You are on page 1of 83

[07/11, 16:57] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....

*💦

*NA:SLIMZY*✍🏻
Wattpad@slimzy33

*marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎

*RUD'ANI*💥

*DUHU.....*🌑

*1*

Hannunta dafe da kuncinta, batare da yabari ta dawo hayyacinta daga azabar data sauka a tsakiyar
kwalwalwarta ba, cikin zafin nama ya ƙara sauke mata wasu tagwayen maruka, yana nuna ta hannu ya ce
"How dare you talk to me like that eh? Sai na kashe ki a banza na kashe jakar ƙauye babu abinda uban
wani ya isa ya yi, empty head" Sameer ya riƙe hannun abokin nasa yana dukan kafaɗar shi ya ce "Common
my friend, akan wannan kake ɗaga jijiyoyin wuya?" A fusace Mansoor ya ɗaga hannu ya ce "Sam, barni irin
jakan ƙauyen nan maganin su kaci uban su" Cike da tsiwa hawaye na zuba a kuncinta, amma bata karaya
ba DINA ta ce "Kaci ubanka dai, nawa uban ba zai taɓa ciwo ba, daman daka ganinka maye ne kai wlh" Sam
ya saki baki yana kallon Dina ganin bakinta yaƙi mutuwa, Mansoor wanda ake masa laƙabi da Man ya ce
"What!" Sai kuma ya yi kanta, da gudu ta take ƙafafuwanta ta ruga a 136 tana cewa "Ohho dai kaji da
warin wiwinka....."

cikin zafin nama samir ya rukosa wanda tuni dariya ta cika masa ciki ya cafko mansoor da jikinsa ke rawa
kamar mazari yace"calm down man ya karamar yarinya kamar wanan zaka bita?idan ka bita me zakayi
mata?bayan kaine zaka zama abin kallo a cikin garin nan dubeka fa?"samir na nunasa da yatsa ya cigaba da
magana "karka zubar da class dinka akan DINA kaji abokina kaima narasa dalilin dayasa kake shiga
sabgarta"wani kallo mansoor yayi masa batare da yace komi ba kawai ya jinjina kai saidai kallo daya zakayi
masa kasan cewar yana cikin tsananin bacin rai yayi fushi,samir murmushi kawai yayi dan yasan man bazai
taba magana ba yayi mamaki ma da har yayi musayar wadanan words din da Dina shida maganarsa ma in
kana tare dashi zaka iya kirgawa kasantuwarsa miskili marason magana da izza,....wucesa yayi kawai
magana kasa kasa kamar bayaso yace "kasameni a mota"be jira mai samir zaice ba yayi gaba abinsa yana
bin yaran dake tsaitsaye suna kallonsu da wani irin kallo mai cike da kyama yana mamakin meye abun kallo
a wajen su?bude motarsu yayi ya zauna a mazaunin mai zaman banza ransa a bace yake idanuwansa sun
kada sunyi jajir kansa ya dau carji maganganun DINA ke yawo a kwakwalwarsa"kaci ubanka dai daga
ganinka maye ne kai nawa uban bazai ciwo ba...mai warin wiwi"ransa ya kara baci ya runfe idonsa ita yake
gani lokacin da take fada masa wadanan maganganun tunda yake wata mace bata taba masa kallon banza
ba ballantana ta daga harshenta ta zagi ubansa......DINA....ya furta a zuciyarsa,yaja gauron numfashi ya
sauke yayi murmushin gefen fuska kamar yadda ya saba kuma dabiarsa ce koda yana cikin bacin rai,

Sam kuwa shafa sajen fuskarsa yayi ya saki lallausan murmushi yace "DINA Akwai karfin hali amma burgeni
kikayi inason mace mai courage"ya cije lebensa yana bin yaran wajen da kallo ya hangi wata yarinya tsaye
ta tsaresa sa ido kamar zata cinyesa,murmushi yayi mata ya yafitota da hannunsa ta juya zata gudu ya
karasa da sauri "dakata babu abinda zanyi miki kinji tambayarki zanyi ina ne gidansu DINA?"yace yana
murnushi ganin dik yadda ta tsorata yasan halin yan kauye,

cikin hausarta ta kauyawa tace"can ne gidansu bari muje in nuna maka amma kada kace nice na nuna
maka kaji?"jinjina mata kai kawai yayi yana murmushi burinsa kawai yasan gidansu dan tunda suke
haduwa da ita bai taba sanin gidansu ba gashi yau sun kwashi kallo da mansoor beyi hira da itaba yana
kewar hirarta da wawtarta, haka suka taka dik inda suka gifta su ake kallo,
Mansoor dake cikin mota na mamakin ina kuma sam zashi?yana kokarin kunna wiwi a hannunsa ya janyo
wayarsa zai latso numbersa kiran da ya shigo wayarsa ne ya kara bata masa mood yayi jifa da wayar
gefensa ya kwantar da kansa jikin kujerar motar yana sauke numfashi minti minti yana zukar wiwi.....

******
"Dina meyasa kikeso ki rinka saka kanki a matsala?yanzun gashi saade tace taga lokacin da kika zagi
wadanan yan birnin guda biyu da suke zuwa gidan gonar nan dake bayan gidan mai gari?meyasa kika
zageshi?har ya mareki?dubi yadda yatsunsa suka fito a gefen kumatunki?ko kin manta matsayinki ne?
babanki ba kowa bane a garin nan face mai facin tayar mota ni karki daukomin masifa"innahrta cike da
fada takeyi mata magana,

dina tadan tura baki tasa dumamen tuwo a gabanta ta gagara koda gutsurar loma daya tsananin takaici da
bakin ciki yasa wasu sabbin hawaye masu zafi ke kara zubo mata daga kyawawan feraren idanuwanta masu
daukar hankali,dikda haka bakin Dina be mutu ba "Innah ubana fa ya zaga harda cewa sai ya kasheni fa wai
yaga wanda ya tsayamun harda zagina yayi da turanci ya fadi wasu maganganu"ta zumburi baki,innah ta
tabe baki tace "koma meye yayi miki kece kikaja tunda kike shiga sabgarsu tunda ai ana ganinki da dayan
aka fadamun dik garin nan labarinsu akeyi baa san daga ina suke ba kuma an tabbatarmun kina zuwa
wajensu to ki shiga hankalinki tunda har maganar kisa ta shigo ciki"kwafa DINA tayi "innah ba abinda ya isa
yayimun in turanci yake takama dashi nima ai baba yace zai kaini makaranta in zama likita"innah bata kara
saurarenta ba ta dauko bokitin ruwan data ja a rijiya ta soma tatar kullun koko,

sallamar yarinya ce ta sa innah juyowa "ke yau bazamu siyi gyadar ba anata ciki wanan zamanin waye yake
ta maganar siyen gyada?"girgixa kai yarinyar tayi tace "ba gyada na kawo ba wai DINA tazo inji wani
balarabe"

"balarabe?kodai wanda ta tsokana ne ya biyota ya kasheta?"innah jikinta ya soma rawa,zumbur DINA ta


mike taci dammara da dankwalin ta ta dauki tabarya "koni koshi a garin nan idan be kasheni ba ni zan
kasheshi "DINA ta fice bata jira mai innah zatace ba hanlalin innah ba karamin tashi yayi ba tayi jifa da
abun tatar koko ta soma salati tana kwalawa DINA kira,ko saurarenta batayi ba sai surutai da takeyi,

Sameer na tsaye ya harde hannuwansa a kirjinsa yana facing kofar gidansu tun daga jikin labulen buhu
yake hangenta ya soma tuntsirewa da dariya yana hango abinda ke hannunta Yana kara kwashewa da
dariya yace "DINA...ho"yana murmushi tana yaye labulen buhun tace "ina yake dan wiwin nina fishi..."kasa
karasawa tayi ganin samir tsaye yana tuntsurewa da dariya,sakin tabaryar tayi tana murmushi tana kici
kicin kwance dammarar da tayi "ah ah Dina kinyi shirin fada ne?"ta zumburi baki cike da shagwaba tace
"ehh mana ba yace kasheni zaiyi ba?"tayi farr da ido ya kurawa fusharta ido yadda tayi jajir ga shacin
hannun mansoor kwance a fuskarta cike da tausayawa yace "taho nan kawata DINA zo inji na biyoki ne
nayi bikonki sam bazan juri zama nikadai batare da kawar hirata ba"

tad'an washe baki tace"Allah dagaske?"gira ya daga mata yana murmushi ta hararesa"kaima bazakayi
magana bane irin na abokinka kurma?"tuntsurewa da dariya yayi yace "nasan sai kin magantu yanzun dai
nazo bikonki kizo muje wajen hirarmu"

"Allah ya sauwake inje ya dukeni ya kasheni?bazanje ba banason ganinsa"bata fuska samir yayi ransa
yadan sosu ganin haka yasa DINA tadan natsu "banason kina fadin haka akan abokina kinsam yadda nake
tsananin kaunarsa kuwa?"ta ware ido. ta harde hannuwanta a kirjinta tace "saika fada ku Yan biyu
ne?"girgiza mata kai yayi yace "ko daya mu abokai ne aminina ne inajin tsananin kaunarsa mudin abu daya
ne da Ruhi mabanbanta abinda ya bambantamu kenan kowa nada gangan jiki da ban da ace gangan jiki
daya ne da nafi farin ciki babu abinda zai rabamu"murmushi tayi ta fahimci akwai tsananin shakuwa da
kauna a tsakaninsu saidai sunada banbanci wajen halaye,
"Yanzun dai ki gafarci abokina ki yafe masa marukan da yayi miki kinji?"ta tabe baki kamar zatayi kuka tace
"da zafi fa?"cike da shagwaba tayi maganar,ya zuba mata manyan idanuwansa yana murmushi yace
"nasani kiyi hakuri da wanine yayi miki marin nan da zan rama miki amma bazan iya rama miki marin nan
ba sakamakon Man ne yayi mikisu?"tace "meyasa?"

"saboda idan na maresa tamkar kaina na mara"tayi yar dariya tace "shikenan muje"ya jinjina kai yaja wata
sassanyar ajiyar zuciya,suka jera innah ta fito da sauri ta kwala mata kira "DINA ina zuwa?"murmushi Dina
tayi mata tace "ba dadewa zanyi ba yanzun zan dawo"cike da ladabi sam ya gaida innahr DINA sanan suka
jera tabi bayansu da kallo cike da fargaba da tsorom kada yaudararta sukeyi su aikata mata wani mugun
abin tasan halin DINA sarai gabanta na faduwa ta juya ta Shiga gida....

******
daga cikin motar ya kure kida yana bi a hankali idonsa a lunshe hannunsa rike da wiwi yaji ana kwankwasa
glass din windown motar dan tsaki yayi yasa hannu ya rage wakar sanan ya bude motar a fusace yaga
waye,sam ya gani tsaye da Dina tana ta dariya sun shagala suna dariya ransa ya baci ya tsaya yana kallonsu
saidai gabansa ne ya yanke ya fadi idonsa dayayi tozali da shacin hannunsa a kumatunta,ya lura hira sukeyi
basusan ya bude ba hakan yasa yayi gyaran murya,take dukkansu suka tsaida dariyar da sukeyi sam ya nisa
yace "ohh ashe ka bude nayi tunanin baka bude motar ba bakaji ba ai"DINA ta dan yatsina hanci warin ya
dake hancinta tasa hannu ta rike hancinta tana mazurai,wani kallo mansoor keyi mata wanda taji kamar ta
saki fitsari,da sauri ta cire hannunta daga hancinta taji kawai yayi kwafa yace "ashe kinada tsoro"ta
murguda masa baki kawai,yayi dariyar gefen fuska ya juya yana fuskantar sam yace "yadai what do you
want"girgiza masa kai kawai yayi "nadauka baka ciki ne ka Shiga gida ai shiyasa"ya jefa masa wani kallo
"kadameni dayawa"mansoor yace yana satar kallon DINA samun kansa yayi da son kallon kwayar
idanuwanta,juyowa tayi suka hada ido yana kallonta take ya kauda idonsa gefe daya yace"sai ka shigo bari
na Shiga ciki yau zamu koma?"yana tambayar Samir ne cike da isa da gadara,

"yadda kace"samir na murmushi cike da zolaya yace "kardai wanan fad'an ya rikide ya koma soyayya",

wani kallo yayi masa,kawai bece komiba yayi gaba abinsa,

"a gayas"DINA tace tana binsa da harara,murmushi man yayi kawai ya juyo idonsa da nata suka hadu wani
yarrrrr Dina taji tayi saurin dauke idonta cikin zucuyarta tace Allah yasa beji ba......
********
"momy tun safe nake kiran ya mansoor baya daukar wayata bansan meyasa ba"cike da shagwaba
matashiyar budurwar ke magana tana kallon momy idonta yayi rau rau,
"tou ke ya nabeeha inda sabo ai kin saba da miskilancin ya mansoor meyasa kikeso kidamu kanki kinsan
yanayin abu lokacin da yakeso kuma ya gadama ne ni narasa gane kan wanan abun naku"

"bazaki gane ba rufaida ni bansan meyake zuwayi wanan kauyen ba ma nafara suspecting dun wani
abu"tayi maganar a kufule cike da kishi sai lokacin momy ta yi magana "nabeeha kinfi kowa sanin mansoor
ai karma ki tunanin akan mace yake zuwa wanan wajen raayinsa ne nima banida yadda zanyi kuma shi
yasan bazai dauko mun wata yar kauye ya kawo ba"..

rufaida tadan ja tsaki tace "a birni ma beso mata ba sai a kauye?dama kincire wanan a ranki kawai kiyi
kokarin samun soyayyarsa kawai in kinada saa"rufaida na maganar ne tana kokarin saka kayan bacci tana
daure da towel momy ta yunkura tace "da nasan abinda kika kirani kicemun kenan da banzo ba wallahi
keda mansoor bazan iya da fitinarku ba"momy na maganar tana kokarin fita cike da tausayn nabeeha,

kara dialling wayarsa tayi a karo na ba adadi,


yana kwance ya kishingida yana kallon kiran nabeeha na shigowa ko motsi beyi ba balle asa ran zai dauka
sam dake gefensa yace "baka ganin kiran nabeeha ne?ka dauka mana kaji me zatace"

mamsoor ya kallesa ta gefeb ido yace "amma kasan DINA dazun tabani mamaki?"samir yayi murmushi
yace "mamakin me ta baka abokina?"shiru yayi bece komiba ya lumshe idonsa kawai kwayar idonta yake
gani masu zara zaran gashi da yalwar gashin gira,sanan amon sautin muryarta tana zaginsa keyi masa yawo
samir ya cigaba da danna laptop dinsa har ya manta da suna magana yaci mansoor yace "tanada courage
sosai....babu macen data taba kallon tsabar idona ta fadamun magana sai ita"murmushi samir yayi yace
"toh fa to kayi mata magana mana?nima inaso ku sasanta ko saboda....."sai kuma yayi shiru be karasa ba
ya cije lebensa yana cigaba da danna laptop dinsa,

"dawa zamu sasanta?ni?hmmm lets see"kawai yace ya dauko wayarsa dake cigaba da ruri ransa a bace
yace "owoooo nabeeha why?you are disturbing my peace"ya dau wayar a fusace yace "i dont want to talk"
ta sauke ajiyar zucuya tace "why?"zucuyarta na cigaba da azalzalar ta da tsananin kaunarsa yace
"later"kawai ta kashe wayat gaba daya yayi jifa da wayar ya janyo bargo ya lullube kansa ya lumshe ido
DINA yake gani kawai dariyarta da fararen hakoranta,idonsa a lunshe yake murmushi,...
******
DINA na zaune a gaban mahaifinta bayan innah ta gama labarta masa komi daya faru yau ta dora da "kaja
ma yarinyar nan kunne kada ta daukar mana abun kunya a garin nan dan dik garin nan maganarta akeyi ni
banason alakartq da yan birni"

mahaifin dina yayi murmushi yana kallon dina yace"kinji abinda innahrki tace ko?nima ina wajen gyaran
facin taya aka fadamun abinda ya faru anga lokacin daya zabga miki maruka ya biki aguje DINA ki rufamun
asiri idan daukar magana zaki aurar dake zanyi"da sauri ta zabura tace "haba baba ka manta kace zaka
kaini birni inyi karatu?ka manta likita nakeson zama?"mahaifinta ya daura fuska yace "tou indai kinason
zama likita kada na sake ganinki da wadanan yaran yan birni kinji na fada miki ko?idan nasake ganinki dasu
aure zanyi miki kuma bazaki karatun likitancin ba"sosai Dina ta tsorata ta gyadawa mahaifinta kai "bazan
sake zuwa wajensu ba"

"dakyau tashi kije ki kwanta dare yayi"mahaifinta ya bata umarni,ta mike ta kwashe kwanukan da sukaci
abinci sanan ta Shiga dan dakin dage gefen na innahrta ta rufo kofar,
ta jingina da jikin kofar tace "yanzun ya zanyi da abokina samir mai kirki?gashi baba ya hanani muamala
dasu"zuciyarta babu dadi tayi rau rau da ido tad'anyi tsaki tace"gashi inada kudirin ramuwar gayya akan
wancen dan wiwin yanzun ya zanyi?bazai mareni yaci bulus ba"ta shiga safa da marwa a cikin dakin tana
tunani yadda zaayi ta dauki fansa akan mansoor....murmushin mugunta tayi take tace "yauwa nasamo
mafita bazan taba barinka haka ba"tayi tsalle ta fada yar katifarta tana dariyar mugunta......

