu,Goggo tace ubanka Kai fitsararre,wayar ya kashe yana dariya
shi masifar Goggo dariya take bashi,gata a waye ba ruwanta.

Spark Chika ya sake kira yace an gama hada bed din? tace ae tun dazu ma har Yan
aiki sun gyara ko Ina yanzu kayanta nake shirya mata,yace yawwa Yar Albarka Allah
ya baki yayana ko ta biyu ya Kara Dake,Chika tace amma baka kaunata wlh,ni kaninka
nake so,Yace to Allah yasa,tace Ameen,yace kin bude kayan Lefen Nan? tace ae yace a
kwai Nighty din Nan zaki ganta wata gantalalliya pink,kin ganeta? Chika tace ban
gane ta ba,yace wata tsirarar riga haka,wata zaki ganta tafi ko wacce watsewa da
tambadewa? Chika tana ta dariya tace na ganta yace to ki ajiyeta a Saman bed ba
ruwanki da ita.

Chika ta ninke ta tare da ajiyeta a Saman bed daga Dan kasan pillow kadan ta
fada Masa Inda ta ajiye, har su towel duk sababbi aka saka guda biyu biyu komai
sabo aka canja,Spark Yana ta waya da Chika yana sata tana shirya kayan da suka dace
ba sai an nema ba,Yini tayi tana aikin,abinci sai dai taga an kawo mata take away
lafiyayyen da kayan Sha.
Tana gamawa ta dawo aikin Naila itama wannan ba sai sunyi waya ba ta san
komai,tana gamawa yamma tayi likis, sallah kawai ke tsaida ta da cin abinci,sai da
gidan Nan ya koma neat ko Ina an gyara shi Kal Kal,ta hau turare gidan da kayan
kamshi, ko Ina lungu da sako,har makwafta sai da aka raba musu kamshin.

Naila tana ta bacci lokacin dangi ma duk sun tafi sai Yan gida sunce ai a
hankali zasu je gidan Amarya ganin gida.
Goggo ce ta tashi Naila tace taje tayi wanka,Naila tace nayi a can ni a kaini
haka na gaji muje can ni yayi min wankan da kansa,Goggo Baki bude take kallon Naila
tace zaki tashi ko kuwa,Ga kayan da zaki sa kin San komai da kanki kika zaba ma wai
ni wacce irin fitsara ce ne wannan? Kya fada min wanka da miji.

Naila tashi tayi taje tayi wanka,suka sake wani hada mata na turare tayi ta fito
ta shirya,Cikin Material Dan kasar India tayi kyau dinkin riga da Skert ne,sosai
tayi kyau,Kawayen Umma ne Suka tayata shiryawa sannan suka fito kaita suma duk
sunyi wanka sun canja kaya,Maman Rafeeq,Lateefa,sai Badia sune suka rakasu domin
Ango shi baya African time har ya turo motoci aka kwashe su zuwa gidan.

Chika tayi wanka itama ta canja kaya tana jiransu,suna zuwa duk wata addua sai
da suka tsaya aka yi sannan suka shiga ciki a Palo sai da suka yi suna ta kallon
gida suna guda,ko Masu kudi suka Kalli gidan sai sun Kara bare talakawa da mutan
kauye,za a saka Naila a dakinta tace can ne Goggo waccen ne dakinsa.

Dan Allah ku dinga sharhi


Idan ba a sharhi bama iya typing..

Masu Sharhi Ina matukar godiya.

AsmaBaffa
[12/28/2023, 3:04 AM] AsmaBaffa: PAID GROUP 300

ACCNT NO
0175487861

YAN NIGER
+22790795939

🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

BOOK1

86-90

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM

Page naki ne
MOM SAFWAN
*MISKI 4in1 Hamil musk*🌹 munkawo original miski daga *Egypt* miskin da indai kinyi
amfani dashi zakiji dadi sosai domin kuwa sekinyi godiya hajiya💃💃 👍 yana dauke:
1.*Musk oil* Ana sakashi acikin gaba sannan zaki iya ringa shafawa a pant dinki
lokaci zuwa lokaci ba lallai sai bayan gama al'ada inda hali za'a iya ringa sawa
Koda yaushe yana maganin infection yana gyara gaban mace sosai 🙈ko yaushe gurin
yakasance cikin kamshi 😇 kamshin sa yana zama sosai bayaga haka sunnah ne amfani da
miski
2.*Musk cream* Ana shafawa ajiki gaba daya musamman irinsu cinyoyi, kasan mara
yana sa jikin mace koyaushe yakasance cikin kamshi kuma yana gyara fata, yasa tayi
laushi
3.*Musk soap* sabulun tsarki na Musk; wannan sabulun miski ne ana tsarki dashi
yanada kyau sosai👍👍 yana kashe infection sannan yana wanke duk wani datti dake
gaban mace da karni musamman bayan gama period 🙈
4. *musk powder* Ita wannan powder din ba normal powder bace tana da sinadarai masu
kyau acikin ta🤭 tana magance warin jiki, warin kashi sannan duk gurin da ake sa
turare zaki iya ringa shafawa ita a ko ina ana iya shafawa har fuska in kinso zaki
iya sawa ko ina dai ajiki zaki iya ringa shafawa💃😇

Gefedaya munasaida ingantattun magungunanmata nasokoto munamaraba damasu siyandaya


kosari numbermu itace 09039320715 pls inbasiyazakiyiba hajiya karmubatawa juna
lokaci

Goggo ce tace ku kaita dakin data nuna yanzu haka sunyi tsarin su da Mijinta
mayatacce, har dakin suka shigar da Naila,suna kallon gida komai na gidan Golden
and milk ne har kitchen da kayan ciki,Goggo tace jar Uba zaki Sha aikin gyara Naila
komai me haske aka saka,Chika tace ai iya girki kawai zata dinga yi da gyara
bedroom dinta da nasa akwai masu aiki ana biyansu,zasu dinga zuwa kullum 8am to 5pm
mata su biyu, Dakin Ango Kuma White and Golden ne,bedroom din Naila ma itace ta
zabi kalarta da take so light pink and white,Sauran Rooms Kuma color din da suka
dace da palon ya zuba musu,palon Sama shi Kuma brown and Golden ne nasa tsarin,masu
aikin ya dakko na musamman aka tsara Masa gidan yanda yake son abinsa.

Goggo tace Kai jama'a gidan yayi gida ku tashi mu ganewa idonmu kallo,Naila
harda cewa Kai Allah da Iko yake Tantiriya a wannan gida,ba zagin da gulmar da ba a
yi min ba,ai Yar iska ce bla bla bla,to ko karuwanci nakeyi haka zai ganni aure
ni,ai mutum rabonka baya wuce shi,ko mace a gidan karuwai take sai Kiga tayi dace,
shi yasa ba son zagin mutum kana aibata shi, Ni indai haka gidan yari yake to Allah
Kara Masa albarka,.

Goggo tace ke dai bari kar Kiga gulmar Hashimu da akeyi ana Masa dariya tun yana
yaro yau gashi Allah ya yarda, yaran Hashimu sai arziki suke yi ana ta Masa dariya
ana kiransa da Dolo,Tani tace ai yafi Kubra hankali wlh ke ba Kubra ba kadai ba, da
yawa yafi mutane ganewa ne ba a yi sabo da yana da shirme watarana amma Hashimu ba
dolo Allah ya halitta ba,mutane dai kawai akwai su da son yiwa Allah shishigi a
cikin lamarinsa,abin gulma da yi da mutum yanzu bashi da yawa, yanzu Gulma ce ke
cinye ayyukan mutane na kwarai,kullum cikin hirar mutane ake,makwafta na gulma a
junansu,Yan uwa na gulmar Dan uwa,ko Ina munafunci yayi yawa.

Baka ba mutum ci da Sha ka zauna kana gulmarsa,Kuma idan ance rashin aikin yi
ne ai masu aikin ma yi suke,suna wajen sana'a suna gulmar mutane,Hashimu kuwa ba a
gulmar wani da shi,ai Hashimu ko shugaban kasa kike zagi bazai goya miki baya
ba,idan kika ce Abatcha yayi sata, haka zaki ji yace kin tabbatar? Zaki sheda a
gaban Allah,idan kika ce a mulkin buhari anci wuya haka yake cewa ni ban ji ba,
lafiya Lau nayi rayuwa ta a shekarar ma nafi samun kudi,idan kika ce Kai Obasanjo
ya cuci kasar Nan,yace a'a ai baki fahimce shi bane, shi ya kawo mana wayar
Cellular, shine ya wayar da yan Nigeria, shi akan Obasanjo ya waye,gashi ana ta
social media kowa ya waye sai tambada iri iri, Goodluck Abba yace mugunta aka hada
Masa aka dinga kashe mutane sai da aka sauke shi ta karfi,Allah yasa ma ya
musulunta kowa ya huta da gulmar da akewa Goodluck.

Naila dariya tayi tace ai Abba yace shi ba ruwansa Yana Jin dadinsa a kasar nan
tunda shi aka yo shi musulmi to ko iya haka ya gode,ba abinda zai dame shi,gashi da
yaransa suna Masa komai me zai dame shi Allah sarki Abbanmu.

Goggo kallon gidan suka fita ko Ina lungu da sako suna furta hodi amma anyi
asarar dukiya a nan,sai dare kusan 9pm sannan aka tattara su tare da Maida su gidan
Mima,ba wulakanci suna Jin tsoron Goggo salin alin aka basu dakunan kwana da
abinci,Goggo tace Kai ku kawo min yaji girkin ku salab ba gishiri,Tani tace ba a sa
gishiri sai shegen Maggi har tsakar Kai,a bamu yaji mu dangwala da kazar ta fi
shiga,haka aka basu yaji,Goggo tace Sanyi nake ji a gidan Nan,tiles zai kashe mu da
Sanyi, a kawo shayi ruwan bunu banda Madara,na saba a Makkah kullum sai na
Sha,Larabawa sun koya min mummunar al'ada,Me aiki aka sa ta kawo shayi ko wanne
dakin suka sha abinsu,Mima tace jaraba sun sauka a gidana Kuma sai addua.
Badia tace ni Goggon Nan anya bata da bindiga a jikinta kuwa, Goggo kwanciya
suka yi bayan sunci sun sha suna Hira,Tani tace Naila zata kwashi kashinta a
hannu,Ina tausaya mata wlh,Goggo tace ai duk soyayya ta rufe mata Ido ta zaci ba
komai,shi yasa ai na zugata nace ba zafi kar ta damu kanta, babu komai dankon kauna
yake karawa,Tani tayi dariya tace Yar banza harda cewa to, na tabbata gobe ranga
ranga zamu sameta,Allah yasa muje tayi kuka ni Kuma lokacin zan ci Ubanta dai dai
gwargwado, ai rashin kunyar data nuna mana sai na wanke ta tasss,Allah ya kaimu
gobe.

Naila kuwa su Goggo suna tafiya ta mikawa Chika hannu suka tafa,Chika tace saura
ni Daya nima tafiya zanyi,Naila tace ki bari Spark ya shugo sai ki tafi zai sa a
kaiki gidanku ke da su Basiru Kusa,Dariya suka yi tace saura bikin Basiru da Uwar
raino,Naila tace abu namu,Chika tace naji kamar motar angon ma ta shugo,Naila tace
shine gashi nan yana kirana a waya, dama yace Ina ganin kiransa to ya shugo gidan
nan, Chika tace to dai karki bada mu,Banda kuka a saki jiki a sha love,Beauty tace
ba zafi duk karya ce,Naila tace ai kin san nima a no wan carry last,to haka nake
son ji,Naila tace Dan lelena fa Spark ah ai dole ma a ajiye tarihi.
Chika tana zugata tace sai tawan suka tafa tace bari na kira Abba na fada Masa
an kaini gidan mijina,dama na fada Masa sanda muka shugo Abuja lafiya nace mun
sauka lafiya,Umma wayarta bata shiga,Chika tace kina son Abban Nan naki da
yawa,Naila tace ke ai fada ma bata baki ce, rayuwa ai sai da Abba,5 and 6 muke da
Abbana,duk shirmenka Abba sai ya dauke shi, Abba baya nasiha a kaina ya fara kinji
dai yanda ya dinga fada min gaskiya waye ma yayi min fada irin na Abba ko Umma
Albarka wlh,sannan Sanda ta Ina sane da ita a gidan Mummy, Mohsin bai dauki gadonta
ba,sai ranar karshe idan asiri ya tonu zan dakko ta,wannan Sandar me nasibi ce ko
na mutu a binne ni da abata,Chika tace au Walakiri zaki ragewa hanya da Sanda
kenan? Dadin ya dauka ya jibge ki,sai kace ta tsafi Yar iskar Sanda anki mantawa da
ita,tace Dan Allah kije gobe ki dakko min abata, Spark bai san sandar nan ba haba
ai na ma boye Masa sirrina,Chika tace sandar har wani sirri ne da ita wlh bazan
dakko ba.

Abba ta kira a waya,bugu daya ya daga,yace Nailata,na'am Abba,yace to dazu Tani


ta fada min komai gidan Ango sun jefar da maganganu ko? Naila tace a'a Abba kawai
basu fahimta bane kasan Fulani da zuciya,Abba yace hakane, lafiya Lau aka yi komai
a dakin ma fa Mima nayi bacci,kaga da akwai wani Abu ai da bazan hau gadonta
ba,Abba yace hakane to koma sunyi ko basu yi ba karki fadawa kowa,ko mijinki karki
fada Masa dama dole duk Inda aka Kai mace sai tayi hakuri sabo da zata ga canjin
rayuwa ba wacce ta Saba da ita a gidansu ba,zata hadu da masu hali ko tarbiyya ko
al'ada wata iri daban wacce bata Saba Gani ba.

Karki zama Hanan kullum Kai Kara,kiyi hakuri kowa hakuri yake da Inda ya tsinci
kansa,dole zaki ga dabiun wani gidan da naku ba daya bane,Naila tace to,Yace yawwa
yanzu kina Ina? Naila tace gani a kan gado na,to sai da safe, Naila Ummanku tayi
bacci gata Nan Ina mata tausa wai ta gaji, Naila tace to bye ta kashe tana dariya
tace Abba yanzu fa ya gama nasiha kai Abba nidai kar yaje ya Kuma yiwa Umma ciki
wlh,nazo Ina da ciki uwata tana da shi ni wannan abin kunya ni Naila Ina zan Kai
shi,daga tausa Kuma ba sai Kwalbewa ba ni dai Abba zai bada ni wlh.

Naila ta Kalli Chika tace kin San tsoro na yanzu shine kar ace maganin nan da
kika sakawa Spark ya taba shi,sai yau na tuna wlh Kaka yace idan namiji jarababbe
ne baya taba su sosai,idan ya sha zai dinga Jin sha'awarsa normal amma ana yin nisa
da deep romance bazai iya komai ba zata kwanta,shine nake ta tunani ko Spark yana
daga cikin irinsu,wlh abin ya dameni idonta ya ciko da kwalla tace na cuce shi
yanda yake ta zumudi.

Chika tace karki damu ba dai kin taho da maganin matsalar a jakarki ba? Naila
tace ae suna Nan,to idan kika ga ya gaza sai ki bashi ya Sha shike nan amma a boye
zaki saka Masa ya shanye,Naila tace na yarda da maganin kaka babu karya a cikinsa
wlh zai wahala Kiga baiyi tasiri ba,amma ba komai ai akwai maganin matsalar sai dai
Yana da karfi kinga ba taba yi nayi ba kar yayi min warka warka na kusa
mutuwa,Chika tace koma mene laifinki ne haka zaki karbi Hallare a duk yanda tazo.
Kece ai kika cuceni da kika zuba Masa yaci,ya zanyi ai dadin abin ma ance ba wani
zafi,da sauki ko zanji wahala kadan ne.

Spark ne ya shugo ya Sha wanka new Shadda fara ba irin ta dazu ba,sai kamshi
yake kawai,Naila ta Kalli Chika data mike tsaye tace ni waye zai kaini gida? Spark
yace ga Misam can zai Maida ke ai nasan da zamanki Chikar gayu,sannu kin Sha aiki
na miki Alkawari amma bazan fada miki ba sai na cika,amma ki sani za a miki
bajinta,Chika tayi dariya tace na gode,Naila tace ni Kuma Amaryar fa? Yace ai ke
sai dai ki min bajintar.

Chika tace Amarya sai gobe Kuma zanzo,Naila tace ni me zan baki ne? sai kin
nutsu ai zan dawo gobe Chika ta fice da sauri,tana zuwa gaban motar Misam ta shige
tace Ina yini,da kyar ya amsa mata tun daga lokacin bata sake Masa magana ba.

Har ya dauki hanya ga wata Babynsa tana jiransa a Hotel sai waya take buga Masa,
yace mene number din Room din? Yana ta faman tsinka gudu a titi Yana sauri ya tafi
shekewarsa,Chika tana ji yace 44 number din?

Wani kishi ne da taikaci ya lullube Chikar gayu,cikin masifa tace slow down
malam,yace Ina ne gidan naku? tace I said ka Sauke ni a nan wlh,Mamaki ya kamashi
yanda take bala'i da masifa,ba shiri ya gangare yayi parking ta bude mota tana
tsaki tace kwarto,Manemin mata,tirrr da haihuwarka,motar ta balle ta fice ta sake
lekowa ta zuro jikinta gaba daya ciki tare da kwada Masa Jakarta a kansa tace Dan
Iska kwarto,Kansa ya dafe da Sauri kawai sai ya suma,Chika ta zaci wasa yake,tace
Kai tashi dalla kwarto, ta fara jijjiga shi,Taga da gaske ne,ruwa ta dauka na roba
a gaban motar ta fara yayyafa Masa tana girgiza shi cike da damuwa tana hawaye tace
na shiga uku gidan yari zan koma.

A hankali ya farka kansa ya dafe sosai Yana Masa ciwo, Chika tace wayyo
Alhmdllh Dan Allah kayi hakuri,koma sit din chan na kaika Inda zaka je mu rabu
lfy,da kyar ya iya komawa Daya bangaren ta tuka motar da kanta,tace wanne hotel?
Ya fada mata Yana dafe Kai yace kiyi sauri maganina Yana can,Chika taja a tamanin
ba wani kwarewa tayi ba amma giggiwa irin tasu ita da Naila basa tsoro.

Tana driving har hadadden Hotel din da yake da permanent room dinsa a can ko
karuwar tasa ma nata ta kama ba a shigar Masa dakinsa shi baya iskanci a dakin
baccinsa sabo da mutum ne me Ibada,Yana Ibada kawai ya Saba da matan ne ko ya tuba
sai ya koma ruwa.
kamar wani dan giya haka ya fito Yana tangadi,Chika tace wai wannan wacce cuta
ce da shi haka? Bata San Yana yawan yi ba idan ya shiga shock,har kasar waje sun
Sha zuwa ance baida matsalar komai,da yawa suna bada shawara akan yayi aure maybe
ya warke,sai magani ake bashi idan abin ya faru ya Sha kawai,Abu kadan Yana sawa
zuciyarsa ta tsaya shi yasa Yana shiga shock da wuri zai sume,a baya ma kamar zai
wuce lahira da kyar ya farfado.

Fitowa tayi tare da rike hannunsa suka tafi ciki,Key din dakinsa ya Bata,yace
ungo bude,ta karba hannu na rawa ta bude tare da shigar da shi ciki,Saman bed ya
fada ta Kalli gefe taga harda Sallaya da Qur'anin sa,tace Allah ya shiryeka,yace me
kika ce? No ba komai cewa nayi kana da mutunci,yace Ohhh ai haka nake,Chika ta
Harare shi,yace ni kika zaga? tace yaushe? a mota,ta fara murmushin dole tace karya
nake da kaina nake ai Yar iska nace jinane baka yi ba,kika ce min kwarto? gidan wa
na haura? Ko na bi matar wani? Chika tace sorry ban San haka kake ba ai ashe Kai na
gari ne,Sorry amma ai ba kwarto bane sai dai mata su nemi mijin wata,mijin wata dai
ana nemansa amma baka neman matar wani, yace bani maganina wlh da baki janye
maganarki ba sai na aureki na nuna miki Baki da wayo,Chika wani haushin kanta ya
kamata tace Ashe aurena zaiyi ni me yasa na karaya ne gaskiya ni jaka ce,a fili
tace na janye maganata kwarto an fada Dan iska idan Kai ka isa kana ji Kai Kaine ka
aure ni ka gani idan har iyayena zasu yarda da Kai Kai din banza me bin mata
mazinaci Dan Kwalbewa.
Ai naga alama kanki Yana fisga amma zan saitaki wlh sai kin maimaita zagin da
kika min, Chika harda girgiza kirji tana wani fari da murgude murgude na rashin
kunya tace in ka isa kace Jikar Emeka ce ni daga Enugu nake,idan ka isa in bar
kasar nan,mikewa yayi har taji tsoro ko kamata zaiyi sai Taga maganinsa ya dakko da
ruwa ya kora ya koma Saman bed ya kwanta,tace ka ji sauki ka kaini gida,yace ga key
din nan ki tafi da motar gobe na karba,Chika tace idan na tafi da ita wlh sai na
hau tafi sati biyu a hannuna,yace Ina da wata ai sanda kika ga dama ki dawo min da
Abata.

Mikewa tayi ta dauki key din zata tafi taji ya riketa ram,tsoro ne ya kamata
jikinta ya fara bari kamar mazari,dariya ma ta bashi tana cewa Dan Allah karka keta
min haddi na,yace wato ni ga Dan iska,ai yanzu ba a yiwa mace dole da kansu suke
kawo kansu,Amma tunda kike zagina sai na Sha bakinki yau,iya karfinta ta dage zata
kurma ihu ya rufe mata Baki da hannunsa yasa hannu daya ya rike hannayenta ko motsi
ta kasa,Hannunsa ya janye sannan ya saketa yace Kinga Qur'ani na da Sallaya kinci
darajar wannan bana aikin Haram a gaban su,wane mutum cewar Chikar gayu,indai dakin
Nan kika shugo to consider your self Safe,da sauri ta daga Kai ta ja baya ta bude
kofa ta fice da sauri.
Motar ta shiga ta tafi,ya koma ya kwanta sai yaji kamar karta tafi ta
barshi,dama bata tafi ba,kansa yayiwa fada yace to wace ita ne da ka damu,tsaki
yaja ya lullube kansa da bargo,Karuwa har ta gaji da kira tayi bacci,yarinya
Matashiya ta jefa kanta a masifar bin Maza sabo da abin duniya.

Ango kuwa a Jikin kofar ya tsaya tare da saka key sannan ya tsaya a wajen tare
da harde hannaye a kirji Yana kallon Amaryar sa Naila yana murmushi,murmushi ta
saki tana wasa da yatsunta sai kallon zoben nan da ya makala mata take,shi Kuma
lallen nata yake kallo, karasowa yayi gabanta ya ajiye Ledojin da suke
hannunsa,hannayensa yasa masu Laushi ya riko hannayenta tare da mikar da ita
tsaye,ya furta tsaya a nan, ah'ah irin wannan kyau haka, Karahima inji mutan
kauye,Naila tayi dariya tace karka ci min mutunci Karashima suke cewa ana ce mata
Karisma Kapoor wani Karashima,Yace to dai haka naji Rayya tace ai kayi dace Inda ka
san Karahima ce matarka,kinyi kyau seriously, a hankali ya rungumeta sosai a
jikinsa,Kafarta ta Dora a Saman tasa dayar kafar ma ta aza ta Saman Daya kafar,
cikin rada tace to ai banga kayi rawar murna ba,yace dan Allah har kin sa naji na
zama tababbe,sai kace wani dan iska, kamata na fara rawa ai na tabe,Irin marasa
kunyar yara ke rawa su Rafeeq,wannan rawa ya iya ta kuwa sosai ,rawa ai sai mata
kune bakwa tsufa da rawa,Naila tace ni ban iya ba ai sai ta Yan Fulani da kafa daya
da kirji,yace Ina so haka ai,suna magana ya Maida hannayensa Saman bumbum dinta
Yana shafawa yace ga jakin Babangida na ya karu cikin rada a hankali har suka fada
saman bed.
Mayafinta ya janye Yana shafa kwantaccen gashinta Wanda ya Sha gyara,Yana sake
Maida shi baya Yana a Samanta, goshinta ta nuna Masa da yatsanta yayi Mata kiss,ta
nuna Ido shima yayi Masa,sai hanci ta Saman tips na hancin ta yayi Masa,shima tace
to shike nan,yace ai karya kike,bakinta ta rufe da hannu tana dariya tace sai
anjima,yace ai anjiman tayi please, Okay kadan to, lips ya hade da nasa zai lalubi
harshen ta sai ta janye tace Uhm Uhm,sai anjima,hararar wasa ya mata yace Ina ganin
ta kaina,duk dai tsiya yau baza ki kwana haka ba.
Tashi muyi sallah kar anjima ta wuce ace sai gobe,Naila tana dariya tace haba ai
a tsine min,yau ba sai gobe ba zaka angwance,Murmushi yayi a ransa yace bata san
Dawan garin ba.

Naila wanka ta sake shiga kasa hakuri yayi ya tashi yace Allah yasa Bata sa key
ba na Sha kallo kafin anjima tayi,toilet din ya Murda yaji ta sa key,yace ni yanzu
nayi wanka na bazan sake ba,Ina naga nutsuwar wani wanka to sai kace agwagwa,wanka
dai biyu a rana ai ya ishi mutum wlh bazan sake ba,ita tayi ta wankanta,kayi ta
wanka kamar agwagwa,ai da dai kowa yasan wanka biyu nake yi ai yayi,yanzu Kuma
gashi za ayi ta yin na sunna kullum wanka ya karu ya zama sau hudu sau biyar,dole
na Nemo maganin Mura,Ina dan wankana biyu shike nan ta kare yanzu sai biyar,Mura
salamu Alaykum,da asuba kafin in tafi Sallah nayi wani inje inyi sallata cikin
nutsuwa.

Za aga daidaita sahu a masallaci ko liman sai yaga canji,me gida ya iso,liman
ya daina mana yanga a masallaci muma munbi layi,dama na tsani liman din nan kullum
sai yayi wa'azin gwauraye yace bamu da amfani,to yanzu kuwa Ina zuwa zance liman
How far,ba ruwana da shi in yaga dama ya kwana yana wa'azi akan masu kudin da basa
aure.
Dole ma gobe da ni za ayi sallah da asuba ko dan liman,ya sake cewa yanzu nayi
aure ma Ina zan zauna ta rainani Taga bana zuwa Sallar asuba sosai ai kullum muna
sahun gaba a jam'i ai ka girma Spark,ka zama cikakken namiji.

Yace yawwa sex kuwa sau uku zan dinga yi kullum,inyi da asuba,inyi da dare
sannan Ina dawowa daga Office na Dan sauke gajiyata,daga nan.....Naila ce ta bude
toilet ta fito daure towel tace naji kamar kana magana,yace waya nayi,tace okay,sai
kace tsohon maye ya bita da kallo ya ganta mulmul yace Allah ya Kara miki Lafiya
Amarya kinji kiyi ta lafiya karki dinga cuta kullum In dan samu sau haka ya nuna
mata yatsunsa uku,Naila murmushi tayi tace Ameen,Karki shafa mai bana so na tsotsi
chemical,Naila tace to bari nayi Alwala nazo da abata kin ballata,Ya shiga
toilet,Yana shiga yace yanzu nidai nayi wanka wlh amma ai da kunya ita ta sake
wanka ni Kuma taga banyi ba yo ko na karya ne ai nayi.

Ya tube kayansa yace nidai bani da nutsuwa Sallar ma zan iya,haka yace ya na
iya yayi wani wanka Kuma bai dade da wanka ba ya sake sabo Yana cewa nan gaba ai
halin kowa zai fito nidai nasan me tsafta ne ato,bari muyi zaman karyar mu na
farko,yayi wanka da Alwala ya fito,Yana fitowa shima turare kawai ya shafa ya zura
jallabiya ta saka doguwar Yar riga marar nauyi ya jasu sallah,suka yi addua,zo kaga
saurin Jan sura wajen Spark,suratul khausar da suratul Iklass ya ja shima da sauri.

Kanta ya dafa yayi adduoi sannan ta mike yace Zauna a cinye better din Nan
kina saka kayan bacci tawa ta kare Kuma,Naila ta zauna ita abin na Spark har ya
fara Bata tsoro,sai ga Naila an fara yin lakwas,zama tayi sai yanda yace da
ita,Abincin ma haka ya dinga bata,kafin ta cinye na bakinta ya yanko Naman
again,Yana ci shima da sauri,Gani yayi kamar zata yi kuka,kansa ya saita ya fara
janta da wasa yace ya naga kinyi shuru ne,Naila tace Kaine to kake ta abubuwa,yace
to son matata ne ya jawo,ai hutawa zakiyi yarinya ko bakya son madarar Nido din ne?

Naila tace tace ai dai ba zafin ko? Yace haba ni na miki da zafi Allah ya
kiyaye ai me dadin zamuyi,mu ai na musamman ne ko? tace to,yace kin koshi ne? tace
ae,yace to madarar fa Yar garinku Kin ganta ta shanu,Naila ta mika Masa baki ya
dinga bata sai da tace ta sha iya cikinta,mikewa yayi ya miko mata rigar baccin da
yasa aka ware,Sallayar ya ninke ya ajiye,Ya kashe wayoyinsa ,yace Ina wayarki? tace
na kashe na jona charge,yace Alright,kayansa ya cire sai boxers.

Jikin gadon ya danna Labile ya sakko ya lullube ko Ina na bed din amma ana
hangowa sharara da shi,sai kyalkyali yake,wasu Yan dim light suka kunnu a ciki suna
ta canjawa kala kala a ciki,Naila haka ta saka rigar baccinta,sai yayi kamar ma
baya kallonta,Naila ta Kalli kanta tayi kyau Dan kyau amma kominta ana
Gani,kallonsa tayi taga ba ita yake kallo ba.

Bed din ne ya birgeta sosai taje tana murmushi tace a ranta a film nake
gani,shigewa tayi ciki sai kamshi take ji a ciki,Naila tayi tsalle a ciki da
gwiwoyinta tana Jin dadi.
Spark Yana shigowa tace na manta ban kuskure bakina ba,riketa yayi yace na
shanye ragowar abinda ya makale, zata ce ita a'a taji ya dagata da hannu daya taji
karfin masifa,da sauri ta kalle shi, da mamaki sai dai tayi shuru tayi
murmushi,Nutsuwa yayi sosai ya saita kansa,gaba daya komai ya kwance Masa har ya
fita a hayyacinsa,kwanciya yayi yace kwanta Baby,Kwanciya Naila tayi itama suna
facing juna,Taga har idanuwansa sun ja.

Naila irin Tausayin nan harda komawa jikinsa ya matseta Yana murmushi yace Yar
Aljannar Amarya kenan,taji dadi ta sake langabewa a jikinsa,wayo ya mata yace
kwanta na miki tausa sai kiyi bacci,Naila tace a ranta nufinsa haka zan kwana
lallai maganin Kaka ya kashe min mijina.

Kwanciyarta ta gyara yace baya zaki juya,ta juya tare da Kifa cikinta ta
mimmike hannaye,saitin Kafafunta ya ya dawo ya fara matsa mata yatsu a hankali zuwa
tafin kafa,Naila harda da cewa Uhmmmm...kafafun ya shiga matsawa zuwa gwiwarta ta
baya sai ji tayi Yana lallasheta,ya gangaro wuraren cinyoyinta a nutse,Naila har ta
dauki sako ta kawo wuta,har ya gangaro bumbum dinta ya shiga Murza su yanda yake
so,Naila chaji ya Kai chaji sai Uhmmmm take cewa,Ya tafi zuwa bayanta ya fara
kissing wuyanta,har tambayarta yake ya kika ji? tace sweet Kai fa Kaine ma sugar
sai dai bado Yana ta hawayen kauna,Spark yaji dadi yace wow turn,Naila ta juyo,a
samanta ya kwanta tare da dago bayanta ya zuge zip din rigar ya cireta ya jefar da
ita,rudewa yayi ya sake susucewa Naila taga jikinsa kamar na Dan tauri ana kada
Masa Ganki,baki ta saki ita Bata taba ganinsa haka ba.

Naila tace Allah sarki Dan tuzuru na an dade ana hakuri ta jawo shi ya fado
kanta ta shigar da bakinta cikin nasa,suka fara tsotsiyar su baji ba Gani,Naila da
kanta ta juya ita ga jaruma,ta koma tana goga Masa na Shanun ta a
kirjinsa,haukacewa yayi gaba daya sabo da tasan inda yake yawan cewa ta taba Masa
da Hakan tayi amfani ta hauka Spark ya koma kamar wani soko,ya fara Sambatu,ga
Hallare a tsaye kyam,boobs dinta yake sarrafawa yanda yake so,Yana fara Sha Naila
ta wani turo su,gaba dayansu Nishi suke na sweet,Ya dade Yana jiyar da ita dadi sai
da ya koma down ta wargaje kafa ya fara mata wani irin sucking,Naila ihu ta ke
sosai tace Allah ya tsinewa Wanda yace aure ba dadi,ni indai da wannan ko dukana
ake wlh bazan fito daga gidan miji ba.
Spark sai da yayi dariya,yace dama waye zai sake ki ma ai babu mutu ka
raba,Naila tace ayi ta Kwalbewa banga Laifin Abba ba,Umma kiyi ta haihuwarki,
sarrafata yake kamar ba gobe,ya tsotsi can ya taba can,

Ihun dadi take yi tana sake sakar Masa jiki Wayyo... Zan mutu.....sai da ta Kai
karshe Spark zai fara neman hanya kawai Hallare ta sauke tayi kwanciyarta Kuma shi
ba releasing yayi ba,Naila ce taji cak an tsaya ta kalle shi tace mene,mararsa ya
rike ya bingire a Saman bed din,Yana Nishi ouch zan mutu,Mutuwa zanyi,Naila ta rude
ta mike zaune,ta Kalli Inda ya rike ta Kalli Hallare,tace ke haka za ayi dake? Ashe
baki da mutunci dalla tashi,ki tashi,yatsa ta sa ta dago Hallare ta saki taga tayi
lakwab,tace baki da Amana wlh kin Kuma bani haushi,dunkulewa yayi Yana rike da
mararsa yana Nishi,cikinsa ya kifa yana murmukususu yana furta zan mutu,Naila yar
rigar baccin ta Maida jikinta a gurguje ta dire kasa.
Ta jawo Jakarta ta dubo magungunan ko wanne da Yar takarda a ciki na rubutun
aikin da yake yi gudun mantuwa,a nutse ta duba da sauri ta tabbatar shine sannan ta
zuba yogurt a glass cup Dan kadan ta zuba Dan maganin dama dan mitsil ne, juyawa
tayi sosai cikin sauri tana Jin Spark Yana ta kiranta,Yana ta birgima a Saman bed
din,Naila tace gani nan fa madarar Nido ce take so ta fito Kuma no way, Spark dai
Ina kamar zai mutu Naila ta dawo Saman bed din.

hannunsa ta rike ya kankame hannun nata,a kunne ta rada Masa tace tashi na
baka magani,bazan iya tashi ba ya furta yana hada zufa sabo da wahala,da kyar ta
lallaba ya dago da kansa yana daga kwance ,a haka ta fara bashi maganin Yana
shanyewa sabo da yaji wahala shi indai maganin gargajiya ne baya sha,na baturen ma
da kyar yake sha sai yaji uwar bari, haka ya shanye maganin tas Naila harda zuba
ruwa a cup din wai dan kar ma wani ya makale ta bashi ya shanye.

Kansa ta Maida Saman cinyarta tana shafa bayansa a hankali cikin sigar
lallashi da lallabawa,ko minti talatin ba ayi ba taji yayi luf ya daina kukan ciwo
zai mutu,shuru taji yayi suna haka taji Yana sabon hada zufa duk kuwa da karfin AC
din dake dakin.

Suna a haka taji ya fara mata tabe tabe a jiki,hannunsa ta bige Dake kirjinta
tace baka fa da lafiya,na warke ni ki kyale min hannuna ya furta Yana dariya a
hankali,hannunsa ya Maida Saman Boobs dinta yana latsawa yana murzasu yanda yake
so,a hankali ta sake kawo wuta,a nutse bakinta ta shigar shikin nasa suna ta faman
tsotsar juna,yanzu Kam baya hayyacinsa Sam ya kasa control din kansa bare ya wani
bi Naila a hankali,tasan Kuma maganin ne,komai yanzu a haukace yake mata shi,tun
bai fara komai ba ta fara rokonsa,Dan Allah ka bari haka na gaji,amma baya Jin kira
sarrafata yake yanda yaga dama,Naila taji Abu ya wuce hankalinta ita dai,Boobs
dinta ta rufe da hannayenta biyu tana cewa wai sai ka cire su ne yau gaba daya ka
huta,hannayenta ya cire ya janye ta karfi,muryarsa tana rawa yace please yaci gaba
da abinda yake,Naila yanda yake Saman bed amma sai ya dinga dagata Yana jujjuyata
yanda yaga dama shike bata mamaki,tace karfinka yayi yawa wlh amma dai sunanka
Aliyu ko ka Maida shi Ashraf, har ta bashi dariya amma baya cikin
hankalinsa,kwanciya ya gyara mata tare da komawa Samanta kamar zai cinye mata baki
haka ya yake tsorsar su ya rasa ma ta Ina zai kama,jikinsa rawa yake kamar me ko
magana ya kasa sai Nishi...
Naila tace wai nakuda kake ne ni ban gane ba,ko kulata baiyi ba ya koma down
dinta,Yana shafawa a hankali da hannu, Naila ta fara susucewa ganin haka sai yaci
gaba tana ta kukan dadi,a ransa yaso yasa yatsa ciki amma Yana sawa yasan makomar
kawai gwara yayi me gaba daya tunda ta gama jikewa, wannan kukan dadin da take wani
zuga shi take yi,gyarata yayi sosai yanda zaiji dadin harka,Naila ta Dan saki jiki
ya fara goga mata Hallare a wajen tana Jin dadinta kawai ya nufi ciki,ya fara
kokarin shiga ko a hankali baibi ba bazai iya ba, baya hankalinsa ta karfi ya shigi
Naila Yana adduar saduwa da iyali itama da kyar ya tuna.

Naila babu Dan wani kokari ma sai kuka,ta bare baki duk dauriyar tata,sai ihu
take Innalillahi wa Innailayhirrajun,Allahumma ajirni fi
musi......ahhhhhhh....Kaka,Abba......Abbaaaaa.....Yaya Mohsin....zai kashe ni,da
azaba tayi azaba Naila kasa magana tayi da ihu sai faman rusar kuka take yi Kamar
wacce ake yankawa babu sauti Kuma, Spark ya kasa control kawai dadinsa yake ji shi
marar misaltuwa,Bai taba zaton haka ake ji ba,ga maganin da Naila ta bashi shine ya
karawa abin armashi, yaji ya kasa kawowa da wuri,gashi Yana Jin kukan Naila amma
dadin kukan ma yake ji,yasan a kansa bata taba ba amma ya kasa yayi controlling
kansa,sambatunsa kawai yake yi Wanda shi kanshi Bai ma San me yake fada ba,ita
Naila kuka da wahala yasa tana jinsa amma bata ganewa,Kalmomi yake furtawa masu
nauyi a Baki iskancinsa kawai yake fada,sai Kuma yabon Naila da yake ta yi Kamar
wata sarauniya haka yake ta yabon ta Yana bayyana yanda yake sonta matuka.

Sai da ya koma Sunan Naila kawai yake iya kira ko ya furta I love you yafi
dubu,You are so Sweet,sanda ya kwashi dadinsa iya dadi sannan ya samu ya kawo,ai
kuwa Naila taga yanda ake barin madarar Nido, Naila sai da ya dagata sannan ta ja
numfashi,ta jike jikinta da hawaye,amma ta wani bangaren taji dadi sabo da ya warke
ta fita hakkinsa tunda itace ta saka Masa magani.

Kuka yaki karewa Naila sabo da azaba,ko hannunta ta kasa motsawa,Yana gefenta
Yana hutawa ya kasa magana,sai murmushi yake Yana Jin dadi ji yake kamar ya Maida
Naila cikinsa ya huta,Ya kasa magana sai fuskarsu ya hade waje daya,hancinsa Yana
Saman nata hancin Yana murzawa a hankali.

Naila tana jinsa duk haushi take ji,tace wlh ni ka dameni ka kyaleni bana
sonka,tun kafin na zageka ka kama kanka,wlh bani da mutunci karka ganni haka zan
iya zaginka duk girmanka ba ruwana,hannunta ya ruko a hankali ya Maida yatsanta
bakinsa Yana tsotsa yana dariya,yace ni ai da zaki zageni sake yi zanyi Kinga ma
Kari take so,Naila tace ashe zaka mutu kuwa baka samu ba,ta sake fashewa da kuka
tace wlh da nasan hakane wlh bazan yarda a kawo ni ba,dariya ta bawa Spark,jawota
yayi jikinsa ta kwace jikinta tana ihun zafi zafi...ciwona....haske ya kunna ya
Kalli wajen yaga yanda wurin ma ya Baci harda jini amma ba yawa,Yana kallo yasan ya
ji mata ciwo da yawa,tunawa yayi da yanda ya dinga aiki ba ruwansa,I'm sorry Baby
na kasa control ne wayyo haka wajen ya dawo shiiishsh.....ohhh....dole kiji
zafi,bari na miki wanka,karka daga ni Naila ta furta da masifa tace wlh kana taba
ni zanji zafi wlh,haka zaki daure,ni karka taba ni bana so,yace ai ya zama dole ki
Sha ruwan zafi.

Haka ya dauki Naila chak kamar Jaririya tana ta kuka ita zai kasheta,haka yaje
ya hada ruwan me shegen zafi da gishiri,ya sata ciki tana uban ihu kamar me wayyo
Allah na tana kuka amma Spark yace so kike na barki ki ta min kuka a haka,ai dole
ki warke,tana ta kuka bata ma iya magana,a toilet din ya zaunar da ita bayan ya
gama mata azaba da ruwan zafi.

Ganinsa tayi ya dawo da sirinji sabo da wani ruwa a cikin wata kwalaba kamar
wani Likita,yace kin San wannan ruwan? Naila tana kuka ko kulashi Bata yi ba,yace
to na Yan kaciya ne likitoci suke fesa musu a wajen, da wuri suke warkewa tana
kamewa,dama ni kin San Ina da abokai likitoci, sabo da wannan rana suka bani na
tanadi komai,ke kin San yanda na shiryi wannan rana ba abinda baza ki ga na dakko
ba,karki mamaki Chika ce duk ta Adana min abina.

Naila kanta ta dauke kawai tana Jin haushi,sai shesheka take,ruwan ya zuko
sannan ya cire kan allurar ya ajiye gefe,yace bude min cinyar nan,Naila kunya ta
kamata taki budewa,yazo da kansa yace nasan komai fa,sabo da kallon wajen Nan har
tawadar Allah na ganta mene na wani kunya,dariya taso ta kwace mata tace ni bani da
tawadar Allah wlh,Yace to tabon kurajen infection ne kenan,tun yaushe tabon suka
goge zaka min sharri, dariya yayi yace to bude kinji Yar Baby kar na bude ta karfi
kice na Kuma yin famu.

Da kyar sai da ya Sha fama sannan ta bude kafafun ya fesa mata ruwan sosai,sai
da taji zafi amma ba yawa daga Nan Kuma ta rage Jin zafin sosai,yace sai gobe da
safe da rana da dare sai an fesa har 3days kin ganshi a nan na jiye miki idan ma
aki fesa da kanki ba ni zan saka miki da kaina.
Naila da kanta ta Dan iya mikewa tana dafa bango tace kugu na ya karye bazan iya
tafiya ba.

Ke dai raguwa kawai cewar Spark, ya dakkota bayan sun tsarkake jikinsu,gashinta
ya goge mata,harda shafa mata lotion,ana yi ana lashe mata jiki ana tattabe mata
boobs,Naila taga jaraba yau,rigar baccin ma ashe yayyagata yayi a jikinta sabo da
tsabar ya zauce,Naila ta ganta a yagalgale,tace ka yaga min riga wlh sai ka biyani
Ina sonta shine ka yagata,yace oh sorry zan siyo miki wata,ni irin abata nake so
wlh idan baka biyani ba tam.
Zan biya mana ya furta Yana taje mata gashi,ya gama ya kama da ribbon,sannan ya
sa mata pant ya dakko wata rigar sabuwa ta bacci a lefe, ya bata ta saka riga da
wando 3quirt marasa nauyi dasu masu kyau.

Naila tayi tsit kamar ruwa ya cinyeta sai abinda yace, turare ta shafa,bed din
ta kalla sanda ya daga labilen suka koma sama,Ashe towel ya sa a kasanta duk iya
towel dinne ya baci, bata san ma ya sa ba,towel din ya cire ya sa a washing Machine
sannan ya fito ya gyara bed din sosai,ya kwashe tarkacen kayan ciye ciyen zai Kai
kitchen,Naila tace zanci,ya dawo mata dasu gabanta Inda take zaune a kujerar
Mirror, ya zuba mata madarar, ta karba sannan ya tafi ya barta.
Toilet yaje ya gyara ya ciro towel din ya shanya sannan wandonsa ma ya wanke ya
shanya,rigarta da tissue da sauran tarkace ya zuba a Dustbin sannan ya fito shima
ya shafa lotion sai wani farin ciki yake,Yana damunta da surutu,ko kulashi bata
yi,abinta take ci,sai da ya gama shiryawa ya saka wani boxers din kawai yazo shima
Yana Jin muguwar yunwa ya fara cin Naman Yana kora madarar sai da ya koshi,Naila
tana ci tana yatsina a haka ta koshi,ya kwashe ya Maida komai kitchen,Naman a
Fridge ya saka da sauran tarkacen na ci,daukanta ya sake yi tare da wanko mata
hannu sannan suka dawo ya kwantar da ita Saman bed ya kwanta a gefenta.

Yace my love,Naila kanta ta dauke ta juya baya,dariya ta bashi magana ma ta


gagareta,sai hawaye da kuka,ya hau lallashi yace bazan sake ba,Naila tana kuka tace
wlh Hallare Bata kwanta ba ai na gani,Kari take nema na rantse da Allah ba a kaina
ba sai dai ka mutu,sai dai a kashe ni bazan sake yarda ba,to ya zanyi ni ban San
wanne magani kika bani ba,amma Kari nake so,Naila tace ashe zaka mutu kuwa yau,to
ai ba yau nace ba ya furta,Naila tace har gobe ma da jibi da gata da citta da kanwa
da tagargade da gimba bazan taba yarda ba wannan ai yaki ne guda,ni akan wannan
gwara na tafi gidan mu bazan iya zama ba,wannan mugunta taka sai an rubuta ta a
littafi, tarihi ne guda,ban taba ganin mugun mutum irinka ba Spark,ka bani
kunya,ban San haka kake ba,da nasan haka kake ko kulaka bazan yi ba.

Spark makalewa yayi a jikinta ya dabaibayeta kamar maye,shuru tayi sabo da kar
ma yace zaiyi wani Abu,amma duk da haka dukiyar fulaninta sun fada mata yanda ya
dinga wasa dasu Yana cikin shansu ma yayi bacci a haka,Naila tace wai haifarka nayi
ne,ta janye jikinta ya sake janyota Yana bacci,tun tana kokarin hanawa har bacci ya
kwasheta,zazzabi ya rufeta na wahala tana bacci,ta farka tana rawar Sanyi,Zafin
jikinta ne ya farkar da Spark,yaji tana Nishin zazzabi,tashinta yayi yace zazzabi
kike ne? Naila Kai ta daga Masa tana ta faman hawaye, magani ya bata ta Sha ta
kwanta tare da shigewa jikinsa tana Jin dumin jikinsa har ta samu zazzabin ya sauka
tayi bacci.

Washe gari Abba Yana tashi da Naila ya tashi a ransa yace Naila ta tana can
yanzu nasan tasha bandashe da kuli kuli da yaji har da Maggi,Allah sarki Nailata
tana can ita kadai ba Dan uwa a kusa bare na tura a gano min lafiyar ta, ya kira su
Goggo yace lallai anjima suje su gano Masa lafiyar yarsa, Umma tana jinsa dariya
tayi tace ni wlh Ina murna bana so ma Naila ta samu sassauci sabo da bata da kunya
ko kadan,Abba yace ai dama bakya kaunarta ni Ina son abata,Umma tace kana ganin
zumudin da take ai gwara haka.

Mohsin Kuwa Beauty dinsa ya hakura ya barta kwana biyu taji sauki amma ana
biyun nan sai yaki yarda,Beauty duk da zafin da ta Sha haka ta hakura ta bashi kaya
ya ja sabo da tana da kishiya,dama dagiyar mata wasu bata tashi sai suna da
kishiya.
A ranar da safe Kuma Maman Hanan ta rakota gidan miji da kanta.

Sabo da hauka da rubutu ta rakota galon guda ta boye abinta,sai data wanke
fuska da wani rubutun sannan tayi kwalliya suka nufi part din Beauty suna
bugawa,Beauty tana kwance a jikinsa tace waye? Muryar Hanan taji tace shugo mana
Aunty,babu ko tunanin ta tashi a jikinsa ta sake yin Mala Mala a jikinsa,Hanan
kamar ta hadiyi zuciya.
Maman Hanan ta gallawa Beauty Harara tace to rasai rasa kunya sai ki tashi ai
zamu yi magana da me gidan,Mohsin yace ba sai ta tashi ba ku Fadi abinda ya kawo
ku,Hanan ta kalle shi da sauri,tace Uwata ce fa,yace ni uwata ce to? Beauty ce ta
rufe Masa Baki da hannu tace bari na tashi irin kissar Nan bafa tashi zata yi
ba,yace ba Inda zaki,suyi maganar su a Nan,Maman Hanan tace Mohsin dama haka kake?
Yace sai yau kuka sani kenan?

Beauty tana jinsu harda gyara kwanciyarta a jikinsa,Hanan ce ta fara masifa


amma ka cika butulu Mohsin Kuma wallahi yanzu nasan Kai baka San arziki ba,Ashe
baka da mutunci,idan Kai Dan halak ne ka sake ni butulu macuci azzalumi,tun baka da
Sisi nake zaune da Kai wato yanzu ka auro Yar me kudi wannan tsinananniyar wacce ko
nonuwan ma bata da su duk ciko ne,shine ka zauce haka.
Beauty ta Kalli Hanan ta jawo hannayen Mohsin ta Maida Saman Boobs dinta tace
akwai bra? Mohsin yace karki biyewa haukarta ai ta haukace Kuma wannan wa yake ta
ita ni da nasan kan abubuwana,nonuwa subu subu,Maman Hanan salati ta saki tana tafa
hannu tace Mohsin a gaban nawa? yace Laushi gare su Iya,kwana Nan zanje na Kara
sadaki akan na baya sunyi kadan a haka,Beauty harda dariya Dan ita kanta ta Dan ji
nauyin Maman Hanan amma su suke jawowa sun hanata sukuni kwata kwata.

Hanan kuka ta saki taje ta cakumi Beauty wlh sai kin fada min waye bokanki,
Beauty ta saki kukan kissa tace ta yakusheni Baby wayyo idona,Mohsin takaicin su
Hanan ya isheshi kullum sai tazo Masa bangaren Amarya,saura kadan ya saketa amma ya
danne,yace ku bar min part dina,wlh Kun dameni ba dama wai mutum ya huta,Beauty
tace so take ta kallar min nonuwa na,ita din banza waye zai gansu sai ni kadai
cewar Mohsin,Beauty tace wai mutum bazai huta ba,tunda nazo gidan Nan an hanani
nayi amarci lafiya,yace Ku fita nace ya fada a tsawace,Hanan suka yi waje,yace
wannan wacce masifa ce sai anzo Maka bangare,Beauty tace gonarka suke so su kalla
yanda kake noma wlh idan na gaji zan bude a gabansu,Nooo ..karki bude min gonata,,
wannan marasa hankalin su kalla suna da kambun Ido su cinye min abu.
Tashi kaje to kaji me suka zo da shi kaga da mamanta suke tafe baza taji dadi
ba,zata ga an wulakanta musu uwa,Kuma babu dadi Hakan,Mohsin shi da kanshi Yasan
Beauty akwai kissar masifa yanzu ta zuga shi ya gama fitsara Kuma ta canja yanzu a
bayan idon su,amma ko ba komai tana da hankali,mikewa yayi tace muje na rakaka kar
su yiwa mijina masifa,tare suka fito ta saka hijab jilbab,suna karawa part din
Hanan har Maman ta fice ta tafi gida.

Sai Hanan suka samu ta cire rigarta ta dakko wasu kayan a palon wai zata saka Kuma
karya take Jin motsin Mohsin tayi ta cire ko zata birge shi,harda Juyowa a haka
tana wani rawa da su,Beauty ta jawo plate a kusa ta shiga kida tace sai da kalangu
naga alama irin wannan rawa haka.
Beauty tana mata kida ta hade rai ta kama kanta,Beauty tace mu namu ko da riga
bouncing suke ba sai an cire ba,Kuma wlh Dan ya Gani ko a jikina nasan matarsa ce
ke to mene Dan ya gani kin birge shi,ki kwantar da hankalinki Hanan mu zauna
lafiya,karki tunzura ni na fara nuna miki kalar nawa haukar.
Hanan tace wlh Allah ya kiyaye min zaman lafiya da kishiya har abada,wlh duk
duniya bani da makiyiya kamarki,wlh da zan iya da na iya kashe ki har lahira ta ja
tsaki ta juya bedroom.

Mohsin ya juya zai fita,Beauty ta rike shi da sauri tace jeka wajenta Dan Allah
babu dadi sabo da Kai take wannan kishin tana sonka kana ji zata iya kashe ni duk a
kanka fa,jeka kawai kaji damuwarta.
Yace ai sai taga kamar ma tsoronta akeyi,kaje dai kawai Beauty ta juya tare da
komawa part dinta tace matar da ta furta zata iya kisa ai sai a hankali,amma zanyi
maganinta nima daga yau na daina kyaleta wlh.

Mummy kuwa da safen Basiru yasa wasu Dattijai suka yi shiga ta alfarma Chika ta
biya aka yi hayar su suka Kai kudin auren Mummy, kudin ba yawa abin kunya amma
Mummy tace ai dama ya fada mata yace shi sai ya auri mace take Jin dadin duniya a
gidansa,ta Hana kowa magana ita baza a zagi Basiru ba,ai idan anyi auren zata huta.
Basiru ya gama tsarata ta hau Kuma ta zauna,sati daya kacal aka tsaida rana,sabo
da murna Mummy harda girki za a kaiwa Spark da safe da wuri kayan Kari,da kanta
zata Kai daga Nan ta bashi labari yau da sassafe an Kai kudi ma an sa rana.

Sai da ta gama shirya girkinta sannan tayi wanka cikin atamfa me tsada,dinkin
ya gama dameta ta ko Ina,ta yafa siririn mayafinta ta shiga mota sai gidan Spark.
Da asuba kuwa Spark da wuri har liman din ya riga shi zuwa masallaci,Liman ya
shugo bayan an idar da Sallah Liman ya mika Masa hannu ai kuwa yace Liman How
far,Liman murmushi ya saki yasan Ango ne tunda sunje daurin aure,yace ya iyali
Ango? Spark yace lafiya Lau,itace ma ta tashe ni shi yasa ban makara ba,harda bawa
Liman kudi yace a saka a asusun masallaci,ya juya ya fice.

Lokacin da ya dawo Naila tayi sallar asuba suka koma bacci har 11am sannan Mummy
tazo tana buga musu kofa,Naila tana jikinsa ya zame kanta a hankali ya tashi,Idonta
ta bude tace mene ne Ina bacci zaka tashi ta kwada Masa pillow din tace bana son
pillow jiya ka gama illatani shine baccin ma bazanyi ba a jikinka ba,murmushi ya
saki ba shiri yace kofa ake bugawa baki ji door bell ba,Naila ta danji sauki amma
bata iya tafiya da yawa sabo da ya gama da ita gaba daya,tunaninta su Goggo ne tace
sai ta fita itama, daukanta yayi tare da ajiyeta a kasa da sauri ta riko kugunsa
sosai Jin zata iya faduwa,a haka suke tafiya a hankali,har suka fito Palo ya bude
kofa,Yana budewa Mummy ya gani da basket a hannunta,yace dama kece Mummy,tace nice
ta harari Naila tana kallonta ta rasa Inda ta Santa.

Spark Yana kallon yanda take hararar Masa mata,yace Mummy kin San Ina rama
Harara fa,Naila dai Ina Kwana ta furta tana rike da kugun Spark,Mummy ko amsawa
bata yi ba tace ke kuwa Yar Nan Ina zaki Kai jaraba,Amarya guda amma kin makalewa
miji tabbacin an Saba a waje.

Naila tace bani da lafiya ne jiya kwana yayi a kaina ai kin San dole naji jiki,
Spark ko a jikinsa yace wlh kuwa Mummy,zancen Mummy ta share tasan basu da kunya
tace kaga ni karka isheni aurena next week ka shirya har dinner zanyi,Spark yace
Kai Mummy yanzu auren ma sai kinyi gasa da dan ki wato dai ni baza a barni naji
dadina ni kadai ba kema sai kin sake jin wani ai shike nan Allah Sanya Alkhairi
Allah kawo kazantar daki,Naila dariya ta boye ta sa fuskarta a damtsensa tana boye
dariya,Mummy tana kallonta ta harareta,tace wai ni Yar Nan ni sa'arki ne? sai ki
dinga dariya haka kawai mene a jikina kike dariya,Naila komawa tayi gaban Spark
tana jikinsa ta cusa kanta a cikin kirjinsa tana ta faman dariya,wai ita kawai
azabar da Mima zata ji take hango mata tana Jin dadi tana dariya ita tunaninta ko
yaushe haka ake ji idan anyi sex,ba a Jin dadi.

Spark tayiwa rada wai ka fadawa Mummy karta soma Kai kanta dakin miji wlh zata
mutu,Spark yayi dariya shima ya rada mata yace ai ta Saba ne yanzu ita ai dadi zata
ji ba zafi ba,Naila tace bazan yarda da karyar Maza ba kunyi degree a Yaudara,Mummy
ganin abinda suke ta yi suna wani dariya ta zuba musu Ido tana hango kanta ita da
Basiru Kusa suna zuba love,Spark yace mu zauna,Naila tace bazan iya ba ai babu
duwawun zama ka gama ji musu ciwo,Mummy tashi tayi tace gidanku ba gidan zuwa bane
ta fice ko sallama babu.

Tana fita ta hadu da su Goggo an kawo su,kallon banza tayi musu ta shige mota ta
wuce,Su Goggo suna shugowa Naila ta matsa daga Jikin Spark ta zauna a gefe,Goggo
tana kallon Naila dariya ta kamata a ranta,domin Naila ta fita a hayyacinta kana
Ganinta kasan bata da lafiya,ga Idanuwa a kumbure alamar sun Sha kuka,Spark yace
sannunku da zuwa,suka ce yawwa ya gaida su su Rayya ma suka gaishe shi,Naila ma ta
gaishe da kowa sannan Spark ya tashi ya haura sama ya shiga toilet wanka.
Naila tana wajen su Goggo,Goggo tace mu yau Kuma ai sai tafiya,Naila kuka ta
saki Wiwi bilhakki,taji Maza Tausayin kanta take ji ba kowa a kusa,Goggo tace Kinga
bana son gulma ke da Sweety dinki ko ba haka kika ce ba? Naila tana kuka tace wlh
na tuba wlh bani da kamar ku,Goggo tace a'a ki rike mijinki,Dan Allah ku tafi dani
aradu jiya na kusa mutuwa,Goggo tace mu bamu son Jin komai Naila ke da mijinki ai
sirri ne,Naila tace wlh sai na fada zafi wallahi gwara a zuba min yaji kawai nasan
yaji ne yafi min,Ya ragargaza min kuguna bana iya tafiya dole na fada bazan zauna
ya kashe ni ba a nan.
Goggo tace zan makeki aradu yo ni naga yarinya sai ki fada mana,Jiya bacci kadan
nayi wlh Allah yace bazan yi ba, ni dai a kaini gida na fasa auren,Tani tana dariya
tace muje ciki a gyaraki,Naila tace shike nan Kuma bazan Gyaru ba kashina ya goce
bazan taba dawowa dai dai ba,Goggo tace tashi to mu gani,hannu ta miko musu tace
sai an daga ni,Rayya tace cab haka Iro yayi min nima.

Goggo sun zaci wasa ne sai sune suka daga Naila sannan suka shigar da ita wani
bedroom kamar karyayya,har ciki suka kaita toilet,Goggo tace anya kuwa ba sai anyi
dinki ba ke mu gani Dan ubanki,Naila tace wlh bazan ku ganar min ba.