*SLIMZY*
✍🏻
[08/11, 12:04] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎

*RUD'ANI*💥

*DUHU...*🌑

*2*
washe gari,
Innah na zaune akan tabarma ta kunna radiyo baban Dina na zaune a gefenta yana gyara jakarsa zai fita
yace "ina Dina?ko har yanzun bata tashi ba tana kwance tana sakarci?"innah ta girgixa kai tace "natasheta
sallahr asuba dai amma banida tabbacin ta tashi tayi sallahr yanzun nake shirin daukar bulala na shiga na
tasota"bata rufe baki ba Dina ta fito tana Mika hade da salati wani kallo baba yayi mata yasa ta katse
hammarta ta durkusa a gabansa "ina kwana baba katashi lafiya?ina kwana innah?"kusan hada baki sukayi
"kinyi sallah ne?"ta jinjina kai "ehh nayi sallah"tace gabanta na faduwa alhalin batayiba fashin sallah takeyi
kunyar ta fadawa innah takeyi,"dakyau dama ke nake jira na gargadeki kafin na fita kar inji kinje wajen yan
birnin nan kin nemesu fada kinji na fada miki ko su sakaki a mota su gudu dake bamu saniba"murmushi
Dina tayi tace cikin ranta "ai saidai su koma a kafarsu dan badai da wanan motar tasu ba badai akanta dan
jiji da kan nan ke hura hanci ba kamar wani basarake"baba ya daka mata tsawa ganin tayi shiru tana
murmushi yace "ke murmushin me kikeyi?"ta girgiza kai a tsorace "wani abun dariya na tuna,Allah ya tsare
ya bada saa"tacewa mahaifinta ganin yana kokayim zura takalminsa tun sassafe yake fita daga kauyen yaje
bakin hanya gyaran tayar mota,bayan fitarsa ta zauna a gefen innah ta soma zuba mata hirarta mara kan
gado cikin hirar harda labarin sameer take ba innahrta wadda gaba daya batasan ina ta dosa ba,

minti kadan kamar an tsikareta ta mike "innah zani gidan su lubabatu na dubota kinga idan Rana tayi bazan
iya zuwa ba"shiru innah tayi tana karantar DINA ganin ta zuba mata manyan idanuwanta yasa ta gyada
mata kai "kiyi sauri kada kidade kuma karki biya wajen wadanan mutanen"ta jinjina mata kai tana
murmushi,

mansoor kasa sukuni yayi haka kawai yakeson ya fita zaga gari ko zaiga mara kunyar daya dauki dammarar
koya mata hankali dan haka Sameer na bacci ya dauki wayarsa yasa ear pice kunne daya,yana sanye da
wasu kayan sanyi masu ruwan toka kansa babu hula yabi cikin garin yana tafiya yana haduwa da almajirai
yana basu sadakar kudi dik wanda ya gaishesa saidai ya daga musu hannu yayi musu murmushi,DINA ya
hango ta bullo ta wani lungu tana tafe tana rera waka da zazzakar muryarta tsaki yayi yace "shashasha tana
tafe tana waka kamar ba mace ba"yad'anyi tsaki ya makale a jikin bango tazo ta wuce,wani iri. faduwar
gaba taji da sauri ta juya babu kowa sai wani irin kamshin turare takeji wanda ta rasa a ina ta taba jinsa,jim
kadan tayi a cikin lungun tana waige waige yana kallonta da narkakkun idonsa gashin kansa yasha gyara sai
walkiya yakeyi tayi tsaki "sauri nakeyi kafin su tashi subar garin nan in rama abinda nayi niyya yau saidai
mutum ya koma birni a kafa"tayi maganar tana kwafa,ransa yadan sosu yasan dashi take ya danne
zucuyarsa kada ta gansa yabi bayanta tana tafe yana biye da ita wayarsa ya fito da ita ya danna recording
da video tana wakar sarmadan ya masoyi sarmadan sarmadan....tsaki yayi yace "village girl baki sai rashin
kunya"ya girgiza kai har suka isa kofar katafaren gidan gonar mahaifinsa ya makale a jikin gate,tana waige
waige babu kowa a wajen sai kukan tsuntsaye dake bishiyoyin dake cikin gidan ta daga kanta tana kallon
bishiyoyin cike da tsiwa tace "ni tsorom wanan bishiyoyin nake da wadanan tsuntsayen masu kukan
tsiya"da sauri ta cire abun iskar tayar motarsu duka hudun tana cikin cire na karshe ta gagara cirewa tayi
gumi kawai taga mutum tsugunne a gefenta,damm gabanta ya yanke ya fadi ta dago ido nan da nan jikinta
ya soma kyarma tana kokarin mikewa ya cafki hannunta "Dan Allah kayi hakuri kaji karka fadawa innah ta
kada ka kasheni kaji zan gyara muku tayarmu na iya wallahi"sosai tabashi dariya yadda jikinta ke rawa
yasan tsananin tsoro take ciki da furgici,cije lebensa yayi hade da sakin murmushin gefen fuska yace "let
me help you and removed it"kallonsa take bata gane meyace ba sai gumi dake karyo mata,

"kace?"ya girgiza kai yace "wawuya batajin turanci"tadan tura baki tace "niba wawuya bace"a ciki yace
"me kikace"girgiza masa kai ta shigayi tana kokarin kwace hannunta daga rukon da yayi mata ko motsa
hannunsa ta gagarayi,

sameer ne zaune gefen gado ya shirya tsaf yana kiran wayar mansoor bata shiga tsaki yayi "ina kuma man
ya shiga?inaso na fita na nemi DINA kafin mubar garin nan amma ya kama ya fita ina kiransa baya Shiga"

ya sake kiran wayar cikin saa ta shiga yana rike da hannunta ya kafeta da ido waya ta shigo wayarsa yace
"yauwa ina tunanin hukuncin da zanyi miki ne ga abokinki ya kira"fuskarsa a daure yayi maganar take
hantar cikinta ta kad'a cikin seconds hawaye suka shiga zubowa daga idonta yasa hannu ya dangwalo
hawayen yayi murmushi sanan ya danna recieve yace "yes i can hear you"

"kana ina ne haka?natashi tun dazun na shirya inaso na shiga cikin gari sanan mu wuce ban ganka ba ya
kamata mubar garin nan da wuri ana jirana ne nasa hannu a wata takadda a kamfani"harshensa ne ya
sarke ganin yadda ta jike da gumi har zai fadawa Sameer yana tare da DINA sai kuma ya fasa still idonsa na
kanta bayaso sameer yayi wani tunani,bayajin zai iya fada masa cewar ita ya fita nema bawai dan yanajin
wani abu akanta ba "kadan jirani ganinan zuwa"be jira mezaice ba ya katse wayar,

tsaki samir yaja ya kalli agogo ya dafe kansa "bazan tafi ban hadu dake ba kawata kodan in kara baki hakuri
akan abinda man yayi miki"cikin takaici yace....."ko ina yayi oho mtswww"yaja tsaki,

share mata hawaye man keyi batare da yace komiba ya saketa ta mike da sauri ya hango nadama a kwayar
idonta dikda yadda suke fada yasan ta tsorata "goge fuskarki"yace cike da isa,ba musu ta goge fuskarta
yace "meyasa kikayi hakan?menene dalilinki na bata mana mota"tayi shiru batare da tace komi ba shima
shirun yayi yana Danna waya amma yana kallonta ta gefen ido yana kallon yadda take gyara tsayuwa yasan
guduwa zatayi ya juyo da sauri "idan kika gudu ko?har gidanku zan biki"yace a takaice ta tsugunna a
gabansa "kayi hakuri ya mansoor"yadda ta kira sunansa a marairaice yasashi saurin kallonta ta hada gumi
sai zare ido yakeyi "ina jinki kina cewa zakiga a ina zamu tafi gida ko?"ta girgiza kai ta tabe baki cike da
shagwaba tace "ba marina kayi jiya ba shine nazo na cire muku iskar tayar mota dan in rama abinda
kayimun jiya kuma ai nabaka hakuri"shiru yayi yace "is okay you can go"bataji me yace ba yasa ta cigaba fa
tsayuwa yayi banza da ita kamar bazaice wani abu ba yace "kitafi nace"a dam kausashe yayi maganar ta
tsorata yasa tayi kamar zata zame sanan ta runtuma aguje tanayi tana waigensa murmushin gefen fuska
yayi ya shafa kansa sanan ya karasa ya shige gate din gidan yana murmushi,

kicibis sukayi da sameer ya rukosa "where are you going"wani kallo sameer yayi masa yace "kaida zaka fita
kona tambaya inda kaje?ba ina bacci ka fita ba?"Sameer yayi maganar cikin fushi,mansoor yayi murmushi
ya dafa kafadarsa "am sorry friend na fita zaga gari ne coz i cant sleep daren jiyan nan"Sameer ya sassauta
yace "menene ya hanaka bacci?"cike da kulawa ya tambayesa ya girgiza kai "nothing"sam yace "abinda ya
hanaka bacci ba karamin abu bane its okay ina zuwa"be jira shima me zaice ba ya fice mansoor ya tabe
baki ya wuce ciki abunsa yanata murmushin nasarar tsorata DINA da yayi yasan bazata kara mai rashin
kunya ba koda yazo watarana sun hadu,

kusan awa guda sameer ya kwashe yana neman DINA be ganta ba sosai ransa yadan baci,beji dadin hakan
ba , gashi mansoor nata kiran sa a waya yasan kiransa yakeyi su tafi bayan shi yaja masa rashin gani DINA
din dikda mansoor besan me yakeso yayi ba,haka ya kamo hanya ya nufo gidan daidai baban DINA ya gama
saka musu iskar tayar mota mansoor ya ciro kudi wajen dubu goma ya mikawa baban DINA yana kallonsa
kamarsu daya da mahaifinta dan dai ita fara ce"yaro wanan kudin yayi yawa"cike da girmamawa yace
"baba ka karba ka kara ka siyi kayan abinci"shiru baban DINA yayi kamar fa su akace DINA tayiwa rashin
kunya kamar zaiyi magana ya wuce yana mamakin ladabi irin na mansoor,shima sameer mamakin yadda
mansoor ya girmama mutumin yayi "ya ina kasan wanan?meyasamu tayoyin motar?"bece komiba yayi
gaba abunsa ya zauna mazaunin driver yace "shigo ni mu kama hanya"Sameer yasan ran abokinsa ya baci
dan babu abinda ya tsana kamar jira.....

cikin zolaya Sameer yace"nafika kosawa mutafi ko ka manta masoyiyata tayi kewata nima nayi kewarta
sosai?"mansoor yayi murmushi "nasani ai tunda kwana kukai kuna waya kamar zaku cinye juna shegen
kaya dik ka gama tsotse yar mutane bayan su daddy kai sukewa kallon mutumin arziki dan dai kawai ina
shaye shaye"ntsww yaja tsaki,

sameer ya shafa sajensa yacev"bazaka gane yadda nakejin shaukin kairatu bane"tabe baki mansoor yayi
yace "shege ka fito ka aureta"Sameer ya bugi kafadarsa "ko bakace ba"
mansoor ya cigaba da driving minti minti Dina ke fado masa a rai...

******
"wai nikam yaushe yaran nan zasu baro kauyen nan sudawo ne?yau kwnansu biyu a can fa kamar
"dattijon da bazai wuce shekara sittin a duniya ke magana kallo daya zakayi masa ka hango tsananin kamar
sa da mansoor,yana kallon mahaifiyarsa da kannensa dake zagaye da dining table din kowa na break fast
rufaida ta kalli nabeeha daketa juya tea tun dazun bataci komiba sai juyawa takeyi tayi kasa da murya "tin
dazun bakici komiba fa"momy ba lura dasu suna kus kus tace"kus kus din me akeyi ko kunsan mansoor din
na hanya ne"rufaida tayi murmushi tace "ah ah kawai dai"da sauri nabeeha ta take kafar rufaida ta girgiza
mata kai maana kar tayi magana a gaban Abbah,"tou kuyi ku tashi a shirya musu kayan karin kumallo in
sungadama da wuri zasu dawo"ta kalli agogo sha daya da rabi na safe nabeeha ta ture cup din tea din tace
"nakoshi idan kingama ki sameni a kitchen mu hada musu breakfast"rufaida ta jinjina kai momy tausayin
nabeeha takeyi fatanta kawai mansoor ya amince,
daddy yace "wainikam ko yar gida zaayi da nabeeha ne?"momy murmushi tayi kawai tana gyada kai
sallamarsu ce tasa parlorn ya rude "laa ga yaya man gasu sun dawo"rufaida farin ciki ya lullubeta shi kuwa
gogan kallo kawai ya bisu dashi sameer ne yaketa faraa ya tsugunna a gaban momy da daddy "daddy barka
da safiya"

"ai nadauka a can zaku zauna muzo biko ko mu biyoku da kayanku yan kwal uba dam kunga baku da
mata?"d kunada iyali bazaku tafi kuki dawowa ba"sai lokacin mansoor yayi magana "just two days dady
shine mun dade?"ya ja kujerar gefen momy ya zauna "good morning momy"cike da farin ciki take bubbuga
bayansa,"welcome,sameer bismillah kuzo kuyi breakfast ga nabeeha can yanzun ta shiga kitchen naga yar
gulmar nan taje sanar mata kundawo "sameer yayi murmushi ya dubi mansoor "a nan zamuci abinci ko
can gida wajen ummah nasan tayi maka alkubus"murmushi yayi "yes muje can kaima din nasan kafison
can bakaso dai katafi kabarni yanzun mu shiga muyi wanka sai mu wuce"daddy yace "ai dama nasan
bazaku rabu ba zamu gani in kukayi aure koda yake dukkanku baku shirya yin aure ba"Mansour ya lumshe
ido DINA ta fado masa sai kawai ya share yana dariya suka nufi sashen mansoor don suyi wanka....

********
zaune suke a wani kayataccen garden a cikin gidansu sameer matawalle kallo daya zakayi musu su baka
shaawa domin hatta da gyaran gashin kansu iri daya ne,sameer na rike da glass cup yana sipping juice
hannunsa rike da wayarsa suna video call da khairat,minti minti yakan saci kallon mansoor dake faman
blushing hannunsa daya rike da tabar wiwi da yake zuka ko cikin kwanciyar hankali,lumshe ido samir yayi
akwai wani bakon lamari a tattare da mansoor dake Sashi wanam blushing din dikda yasan dabiarsa ce
kasaita da rashin son magana da tsananin zurfin ciki, ajiye wayar yayi batare da yacewa khairat komi
ba"wai nikam man naso ace ka nemi gafarar abokiyar fadan ka DINA"juyowa yayi da sauri cikin wani irin
yanayi yace "ni kuma?bayan zagina da rashin kunyar da tayimun da haduwar da mukayi dazun na
kamata?"sameer ji yayi juice na kokarin sarkesa cikin mamaki yake kallon abokin nasa "ka kamata a ina?
kana nufin kai ka hadu da DINA yau?"gyada masa kai yayi cikin ko in kula yace "yess na hadu da ita,a karo
na farko that village girl ta bani tausayi na fahimci jahila ce saidai kuma haka kawai abubuwanta kedan
bani nishadi"wani kallo sameer yayi masa yace "really? don't tell me you are in love"

"with who?....that village girl?. haka,kawai dai tadan burgeni ne i just want to change her"gaban sameer
yayu dan kayataccen murmushi yace "ohh really kodai soyayya?da ka gwada yar soyayyar nan da ita kaga
idan munje kauye ka rinka rage zafi a birni kuma ga nabeeha gida biyu maganin gobara" yayi maganar yana
wani shu'umin murmushi. ya cigaba da magana "hmm am so happy to hear that from you of all people
mansoor......"lumshe ido mansoor yayi take ta fado masa a rai ya dire tabar wiwi din ya janyo gorar swan
water ya bude ya duddula a bakinsa idanuwansa suka kankance yace"see ba soyayya zanyi da ita ba i just
want to change her,da kake maganar rage zafi a kauye tayaya?wanan yar kankanuwar yarinyar?see look
bazan iya abinda kake magana ba, ballantana inji ina sonta" ya janyo wayarsa "come and see
something"yacewa sameer da tun tuni ya ajiye cup din dake hannunsa ya matso kusa dashi , videon Dina
ya kunna musu suka fara kallo daidai lokacin data dan furgita ba karamin dariya taba mansoor ba sai kawai
ya soma dariya,sameer kuwa mamaki ne ya kashesa tunda yake be taba ganin dariyar mansoor ba dik
amintarsu kodai son DINA yakeyi?take zuciyarsa ta gargadesa "ba sonta yakeyi ba anya mansoor zaiso
Dina?bayan ga nabeeha dake hauka akansa ko kallo bata ishesa ba"suka cigaba da kallo,sameer ya rinka
yiwa mansoor hirar dina shi kuwa samun kansa yayi da jin dadi sai murmushi yakeyi yana kara bashi
support akan ya canjata, zaiyi matukar farin ciki idan ya kasance mansoor yasamu abokiya.....wuni sukayi a
garden suna hirar Dina kafin daddare mansoor yayi sallama da sameer ya nufi night club....

sameer kuwa wajen khairat ya nufa,

suna zaune a cikin mota yana rike da hannunta suna fuskantar juna yana shafa lallausan hannunta yana
lumshe ido ta dubesa cike da tsananin shauki tace "nayi kewarka sam....katafi kauye kayi zamanka abunka
kullum sai nayiwa ummah kuka idan ta tambayeni menene saina kasa fada mata"

"khairatu nima ina tsananin kewarki musamman...."ya kashe mata ido yana nuna mata kirjinta da suka
cicciko a cikin rigarta ta lumshe ido "nida kai yan uwane me zaisa bazaka bari na sanarwa ummah cewar
soyayya mukeyi ba?muyi aure?? munada dangantaka fa kasani"ajiyar zucuya ya sauke "haka ne karki damu
ni zan sanarwa da ummah cewar ina sonki kuma aurenki zanyi"wani farin ciki ne ya lullubeta ta fada
kirjinsa da sauri ya rungumeta yana sauke ajiyar zuciya yana son khairat sosai kullum kara tsunduma yakeyi
a kogin kaunarta,bayaso yayi aure yabar mansoor ne yafiso suyi aure tare haka yasa hannunsa yana murza
nipples dinta tana sauke numfashi yana kara jadadda mata irin kaunar da yakeyi mata sun dade tare sanan
ya kira mansoor kafin yabar wajenta,
*********
juyi DINA tayi tacewa innah "nifa mamakin wanda ya bawa baba kudin nan nakeyi gaskiya beji dakyau ba
ba Mansoor bane sameer ne"innah tayi mata wani kallo "kinfisa sanin su kenan?yace mansoor yaji
ankirashi ke kince sameer to wai ya akayi kikayi musu farin sani haka?murmushi kawai DINA tayi cikin
zucuyarta tace "banajin wanan mai girman kan tsiyar yasan darajar Manya ballantana har ya dau kudi ya
bada a matsayin kyauta kuma cikin girmamawa" innah tace"ke tashi kibani waje inata magana kinyi banza
dani?"tura baki DINA tayi ta koma gefen tabarma ta zauna ta rafka tagumi yau tayi abun kunya,mutumin
daya tsaneta yake kyamarta shi ya kamata tana musu barna Allah yasa dai bai fadawa abominsa ba mai
kirki.....ta gyara kwanciya akan tabarmar haka kawai tasamu kanta da shafa hannunta tacw "dan iska harda
wani tabani dama mashayi ai ba abinda suka sani sai iskanci "tace a fili innah ta zaburo "waye ya tabaki
DINA?na shiga uku ni hajara "tayi kan DINA a tsorace dina ta mike tana mazurai da ido waye zata fadawa
innah ya tabata?gabanta sai faduwa yakeyi.....

*SLIMZY*
✍🏻
[08/11, 16:21] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎

*RUD'ANI*💥

*DUHU....*🌑

*3*

Innah tayi kanta ta shak'o wuyanta "waye ya tabaki naji kina fada?fadamun dama wajen yan iska kike
zuwa?"girgixa kai tayi idanuwanta sukai rau rau,babane ya shigo da kunshin bakar leda yana fadin "innar
DINA ina kike ga tsire na siyo mana mudan maida mugun miyau kwana nawa rabonmu dashi kai wanan
yaro Allah yayi masa albarka"kokarin zama yakeyi shasshekar Dina yaji ya zabura "ke innar dina lafiya
meyafaru?ya kika shakuremun yarinya zaki kasheta?"ya fuzge hannunta yace "ina magana kinyi banza
dani?kasa mai magana tayi tsananin bakin ciki da takaici sai haki takeyi Dina a raunane tace"Innah nifa ba
abinda nake nufi ba kenan nifa bance wani ya tabani ba"ta mike ta koma bayan babanta tana leken
mahaifiyarta kamshin tsire ya cika Dina dikda shakar datasha be hana miyaunta tsinkewa ba innahrta ce ta
labartawa babanta abinda taji tsaki yayi "kema kin biyewa shashanci irin nata kila ma karyarta ne kinsani
sarai dagangan ma sai Dina ta hada magana kuma tayi daidai da ita Allah dai ya shirya mana"kwafa innah
tayi ta wurga mata harara Dina ta zumburi baki tace "innah to tsiren fa"dariya tabawa baba yace "Dina
kenan dik shakar da kikasha wato hankalinki nakan nama"itama dariya tayi ta rufe fuskarta da tafikan
hannuwanta....
*******
zaune yake akan kujera gabansa makeken table ne cike da kayan kwalam da shaye shaye mata ne zagaye
dashi ya jinginar da kansa jikin kujera,wata ce tazo tana goga jikinta jikinsa cike da kwarkwasa tayi kasa da
murya"Man....yadai yau tunda kazo mashayar nan kakasa yin komi sai zukar taba kawai kakeyi"dago
rinannun idanuwansa yayi ya kalleta ya kauda kansa bece komi ba,ta cigaba da magana cike da shagwaba
da yanga tayi farr da idanuwanta kyakkyawa ce ajin farko kallo daya zakayi mata kasan yar manyan
mutanece "common lets dance please we miss you two days"hankadata yayi gefe guda sauran matan suka
kwashe da dariya suna nunata da yatsa "Tee kin kasa kyale man ko?ke a dole sai kinsamu soyayyarsa sai ya
kulaki ya baki attention?yanzun dubi abinda yayi miki da girmanki da ajinkina wajen nan Tee dan
maliki"wadda aka kira da tee ta mike ranta a bace tana jifansu da harara cike da takaici ta kalli rigar dake
jikinta,wata jar rigace suppegetti gown red a jikinta batada sama ta matukar karbar jikinta kirjinta dik a
waje yake Allah yayi mata wani irin shape na daukar hankali idonta jajir take kallonsa tanajin zafin abinda
yayi mata amma samun kanta tayi da marairace murya "man....menene na rasa?meye banidash?ka dubi
yadda ka dizgani cikin mutanen wajen nan?"bece komiba sai wani irin zafi da zuciyarsa keyi dik abubuwan
daya sha dan ya cire tunanin Dina daga kwakwalwarsa da shashancinta ya kasa cirewa daya rufe idonsa ita
yake gani,guntun tsaki yaja ganin tee tacigaba da tsayuwa cikin tsawa da izza yace "get out of my side
nonsense"yayi tsaki what?ta dafe kirji nan hankalin kowa ya koma kansu "ka kirani nonsense?dan kaga ina
sonka?me ka fini dashi?"tana maganar ne muryarta na rawa tana kokarin hadiye kukan dake kokarin kwace
mata ta danne zuciyarta ta hadiyi wani miyau mai daci tace "soyayya taja mun? kayimun haka?its okay
zaka kamu da soyayya kuma zaka jarabtu zakaji abinda mata keji akanka kuma bazan taba daina sonka ba
Mansoor"ya mike tsaye jikinsa har rawa yake ya daga hannu ya sauke mata mari,ta dago ya kara sauke
mata mari jijiyoyin kansa suka firfito "idan kika sake wata magana anan saina datse miki harshe keda
magana harabada",tsittt wajen yayi sai mazurai yakeyi yana bin guys din dake wajen da kallo,ya kai hannu
ya dauki wayarsa da makullin motarsa ya fice daga wajen teemah ta durkushe "ni ya mara? wallahi saina
fadawa daddyna kuma duk runtsi saina aureshi"dariya matan wajen suka kwashe dashi "iska na wahalar da
mai kayan kara"cewar wata dake sanye da mini skirt tana karkada kugu wani yazo ya ruko kwankwasonta
yana shinshina wuyanta,

"dama wani kikasamu kika rage zafi dashi"suka kara kwashewa da dariya...kwafa tayi ta kalli yan matan
dake rike da jakarta cikin tsawa tace "muje"ta fice daga wajen suka hau mata ihu,

"zamuga me zai faru fadan masu kudi nifa yau tunda naga mansoor cikin wanan mood din na shafawa
kaina lafiya sai wani video yake playing yana dariya"yan matan dake table din suke magana cike da gulma
suna kasafta abubuwan dake table din...
******
karfe daya na dare tafe yake a kan titi bakajin karar komi sai kukan karnuka ya kira Sameer a waya wanda
har ya dawo daga wajen khairat ya kwanta "hello sam.....kayi bacci ne?"

"yes ina shirinyi kana ina? yanzun nake tunaninka dama ka wuce gida ne ko nan zakazo ka kwana?"shiru
mansoor yayi sanan yace "ganinan zuwa muje gidan mu ka shirya idan naje gida nikadai daddy fada
zaimun kuma bazan dauka ba a halin yanzun zucuyata zafi takeyi"murmushi samir yayi yace "calm down
kaida waye?"mansoor yace "kadai ganinan zuwa"ya katse wayat yaja gauron numfashi ya furzar da wata
iska mai zafi ya furta "DINA....why meyasa kikeson damun zucuyata da tunanin rashin kunyarki?'ya furta a
fili yana murza sitiyari cike da kwarewa ya karaso gidansu sameer horn daya yayi saiga sameer ya fito cikin
kayan bacci riga da wando ya bude gaban motar ya shiga mansoor yaja,....

"wai karkacemun tuntuni kana club kana ta shaye shaye anya man?ka rage wanan abun
mana?"murmushin gefen fuska yayi yace "ko kaima Dina din ne zaka kirani da dan shaye shaye?"Sameer
yayi dariyar yake yace "na lura kanason maganar Dina tunda muka dawo gabaki daya inata kokarin gano
menene a cikin zucuyarka amma nakasa"hararsa yayi "babukomi kawai dai inason mace mai courage gashi
ta fito a kauye ba type Dina bace wanan kawai i just want to change her rashin kunyarta yayi yawa saidai
banason abu daya da take cemun"

sameer yayi yak'e "ai saika daina tunda kanasom canjata itama sai kayi abinda takeso kabar shaye shaye"

"no way "kawai yace daga nan be kuma cewa komi ba shidai sameer tunani ne cunkushe da cikin zuciyarsa
yanaso mansoor ya sauya amma waye zai sauya sa?be ankara ba yaji shiru jiyowa yayi yaga mansoor yayi
parking ashe har sun iso ya tsura masa ido "meyafaru?did i offend you?"ya kafe Sameer da ido adan
raunane "look kayi hakuri nima shaye shayen nan inaso na daina but am addicted to its kayimun addua kaji
banason naganka cikin damuwa"sameer ya girgiza masa kai yace "bana cikin damuwa abokina kaji?inayi
maka addua kaidim rabin jikina ne babu wani abu na wanan duniyar da zakayimun wanda zai haddasamun
bacin rai ko damuwa?inayi maka uzuri koda yaushe kamar yadda kake tsananin damuwa da lamarina
nima"murmushi yayi kawai yace "Thank you"sukayi musabaha suka rungume juna,

nabeeha ke kaiwa da komowa a sama babban parlor hannunta rike da waya ta hango hasken motarsa ta
kalli agogo karfe biyu na dare,ta koma da sauri ta zauna a kujera jagwab ta dafe kanta cike da tsananin
takaici anya bazata bar gidan nan ba kuwa?an turota ta nemi soyayyarsa amma yau shekararta daya a
gidan beyi magana da ita sau goma bawani takaici ne ya tokare mata kirji ta mike da sauri jim motsin
shigowarsu ta soma saukowa daga stairs cike da yanga,

"ah ah ga mutuniyas batayi bacci ba nabeeha me kikeyi har yanzun baki bacci ba?"murmushi tayi "sannu
da zuwa ya Sameer"tana maganar tana satar kallom mansoor da ko kallonta beyi ba ya kunna wutar
parlorn haske ya wadata ko ina,ya kamata tana kallonsa "ke lafiya kike kallona?"dam tura baki tayi kadan
cikin kissa da shagwaba tace "ina jiranka ne na hada muku dinner baku dawoba shine na zauna
jiranku"wani takaici ne ya cikasa yayi tsaki "look beyi miki kyau ba dama kin daina"ya kama kai zai wuce
cike da tsokana Sameer yadan daga murya yace "waye yakewa kyau?"hararsa yayi sanan yace "that village
girl" dariya sameer kawai yayi ya girgiza kai ya mike Mansour yace "lets go"nan suka jera cike da nishadi
suna Hira,sameer na tsokanarsa,

komawa nabeeha tayi ta zauna jagwab akan kujara ta dafe kai tace "village girl?"ta maimaita kanta na sara
mata "waye village girl?"tambayar da tayiwa kanta kenan cike da tsananin kishi ta yunkura ta mike tana
wasa da yatsunta "kardai yayi budurwa a kauye"wani abu taji ya caketa kamar mashi take kishi ya rufe
mata ido kenan wajen budurwa yake zuwa?kamar mansoor ya rasa waye zaiso sai a kauye?da sauri ta
bawa kanta amsa "no no its wont happen,nikadai zaiso saboda shikadai nakeso bazai taba son wata yar
kauye ba,momy bazata barsa ba dan babu abinda momy ta tsana take kyama sama da talakawa,balle ace
yar kauye ce?dole zata sa masa ido ta gano who's that village girl he's talking about wadda ta fita iya
shagwaba.....
*******
tare suka shirya suka fito suka gaida momy sanan sukai mata sallama kamar yadda suka saba shirin office
da fita tare sukeyi dikda kowa yana aiki a kanfanin babansa ne Sameer matawalle matashi ne kuma da
daya wajen mahaifinsa wanda yake tsananin so yakeji dashi dik abinda Sameer keso shi akeyi masa,a kofar
kamfanin matawalle Mansoor yayi parking "thank you driver idan an tashi zakazo ka daukeni ko insa driver
ya kawoni office dinku?"mansoor ya jinjina kai yace "yadda ka gani,lets see dai idan ban tafi kauye naga
wani sakarci waccen yarinyar keyi ba"fuskarsa a daure yayi maganar,samerr mamaki ne ya cikasa kafin ya
dakatar dashi yaja motar ya barsa nan tsaye,ransa yadan sosu ya tsaya yaji me zaice be tsaya ba,me zaijeyi
kauye wajen Dina?koda yake bazata sauraresa ba dama zama yayi ya nemi yardarsa ya kama kafa ta
wajensa,ya kada kai kiransa zanyi karyaje ya lalata komi nafiso na lallaba masa ita,yayi tsaki ya nufi hanyar
da zata sadashi da ofishin mahaifinsa,ko wace hanya yabi gaisuwa akeyi masa cike da girmanawa sameer
kenan matashi maiji da kudi da naira wadda dik abinda yasa agaba yakeso cikin kankanin lokaci sai ya
samu,

tura office din mahaifinsa yayi ya shiga cike da girmamawa ya gaishesa ya nemi kujera ya zauna "yadai
Sameer ina abokin naka?bezo ya gaisheniba ya wuce ko?"sameer yayi murmushi "nasan meyake gudu"

dariya abban sameer yayi yace ",gudun in tambayi yaushe zaayi aure akeyi ko?nagaji da ganinku haka
gaskiya musamman kai Sameer gara mansoor yanada yan uwa amma kai bakada kowa kai kadai gareni ina
bukatar kayi aure dan insamu jikoki"shafa keya sameer yayi yace "soon Abbah ina gab da gabatar maka da
matar da zan aura cikin kankanin lokaci,"farin ciki ne ya lullube Abbansa yace "dakyau da nayi Maka
gagarumar kyauta"sameer dariya yayi ya janyo takaddun da abbansa ke jira yazo yasa hannu ya soma sama
musu hannu daya bayan daya yanayi amma zucuyarsa na wajen mansoor Amininsa kiran khairat ke
shigowa wayarsa ya saci kallon mahaifinsa ya cigaba da sa hannuna takaddun....

********
Tunda ya hango mahaifinsa da wasu maaikata guda biyu gabansa ya fadi irin kallon da sukeyi masa da irin
hararar da daddy ke watsa masa yasa yadanji tsoro amma dayake namijin duniya ne hakan be nuna a
fuskarsa ba saima kara daure fuskarsa da yayi tamau tamkar be taba dariya ba haka ya karasa inda suke
cikin ladabi ya gaida mahaifinsa ba yabo ba fallasa daddy ya amsa sanan yace "shiga office ka jirani"ya kalli
daddyn zaiyi magana yace "nace ka shiga office ka jirani ko?"ransa ya dan baci taya agaban wadanan
maaikatan daddy zai masa tsawa?,bece komiba yasa kai ya wuce ko waigensu beyi ba ya bude office din ya
Shiga yana bin ko ina da kallo yayi tsaye ya zura hannunsa a aljihunsa,ya kalli agogon dake manne a jikin
bango kusa da tankamemen hotonsa dana daddynsa gefe hoton daddy ne da governan garin,ya danyi tsaki
"nifa banzo office din nan da niyyar zama ba fita zanyi"be rufe baki ba daddy ya shigo dauke da sallama
yana bin mansoor da wani irin kallo shekeke ganin haka yasa mansoor zama a daya daga cikin kujeru
bakaken dake zagaye da table din daddy "ai na dauka a tsaye zaka tsaya kana jirana ka nunamin ka kai
karshe a rashin kunya"wata ajiyar zuciya mansoor kawai yaja ya sauke ya durkusar da kansa batare da yace
komiba saidai cikin zucuyarsa na azalzalar sa to meye yayiwa daddy haka?maganar daddy ce ta katse sa
"mansoor nagaji da halayenka na wulalanci da tozarci abun har ya kai kan yar gidan danmalilki?"sai lokacin
mansoor ya dago kai ya kalli daddy,,"kalleni da kyau jiya kacemun kana gidansu sameer abokinka yau kuma
Alhaji ibrahim dan maliki ya kirani akan yarsa fatima Da ka mara a mashaya jiya inda kasaba zuwa ko?"

"Daddy....tafada abinda tayimun"

"babu ruwana da abinda tayi maka dan nasan halin isarka da izzarka ina jiye maka ranan da zakayi
danasanin wanan halin naka,na gida baka barmu ba na waje ma haka,nayi nayi ka kawo matar aure kaki to
bari kaji wanan yarinyar daka mara itace sadakin aurenka dan ita zan aura maka tunda bakada
mutunci"....cikin ko in kula mansoor yace "bana sonta bazan aureta ba....inada...."sai kuma yayi shiru
daddy ya tsura masa ido yana karantarsa akwai abinda yakeso ya fada saboda miskilanci da zurfin ciki irin
nasa ya kasa karasawa "kanada wa?kanada wadda kakeso?"girgiza kai kawai yayi ya mike "ina kuma
zakaje?munada aiki dayawa yau a office dun nan koma ka zauna"

"Daddy sameer zanyiwa rakiya yana jirana"shiru daddy yayi yana kallonsa yanaso ya gano wani abu a
fuskarsa tamkar akwai yar damuwa amma ya kasa gane hakab,"bazan hanaka ba tunda sameer ne amma
dik inda azahar tayi maka kazo kasameni ina jiranka"murmushin nasara mansoor yayi ya dibi makullan
motarsa daya dire a table din daddy da wayoyinsa ya fice daddy ya girhiza kai yace"Allah ya shiryamun kai
mansoor amma tabbas aure zanyi maka dan shi ya dace dakai'daddy ya janyo wasu files da aka ajiye masa
ya soma duddubawa....