Ayi sharhi please

Na gode masu yi min Ta'aziyya duka na gani na gode sosai,Allah ya saka da alkhairi

AsmaBaffa
[12/29/2023, 12:13 PM] AsmaBaffa: PAID GROUP 300

ACCNT NO
0175487861

YAN NIGER
+22790795939

🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

BOOK 1

91-95

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA GA
AIDA MAMAN TASNIM

Page naki ne
REINA

*MISKI 4in1 Hamil musk*🌹 munkawo original miski daga *Egypt* miskin da indai kinyi
amfani dashi zakiji dadi sosai domin kuwa sekinyi godiya hajiya💃💃 👍 yana dauke:
1.*Musk oil* Ana sakashi acikin gaba sannan zaki iya ringa shafawa a pant dinki
lokaci zuwa lokaci ba lallai sai bayan gama al'ada inda hali za'a iya ringa sawa
Koda yaushe yana maganin infection yana gyara gaban mace sosai 🙈ko yaushe gurin
yakasance cikin kamshi 😇 kamshin sa yana zama sosai bayaga haka sunnah ne amfani da
miski
2.*Musk cream* Ana shafawa ajiki gaba daya musamman irinsu cinyoyi, kasan mara
yana sa jikin mace koyaushe yakasance cikin kamshi kuma yana gyara fata, yasa tayi
laushi
3.*Musk soap* sabulun tsarki na Musk; wannan sabulun miski ne ana tsarki dashi
yanada kyau sosai👍👍 yana kashe infection sannan yana wanke duk wani datti dake
gaban mace da karni musamman bayan gama period 🙈
4. *musk powder* Ita wannan powder din ba normal powder bace tana da sinadarai masu
kyau acikin ta🤭 tana magance warin jiki, warin kashi sannan duk gurin da ake sa
turare zaki iya ringa shafawa ita a ko ina ana iya shafawa har fuska in kinso zaki
iya sawa ko ina dai ajiki zaki iya ringa shafawa💃😇

Gefedaya munasaida ingantattun magungunanmata nasokoto munamaraba damasu siyandaya


kosari numbermu itace 09039320715 pls inbasiyazakiyiba hajiya karmubatawa juna
lokaci

DAN GIRMAN ALLAH KU DAINA FITAR DA SHI,NA GROUP DINKU NE FA KU KADAI LITTAFIN,IYA
GROUP DINKU,DAN ALLAH MASU BAYARWA TA PRIVATE KU SANI BA IZINI NA WLH.

Goggo ce ta fara fada tace zaki tsaya ko sai na make ki,da kyar Naila ta bari
suka duba ta,Goggo ta hau salati tace anya kuwa ba sai anyi dinki ba,duba ki gani
Tani,Tani tace dole a nemo Likita fa mace ta duba mana,Goggo ce ta fito sai ga
Spark ya Sha wanka cikin wata sabuwar Gezna Yana walwali kalar Silver, sai annuri
yake Goggo tace ka kira Likita mace ta duba yarinyar mu,mu tabbatar ba sai anyi
dinki ba,wannan wlh ni na san za ayi haka,Spark yace ba fa wani dinki ni nasan kan
abin na gani ba komai,Goggo tace Dan Allah idan zaka Nemo Likita ka nemo ko wallahi
na fita da ita har asibiti,Spark ba yanda ya iya da su haka ya kira Nurse din Mummy
tazo gidan ta duba Naila sosai tace babu dinki ba sai anyi komai ba zata warke ta
rubuta magunguna tace a siyo mata zata fi saurin warkewa,sannan Dake babbar macece
ce ta kira Spark gefe tace ya bari ta warke kar ya sake nemanta Kuma ya dinga bi a
hankali ta bashi shawarwari.

Spark Yana gama ji yace tabi ta bayan kunne a gaban Nurse din, sai kace kune
Allah to bazan bi dokar ba,ba abinda zai faru,za a raina min hankali,Allah yace ayi
kuzo Kuna min shishigi, arna dubu nawa na kashe jiya sai Allah ne yasan adadi,Ina
ta kashe su a cikin dadi ba wani takobi,Nurse tace ai Kai zaka aikata Spark banyi
mamaki ba,idan ka gama da ita ai ka rasa Kuma,bazan rasa ba inshaallah,ku likitoci
kullum sai mugun fata,sanda Naje nayi aure na da wa nayi shawara shike nan ban isa
nayi komai ba sai a dawo ana damuna.

Su Goggo dai sai da suka tabbatar an siyo magani sannan suka yi sallama da Naila
zasu tafi gida Kuma,Naila ta bawa su Rayya powder da jambaki da sabulai na kwalliya
cikin na lefe ta eba,ta bawa su Goggo ma suka ce baza su karba ba suje su kwashe
mata kaya dama kawaye ake bawa kawai.
Rakasu tayi har mota suka tafi,daga can Spark yasa cikin cousin dinsa yace ya
Maida su gida na Kano su kawayen Umma ne sun waye a sasu a jirgi zuwa Kano,su Kuma
na riga sunfi kusa da Jos a sasu a na Jos ya rakasu har kauyensu sannan ya
dawo,Yana murna zai samu kudi yayi yanda ake so kuwa.

Naila da kyar ta koma sama tayi wanka ta kalkale ko Ina a jikinta ta fito ta
shirya a hankali ta saka atamfa half boubou wacce gaba yafi bayan tsayi da skirt,ba
karamin kyau tayi ba,tayi daurin dankwalinta me kyau Wanda shima daurin koyo take
faman yi kullum a waya iri iri,tana da basira shi yasa take iya nadawa kanta.
Tana shafa turare ya shugo bedroom din,Nan take ta koma kalar tausayi dan kar ma
Spark ya ganta normal,abincin da Mummy ta kawo ya shugo musu da shi yasan fitar ma
matsala ce a wajenta.

A baya idan ya Kalli Naila sai yaga tana Jin dadi amma yau sai yaga ta dauke Kai
da sauri duk ta diriri ce ta fara soshe soshe kamar me kaikayin jiki,yace wai me
nayi ne? Naila tace wa ta nuna kanta tace ni a'a ba abinda kayi,kalle ni to
hannayenta ta hade waje daya ba tare da ta kalle shi ba tace to ni da na kalle ka
Kuma sau nawa Kuma ko a prison ai na kalleka da yawa tayi dariyar dole Kuma duk
Bata kallonsa sai kallan gefe da gefe take,hannayenta ya ruko a hankali,idon Naila
ya ciko da kwalla,yace mene ne? Ko Kari kike so ne? Kai yanzu idan nace ka Kara sai
ka Kara yi?

Wa yaki dadi da gudu ma zanzo,Naila shuru tayi tare da canja zancen tace ni
dama gidanku ka kaini,gidan Mummy? gidanku na asali gidan Mima naga da yara kannen
ku da yawa sai ka kaini yau ma na yini mu Saba da su sosai,Spark ya gano wayon
Naila, yace ni ba gidanmu bane,ko ance miki ni gidanmu ne ban taba kwana ciki ba,to
kira Chikar Gayu tazo ,tace baza ta zo ba sai yamma, Gani na isheki nima ai Chikin
gayu ne idan ita Chikar gayu ce to ai nima Chikin gayu ne,zaki sa ma na kulle gidan
gaba daya,shuru tayi ya dakko ta ya Maida ta gefen bed din suka zauna ya hada musu
tea da kayan soye soyen a Baki yake bata har suka koshi,ya kwashe komai ya Kai
kitchen masu aiki sunzo suna ta gyara gidan ko Ina, shine ya gyara bedroom din ya
samu har ta fara bacci,tashinta yayi da kiss a baki,ture shi tayi da sauri tana
harararsa, yace makwaftanmu sunzo gasu can sun Kai su biyar.

Naila jiki ba kuzari ta mike tace ya zanyi yanzu tafiyar ma da kyar nake yi kana
gani ga mutane kowa ya gani sai ya gane sabo da Allah wannan abin kunya Ina zan
kaishi,Spark yace ni tafiyar ma birgeni take yi wlh sai naji kamar sake yi nake
yi,taso na dauke ki,Zasu ce bamu da kunya,ai gwara suce bamu da kunya akan a Ganki
kamar wata Yar kaciya Kuma da gefe daya fa kike tafiya,Spark daukanta yayi cak ya
fice da ita Yana mata rada a kunne,tana wutsil wutsil da kafafu,har Palo ya kawota
ya ajiyeta a kujera sannan yace bata min lokaci zata yi na dakko muku ita,Yan layin
ne dukkansu sun San Spark sabo da shi Spark duk Inda ya shiga ana zama da shi lfy
duk Yana zuwa suna gaisawa da makwaftan sa,sabanin wasu suzo unguwa babu Wanda suke
kulawa sabo da suna da shi,babu kyakyawar mu'amula da mutane,ba abinda zai faru na
jaje mutum yaje ko na farin ciki yaje,ko Kuma Ta'aziyya,wani maigidan ma sai
makwafcinsa ya rasu bai sani ba,baya kula kowa ya fita da sassafe ya dawo da dare
bai ma San me ake ciki ba a unguwa,wani iyalan sa ma bazai bari suyi harka da kowa
ba,wani abin kuma idan ya same ka kafin ma Dan uwanka yazo makwafcinka yayi Maka
shi,shi yasa Spark Yana zuwa duk abinda ya faru har gudun muwa yana bayarwa komai
kudin mutum.

Yaran layin indai yaga wasu ko bai sansu ba Yana basu kudin school sai yayi ta
rabawa yara alawa da kudi,duk sun San Spark matan ma da basu sanshi ba sun San
sunansa a baki.

Zama yayi a gefen Naila yace wannan duk makwaftan ki ne,Kinga Hajiya Babba,ga
Aunty Maryam,Aunty Maijidda,wannan Ummu Salma,Kinga Aunty Naja'atu,Naila da fara'a
ta gaishe su suka amsa tace Sunana Naila,suka ce kamar yanda ya fada miki
makwaftanki ne mu da fatan watarana zaki kawo mana ziyara,Spark yace zan kawo ta ai
gidan ko wacce,Hajiya Babba tace ai ka kyauta wannan shine zaman tare ai hakkin
makwaftaka ne,ace sai dai talakawa suyi mu banda mu ai bai dace ba sabo da Allah ya
rufawa kowa asiri,Naila haka duk langonta ta mike tana daidaita tafiyarta ta shiga
kitchen.

Ruwa da lemo ta kawo musu sai kayan gara da aka yi mata dublan da Alkaki harda
Chin chin ta kawo musu,tace Dan Allah kuci idan ma baku ci ba sai na zuba muku
abinku a Leda,kadan suka ci suna hira,Hajiya Babba tace Amma Spark matar nan taka
Yar Fulani ce ko? Spark yace sosai ma,tace ai naji maganarta gaba daya gata
mashaallah kayi dace,harda cewa na gode cewar Spark.
Sun Dan jima sannan suka tafi,Naila tace gwara na zauna a palon kar wasu
suzo,kafin ta rufe baki kuwa sai ga wasu makwaftan suma sun zo,suma Spark ya
gabatar dasu basu Dade ba suka tafi,sai Kuma ga Yan uwan Spark Badia da Anam,sai
wasu Yan matan su biyu suka zo,sai Arham,da Shahid suka zo gidan.
Badia tunda ta shugo take kallon gidan tana wani tabe baki,Naila tace sannunku da
zuwa,iya mazan ne suka amsa da fara'a ba ruwansu amma su Badia ko amsawa basu yi
ba,Badia tace Kai ku zauna mu da gidanmu suka zauna,Naila tunda Taga haka sai ta
kama kanta suka gaisa da mazan kawai ta share su Badia,au mu baza ki gaishe mu ba?
haba yara Kuna kannensa ni zan gaishe ku Yayanku nake aure fa.
Arham yace da gaskiyarki Aunty wlh karki gaishe su.

Spark ne ya sakko daga step ya daure fuska ba wasa ganin su Badia, System dinsa
ya dakko ya sa a charge sannan ya dawo ya zauna ya jawo Naila ya dorata Saman
cinyar sa,Arham yace Yaya Spark ya kalle shi babban yatsa ya dagawa Spark wai yayi
dai dai,dariya Spark yayi yace yaro kayi biyayya ka samu aikin yi,Arham yace ai
tun jiya nabi ma,Dan Allah ka bani kudi na siyi wani agogo da wando,Spark yace ai
baka da matsala indai kabi Amarya ba wando ba har da rigar ma sai a siya
Maka,Shahid yace gaskiya Yaya wlh ka iya zabe,Spark ya mika Masa hannu yace mu
gaisa,Naila dariya tayi tayi derere Saman cinya tace Arham Dan shiga kitchen ka
debo muku drinks nidai bazan tashi ba,ya shiga kuwa ya debo musu harda kayan gara
din ya zubo musu,a hankali Naila ta zame ta koma Saman kujera,Badia taki ci tace
sai kace mayya,Spark yace to da mece ke? Ai mayyar ce ke duk gidanmu ai kece kike
kama da mayun,ai kece full definition na mayya,Anam tayi dariya,yace Ido kamar na
kwado zaki zo ki min iskanci,ko baki San gidan wa kika zo bane.

Naila ce ta katse maganar tace ya ka bar System din a can? so nake tayi
charge,tace okay tun safe muke baki ai,ni fa Chika bata zo ba har rana tayi,Spark
fuskarsa ya dora a Saman kafadarta yace zata zo ne.
Spark kannensa ya kalla mata Wanda basu da aure yace kai kuyi Maza ku saka kuka
kuce Papa ya muku aure akwai baiwa a cikinsa,Arham suna dariya suka ce Lallai Yaya
ka fara canjawa baka taba fa shiga harkar mu amma gashi yau sanadin aure muna ta
Hira harda dariya,yace ka taba ganin me Iyali shashasha? yanzu ko kanka na shafa
sai kayi albarka yaro,har su Badia dariya ya basu,Da kuwa ni kaina bani da albarkar
bare na shafawa wani yanzu kuwa yaro kayi kokari na sa ma albarka binka zata yi,
sun Dade suna cin dariya Spark yayi aure ba zaman lafiya,suna komawa gida suka hau
bawa Mima labari,wlh Yaya bashi da kunya har muka taho tana cinyarsa,Mima tace ku
kuka Kai kanku ai ,Kuma ko me tace Mima wlh baya musu Inda kisan rakumi haka take
jan sa cewar Badia,tace itama ashe irinsa ce tayi shuru har da gyara zama sai faman
rada suke yi,Mima tace wannan anyi tambadaddiyar Amarya,ai zanje ne da kaina.

Kwanciya Naila tayi a kujerar tayi matashi da cinyar Spark Yana ta mita yace ko
dan Nono ban taba ba yau an hanani sakewa sai an jawo min ciki ya fito banyi komai
ba ban more ba Amarya ta samu ciki yau lafiya gobe Amai...kafin ya rufe baki Misam
ya shugo, ya tashi Naila yace ke tashi kar gaban rigarki yayi kasa Mayen mata yazo
kar ya ganar min nawa na sunna,Misam yaji haushi ya juya zai tafi Spark yace Allah
ya raka taki gona dama ni haka nake so duk kunbi Kun takura min,Misam dawowa yayi
yace to na fasa tafiyar ya zauna,Rafeeq ne ya shugo shima yace girki ne ya kawoni
Muji hannun Amarya,Spark yace sabo da matarka ce ba,ko ni banci ba bare kai,a dinga
godiyar Allah Spark, jiya ka koshi fa da dare, Amarya ba ta ciyar dakai ba,Naila
duk rashin kunyar ta sai da taji kunya,su kuwa ko a jikinsu,Spark yace girkin akwai
dadi ba'a koshi ai,Misam zaiyi magana Spark yace karka ce mana komai ato, baya so
ya tonawa Misam asiri yace Yana neman mata,dariya Misam yayi yace zan baku mamaki
wlh,Rafeeq yace Ashe Spark sabon Uba zaka yi kwana Nan? Uban wa?Spark ya furta yace
sai dai uban wasu ba nawa ba, Mummy zata yi aure Ashe cewar Rafeeq,Spark yace shine
Kuma Ubana,Rafeeq yace naga Sai zumudi Mummy take,Misam yace ai tuni na gane Maman
Spark Harija ce,ai wajenta yayi gado,Ubanka ne Hariji marikin ka dai shine me
mataye,Naila tana ji a ranta tace yau na shiga uku sai buzu na,Hannun Hariji na
fada shi yasa abin yayi yawa sai hawaye ita kadai ta boye fuskarta a Jikin Spark
suna ta hira ita Kuma tana ta kuka,Spark yaji dumin hawaye a jikinsa da sauri ya
dago fuskarta yace me aka yi miki Kuma? Naila tace ba komai,Rafeeq ne ya Kalli
Misam suka hada Ido yace ka tsorata Amarya ba ruwana,Misam yace ni me nace daga
nace Hariji ne sai kuka,idan kasan zaluntar yarinyar nan kake yi ka fada mana,Naila
tana goge hawaye tace ni Allah ya Gani zaluntata yake yi,bana son soyayyar nan Dan
Allah ku kaini gida.

Rafeeq dariya ya kama yi a boye,yace Allah na gode Maka,Spark Allah ya biya yau
naga tsoron Naila,dama tunda nake ban taba ganin Amarya irinta ba babu ta Ido,yau
Naila ce take gudun Spark tab abin babba ne.

Misam yace to ke Amarya haka ake yi daga wasa Kuma,Naila tace ai nasan ba wasa
kuke ba tunda ai ni nasan mene baza ku gane ba,Misam yace baki dauki wa'azin Yar
gidan yari ba kenan,Spark yace ki daina biyewa yaran nan fa zasu kaiki su
baro,Chika ce tazo gidan a motar Misam ta jiya,ta Sha gayu cikin Arabian gown,ta
shugo da sallama,Rafeeq ya kalleta kawai ya dauke Kai,Misam ma haka,Spark yace dama
kuka take kinki zuwa,Chika tayi mamaki tace Naila da kuka? a'a sai dai na karya
Naila da bata kuka.

Naila hawayenta ta goge da sauri tana dariyar dole kamar ba komai,tace naga
idonki a kumbure Amarya lafiya? Naila tace Abba na tuna,Chika tace tabara ce wannan
kawai ta ganin miji in ba iskanci ba kawai ki kama yiwa mutane kuka,Kaine kake
kulata ma,Spark a ransa yace wayyo cika barkono da gishiri na barbada mata,Chika ce
ta Kalli Misam ta dauke kai,hannun Naila ta fisgo ke taso dalla,Spark kamar shi aka
fisgo yace wayyoooo......yasan kwanan zancen,Naila kamar gurguwa haka take dingishi
tana tafiya da gefe daya,Rafeeq yace agwagwa tana wanki,Spark yace zan ci uwarka
wlh, dama sa Ido ya kawo mu cewar Misam,duk nasan ai Yan sa Ido ne suke zuwa Spark
ya fada Yana harararsu Yana danna waya.

Chika har bedroom din Naila tace ke ban fa gane ba lafiya na ganki tafiya
kamar Yar kaciya ke Naila menene haka? Naila ta Maze tace ke dalla Beauty bata yi
karya ba dadi sosai fa,just that na bashi maganin yayi aikin da yawa yaki gajiya
amma duk da haka wahalar kadan ce sai dadin yafi yawa,Chika ta sauke ajiyar zuciya
tace yanzu naji zance,to ya love din? gashi kin Gani Ina ta shagwaba Ina kukan
samun sarari da sangarta ai shi nake yi,kin San Kuma danginsa sai ka nuna musu kai
ma A ce sannan ake zama lafiya da su shi yasa ai kika ga Ina ta Masa kuka.
Amma jiya Madarar Nido ai na kwankwadeta,kamar kar a daina,Chika tace Shegiya
kawata anji sweet dole kiyi shagwaba,Naila tace ei mana karki auri gajere yarinya
ba kowanne gajeren ba amma Mafiya yawa tasu kubewar Miya ce,Chika tace ke nifa tun
yanzu ma nake karewa ta saurayin da nake so kallo,Naila tace Misam din? Chika tace
ae mana amma har yanzu ban ganta ba maye boye kayarsa yake yi a boxers bare ma a
kallar Masa.

Naila tace kawata kiyi sauri akwai dadi kar mu barki a baya,tausayinki nake
ji,to nice jaraba ma nayi kwantai duk anki so na,wannan Misam din sai wani iyayi
yake min na ma daina kulashi,muje ki tayani girki abinci wai suka zo ci,da nace
bazan yi ba,Chika tace kiyi mana karki dogara da surukanki wannan marasa mutuncin
ba kawowa zasu yi ba sai sunga dama,gwara ki zage ki rike mijinki,Naila a ranta
tace rike Miji manya bari kiyi kiji tukun.
Fitowa sukayi zasu shiga Kitchen Misam yabi Chika da kallo,har ya hango irin
dadin da Chikar zata yi ma,Rafeeq yace tunda za ayi bikin Mummy ni zan dakko
malamar gidan yari zan bawa Chika kudi ta dakko mana ita mu da bama bin mata ma
rage zafi da zancen harkoki ko banza naji Badala.

Spark yace idan za kuyi aure kuyi aure ku daina walagigi Kuna tangal tangal da
rayuwar ku,ni Kunga kullum Ina da komai a gidana duk Inda naje zan dawo na
samu,Rafeeq yace yaushe ma na fara balaga ni tab naje na tsufa da wuri,Spark yace
to kar a dinga yawan zuwa gidana ana kallar min mata kuje kuyi ta iskancinku a
gari.

Naila tace me za a dafa musu ne? Chika tace a musu me sauki jollof din
taliya,Naila tace Baby baya son taliya fa gaskiya,Naila tace ita dai tuwo zata
yi,Chika ta dinga dariya tace Amarya guda da tuwo ai sai ayi dariya,ta Dora taliyar
haka ba a son Naila ba,taji nama da hadin kayan lambu, kida Rafeeq ya kunna,Chika
tana kitchen tana tikar rawa, har suka gama komai suka shirya a dining sannan
Rafeeq Wanda dama shi daga School yake ya riga kowa zama a dining,Misam ya zauna
harda gyara riga Yana cewa girkin Amarya zanci,Spark yace Amarya me dadin tuwo da
Miya yau me taliya ce kenan,Naila ta tuna Indomie dinta da salat.

Chika bata da kunya tana ganin Spark ya tashi tana zaune tana rawa,Misam ya
kalleta yayi murmushi,Rafeeq yace ashe su Chika dai ko Ina da ku rawar ma an
iya,Chika tace Kai a gidan yarin ma mune shegun ciki,Rafeeq yace naga alama kece
akan kin fito daga gidan yari kika dinga rawa,Chika tace ai kowa ranar sai da na
raba musu alakoro suka kalla,Misam yace na hanya ma ai sun gani,tace ai gwara ni
bani da permanent uhm uhm...a cikin hot....Rafeeq yaci gaba da cin abincinsa,suna
zaune suna ci suna Hira harda Chikar gayu ita da Rafeeq suke hira,Misam abincinsa
yake ci baya kula su,wata yarinya ya latso a waya ya nuna Rafeeq yace Kalli,Rafeeq
ya leka ya kalla harda kashe Ido daya duk sabo da kallon mace,yace tayi ka sa pics
Dina ko zata kyasa na yaudare ta,Dariya Chika tayi wai ya yaudareta wato ma ba
aurenta zaka yi? Rafeeq yace a'a wanne aure Kuma ai ni da kike Gani Yaudara ce
burina,ba Kuma abinda zan taba mata kawai na yaudari mace na wuce amma matan ma sai
su dinga tafiya wajen Yan iska,da wajena suke zuwa ai da sun huta, ba gara ba zago
zan yaudare su kawai suyi gaba lafiya lafiya,Chika ta samu hanya tace wasu kuwa sai
bin mata ana lalata musu rayuwa.

A dinga bibiyar mata kamar yaran akuya,tana magana tana kallon Misam,yasan da
shi take,tace sai lalata kannen wasu,'ya'yan wasu,yayyen wasu,matan wasu aikin
kenan,me za ayi da Maza irin wannan basu san darajar mata ba Sam,ko aurensu kayi
basu iya dainawa sai dai ka mutu da bacin rai,Misam ya gama daukan zafi,Spark ne ya
fito zai tafi masallaci Sallar Azahar,Rafeeq ya fara dariya ashe an musulunta,Spark
yace Chika rabu da su kije kiyi sallah abinda zai amfane ki,Chika ta mike ta wuce
bedroom a kass,Misam jira yayi bai fita masallacin ba,Rafeeq yabi Spark sun tafi.

Suna tafiya Misam ya shiga dakin da Chika ta shiga tana shirin shiga toilet
taji an fisgota,ta fado jikinsa da sauri ya ture ta sannan ya sake fisgota ta fado
jikinsa ta baya,hannu yasa ya toshe mata baki zata Masa ihu.

Da hannu daya ya rike hannayenta ta kasa kwacewa, seletape ya hango a Saman


mirror ya dakko ya yanko wani ya manne mata baki,hannayenta rike a hannunsa,Chika
sai hawaye Shar Shar, tana ji tana gani ya fara cire mata kayan jiki,sai da ya cire
mata rigarta duk yanda taso tayi kokawa ta kasa yafi karfinta ta ko Ina.
Toilet din ya bude ya jefa ta ciki yasa key,Sannan ya kalleta sosai yace kinci
darajar Spark wlh da yau sai na gama da budurcin da kike takama da shi,ba abinda
zan miki so nake na nuna miki ba abinda bazan iya yi Dake ba idan nayi niyya ta
karfi ma zan iya,amma yau wanka zan miki tas,ya jawo kujera ya zauna Yana rike da
hannayenta.

Chika sai hawaye Daya na bin daya,ta durkushe a kasa alamar roko,shi Kam
surarta ta tafi da Imaninsa,ya tsura mata Ido hankalinsa ne ya fara barin jikinsa
ya jawota jikinsa ya rungumeta,tana ciki cikin kwacewa ya cire Seletape din ya fara
kissing dinta a nutse kamar wata matarsa,Chika tana ta kici kici abinka da so dama
kadan take jira sai ta tsaya kamar gunki tana ta hawayenta,Yana ta faman tsotse
mata Baki dama gashi gwani a sanin mata,Yana dan fara tabe mata kirji ta karo
kukanta bayan dadi take ji tsabar gulma tana kuka ta fake da burburwa tana girgiza
kirji wai duk cikin kuka ne,sai da ya tattabeta sannan badan yaso ba ya hakura,ta
fice da gudu ta dawo bedroom tare da kwashe rigarta a hannu ta bude sip ta shige
ciki ta rufe kanta a ciki ta Maida rigarta,sai lokacin ta tuna bakinta ya toshe
mata ta cire tana hakki,tace kaiii tab amma lallai wannan guy din Dan iska ne,ba
ruwana da shi daga yau har abada.

Misam kuwa Sallar ma baza ta yuwu ba yanzu dai Kam sabo da ya kunna kansa da
kansa,ficewa yayi ya samu Spark sun shugo,yace wai yau baka je masallaci ba Kai da
baka wasa da jam'i,yace nayi tawa a daki yau,Spark yace okay idan Kun tafi ku rufe
min kofar Palo na ni baccin rana zanyi,Naila tayi sallah ta rasa Ina Chika ta shiga
har tayi wanke wanke ta gyara wajen ma neat,tana karasa goge kitchen Misam yace
Aunty mun gode mun tafi,Naila tace nice ai da godiya suka fice,suna fita Rafeeq
yace me kayiwa Yarinyar Mutane Misam.

Me zan mata kuwa da ya wuce na lallatseta na fito wlh taci darajar Spark amma
indai taci gaba da zagina da mazinaci wlh sai na yi da ita,Rafeeq yace haba mana
Dan Allah karka yi ta daina ma daga yau,amma taji dadi? Misam yayi dariya yace taji
dadi zaka ce ko naji,kawai sai na fada Maka sirrinta baka da hankali,ko Karuwa ce
bazan fada ba bare Chika mutuniyar mu,kawai dai tana Dan birgeni shi yasa ma na
damu naje na kalleta in and out sai Kuma ta tsokane ni,ni yanzu wlh ma akan wata ta
bani kanta gwara Chika ta bani kirjinta yafi min.

Rafeeq ya dinga dariya yace karfa ko ka tabowa kanka Kuma anzo madakata,Misam
yace to wa ya sani ne ni kaina ba gane kaina nake ba karbi key kayi driving
dina,har suka shiga mota Yana cewa amma yarinyar nan anyi baiwa,na daina ganin
laifinta da take raye raye ashe gadara take da baiwar,anya kuwa..anya..wai ka
aureta to mana cewar Rafeeq ,wannan yau tayi fushi baza ta so ni ba,tasan ma fa me
nake yi wace zata so namiji a haka,Rafeeq yace baka San so ba Misam,indai ta kwanta
Maka ka aureta.
Yace ni dai jikinta ya min ba wai so ba,hmmm Allah yasa wani yazo yayi wuuf da
ita ai ka huta.

Spark kuwa Naila ta fake da gyare gyare har dare yaje yayi Sallar Isha ya sameta
a Palo ta idar da Sallah,wato sallah ma a Palo zata yi sabo da tsoro,sai addua take
yi taki karewa Allah kar ka bawa Spark sa'a a kaina,Allah kasa yaji ya gaji,Allah
ka saka Masa bacci me nauyi ya dauke shi,Spark bai san me take roka ba ya daga
hannaye sama wai Yana amsawa da Ameen,Allah gashi Nan kasa muna zuwa ciki bacci me
nauyi ya kamashi,kar ya farka sai asuba.
Tana shafawa shima ya shafa harda cewa Ameen,tana cire Hijab ya dauke ta,ya
karkashe kayan wuta ya kulle ko Ina yace ko waye bazan bude ba dare yayi.

Sama suka haura,itace ta fara shigewa wanka harda danna key,sai da ta gama har
brush ta fito yace ki koma na saka miki maganinki na Yan kaciya,kin yarda tayi zata
yi kuka,kamar ya hakura yaje yayi wankansa shima Yana fitowa har ta gama shirinta
ta saka dogon wandon jean blue da riga me wuya da hannu kamar ana Sanyi,dariya yayi
Taga ya dakko almakashi yace mu fa komai mun tanada ko ki cire da kanki ko suma ayi
asararsu,Naila ba shiri ta daura towel ta cire,ya dakko wata Yar iskar riga me Dan
gajeren hannu da kadan ta rufe duwawu,Kuma baza a sa pant ba,Naila tace wlh sai
nasa,yace karki bata min wanka ki bar min abina,ke bai fi ma kyau ba ki dinga Shan
iska,Naila abin ya zarce tunaninta a haka ta saka pant dinta,Yana Juyowa yaga ta
saka harda hade rai ba wasa ba mutunci yace ba Kya ji ko bari nazo,cirewa tayi ba
shiri Yana kallonta tayi jifa da wandon wai tayi zuciya ta koma Jikin Kofa ta
rakube tana kuka,yace saka wandonki,ta dauka da sauri ta saka,yayi fushi wai shima
ya daina kulata,tana kallonsa ya shirya ta zaci zai saka kayan shiko ko wando yace
idan matar taki ai sai miji shi yayi shi,Naila tace a'a saka saka zan cire,yace a'a
ba wannan zance,ni kin San dai dai nake dake,Ina son mace me taurin Kai ai.

Hannu ya Kai zai rukota ta matsa da sauri duk ta firgita,yace ba abinda zan miki
fa ni wlh,wai kin maidani abin tsoro,Naila da hannu tana nuna Hallare tana ja da
baya tace wannan ce shegiyar Aradu ban yarda,tayi mugun bashi dariya yace alright
ya saka kayan baccinsa wasu maroon sannan yace to kwanta,rigar jikinta ta kalla,a
rigar daidai nipple dinta botin ne a wajen ko wanne side,tace kallo rigar Nan ka
nuna min ma'anarta wlh tunda naga ka nace sai na saka da wata a kasa,Wannen botin
fa? Yace na wasan Ango ne,Ni da iya nan zaka tsaya da sauki amma Sam baka da Amana
Spark.

Ban San sau nawa kike so na rantse ba please mana wai kamar ba Tantiriya
ba,shammatarta yayi ya dakkota yace kina min kuka sai nayi,gwara ma ki rufawa kanki
asiri mu kwanta.
Saman bed ya kwantar da ita shima ya shige ya kwanta ya dakko wayarsa Yana
dannawa Yana dariya shi Daya,Naila ta kalle shi tace ya ma rainani Ina gefensa waya
ta fini,idan wata ce fa suke chat, wayar taga ya manna a kunnensa cikin girmamawa
taji yace Abba Ina yini,Abba ya amsa ko Naila bai tambaya ba wai Kara yake kar ace
ya damu da yarsa,Spark Yana ta jira yaji ko Abba zai tambayi Naila amma shuru har
sun gama waya sai shine ya gaji yace ga Naila,Naila wayar ta karba da sauri.

Ai kuwa tana wayar taji Spark yana wasa da botin rigar dake saitin nipples
dinta,sai ya hade har Boobs din,ba abin tayi magana ko wani sound ba Abba yana
wayar zai iya ji, Umma ya mikawa yace ga Gyatumar ki,Umma tace nice Gyatumar ma zan
rama wlh,Naila tana jinsu tayi dariya suka gaisa Umma tace kalau kike kuwa? Naila
tace to Gani nan dai, a tambayi lafiya a wajen Amarya Umma,kema fa kin San harkar
nan karara Ina naga wata lafiya ni,da za a bani gado a asibiti ma ai da Hakan yafi
kawai nasan jinya nake yafiye min.

Umma tace ai zama da masoyi akwai dadi,Naila tace Kai Umma daina zancen nan
duk karya nake ashe ban San komai ba,daga yau har abada bani ba maganin Maza ba
uwar da na sani ashe haukata nake kawai,Ina ta cewa nasan Hallare ashe ko ta
fitsarin yara ban sani ba,Kaka yaci gaba da sana'arsa kawai na dinga tura Masa
customers.
Umma tace a'a Naila ayi haka ke da kika San kan komai Kuma,Naila tace kuruciya
ce na gane gaskiya,Umma tayi dariya kamar ba gobe ta kashe wayar tana cewa amma
Allah yayiwa yaron Spark albarka.

Abba yace ke dai wlh kina abin kunya baki da tausayi, yarinya kamar ba jininki
ba,ke sanda aka kawo ki watanki nawa kina guje guje a riga,sai dare yayi a nemeki a
rasa kin gudu sabo da tsoro,wanne kuka ne bakiyi ba,duk garin Nan sai da kowa yasan
Hashimu ya angwance,kika cika gari da ihu,mutane da safe aka dinga gulma jama'a
ihun wa nake ji? akace Kubra ce wlh da Dan dolonta Hashimu ai Hashimu jiya Kuma an
Sha dadi,Kubra tace to yanzu nayi mana ihun,Hashimu yace zaneki zanyi wlh ko da
wasa kika ce zaki sake wannan iskancin naki,me yayi saura Kuma,Kubra tace zaka zo
ne,yace nazo din ai dole ki hakura dani bana kuri,kin isa kiyi komai Kubra ta, a
nan ke kike da power.

Mohsin Yana shiga bedroom din Hanan ya sameta tana rusa kuka ta fara
azzalumi,macuci,kana zaluntata sabo da kayi aure ka samu Sabon hannu,yace yanzu kin
min adalci kenan? Me nayi miki na zalunci? Kwananki ya zagayo ne? Yau kwana nawa da
kawo Amarya? Kwana biyu kin tafi yaji,kin dawo anyhow kike shiga part dinta ya dace
kenan? A matsayinki na babba abinda kike yi ya dace?ba irin karar da bana miki amma
bakya gani,me yasa kishi zai sa ki Maida kanki shashasha,yarinyar nan bata nufinki
da komai,Hanan ta sake barkewa da kuka ai gashi Nan komai ita kake yabo,ni na tsufa
ka daina so na,nonon nawa ma ko kallonsa baka yi,Kuma Allah sai ya saka min,Allah
bazai kyaleka ba,ya Kalli Hanan yace wai tunaninki wannan shine zai sa naji
tsoronki? Ki canja tunani idan zaki gyara ki gyara idan baza ki gyara ba ni bazan
zauna kullum kina Bata min rai ba,kullum kina hanya kece wajen Abba kece
gidanku,Ina gargadinki wlh kar ki sake zuwa part din Beauty,naji kina cewa da zaki
iya kisa da ita zaki kashe ko? Zama da irinki bashi da amfani tunda kika fara
zancen kisan Kai,Hanan da masifa tace to sai me ka sake ni mana,an fada maka tsoro
nake ji,Mohsin juyawa yayi ya fice,Yana fita ta saka hijab ta fice sai Rumfar Abba
ta tafi Kai Kara.

Tun daga nesa Abba ya hango ta an sauke ta a Napep,Abba Sadaf Sadaf ya zaga ta
bayan rumfarsa ya buya,Hanan tazo ba Abba,cikin gidan ta shiga tayi sallama,Umma ta
dade bata ga Hanan ba sai yau,Hanan ta fashe da kuka tace nidai da wannan zaman
bakin cikin gwara a fada Masa ya sake ni,Umma tace akan me za a sake ki,haba Hanan
me yasa kike Maida kanki wata banza,yau kwana biyu kacal da kawo amarya gidan,kin
Hana kanki sakewa kin Hana wasu sukuni,iskancin Nan naki ya ishe ni Hanan karki
kaini bango wlh zan iya sawa ya kore ki,wannan wanne irin bala'i da masifa ne
haka,ke dai bakya so a zauna lafiya,Allah ya kaddara Masa auren mata biyu kice bai
Isa ba,ke din banza, wannan haukar da shirme ba Inda zai kaki gwara ma ki shafawa
kanki ruwa kije ki gyara kanki ki zauna lafiya,idan Kuma kinki da kaina zan sa ya
sake ki,ana daga miki kafa bakya gani,Baki da Kara baki da kunya,kin Raina
kowa,Shike Nan yaro sai ya zauna a wajenki kar ya kula waccen sai ke, ubanki yazo
yiwa bauta? Mohsin kowa yasan hakurinsa ba a fada da shi,ba Wanda bazai ba da
shedar sa ba.

Abba ne ya shugo yace Kubra kin so kanki Ba kiyi gaskiya ba,ba haka ake fada
da sasanci ba,kin ware naki kike so,a kira Mohsin yazo Muji ta bakin kowa idan
bazai iya ba kawai ya saki Hanan a huta kowa ya huta,Hanan tana Jin haka ta mike
tsaye tana kuka tana cewa ni dama ba a kauna ta,bari naje gidan zan kwaci yanci na
wlh,Abba yace kaji Yar jakar Uba wanne yanci kike nema Kuma Wanda ya wuce wannan da
kike ciki,bayan uwarki kike so ki koma ki dinga bacci ko kuwa.

Dama ni tuntuni nasan Mohsin hakuri yake Dake shegen jiki duk Kashi,wannan ke
dai ba Yar Albarka bace,ko bacci ya kwanta nasan kullum sai dai ki dinga bibbige
shi da kasusuwa,Ina amfanin Hakan,Hanan tana wani fiffika tace ai shi yasan me ya
aura yasan me yake ji a jikina,da kirjina ma saita Masa tunani nake,Abba haushi ya
kamashi yace au sirrin sa zaki fada mana iyaye guda,nonon naki akan Kashi mene
kyansa to,Amal ta gama da shi,yarinya daya kika haifa ta tarwatsa shi,Kubra kuwa
harda mijinki duk sun Sha amma ba duk budurwa ba,Abba yayiwa Hanan tas,Hanan dai
ficewa tayi ta koma gidanta tace zan canja salo ba komai za a ga tuggu wlh.

Abba ya fice ba a rumfar ya zauna ba wajen Yan majalisa ya zauna yana cewa
kwana nan za aji ta fashe min,kwana nan za a fara gulma ta a gari, suna jinsa suka
ce me zaka siya ne ko wani kudi ka samu? Hashimu yace bazan fada ba amma dai
dama,Mohsin na biyawa aikin hajji,ban so na fada muku ba,Daya a ciki yace Kai kuwa
Ina ka samu kudin? Abba yace ai tun farkon fara sana'a ta ba ci ba Sha,dama burina
na Kai Mohsin aikin Hajji tunda bani da shanu,shi yasa bana cin komai na dinga tara
kudin,amma ka bar iyalanka da wahala? Hashimu yace to iyalanka ne ko Kaine kake
daukan nauyi na?
Abba tsaki ya ja tare da mikewa ya koma wajen aikinsa.

Naila dai ana gama waya da Umma sai aka kira Mohsin,suna cin abinci yace
Beauty ga kawarki ya sa a handsfree,Naila tace my love,Spark yace Yaya dai ga your
love a wajenki,Mohsin yace banji kanwata tana dariya ba yau ba nishadi,Naila tace
hmm kawai,yace yau ba magana kenan,Naila tace akwai mana kawai dai ba damar fada ce
babu yanzu,Mohsin yace ya amarci ana ta Sha, Naila tace ba dadi Yaya,yace ke na
gaba zaki warke zaki Saba ne kinji bana son surutunki,ku dama Yan riga haka kuke
baku shuru da baki,dan Allah karki sake fadawa wani kinji idan ba haka ba bazan zo
gidanki ba,Naila tace a dake ni Kuma a hanani kuka,da ban Sha wahalar ba ai bazan
fada ba,okay bakya son auren yanzu? Naila tace ae,yace to taho gida tunda baki da
hankali sai ki dawo gidan ki zauna,wayar ta kashe tace kaji Yaya daga magana sai
fushi,ai gwara haka ni kaina na kusa zuciya nayi fushi,Naila dariya tayi tace Kai
din?, Ae mana ya furta tace to daina taba min Boobs sun gaji suma,Spark yace cikin
biyu za ayi daya yanzu,ko dai ki tashi ki min abinda nake so naji dadi ko na sake
yin irin na jiya,Naila tace a'a please zan Maka ni ba sai kayi ba.

Naila sabo da ta samu salama ta zage duk abinda ya sata sai data yi Masa,Yana
Jin dadi Yana koya mata abubuwa da yawa,yace to ga kawarki Hallare Kinga ita kadai
ta dauki zafi ki samu ki shanye ta,Naila a ranta tace nidai na shiga uku,Yana faman
Jin dadinsa Naila tana Masa abinda yake so sai da ya rasa Inda zai sa kansa sabo da
maganin Dake aiki a jikinsa yaji bazai iya hakura ba,kwantar da ita yayi Yana Shan
abinda yake so,wayo yayi mata yace bari Kiga yanda ake yin salo,har taji tsoro yace
gwadawa zanyi ki gani ba abinda zanyi ai nace sai kin warke,Naila tace to, ya danne
mata hannaye da nasa yasa kafafu duk ya gama da ita ko motsi bata Isa tayi ba, a
hankali ya taba gabanta yaji ta zama wet,Hamdala yayi a ransa yace ashe kinji
dadi,Naila tace kayi sauri ka gwada na gaji wlh,Spark a hankali yake mata wayo ya
fara kokarin shiga Naila ta tsala ihu,tana rokonsa Dan Allah karka yi Dan Allah
mutuwa zanyi,amma Spark baya jinta Sam haka ya shigeta a nutse,dadi har kwanyarsa
ya manta ma jinya take yi babu daga kafa a harkar Spark Yana ta Sambatu kamar
zararre haka yake Sambatu Yana kwasar dadi,Naila kukan ma ya kafe sai zallan azaba
da take Sha,wayyo Abba kawai take iya fada,shi kuwa gogan ko a jikinsa baya duniyar
ya Lula can wata duniyar Sambatu kawai yake da ihun dadi Yana furta
dadi...dadi....yau ma ya shakata sosai sannan ya juyewa Naila madarar Nido tare da
kankameta a jikinsa,Yana bata hakuri,yace ban San zanyi ba Aljanune suka shige
ni,Naila wani takaici ya kamata,tana kuka kasa kasa tace Kai dai kawai bakin mugu.

A hankali ya fita a jikinta yace I'm sorry,ai Spark ka zama masifa sai Sadaka
cewar Naila tana hawaye,tace yanzu idan ba rashin Imani ba kana gani ban warke ba
ka sake yiii.....sai kuka
I'm sorry kinji Aljanune suka shige ni,ya zanyi da Kai Spark tunda baka da
tausayi ya zanyi,ya sake dawowa ya manne a jikinta kamar maye hannayensa ya Maida
kirjinta,Naila ta rabu da shi ta gaji gaba daya,a haka baccin wahala ya kwashe
ta,shi Kuma na farin ciki yake yi sosai.

Yau makara suka yi Bai je masallaci ba sai 8am suka farka,Yana farkawa ya
tashi da sha'awa matsananciya,shi kanshi ya rasa wanne magani ta bashi bai ki yayi
ta yin sex ba.

Mikewa yayi yaje yayi wanka da brush sannan ya dauro Alwala ya fito ya tada
Sallah,Yana tashin Naila ta sakko da dabara da kyar take tafiya haka ta dage ta
gasa kanta sosai,ta dakko ruwan Yan kaciyarya ta saka ta Nemo maganin su Goggo tayi
amfani da shi shima,sannan ta fito ta Tada sallah, bayan ta idar tayi addua ta
koma ta kwanta Yana zaune Yana azkhar sai da ya gama sannan ya haura Saman bed din
ya koma jikinta suka koma bacci.

Mummy kuwa Shirin biki suke yi tare da kawayenta,Basiru Kusa ba kalar motar da
baya Hawa,Yana ta zuba mata karya,har motar Misam da Chika ta dakko suka canjawa
number yaje da ita zance.
Mummy kawaye sunyi anko ana ta raba Iv kamar matashiya,Rafeeq ne yaje har gida
ya samu Mummy taci gayu zata fita,ya kalleta suka gaisa yace Mummy duk cikin Yan
uwanki kece bakya tsufa,kullum kyau kike yi dole ki samu miji da wuri,Mummy taji
dadi tace ko Spark baya kaunata irin Rafeeq.

Yace Mummy duk kawayen ki Yan mata ki gayyato su da zawarawa masu saukin
shekaru,zamu je mu rufa miki baya,har walima zamu hada ranar da zaki tare ni da
Misam,zamu dakko wata shaharriyar Malama zata yi chaji ranar ta koyawa mata kula da
miji,Mummy tace Kai kuwa Allah ya muku Albarka na gode Rafeeq.

Yace Mummy Allah ya Bada zaman lafiya kiyi Maza kiyi wa Spark kanwa ko
kani,Mummy tace kani dai ai gwara na fara da mazan sunfi,Rafeeq Yana ta zugata ya
mike zai tafi tace tura min accnt number Dinka,ta bashi dubu dari nan take,Rafeeq
yace Allah ya biya Mummy sai munje gidan Basiru Kusa ni zan Kai Amarya,Mummy tace
wannan yara da abin dariya kuke ka gaida gida dai,ya fice wajen kawaye wai shawarar
Dinner suke,shi kuwa Rafeeq ya tafi wajen Naila neman Chika za a gayyato Malama.

DAN ALLAH KAR A FITAR DA LITTAFIN NAN.

A dinga sharhi,idan ba ayi ba posting.

Masu Sharhi Ina matukar godiya.


AsmaBaffa
[12/30/2023, 11:50 PM] AsmaBaffa: PAID GROUP 300

ACCNT NO
0175487861
ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK

YAN NIGER
+22790795939

🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

BOOK 1

96-100

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM

Page naku ne

Uwar Batoola
Hafsa Abdullahi
Hajjafatty
Hajjora Investment

Follow this link to join my WhatsApp group:


https://chat.whatsapp.com/LAizQA6PofSLoFhQ7XeaQx

Ina kuke masu burin suga sun kawata gadajensu da hadaddun bedsheets? Ko Kuma
blankets kike nema? Masu aurar da yara ko kannai da ke kanki uwargida indai kitchen
utensils kike bukata
To kukanki yazo karshe.kuyi joining group din R&U exclusive kitchen and more
Ku more wa idanun ku da kayan kitchen Yan yayi na gayu da zannuwan gado na kowanne
kasa Zaki samu acikin farashi Mai sauki
Kuma Maza Bata barku abaya ba idan Kuna bukatar a hada muku lefe nagani na fada na
amarya Kona uwargida wato na fadar kishiya duk Zata hadamuku acikin kwanciyar
hankali.idan ma akwatunan kawai kuke bukata duk inkuka tuntubi Rumaisa zaku ganewa
idanuwanku
Tana Kano state Kuma Tana tura Kaya kowanne state afadin nageria harma da kasashen
da muke makwagtaka dasu
Zaku iya tuntubarta ta wannan number
07034559202

Naila ko Dan baccin wahalar data fara sai mafarkin Spark take yi ya rike ta Kam
sai ya sake yi tana ta ihu,ihun mafarkin Naila har a zahiri Spark yaji ta kwala
ihu,ta mike zaune a firgice tana kuka a mafarki Ashe har a gaske kukan take
yi,farkawa yayi ya kunna light yace mene? Mugun mafarki nayi wash Allah ashe bada
gaske bane bacci kake yi ma Alhmdllh,wani Abu ne ya sameni a mafarkin? Naila tace
ba a fadar mafarki kar ya faru a gaske abin, kwanta kawai,Spark yace ke ai yanzu
tsoronki baya wuce sex,Abu sau biyu kacal duk kin takura,sau Daya Kullum kacal amma
duk an rasa gane kanki,Naila tace baza ka gane bane wannan abin Dan banzan zafi wlh
gwara wata azabar da wannan kalar,haba ai gwara kunama goma su cije ni,tunda nasan
zafin kunama,to gwara goma su cije ni,Spark yace wai wanne magani kika bani ne?
Naila tace wani magani ne nima bani aka yi,yace Ina so Dan Allah ki Kara min,a Ina
ake siyarwa? Naila tace ban sani ba nima sadaka wani ya bani,bafa Sha zanyi ba na
rantse,Naila tace ai yanzu Allah Daya zaka fada min na yarda akan dai wannan
kwalbewar taka bazan taba yarda ba,anjima kace aljani ne ba Kai bane,dariya yayi
yace to shike nan,zauna muyi Hira tunda mun tashi,Naila tayi kwanciyarta,da sauri
yace ahhhh....ta tsaya da sauri yace mene haka Kuma zaki juya min baya haka aka
ce ,shine Kuma sai ka tsoratani kayi Kara,Rahmar Allah nake nemar miki,kullum sai
Lada nake sawa kina samu,Ana ta kisan arna,da gobe ma zaki bari ai da an kashe na
Yahudawan England,Naila Kwanciya ta gyara a jikinsa,Tashi yayi yace kin tuna min da
wani aiki wlh,laptop dinsa ya jawo tare da kunnawa ya zauna a gefen bed,yace kwanta
kiyi baccinki.
Tace nifa Ina Nan ba Wanda zai danna waya ko wata laptop Malam,ka gama Shan dadi
ka jawo wata laptop wlh baza kayi aikin ba sai kace Dan Yahoo,dariya yayi yace
aikin Office dinne fa kudi zan samu,tace a hakura da su,ko ke da kudin Nan zasu
kare watarana sai munyi fada,kince na kawo nace babu, kina gajiya zaki fara min
tsaki.

Naila tace ai da Office din kake tafiya ka yini a can yafi,murmushi kawai yayi
yace kina takura min zan tashi nayi maganinki,Hajiya Naila Tantiriya, dariya tayi
yanda ya Fadi Sunan,yace ana taba ki sai kuka,Abba da yana ji ya isa ya jiyo
kiransa da kike yi,Naila kamar mage ta dawo jikinsa ta kwanta,ta dauki wayarta,tace
bari nayi tsokana,Mohsin ta kira,kira yafi goma bai daga ba,tace to maye yanzu haka
ana can ana ta kokawa da Nono,Spark yana dariya yace kamar ba Yayanki ba kin takura
Masa,Naila tace Yana ta min masifa,yaki dagawa,kafin ta rufe baki ya kirata back,ta
daga tace Yaya barka da dare,lafiya da tsohon dare haka? lafiya Lau dama kira nayi
nace Yaya Amaryar, Muryar Beauty taji tace kalau nake munafuka,Naila a ranta tace
wallahi Beauty ita dadi take ji ni kuwa zafi to wai ya haka ne ni.

Yaya bawa Beauty wayar, ya mikawa Beauty ta karba,Naila tace karki sani a
handsfree ki rage karar waya,Beauty ta rage volume,Naila tace to ya Sweet
din,Beauty tayi dariya tace ai ni ana min sau uku na warke na dawo Jin dadi,dama
karya kika yi mana kika ce da dadi ashe sai zafi,tace ke dalla banza ai sai anyi
sau uku,duk zafin da kike ji indai ya dawo ki yarda daga shi shike nan sai
dadi,Naila tace kin tabbata? Serious fa nake fada miki,shi yasa ko addua ake cewa
ka maimaita sau uku ashe shima haka,Beauty tace kwarai kuwa ki tambaya kiji,amma da
farko dai boye miki nayi yanzu na fada miki gaskiya amma Dan Allah karki fadawa
Chika,kawai kice da dadi,Naila tace yaushe zan fada ai wlh sai kowa yaji a jikinsa
shima ko wace ba wacce zan fadawa gaskiya,Mohsin ne ya karbe wayar yace wai ke Ina
mijinki ne,auren Nan kuwa kina bin dokokinsa ma kuwa,Naila tace to ba an gama ba
munyi da wuri tun dazu na Hana shi ne da zaka ce wani na dameka, na daina kiranka
ma,Mohsin yace indai kiran dare ne karki Kara bana so,bacci nake kika tashe ni,ba
wani bacci idan bacci kake na dige wlh ba bacci kake ba nasan me kake yi kayi shuru
kawai kar na fada,Mohsin dariya kawai yayi yace laifi nane da nake wasa dake ya
kashe wayarsa.

Spark har ta gama Yana aikinsa,tea yaje ya zubo a kitchen yasan yanzu ko yace
taje ba iyawa zata yi ba,cup biyu ya hado ba Madara yasha hadin su Na'a,Naila ta
kurba tace waye yace ka dinga Sha sai ka Kara karfi kazo ka kasheni,ka kiyayi
gargajiya ba kyau,dariya yayi yace kefa kika dafa da kanki a flask na gani,to daga
yau ya haramta a gidan nan,yace danyi hugging Dina ta baya,Naila sai Gani yayi har
ta koma ta kwanta tana lulluba da bargo,shayinsa ya shanye ya kashe laptop din ya
kasa aikin ma.
Cikin bargon ya shige shima tare da kashe light,jikinsa ya jawota ya
rungumeta,tana jin Hallare a mike,tsoro ya kama Naila ko motsi bata yi a haka bacci
ya kwashe su.

Washe gari Rafeeq gidan Spark yazo,Naila ana kwance an cakare da gayu cikin
Leshi, an zurawa tv Ido a zahiri a zuciyarta Kuma ba kallo take ba tsoron yau take
yi kawai,tana nazari shekaran jiya Spark yayi,jiya ya sake yi watakil anjima ma
yace,a ranta tace ni naga maganin kaka ganin Ido na.
Har Rafeeq ya shugo Bata sani ba sai da ya buga Jikin kujera sannan ta kalle shi
da sauri,yace lafiya kuwa Naila? murmushi tayi tace lfy mana me ka Gani? ta mike ta
zauna a gajiye,yace ba komai kina ta tunani ke kadai ne ai har na gaji da Sallama,
kallo nake ban ji ba,Ina Spark din? yanzu ya fita zaije gaida Mummy,Yace okay, me
yake damunki ne yanzu naga bakya kiriniyarki,kallonsa Naila tayi tace amma kasan ni
yanzu Auntynka ce tunda yayanka nake aure,Rafeeq yace to sannu Aunty ke kanwata ce
ta nawa,Number Chika zaki bani.
Wayarta ta jawo a gefe ta bashi number Chika,yace me kika dafa ne kin San ni daga
School nake,Naila tace ai kuwa anyi Baki Yan ganin Amarya sunzo saura na Spark Yana
kitchen,yace idan yazo kice na cinye,Naila tace to.

Yana shiga kitchen din yaga wasu miyagun flask shi kanshi sun birge shi sosai an
jere su da wani glass bowl,ya bude yaga wata farar shinkafa,ya bude dayan yaga nama
anyi farfe su,ya bude dayan yaga stew tana ta kamshi,bowl din ya bude yaga salat ta
zana love da tumatir din data yanka ta jera su sun Bada love a tsakiya,Rafeeq yayi
dariya yace wato mu sai an nuna mana iyakar mu gwauraye,abincin ma Yar kwalliyar
baza ayi mana ba a girki,fridge ya bude yaga fruits duk ta
yanka,kankana,Apple,Abarba,gwanda suma duk da wani abin yankawa me Bada shape na
love ta yanka,gashi komai Dan dai dai mutum daya,Rafeeq yace kauna ya dauki pics
sannan ya ebo abincin ya zauna ya cinye tas Naman kawai ya rage ya turawa Spark ta
Whatsapp yace kayi hakuri ga girkinka nan na cinye love din da aka zana Maka ni
kam,Spark ya duba ya gani love din ya kalla kawai yaji haushi an bayar da
abincinsa,Rafeeq Yana gamawa ya mike yace idan yazo ki gaishe shi,Naila tace to a
gaida school yace zata ji ya fita.

Bai dade da fita ba Spark ya shugo,gaban Naila sai da ya Fadi,tsokanarta yayi


yace to tashi muje Duty,a kasa tayi sauri ta durkusa tayi kneel down tare da daga
hannaye tana rokonsa Dan Allah ka bari na warke,muje asibiti a baka maganin
control,wlh ban San Kaine Ashraf ba na bawa Chika ta saka magani a abinci Kaci,sabo
da na kashe ma Hallare Dan na rama akan Dan Mummy ashe Kaine,sanda nazo gidan Nan
magani nazo nayi Maka ka warke da na gane Kaine, Spark yace wai Nan nufinki ramuwar
Nan dama da kika ce zaki huce a kansa ita kika min? Naila da sauri ta daga Kai tana
hawaye tace itace wlh ban San Kaine ba,Chika ma Bata San Kai bane sai da ta zuba
Kaci,shine maganin baiyi aiki ba akanka ba tunda Kai Hariji ne sai da kayi aure
ranar farko anyi Nisa sai Hallare ta daina motsi dama to nazo da maganin ciwon
shine na baka ka Sha,Shi yasa baka iya hakura haka Dokar maganin yake Dan Allah
muje asibiti a baka na control,Spark yace to ai ni wannan gata kika yi min ,a rage
min sha'awa na Saba a haka ni godiya nake wanne course ne wannan? Naila tace ban
sani ba,makaranta zan biya miki ki karanta shi sabo da ni,murmushi tayi tace a'a da
sauri.

Okay Kaka ke badawa na tuna shi kika bawa Mummy kenan ta bawa mijinta? Tace nashi
kalar daban ba irin naka bane,yace Ina irin nawan? na zubar da su a shara wlh yau
da safe,Spark ya tafi wajen Dust bin Yana dubawa duk ta zazzage magungunan daga
ledar ta zubar ba dama a samu,yace sabo da me kika zubar? Zafi wlh azaba ce ta yi
min yawa mene amfaninsu,yace to ai wajen Kaka zamu je a karbo na control kin San
hakane Baki fada min ba,sai ai a nemi magani idan na miki illa fa,Naila tace illa
ai an Dade da yinta,ai kuwa gobe tafiya wajen kaka ta kama,amma yau dai kafin goben
Kuma sai kin sake hakuri bazan iya kwana da yini haka ba,kinwa kanki ba ruwana kece
kika yiwa Kanki.
Naila ta zauna tana sharara uban kuka,rungumeta yayi yace nima zanyi kuka Spark
harda shesheka,tace bana so Allah,yace Ina so Allah akwai dadi,kina fara Jin dadi
sai nayi yanga kafin na miki,Baki ta murguda tace wani dadi za a ji a wannan
azabar.

Alright it's okay kinji bazan yi ba sai kin warke Inshaallah bari ki gani ma,a
gabanta ya dakko ruwan ya Sha maganinsa da ya karbo wajen abokinsa Doctor,sabo da
yaga Naila tsoronsa take ji, sai da ya Sha sannan yace Ina abincina? Kanin ka ya
cinye,haka akeyi sai a dinga bayar da abincin me gida? wayarsa ya dannan tare da
nuna mata pics din abincin yace sai ki bayar a cinye min love dina,sai a dafa wani
ai tunda yau ba Kwalbewa ai komai me sauki ne.
Abincin ta dafa Masa me sauki,yace kar a sake bayar min da abinci,kannenka ne fa
na isa na hanasu abin yayan su,yau Naila taci sa'a ya Sha magani baiyi komai
ba,haka ya sake kwana na biyu baiyi ba,kamar zaiyi hauka haka yake ji,amma yayi
alkawari sai ta warke zai Kuma,Naila an saki rai taji sauki sosai har na kwana
uku,an daina tsoro, ta zaci aikin magani ne shi kuwa Spark ya Kara da hakuri ba ya
shan magani,sai aikin kallonta kullum Yana taba ta yasan baza a kare lafiya ba,shi
yasa yake dannewa, ganin ta sake a gidan yau ta fara wankan kana nan kaya,tasa wani
tight black,sai Yar riga me siririn hannu wacce ko cibi bata rufe ba,gashinta da
yake ta tsayi ta gyara ta kama sannan ta fito tana fitowa,ya shugo gidan, wow taji
ya furta, Naila harda canja tafiya,tana tafiya chakwas Chakwas a gabansa ta tsaya
ta juya harda yin tafiyar sarauniyar kyau,Mayen har ya susuce, bayan ta juya tace
ya ka Gani ka ci sadakinka,dariya yayi yace ai tun a daren farko na cinye sadaki na
yanzu Riba zan fara dorawa daga nan wlh har Ribaa sai naci, waist dinta ya kamo
tare da mannata a jikinsa,Mummy ta sake zuwa tana knocking,Spark yace ai Kuma na
shiga uku Dan dadin ma baza a bari naji ,wayarsa yayi connecting da Speaker kawai
kunna kida,yace a rayuwa ba a barina na huta da iyalina,Naila tace bari na saka
hijab,yace bari na duba idan macece ko wacece ba wani Hijab,kinyi kyau Ina son
kallon matata a hanani sakewa, lekawa yayi ta Yar kafa ya bude kofa Mummy ta shugo.