*******
cike da mamaki Dina ke lallon mansoor wanda ke zaune a saman mota a kofar gidansu yara sun dajiye
motar sunata kallonsa, tsayawa tayi daga gefe yace "yadai ki karaso mana ko ance miki cinyeki zanyi?ko
wani abu zanyi miki?"ya tsura mata ido tadan kauda kai ta murguda masa baki sanan ta matso taku daya,
shiru yayi mata bece komiba ya cigaba da danna waya kusan minti goma sha biyar tana tsaye tana
kunkuni,dakyar cikin fushi tace "malam ni zan koma gida dan inada abinyi innah taje cin kasuwa tana gab
da dawowa tasani inyi mata tatar kunun tsamiya da tatar awara babu wanda nayi kana batamun lokaci na
tambayeka ina abokina samir bakacw komiba"ta zumbura baki,

"nace ki matso kinki matsowa ni kuma bazan rinka magana ina daga murya ba ba dabiata bace yanzun ma
kin karyamun doka banayiwa mutum magana sau biyu akan abu dayax"shekeke ta kallesa sanan tace
"saikace wani sarki ko basarake ni kafadamun meye ya kawo ka ko kazone yau din ma ka tabamun
hannuna,yauwa Allah ya isa yabamun hannu da kayi ranan"dariya ce ta kamasa ya soma yar dariya fararen
hakoransa suka bayyana wadanda suka kara masa kyau da kwarjini dimple din gefe da gefen fuskarsa suka
lotsa,Dina sakin baki tayi tana kallonsa yayi matukar mata kyau tamkar balarabe da take gani a TV gidandu
innahrta lubabatu kanwar mahaifiyarta,ganin yadda ta tsura masa ido yasa yace "lafiya?"dariya ta kwashe
dashi "ashe kana dariya na dauka mugunta rka bazata barka yin dariya ba"shi dai bece mata komi ba,ganin
yayi shiru yasa ta matsi daf dashi tace "gani nan to meya kawoka kayi abinda ya kawoka ka kama yan
matan kafafuwanka kabar gidan nan kafin innah ta tadawo kajamun bala'i"dirowa yayi daga saman motar
saura kiris ta kwasa aguje ta dauka dukanta zaiyi taga ya tsaya dab da ita tana jin saukar
numfashinsa,yanajin nata kamshin turarensa take shaka cikin wani irin yanayi tace "kamshin nan akwai
dadi"

"thank you,yauwa Dina ko?"yace yana daga gira, cikin kosawa tace "ehh ina jinka nifa dik na kosa katafi
dan kar shaye shayenka ya motsa kayi mana a kofar gida idan baba ya dawo aka bashi labari yankani
zaiyi,kasan babana beda wasa"sai surutu takeyi dik ta cikasa da magana babu full stop ransa yadan baci
cikin daga murya yace "shout up haba you like talking to much dina baki lura banason yawan magana
ba?"shiru tayi tana kallonsa cike da mamaki "yauwa nazo ne nima na kulla abota dake dan inason na
canjaki Dina"yace cikin wani irin yanayi,cike da mamaki da al'ajabi take kallonsa shima ita yake kallo tayi
masa kyau sosai dikda kayan jikin nata kayan Fulani ne yau amma tayi masa kyau fiye da ko yaushe Hatta
kitson kanta na fulani ne gashin nan sun xubo gaban kirjinta da bayanta ga wani sihirtaccen kyau dake futa
a fuskarta tasha jan janbaki,"umhmm talk kiyi magana zaki abota Dani?"cikin marairaicewa yayi maganar
besan yayi ba,yana kallonta ya daga wayarsa ya kashe mata hoto tayi matukar kyau daidai ta dago manyan
idanuwanta,

daure fuskarta tayi tamau tace "abota dani dakai?Allah ya kiyaye inyi abota dakai ni Dina dama abinda ya
kawoka kenan?to ka tattara yan matan kafafuwanka kabar kofar gidan nan tun kafin in tara maka jamaa,ni
bazan taba abota da dan shaye shaye ba mai isa da izza da mulki irinka ni Dina, niba kowa bace face
mahaukaciya kamar yadda ka zageni,sanan kayi ikirarin kasheni,koda kaga na tsaya ina lallabaka ne dan
karka fito da wuk'a ka lumamun a cikina"tana gama maganar ta watsa masa wani kallo wanda ya kasa
fassara maanar kallon ta kada kanta ta shige cikin gidansu ta rufo kofar langa langar dake kofar gidan,cikin
sauri ya karasa yana bubbuga kofar "Dina Dina ki bude kofar ki saurareni"

"bazan bude ba kabar wajen nan kafin babana ya dawo"ya cigaba da bubbuga kofar yana jiyo sautin
wakarta,yasan leka ta jikin ramin kofar gidan ya ganta tsaye kanta babu dankwalin kitson kanta ba karamin
daukar hankakinsa yayi ba ta juya baya tana tatar koko....ransa ya baci ya kaiwa iska naushi "why
mansoor.....meyasa kazo wajen wanan mahaukaciyar kauyen?ga abinda tayi maka nan"cikin fushi ya nufi
motarsa da sauri ya bude ya shiga ya rufo motar yana huci cike da tsananin bacin rai tunda yake mace bata
taba fada masa abinda Dina ta fada masa ba.....yasa key a motar ya tada motar har zai tafi ya kasa
zucuyarsa nayi masa zafi da tsananin takaici ya kashe motar ya kifa kansa akan sitiyarin motar yaga hakan
bazai masa ba ya bude wani akwati dake gefensa ya ciro wata kwalbar magani ya soma sha ya dauko karan
tabar wiwi ya kunna ya dume cikin motar sha kawai yakeyi idanuwansa sun kada sunyi jajir,bayan ya gama
ne wani irin bacci mai nauyi ya daukesa ya kofa akan sitiyarin motar....
*******
sameer Kiran mansoor yaketayi shiru dik ya shiga damuwa dikda yasan inda yaje hankalinsa na wajensa
magriba ta gabato be gansa ba kuma yasan baya office to yasan gida ya tafi amma meyasa zaitafi gida be
biya ta wajensa ba bayan yasan baya iya good two hours basa tare? tsaki yaja ya kwalawa driver kira
"isyaku....dauko makulli kazo ka kaini gidansu man"yace yana kallon kaiwa da komowa cikim sauri isyaku ya
dauko makulli "muje ranka ya dade"isyaku ya budewa Sameer mota ya Shiga mazaunin baya ya rufe sanan
ya zagaya ya tada motar suka kama hanyar gidansu mansoor,

khairat ke faman kiran wayar sameer ya kasa dauka hankalinsa a tashe yake besan wani hali mansoor ke
ciki ba koya dauki wayarta bazata gane kansa ba yanzun,

"kana nufin megadi mansoor be dawo gidan nan ba?"daddy ke tambayar me gadin gidan yace "ehh ranka
ya dade,tou kenan shifa sameer wani waje sukayi"yana cikin maganar mai gadi yaji horn din mota ya juya
da sauri ya wangle katon gate din gidan saiga bakar motar Sameer matawalle ta shigo daddy yace "au kaga
gasu ma aina dauka wani wajen yaje yau ma"sameer ne ya fito daga motar yace "barka da dawowa daddy"

"barka dai Sameer yanzun nake cigiyarku kaida abokinka ashe kuna hanya shi be gadamar fitowa daga
motar bane?"gaban sameer yadan fadi ya sosa kai yace "nikadai ne daddy"

"Kai kadai?ina mansoor din bayan tun shigarsa office yace zashi wajenka kana jiransa?ina kuma yayi
sameer nasha fada maka kasa ido akan mansoor da wanan shaye shayen nasa a matsayinka na amininsa ka
kasa canjashi"sameer yayi shiru kenan dagaake mansoor kauye ya tafi wajen Dina?daddy ya katsesa "ya
ina magana kayi shiru kafasan inda yake"

"daddy am dama inaga ya biya karbomin magani ne dan gida ya ajiyeni dama bana dan jin dadi nadauka
gida yayo shine na biyosa"daddy kwafa kawai yayi yabar Sameer nan tsaye sameer yace "why mansoor.....
kana wajen Dina ina kiranka baka picking?mansoor kodai son dina kakeyi?"tambayar da yayi a fili kenan ya
koma mota cike da takaici da bacin rai tayaya zai rinka kiransa baya daukar waya bayan a tarihin abotarsu
dik halin da daya ke ciki bayakin daukar wayar daya?haka driver ya juya dashi ya nufi gidansu.....
******
sameer na gefen momynsa yayi shiru tun dawowarsa ya tasa ta a gaba tana lura da yanayinsa "sameer
lafiya naganka haka?ko akwai abinda ke faruwa ne?"girgiza mata kai yayi "babu momy kawai inaso in fada
miki zanyi aure"da sauri momy ta kalli sameer sanan ta rangada wata irin guda tace "Alhamdulillah Allah
ya kawomu ni zainabu aure sameer?"cike da farin ciki take tambayarsa sai yace "aure kuma?ninace miki
zanyi aure?"yace a fili cikin zucuyarsa yace nayi magana a raina ta fito fili menene yasameni ne?tambayar
da yakeyiwa kansa kenan kardai shaukin khairat ke neman haukatasa, ya mike yabar momy a wajen baki
yaki rufuwa cikin farin ciki ta soma danna numbobin daddyn sameer dan ta labarta masa wanan labari mai
dadi....
*****
"bawan Allah me kakeyi a nan ne haka bakasam dare yayi ba inji dai ba wani abun dina tayi muku
ba?"mahaifin dina ke magana rike da buhunsa ya dawo daga bakin hanya,mansoor ya fito daga motar
idonsa jajir warin tabar wiwi ta bugi hancinsa yadan baza hancin ya shaka tabbas wari ne wanan kamar na
abun maye ya kara lekasa cikin wani irin yanayi baba ke kallonsa saidai wanan karon daura fuskarsa yayi
tamau jin warin da mansoor yakeyi "ka rasa ina zakayi mana shaye shaye sai kofar gida?me kake nema a
kofar gidana?"gaban mansoor ya fadi ya kalli mahaifin dina yaga yadda yake jifansa da kallo cike da kyama
da fushi yace "wajen Dina nazo?"

"wajen dina?"baba ya maimaita cikin fushi yana kallon mansoor wanda shima shi yake kallo cike da
fargabar irin kallon da yakeyi masa ya kasa kara furta kalma daya kawai yasa kai ya nufi cikin gida yana
kiran sunan DINA......
*SLIMZY*
✍🏻
[09/11, 09:04] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎

*RUD'ANI*💥

*DUHU....*🌑

*4*
Dina tasa hannunta a cikin kwanon tuwo miyar kuka da yaji man shanu kenan ta gutsuro tace "innah
tuwon nan dadi zaiyi kodan yunwar da nakeji yasa nakosa na kaisa bakina"innah tayi yar dariya "tou wai
dik me kikeyi yau Dina bakici komiba?"ta kai lomar bakinta bata tauna ba baba tagani a gabanta kamar an
jehosa ya zabga mata wani gigitaccen mari wanda ta kidime ta furzo tuwon daga bakinta lomar na kokarin
shaketa ta dafe kumatunta "ke waye yace ki dauko dan shaye shaye ki kawoshi kofar gidan nan?a wanan
daren? Kenan ya tabbata maganganun da mutane keyi mun ana ganinki da yan birni masu shaye shaye
ko"girgiza kai tayi tana hawaye tace "bansanshiba baba nifa Sameer kadai nasani ni bana"ya kara wanketa
da mari ta gefen fuskarta sanan yasa hannu ya fuzgeta yayi waje da ita,cikin alhini da damuwa innah tace
"Dina bakyajin maganar mahaifinki nima dana dawo kasuwa saida nace waye ya ajiye mota a kofar gidan
nan amma kikace baki saniba gashi ai kinjawa kanki maruka har biyu wanda tunda na haifeki babanki be
tabayi mikisu ba"innah ta koma ta zauna ta rafka tagumi,

mansoor na tsaye yana jiyo ihu dina da hargowar baba jikinsa ya soma rawa ya fito da dina dafe da
fuskarta tana kuka yace "gashinan kinganshi kikace baki sanshiba?"ta daga manyan idanuwanta da hawaye
ke gudu a fuskarta kamar an bude famfo fuskarta tayi jajir ta kalli mansoor wanda tuni jikinsa ke tsuma
ganin hawaye a idon ta ga yadda fuskarta tayi pink nan da nan ba karamin daga masa hankali yayi ba ya
kalli mahaifinta ransa a bace idonsa jajir kansa na kara daukar carji, saidai ya danne hakan a zucuyarsa
jikinsa na rawa yace "baba meyasa ka daketa?Dina batasanniba bata taba ganina ba yau tafara ganina,
nazo wajenta batada laifi, da tsayuwata a kofar gidanku,ko kasan cewar da wanine ya daketa ba kaiba da
sai nasa an dauresa?saidai kash kaidin mahaifi ne a gareta dani kaina kanada ikon hukuntamu nida ita
amma da badan haka ba....."galala Baba yayi yana kallon mansoor take ya tuno da fuskarsa yana nunasa da
yatsa yace "ashe kaine?kaine kazo har kofar gidana kakemun shaye shaye?ashe bakada kunya bakada
tarbiyya?idan niba mahaifinta bane kasheni zakayi ko zakasa akaini kiri kiri ne a jefar da dan makulli. cikin
kogin maliya?"cikin fushi Baba ke magagar dina kuwa kallon mansoor takeyi cike da mamaki da karfin hali
irin nasa, yadda shima kallon nata yakeyi ta cikin hasken farin wata,hade hannuwansa biyu yayi alamar
bada hakuri yace "am sorry....nine naja miki ko?bazan sake zuwa ba dikda manufata akanki ta alheri
ce"yace yana kallonta da idanuwansa da suka kankance da tsananin bacin rai ga kansa dake sara masa

"bakada wata manufar data wuce ka lalatamun yarinya ka lalata mun rayuwarta Karna kara ganinka tare da
ita dan bazan bawa mashayi yata ba kuma bazan zuba ido inaji ina gani ka lalatamun tarbiyyar dana bata
ba gashi kasa na sauke hannuwana akanta bayan tunda na haifeta ban taba dukanta ba"cikin kuka Dina
tace "nasanshi baba"da sauri Mansoor ya shiga girgiza Mata kai cikin tausayawa bayaso a taba lafiyarta ta
cigaba da magana "nasanshi amma abinda kake tunani bashi bane shidin mutumin kirki ne kuma bashida
wata matsalar daya wuce shaye shaye"

"shaye shaye babbar matsala ce Dina in kina ganinta karama banaso mu cigaba da musayar miyau dake a
kofar gida waiga kiga yadda kika taramun mutane".....yana gama magana ya fuzgi dina yayi hanyar shiga
gida da ita mansoor yace "idan shaye shaye matsalata nadaina daga yau"da sauri Dina ta waigo tana
jifansa da wani irin kallo mai cike da tausayawa hannunta ta daga ta baya alamun bye bye...jijiyoyin kansa
dik suka firfito "Dina......"ya furta ya koma ya fuzgi motarsa kamar zai tashi sama aguje yara ke gudu
sunayin baya ganin kurar data tashi ta baibaye mutanen wajen,

"malam kayi saurin yanke hukunci akan yaron nan bayan shine wanda ya taimakeka da kudin nan"shiru
baban dina yayi cike da bacin rai yake musamman yadda jamaa sukayi cincirindo akofat gidansa yasan
yanzun zaa fara maganar nan zata dauka a cikin gari....
*******
"wai nikam ina mansoor ko gidansu sameer ya kwana jiya banga dawowarsa gidan nan ba"cewar momy
data samu rufaida da nabeeha a parlor da zaheed sanye da uniform din makaranta yana breakfast,

"momy be kwana ba kila yana can tare da village girl"da sauri rufaida da momy sukace "village
girl"nabeeha idonta jajir ta jinjina musu kai "tabbas da bakinsa ya fada"take fuskar momy ta sauya nan da
nan annuri. fuskarta ya sauya daga faraar da takeyi zuwa akasin haka a fusace tace "village girl?mansoor
din?wacece wanan?yar talakawa?"ta jero wadanan tambayoyi. zaheed ya ture cup din tea yace "momy
naga kamar ya Mansoor yana dakinsa ya dawo"

"ya dawo?"rufaida da momy suka hada baki,bata jira me zasuce ba ta shiga bin benen gidan cikin sauri
fuskarta a daure take taka benen gidan zucuyarta cunkushe da bakin cikin jin abinda Mansoor ke shirinyi,
hayewa sama tayi,

tura kofar dakinsa tayi kamshin turarensa ne ya bugi hancinta wanda koda yaushe haka dakinsa yake
sanyin AC ya kama tiles din dakin duhu ne bata ganin komi saidai tana jiyo sautin kida dake tashi a
Bluetooth din dayasa a kunnensa,yana kwance a makeken gadonsa ya lumshe ido bakinsa a bushe yana
sauke numfashi sama sama ta kunna wutar dakin "mansorr....dama a cikin gidan nan ka kwana"hasken
daya wadatu a dakin yasashi dan bude idonsa kadan dishi dishi yake ganin momy a tsaye a kansa
fuskarsata babu walwala,be damu da hakan ba,yasa hannu ya kare idonsa "momy...banason haske
kinsani"ya runtse idonsa,kwafa tayi tace "tashi kafadamun meke damunka?inada tarin tambayoyi da nazo
dasu"zucuyarsa zafi takeyi masa bayason magana gashi momy tazo masa da wasu maganganu da alama
cikin fushi take,neman waje tayi ta zauna a kujerar dake kusa da gadon"tashi"tace tana basa
umarni,dakyar ya motsa ya mike ya zauna ya jingina da jikin gadom ya zuba mata manyan idanuwansa da
suke jajir tun daren jiya"momy meya faru?"ya jefa mata tambaya yana kallonta da manyan idanuwansa "ba
abinda be faru ba jiya ina kaje?"shiru yayi besan me zaice mata ba dan be fada musu zashi kauye ba,tayi
shiru tana saurarensa "ina tambayarka inda kaje ka fadamun sanan waye village girl?da kafadawa nabeeha
jiya?"damm gabansa ya yanke ya fadi yana cigaba da kallon momy can kasan zuciyarsa kuwa nan da nan ta
soma tafarfasa wato munafukar yarinyar nan har ta kai yar maganar da yayi subutar. baki wajen
momy?"sameer ne yayi sallama cikin dakin,hamdala Mansoor yayi cikin zucuyarsa,momy na ganin sameer
ta fadada murmushinta "ah ah barka da zuwa da guda kaine da sassafe?kaga ragon nan kai gashi kayi
Shirin zuwa aiki ma"kallonsa sameer yayi yasa mansoor sakin murmushi yasan sameer na fushi dashi sarai
dan yasan irin kallon da yakeyi masa kenan,momy mikewa tayi ta harari mansoor "zamu hadu dakai
zakaimun bayani ba kyaleka nayi ba"tana maganar tana zura takalmi tasa hannu ta kashe switch din AC
tace "gaka da ciwon sanyi amma kullum kana cikinsa,matarka ta shiga uku"

tana fita sameer ya zauna inda momy ta tashi"oya yimun bayanin dalilin dayasa kaki daukar wayata jiyan
sanan kana ina a wanan lokacin?"cikin wani irin yanayi dauke da damuwa Mansoor yace "Afwan nasan
nayi maka laifi but am sorry kaji?ina kofar gidansu Dina bacci ne ya daukeni"ya cije lebe da sauri sameer
bakinsa har rawa yakeyi "kofar gidansu dina bacci ya daukeka?me kakeyi haka a wanam lokacin a kofar
gidansu "yana maganar gabansa na faduwa fatansa kar mansoor ya lalata komi, burinsa kawai yaji ansa
daga bakin Mansoor yace"naje ne na kulla abota da ita domin in canjata saidai bansamu karbuwa ba
sakamakon bata muamala da yan shaye shaye"wata sasanyar ajiyar zuciya sameer yayi yace "da sauki komi
zai gyaru" cike da gatse Sameer yace "idan kanason abota da ita saika daina shaye shayen"sameer ya
tsurawa mansoor ido yaji me zaice,
shiru mansoor yayi cikin wani irin yanayi yace "yeah i think so....zan daina shaye shaye"zabura sameer
yayi " you mean dagaske zaka daina shaye shaye saboda DINA...."jinjina masa kai mansoor yayi hade da
murmushi ya gyada mai yace "da wahala amma zan daina a gabanta dik lokacin da zamuje kauye zanyi
avoiding inaso nasaba da ita in jata ajiki inaso na canjata,i feel bad honestly jiya da badan mahaifinta bane
ya mareta da sai na dauresa"cike da mamaki sameer ke kallon mansoor da fuskarsa a daure take kana
hangi damuwa a kwayar idonsa, tausayin abokin nasa ya kamasa ta wani bangare zucuyarsa cike take da
rudani yace "i support you....man ka nemi shakuwarta ka bata kulawa sanan i think ka sa hannu wajen
cikar burinta"mansoor kallon sameer yakeyi wani farin ciki ne ya lullubesa yace "I know you are my
companion always abokina ya rayuwa zata kasance idan bamu tare?kasan kwana nayi da bakin ciki da
tunanin yadda zan bullowa lamarin i just like the girl"murmushi sameer yayi idanuwansa suka danyi ja yace
"really so Dina ta shiga ranka haka?lets me clap for her"tafi sameer yakeyi amma can kasan zucuyarsa cike
take da rudu,ta wani bangaren yana tausayin Mansoor din musamman yadda ya samesa da damuwar da
yaga ya shiga,yaye blancket din daya rufa dashi yayi ya zuro kafafuwansa kasa yasa takalminsa dake gefen
gadon "lets me take my bath.....kasa nasamu karfi amma bari na fito na baka labarin yarinyar nan jiya
harda Allah ya isa tayimun"yana murmushi yake maganar cike da mulki sameer mamakin mansoor yake ya
zare rigar jiminsa ya ja towel dake sagale jikin rag ya daura akan boxers dinsa yace "five minute
friend"jinjina masa kai yayi ya shiga toilet sameer remote ya dauka ya kunna TV ya dawo ya zauna,ya ya
zaro wayarsa daga aljihun gaban rigarsa zai danna, notification ne ya shigo wayar Mansoor dake kan side
drawer da sauri idonsa ya sauka akan hoton Dina Da kayan fulani nan da nan shi kansa yaji tsigar jikinsa na
tashi ya shafa hoton yana murmushi, "DINA ta man .."yace yana wani killer smile,
nabeeha ta shigo da tray kato dakin da warmers akai tasha riga da skirt na atamfa kanta babu dankwali
kitson kanta kalaba kanana sun zuba a bayanta daidai mansoor ya fito daga toilet daure da towel ya daka
mata tsawa "ke waye ya baki izinin shigomin daki?"jikinta ne ya soma rawa da sauri sameer yace "nine ta
nemi izini na bata ta shigo"kwafa yayi yana goge jikinsa da karamin towel yace "and lets me still remind
you that village girl still tafiki komi"nan da nan idonta suka ciko da hawaye sameer beji dadin abinda
mansoor yayi ba "sorry nabeeha jeki abunki"tana fita sameer ya rufe mansoor da fada Wanda ko kala bece
masa ba yana zaune gefen dressing mirror yana murza mai a jikinsa da turaruka kala kala minti minti yana
smiling,

"kasan Dina harda bye bye tayimun kamar fa zatayi abota dani,"sameer ya dafe kai "ya salam ka dameni da
zancen dina dinan ni anya bazan maidaka kauye ba?"

mansorr bece komiba ya koma gaban wardrobe ya ciro wasu kananan kaya irin na jikin sameer yasa "kasan
me muje restaurant ne kawai ni bazanci wanan abincun da kazamar nan ta kawo ba"tabe baki sameer yayi
yace "babu dai kyau wulakanci,in haka ne muje mana in dauki tawa flower muje kanacin abinci inaba tawa
flower ruwa nasan khairat nacan na jirana tun jiya take kirana bana dauka bayan kaine sila"murnushi
mansoor yayi yace "inaji kamar yarinyar nan yaudararta kake fa dikda kana proving son da kake
mata"Mansoor yayi maganar yana harar Sameer da ke murmushi yace "inaaa inason khairatu sosai bazaka
ganeba"tare suka jero suka fito babu kowa a parlorn suka fice daga gidan sameer na kara karfafawa
Mansoor gwiwa akan Dina....
*******
tafe take tare da kawarta fuskar nan babu wata walwala tana sanye da wasu riga da zani jar atamfa ce da
bakin hijab a jikinta sun fita hayyacinsu sunyi fari tace "kinsan me naji malam yau yace yanada kyau ka
canja mutum idan yana wata dabia ko?"kawar ta jinjina mata kai tace "kwarai kuwa Dina kinsan me jiya na
shiga gidansu rahane naji ana cewa baba ya kamaki da dan shaye shaye a kofar gida ya lakada Miki duka
wai wadanan yan birnin"nan da nan idonta ya ciko da kwalla "ya fa daina,bafa wani abu yake sha ba dama
kuma aiba iskanci aka kamamu munayi ba"tace cike da tsiwa "shine ai tace wai nan lawalli yace yana sonki
kikaki amma da yake yan birni sunzo kin makale musu ba aurenki wanan zaiyi ba kawai lalataki zaiyi"

"tou wai waye yace muku soyayya muke nidashi?"daidai nan suka tsaya a kofar gidansu dina "niba soyayya
muke ba abokina ne kuma ni yanzun ma so nakeyi yazo garim nan in bashi hakuri akan abinda baba yayi
masa"kawarta ta tabe baki "baki daku ba kenan"ta harareta "sau nakeyi in canjashi kodan in shiga aljannah
nasan samir zai bani goyon baya dan shine mutumin kirki"
"ko shine masoyin?"tabi kawarta da gudu ta duma Mata dundu aguje tayo gida ta bankado kofar gidan
tana shiga ta sauya fuskarta ta gaida innah ta wuce daki,

"Dina ga abincinki"tace mata daga cikin daki tace "nakoshi innah sai anjima zandan kwanta inyi bacci
ne"innah ta girgiza kai ta fahimci dina fushi takeyi dasu kuma in ba kuskure tayi ba tun safe bataci komiba
daka ganta kasan tana cikin damuwa,

alkuraninta ta ajiye ta cire hijab dinta ta zauna akan katifarta ta hada kai da gwiwa "tayaya zan hadu dashi
in canjashi na shiga aljannah,gashi yacemun zai daina saboda ni,idan har dagaske yakeyi zai zama abokina
idan kuma nagano karya yamun shikenan zan yanke alak'a dashi tanata surutai ita kadai a daki a haka bacci
ya dauketa,

*******
bayan magriba sameer da khairat suka kawo Mansoor gida kallo daya zakayi musu kasan suna cikin
nishadi da walwala Sameer na makale da hannun khairat a gaban mota yana mata rad'a a kunne,ya tada
mota, har sameer ya tada motar mansoor ya tsayar dashi"dazun a plazar da muka tsaya ka siyi carja na siyi
karamar waya mikomin"Sameer ya sauke glass yana kallon mansoor"me zakayi da karamar waya?kai kana
rike karamar waya ne?" khairat tayi murmushi tace"kai kuma meye naka?"ya tsura masa ido cike da
tuhuma,murmushi Mansoor yayi bece komiba ya kara tambayarsa "tell me me zakayi da karamar waya?"

"bazan iya jure rashin magana da ita ba shiyasa,zan kai mata wanan wayar in rinka jin dik wani motsinta
kasan mahaukaciya ce"wata dariya khairat tayi tace "saida nayi tunanin masoyiyarsa ya saiwa ta kauye to
nidai gaskiya banason abota da yar kauye kar a soma soyayya azo a kawota birni tana badamu"cikin wasa
take magana, "you mean Dina"mansoor ya gyada masa kai,"ko nayi laifi?"girgiza kai kawai sameer yayi ya
ja motarsa mansoor na daga masa hannu,

mansorr na tsaye a harabar gidansu yana jujjuya wayar hannunsa yace "da badan bagidajiya bace da
babbar waya zam siya Mata mu rinka video call tana zuba wanan haukar nata ina mata correction wanan
din ma i think sai munyi special lecture zata gane dauka da kira,village girl"yace Yana murmushi yana tafiya
cike da takama kamar yadda ya saba,
yana shiga parlorn momy ya ganta zaune tanacin fruit "momy barka da yamma"

"barka dai man...ka shiga daddynka nason ganinka"gabansa ne yadan fadi"lafiya?"ya tambayi momy,ta
girgiza kai tana murmushi "ka shiga zakaji koma menene"tace ta maida hankalinta kan tv tana cin apple din
dake hannunta tsaye yayi ya kasa motsi haka kawai ya tsinci kansa da faduwar gaba.....

*SLIMZY*
✍🏻
[09/11, 15:00] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎

*RUD'ANI*💥

*DUHU....*🌑
*5*
"yanzun ke innahr Dina Ashe abinda ke faruwa Kenan baki fada mana ba?dama ance akwai wasu baki yan
birni da sukazo daga cikin birni kamar turawa tare ake ganinsu da Dina koda yaushe na karyata sai gashi
labari ya isar mun cewar ai salisu ya gansa a kofar gidan nan yana shaye shaye kuma yace wajen Dina
yazo"shiru innah tayi tana sauraren mahaifiyarta dake zaune gefenta tasi'u ne dan gidan goggo lubabatu
kanwar innahr dina,"ina magana kinyi shiru bakice komiba bayan magana taje har wajen mai gari to
labarinku akeyi kaf a garin nan yanzun akan Wandan Yan birnin sun gama lalata Dina"da sauri innah ta kalli
mahaifiyarta dake magana cike da masifa tace "baba kulu anya maganar da ake fada gaskiya ne Dina
bazata tabayin lalata da wani ba a cikin garin nan balle wajen garin nan kuma wanan yaron da ake
magana"Dina ce ta fito daga daki ta tsaya tsaye tana binsu da wani irin kallo musamman da taga tasiu tare
da kakarta tasan daga wajensu munafuncun ya bullo tsaki taja ta tsirtar da miyau ganin wani kallo da tasiu
keyi mata da jajayen idanuwansa ya washe baki hakoransa jajir kamar ruwan goro "wanan maganar karya
ce makirci aka shirya dan aga bayanmu an bata mana suna babu wani Dan shaye shaye kuma ai gara
Mansoor shaye shaye yakeyi ba mazinaci bane"tayi maganar tana watsawa tasiu wata irin harara,

"ke waye mazinacin?dawa kike?"tasiu yayi maganar yana mazurai ta rike kwankwasonta tace "Kai idan
kana ganin tsoro nakeji na fada maka mazinaci ne kai banajin tsoronka ban kama ka da asabe a lungun
gidan mai gari ba ta dauko talla ka sauke kana tattaba ta?idan karya nake Allah ya tsinen"salati baba
kuluwa ta rafka "au kema neman abinda zaki kare kanki kikeyi?zaki kulla masa sharri tou kisani idan ma
soyayya kukeyi da wanan balaraben baxaki taba aurensa ba dan bamusan kosu waye ba sun gina gidan
gona a kauye suna zuwa bamu san irin kudinsu kona shan jini bane yauwa ko kinki ko kinso baki isa ki bata
mana suna ba"innahr dina ranta a bace ta share hawayenta zayayi Magana dina ta amshe "oho dai niba
soyayya mukeyi ba yauwa abokantaka yakeso muyi kuma yace indai na Amince zai daina shaye shaye kuma
malamarmu tace yanada kyau ka zama silar shiriyar wani dan haka zan gwada tawa saar indai yazo garin
nan "wani gigitaccen mari Dina taji ta bayanta da sauri ta juya taga babane ya shigo da buhunsa a hannu
yace "ke dina da kunnena nakejin zaki abokantaka da dan shaye shaye akwai abokantaka tsakanin namiji
da mace ne?inba lalatattun yan birni ba?ke dina anya kudin da nace zan samu in kaiki makaranta ma zai
yuwu ba aure zanyi miki ba?"ta dafe gefen kumatunta ranta a bace zucuyarta nayi mata zafi da zarar aka
Kira mansoor da dan shaye shaye ita kadai take kiransa da hakan itama tanayi ne badan zucuyarta naso ba
sai Dan tanajin matukar zafi idan ta gansa Yana bushe bushen nan kasancewarsa kyakkyawa ajin farko uwa
uba ga turanci alamu sun nuna yanada ilimi sosai,

baba kulu ta mike ta kakkabe zaninta tana nuna dina "kai tasiu tashi mutafi ka gayawa luba idan kaje ta
fara shiri ko taki ko taso sai ta aureka inaga salisu abinda zamuyi kawai shine muyi auren yaran nan shine
zai raba Dina da wadanan yan birnin kuma tasiu kasa ido sosai akan dina dik inda kaga tayi ka bibiyeta kaga
da su waye take tare ka fadawa mahaifinta gashi"ta nuna baban dina dake tsaye ransa a bace , Baba kulu
surukarsa ce an basa auren mahaifiyar dina ne kasantuwar ansan wasu kakanninsa amma shi kansa
bashida kowa a garin bayaso Dina ta auri tasiu da wani zai fito daban bashi dinba a gaggauce zai aura masa
ita,innahr dina kuwa zaune tayi kamar an dasata dole tasa salisu mahaifin dina ya aurar da dina ga tasiu ko
bayaso kodan kada ta raba mata zumunci,
bayan fitarsu zama yayi yaba fuskantarta zaiyi magana ya dago ido ya kalli Dina "ke tashi a nan kafin in
kakkaryaki dik wanan masifar kece kika janyota ai gashi nan yanzun abinda baba kulu tace bani waje"ta
tura baki gaba tana kunkunai ta shige daki tana bubbuga kafa cike da takaici tace "ko yau yazo garin nan
zan kulasa saboda ina kwadayin samun lada ko zaa kasheni ai shima da ne kamar kowa"ta zauna a kasa ta
rafka tagumi,

"kinaji innahr Dina kiyi hakuri kidaina wanan kukan,sam banason tasiu ya auri dina saboda kinga basu dace
ba ki duba kiga irin dabiun tasiu kwanaki ina wajen mai gari aka kawosa akan ya saci kaji uku an gansa dasu
zai saidawa wasu baxanso yata ta hada iri da barawo ba"wani kallo innah tayi masa "sai da dan shaye
shaye ko?"cije lebe yayi yace "da wani zai fito daban basu ba da zan bashi da rayuwar dina ta lalace ko
fahimceni"innah ta mike ta kakkabe zaninta tace "ni baxakajamun masifar baba kulu a garim nan ba koba
komi mahaifiyata ce"tana gama maganar tayi daki,ransa nayi masa zafi da kuna ba wanda ya jawo fitinar
nan sai Dina data shigewa wadanan yan birnin dole ma zan rabata dasu ya mike yabi innahr dina daki,...
********
"ya naganka dik kana wani mazurai mansoor daga ina kake ko kauyen ka tafi?"gabansa ya fadi ya girgiza
kai "tunda son zaman kauyen kakeyi nasamo maka mafita"a kufule daddy yayi maganar, Mansoor yadan
ware ido cike da faduwar gaba yana jiran me daddy keson fada masa "kai nasamu wani distributor daga
U.K zaa turo mana dabbobi daga can irin nasu da naso na turaka can din ne"gaban mansoor ya yanke ya
fadi wasu zufa ke tsattsafowa daga goshinsa ya kallli daddy yana jiran me zaice daddy ya tsare sa da ido
yana karantar yanayinsa,cikim zucuyar mansoor kuwa fadi yakeyi "no no am not going any where daddy i
don't want to go i want to change that Village girl no matter what idan natafi ya zanyi?waye zai rinka
baxamun wanan haukar tata?"daddy yace "kai tunanin me kakeyi haka?"da sauri yadan lumshe ido hade
da murmushi "ba tunani nakeyi ba ina jiran naji me zakace ne"daddy ya girgiza kai yace "you are hiding
something to me mansoor"shima girgiza masa kai kawai yayi ba yanzun yakeso asan yanada wata
dangantaka da Dina ba,"tou dama so nakeyi kuje garin can kaida sameer kusamu sati daya idan sun iso
zuwa jibi ni kuma zansa a motoci a kawo muku can da maaikatan can asa komi yadda ya kamata a cigaba
da kula dasu"cakkk Mansoor yayi yana kallon daddynsa ji yakeyi kamar a mafarki daddy ke maganar yace
"you mean daddy zamuje kauye muyi sati daya?"daddy ya jinjina masa kai "yes ko kanada wani abinda
kakeyi a nan ne daya wuce yawon club da shaye shaye mansoor? gara katafi kauyen ka zauna a can da
maganar daka daukomin ranan fisabilillahi yar aminina ka mara?haba mansoor ka kira sameer ko kuma ni
zan kira daddynsa akai dan nasan shima bazai zauna a nan baka nan ba kaima bazaka zauna kai kadai Acan
batare dashi ba"wani farin ciki ne ya lullube Mansoor yayi wani murmushi da ya karawa fuskarsa kyau yace
"Toh shikenan daddy zamuyi shiri"yana gama maganar ya mike cikin farin ciki zai fita daddy ya tsayar dashi
look,cakk Mansoor ya tsaya hade da juyowa "momynka tayimun bayanin tsakaninka da nabeeha idan ka
dawo zaayi zancen aurenku ko hakan zai zama silar dena Shaye shayenka,wani faduwar gaba yaji cakk ya
tsaya ya kasa motsi jikinsa ya soma rawa,dakyar ya seta natsuwarsa ransa a bace yake ya kasa cewa daddy
komi wato nabeeha ce musu tayi shi zata aura?bazaice komiba yanzun dan kar ya bata shirinsa na zuwa
kauye daddy ya fasa amma yasan me zaiyi,fitowa yayi daga sashenn daddy yana fitowa yaji hayaniya cike fa
gidan ransa a dan bace,

momy na zaune a parlor. ya sauko ya hada girar sama data kasa,ganin wacce ke zaune gefen momy ya
soma dariya yace "welcome my favourite",dariya itama tayi masa wata matashiyar macece da momy Zata
dan girmeta saidai daka kalleta kasan yar uwarta ce dan suna tsananin kama "my son kwana biyu ina ka
boye?"da sauri nabeeha ta amshe "baya zama yanzun kauye yake tafiya"tace "really kauye?doing
what?"zura hannunsa yayi aljihunsa ya watsawa nabeeha harara yace da wani irin kallo mai cike da
tsana,tayi saurin kasa da kai yace "and yanzun din ma can zan tafi so sai ki cigaba dasamun ido"momy ta
amshe "ka tattara ka koma can ma koma me kake kullowa watarana zai fashene kuma nagama yanke
hukuncina"tana hararsa take maganar,....ya zauna gefen Aunty zaleeha yace "Anty inataso nazo nasameki
akwai muhiimiyar maganar da nakeso muyi,kinsan ke kadai nake fadawa abuna"yayi maganar fuskarsa a
daure as usual dariya tayi tace "nasani ko nasamu suruka ne?"da sauri ya girgiza kai yaga dukkansu shi
suke kallo ya harari rufaida "munafuka lafiya?"gimtse dariyarta tayi ta mike "babu ruwanmu kaida Antu
zallyn ka ne mu yan kallo ne ya nabeeha muje daki kiji wata magana"gaba daya hankalinta yana kansa ta
tsura masa ido tanajin wani irin kishi akansa tana tsananin son ya mansoor gashi har yau hankalinsa baya
kanta dikda momy ta fada mata ta fadawa daddy soyayya suke,rufaida ta zungureta "mai kike kallo ne
haka"Anty zali tayi dariya tace "ya man take kalla"shi kuwa cewa yay"ai mayya ce, let's me call Sameer
akwai albishir dim da zanyi masa ma,karku batamun mood, Anty zali now zan kiraki kawai ko kuma gobe
kafim nabar garim nam zan shigo gidan naki"tace "okay sir"tana murmushi shima murmushin yayi mata ya
mike ya shafa kan yaronta Adnan dake zaune gefenta ya ciro wayarsa daga aljihunsa ya fice,

Anty zali ta juya ta kalli momy tayi kasa da murya "wai nikam har yanzun yaron nan be fito da kowa da zai
aura ba?ko sun daidaita da nabeeha ne?"ajiyar zuciya momy ta sauke tace "ina fa ko kallon arziki baya ma
yarinyar nan zaleeha gashi tana matukar kaunarsa kuma kinsan yar hajiya nafisa ce aminiyata dikda na
sanarwa daddynsa soyayya suke kuma so nakeyi ayi aurensa nan kusa dan nasan shirin da mahaifinsa keyi
masa shine besaniba kawai,ni ina zargin akwai abinda yake boyewa amma tabbas idan yazo gidanki zai
sanar miki inaso ki bashi shawara ya taimakeni kar ya watsamun kasa a ido ya nemi yarinyar nan
nabeeha"Anty zalli tayi shiru tana saurare. yar uwarta tace "tou kinsan mansoor din ne juyayyen mutum
ne but i will try kindaiyi saurin yanke hukunci ne,amma wani shiri daddyn keyi masa?"