Naila harda durkusawa Ina yini Mummyna, Mummy wata Harara ta watsa mata tace da
ban yini ba Kya ganni Fitsararriya,Naila ta share tace Ashe Kuma haka abin Alkhairi
ya samu an samu miji Allah ya sanya Alkhairi,Allah ya Bada zaman lafiya,mun kusa
yin Kani ko Kanwa Baby ta dafa Kafadar Spark,tace Inshaallah namiji ne na farko,
Spark Mummy ya kalla yaga har wani murmushi take yi,ta Kalli Naila da kulawa tace
Yar Nan ya gidan? Sabo da ta yabi aurenta,fatan dai kalau kuke zaune ke da Mijin
naki,ai na ganki ma da lafiyarki,Naila tace kayya Yar lafiya dai Mummy,karfin hali
nake kawai,Mummy tace zaki Saba ne duk da haka muka Saba,Spark yace Mummy wai mene
haka,yarki ce fa,to kunya ce take cutar mu hausawa baza mu dinga sa yaran mu a
hanya ba,Mummy na magana Spark Yana can bai ma San tana yi ba ya kafe Naila da
kallo.

Mummy ta kalle shi kawai ta Kalli Naila Dake ta faman Masa fari suna ta magana
da Ido ba Wanda ya sake kula Mummy, Naila ce ta mike ta kawowa Mummy kayan motsa
baki,Mummy ta kallon su tace nifa kuyi hakuri Mima nake jira biki saura 2days zamu
je Inda za ayi Dinner shine nace mata mu hadu a Nan,Spark yace ai da daga bakin
gate kika jirata zata fi ganinki,to a Nan nayi niyyar zama,Spark shuru yayi yace da
Naila zo ki min tausa,Mummy tace wlh ba a gabana ba wanne irin iskanci ne,a kanka
aka fara aure wai wannan wacce Maita ce haka,Naila ce ta tashi ta shige bedroom ta
barsu suyi hirar su, tana tafiya Mummy tace to ai sai idonka ya huta ta shiga
bedroom,karfa ka kashe musu yarinya ka dinga bi a hankali,ba haka ake yi ba,ka
dinga daga kafa please,Spark bayan kunnensa ya daga kawai wai ta wuce ta Nan,duka
mummy ta zuba Masa a baya tace wato baza kaji ba,Yace na ji mana tundan Ina jin
abinda ake fada.
Mima ce ta shugo,Spark yace Mummy ga yayarki nan tazo,Mima ya kalla yace tun
dazu kanwarki take ta jiran ki,Mima tace ke taso mu wuce sauri nake yi,Spark yace
ai gwara kuje dare Yana ta yi,shekaru sun ja kar duhu yayi ku kasa Kai kanku gida.

Kofa ya bude musu yace ku gaida gida ya rufe kofar ya dawo,,Mima tace ni wanna
ko ayu na Haifa ne,wannan jaraba haka,Mummy tace akan wannan Yar iskar Yar Fulanin
dajin duk ya zauce.

Naila ya kira Honey.....Naila ta fito tace nifa bana son wani suna sai Baby,ni a
soyayya idan ba a ce min Baby ba sai naji kamar wata gardiya Allah ta furta da
shagwaba,dariya ta bashi wato sabo da ya kyaleta ta huta taji sauki shine take
faman wannan salon sabo da ya rantse sai tayi 7days,gashi just 3days aka yi ya gama
sarewa,Jawota yayi ta zauna a cinyarsa,tace ka Sha maganin kuwa? Yace na Sha
mana,Naila taji dadi,Bata San sau Daya ya taba Shan maganin ba,har bacci yake kasa
yi sabo da jaraba,jiya Sallar dare ya dinga yi.

Naila ya kira Babyyyy....tace Na'am dama yanzu nake cewa gwara nayi azumin
kaffarar nan bazan iya hakuri ba,ki tausaya min,Naila mikewa tayi daga jikinsa ya
sake fisgota ta fado kansa,tace Dan Allah kayi hakuri na warke wlh ban warke ba,ko
mene zan Maka ka kawo sai a barni na huta,yace nooo ni gaskiya a'a,wannan ba matter
ce ta boyfriend and girl friend ba Baby,matter ce ta aure,Naila ta saka kuka tace
ni shike nan bazan yi walwala ba,Spark yace wannan ai itace walwala da shanawa
Baby,ki tsaya ki nutsu Dan cikin Nan na zamani kema ki samu bakya ganin yayinsa
amare suke yi,ko wacce ki ganta da cikinta tayi kyau abinta,Naila tace cikin ne ake
wani kyau ni wlh bana so zafi,Baby abin nan...ehmm...Yama sunanta Hallare din Nan
taka bata wasa bace,tayi girma da yawa.
Spark ya jawota Yana lallaba ta,Naila tace ni dai zafi a canja salo,Spark yace
okay indai Style ne ai sai a canja,amma fa wannan shine kawai me saukin,Naila tace
ba wata hanya? Kaga dadin duwawu kenan guda biyu ko Allura za a yiwa mutum idan aka
yi a Nan barin sai gobe a canja Daya side din,Spark yace wannan hanya Daya ce Dodar
daga Channel har cikin gona.

Kamar zaiyi mata kuka ya marairaice tace ni ya zanyi idan na mutu shike nan ka
huta ai,nidai bazan gudu ba ato kaina akwai tauri ba Inda zanje in ka tausaya min
ruwanka,Spark yace zanji Tausayin a gaba,muje ke da zaki samu Lada idan nayi mu
karkashe arna,mikewa yayi yace muje Babyna,Naila ta fara tirjewa ya rike hannunta
tana tirjiyewa tana wash zafi....ya wani marairaice shike nan tunda so kike na
mutu,ya rike mararsa Yana Kara,Naila tace muje amma da ka bari ko Juice mun
Sha,yace akwai babban Juice Allah ya miki shi na sha wannan, Naila tace Juice Baby
yace so sweet muje na Sha a ciki.

Idonta ya ciko da kwalla ya tasa keyar ta gaba har bedroom,tace ni yau a zaune
za ayi nafi Jin sauki,yace ae zai fi sauki kuwa,suka tafi suna shiga ciki,Naila
tace irin waccen zafi a canja wani,yace zabi da kanki tace Ina laifin ma bend down
ai zaifi,yace ki dai zaba karki ce na cuce ki.
Naila tace gwara nayi bending down tsaya daga nan,Spark yace shike nan Kuma daga
zuwa sai afkawa tab ai sai Juice din ya fito,Naila ta zura Masa Ido tace tace Kai
Spark duk taurin kaina dole na fara guduwa kwana uku kacal hutu,Spark yace wato ma
banyi abin kirki ba ko?

Magriba tana
gabatowa kayi kayi,Spark yace kina tsaye a Jikin Kofa Ina gefen bed kina ce min
nayi nayi,karasowa tayi a tsorace tace ni bana son abin nan ka hana Kuma a tsaneka
ko wata kwartuwar me rariyar Bado tazo ta tayi gaba da mijin,.
Spark fushin karya ya yi yace na hakura na fasa jeki kawai ya ci Magani,Naila
tace sorry,kin kulata yayi,hannunsa ta rike tace nace kayi hakuri zan yarda,yace
you sure? tace ae a'a ae,tsaki yaja yace to jeki,Naila tace na tabbatar na yarda
100%.
Oya come....Naila taje tace su Hallare manyan arna kune da garin,dariya Spark ya
danne,yace zo kiji Yan matan Abba Yar budurwata,Naila tace Ina wata Yan mata ni ka
daina yaudarata ka gama ragargaje waje kace Yan mata,Budurwa yan matan wa,duk burwa
ta kirki haka Badonta yake? tsakani da Allah haka yake? ni nawa haka yake da Sanda
Ina gidan ubana,karka sake ce min budurwa na wuce ajin budurwa,kana zubar min da
mutunci,wahalar da Nasha budurwa ta Santa ne indai ta kirki ce,sai ka dawo kana ce
min budurwa kana rage min daraja,duk budurwa aka ganta da namiji ba sunanta Karuwa
ba,Good House wife ce ni,kullum sai an rubuta min Lada kala kala.

Tana surutunta ya jawota jikinsa ya da wayo da wayo ya rinjayeta suka fada


romancing sosai,Naila ta kawo wuta da wuri,tana cinyarsa suna facing juna duk ba
kaya a jikinsu,tuni ya raba su da kayan,Naila taji dadi tace yanzu abinda za ayi
dadin Nan fa bazai yuwu ka dinga kwashewa ba ni Ina Shan azaba na daina kunyar
nan,Ka samu bado ka goge shi tas da Hallare bada cewa nayi ka shiga ba ka gane ai
yanda kake min wayo sai kayi ciki to ba haka ba uhm uhm yanzu sai naji dadina tukun
sai Kuma mu tafi wajen kukan,Spark ya dinga dariya yace kin samawa kanki mafita
kenan,a ransa yace zaki bayani,Yanda tace haka ya mata da kanta tace ni ka shiga ai
kuwa Spark dama shi jira yake Yana shiga tun kafin ma ya karasa ta fara ihu da
kuka,ai ba style din nan nace ba me sauki nace ayi min,tana ta faman ture shi tana
kuka,Dama ya kwana har uku baiyi ba,ai kuwa yau ma ta fadawa mutanen garinsu,jego
ya dawo sabo Dan wannan karon da kanta ta gudu ta canja daki,ta kulle da key,Spark
yace Inama kin tsaya da yau wlh har second round Dan ni yau abin ma yafi na
kullum,Naila kuwa tana kulle kofa tace Ina na sauke taurin Kai,baza ta sabu ba,bari
in kira kaka kawai a San yanda za ayi,Wayar Kaka ta kira Yana dagawa ta fashe da
kuka,ta hau bawa kaka Labarin tun zubawa Spark maganin sha'awa da suka yi har zuwa
first night,Kaka yace me yasa tun farko baki fada min ba,ai ba wannan zaki bashi
ba,kinyi ganganci amma sai dai kiyi hakuri ko magani ya sake shi mijinki haka
yake,idan ba jarababbe bane to da kina zuba Masa wannan na farkon zata daina aiki
ko motsi amma tunda kika ga haka ai jajirtacce ne Naila,Banga abin damuwa ba.
Naila tace kawai Dan kana namiji Kai kaka me ka sani ma a duniyar,yace to kuwa
dole gobe Goggo tazo gidan nan tunda bakya Jin magana.

Spark ranar shi kadai ya kwana,washe gari bai ga Naila ba ta buya,har ta sake
kwana na biyu duk ya damu gidan ya Masa zafi ya rasa Inda zai sa kansa,yaje yayi
yayi ta bude taki,Goggo ya kira a waya ya fada mata komai,Goggo tace in kaso ma
gobe zanzo garin,ai Kaka ya fada min ,Spark yace Goggo gobe tayi nisa tun shekaran
jiya da ban ganta ba,Goggo tace in ka sa tsiya zan fasa,yace na hakura Allah ya
kaimu.

Duk da haka Spark Mohsin ya kira dama dake mazane ya goyawa Spark baya,ya kira
Naila tana dagawa sai masifa bani ba ke tunda baki San me kike ba,Ina soyayyar taki
da kike Masa? Naila tace ta Kone kurmus na kankare kanzo na watsar,wai da zaka ce
Lallai na hakura kana da Badon ne ko naka ne jikinka ne,ku kyale ni na huta na
warke wlh bazan iya ba,Bana warkewa ake sake yi ni baza a tausaya min ba,Mohsin
sakkowa yayi ya dawo lallashi da kyar ya shawo kan Naila ta bude kofa ta leko a
hankali,Ido biyu suka yi da Spark.

Suka tsaya suna kallon juna sai kace Wanda suka Shekara basu ga juna ba,tace
Ina sonka Baby Dan jikinka gwanin birgewa kamar kar na daina kwanciya amma Hallare
ta hanani naji dadi,ana ta Amarya Amarya amma Kuma Amarya Ina, yace kin fiye
gaggawa sau nawa aka yi kwata kwata uku kacal amma kece kike complain,har 3days
nayi ban taba ki ba good 3days kawai dan ki huta,ba wai Dan bana so ba fa, karki
tunanin magani nake Sha na iya hakura,ba maganin da nake sha,Naila ta kalle shi
tace to ya zanyi yanzu dai Kaji haushi? Juyawa yayi zai tafi ta rike shi da sauri
tace I'm sorry,wlh Ina so kaji dadi kasawa nake yi zafi,Spark ga saurin fushi yace
yanzu dai akan haka kike kulle kofa kina buya? to ki daina ki sakata ki Wala kiyi
amarcinki.
Naila tace to ayi amarci haka ba Yar tabe tabe,ta bashi dariya kawai ya danne
yace a'a kiyi ta hutunki,kawai ya wuce bedroom dinsa ta biyo shi,fushi kayi wai?
akan me? Dan Allah ki rabu Dani,abinci Yana Kitchen kije kici to ki daina buya kina
dakko drinks kina sha indai Spark ne bazai Kuma taba ki ba,Naila tace ahhhh to wa
zaka taba me kake nufi?

Files ya kwaso da yawa da laptop ya dawo Palo ya zauna da biro Yana ta


aikinsa,duk da Yana so ya shareta amma aikin ma ya kasa yi sai dama dama yake.
Yana kallonta taje tayi wanka ta chakare cikin riga da skirt na atamfa ya mata
masifar kyau Sabuwa gal na lefe tana kamshi ta fito,ta wuce kitchen harda Jan
gashinsa ba tare data waigo ba tayi gaba,ya bita da kallo har ta shige kitchen ya
kasa dauke idonsa.
Take away ne lafiyayye ta zauna tana ci tana kallon film,har ta cinye abincin bai
kalleta ba,abin ya dameta sosai Yar yabawa ba ayi ba,Baki ta turo gaba tayi
tagumi,yaki kulata har wayarsa ta hau Kara,ya duba yaga Mummy shi ya manta ma gobe
Dinner, ya daga Dake yau anyi fada da Amarya ya tsaya ya Dade suna ta hira da Mummy
harda dariya,tace gobene dinner saura kaki zuwa,Yace Allah ya kaimu,tace jibi
daurin aure da Kai Amarya,Spark yace da tariya dai wanne Kai Amarya Kuma,Mummy tace
to da tariya tunda Kai komai nayi ban iya ba,yace Allah ya kaimu.

Yana waya bai ma San Naila ta dawo jikinsa ba ta Dora kanta a kafadarsa,ya
janye kafadarsa,yace mene haka yanzu ina tabaki ki fara kuka ki daina zuwa jikina
ki rabu Dani ki huta,hutu kike bukata na takura miki abeg you ki huta abinki, Naila
tace shike nan daga naji zafi na nemi hutu ba uzuri ba komai,har yaushe aka kawo ni
gidanka,ban San kowa ba a garin Nan bani da kowa nace Ina sonka naji na Gani aka
baka ni shine kullum Ina yarda Dan kawai na nemi hutu naji tsoro na buya sai kaji
haushi ko sati ma sai gobe zan cika sati a gidan Nan amma har ka fara nuna
min....ta fashe da kuka....tausayi ta bashi yace to ba fushi nake ba so nake na
baki space ki huta ki daina Jin tsorona kina kulle kanki a daki ki kwana ki yini
baki fito ba,idan akace nine silar Hakan ai bazan ji dadi ba,nafi so kullum muna
cikin farin ciki,nasan Ina takura miki da takura shi yasa tunda ta Kai ga haka ai
ya dace Kuma na hakura ko da zan cutu,idan nace normal zamu na romancing etc bazan
iya hakura ba ne,Kuma ni ba fatana ko yaushe naga kina kuka ba,bana son korafi
ni,Ina zuwa kullum sai munyi jayayya munyi kokawa an Kai ruwa rana ina dalili
Naila.

Naila tace wannan tace wancen yace shi ba haka yake nufi ba kawai ta huta shi
dai bai sake tabata,ta damu iya damuwa,har ya gama aikinsa sai wurin 11pm ya gama
aikin tun 8pm yake Abu daya,sabo da kar yaje kwanciya ma yaji Yana son sex.
Naila taje tayi Shirin bacci ta fito tana ta jiransa tana Jin bacci taki yi,shi
take jira kawai har sai da ya gama.
Yace tashi mu tafi tunda baza ki kwanta ba,zata wuce gaba yace tsaya a baya tabi
bayansa suna shiga bedroom ya kashe light tace da kayan jikinka zaka kwanta yace
ae,ya kwanta ta kwanta kowa a gefensa yace karki dawo jikina Kuma kiyi ta hutawa.
Naila a ranta tayi dariya sai nacin fadar tayi ta hutawa yake wannan ya tabbatar
haushi yaji.

Yau da kyar yayi bacci,ita kuwa bacci me dadi ma tayi,ya sake Jin haushi ganin
har makara tayi,da sauri ya shirya ya wuce Office mutumin da ya dauki hutun 2mnths
ko sati daya tal ya dawo aiki.
Naila tace Office ya tafi ban sani ba,wannan anyi Hariji ya dawo ya dinga ta yi
ya zanyi zan daina kukan,haba daga Dan Abu.

Aikinta ta gama ta karya ita daya ta gyara bedroom dinsu sauran kuma Yan aikin
suka yi,tana zaune da guntun wando Short da Yar riga tana kallo sai ga Goggo,tace
Ashe da gaske kaka yake yi,ta bude kofa Goggo ta shugo da Leda viva ta magungunan
gargajiyar su,Naila tana ta murna Goggo tazo tace Goggo zauna, Goggo tace Naila
rashin kunya timbir haka,Naila tace ai Dan kece da wasu ne kafin na bude ai zan sa
Hijab,taje ta kawowa Goggo kayan Kari ta hada mata shayi me kauri ta soya mata kwai
da dankalin turawa,Goggo ta cika cikinta taf sannan ta gyara zama,tace gidan Nan
yayi Naila Ina zamu bari wata ta shugo idan ba kaddara ba,Naila ki rufawa kanki
asiri idan ba so kike mijinki ya fara neman mata ba.
Naila tace Goggo wlh da zafi,ga abar katuwa,Hallaren tayi girma Goggo
zafiiiiiii,Goggo tace to ai shine abin so Naila,shine cikakken namiji Wanda idan ya
kira sai an amsa.

Mata nawa akan ta mazajensu karama ce suka gudu suka kashe aure,wannan Naila
itace take kashe auren mata da yawa suke tafiya neman me babba,ita ake so,a hankali
zaki Saba,duk muma munyi da haka muka Saba,Ina fada miki zaki ji dadi Nan gaba
kadan,ki kwantar da hankalinki ki daina raki da kwailo,Maza basa son korafi.

Haba Naila Ina ganinki me wayo jaruma,da yawa suna Jin zafin kafin su Saba amma
suna jurewa su hakura ba kuka,ba korafi ba tashin hankali da kulle Kai a daki,idan
kinki ji Kuma Kinga mijinki dai irinsa mata ke nema matan banza suna Nan a
gari,wata zata kwace miki miji a waje ko ya fada neman mata ko ya miki
kishiya,Naila tace Allah Goggo? Goggo tace ae Naila ko so kike wata tazo ta shugo
wannan kantamemen gidan Wanda bama fata.

Ki rufa mana asiri ki rufawa Hashimu Dolo asiri Naila,ki bawa mijinki abinda
yake so,wannan cinyoyin Naila ki dinga bude Masa,idan yace ki bude ki bude,uban
mene a bado din nan ne haba Naila Ina zaki bamu kunya ki Bada mata,Ki daure idan
Yana so ki jefe shi da Badon nan Naila,Goggo harda tafa hannaye tana mika hannaye
tace ya Ilahi kukan uban me zakiyi Naila,Ina ganinki kamar wayayya ashe banza ce
raguwa,duk tashen da kika yi Naila,duk gidan yarin da kika je kika Sha wahala sai
ta bayar da Bado ce kawai zaki kasa,idan kika fara Jin dadi wala'allah sai kin
fishi naci,Naila taji fadan Goggo tace yanzu Goggo sai ya min kishiya? da gudu ma
kuwa,dama kishiyar ce da sauki neman mata nake jiye miki Naila.

Kinga tashi muje Dan ubanki yau Dan iskan Badon sai ya warke muje,Naila tace ai
fa naji sauki bai Kai na farko zafi ba,Goggo a na karshen nan da kaina nace ya
shiga sai naji zafi Kuma ban San nace ba wlh dadi ne ya kwashe ni,Goggo tace ai kin
kusa ma Naila ki daure kadan kinji,idan ya dawo ki lallashe shi ki bashi ya samu
nutsuwa,ba na so yasan nazo ma,Muje kitchen a fara tafasa wannan zama zakiyi a
ciki,suka tafi da Naila, taji kishiya duk ta rude.
Ranar yini Goggo tayi tana gyara Naila,ta sa ta shiga ruwan magani ta zauna,ta
Bata wani ta Sha,ta nuna mata yanda ake yi sosai zuwa 3pm ta bar gidan ma ta tafi
gidan wata Yar uwarta a Nan Suleja gobe da safe ta koma kauyensu,Naila ta Bata
kudin mota har da na kashewa da na kaka ma.

Kafin Spark ya dawo gida ya dau kamshi ta ko Ina,ko wanne lungu da sako sai da
ta turare ko Ina,da kuwa indai Yan aiki basu yi ba baza tayi ba sabo da kukan
wahala da take yi bata hasala abin kirki,yau kuwa toilet dinma kamshinta daban,tazo
tasa waya a gaba ana tsara girki ta gama kwalliyar girkinta da love da wacce
tsiya,5pm take tunanin dawowarsa ta sani tun tana gida yace 5pm yake dawowa,amma
tace nasan fushi yake yi bari na bari idan nayi Sallar magriba sai nayi wanka,Sai
da tayi har Sallar Isha bai dawo ba.

Taje tayi wanka ta saka wani guntun wandon fari da Yar riga me gajeren
hannu,gashi ya Sha gyara ko Ina kamshi take yi,tana gama ta nufo Steps Yana
shugowa,mamaki tayi ganinsa da wata shigar daban wacce ba da ita ya fita ba,Shadda
ce me tsada ya saka wata ita ba fara ba ita ba golden ba,ya shugo Yana
kamshi,wankan na daban ne wannan,lalacewa tayi tana kallonsa,yace wai Baki shirya
ba? tace Ina? Dinner din Mummy,Ina Amaryar zanje Dinner,satina Daya fa yace to me
kike a gidan,ki shirya mu tafi kawai idan kin zauna ma me kike yi,ga Abinci to Kaci
kafin na shirya,yace na koshi ni,tace wai mene haka Dan Allah,idan na dawo zanci
to,tace to ta juya ya fisgo hannunta ta dawo ya rungumeta yace ko a fasa ne? tace
muje mana Mummy guda tana aure,sama ta haura ta fara shiri kamar itace
amaryar,tasan bazai kaita make up ba baya so,da kanta tayi tare da daurinta,ta zabo
Leshi kalar shaddarsa,tayi kyau sosai da sosai,sai yaji baya son ma fitar Sam.

Amma haka ya daure ta karaso mayafin a hannu,Murmushi yayi yace kinyi kyau,tace
hmmm kawai tana murmushi,kulle ko Ina yayi ya rike hannunta suka tafi,mota ya bude
mata tashiga shima ya shiga Yana driving da kansa yau suka bar gidan.
Tun kafin su karasa suke Jin tashin kida mata kuwa kamar anyi ruwansu,Yan mata
zawarawa,matan aure duk gasu Nan,Basiru Kusa Ango,Naila kamar Bata San da auren ba
bayan itace take bada kudin,komai me tsada Basiru Kusa ya saka,ya Sha kyau gashi me
Jikin kiba ka rantse Alhajin gaske ne.

Mummy taci make up ansha hular gashi doguwa ga dauri an mata me kyau, kowa
yasan tayi kyau ba karya,komai na Yan gayu,kalar kayan angon ya dace Dana Amarya,su
Mima sai barin Naira ake yi,Dangi kuwa ko Ina sunzo,har babban yayan su Spark
Khalid da matarsa suna wajen.
Spark Yana shiga da Naila Khalid yace Shegen kaya wlh nasan za a rina,Spark ya
karasa suka gaisa yace Naila ga babban Yaya,Naila ta gaida shi ya amsa da fara'a
hausarsa Khalid Bata fita sosai sabo da aikin sojansa a can Lagos yake,yace karki
biyewa yaro fa bashi da kunya,yarinya ce ke da kuruciyarki karki yarda ya Baki ciki
da wuri kinji,Naila a ranta tace babban Yaya guda ana ta cewa shine me hankali,yace
wlh gaskiya ne ba karya wannan yaron na Sanshi tun Yana yaro,Spark rada yayiwa
Khalid yace mene haka Ina lallabawa zaka sa taji tsoro,Nan fushi fa nake yi so nake
taji tsoro ta bani Kuma kazo kana yaga ni,yawa kake,Rafeeq ne ya zuro Kai ya hada
da nasa Inda suke radar wai sai yaji shima,Khalid yana dariya yace Kai shege Banga
laifinka ba ka Mori sadakinka,Spark yace na fara Dora Riba tuni kwana nan zan fara
cin Ribaa,ribar sai ta ninka kaga na shiga Ribaa Kuma.

Misam ne yake ta sintiri a wajen ya kasa zaune ya kasa tsaye kawai sabo da
Chika tayi saurayi sun fita waje suna ta zanje da wani Dan matashi,shine yake ta
zuwa Yana lekawa ya Gani ko sun gama zancen amma sai ya gansu tare,fitowa yayi daga
ciki yazo ya samu Chika ya Bata rai yace ke me kike yi a nan,ni bazan yarda da
wannan ba an bani ke Kuma kizo kina cin amanata,saura kwana nawa bikinmu saura sati
daya amma kina kula wani ya miki kyau bani mukullin motata,Chika Kuma motar Misam
tana wajenta ta mika Masa key din ya fisge kamar gaske,Mutumin matashin yace amma
baki da halin arziki,yanzu bikinki saura sati daya kika ce min Baki tsaida miji
ba,kin Bata min lokaci,har mota ya baki kike jawa,me yasa Baku da Amana ne
Mata,Chika zata yi magana yace dakata wannan ko mijinki ne naga alama zaki iya cin
amanarsa,ba a haka dani,nema cikin nema,Chika tace karya yake wlh,ga zahiri na Gani
tunda yace ma ki bashi mukullin mota Kuma kin bashi jikinki na tsuma, ya ja tsaki
ya juya ya koma ciki,Misam yana ji ya labe Yana ganin sunyi baram baram ya koma ya
zauna wajen Rafeeq.

Chika ta dawo ciki ranta a bace ta samu wuri ta zauna ita Daya,Misam ya kalleta
suka hada Ido ya tuntsire da dariya ya mike yaje ya ajiyemata key din motar a table
dinta ya koma ya zauna,wajen Rafeeq,Rafeeq yace ga wata nan ta shugo a'a'a kiriga
wannan ta Shekara sittin ta bangaren Mummy ce wannan amma fa ta tara duwawu
jibgi,wai wai wai Misam wannan ace Kuna sex tana riding on top Dinka,Misam yace Kai
dai ka daina Bada misali a kaina,to ba Kaine Dan iska ba,Kai mene to yanzu tunda ka
zauna kake kallon mata kana gulma,wa yace suzo su bude Jikin ai talla suke,wata
tazo wucewa yace Yar tsila sii sii,budurwa ta rasa a Ina ake mata Dan kira ,Misam
yace a haka zaka kare wlh,suna dariya,yace wai Spark harda wani kare duwawun
matarsa ko uban me zamuyi da shi oho cewar Misam,Rafeeq yace ko ta uban waye sai na
kalla ba ruwana, ba ni nace su sake su su fito ba,bari na tsokani Spark,kasan Allah
ba a wasa da Spark akan matarsa idan ba so kake ya kwace jarinsa ba,Kuma wlh naji
yace ya siya Maka mota ka kyale shi ya baka motar Nan lafiya.
Rafeeq yace ai sai na tsokane shi Mayen mace ,yarinya sai tunani take ya kure
mata maleji wlh rannan da naje ta bani tausayi,sallama nake bata sani ba,Kuma Ina
kallo tana hawaye a boye,Misam yace ni bana tausayinta wlh dama yanda suke ta wani
fitsara su ga masoya.

Rafeeq ne ya tashi sai kallonsa mata suke yi suna so ya kyasa ga wanka a wajensa
ba a magana,wajen Spark yaje Inda daga shi sai Naila a zaune yace Yaya baza ku Dan
shiga fili bane bani aron matarka muje muyi liki,gwara na samu Yar rakiya kunyar
mata nake ji sun zuba min Ido,Spark ya kalle shi kawai ko kulashi baiyi ba,Mummy
Amarya ana fili ita da Ango har rawa take yi tana chashewa a gaban mutane da
girmanta,Rafeeq da Misam sai dariya suke,Rafeeq burinsa ya cika mata har sai da Ya
gaji da kallo sannan yace bari na tashi na tafi gida yau idona ya samu sinadarin
karfin gani,Misam yace sai gobe Malama Ikramatu zata zo,Rafeeq yace ai gobe kasan
Allah duk wani sa Hijab dinta sai naga kirjinta gobe,Misam yace indai ba riga zaka
cire mata ba ai da sauki,yace bazan cire mata riga ba ni ba irinka bane Dan
iska,amma gobe Ikhram take ko sai na cire mata Hijab wajibi ne a zaune take,zan
gani kalkalar da take har Jikinta akwai kalkalar ko babu.
Misam yace Allah ya shirye ka,ni kaini gida yau a gidanku zan kwana,ba Bariki
kenan?Uwar Bariki sabo da nace ka kaini gidanku.

Naila da Chika ne suka kebe gefe,Chika tace ya amarci? Naila tace tsakani da
Allah bazan iya boye boye ba ban iya ba,Chika da zafi wlh harkar nan da zafi,Chika
tace ya Kai cizon kunama? Naila tace ai gwara kunama goma su harbeki lokaci
guda,Chika tace mu ba ruwanmu indai za a Saba zamu bi layi kece dai raguwa,Naila
tace Allah ya nuna mana,Chika tace Ameen,ya kika ga shiri ya hau gobe Basiru zai
gwangwaje,Naila duk da ta zubar da maganin Kaka sai da ta ajiye na Basiru har da
over dose za a yiwa Basiru sabo da ya tsumu sosai ya dagargaje Mummy.