"ai mutumin kine,zaiji maganarki,shirin sama masa course yakeyiba Cyprus"ta jinjina mata kai tace "
shikenan i will handle him,yanzun dai a zubamun dambun da akace anyi zamu tafi dare nayi cewa nayi
mun kwana biyu bamu leko ku na nabaro su walida a gida su kadai"ta yunkura ta mike momy ta mike tace
"bari nayi magana da masu aiki su kawo miki mota"Anty zalli ta kwashi makullin motarta dake centre table
sukai sallama ta fice....
********
cikin tsananin farin ciki mansoor ke maganar "amma kasan menene?inaga a kwana bakwai din nan da
zamuyi a kauye zan seta mara kunyar nan dan naga alamar batada mafadi"yana maganar yana murmushi
ta gefen fuskarsa yadan kishingida akan sofa yana lumshe ido kammaninta yake gani a kwayar idonsa
kunnensa makale da waya, Sameer ya nisa yaja gauron numfashi yace "amma dai kasan in kace zaka matsa
mata wanan abotar da kake shirinyi da ita bazata dore ba?kasan Dina abinda na fahimta baayi mata dole
basata tayi abinda batayi niyya ba sanan tayaya zaka samu lokacinta bayan ka manta ka fadamun kayiwa
babanta rashin kunya saboda ya mareta?sanan ya ganka kiri kiri kana shaye shaye?"lumshe idonsa yayi ya
mike ya zauna cikin dan damuwa yace "i will handle it,coz bazan iya jure rashin yin magana da ita ba kuma
koda babanta be amince da alakar mu ba tunda ba aurenta zanyi ba nadan lokaci ne i just want to change
her inason na seta ta ne"sameer ya ja numfashi yace can kasan makoshi "baka sonta kake nufi?ko kanaso
kacemun dik damuwar nan ba soyayya bace"

"no no no you are misunderstanding me friend yarinyar nan soki burutsunta kawai nakeso in canja dan na
lura batada hankali"sameer ya nisa yace "banason kana kiranta mahaukaciya kawai inaso kasamu
hankalinta ka gyarata sosai yadda zata koma cikakkiyar mace mai aji"dariya mansoor yayi yace "really i am
just feeling some how yau nine nadamu da damuwar wata?watan ma mace?ina mamakin kaina kaga dare
nayi gobe da sassafe ka shirya mu kama hanya saboda inaso da munje mu nemi yadda zaayi
muganta"sameer ya jinjina kai yana murmushi wanda shi kadai yasan dalilin hakan yace "angama ranka ya
dade yaya man,nima na d'ana"ya masa gwalo ta wayar ya kashe,

mansoor ya rufe idonsa yana murmushi ijust hope i can change you Dina.....kina bani tausayi sanan
wadanan manyan idanuwan ina tsananin kewar ganinsu musamman yadda kike harara....ya diro daga kan
sofa ya fada kan gadonsa ya kifa cikinsa yana sauke mumfashi.....

sameer wadrobe ya bude da safe bayan ya gama shirya kayansa momy ta shigo cikin dakin ta samesa yana
kallon kudaden dake ciki yana dan tunani "yadai dan gidan matawallen naira?harka hada kayan ne?niko
kaida mansoor yadda kuke zumudin zuwa kauyen nan kodai a can zaku nemo mana matan kauye muyi
surukai dasu?dariya yadanyi yana sosa keya yace "momy Kenan matan kauye kuma idan ma matan kauye
ne ai suma mata ne"momy tace "umhmm maganata na kan hanya naga ka bude drawer kudi me zakayi
dasu haka?"

"ehh inaso na dibi kudi naje dasu inaso nabawa mabukata a kauyen nan ciki kuwa harda mahaifin Dina dan
bashi da jari"momy tace "Dina kuma wacece haka me wanan sunan?ko itace surukar tawa"tana murmushi
tana dukan kafadarsa ya girgixa kai yana murmushi "ah ah ita din budurwar...."sai kuma yayi shiru ganin
yana nema yayi baran barama "budurwar waye?zaku fadi gaskiya ko budurwar mansoor ce"..

"da sauri yace "ah ah"tace "kwaji dashi" momynsa tace "yauwa wai nikam khairatu soyayya kukeyi ne?" da
sauri sameer ya dago cikin zucuyarsa yace"no no ba yanzun nakeso kisani ba momy sai mansoor yasamu
matar aure,yace "no just friends" tayi murnushi kawai, mansoor ne ya Shiga Kiran sameer yana kallon
wayar yasan kila yazo ne yau mansoor ne da sammako haka?dik yasan zumudin me yakeyi so yakeyi yaje
su daidaita Da Dina kuma bayajin hakan zai taba yuwuwa saboda mahaifinta,sanan Shinkansa yasan
momynsa bazata amince da yar talaka ba ballantana bakauyiya,"ka dauki wayar mana"momy tayi maganat
yace "share man ne nasan yazo ne"be rufe baki ba Mansoor ya shigo da wayarsa a hannu "ya kana ganin
ina kiranka baka dauka"Sameer na kokarin rufe akwati mansoor yaga kudin daya zuba ciki "me zakayi da
kudi"ya girgiza kai "nothing "yace beson ya fada masa mansoor be nemi sani ba suka fito tare da momy
sukai breakfast suka fito suka Shiga mota suka kama hanya,

a hanyarsu suna tafe sun kusa shiga garin ya kalli mansoor dake tuki sameer ya ce "ina kayan harkarka
ne?"mansoor yayi shiru sarai yasan me yake nufi be tanka masa ba ya sake cewa "ina kayan
harkarka"mansoor ya hararesa "nayi mata alkawarin inhar zatayi abota dani bazanyi shaye shaye ba dan
haka daga nan har mubar garin nan bazan taba Shan komiba dikda nasan da kamar wuya but i will try
narigada nasaba da shaye shaye"daidai nan suka gifta ta gaban mahaifin Dina da ya hada gumi a cikin
lemarsa yana zaune a bakin hanya,

"Baban Dina wadanan basu bane yan birnin nan?"mai kayan miyan dake gefensa ya nuna nasa motarsu
Mansoor data shige zuwa cikin kauyen,baban Dina ya jinjina kai "zai yuwu amma wanan farar motace
wadda nasaba gani baka ce amma dai nasan su ne"

"mutanen Dina sun sauka kenan"shiru mahaifinta yayi zuciyarsa na tukuki tabbas zai dau tsaro da mataki
akan Dina dan besan wanan karon dame suka zo ba,

wani irin burki mansoor yaja wanda yasa sameer buguwa da jikin motar ya koma da baya ya daki jikin
jujerar motar ta tsaya jikinsa ne ya soma rawa dan a tunaninsa mutum suka buge ko accident sukayi,ya
dago kansa gabansa na tsananin faduwa yaga Dina tsaye ta gefen motarsu mansoor ya tsura mata ido ko
kiftawa bayayi itama shi take kallo gani takeyi kamar a mafarki sune?.....

*SLIMZY*
✍🏻
[10/11, 07:58] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

JAMA'A, INA GABATAR MAKU DA ROYAL EXQUISUTE, GIDAN GYARAN AURE, GIDAN AMINCI, GIDAN GIGITA
MA'AURATA, JAMAA INA AMARE? UWAYEN GIDA? ZAWARAWA? DA KUMA MASU JEGO, INA MATA?
MATAN DA SU KA AMSA SUNAN SU MATA? MATAN DA SUKE SON ZAMA DARAM DAM A ZUKATAN
MAZAJEN SU? MATA ƳAN ƘWALISA? TO WALLAHI ROYAL EXQUISUTE NA KU NE, SUKE DA INGANTATTUN
KAYAN MATA NA GYARA BA WAI TAWULWULBA, BA WAI SHA KA TAFI BA, KAYAN MATA DAKE ƘARA DARAJA
DA ƘIMA WAJEN OGA, GA SAUƘI GA ARHA, GA KUMA AIKI..ROYAL EXQUISUTE ZATA GYARE KU
KI TUNTUBI WANNAN NUMBER 08030644073
Location kano,nationwide delivery

*6*

juyawa tayi da sauri zata bar wajen,cikin zafin nama mansoor ya bude murfin motar yasha gabanta yana
jifanta da wani irin kallo wanda yasa ita kanta kasa kallom kwayar idonsa wani irin kwarjini yayi mata
gashin kansa yasha gyara sai kyalli yakeyi yace "ina zakije batare da kin gaishemu ba ko baki ganmu
bane?"gabanta ne ya yanke ya fadi ta juya tana waige waige kamar me neman wani abu shima juyawa yayi
idonsa ya sauka akan Sameer daya tsura musu ido daga cikin mota,wani murmushi yayiwa sameer ya juyo
yasa hannu sa a aljihunsa "uhmm kiyi magana kin tsuramun wadanan manyan idanuwan naki masu kama
da"da sauri ta murguda baki tace "oho dai sunfi naka kyau ni matsamun na wuce?"tana fadin haka suka
hada ido da Sameer ta washe baki tana waving dinsa cike da farin ciki,lumshe ido sameer yayi yana kallon
yadda ta cika da farin ciki da ganinsa ya maida kansa yana dariya,

"idan baki gaisheniba bazan matsa ba,Dina bazaki canja ba ko?yanzun daga shigowarmu garin nan ke
nafara gani ko kinsam saboda ke nazo?"ta ware ido tana murmushi "tou ba kai bane ka somamun magana
cikin isa yadda kasaba tou ai nima inason ganinka domin malamarmu tace"da sauri ta kwabi kanta tayi
shiru "yace mene me malamar tace?"daga idonta tayi sukai ido hudu da mahaifinta wanda yasa ta kwasa a
guje kamar wadda ta hango mayunwacin zaki,da sauri mansoor ya juya yaga mahaifin Dina jikinsa yayi
sanyi ganin irin kallon da yake jifansa dashi,ransa ne yadan baci,ga kallom kyama da yaga mahaifinta na
binsa dashi,ya cije lebensa "Barka"yace yadan rusuna ko kallonsa beyi ba har zaiyi magana ya wuce dan
babu amfani yayi magana,ganin haka yasa sameer fitowa daga motar cikin sauri ya karasa ya tari mahaifin
Dina cike da girmamawa ya tsugunna "barka da warhaka baba"da sauri ya dubi samerr yadanyi murmushi
ganinsa cikin kamala yace "barka dai dan saurayi kun shigo?"ya jinjina masa kai yace "baba naga mansoor
ya gaidaka baka amsa masa ba naga kamar"daga masa hannu yayi "karkacemun komi dan Allah dan
saurayi bana bukata rokonku daya nakeyi shine kunzo ko tou ku kyalemin yata banason in kara ganin
wancen mashayin a kofar gidana idan ba haka ba zan samu mai gari a nemo iyayenku"yana gama magana
yasa kai abunsa,sosai sameer yaji ciwon sunan mashayi da mahaifin Dina ya kira mansoor dashi zuciyarsa
nayi masa kuna ya juyo a sanyaye ya bude motar ya Shiga yace "muje"mansoor ya lura da yanayin sameer
tsaf amma dayake miskili ne bayason magana ya share ransa a bace yake wanan mutumin da badan shine
ya haifi Dina ba da wallahi sai yaga wanda ya tsaya masa dubi yadda ya razanata ta ruga aguje yanzun inda
garin gudun nan ta fadi wani abu ya sameta fa?cije lebensa yayi "idan shi ya haifeta ai bashi ya halicceta
ba"yace a fili da sauri sameer ya kallesa cike da mamaki da karfin hali irin nasa yacev"waye kakewa wanan
maganar?"

"Baban Dina"yace a takaice daidai nan suka iso kofar gidan gonarsu wani mahaukacin horn mansoor ke
bugawa da sauri mai tsaron wajen ya fito ganin su mansoor ya washe baki yace"barka da zuwa ranka ya
dade"yana daga hannu ya wangale gate din suka shige cikin farin ciki ya karasa ya tsugunna har kasa yana
gaishesu dakyar mansoor ya amsa ransa a bace yake ya tsaya daga gefe yana kalloon bishiyoyin dake cikin
gidan,daga bayansa sameer ya dafa kafadarsa "Man....ya daga zuwan mu zaka fara bacin rai while kana
cikin farin ciki da zuwan mu kauyen nan?"

"mutumin nan ya batamun mood akwai abinda Dina zata fadamun ya katse ta"sameer yayi murmushi cikin
zuciyarsa yace man da karfin hali mutum da yarsa?a fili yace "muje ciki mu kintsa muyi wanka mu huta
bayan laasar mu nemeta"sameer yayi maganar cikim sigar lallashi mansoor ya kallesa fuskarsa da damuwa
yace "are you show zamu ganta?wanan mutumin zai bari?"sameer ya jinjina masa kai....
******
cikin sauri Dina ta danna kofar dakinta tasa sakata ta ciki innahta na tsaye jikin kofar tana jiyo yadda take
sauke numfashi "Dina lafiya?kinyo tsokanar taki ko?daga ina kike aguje kamar wadda aka biyo?kinyi shiru
dubi yadda kike sauke numfashi nema kike kitada ciwonki ko?tou idan kin yada ni banida kudi babanki ma
bashida shi"mahaifin Dina ne ya shigo a fusace yana mazurai "ina Dina take?wato bazata tabajin maganata
ba ko?"kallonsa innah keyi cike da fargabar mai Dina kuma tayi?katse mata tunani yayi "ina ta shiga?"da
hannunta nuna masa dakinta a sanyaye tace "tambayar da nakeyi mata kenan yanzun haka naga ta shigo
aguje"sharce gumin dayake fesowa a goshinsa yayi Rana na haska idonsa kasantuwar rana ta kwale azahat
tayi yace "kamar nasani na biyo sahun motarsu bayan wucewarsu ta gabanmu sai gashi na ganta tsaye da
wanan yaron mashayi wai ashe mansoor sunansa sai yau nasani in kinga abokin nasa kamili amma shi a
kwayar idonsa kadai kika kalla kinga tsagera ga wani jida kai da yakeyi to wallahi Dina inaga nakasaki zanyi
idan naganki dasu kamar yadda naganki yau"yana gama maganar ya juya cikin sauri ya fita innahr DINA ta
shiga tafa hannu ta karasa inda take yanka awara tace "nashiga uku nidai Dina bansan yadda zanyi dakeba
inaga tasiu kawai zaasa su turo a aura mikishi babu wani tsaye tsaye dubi yadda kika taso mahaifinki a cikin
rana"daga Daki dina na jiyo dik abinda ke faruwa jin alamar mahaifinta ya fita yasa ta sauke numfashi ta
zube a kasa ta dafe kirjinta da har lokacin yake lugude ta tabbatar yau da babanta ya kamata kashinta ya
bushe gashi bata gama magana dashiba yanzun tayaya zata hadu dashi?"tambayar da tayiwa kanta kenan
ta kalli windown dake jikin dakinta ta saki lallausan murnushi tace "ta nan zanbi inje in nemoka ya
mansoor inaso nasamu ladan sauyaka"tana maganar tana lumshe idanu tace "gashi yau yayi kyau Allah
yasa dagaske dai ya daina shaye shayen"adduar da tayi kenan tana kokarin zura hijab dinta ta daure
takalminta a jikin zaninta ta kama jikin windown carab ta d'ane sama ta dira ta baya ta kalli Nisan katangar
ta sauke ajiyar zuciya "yanzun yaya zaayi idan nadawo nashiga?"gabanta ya fadi tanabin Nisan katangar da
kallo ta tura baki tace "oho sai shi ya rakoni ta lungu ya haurar dani ai dogo ne"da wanan tunanin take tafe
ta jikin lungun tana wakar ta,
********
cikin farin ciki nabeeha ta rungume mahaifiyarta data fito ta gansu tare da momy "ummah yaushe kikazo
shine baki fadamun ba?"momy tayi murmushi tace "ja'ira nasan da zuwanta naki fada miki ai naga fushi
kikeyi saboda mansoor sun tafi kauye"nan d nan yanayin nabeeha ya sauya ummahnta ta lura da hakan
tace"ohh bataso ya tafi ko?ai nasan zamanta gidan nan zaisa su shaku na matsu a had'a zumuncin
nan"nabeeha zatayi magana momy ta katseta bataso ta fadawa mahaifiyarta Mansoor basu daidaita ba
"kedai bari hajiya nafeesa kauye suka tafi take fushi bayan daya dawo maganar aurensu zaayi dan bazai bar
kasar nan ba sai an daura musu aure kila su tafi Cyprus din tare"wani farin ciki ne ya lullube nabeeha suka
hada ido da ummahnta ta kashe mata ido,ummahnta tace "iyyee kice kasar waje zashi"

momy ta dubi nabeeha "saura ki fada masa dan besaniba haukar banza yakeyi in ma wata yasamu a
kauyen saidai suji shiru dan bazai aure yar talaka ba balle ba kauya besan shirin da mahaifinsa keyi masa
ba so muke ayi auren ko zai daina shaye shaye ba karamin jihadi kikayiba na amincewa yarki ta auresa
kuma kinsan yana shaye shaye "hajiya nafeesa cikin zucuyarta tacw hmmm bazaki ganeba inada tawa
manufar wanda nikadai nasani a fili tace "ai d'a na kowa ne balle mansoor ai kamar nina haifesa dama
akan inji inda maganar ta kwana nazo dan mu soma shiri"nabeeha mikewa tayi ta kwasa aguje ta nufi daki
wajen rufaida tana Shiga ta d'aka mata duka tana kwance ta tashi "ke lafiya kika bugamun wanan Dukan
kamar wadda aka daurawa aure da yaya man?"tayi farr da ido tacw "meya rage"rufaida ta gyara zama "ban
ganeba "nan nabeeha ta labarta mata,take taji mood dinta ya sauya take tausayin mansoor ya kamata
tanason yayanta batason asashi a damuwa dikda be sanar mata ba amma tasan soyayya yakeyi a boye
wato yankan baya zaayi masa a aura masa nabeeha?take tace nono dole nasanar masa,ta furta a ranta
yadda zaisan ta inda zai bullowa lamarin dikda tana nunawa nabeeha tana tare da ita,a fili kuwa mikewa
tayi ta soma rawa tana taya nabeeha murna,