Spark bai dade ba yace su Koma gida suka tafi Yana ta Dan fushinsa Naila duk ta
damu,suna komawa ya zauna a Palo,tace abincin Baby kazo Kaci baka ci komai ba tun
safe,yace like you care,kin damu dani ne,Naila tace Dan Allah Kaci baka ci abinci
ba,yace bazan ci ba na fasa na gaji ki rabu Dani kawai kije kiyi ta hutawa,ba Kya
so na taba ki bakya so nazo kusa dake,ko yaushe complain kuka,bayan ki,kafafu waye
waye ciwo ko yaushe, sai abinci zaki dameni sai naci ga babban abinci kin
Hana,Naila tace to kayi hakuri zan yarda na yarda na daina kukan zan jure,amma Kaci
abincin yace zanci amma in one condition sai na samu Bado,Naila tace amma da ka
fara cin abinci,yace a'a ni ban yarda ba in kina so naci sai mun fara shiga bedroom
naci Abincinki sai na dawo muyi maganar girki,Naila tsoro ya kamata ta daure tace
amma da anci abincin yace mu fara zuwa naci abincin tukun sai na dawo wajen
girki,bakya ganewa ne,abinci zaki bani naci sai na dawo wajen girki,Naila a sanyaye
ga tsoro tace to shike nan muje,ya tasa keyarta gaba tana Jin tsoro tace ga abinci
baka ci komai ba,yace muje dai,bamuyi wanka mun canja kaya ba,yace zamu yi na
tsarki duk wanka ne ai sai mu hada Dana sabulu.
Maganar Goggo ta tuna Banda korafi da jayayya za ayi kishiya, Yana ta boye
dariyarsa yaci nasara,bari na cire miki ma ya fara tayata duk ya cire ko Dan kunne
bai bari ba,Jikinsa har rawa yake, Naila tana danne tsoronta yace calm down okay
bafa yaki bane ke kin San sai nasa kinji dadi tukun,Naila tayi zuciya tace ke ki
fara mana Tantiriya dake,rungume shi tayi Yana tsaye,ajiyar zuciya suka sauke
lokaci guda a tare,ya shigar da bakinsa cikin nata,suka fara Murza juna,Boobs dinta
da suke a cike bulbul ya kama ya fara sarrafasu,Naila sai lumshe Ido Kuma,har
mamaki take bashi a farko finsa zakewa take yi,da kanta ma take gogenta,ta zauce ta
fita a hayyacinta,kafafunsu sun Gaza daukansu Saman bed suka fada,Naila tana
Sambatu Yana sa baki a bado Kuma sai ta fara wash....wayyo...shima sai wani yabo
yake har ya samu a nutse ya shigeta Yana shiga tayi Kara,a hankali tace
zafi....Bata bari yaji me take cewa ba amma cewa take zafi zan mutu,Bai gane yaren
da take ba amma an samu afwa bata yi kuka ba sannan bata ce ya daina ba ta gaji,a
dole ta hakura, amma kafita ta Sha matsa sabo da zafin take rike katifa Kam,Naila
taji wuta dole ta fara wash...sai yaji dadi wani Kara Masa kaimi take yi ,ya tsani
ayi dankam kamar gawa,tunda ta fahimci Hakan sai kawai tayi ta fada tana Nishin
wahala,yau Spark yaga kokarinta ta bashi mamaki sai da ya gamsu matuka ya
kyaleta,Naila sai da ta huta tace wayyo Allah aure ban san haka kake ba,Kafafu ta
bude tace fifita min da Baki, ka surfe ni yau,na Sha sissika da surfe,Spark yace
zafi? Naila tace ba abinda babu,da zafi,da azaba,da turiri,da huci komai
akwai,Dariya yayi yace ban taba Jin dadi ba irin yau,ai ni sai yau ma nasan Ango ne
ni,Naila tace uhmm...ba dole ba...da Baki ya dinga aikin fifita Yana Hura iska,tun
Naila ana Jin salama da sa'ida sai ta koma Jin dadin abin,sabo da yana ta wasa da
boobs dinta,tunda yaga ta fara mimmikewa tana makalkale shi,sai da ya tsaya da Baki
ya jiyar da ita dadi,sai ga Naila tace da haka kake kullum ai da bazan gudu ba,idan
na gama Shan zafin sai ka min fifita,yace to amma kin Dan fara sabawa fa yanzu
ranar farko Dana biyu na isa na taba bado ko da harshen ne kuka zaki yi,Naila tace
na matsu na Saba nima na huta,in kika Saba da to ya kenan? Naila tace za aci uwar
Saba sai mun balla gadon Nan ranar,dariya yayi yace Allah yasa,yace abincina,tare
suka yi wanka suka fito,suka ci abincin daga Nan suka kwanta a Palo suna kallo suna
hirarsu ta masoya.

Washe gari aka daura auren Mummy da Angonta Basiru Kusa akan sadaki dubu
Dari,Mummy tace wata budurwar ma sai dubu ashirin wlh kudin Dan akuya ne
sadakinta,Da Yamma har jirgi Rafeeq ya biyawa Malama Ikhram sabo da jaraba,shi yaje
da mota ya dakkota tana shiga motar yace zan danyi ganganci da ke Malama sai dai
kiyi hakuri ya dinga tafka gudu da ita a mota kamar zasu kife,Ikhram ihu ta dinga
yi a mota,wani abin idan yayi sai dai kaji kan Malama kummm a Jikin glass din mota
ko ta rufta kasa,Kafin ya kaita ta Jigata sai haki take tun tana ya subhannallah
har ta daina ta koma ta rike Rafeeq Kam.

Rafeeq yace Alhmdllh Allah ya Kara wuta ya hantsilo da ita ta fado


jikinsa,tace wai kwaya ka Sha ne Dan Allah zaka kashe ni,Rafeeq gangarewa yayi ya
taka birki ji kake Kuuuuuuuuu kyaaaat....Malama ta fashe da kuka,Rafeeq ya kalleta
yace sakar min hannu,da sauri ta saki damtsen sa data rike ta kanta sabo da
wahala,kasan motar ya duka kamar zai dakko abu Hijab dinta ya tattaro ta kasa ya
fyalle shi sama ya cire lokaci guda, yace Dan Allah ki dinga Shan iska haba Malama
Ikhram,vest ya Gani a Jikin Malama da wando dogo tight ta tsuke ta dame,kirjinta
sai shining yake,yace Kai Malama dama haka kike,wanne club zaki je?
Ikhram kunya taji tana kokarin kwace Hijab dinta yace me zan gani Malama Abu
hani'an haka,bra dinta ya kalla yace number nawa ce a Uba uban wannan kaya haka,Ina
zaki da su Yar karama dake sai fuska kuyas,Uhmm Maida hijab dinki karki kwana kina
min Alqunutu,ya sa mata Hijab din yace kiyi hakuri,ya tuna karyar Spark sai ya
tafkawa mutum rashin mutunci yace ba yinsa bane Aljanu ne,shima yace Ina da aljanu
dama watarana sai naji Ina so na Kalli mace tsirara,Malama ta zaro ido dan ita dai
bata gane wannan Rafeeq din ba.
Motar ya kunna ya tuka a hankali suna tafiya,Malama ta zama gunki a mota,tsoro
ma ya kamata ko Yan Yankan Kai ne,Yana driving Yana chating da Misam yace naga
Kirji naga Malama da Shirin club akwai lauje cikin nadi Malama Ikhram dai ba Malama
bace Kuma sai nabi diddiginta bazan taba yarda ta bar garin Abuja ba sai naga Ina
ta dosa,Misam Yana ta dariya.

Mummy kuwa da mata Yan uwa maza da mata an hallara Malama kawai ake jira,daga
wajen Kuma za a kai Mummy dakin mijinta,Shi Basiru ma ya matsu domin tuni Chika ta
bashi tsumi ya Sha,a haukace yake Mummy yake jira Ido rufe.

Yau Sadakar Bakwai shi yasa banyi da wuri ba

A dinga sharhi pls.

AsmaBaffa
[1/1, 12:04 AM] AsmaBaffa: PAID GROUP 300

ACCNT NO
0175487861
ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK

YAN NIGER
+22790795939

🏫TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI
BOOK 1

101-105

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA GA
AIDA MAMAN TASNIM

Page naku ne

Mom Khalisat
Zainab Usman
Maman Samha
Rukey Mu'az

Rafeeq yace ke Malama a haka zaki je wa'azin sangalalin hannaye a wajen


tumbir cikin Hijab,Ikhram ta Harare shi ta jawo carbinta a jaka tana ja,Rafeeq yace
a wanne gari kike ne da zama? Malama tace bani da gari zaman kaina nake,Rafeeq yace
zaman kanki? Karuwa ce ke? Ikhram tace idan zaka biya me zai Hana ayi da Kai,yace
me yayi zafi ni ko nono ban taba tabawa wata ba tun na uwata Kuma tana yayeni shike
nan,Ikhram murmushi tayi tace ai yaro ma Yana Shan nonon uwarsa Yana mulmula daya
Ashe kaima ka Dana,Rafeeq yace sosai kuwa ai shi yasa kika ga na iya hakura da na
matan banza to na Sha na uwata na koshi.
Malama tace uhm Allah ya amshi tubanka,yace Ameen,ke ya akayi kika hada kaya
haka a fuska Kuma ba kama,Malama tace idan so kake ka biya a baka ka Sha,Rafeeq a
ransa yace Malama Yar iska ce ashe yanzu da zan biya sai kaga carbi a kasa,yace Ina
da aure matata ta isheni,Malama Ikhram tace wa'azin yau har da Kai a ciki,fatan
kana gingering dinta,Rafeeq Malama ta birge shi Yana son me zancen iskanci shi yasa
Naila take birge shi akwai subutar baki,Sai yake ganin Spark yafi kowa sa'a,shi
indai za a dinga kauce hanya to ai ya gama kure karshen iskanci,Malama satar
kallonsa tayi tace time yayi fa,sannan masauki na Kuma a Ina zan kwana? Rafeeq yace
gidanmu mana tace to,Allah ya Maka albarka,yace ke bakinki har tsarki ne da shi
zaki ce Allah ya min albarka ba abinda kika iya sai zancen batsa kice wa'azi
kike,dariya Malama tayi tace to da na dinga zancen iskancin a banza fa ai gwara
nayi me dalili,duk yau sai Kun koma gida Kuna neman mace Ido rufe yau chaji zanyiwa
ko wanne me sauraren wa'azi,Rafeeq yace ai sai kice muzo da condoms kowa a jikinsa.

Spark kuwa yana kwance zaiyi bacci yace da Naila Baby ki shirya kije Walimar
ku yau malamarmu zata zo ki bude kunne ki ji ki dawo naga wa'azin nan yau nasan
anji wa'azi, ga key Nan ki Kai kanki ko driver ya kaiki,Naila tace zan Kai kaina.
Shiryawa tayi Yana bacci ta Sha gayu cikin Egyptian gown blue taji ado rigar
kamar balarabiya haka ta fito,ta sa takalmi me tudu da jaka golden kalar adon
rigar,Key din motar ta dauka sannan ta Dan hau Saman bed din ta masa kiss a Saman
lips,idonsa ya dan bude kadan,tace zan wuce? Ayi driving a hankali,ko dawo da wuri
tace to karfe nawa? 8pm karki wuce haka,tace Inshaallah bye ta juya ta fita ya koma
baccinsa sabo da jiya bai bari sun yi bacci ba.

Naila yau an zabi mota iya mota an shiga ana tuki harda yin video a mota tana
Jin kida irin dadi ya Kai dadi ana hutawa,Mohsin ta turawa tace ya kaga Yar gidan
Hashimu Dolo,Mohsin Yana duba Whatsapp ya Gani Yana ta dariya,ya mata reply yace
nima Abba ya biya min Makkah yarinya,bana sai keta hazo Inshaallah,Ashe Abba duk
talaucin da yake Shekara da shekaru Ina fama da gida wai duk burinsa ya kaini
Makkah na sauke farali,Naila tace you deserve it ai Yaya,ko me Abba ya Maka bai
Fadi ba Kaine komai na gidan,ka faranta musu kaga Dan ya Maka ai ba komai,Yace
Baban Beauty da yaji yace wai Abba yayi wani abin da kudin zai biya mana muje ni da
Beauty wlh Abba yaki yarda yace sai dai ya biyawa yarsa kawai amma shi lallai da
kudinsa zanje,nima Kuma nafi son haka,dama Abba ai zai fi Jin dadi yanda ya Sha
tarin nan,Chika ce take ta yiwa Naila horn fiiiiii a motar Misam,Naila tace
yarinyar nan taci abinci ta kwacewa bawan Allah mota,giggiwa irin tasu hannunsu bai
wani fada ba.

Suna parking a wurin walima suka ji Mandiri na tashi,Mummy wai dole sai anyi
kida ita,Rafeeq Yana parking da mayyar jallabiyarsa tsangalalliya wai shi yazo
walima harda hula,Misam yazo tare da Wahida taci gayu sosai gata kyakyawa,Chika
tana ganinsu ranta ya baci yace wato ta bar Spark ta dawo wajen Misam wlh ni uban
yarinya zanci ba irin Naila bace.
Naila ce tayi parking ta fito,Rafeeq yace uhmm kaga matan manya,dariya Naila
tayi taje suka gaisa,Misam yace kinyi kyau gaskiya,Naila tace zanyi recording na
kunnawa Yayanku,Chika ce ta fito Chika ita riga da skert ta saka wasu na larabawa
Wanda ko ya kayi motsi sai jikinka ya kama rawa,Misam Yana kallonta ya hadiyi mugun
yawu,Rafeeq ya radawa rikeni rikeni cassava ta motsa,Wahida tana jinsu a
kunnenta,tace wlh halina daku duk Yan iska ne Family wannan gadon Zeenatu ta bar
mana masifa,Rafeeq yace Ke ki rantse ba a Shan mintin ki? Wahida tace na rantse
yace karya kike ni da na Ganki da idona a motar sabon saurayinki, har horn na miki
na haske ku da fitila,Wahida tace tace Body no be Zuba Rock,Naila ta kalla Dan ta
cusa mata haushi tace tunda Spark ya daina romancing Dina na shiga garari.

Naila tace lie lie wlh ko da bama tare baki isa ya tabaki ba bare Yana so na
tun lokacin me zai ci da ke,idan ma ya tabaki kince da,to yanzu fa? Ko kallonki
zaiyi ma,sai dai hakuri yarinya kafin na fito ma sai da na Sha madarar Nido ya Sha
juice,Malama Ikhram ta zagayo ta fito daga mota tana Jin zance ta karbe tace juice
dinma me bubbugowa a lokacin,a tabaka ya fito wannan sai ikon Allah waye ya isa ya
kirkiri wannan,mazajen babansu ne yayi ruwan,ke baki da kunya a gaban mazan kike
wani body no be Zuba Rock duk yan iska ne mu,a gidan yari muka yi degree ki shiga
hankalinki,Chika tace na so,bana so ma nayi magana sabo zan iya Marinta a wajen,ke
Spark ne zai taba ki,Naila tace ke badan Ina da aji ba yanzu kin isa ki min
magana,to yanzu ni bana harka da Yan mata nafi karfinku,da masu karbar Hallare nake
yi kullum sune dai dai ni.

Malama tayi ciki tuni tana duba agogonta,tana shiga kowa Yana jira yaga babbar
mace Malama sai aka ga Yar budurwa yarinya,Mima tsaki ta ja tace yanzu wannan ce
malamar, Kai amma Rafeeq kawai Yan iskan yara suka taramu a Nan,Mummy da Yan uwa
sai kallon juna suke suna tabe baki,gaba daya abin ya sire musu Yar cikinsu,Mummy
ranta ya baci ta tsurawa Rafeeq Ido kamar tace a dawo mata da kudinta data biya aka
dakko Malama har kyauta tayi Masa,Baseeru Kusa kuwa shi a matse yake sosai baya son
wa'azin shi burinsa a Kai Amarya
Naila ta shiga ta zauna,Wahida ta zauna a kusa da ita tana Jan tsaki tana jefar
da magana,talakawa anyi clean anzo Abuja,Naila tana jinta ko kallonta Bata yi ba.
Rafeeq da matasa duk sun zauna,Malama ta karbi Speaker,anyi tsit ana
jiranta,yace dan Allah Mata su ware gefe daya Maza ma haka,ba Wanda yayi
motsi,Rafeeq tayiwa Dan kiranta da ta Saba siii siii hey....ya juyo ya kalleta tace
saita musu zama wa'azi muka zo ba Party ba,fito ta yiwa Chika tace tashi Chika ki
ware min mata,Chika ta mike duk girman matan wajen da masu kudi tace a tashi a
ware,Maza kuyi chan,itama ta samu saitin Misam tayi Masa fito tace Maza ku kama
kanku,Rafeeq yace mu ga kugunmu ga na mata,Kamal yazo wajen Yana ta dariya yace yau
sai bari naji wa'azin nan me za ace.
Malama taga duk sunki tashi tace zan tafi wlh na fasa,Rafeeq yace karku jawo
mana masifa Malama zata tafi ku tashi ku koma can shi Kuma yaki tashi ya samu wata
ya makale a kusa da ita.
Mima ce tace ke dalla bama son iyayi kiyi abinki a haka duk Yayanmu ne Nan sabo
da haka ko wani kika ga ya rungume wata to Yar uwarsa ce,Ikhram tace
abomination....haramun ne,Amarya wani takaici ya isheta,Chika tace Malama fara
aikinki idan sunji ruwansu.
Taro ta bude da addua sannan tace tana wata kalkala kamar zata yi amai sabo da
larabci Alhmdllh wato ainihin naga Amaryar ma babba ce haka angon ma ba laifi,Allah
ya Bada zaman Lafiya,Mummy tace Ameen,Rafeeq ya fara boye dariya ganin Angon idonsa
yayi ja sai kallon Mummy yake kamar zai cinyeta ko kunya baya ji sai kace ya samu
tv,text ya turawa Misam yace Kalli Ango dan Allah.
Misam Yana karantawa ya Kalli Kalli Ango Bai San sanda dariya ta kwace Masa
ba,su Arham duk suna zaune mata San nan kowa yazo gasu da shegen yawa.

Rafeeq ya sake turo message yace Allah yasa Mummy tana period yau,Misam yace
a'a ai itama so takeyi kaga katon bahon data siyo da naje jiya a toilet dinta na
ganshi wai tsumi takeyi tana zama a ciki,Rafeeq Yana duba waya Yana dariya yace ai
dole sai da liki ta dinga Dan like wajen, Malam Ikhram wa'azinta ta fara sosai kowa
Yana jinta gaskiya take fada Sosai game da aure da abinda Allah yace,da Kuma duk
wani sharudan zaman Aure,ta jawo Aya da hadisi ta fassara,har ta gangaro yanda ake
tarairayar miji,Rafeeq wayarsa ya Maida Aljihu ya nutsu,duk mazan nan suna Jin ance
wai ake kula da miji ne? Kun San komai Yana tafiya da zamani,karki kice wai ke tun
daurin dankwalin zamanin Da can da kika iya shi zaki yi a yanzu,Inaaaaaa Sam Hajiya
an barki a baya,Zamani zaki shiga kema duk abinda zamani yazo da shi da haka ake
tafiya.

Idan sabon daurin dankwali ya shugo to kar abarki a baya waje cikarawa me gida
shi,haka sabon dinki,da yawa ana siya mana sutura me tsada amma sai ki dinga kallon
ai kin girma kin tsufa kina da yara sai ki kaiwa tela ya miki dinki made in Da,wata
shegen son kudi miji ya baki kudi kiyi dinki na Gani na fada sai ta rage ta bawa
wata kawai tayi mata me araha marar kyau,ko bakiyi kwalliya ba Hajjaju matukar
dinkin ya hadu wlh sai kinyi kyau a ciki shape dinki ya fita,amma kinje kin Masa
dinki sai a hankali zaki ga sai a hankali.

Chika ce ta daga hannu tace Ina da tambaya Malama,Na'am wai ya akayi ne gashi
Ina daukan wanka amma mijina baya yabawa Kuma Ina kokari nayi,Ikhram tace wankan
Bai Kai wanka bane,ai indai kinji miji Bai yaba ba duk da ana samun Wanda ko zaki
yi basu yabawa to amma Mafi yawa wankan da akeyi Bai Kai wanka,kiyi wanka kamar
zaki je Dinner ki Gani karya yake wane shi sai ya yaba.

Sannan mace ta zauna ta lalata kanta wai har sai tayi aikin gomnati sannan zata
siyi sabulu me kyau wlh baki hadu ba,in har kin hadu karya yake ya hanaki shi din
banza,ke kike da idon gari ba,idan kina biyayya,kina hakuri,kina gyara kanki in and
out wlh lungu da sako,tsabtar jiki,gida,sutura da komai sannan kina cikawa da
daukan shegen wanka ki Gani ya isa ya hanaki kudin sabulun,sannan mu mata muna
zubar da darajar mu da kima ta ya mace shi yasa muka fi samun matsala mu
hausawa,girman Kai Yana cutar damu,kinyi laifi baza ki accepting ba,hakuri kinfi
karfin kiba namiji,sannan ta rashin kulawa ta matanmu,kina fara yin yara sai gaba
daya hankalinki ya koma kan yaran ki kyale mijin naki,komai an daina,Yar shagwabar
ma babu,duk kin ballagazar da kanki.

Kishiya kaddara ce amma ana so idan anyiwa mace ta tabbatar cewa idan wata ta
shugo ba abinda zata nuna mata,ba abinda zata yi Wanda ita bata riga tayiwa miji
ba,amma Baki San bacin ran me gida ba naki San farin cikinsa ba,ko baya ganin
abinda kike yi karki fasa kiyi iyakar iyawarki ko bayan ba ke sai yaga
amfaninki,Kuma wani baya yabon mace a gaban idonta amma a bayan idonta Bata sani ba
duk Inda ya zauna sai ya yabeta tana da wani matsayi a wajensa Wanda ita Bata sani
ba just Kinga naya yabonki kin damu ko kin daina kulawa da shi Baki San Kuma a
ransa bashi da kamaki.

Maza yawanci haka suke ba sai an fada miki ba amma ke Baki sani ba Ashe kece on
top,ke Kuma kina Nan kina zage zage baya sonki yanzu ai kaza kaza a garin haka duk
ki watsa kanki a wajensa,Sannan mace ita fa Yar kwalliya ce da gyara duk kyan mace
idan ba gyara to aikin banza ne,bare yanzu an waye kayan gyaran jiki gasu Nan iri
iri,ki gyara headquarter,amma kin zauna sai sanda zaki wanka zaki wanke Headquarter
Hajiya baza ki haifi da me Ido ba,a kalla a wanke sau uku da ruwan zafi ga sabulan
wanke Headquarter ne iri iri yanzu da masu tsada da masu Araha a samu a dinga siya.

Bakya wankewa bakya gyarawa Kuma kina jira mijinki ya Kai Baki Nan wajen
mahaukacin inane shi,har su Mima suka kwashe da dariya,duk ga yaransu kowa baya Jin
kunyar kowa ana magana haka,amma ba ga iyayen ba ga yaran nasu kowa yayi
mirsisi,Rafeeq yau shi dai Shar da shi ana zancen abinda yake so,Kamal yace bari na
tashi na fece an fara zuwa wajen da zai gagare mu ji.
Chika tace Malama da hammata a dinga gyarata,Malama tace yawwa a dinga aski akan
lokaci,sabo da haka a Headquarter din ma ba kullum zaki dinga sakewa kina kwalkwal
ba haba ba style ai ko Carlos Kya dinga yi watarana,Kamal tashi yayi yace naji
rabona ni Kuma ai,Ikhram ana bayani har zaga wajen take,har tazo idan an samu ciki
Nan ma ya ake kula da me gidan,har haihuwa,ana gama na haihuwa da yanda za a gyara
jiki tace sai yanzu muzo tarbiyyar yara Kuma amma kafin lokacin yanzu Ina siyar da
ingantattun maganin Mata sa me gida suma,su makale mata,duk akwai,da turaren musk
na sawa a wajen ai Kun gane.
Naila ce ta daga hannu tace Ina da tambaya,tace Malama mace zata iya saka zuma a
wajen wato idan za ayi abin Naila ta nuna da baki sai ya lashi honey,Malam tace
babbar tambaya na gode miki wannan ma dai dai ne.

Mima kasa hada Ido tayi da yaranta sabo da dole sai da taji kunya,Naila a
ranta tace duk Tsohuwar da bata ji kunyar yara da jikoki ta tashi ba muma surukai
baza mu ji ba.
Mima so take yi ta siyi maganin Ikhram na mata amma ga yara,haka Maman Rafeeq,da
sauran Yan uwan Mima sai Kus Kus suke yi ya za ayi su siya,Misam ne yaji suna ta
faman Kus Kus,wannan ta taso ta radawa wannan,yace kan bala'i Kai Ashe harda
tsofaffin basa hakura.
A waya ya turawa Rafeeq yace Uwar rainonka tana so tayi chaji,Yace zan siya mata
ai shi mijin nata ma ba sonta yake ba sai dai a siya mata,Misam yace Kai banza ga
Naila wlh ance Kakanta Yana Bada magani kaje ka samo mata ta Sha ita da mijin Wanda
zai haukace mata itama maybe ta Gyaru,Rafeeq yace haka za ayi amma bana so ta haihu
ni bana so ayi min Kani ko Kanwa su isheni kishi nake gwara ni kadai nayi shagwaba
ta,Misam yayi dariya yace Allah ya shiryeka baka so ta samu nata itama.

Malama tana gama talla tasan dama yanzu baza su iya siya ba sabo da haka mata
suke yi sai dai a sirri,ai kuwa ta dawo taci gaba da bayani akan tarbiyyantar da
yara,tun daga farawa su Mima suka tabbatar sunyi kuskure tun farko,sannan su kansu
sun San iyayen su basu basu tarbiyya ba,Malama Ikhram tace mu da kanmu iyaye muke
raba kan yaranmu,kinki tsayawa yaranki su fahimci Allah da addinin Allah,ko Kuma
sunyi karatun addinin ma amma duk abinda yaro zaiyi baza a Masa fada ba,a gaban uwa
yaro Yana zagi na rashin mutunci baza a nuna Masa ba dai dai bane,a gaban iyaye
yaro zai dinga rawa baza a nuna Masa kunya da cewa wannan ba Abune me kyau ba a'a
wasu iyayen ma da yaran nasu suke rawa musamman mu iyaye mata,mune masu tarbiyyan
yara mazajen sun fita nema sai ke sai yara,ya kamata mu San Amana Allah ya
bamu,Yaro ko yarinya kaji suna wakokin batsa,magana ta batsa,ta banza ta fitsara
amma baza a iya Masa fada ba bare a nuna Masa ba kyau,yaro zai zagi babba ko waye
bazan a Masa magana ba,aje gidan wasu da yaro sai ka gane basu da tarbiyya komai
suka samu lalatawa zasu yi uwa tana kallo baza tace ya bari ba.

Musamman masu kudi yaro bai San darajar komai ba zai iya fasa tv,ya lalata
remote etc amma ko Harara yaro bai sani ba,yaranmu yanzu sun zama samari sun zama
Yan mata amma sunga babba baza su iya gaida shi ba wasu ma kallon arziki baza suyi
Masa ba,sannan wasu idan zasu gaida mutum komai girmansa Ina yini kafin ki amsa ma
ta Kara gaba ke kika sani,Kuma wai abin mamaki a gaban iyaye,wasu ma kannen uwarsu
ne,wasu yayyen Uba,ko Yan uwa,amma basu da darajar ma da zasu musu gaisuwa me
kyau,yanzu haka akeyi ba talaka ba me kudi,wasu ma yaro sai ya dinga kwana a wani
wajen basu sani ba,Yaronki Yana can ya kama hotel Yana da permanent room baki sani
ba sabo da rashin kula da Amana.

Yarki kin barta tana ta Tara samari tunaninki farin jini ne kina tana Nan har
sai an samu wani ya lalatata gashi ta samu na auren ance sai tayi karatu dole,wasu
Kuma basu samu mijin auren ba amma an takura an hanasu sakewa karshe har sai sun
zabo Wanda basa so sun aura haka,daga Nan Kuma sai Kiga yarinya da aurenta tana bin
Maza,idan tana da Wanda take so ta koma suna aikata masha'a sabo da kowa Yana da
taste ba a bari mace ta zabi Wanda ya kwanta mata kawai tayi aure,shi yasa zawara
suka mana yawa,da yawa yan mata gasu Nan suna complain cewar sabo da basu da mijin
aure iyaye da Yan uwa sun matsa musu lallai sai sun fitar da miji,gidan yayi musu
zafi,har Yan uwa daina shiga suke yi karshe yarinya tace ita koma waye ya fito aura
zata yi karshe ta auri Wanda Bata so,gashi aure ba abin wasa bane halin kowa sai ya
fito mace ta auri Wanda take so ya aka kare bare Bata sonsa yaushe babu so zata
zauna ya mata wani wulakancin dole yarki ta dawo bazawara.

Kina da Maza namiji ya samu wacce yake so take sonsa indai an yaba da
tarbiyyarta mene ne,a'a mu yanzu masu kudi sai masu kudi talaka sai talaka,yarinya
Abi a tsaneta idan an aurota gori ma ya isheta Yar talakawa,Naila tace gani nan a
sa dani,duk matar da tayi sake yaranta suka taso ba tarbiyya karshe sai tayi kuka
da Dana sani,a yawaita yiwa yara addua kullum ana sa musu albarka sannan a basu
tarbiyya shine mafita,amma a zubawa yara Ido suna iskanci suna badala da Sunan
wayewa wlh ba daidai bane,Kuma suna girma a haka gyara bazai yuwu ba sai dai
addua,su Mummy dukkansu suka yi tsiiitttt kamar ruwa ya cinye su.

Malama tace wlh yara da kudi ku sani duk jarabawa ce kaddara ce,idan kin tafi
dasu daidai kiji dadi idan aka samu aka si Kuma kiyi kuka da idonki,duk Wacce tayi
aure kafin ta haihu ta sani aiki ne ja a gabanta matukar ta kusa aure ta shirya
aure wata hanya ce ta producing 'ya'ya, yaro zakiyi producing,Producing Abu kuwa
ana bukatar kayan aiki sosai,shine dole kiyi bincike kisan wa zaki aura,shima dole
yayi bincike yasan wa zai aura sabo da abinda zaki producing ba Abu ne na wasa
ba,tsatso na kirki ake nema sai ayi producing Abu ingantacce,ko a sahabbai ku
bincika tarihi kuji kalar mataye da suka aura,haka ko matayen su ku bincika kuji
mazajen su waye ya tsatson yake,sannan ku bincika yayansu da suka Haifa Kuma kuji
Yaya suka taso su waye su sannan wanne tarbiyya suka basu me yayan suka zama a
duniya,sun amfani duniya ko basu amfani duniya ba,amma mu munzo ba lissafi kawai
kyau sura,kyau sura ita ake aure yanzu,daga an kaiki a bude Banana ki bude fanke ko
gurasa faaaa sai yara yuuuu Kuma an barsu sakaka, yawwa a kiyaye a kula,ayi mana
addua iyaye gamu Nan duk Yan banza ne muma,aka fara dariya,Arham yace harda ke
Malama tace harda ni nima Nan kwalluwar kaina ce baka ji lafazi na bane,ai mu gyara
muke yanda za a daidaitawa miji kayan harka.