*********

mamsoor tafe da wando jeans three quarter blue da farar riga armless mara hannu kunnensa manne da
Bluetooth kamar koda yaushe fuskarsa babu annuri sameer ne yayi murmushi "dik fushin nan da kakeyi na
menene?saboda Dina ta tafi?meke damunka ka Shiga damuwa haka abokina?kofa abun naka yau baka
zuka ba"Mansour ya kallesa sanan ya nuna masa mahaifin dina dayazo wucesu yana watsa musu wata irin
harara ya gifta "Allah kadai yasan meyayi mata ni damuwata ma kar dukanta yayi"sameer ya cije lebensa
yace "nafika damuwa da halin da take ciki mansoor"
"kamar yaya?"Mansoor yayi masa tambayat yana kallon kwayar idonsa,zai bashi amsa yaga Dina ta bayan
wata bishiya tana lekowa sameer sakin baki yayi yana kallonta cike da mamaki ya murza idanuwansa ya
kara kalla yagani ita din ce?mansoor ya juya yana fadin"mai kake kallo na tambayeka baka bani amsa
ba?"idonsa ya sauka akan Dina dake tsaye tana waige waige,mamaki ne ya kashesa yacev"Dina kece?"ta
jinjina masa kai ta yafitosa cikin sauri yabar Sameer tsaye yana kallonsu baki bude,mamaki ne da al'ajabi
ya hanasa magana, kwalawa mansour Kira yayi ya juyo "man bari nabi ta nan baya zan sameku zan kira
wayarka ka fadamun inda kuke"mansoor ya gyada masa kai sameer ya juya yabi ta hanyar da baban Dina
ya wuce zucuyarsa na azalzalarsa,khairat ce ta fad'o masa take ya tuno da abinda ya faru tsakaninsu daren
jiya bayan yabar gidansu mansoor,da sauri ya curo wayarsa yayi dialing numberta yana tafiya a hankali,ta
dauka daga can bangaren tana kwance idonta a lunshe tanajin wani zazzabi da ciwon jiki batasan shi bane
saida taji muryarsa ta daki dodon kunnenta,ta zabura ta zauna tana sanye da pink din rigar bacci"na dauka
bazaka kiraniba tunda hakarka ta cin ma ruwa,zucuyata cike take da tsananin fargaba akan na mallaka
maka jikina a daren jiya sakamakom shaukin soyayya karka gujeni,sai gashi har gari ya waye baka
kiraniba"ta karasa maganar cike da shagwaba wasu hawaye masu dumi na zubowa daga idonta,

"no no khairatu...karkice haka calmdown nayi laifi okay?kidaina kuka amma ai kinsan ko ban kirakiba kina
nan makale a cikin zucuyata?"

"tayaya zan gane hakan?"tace tana sauke ajiyar zucuya , lumshe idonsa yayi ya tsaya daga inda yake yace
"kinsan yadda nake jinki kuwa?da kinsan yadda nake kaunarki bazaki shakku akaina ba khairat babu
mancen da zucuyata ta makance akanta saike tawan,kiyi hakuri yanzun dai kin gasamun kanki?"tayi wani
juyi tanajin zafi a kasanta ta share hawaye ta gyada masa kai "ehh amma ba kamar yadda kai zakayi ba
yanzun kana ina?"

"na raka mansoor kauye yau zamuyi kwana bakwai,amma ki kwantar da hankalinki gobe da yamma zanzo
nasameki"ta sauke ajiyar zucuya "bazan iya jure kwana bakwai batare da kaiba"nan ya cigaba da
lallashinta suna musayar kalaman soyayya,

jikin wani dutse suka samu suka zauna shida ita sun dauki kusan minti goma babu meyiwa wani magana
yaga ta mike tana kakkabe zaninta yacev"lafiya?"tura baki tayi ta hararesa,wani yarrr yaji harar da tayi
masa sosai ta burgesa ya saki wani tsadadden murmushi yace "umhmm complainer mainayi kika mike ina
zakije?"ta kauda kanta gefe zata fara tafiya da sauri ya ruko hannunta,kamat wadda akasawa shocking tayi
saurin janye hannun ta juyo cike da masifa saidai yadda ya zura mata kyawawan idanuwansa yasa ta kasa
magana taji jikinta ya saki yace "what menayi?"...girgiza kai tayi "bazan iya wanan abotar ba kasan riskin da
na dauka nataho wajenka?nasan cewa komi babana zaiyi maka sai kazo kofar gidan mu kuma hakan ba
karamin haddasamun fitina zaiyi ba,hakan yasa na dauki riskin tahowa wajenka koda hakan zai zama
sanadiyyar bacin raina"ya tsurawa pink lips dinta ido sosai take burgesa komi nata musamman manyan
kyawawan idanuwanta "kuma nazo kayi shiru sai kace kurma ba sai intafi ba tunda bakason maganar dani
bakaso mu daidaita bayan da kanka kayi bikon fadan da mukeyi?"ta murguda mai baki, shiru yayi ya zura
hannunsa a aljihunsa ya kasa magana besan ta ina zai fara ba shi.mutim ne bame yawan son magana ba ta
kara kuluwa ganin yadda ta tura baki yasa yace "tsaya Dina...ni mutim ne mara son yawan magana a hakan
ma kece silar da nake iya jefa words fiye da uku cikin magana,idan kika tafi biyoki zamyi dan babu abinda
nafi bukata fiyeda cikar burina"

"menene burinka akaina?zaka cutar dani ko? zakaimum ramuwar gayya ne?"tayi maganar a sanyaye,yayi
murmushi "no i want to change you Dina,inaso na canjaki saboda inaso nasamu wani kusanci dake wanda
narasa dalilin dayasa zucuyata ke matukar son kasancewa tare dake,ni mutim ne da banason damuwa
nafison kadaici akan komi amma sanadinki da zuwa kauyen nan ya sauyani"

"kana nufin zaka iya sauya komi ciki harda shaye shaye?"ya zuba mata idanuwa yana kallon yadda itama
take kallonsa kokari takeyi ta gano cewar karya yakeyi ko gaskiya ne,shima ita yake kallo Dina baxan iya
sauyawa daga shan abubuwa ba saidai zan daina dik lokacin da muke tare dake bazan taba bari kigane
hakan ba"kayi shiru"tace tana cigaba da kallonsa "tabbas zan daina ko ince na daina shaye shaye"farin ciki
ne ya lullubeta ta jinjina kai "nima dik abinda kakeso na daina zan daina"yayi murmushi yace "good"ya
nuna mata wuri yace "to mu zauna"ba musu ta zauna,shima zama yayi yasa hannu a aljihunsa ya ciro waya
karama nokia mai shegen kyau ya mika mata ta tsura mssa ido cike da tsoro "karba nace"yace fuskarsa a
daure,babu alamar wasa yasa hannunta na rawa ta karba tace "me zanyi dashi ya man....."yadda ta kira
sunansa ne ya daki dodon kunnensa yace "maimaita me kikace?"ta girgiza kai cikim zucuyatta tace meyasa
zan kirasa da hakan kila ma kwaba nayi ta cigaba da kallomsa da narkakkun idonta,yace "Dina bazan iya
jure rashim jinki ba shiyasa nazo miki da wanan itace zamu rinka magana ta ita wayar salula ce"dafe kirji
tayi cike da furgici "rufamun asiri indai ba so kakeyi baba ya yankani ba"mansoor ya nisa "boyewa zakiyi
bazatayi kara ba bazai taba sanin kinada ita ba kinji?dam Allah karkicemim bazaki rike ba"ta sauke ajiyar
zucuya bazata iya masa musu ba kamar yadda beyi mata musun daina shaye shaye ba,ya zauna gefenta ya
karbi wayar cikin minti goma sha biyar ya koya mata komi yadda zata kirasa da yadda zata amsa waya idan
ya kira sanan yasa mata ita a silent ya kira taga haske kawai tayi da dan vibration sanan yace "ki riketa da
kyau karki bari kowa yasani kinji?"ta jinjina masa kai tace "babu wanda zai sani ina abokina?"ya waiga bega
sameer ba dik a tunaninsa yana kusa dasu, yace "zaizo yanzun ki bani labarin kauyen nan"tayi wata dariya
sanan ta gyara zama,

sameer na tsugune gaban mahaifin Dina inda yake facin taya"yaro wanan kudin kabani su ne a matsayim
cin hanci nabarku da yata ku lalatamun ita?na barwa dan shaye shaye ita ko?"shiru sameer yayi yace "baba
wallahi zakka ce na fitar ba kai kadai na kawowa ba duka mutanen kauyen nam dik wanda yakeda rabo zan
basa baba,Dan Allah ka karba yadda kake tunanin mansoor niba haka nakeba banashan komi baba ance
baa maida hannun kyauta baya baba ka karba saboda Allah da annabi"shiru yayi yana kallom yadda
sameer keda natsuwa da kamala ya kalli goshinsa yaga ladanim sallah ya fito masa yadda yake lallashinsa
da girmamasa yasa jikinsa yayi sanyi dik irin bakaken maganganun daya fada masa,ya kalli bandir din yan
dubu dubu daya bashi yaji tsoro yace "anya yaro dik wanan kudin ba sayeni kayi ba?"murmushi Sameer
yayi cikin zuciyarsa yace da lallashi ake fito da kura daga rami a fili yace "nina baka baba ka karba bakomi
bane wanam karkasa komi cikim zuciyarka sanan maganar Dina badan muzo wajenta ko muyi yawo da ita
nabaka ba ko kadan "ajiyar zucuya ya sauke ya karba yayi masa godiya ya juya ya bawa Mai kayan miya
dubu hamsin Sukayita sa masa albarka sanan yabar wajen baban Dina yabi bayansa da kallo zucuyarsa
cunkushe da tunani barkatai,

tafe yake cikim sauri yaga kiran mansoor "ya man kuma ina?"Mansoor ya kalli wajen yayi shiru yaga Dina
na dariya yace "oho wejen wani dutse kai muke jira zan rakata"ajiyar zuciya sameer ya sauke yace "har kun
gama kenan"mansoor murmushi yayi ya dire wayar yace "yanzun tafiya zakiyi?"ta lumshe ido tace "ehh
tou nima banson tafiya"tayi tagumi tana kallomsa ya daga mata gira daya yace "nayi miki kyau ne?"ta
gyada masa kai tac"ehh amma baka kaini kyau ba"yar dariya yayi tin daga nesa sameer ke kallom yadda
faraa ta mamaye fuskar Mansoor yayi matukar mamakin yadda Dina ta amince da mansoor lokaci daya
suka shirya dik irin yadda mansoor ke kyamarta da maruka datasha ya karaso "wai ina kajene?"mansoor
keyi masa tambayar yana lura da yanayinsa "kayi mun magana naganka wani iri ko bakada lafiya
ne?"girgiza kai yayi yasan tabbas mansoor son Dina yake saidai tausayinsa yakeyi,suka hada ido da Dina
tayi masa murmushi "Abokina kaki ko kallona"murmushi yayi mata yace "ina muka dosa?"Mansoor yace
"cikin gari amma Dina bataso a ganmu"sameer yace "really?"Mansoor ya gyada masa kai yace "we talk
later"sameer ya gane akwai magana a bakin mansoor,
tafe suke suna yar hira mansoor da Dina suna gefe yayinda Sameer ya ciro wayarsa ya kira mahaifinsa
suna video call,

Mansoor wayar rufaida yagani tana kiransa ya kalli Dina yaga shi take kallo,besan me rufaida zatace ba bari
ya bari in sun koma gida ya kirata,

tasiu ne da tawagarsa suka hangi Dina dasu mansoor wani kishi ne ys lullubesa ya kalli abokansa yace
"waccen ba Dina bace?"suka hada baki "itace matarka ba "ya jinjina kai yace "ku muje muci ubanta a
gaban yan birnin sanan in fada musu nine mijin da zan aureta"da wanan tunanin suka nufi su mansoor
wandanda ke tahowa gaban Dina ne ya Shiga faduwa ganinsu tasiu sun dumfarosu jikinta ya soma rawa
tasan halinsu tasiu sarai tsoronsu akeyi a kauyen kar yazo ya kunyatata a gabansu mansoor sanan ya
fadawa baba ya ganta dasu.....

*SLIMZY*
✍🏻
[10/11, 15:17] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦
*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

JAMA'A, INA GABATAR MAKU DA ROYAL EXQUISUTE, GIDAN GYARAN AURE, GIDAN AMINCI, GIDAN GIGITA
MA'AURATA, JAMAA INA AMARE? UWAYEN GIDA? ZAWARAWA? DA KUMA MASU JEGO, INA MATA?
MATAN DA SU KA AMSA SUNAN SU MATA? MATAN DA SUKE SON ZAMA DARAM DAM A ZUKATAN
MAZAJEN SU? MATA ƳAN ƘWALISA? TO WALLAHI ROYAL EXQUISUTE NA KU NE, SUKE DA INGANTATTUN
KAYAN MATA NA GYARA BA WAI TAWULWULBA, BA WAI SHA KA TAFI BA, KAYAN MATA DAKE ƘARA DARAJA
DA ƘIMA WAJEN OGA, GA SAUƘI GA ARHA, GA KUMA AIKI..ROYAL EXQUISUTE ZATA GYARE KU
KI TUNTUBI WANNAN NUMBER 08030644073
Location kano,nationwide delivery

*7*
Kallon Dina mansoor yayi ganin yadda yanayinta ya sauya ta Shiga damuwa lokaci kankani,ya kalli tasi'u
daya harde hannuwansa a kirjinsa yana jifansu da wani irin kallo,sameer cike da mamaki yace "ah ah kaga
gayun kauye wadanan Kuma su waye?"cike da zolaya yayi maganar mansoor ya sake kallon Dina yace
"umhmm talk su waye wadanan?turosu akayi?ko mahaifinki ne ya turosu"da sauri ta kallesa cike da
mamaki tace "mahaifina?mai kake nufi?kanaso kacemun haushin mahaifina kakeji akaina?"yadda tayi
maganar yasa jikinsa yayi sanyi,ransa yadan baci yadda tayi amma saidai sam bayaso daga zuwansu su fara
samun matsala haka nan yasamu kansa cikin natsuwa kasancewa da ita, ba yanzun bane zai nuna mata
tsananin haushin mahaifinta da yakeji akanta ne,karasowa su tasiu sukayi ya daga hannu zai kaiwa Dina
mari da sauri cikin zafin nama mansoor ya sauke masa mari ya kara sauke masa "kai kai waye da zaka daga
hannu kace zaka mareta?mai tayi maka?da ka mareta yau da ka kwana a daki mai tsananin duhu wanda ko
tafin hannunka bazaka gani ba,saina nuna maka kai karamin dan iska ne jahili"cikin fushi mansoor ke
maganar jikinsa har rawa yakeyi,sameer ne ya rukosa "common kayi saurin hannu man meyasa ka
maresa?"kallon da mansoor yayi masa yasa yaja bakinsa yayi shiru, tasiu ya gyara tsayuwa yana shafa
gefen kumatunsa yace "mari na kayi akan na kamaka da matata?matar da nake shirin aure?"kafin mansoor
yayi magana Dina ta karbe cike da rashin kunya tace "Allah ya tsari Dina da auren dan iska mazinaci irinka
aida in aureka gara na kare rayuwata a haka,uban waye ya baka auren nawa?"tace tana rike kwankwaso
mansoor jikinsa ne ya soma rawa ya ciro waya daga aljihunsa yace "idan baku bar wajen nan ba yanzun
nan zan kira yan sanda su kameku su kaimun ku birni su ajiye har sai lokacin dana dawo babu Kuma wanda
ya isa ya karbeku yasan inda kuke"ganin haka yasa abokan tasiu ja da baya cike da tsoro nan da nan fuskar
tasiu ta kumbura gefen idonsa tsare mansoor da ido yayi yace "kasa a ranka saina aureta badai kazo daga
birni bane dan ka hure mata kunne ka tsaya kaga me zai faru"ya juya yana fuskantar Dina yace "ke kuma
zan samu baba kulu a yau din nan zan sanar mata da komi kuma zan fadawa mahaifinki da wanda na ganki
kinsan sauran"gaban Dina ya fadi jin zai fadawa babanta ya ganta da mansoor tabbas ya fada masa
kashinta ya bushe dan yanzun babu wanda yasan inda take,yana gama magana ya juya da sauri cikin sanyin
jiki tace "Tasi....."mansoor ya fuzgota ganin tana kokarin binsa yace "ke kiransa kikeyi? tsoro kikeji kada a
gayawa mahaifinki ya dafaki?ko ya yankaki?"ta kauda idonta gefe batare da tace komi ba sameer ne ya
matso yace"ya isa haka wanan gayen ya kamata mu dauki mataki akansa man amma kabari mukoma gida
muyi magana tukunna dan naga yanada courage"Mansoor ya gyada masa kai suka cigaba da tafiya gabaki
daya Dina bata cikin hayyacinta har sukazo ta bayan gidansu ta kallesa "me zakayiwa tasiu?"a sanyaye tayi
maganar idonta jajir,

haushi takeso tabashi ta damu kenan bataso a taba lafiyarsa ko mene? banza da ita yayi kamar beji ta ba,ta
matso daf dashi ta marairaice fuska "kada ka cutar dashi idan ka cutar dashi hakan zai iya zama sanadiyyar
yanke abokantakata daku kaji?"a hankali ya dago ido sa ganin yadda ta marairaice fuska yace "now tell me
meye tsakaninki dashi?"sameer na tsaye yana kallon yanayin mansoor tabbas mansoor son Dina yakeyi ga
kishinta nan a kwayar idonsa amma ya kasa gane hakan ya kasa yadda soyayyarta ke dawainiya dashi,nan
Dina ta kwashe komi dake shirin faruwa na aura mata tasiu ta fada masa,

hankalin mansoor ba karamin tashi yayi ba yace "what?aura miki wanan gajan?"ta jinjina kai idonta ya
kawo ruwa tace "bazan auresa ba saboda mahaifina bayason hadin,innah ta ce keso saboda shidin yaron
yayarta ne"Mansoor ya cije lebe ransa ba karamin baci yayi ba ta kalli window din sanan ta dubesu ta kasa
fada masa me takeso,kafeta da ido yayi yace "inada feelings akan akwai abinda kikeson fadamun"ta
sunkuyar da kai cike da kunya tace cikin zuciyatta taya zan fara fada masa ya dorani ta window din nan in
dura?,katseta yayi "mu zagaya naga shigarki cikin gida"da sauri ta girgiza kai "kinajin tsoron a ganni tare
dake a fadawa mahaifinki anga mashayi a kofar gidansa?"girgiza kai tayi tace "ko daya kawai dai da zan fito
ba ta kofar gidanmu na biyo ba na taho wajenku"cike da mamaki mansoor da sameer sukace "ta ina kika
biyo?"tana murmushi ta nuna musu window din dukkansu dariya sukayi mansoor mamaki ne da al'ajabi
yasa ya kara bin window din da kallo,