Duk da wa'azin ya shigi kowa amma Ikhram sai ta dawo taci gaba da koya yanda
ake kwanciyar aure,duk mazan Nan suka nutsu suna ji sai iskanci suke yi kamar ba su
aka yiwa wa'azi ba,Mima tace gaskiya zan gyara nima yau Mijina Papan yara zai ga
canji ya zama dole,har na manta da shagwa rabona da ita tun ina Amarya,yau kuwa ta
dawo sabuwa.
Sai 7pm aka gama wa'azi sannan,Malama ta fito, tasan kan tsiya ana can ana
Mandiri ana liki mata Kuma suna ta lallabawa waje wajen Malama suna siye maganin
Mata,Mima da ta fito sai da ta Kalli gabas yamma kudu da arewa ta tabbatar ba Danta
a kusa sannan ta siya,Rafeeq yana kallon ko wacce cikinsu Malama tana ta
ciniki,Basu San ma ya fito ba ya rabe a bayan mota, sai da suka gama siya yaga
Mamansa bata zo ba yasan zai wahala idan tana da kudi Kuma maganin yaji da tsada
sosai na manya ne,Wajen Ikhram ya karasa yace yawwa maganin naki wanne mata suka fi
siya yafi yi musu amfani? Ikhram ta nuna Masa kala hudu,ya Bata kudin sannan yace
muje na nuna miki matar da zaki bawa a sirri karki kice ni na siya ko wani,kawai
kice Dan Allah kece Maman Rafeeq? Idan tace ae kice school dinmu Daya Dake ki bata
kice kyauta kika bata,Yanda yace haka Ikhram taje ta kira Maman tasa gefe ta mata
bayani ai tasan Rafeeq ajinsu daya,ta bata tace gashi Mama kyauta na baki,Mama tace
ayi haka? tace wlh ba komai suna da amfani,ta karba ta zuba a jaka tana ta godiya.
Ana tashi daga Walima dama an gama shirya komai da bangaren Amarya a gidan
Daddy Beauty,Mummy ta gama kulle gidanta ta bar masu gadi kawai zasu dinga gyara
mata shi kafin tasan abin yi,anci an Sha a wajen Walima kawai aka wuce Kai
Amarya,duk Mummy ita kallon da take wa Chika ai kishiyarta ce sabo da Baseeru yace
baya sonta yanzu Mummy yake so shi yasa ya ballagazar ita take abinda taga
dama,sabo da Chika idan ta Kalli Mummy sai Harara tsakaninsu,a dinner ma haka tayi
a wajen Walima haka,Mummy tace nasan kishi ne ya zakiyi da ni miji dai na aura.
Naila da ita aka Kai Amarya Chika Kuma tayi bangarenta tana zage zage,su kansu
su Mima mamaki suke da suke ganin Chika a lamarin auren,amma Allah bai sa sun
tambaya ba,sun zaci kwashe kwashe Mummy ne.

Ana Kai Amarya Naila taje suka gama tsarinsu ita da Chika da Baseeru,Chika tace
Baseeru ka dakata kamar ka samu turmi,Baseeru yace baku San iskanci na ba wayyo
labarina kuke ji,ai ni wlh sai nayi sati biyu ban leko ba,ke dai kawai Chika ki
dinga dado girki kina kawowa,ni yanzu ma lokaci kuke bata min da tuni na fara Blue
film,Naila wayarta ce tayi Kara tana dubawa Taga Baby,7:30 har ya kira tun 8pm din
bata cika ba,tace Kinga Baby yana kira tafiya zanyi,Baseeru yace yawwa jeki kema
kiyi Blue film dinki da mijinki a bar Chika da Hausa film.

Chika tace kaji da shi dauki kazar amarcinka ka wuce,Baseeru yace ice ko da
Madara a ciki sabo da nafi kuzari,Chika tace akwai Dan Allah sun tafi Yan kawo
amaryar jeka ka surfata sosai,Baseeru ya dauki Leda ya fice sai bangaren Amarya.
Naila tace Chika na tafi muyi waya,tace kudi Hajiya Naila, tace zan tura miki
anjima ki bari naje wajen Oga banyi girki ba,ya fada min 8pm na tabbatar Ina
gida,Chika tace Dan Allah jeki karki dameni da zancen Oga Yan Yan Yan,Naila ta tafi
tana dariya,mota ta shiga ta wuce,sai kira yake ta yi, ta daga wayar tace na kusa
fa Baby, yace kin barni a gidan ni kadai yunwa nake ji,Naila a ranta tace shagwaba
da wace take bashi,wucewa tayi joint din Rafeeq,ta samu Oga Rafeeq ya hakimce a
kujera ma'aikata suna ta aiki,Malama Ikhram tana zaune tana cin shawarma iya
cinta,sai ta, Naila tana zuwa tace hot shawarma da Ice cream Oga a bani na tafi
sauri nake,Rafeeq yayi dariya ya kira Waiter yace a bata hot shawarma da Ice
cream,Nawa kike so madam? tace guda uku Ice cream din ma uku a bani fried
chicken,Rafeeq yace kar ku Karya min jari,Naila tace zamu dora ka,yanda tace aka
bata,Malama tace gobe zanzo gidanki kafin na tafi,Rafeeq yace jibi dai zaki tafi
wanne gobe sai jibi,Naila tace Allah ya kaimu.

Parking Naila tayi a gidan,ta fito ta shiga ciki da ledarta,Spark ya labe a


Jikin Kofa tana shugo ya fito yace taaaaf....tsoro taji ta dafe kirji tace ka
tsoratani wlh,matsoraciya ya lakace mata hanci tare da rungumeta yace kinyi kokari
8:10pm kika dawo.
Haka kika yi kyau ban sani ba kika fice a haka da guntun mayafi,Naila tayi
dariya tare da kankame shi tace jikinka dadi wlh,naki ai yafi nawa,janta yayi suka
zauna ya cire mata takalmin,ya karbi jakar ya cire mata mayafin,duk su Dan kunne
abin hannu ya cire mata da kansa,sannan yace me kika siyo min,Ledar ta mika Masa ya
duba yaga ta Rafeeq ce,yace can kika biya kenan tace ae,kin tambaye ni? Ai ka yafe
min na sani, idan na fada maka ai zaka barni ma,ya bude ledar yace kin huta
girki,Ice cream din zai huce Baby yace to Daya ai ya ishe mu jeki ajiye wannan a
fridge.

Taje ta ajiye ta dawo wajensa ta zauna suna ci tare suka Sha ice cream din har
roba biyu, yace muje to kiyi wanka,tarkacenta ya kwasar mata suka haura sama,ta
shiga toilet,ya Adana mata kayanta sannan ya cire kayan jikinsa ya canja na bacci
ya kwanta Yana jiranta,Naila ta fito tayi Shirin bacci ta haura Saman bed,suka
kwanta Taga bai fara tabe tabensa ba,suna ta hira shuru baiyi komai ba,har ya fara
bacci,mamaki ya kama Naila,tashi tayi zaune ta kunna hasken wayarta ta haska
Hallare a wando ta ganta dai ita ba a kwance ba ita ba tsaye ba,ta taba a
hankali,ta Kalli fuskarsa Yana jinta dariya ta bashi ya danne da kyar,Bata San
Lambo yayi ba Dan kar tace ya dameta shine yayi wayo, Naila tashinsa tayi tace
Baby...Baby...tashi,idonsa ya bude da kyar a dole bacci yake wai,tace Baby kalau
kake kuwa tun rana kake bacci,yace kalau nake mana baccin Dana Tara nake
ramawa,Naila tace uhmm shine baka taba ko kirjin ba lafiya? Ko wani abin nayi maka?
yace a'a wanne irin laifi ana zaune kalau Amarya Bata laifi ai na gaji ne kawai ban
San me yasa ba,Naila tace haba aci kullum ya zaka ce ka gaji,ai na daina kukan Kuma
jiya ai zafin Bada yawa ba,wlh bazan sake kuka ba na dawo Tantiriya ta, Spark yayi
murmushi yace to kwanta yau me midnight ce,Kai dai kace ka gaji Dani kawai yau,na
daina birgeka,ka daina sha'awata,Spark a ransa yace shege ni ta Saba a haka Yana
Jin dadi,a fili yace bana so na dinga takura miki ne, Naila tace to shike nan ni
bari na kwanta tunda sai dare,yace nooo wasa fa nake yi ai yau sau biyu zanyi,Naila
taji dadi ta zaci ta daina birge shi,to tsiyar mata kenan da sabo,in suka Saba ana
Abu idan ba ayi ba sai ace da matsala.
Jikinsa ya dorata Yana kwance,Naila tace Malama tace a dinga canja Style,yace
baki gane ba Angel sai kin Saba za a canja ana miki yanzu first night zai
dawo,Naila tace to kar first night ya dawo bana sonsa,ke yanzu na doraki a samanta
kina Riding Dina zaki iya? Naila tace har na fara Jin zafi,Dariya suka yi,Yau ma
Naila ta tsaya sosai suka Mori juna,har ana danyi ta fara Jin dadi kadan,tace
a'a'a'a ya zaci zafi taji ma,yace Sorry,tace wanne Sorry kai bawan Allah an fara
zuwa wajen,Hallare ta fara abin arziki,Hallare faaaaaaaaaa.......wash......Dadi
dadi kadan zafi zafi Kuma amma dadin yafi yawa......wash.....zan haukace....Spark
Yana Jin farin ciki ya ishe shi,Naila ta fara Jin dadi sai cewa yake Alhmdllh,
Alhmdllh,dadinki yayi yawa....Naila tace ci gaba a hankali,Spark yace okay Yana
binta a hankali yanda take so har Naila ta kamo hannayensa ta Dora a Saman Boobs
dinta tace zanyi fitsari wayyyooooo.....zanyi fitsari.....Spark ya gane ba fitsari
zata yi ba sai dai releasing yace to yi abinki kinji,tana ihu tace fitsari.....ta
kankame shi sai kace zata cinye shi jikinta Yana rawa sosai ta,wannan abin da take
yi shi ya jawo Spark ya kawo da wuri itama ta kawo.

Naila tace yau zafin kadan naji,yace to Goggo ta gyara min abata,Naila wayarta
ta jawo tana dubawa,me zaki yi? tace Abu zan turawa Chika,Me? Abu ne,oh baza ki
fada min ba,tace kudi zan bata,yace manya,nawa za a bata? Naila tace 20k,yace to
bani accnt din nata,ta bashi ya sa a wayarsa ya tura mata 50k yace done,tace har
50k an gode yace uhm yau dai godiyar ki bani sau biyu,Naila tace ai Hallare ta fara
mutunci zan yarda,Rungumeta ya sake yi sosai a jikinsa Yana Jin didi.

Mummy Amarya Baseeru sai rawar kafa akeyi,sunyi Nafila sunci abinci sannan yayi
wanka dama Baseeru akwai tsafta,Mummy ma tayi wanka ta shirya tana kamshi aka saka
rigar bacci nonuwa kaya guda Shirim Baseeru yace wannan ai sai na nutse gaba daya a
ciki baza a Ganni ba, wannan idan ba tallafar su zanyi ba ai sunfi karfin hannayen
ma,sai dai in kwashe su inyi can dasu inyi Nan da su,Mummy ana kwarkwasa ana kallon
Baseeru ya gama Shirin bacci,yasa jallabiya marar nauyi ko wando babu,Mummy tana
murmushi Baseeru ya rungumeta,duk girman Mummy sai da ya iya dagata ya dorata a
Saman bed,amma da sauri ya saketa Yana Nishi da hakki sabo da nauyi,Baseeru ya fara
cirewa Mummy riga,abubuwa suka bayyana ya fara tura kansa tsakiyar na Shanun Mummy
yace shigar Dani ciki Uwar Dana Spark,Mummy tace kaje Ina sai kace rago Kai Alhaji
Baseeru kamar ba wayayye ba kamar baka keta hazo kana ganin duniya,Ina ka bar su
kiss ne,Baseeru yace na zauce kaunarki ce kawo bakin Miko shi ya zanyi ni tsakani
da Allah ban taba yiwa matata ta farko ba,Mummy tace to ni ai ba Chika bace a waye
nake,Mummy ta chafki bakin Baseeru taji fes da shi tace bini ni zanja ragamarka,ta
samu Baseeru ta kwance Masa basira gaba daya,ta gama lugwigwice shi,sai dadi yake
ji,yace na baki ni, ki yanda kika ga dama Yana Nishi Yana Jin dadi,Mummy a ranta
tace a fada mana wayewa da sarrafa miji mu da muke tsohon hannu,Baseeru ta sawa
boobs dinta a Baki,Baseeru yace mama tana bani mama insha in kohi,Mummy tace mene
ka kohi kamar Dan kauye,ta ci gaba Baseeru Yana tayata duk ya rasa Inda zai kama a
Jikin komai yayi Masa yawa,Baseeru ya dakumi Mummy Yana lagude boobs yace Over size
Dina sun koshi bulbul da su,Mummy ta kwanta wai Baseeru ya sa Baki a bado Baseeru
yace a'a Uwar Spark Ina laifin Banana amma baki kawai kuraje su fito min gobe a
baki ,Mummy ta jawo kansa ta danna shi,Baseeru ba yanda ya iya haka ya dinga yi,da
sauri ya wayance ya Kai ga shiga bado,Mummy ta Sha Gyara,Baseeru ya susuce ya zauce
dama abin nema ya samu,Mummy an Dade ba a hadu ba tace da tsohon mijina ne da tuni
ya kawo jaraba na huta.

Baseeru yace karki sake kiran tsohon mijinki a gaba na zan Saba miki,zan ci
mutuncinki,Ina Mummy Sambatu take kawai taji abinda bata ji ba tsawon rayuwarta
mijinta rago ne,ihu take da Nishi tana sambatun dadi,shima Baseeru haka,Baseeru
kamar inji baya gajiya Mummy ma haka take ko alamar ta gaji bata yi,sai da suka
dauki lokaci dai dai misali kafin su samu gamsuwa,Baseeru yau ya gwangwaje,ya Dade
Bai ji mace me sweet din Mummy ba sabo da ta kashewa kanta kudi sosai.
Yau kawai a cikin nishadi suke,bayan sunyi wanka suka kwanta bacci Baseeru yayi
pillow da kirjin Mummy Yana ta sheka bacci.

Rafeeq kuwa Malama tana koshi ya kaita gidansu,Dan iskanci sai ya kaita
gidansu shi da Islam,gidane me kyan gaske yaji alatu Dan madaidaici sama da
kasa,Rafeeq a sama Islam abokinsa a kasa,sai da suka shugo Malama tace Ina Umman
taku? yace tana gidan Mima anjima zata dawo muje na rakaki dakinki,Islam ya Kalli
Malama karon farko,ya Kalli Rafeeq Yana boye dariya.

Rafeeq ya kaita har bedroom dinsa neat da shi yace ga toilet Nan kiyi
kwanciyarki,tace to na gode,fita yayi Malama tana tunani dai tayi wanka ta fito ta
saka kayan bacci dogon wandon da riga tana Shirin kwanciya Rafeeq ya shugo kawai
Dan ya gani Yaya,yace Mama ta dawo yanzu amma ta sake fita wai tayi mantuwa,tace
Eyya ba damuwa ya kurawa kirjinta kallo yace am..am...zaki Sha ruwa? tace
Alhmdllh,lemo fa?tace to kawo min,yace okayyyyyy.... Yana kare mata kallo,ita bata
ma kula ba.

Yaje ya kawo mata ta karba tana godiya,zama yayi a gefen bed din,tace dama zan
kwanta ne ai zaka iya fita,yace Dan Allah wata sura nake so ki Kara min,tun rannan
nake so a biya min ga malama yanzu please.
Ikhram tace okay dakko Qur'anin,Yana fita ya dawo Yace na manta na kaishi gida
jiya,Ki koya min Salatul fati ni Dan izala ne zan dawo darika,tace ai ni Yar izala
ce yace Ooooh....to shike nan amma dai ai bana bar bakuwa ba haka kafin mama ta
dawo,Bargo ta shiga tare da lullube jikinta iya kanta kawai ake gani da fuska tace
zauna to,ya zauna tuni harda Kara gyara zama.

Chika tana gida bayan Naila ta fita ta shirya ta fita zata Nemo abinci,tana
tafiya a kafa Dake wajen ba Nisa sai da tazo cikin mutane kawai taji ta a kirjin
mutum an rungumeta Kam cas a kirjinsa kamshin kawai taji tasan Misam ne,sakinta
yayi ya Kara gaba ko irin ya nuna alamar ma ya taba mutum baiyi ba tana kallo ya
shiga mota ya Kara gaba,tace yanzu haka hotel zai je wata karuwar ya siyawa
abinci,juyawa tayi gida ta dakko motarsa Dake hannunta ta nufi hotel din,binsa tayi
a baya har ciki taga ya shiga wani room daban, Dan wayo tayi ta kama daki a hotel
din Dan ya samu shiga Inda take so,tana zuwa bayan an kaita dakinta ta fito ta nufi
Inda taga Misam ya shiga,knocking tayi ta Murda handle din ta shige gaba daya Allah
yasa ba key,tana shiga ta ganshi shi kadai Yana cin abincin da ya siya.

Kallonta yayi da mamaki yace babanku Yana gaishe ki,tace wa? Abbu Yana gaishe
ki,mamaki ya kamata tace a Ina kasan haka muke cewa Abbu? Yace zo ki zauna ni sai
na Baki tarihinki kaf kiji har dalilin shigarki gidan yari,tace ban yarda ba ta
karasa ciki ta kulle kofar,yace ke wlh karki zaton karya nake zuwana gidanku
Uku,Nan zuwa kika yi ki kureni Ina iskanci,baza ki taba kamani ba Allah Yana rufa
min asiri,zauna kiji ba abinda zan miki,naje gidanku Chika nasan tarihinki Kuma
naji tausayinki,Hannunta ya rike yace zaki aure ni? Kina so na a haka? Chika tace
Allah ya kiyaye na auri me neman mata,ya zakiyi dani na zame miki ciwon Ido,ya
jawota ta zauna a gefen bed yace Dan Allah ki aure ni kinji,Chika tace a'a,why?
shuru tayi yace Ina sonki,taji dadi amma tayi shuru ta mike tace tafiya zanyi,yace
Dan Allah ki kwana a nan,na miki Alkawari ba abinda zan miki,tafiya zanyi akan me
zan kwana sai kace Karuwa,Key ya sa ya zare yace ba abinda zan miki fa,Ka bude min
na tafi,yaki budewa har ta gaji da rokonsa ta zauna a kujera.
Hanan kuwa yau kwana ya dawo kanta,ganin Bai dawo gida na sai 6pm sai haushi
Yana shugowa ta fara korafi da ace Amarya ce ai tun 2pm kana gida baka fita ko Ina
amma Dake kwana nane shine kazo min gida sai 6pm,kwanciya yayi a kujera ya gaji ya
Sha aiki har ma zazzabi yake ji,yace Baki ga bani da lafiya ba ma,ohhhh ta haka ka
bullo wato sabo da karka min komai zaka ce baka da lafiya,sai a ranar kwanana
rashin lagiyar zata zo wlh baka isa ba,sai ka jiyar Dani dadi ko mutuwa zaka
yi,bacruwana da cutarka.
Mohsin yace me yasa Baki da hankali ne wai kin haukace gaba daya,ka dai haukace
amma ba ni ba,tana Masa abinda yafi wannan ya hakura ma amma yau sai ta fada a
akasi yace na sakeki Hanan,saki na yanzu biyu kenan igiyata biyu ta kare sai ka
cike min ta uku na huta gana daya da jaraba,dama ni aurenka ya isheni,auren
jaraba,annoba dangin tsiya dangin jaraba,yace na sakeki saki biyu,dama nayi Daya da
farko na sake ki saki biyu yanzu igiya ta kare babu aure tsakanina Dake har
abada,ya mike yaja tsaki ya fice.

Lokacin Kuma Hanan ta fara tsala ihu tana rusa kuka,Beauty har tayi addua ta
kwanta taji ana knocking,fitowa tayi ta duba sai taga Mohsin ransa a bace,tace
lafiya? Yace matsa na wuce,tace ba kwana na bane ka sani yau,bazan dauki hakkin
wata ba,tureta yayi ya wuce bedroom ya kwanta,ta dame shi da sai ya tashi ya
tafi,yace Hanan babu,fam fam na sake ta gaba daya karki dame ni,Beauty ba kunya ba
sai ta danna wakar barmani choge ba a waya,tana mulamulan duwaiwai kaga na goggoron
dake duwaiwai tana tika rawa,ba sharing ba sharing...ta kashe ta fada jikinsa ta
rungume shi,tace ya naji Jikin zafi....

Abba ne ya fito Yana tafiya wata galleliyar mota ta ubansu ta tsaya a saitinsa
tare da sauke glass aka ce Hashimu Dolo ,wa nake Gani kamar abokina Hashimu Dolo,
Hashimu ya Kalli me motar sai ya washe baki yace Jauro baron mata? Jauro baron mata
daga Ina yaushe kayi arziki haka,Jauro baron mata ne ya fito suka rungume da Abba
suna murnar ganin juna,yace ya iyali? Abba yace Alhmdllh Alhmdllh Kubra Allah yarda
Kubra tayi karko a gidan miji itace dai Daya jal har yau kamar filar machine,Jauro
yace yaranka nawa Hashimu? Hashimu yace guda shida,kwana nan na aurar da Yata,yace
Allah Hashimu,yace wlh ba iskanci ba cikin shege lafiya lafiya muka rabu,Dana
Mohsin har ya Kara aure,ubansa Bai samu ya Kara ba Ashe Karin auren akan Dana yake
shi yake kwashe dadin na hakura na bar Masa

Jauro yace kasan duk aure aurena ban taba haihuwa ba har na gaji Gani Allah ya
sa min son yara shine ni Kuma nake bi gari gari duk Inda naji wata tayi cikin shege
sai naje na rufa mata asiri na auro ta da cikin,Kuma idan ta haihu juyin duniya
nawa ne kawai,ko za a mutu cewa nake nawa ne,Abba yace amma Jauro ba karamin Dan
iska bane Kai,yace sekaru goma da suka wuce naji wata ance tayi cikin shege ta
haihu ai kuwa naje nace nawa ne ta karfi sai da aka bani Dan,Abba ya dinga dariya
yace yanzu nawa ka rike? yace guda tara duk yayan shegu ne Daya ne ciki Wanda bana
shege ba shi Kuma uwarsa ce mijinta ya mutu ya barta da ciki naji labari na aure
ta,Abba yace ai ba kyau wannan ba aure kayi ba,Jauro yace ai ni duk Wacce kaga na
auro me ciki to dama ni ban taba saduwa da ita ba,ko shimfida bamu hadawa ajiyeta
nakeyi a gidana na Bata ci da Sha a raini cikin ta haihu ta yaye shi sai na
sallameta,Yara gasu Nan duk sun zama samari Wanda ma ba Dan shege ba Yana Nan
hamshakin me kudi ne yanzu,sauran ma duk suna da aikin yi da sana'arsu,Abba yace ya
sunan me kudin? Annoor sunansa,Abba yace uhmm a Ina kake zanzo na kawo ziyara,Jauro
yace yanzu na dawo Kano da zama duk da yaran su ai har yau tunaninsu nine na haife
su.

BA EDITING YAU KU KARANTA DA HAKURI.

MASU SHARHI INA GODIYA.


AsmaBaffa
[1/2, 12:24 AM] AsmaBaffa: PAID GROUP 300

0175487861
ASMAU GARBA MUHAMMAD GTBANK

YAN NIGER
+22790795939

🏫TANTIRIYA 🏫
A GIDAN YARI

BOOK 1

106-110

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM

PAGE NAKU NE
Murjanatu Abu Nabanga
Ummy M
Rahma Mamuda (Mmn Hajiya

*👭GARKUWAR MATA👭*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya
mace ta na tattalin kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce,
kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana gyara kanta, duk yawan shekarunki idan
kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da na cika ku da
surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci🌿
🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da
matsalarsa, to shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai
dawo miki da martabarki duk lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki
yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi mai kyau wanda yake kassaara kowane
irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau irin wadanda ba
su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta
humra perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza
da ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in
abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu
shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano
amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna
bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai
kamar kina rayuwa a turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi
kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari DOMIN NEMAN
K'ARIN BAYANI
08089965176
07084653262

Abba ya Kalli Jauro yace yanzu matanka nawa na gaskiya Wanda ba masu cikin
shege ba? Jauro yace matana Uku,Ina Habiba matata ta farko ta kauye ai har yanzu
muna tare sai na karo Na'imatu da Nafisa,Abba yace dole goshinka ya dinga kyalli
Jauro,gashi ana ganinka an San kana cikin kwanciyar hankali,su Kuma masu cikin
shegen fa? Yace ai duk na basu kudi na sallame su mace tana yayewa zan sallameta da
kudi ta ware Danta Kuma ya zama nawa amma duk sun san iyayensu mata da dangin
Iyayensu mata a zuwan aure muka yi muka haife su na sake su.

Can garin da nake Minna an takura min da zagi Ina auri saki daga mace ta haihu
sai na saketa shi yasa muka dawo nan,dama shi Annoor Yana da private hospital a
Abuja,Kano,da Kaduna,yanzu zancen da nake Maka Yana Kano,Abba Yana Jin Abuja yace
garin Albarka garin da 'yata take aure,yazo Inshaallah in kazo ai zaka gansu yaran
sannan zan kawo Maka su har gida wasu daga ciki,Jauro shi da Abba duk kanwar ja ce
kowa da kalar nasa shashancin Kuma abokai ne tun a kauye,tare suka yi wasa,Jauro
iyayensa har yau suna Nan a raye sun tsufa tukuf,Yayi yayi su dawo birni gidansa
sunki,gashi Yana da kanne biyu mata da kaninsa namiji,matan suna aure a
kauye,namijin Kuma yayi karatu Yana birni a kaduna Dan sanda ne.

Jauro shima wani Dolo Dolo ne haka Wanda Allah ya zuba Masa jarabar son bautawa
mata,ko ya in budurwa suna mutunci to fa sai ya mata wahala,duk abinda take so sai
ya samo mata komai wahala,a kauye sanda Yana matashi ko Mai girman bishiya idan
budurwa tace tana so a tsinko mata mangoro ko kanya,dinya,ko dai wani yayan itacen
to Jauro ba sai ma matan sun ce ba zai hau ya tsinko musu,haka idan Abu ne a cikin
ruwa komai zurfin kogin sai ya shiga indai macece, ga shi da Tausayin mata da son
yara a rayuwarsa,sannan shi Yana son sana'a matukar zai samu kudi,sabanin Abba shi
da yafi so kullum ya kwanta ya huta a gida,shi kunyar mata ma yake yi tun Yana
matashi da yaga mata sai dai ya gudu ya buya.

Jauro kuwa sai bautar Yan mata amma idan ya auri mace Kuma to ko hula sai dai a
cire masa,amma matansa suna Jin dadi sabo da shima ba a fada da shi musamman da
mata shi yasa ake ce Masa Jauro Baron mata.
Asalin Jauro tsatson su Hashimu Dolo ne shima suna da dangantaka ta bangaren
uba.

Hashimu yace Jauro wai kuwa ya Tausayin mata har yanzu kana yi? Jauro yace sai
abinda ya karu,haba ai namijin da baya Tausayin mace yayi asara duniya da
lahira,mace me rauni wacce kullum jira take a Bata,fada kayiwa mace sai kuka,Abba
da sauri Yana karkada yatsa yace Banda Kubra karka ka kuma fada ba kowa ba,Banda
Kubra ai Rabon da na ga kukan Kubra tun daren farkon ta a gidana,lokacin da na samu
rikitiba tun lokacin Kubra Bata sake kuka ba sai da zanyi mata kishiya ,ta dinga
rusa kuka,da dare ma iya lallashi bata kulani,ban taba sani ni Hashimu Dolo Ina da
matsayi ba sai ranar,Kubra a baya wulakanci,Masifa ba abinda bata yi min sabo da
bani da kudi,amma fa tana da gaskiya kudin da nake samu bana kirki bane amma tun
Mohsin Yana karami nake Tara Masa kudi idan ya girma ya isa sauke farali zan biya
Masa yaje,shi yasa kudina ba ci ba sha,Kubra ce ta jajirce take Dan teaching har
yara suka girma Mohsin ya samu aiki ya karbe komai na gidan,Jauro yace Kai Kuma
kana ta Tara kudin? Hashimu yace kwarai kuwa Kuma Allah ya nufa bana na biya Masa a
cikin kudin dubu Dari biyu ta ragu na canja su zuwa doller na bashi ya Kara
guzuri,Jauro yace ka birgeni sai dai ai gwara ka ciyar da iyali ka bar Tara kudin
sanda Allah ya hore sai aje,Abba yace inji ubanka kasan Mohsin kuwa abin alfaharina
ne,Jauro yace bai kamata dama ka karawa Kubra kishiya ba wlh kayi mata halacci
itama ai tayi kokari,jaruma ce Kubra, Abba yace ta gaske kuwa har akan gado,Jauro
yace uhmmmm su Kubra an San ta kan tsiya ta mallake ka,Abba yace tuni ma ta gama
Dani har bargona Kubra ta tsotse shi,shi yasa kullum kamar ana Yankan Naman jikina
ita kuwa da kibarta jibgegiya ce amma ba Mai yawa ba,Kai Jauro Kubra bata tsufa
tana nan kullum Kara kyau take .

Kamar ba itace ta haifi su Mohsin ba da Naila ta ba,Jauro Yana dariya yace ai


zubin Larabawa ne da ita,ban taba Jin wani wari a Jikin Kubra ba,ko jego take bata
karni ko wani Abu,in ta haihu ma tafi tsabta Allah sai kamshi,Kai nayi dace fa,Kuma
tasan wanka a gida chakarewa take,da dare idan muka kulle kofa ta sa min kayan
bacci wallahi shara shara, Kai Ina Shan kallo,ka kiyayi Kubra karshe ce ba a ja da
Kubra, Jauro yace ai ni da Sanda na auri Na'imatu zata zo min da kazanta nace ke
wallahi na zare mata Ido Jauro ya furta Yana gwadawa yanda ya zare Idon,yace naci
magani na zare Ido nace karya kike Na'ima ban yarda ba waye ubanki, Allah sai ta
kiyaye ni ta nutsu washe gari Ina shigowa sai naga kakal kakal,nace kin taimaki
kanki,suka tafa da Hashimu Dolo,yace kaji masu zuciya ni Ina zan iya wannan
masifar.

Jauro shi dama idan Yana magana sai ya daddage sosai dole kayi dariya yanda yake
daddage wa idan zaiyi labari Kuma Yana yi Yana gwadawa, yanzu Dan Dolo muje naga
gidan naka zan dawo,Hashimu yace to baron mata muje a kafa suka taka kadan
ya nuna Masa suka yi musayan number, Jauro harda kudi ya bawa Abba masu kauri ya
wuce.

Washe gari Ango Baseeru da asuba ya farka yaji Abu ya danne Masa Rabin fuska gaba
daya,ya bude idonsa Ashe nonon Mummy ne guda Daya,yace sai kace malafa, ya janye
fuskarsa ya tashi Alwala yayi sannan yazo Yana tashin Mummy taki tashi yace ki
tashi kiyi sallah babba dake kina wasa da Sallah,Cikin bacci Mummy tace jiya na Sha
wahala a hannunka Dan Allah ka barni na huta,Ido Baseeru ya zaro yace na Sha wahala
ko kika Sha,ni da kika San nayi adungure a cikin bataliyarki shine zaki ce wani kin
Sha wahala kika Sha dadi dai,ihun da kika yi ni na taba Jin irinsa ma tunda uwata
ta kawo ni duniya,Mummy tace please just go,Baseeru yace wlh sai kin tashi ni bana
tarayya da me wasa da Sallah,bazan yarda da wannan iskancin ba,mene cikon musulunci
idan ba Sallah ba,ba a wasa da Sallah idan zaki tashi ki tashi madam.

Mummy da kyar ta tashi tace Ina Kwana? farin ciki ya kama Baseeru a ransa yace
Kai kaji wlh ta gaishe ni da wuri, shegiya taji Maza wallahi gaishe ni take,Mummy
ta shiga toilet sannan ya fita masallacin,abokin aikinsa me gadi Yana ta
tsokanarsa,Baseeru Yana fitowa yace Sabiu gaishe ni take taji Maza ba sauki,tsoro
na take ji tun kafin tayi Sallah sai gaisuwa,gaishe ni take, suka tafi masallaci
tare suna dariya.
Mummy tana idar da Sallah ba Azkhar ta koma Saman bed sai bacci, Baseeru Yana
dawowa ya kwanta shima,Mummy ya fara shafawa a hankali Yana cewa bacci kike yi?
Mummy Dake harkar Kwalbewa ce sai ta mike tace ai dama da na idar baccin bai dauke
ni ba,Baseeru ya fara shafa boobs dinta Yana wani yabon su kamar na budurwa basa
zubewa,ita da kanta tasan karya yake amma Kuma taji dadi akan ya kushe ta.

Baseeru harda rera mata Waka soyayya ruman Zuma bani na baki mu ta Sha,da dadi
kaso a soka ni dai tawa na rike,ni bazan guje ki ba,me kushen ke zan tatse shi
kamar gyada,Mummy taji tana dariya,yaci gaba yeeeeeeee kece cikon muradina ko kaina
za a datse,yarda ki bani lokacin ki.
Mummy sai taji ta dawo wata danya chakal,daga nan suka fara Kwalbewa
abinsu ,Mummy duk jarumtar Baseeru yau sai data kure shi,sai cewa take kar ka sake
ka kawo,Baseeru yace ya zanyi da ikon Allah Abu ya taho bazan iya ba na Kai
karshe,Kafin ta rufe baki ya kawo,tace to ka huta ka dawo wlh ban ma fara Jin komai
ba,Baseeru Yana haki ya Fadi a gefe Yana hutawa.

Kajin suka sake ci, tasa shi ya koma bakin aiki a haka,Aiki Baseeru yake kamar
doki Mummy kwashe dadi kawai take yi tana Nishi da kukan dadi,ta juya Baseeru ta
koma samansa ta dinga yi da kanta, Baseeru ya sake gajiya haka ya sake kawowa tace
wai ka huta mu ci gaba,Baseeru yace wlh Bada wuri ba,bazan iya ba wannan bala'in da
me yayi kama so kike a kaini asibiti,duk maganin da Baseeru ya Sha wai Mummy tafi
karfinsa a haka da Babu magani kenan sai dai a kaishi asibiti ma kenan.
har rana ta fito Yana haki yana hutawa har ya kwashe 2hrs 9am,Mummy tace muyi
wanka mu ci abinci sai mu sake yi anjima,Baseeru yace zaki kashe kanki fa ki dinga
hutawa,Mummy tace dama ni ban samu miji irinka ba Allah ya cika min burina dole na
more,Baseeru tsoro ya kama shi,ta fisgo shi tace muje muyi wanka yunwa nake ji,Suka
shiga toilet bayan sunyi wanka sun tsarkake jikinsu,ta fito ta shafa lotion dinta
me kamshi,ta tsara kwalliya ta gani ta fada,Mummy Yar gayu ce ta gaske ba dai iya
wanka ba,tana kashewa jikinta kudi,ko Ina kamshi take yi,Baseeru sai mannewa yake a
jikinta Yana Jin kamshin da bai taba jinsa ba,Ita Kuma tana ta wani Jin dadi a
cikin nishadi take.
tace a ranta wlh burina ya cika a duniya ko yanzu asirina ya tonu a kaini prison
dama wannan shine burina Kuma na samu,bare ma nasan bazai tonu ba.

Baseeru suna fitowa dining Chika tasa Sheyi ta shirya abinci,text ta turawa
Baseeru tace kaje wajen Sheyi ka sake karbar maganin tsumin Naila so nake kayi mata
fata fata,Baseeru yayi dariya yasan Mummy tafi karfinsa Dan ma da taimakon
maganin,yace a ransa wannan masifar ko a jinin su yake ne danginsu, shi yasa suke
iskanci dole su kasa rike kansu su dinga bin Maza ko Maza su nemi mata.

Baseeru suna gama karyawa yace bari na dawo,tace a dawo lafiya,Yana fita wajen
Sheyi yaje,tace Ango Yaya? yace bani tsumi ayi Overdose tafi karfina billahillazi
wannan sai Kun kaini asibiti an Kara min ruwa ko Leda biyar ce,Sheyi dai bata San
kan auren ba ta dinga dariya tace naga karyar iskanci Baseeru,Kai ba Dan iska ba to
ga mace nan Ajiya Babba tana magana da hausarta bata fita,yace ke munafuka bani ya
karba ya fice,a boye ya shanye maganin sannan ya koma ciki.
Yana komawa Mummy ta hau lagude shi.

A lokacin kuwa Spark ya tashi Naila da wuri yace kije a ramawa kura aniyarta
kiyi girki na kaiwa Mummy,Naila Dan kanta taji Yana ciwo ko Bata fi 8days ba a
gidan miji wai tace kaji kaina na ciwo ko ciki ne Dani,na fara laulayi,Spark yace
ta Allah ba taki ba yaushe naci amarcin da zaki samu ciki me nayi ma,Naila tace ai
zamu gani na kusa fara period, Innalillahi wa Innailayhirrajun daina fada min bakin
labari,akan kiyi period ai gwara ace cikin kika samu yanda zan samu Bado
lafiya,dawo ciki ne Dake Allah ya raya,dariya tayi tace 3days nake yi ai ba
dadewa,Naila murna take ko banza ta Dan huta duk da ta fara Dan Jin dadin amma tana
Jin zafin ma ba yawa gwara ta huta,girki taje ta shiryawa Mummy,Spark ya shirya
cikin 3qutr da Yar riga ya karba,Naila tace zan bika yace no yanzu zan dawo fa,ki
zauna na dawo muci abincin ko? tace ae tare da zama a kujera,kiss ya manna mata ya
fice,Yana fita Naila ta jawo wayarta ta kira Beauty.
Beauty tana kitchen Mohsin ya fita aiki,Naila tace ya ake ciki ke,Beauty tace
kalau Ina fada miki anyi gaba da shegiyar saki uku igiya ta kare ba saura,yanzu
harka nake,Kinga yanda yake ji Dani kamar kwai,Naila tace dama ni na fada tuni na
Dade da sakin Hanan amma ta makale,yanzu nasan kayan Yar banza sun Sha fitsarin
yara.

Beauty tace naji Naila kina dariya kamar da magana a bakinki,Naila tace ance ba
kyau fada an hanani amma daga wannan bazan sake fada ba,bazan sake fadar sirrinmu
ba tunda babu kyau,daga wannan na daina shine na karshe,Ina fada miki Hallare
dai,Beauty tace ae mutuniyarki kuwa ya akayi? Naila tace Hallare an waye anyi clean
yanzu Hallare ta fara hankali,jiya sai naji abu kamar daga sama in fada miki Dadi
dadi dadi,Beauty ta dinga dariya tace dama na fada miki ai ni yanzu bana so ma yayi
nesa dani,Naila a'a duniya sabuwa tamu na gode da na hadu dake Jamilu gashi na
auri Yayanki me Hallare duk gardi.

Naila tayi dariya tace wlh karki bari yaji kina fada min Hallarensa da gardi
idan ba sai yazo ya dinga min bala'i ba,Beauty tayi dariya tace wayyo Hallare
dadi,Naila tace ahhhh ke abin naki yayi yawa,Beauty ta sake shekewa da dariya tace
jira nake ya dawo wlh, Naila tace bari na hada kiran da Chika mu tayar mata da
hankali.
Chika suka hada kiran da ita tayi joining lokacin Chika a dakin Misam bacci ya
kwashe ta jiya,sai ya tasheta ta koma bed din shi ya fice ya koma daya dakin a can
ya kwana,tana kwance ya Sha wanka Yana kamshi ya shugo dakin ya zauna a kujera tare
da sawa a kawo mata breakfast.

An kawo kenan su Naila suka kira ta,tana dagawa tace amare,Beauty tace Allah
sarki Ina Jin tausayin ki,ba Hallare ba komai,Chika ta saci kallon Misam Dake danna
waya,tana so tayi magana ba dama ita yanzu tsoronsa take ji kar ya taba mata kirji
taga kwallon shege ne,tace Uhum ba komai Allah zai kawo min tawa,Naila tace ke
munafuka a Ina kike ne kin kasa magana,Chika tace Ina gida,duk yanda suka Kai ga
son Chika tayi magana ta kasa tayi mukus,sai da tace Allah ya nuna mana
lokacin,suna ta tsula iskanci daga tace uhm sai Allah ya kaimu,Misam Yana Gani
yasan wata maganar ake mata sabo da shi taki magana,Yace da Abaya ne da yanzu ta
fada min abinda taga dama,da yanzu ta yi min fitsara,yanzu kuwa Dana lallatse ta
gashi ta kiyaye ni,tana sake min iskanci zan sake tabawa ko banza naji dadi,har so
yake Chika ta Masa rashin kunya amma taki yi Dan ya samu hanyar latse ta amma taki
yi Sam Sam.

Su Naila suna cikin hirar Hallare Mohsin ya dawo karaf a kunnensa yaji Beauty
tace Naila kinji sweet Allah na zaci suma nayi,Yana zuwa ya karaso ya fisge
wayar,yace hello,Naila tace na shiga uku Yaya ne Kai da ka tafi aiki me ka dawo yi
gida,ubanki na dawo yi Naila wlh zaki ci ubanki,wato baki da hankali ko shine kika
kira matata kina koya mata zancen banza,Naila tace wato ni bani da gata tazo tana
lalatani zaka ce nice nake koya mata sabo da nice shegiyarka,Yace kin girme ta,a
ciki wa zai koyawa wani,ke kina da kunya ne dama,riga ta gama lalataki shegen Baki
kamar rariya ke a duniya baki da sirri komai sai kin fada kenan,Dariya Naila tayi
tace ai dai nace daga wannan shine na karshe nayi hankali Kuma babu kyau na daina
fada daga yanzu na daina,Kuma ma ai yabo nayi ba zagin Hallaren nayi ba bare kace
Ina Hana Spark,ni yanzu Yaya ko kace na Hana shi yaushe zan hana,wlh zan iya gaba
da Kai akan haka,dariya Mohsin ya boye kawai Dan Naila yasan kafin ta shiryu ta
daina sakin baki sai an Sha fama a haka ta girma.

Wayar ya kashe ya juyo kan Beauty Yana mata fada amma Beauty ta dinga girgiza
Boobs tana a girgiza kwankwaso kwasokwaso,Mohsin sai ya dawo wani Dolo shike nan
Kuma sai yayi mukus ya jawota jikinsa,tace me ya dawo da Kai ne yanzu? Yace
Bado,shi na dawo a bani na koma,daukanta yayi sai bedroom.

Spark kuwa har gidan auren Mummy yaje,shi tunda yaga gidan yaga Bai ci ace
Baseeru ne zai iya Gina gidan ba a ransa yace Allah yasa dai Mummy ba buhun kusa ta
auro ba,kudi basu da kama,yayi parking aka nuna Masa part din Mummy,Suna bedroom
ita da Baseeru tana tatse Baseeru wahala ta ishe shi,karfinsa ya kare Allah ya
taimake shi Spark yazo yana ta knocking har ya gaji ya shiga palon,Yana shiga yaga
Baseeru ya sakko daga sama da gudun bala'i ya fada kitchen a guje Yana rike da
wandonsa Yana gudu Yana kokarin daura tazugen sa,Ya hada gumi ya Jigata Yana Nish,i
ya bude fridge ya zaro robar ruwan Sanyi ya balle ya kafa a bakinsa kwat kwat kwat
harda matse robar ruwan bai sauke ba sai da ya shanye tas ya ajiye Yana Nishi,Yana
furta wayyo Allah wayyy wayyy....zata kashe ni,Spark Yana jinsa dariya ta kusa
kashe Spark.

Zama Yayi ya harde Yana latsa waya sai ga Mummy taci kwalliya ta fito palon
taga Spark, tace Dan iskanci zaka zo baza ka fada min ba,Spark ya kurawa Mummy Ido
har ta zauna Yana kare mata kallo,tace uban me kake kallo a jikina,dariya ya fara
yana rufe bakinsa da hannu,tsaki ta ja tace me ka kawo min? yace Naila ce tace bari
mu ramawa kura aniyarta,muma kin mana a first night kema a thousand Night sai mu
rama miki,tace kaji da shi,Ina Alhaji ya shiga ne? Alhaji.....Alhaji..Alhaji tana
kwalawa Baseeru kira,Spark yace Alhaji Manya,tace wlh zan Saba Maka Spark ubanka ne
fa,kamar mahaifinka ne,yace wlh ba kamar mahaifina bane bana sonsa bazan karba
ba,mijinki dai amma ni ba ubana bane ya isa ya haifeni,to kuwa sai ka rusuna ka
gaisar da shi,yace ai ni ko ku Kun San sai naga dama nake gaisuwa badan yanzu bama
da nayi aure Amaryata tana ta nuna min rayuwa tana bani tarbiyya a bed ta Ina nake
kula ku,yanzu ne nake hankali Ina nutsuwa,au itace ma take baka tarbiyyar? Spark
yace ahhh itace, jam'i akan lokaci rannan ma da Liman bwai zo ba ni na ja
Sallah,duk Tarbiyyar Amarya ce,Kuma tafi iyawa,tafi iya bada tarbiyya dan ni nafi
Jin maganar ta,wato itace ta Isa da Kai? Yace kamar dai hakan,dariya tayi tace
Allah ya shirye ka,bani abincin ta janye gabanta.

Baseeru ne ya fito daga kitchen ba riga sai yanzu yaji kunya da yaga Spark,Spark
yana sani yace Babaaa....harda shagwaba,Baseeru yace Na'am Danaaaaaaa.......shima
ya fada harda ja a karshe,Spark a ransa yace lallai wannan kwallo ne,Hannu Baseeru
ya mika Masa suka gaisa,Spark yace Yaya Mummyn tawa, Mummy tace tashi ka tafi
gidanka wannan wanne irin rashin mutunci ne,sa'anka ne,Baseeru yace easy easy ba
yiwa yara haka,su yara da dabara da lallashi ake bi da su,yaran namu na yanzu basa
ji,sai addua fada da zagi ba shine ba yaron nan Spark ki dinga binsa a hankali,wani
bakin ciki ya kama Spark ransa ya baci matuka abinda Baseeru yace Masa shine yaron
ma,da aurensa da komai,Nan take ya dawo asalin Spark dinsa kamar bai taba dariya
ba,ya mike yace Mummy warn your Husband,warn him Ina da matata ko bani da mata nafi
karfin yace min yaro,Mummy taji tsoro Bata son fushin Spark ko kadan shi yasa ta
lalata shi a haka da ransa ya baci sai taji tsoro ta fara lallaba shi dole yaro ya
dinga abinda yaga dama,yace nifa Mummy ba rashin kunya nazo yi miki ba sometimes
Ina yin Abu ne da kawai na miki wasa watarana Kuma kune kuke bani haushi Kuma shiga
gonata Ina muku rashin kunya,ni Kun San halina indai za a shiga gonata ni gaskiya
baza a ji dadi ba amma idan aka kyale ni sai a zauna lfy,Mijinki ne Kuma ai na
gaida shi sabo da nazo na gaida ki da shi nazo amma Kuma sai ya ce min yaro da aure
na magidanci da ni,da iyalina,abinda yake yi nima in na koma zanyi sai nayi Wanda
ya fi nasa nasan na fishi jarumtar shine zai ce min yaro, ya juya zai fice Mummy
zata bishi Baseeru ya riketa yace kyale Dan banza ya tafi ,yace Dan ubanka kafinl
ruwa gudu wato baza ayi Maka fada ba,to wlh baka isa ba ni tarbiyya zan baka idan
Iyayenka sun kasa ni zan iya da Kai,bazan auri uwarka Ina gani ka lalace ba, Spark
Yana jin Baseeru yana Masa fada harda zaginsa,Spark yace yaci darajar Mummy wlh da
sai na daure shi..

Naila ganinsa tayi ya dawo ransa a bace,tace me ya faru? ka fita normal ka dawo
da bacin Rai,waye ya taba min mijina,Spark yace share kawai,Kunun Aya ta kawo Masa
da ta hada ya dau Sanyi ya Sha Madara,tana bashi a baki tana shafa gemunsa Spark
sai ya warware ya manta ma da bacin ran ta sashi a gaba tana ta Masa hira tana Masa
abin dariya bai ma San ya fara dariya ba,kwanciya yayi a jikinta suna ta hirarsu ta
masoya cike da so da kauna.

Rafeeq tunda ya zauna a gefen bed ta shiga bargo suna ta hira duk son yaji
sirrinta taki yarda,har bacci ya kwasheta bata sani ba, Rafeeq yace ni dai gaskiya
ba da zuciya daya na baki gado na ba,a dakin wa zan kwana ni bana kwana da kowa a
kan bed ko na namiji ne,bare mace,Ni ko aure nayi Ina zan iya kwana da matar bana
son takura,amma ni wlh a bed Dina zan kwanta Baki isa ba Malama ni dama Bada zuciya
daya na baki room dina ba,ba a shigar min room,Malama tana can ta na baccin gajiya
Rafeeq ya bude bargon ya shiga yace ni bana son kwana da wani za a takura min ni,ni
ba Dan iska bane ta sa zan kwana da mace Allah ya isa Alhaki a kanta ya ja pillow
ya juya kansa can saitin Kafafunta suna yi kwanciyar Kai da kafa,Malama bata sani
ba,Rafeeq yayi adduoi sannan yace har yanzu ban wani balaga ba ai,Dan kawai ya samu
nutsuwa a ransa ya kwanta yake ta kawo uzuri wa kansa har yayi baccinsa.

Malama tana ta bacci ta saki bacci bacci yayi nisa tana juyinta ta dawo jikin
kafafun Rafeeq,kirjinta gaba daya a kan kafarsa,Yana bacci yaji Laushi lumis ya
sake gyarawa har gari ya waye ya rigata tashi sabo da kafarsa data danne,Dan motsa
kafar yayi yaji Laushi da sauri ya fisge kafarsa ya tuna tare da Malama me ya tashi
da sauri,yace ni me ya kaini kwanciya da mace, Istingifari,ya lallaba ya leka
fuskar Malama tana ta bacci,yace wannan ta fiye baccin tsiya, bargon ya bude a
hankali yaga rigarta wuyan ya koma gefe rabin breast dinta daya a waje,Rafeeq ya
kura Ido ya dinga kalla kamar Dan iska sai da ya ga zata tashi yayi sauri ya
lulluba mata abinta ya fice daga dakin da sauri a zuwan ba a nan ya kwana ba,sai da
yayi wanka ranar Gayun na daban ne ana da bakuwa,Islam Yana kallonsa yana ta
dariya,Knocking yayi dakinta da tire na abinci a hannunsa,tace shugo lokacin ta
shirya ta sake tsukewa cikin jean blue da riga tshirts tana zaune Saman bed tana
Jan carbi,Rafeeq yace ni na rasa gane mata wannan Ina ta dosa ne.
Yana shiga tayi murmushi tace good morning ka tashi lfy,ya daure fuska yace
lafiya tare da ajiye mata tire din a gefen bed,Yace kinyi bacci sosai dai ko?
Malama tace wa zai bamu bacci mu malamai kwana muke Sallar dare,ai sai karshen dare
muke bacci,lokacin da nayi bacci kana dakin Nan ai baka dade da fita ba na tashi na
dukufa.

Rafeeq a ransa yace asusuwida karya matar Dana kwana tare da ita duk kafa ta
tasha laushin kadararta zata ce wai kwana take Sallah,a fili yace ki dinga sani a
addua,tace Inshaallah,yace ga Abinci Nan,tace na gode zauna muci tare,Yace a wanne
hadisin aka halatta cin abinci da matar da ba muharrama ba? tace amma ai ka iya
zancen Nono,yace to abinda na Sha na girma ba dole na dinga tuna shi ba Ina kewarsa
in Kuma zaki tuna min to,Malama ta hada tea dinta ta kurba tace sai dai ka hada da
bado din sai a baka ai ka daina iskanci a baki ka tsaya kayi na gasken guy,a baka
ta back a baka front, ta daga Masa gira tace ya kace? Rafeeq yace a ransa wannan
malamar tafi karfina Yar iska ce,yace karki lalatani ni bana kula mata wlh ki
tambaya kiji ban taba hira da mace ba wlh ni sai a kanki,Ikhram tace to nufinka Nan
sa'a nayi ko dace don kayi hira da ni? Ai ka godewa Allah da nake kulaka Kaine ya
kamata kaji dadi Kana Hira da Malama Ikhram,wai ya sunanka? Yace ban sani ba,ya
dauki tea din nata zai Sha tace bani abina abina ka hada naka,mika mata yayi ya
fice daga room din.

Mima kuwa tayi tunani taga Misam yana da saukin Kai,Tausayin Wahida take yi
irin yaudararta da Spark yayi kawai sai tace ai Taga Wahida suna Dan shiri da Misam
sabo da haka shi zata sa lallai ya auri Wahida ko Dan mahaifiyarta dake
prison,Chika tana tafiya daga Hotel din Mima ta kira Misam lallai yaje tana son
ganinsa,ya zaci wani abin ne yaje da wuri,Yana shiga bedroom ta ja shi suka
zauna,tace Misam? Yace Naam,ni na haife ka ko? yace ae ke kika haife ni a labari
amma ai ni ba a wajenki na taso ba a wajen Kawu na girma an tana bani labari dai
kece kika haife ni,Mima tace what ever dai kasan nice na dauki cikinka wata Tara,na
Sha nakudarka na haifeka,yace ta ya zan sani sai da aka bani labari ni nasani ne?
lokacin ai ba ni,Kai karka Raina min hankali tambayarka nayi kasan dai nice uwar
dana haifeka ko? Uhmm yace,tace to Wahida nake so ka aura Kuma wlh kace a'a bazan
yafe Maka ba sai ka aure ta,Misam yace Wahida din zan aura wasa kike ko me wlh Ina
da wacce nake so ni,idan Kuma kince haka to kuwa sai dai a daura min aure da mata
biyu rana daya,Waidan da duk Maza sun tabe ta kowa bashi jikinta take,Mummy tace
Kai Dan uwarka wacce macece baka taba ba,ko iskancin da kake an fada Maka bamu sani
bane,mene baka yi zinace zinace,Misam yace ba komai zan miki biyayya amma sai dai
na auri mata biyu amma ni bana son Wahida Kuma ba abinda zan mata a bawa Rafeeq
mana shine baida budurwa a bawa Rafeeq ita Dan Allah Mima ni wlh Ina da wacce nake
so idan taji baza ta aure ni ba,Mima tace Kai ka sani Kuma saura kaje ku hada baki
da yan uwanka da Yan uwanka da ubanka ka sani ban yafe ba indai baka aureta ba,Yace
yanzu akan wata zaki min baki,ki bari naji da abinda yake damuna mana amma ki min
baki akan wata mace,ai banyi Maka baki ba nace idan baka bi umarni na ba,tashi yayi
ya fice kawai ya bar gidan.

Ransa a bace kamar zaiyi kuka,Yana Fita Mima tace wlh cikinku ko Rafeeq ko Kai
dole sai kun auri Wahida uwarta tana prison yarinya me kauna ta ai sai a taimaki
uwarta taji sauki a ranta tunda yarta kenan mace sauran Maza ne.
Misam Yana fita yace bari na tafi wajen gagararre Spark ko zai samo min mafita
sai ya wuce gidan Spark,shi Kuma Rafeeq Mayen Malama yana can Yana faman bauta,tasa
ya dauketa a mota sai tace ya kaita waje kaza ya kaita waje kaza Yana ta faman
gantali da ita a mota,shi wani dadi ma yake ji kamar kar su rabu tunda Malama ta
iya sakin zance shi lafiya Lau.

Misam ya shiga gidan Spark afjajan suna bedroom suna soyewa sai faman kwalawa
Spark kira yake,Spark.....Spark.....Amarya.....Naila....Aunty....shuru suna jinsa
ma,Spark yace rabu da shi Misam ne, Misam zama yayi Yana jiransu shuru shuru sai da
suka gama abinda suke yi suka fesa wanka suka fito,Naila tace yau ma zafin ya Kara
ragewa saura kadan,ya dauketa Yana murna yace na yau yafi na kullum yanzu nasan ni
Ango ne,Kai ban taba Jin dadi irin na yau ba,Naila tace na rasa Wanda yafi Maka
dadi kullum sai kace na ranar yafi dadi,Goyata yayi a bayansa suka karaso, Spark
yace ya aka yi kake ta kwala min kira,ai dama Kuna kuna jina? Ina jinka mana Ina
can Ina ta Sparking ya zan kulaka,menene haka kamar anyi mutuwa?.

Naila ta sakko daga baya suka gaisa ta shiga kitchen ta kawo Masa abinci da
kayan Sha,yace na gode,tashi tayi ta koma Sam sabo da idan Dan uwa yazo ya kamata
ka bar su suyi sirrinsu.
Spark yace ya aka yi? Yace Mima ce tace sai na auri Wahida ko Kuma Bata yafe min
ba,Spark yace ba wani Mima baza ta iya yi Maka baki ba,duk tafi sonka fa ai ko ni
da bama shiri baza iya min ba bare Kai tab,Misam yace tace wlh sai an daura,Dan
Allah share zancen nan Kai kamar baka da wayo kace ka yarda a daura da mata biyun
ranar sai taji an daura da daya tal,wai yarinya ita bata da samari ne sai mu,dama
Dan iskan Nan aka likawa Rafeeq,Misam yace tab ai tasan da kyar ya dawo ma Yana
zuwa gidan tana cewa ya aureta zai daina zuwa baza su sake ganinsa ba.

Wa kake so Kai to dama Manemin mata Yana soyayya? Misam yace bana son wulakanci
Chikar gayu nake so,Kake sha'awarta dai,idan Dan sha'awa ce wlh bazan aure ba,Ina
da matan da suka fita ma,amma shi so na daban ne,Kai ni duk matan da nake kulawa ma
babu kamarta ciki a dalilinta ma na rage kula mata sai na Dade banyi sex ba,sabo da
tsoro nake ji kar ta kamani,Spark yayi dariya yace tsoro? Chika din? Yace wlh sai
naga kamar zata ganni hankalina baya kwanciya tsoronta nake ji ni dai.
Spark yace Kai dai baka son Wahida? yace ae yace an gama ba a boye ma za ayi ba
Kuma Mummy da kanta zata hakura ni na fada Maka zanje gidan.
Misam yace har naji dadi ya fara cin abincinsa.

Annoor yana zaune a Office dinsa yana shegiyar yangarsa da ya Saba yaga Yan
sanda sun cika Masa Office,ko dagowa ya kalle su baiyi ba,Dan sanda suna cewa You
are under arrest amma ko kulasu baiyi ba,wani a ciki yace Malam da Kai ake magana
Wayarsa yaci gaba da latsawa,tsawa suka Masa ko gezau,wani a ciki ya daga hannu da
niyyar marinas Annoor ya rike hannun ya kwashe dan sandan da Marika har biyu,yace
ni zaku rainawa hankali kuje zanzo,waya suka yi aka kawo musu motoci da Yan
sanda,mutane suka cika makil a Private hospital din nasa,yaki yarda a
kamashi,mutane aka taru ana bashi baki akan yaje kawai kar su tozarta shi,yace shi
ya Isa yace wai zai min aski Ina askin banza doka ta Bada dama ayiwa wani aski haka
kawai,Tara suma da kitso haramun ne? In nayi laifi ka kamani amma wai batun kace
min sai mun Maka aski bai taso ba,ko uban waye bai Isa ya min aski ba,yanzu duk
akan aski kake wannan masifar cewar Dpo yace ae ai rainin hankali ne,idan laifi
nayi quietly a kamani amma zaizo yace zai min aski ubansa ne ya fito min da
gashin,Yasan irin kudin da nake kashe Masa,kasan man nawa nake shafawa? Inama ya
taba min gashi ya gani,kamani a kamani na yarda idan laifi nayi amma na mene zasu
shugo suce za a min aski burar.....Shaver....shaver taci kut....hour suka kwashe
Annoor Yana bala'i akan sumarsa,sai da mutane suka dinga Bada Baki sannan ya hakura
yabi Yan sanda Station dan shi bai San me yayi ba kawai dai ya gansu a Office
dinsa.

KARSHEN BOOK 1
MU HADU A
BOOK 2

MASU SHARHI INA MATUKAR GODIYA

ZAMU HUTA NA KWANA UKU KO BIYAR ZAN DAWO MU DORA DAGA INDA MUKA TSAYA

Book 2
TANTIRIYA A GIDAN YARI
YARAN JAURO

Bangaren su Misam duka za aci gaba.

AsmaBaffa

You might also like