"kina nufin durowa kikayi kikazo wajen man?"sameer yayi maganar cike da tsokana,tura baki tayi zatayi
kuka da sauri mansoor yace "ya isheka Sameer"gimtse dariyarsa yayi sameer ya juya kiran khairatu ya
shigo wayarsa,

"yanzun in daukeki in doraki kenan."ta gyada masa kai,murmushi yayi ya matsa daf da ita yana kallonta
itama shi take kallo cikin wani irin yanayi kallom da yakeyi mata yasa ta runtse idonta cike da kunya,hakan
ya bashi damas sa hannu daya ya dagota ya tallabota ta kasa da dayan hannunsa ya dorata saman window
din dai dai nan sameer ya juyo,sakin baki yayi yana kallon yadda mansoor ke rike da dina tana kokarin
direwa,da sauri ya kashe wayarsa ya soma musu video tana kyalkyala dariya shima dariyar yakeyi yace "sai
nauyin tsiya me kikaci haka kikai nauyi?"tayi murmushi tace "awara"tana fadan haka ta rike wayarta da
kyau ta Dira cikin dakin yana juyowa yaga sameer na dariya ya hade rai yace "muje"suka soma tafiya.....

murmushi Dina kawai takeyi tana sauke ajiyar zuciya bayan dirarta cikin daki,bugun kofar dakin yasa
gabanta ya yanke ya fadi ta sauke ajiyar zucuya tace "nagodewa Allah yasa nadawo da badan hakan ba da
asirina ya tonu"tace a fili da sauri ta bude akwatin garwarta ta tura wayarta ciki sanan ta cire hijab dinta ta
cire dankwalinta ta bude kofar dakin tana murtsika ido,saida gabanta ya fadi ganin baba kulu da su tasiu
tare da innahrsa "na fada muku ba Dina kuka gani ba Dina tana cikin daki kaga ma bacci ta tashi
kungani"wani kallo baba kulu keyiwa Dina sanan ta dubi tasiu da idonsa daya ya kumbura yayi baki kamar
wani abu ya cijesa tace "kace kaga Dina da wanan yaran yan iska na birni"kallon Dina tasiu yayi cike da
mamaki yace "wallahi naganta a gabanta ya mareni har sau biyu saboda ita har ya kumburamun fuska
sanan da bakinta tace ko zan mutu bazata aureniba data aureni gara ta mutu batayi aureba"Innahr Dina ta
dubeta tace "wai haka Dina tsakaninki da Allah nasan bakya karya koda kuwa laifi kikayimun"Dina gabanta
ya fadi tabbas batayiwa mahaifiyarta karya amma yau ce rana ta farko da zatayi dan ta kare kanta "innah
nifa ban fahimci abinda suke fada ba wadanan dan ni yanzun na bude kofa bacci nakeyi tundazun da baba
yazo ya fita ta ina suka ganni?tayaya har nayi musu magana kurwata ce tazo?"ta karasa maganar tana
harararsu duka,innahr tasiu tace "kinga in zakuba yaron nan yarinyar nan kubashi idan bazaku bashiba ku
fada mana kawai mu cire rai da aurenta,inma bashi dinba mezaiyi da Dina yar dake yawo da yan iskan birni
yan shaye shaye,waye yasan ma me sukayi da ita ragowarsu zai aura"Dina ta harzuka tace ko kuma ni in
auri ragowar yan talla ba,wanda kuke zargin dan iska ne shi ba dan iska bane kuma yabar shaye shayen a
dalilina"innahrta ta kai mata duka a baki take taji wani zafi ya ziyarceta ta rike bakinta tana baka musu
harara tasiu kuwa kwafa yayi yace "zasuga abinda zanyi musu"ya juya da tawagarsa sukayi gaba sukabar
baba kulu da mahaifiyarsa da innahr Dina suna magana,Dina furucin mansoor ne ya dawo mata kada su
tasiu suje wajensu sukai kansu dan tabbas bata yarda da furucin mansoor ba ta juya ta koma daki....
*******
mansoor na rike da waya yana sauraren rufaida cike da rudani yace "ohhh really shirin aure da nabeeha
akeyimun?tou wallahi bazan aureta in tafi kasar waje da ita ba babu inda zani "yana maganar ransa a bace
rufaida ta nisa "na fada maka ne dan ka shirya domin nasan baka sani ba amma ya man Dan Allah kada
momy tasan nina fada maka"ta marairaice jinjina mata kai kawai yayi "ok"ya katse wayar sameer dake
sauraren komi yana gefensa ganin yadda mansoor ya Shiga damuwa yasa shima ya Shiga "common kai fa
namiji ne meyasa zaka Shiga damuwa?babuwanda ya isa yayi maka auren dole beside idan bakason
nabeeha ga Dina mana"da sauri mansoor ya kallesa "yess ga Dina ko zakacemun ba sonta kakeyi bane?
man kanason Dina tunda har ka iya kasa sukuni saboda ita mansoor ka fadamun abinda ke cikin ranka
akam Dina"ajiyar zuciya mansoor ya sauke ya zauna akan sofa ya dafe kansa sameer na tsaye yana
kallonsa,ya mike da sauri ya bude jakar daya zuba kayan shaye shayensa ya shiga cirowa da sauri sameer
ya rikesa "lafiyanka?maganar aura maka nabeeha ce tasa zakayi shaye shaye bayan ka tabbatarwa da Dina
ka daina hakan yasa ta amince da kai a matsayin aboki bayan nasan ba abokantaka bace soyayya
ce?"girgiza kai yayi "bazan taba iya daina shaye shaye ba na fada mata ne kawai dan ta Amince dani domin
ina tsananin bukatarta a kusa dani halayenta da dabiunta suna sakani nishadi, kasancewa da ita na samu
natsuwa da kwanciyar hankalin,infact Dina is my peace of mind"murmushi sameer yayi mansoor ya bude
kwalba daya ya shiga sha yana lumshe ido sameer na tsaye ya harde hannunsa a kirjinsa kalaman mansoor
keyi masa yawo akai,yana fadin itace peace of mind dinsa amma yace ba soyayya sukeyi ba?yana nan tsaye
har mansoor ya shanye kwalbar ya janyo tabar wiwi ya kunna ya soma zuka yana busar da hayakin
idanuwansa jajir ya kalli sameer "da kake maganar in auri Dina tayaya?ka manta da kiyayyar da mahaifinta
keyi mun?ko ka manta ne in tuna maka?baxan taba zuwa in durkusa in rokesa akan yarsa ba beside Dina
ba aji na bace yarinyar data taso a kauye ta girma a kauye batasam komi ba"

"idan haka ne saika hakura ka auri zabin iyayenka nabeeha tunda tana sonka kuma kun dace"tsaki
mansoor yayi "zabin momy ce ita bana daddy ba kuma bazan aureta ba bazan taba auren nabeeha ba dik
su gama shirinsu akai zuwa lokacin da zan koma zan rusa musu plan"murmushi Sameer yayi "amma kasan
momy bazata amince da yar talaka bakauya ba?"

"wai kai waye yace maka inason Dina?how many times zan fada maka canjata nakeso nayi?look babu
soyayyarta a tare dani banajin hakan babu alamun kaunarta a zuciyata"shiru sameer yayi tabbas mansoor
ya bashi tausayi sosai yana tsaka mai wuya ya kasa amincewa da yanason Dina amma tabbas soyayyarta ke
dawainiya dashi,hayaki ne cike da dakin lokacin da sukaji motsi ta ta cikin gidan,kallon juna sukai sameer
yajiyo muryoyinsu take ya gane su tasiu ne ya karasa yaja labulen window din ya gansu ya juyo yace "man
mutuminka ne suka biyomu su dau fansa"yayi mgnr yana dariya mansoor ya mike yace "good ya kawo
kansa kira su captain dake baya suna ba dabbobin can abinci da masu tsaro su kamasu su dauremun
su"sameer ya jin jina kai cikin seconds ya kira captain ya shaida masa,

tasiu na kokarin ciro wuka ta baya yaji an cafkeshi yana juyawa yaga sojoji cikin kaki sun zagayesu sameer
ya kalli mansoor sukai murmushi suka saki labulen.....
*******
misalin karfe goma na dare Dina na kwance a daki tayi shiru tunanin kudin da mahaifinta yazo dashi yace
sameer ne ya bashi takeyi me hakan ke nufi?sunba mahaifinta kudi ne dan wata manufa? Mansoor take
tunani tayi murmushi shine ma zaiba Sameer dan yaba mahaifinta,meyasa zaiyi haka?matsalar sa shaye
shaye kuma ya daina tasan babanta zai amince da abotarsu matukar ya bari,

mansoor wayarsa ya ciro a jikin carji ya kalli sameer ya tabe baki yana waya da khairatu "malam da mun
koma ayi maganar aurenku kawai ba sai ka jirani ba wanan soyayyar da kukeyi tsaf zaka haikewa yar
mutane"ya daura fuska mamakin maganar mansoor sameer yakeyi be tanka masa ba yana murmushi ya
kwanta ya ciro wayarsa,

"wanan village girl din ko tayi bacci oho"yayi dialing numberta daya sa mata a wayar,

wata zabura Dina tayi jin wani vibration a cikin a kwatinta ta dafe kirji gumi ne ya shiga karyowa a goshonta
"maciji nashiga uku a cikin a kwatina"wani fitsari taji yana naiman kufce mata ta Shiga sintiti cikin
dakin,can taji shiru wayar ta katse,
tsaki yayi ya sake dialing a karo na biyu "common ki dauka Dina ki dauki wayar nan i cant sleep without
talking to you common"Sameer ya kallesa ya girgiza kai,

a hankali ta taka gabanta na faduwa ta leka akwatin wayar tagani tana haske,dafe kirji tayi ta runtse ido ta
sauke ajiyar zucuya ta waiga jikin window kar innarta basuyi bacciba taga ba kowa sai hasken farin wata ta
dauki wayar ta kara a kunne "ko kinyi bacci ne in barki"yace cike da isa,

girgiza kai tayi kamar yana ganinta "banyi bacci ba ya man....."yadda ta kira sunansa yasa ya mike zumbur
ya zauna ya murtsuke idonsa "mai kikace?maimaita abinda kika fada kinji ya man...."ji yayi tamkat tafi
kowa Iya kiran sunansa shiru tayi tace "nifa kabani tsoro na dauka maciji ne ya Shiga akwatina ashe waya
ce dan gab nake da fita in taso baba da innah a shigo a fitar mun dashi"wata dariya ya kwashe da ita yace
"really?"shiru tayi dan bata fahimci me yake fada ba,

"da kin kwabsa da mahaifinki ya gani da ya kwace da kinjamun wata sabuwar tsanar"shiru tayi jin abinda
yace dukkansu basu sake magana ba gajiya yayi yace "meye labari Dina "

"sai kace wata gidan rediyo?"tace hade da murmuda baki, murmushi yayi samun kansa yayi da nishadi nan
da nan ya mance bacin rai da damuwar dayake ciki,kiran wayar nabeeha ne ya shigo wayarsa call waitin ya
duba yayi tsaki da sauri tace "waye kakewa tsaki badai Abokina sameer ba"ya juya ya kalli sameer daya
dage kafarsa yana waya hankalinsa kwance yace "yayi bacci"tace "toh"nan suka cigaba da hira da Dina
wadda hakan yasa mansoor yaji wata kaunarta na kara shigarsa cikin minti talatin wata shakuwa tashiga
tsakaninsu dikda hirar da sukeyi surkullenta da kauyanci take baza mai,

"yauwa ya man nace karkayiwa su tasiu komi kaji"cije lebensa yayi tunowa yayi da yasa an dauresu yace
"bazanyi ba tunda bakiso"murmushi ne ya subce mata,

innahr Dina zama tayi ta kara fitilar dakin ta taba babanta dake kwance wanda shima ba baccin yayi ba
"tashi kaji"da sauri ya tashi yana kallonta "lafiya kika tasheni cikin wanan daren?"

"nifa ina tsoron mutanen nan kudin nan da aka baka da sunan zakka kar azo siyar musu da Dina kayi"ajiyar
zuciya ya sauke "ko daya,yaron daya bani yanada hankali sameer sunansa, ba irin shashashan abokinsa
bane mashayi,ki kwantar da hankalinki bazan taba siyarda dina ba"

"idan sukazo da maganar soyayya fa?"innahr Dina tayi maganar cike da damuwa,nan da nan fuskarsa ta
sauya yace "babu soyayya tsakanin su domin wanda ke son nata ko mutuwa zaiyi bazan bashi yata Dina
ba"shiru dukkansu sukayi ji sukai kamar ana magana cikin gidan hakan yasa hantar cikin innah ta kada "kaji
ko kamar muryar Dina nakeji kardai yaron nan cikin dare ya biyo tunda ka yanke alaka a tsakaninsu"

saukowa yayi daga gadon cikin fushi yace "idan shine kuwa saina sheme masa kai inyaso uban nasa yazo
garin ya kaini kiri kiri"mikewa tayi Yana kokarin bude kofar fale fale,

kara Dina taji alamun bude kofa idonta a lumshe suna magana tayi saurin budewa ta zabura ta zauna tace
"ya man naji motsin bude kofa kamar su baba ne saida safe"tana gama maganar ta katse ta daga katifa ta
tura waya,mahaifinta daidai nan ya turo kofar dakin ta rufe ido cikin zuciyarta tana adduar Allah yasa beji
ta ba......

*SLIMZY*😍
[11/11, 08:16] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

JAMA'A, INA GABATAR MAKU DA ROYAL EXQUISUTE, GIDAN GYARAN AURE, GIDAN AMINCI, GIDAN GIGITA
MA'AURATA, JAMAA INA AMARE? UWAYEN GIDA? ZAWARAWA? DA KUMA MASU JEGO, INA MATA?
MATAN DA SU KA AMSA SUNAN SU MATA? MATAN DA SUKE SON ZAMA DARAM DAM A ZUKATAN
MAZAJEN SU? MATA ƳAN ƘWALISA? TO WALLAHI ROYAL EXQUISUTE NA KU NE, SUKE DA INGANTATTUN
KAYAN MATA NA GYARA BA WAI TAWULWULBA, BA WAI SHA KA TAFI BA, KAYAN MATA DAKE ƘARA DARAJA
DA ƘIMA WAJEN OGA, GA SAUƘI GA ARHA, GA KUMA AIKI..ROYAL EXQUISUTE ZATA GYARE KU
KI TUNTUBI WANNAN NUMBER 08030644073
Location kano,nationwide delivery

*8*

kallon kallo innah da baba sukeyi tsaki yaja "gashi kim fito damu a daren nan kedai kawai kin tsorata kina
tunanin zasuzo su sace miki yarinya babu mai sace Dina a cikin garin nan sanan kisa a ranki bazan taba
bawa wanan yaron yarinyar nan ba ko shi kadai ne namiji a duniya bazan bawa mashayi yata mara kunya
ba"yana gama maganar ya fice,innah ta girgixa kai ta janyo kofar tabi bayansa,a hankali Dina ta bude
idonta maganganun mahaifinta keyi mata yawo akai,meyasa babanta zaiyi wanan furucin akan mansoor
saboda ya damu da ita?bayan shaye shayen ya daina a dalilinta wanda itace ta zama silar shiriyarsa?sam
bataji dadin furucin mahaifinta ba,kawai be fahimci mansoor bane,ajiyar zuciya ta sauke ta ciro wayar daga
kasan pillow tana kallo,murmushi tayi tana jujjuya wayar "ban gaji da magana da yaya man ba gashi yanzun
na katse wayar kuma ban iya kiransa ba dana kirasa mun karasa maganar mu,naji kamar yanaso yamun
magana akan makaranta,ta gyara kwanciyarta tana rike da wayar cikin zuciyarta tana adduar Allah yasa ya
kira tana son jin muryarsa ashe yana hira haka?

mansoor tagumi yayi minti minti yaja tsaki,ya kalli sameer wanda tuni yayi bacci,ya daga ido ya kalli agogo
karfe biyu da minti arbain da biyar na dare,yayi tsaki meyasa mutumin nan zaiyi musu haka? mahaifin Dina
ya cika tsauri,meye yajeyi cikin dakinta a wanan daren idan ba fiti na ba?dan shi ya haifeta aiba Shi ya
halicceta ba da zai takurawa rayuwarta,tsaki yaja ya koma ya kwanta ya lumshe idonsa, muryarta ce ta daki
dodon kunnensa "yaya man...."wani zabura yayi ya zauna "no no bazan iya bacci ba sai naji muryarki Dina
sai naji halin da kike ciki,i will call you just once in kin dauka shikenan idan bako dauka ba nasan mugun
mahaifinki yana tare dake yana azabtar mun dake,ya cije lebensa ya dauki wayarsa ya sake kiranta,wayar
na shigowa ta zabura ta dauka ta kara a kunnenta,wata ajiyar zuciya ya sauke yace "are you ok?"shiru tayi
bataji abinda yace ba ya sake fada,still batayi magana ba ya ciro wayar a kunnensa yaga tana tafiya ya sake
karawa a kunnensa yace "Dina....."cikim siririyar muryarta tace "naam yaya man....."ya lumshe idonsa wani
nishadi ne da farin ciki ya lullubesa yace "halan bakiji ina magana ba kika share bakice komi ba"

"tou aidai kasan banajin yaren nan naka na yan birni"tayi maganar kamar tana rad'a can kasa da muryarta
tayi wanda hakan ya haifarwa da mansoor wata irin kasala,wani irin yanayi yakeji wanda be taba jinsa ba a
rayuwarsa "kasan me?"ta katse masa tunani Yana lumshe ido yace "sai kin fada"tayi shiru kamar bazata
fada masa ba,tana gudun kada ransa ya baci yace "umhmm ina jinki yi magana"tace "babane daya shigo"

"ya dakeki ko?"yace a kausashe da sauri tace "ah ah,cewa yayi bazai taba baka ni ba idan ma siyansa
kukesonyi da sameer ya bashi kudi,ko kai kadai ne namiji a duniya"wani irin bacin rai ne ya ziyarci mansoor
nan da nan jijiyoyin kansa suka firfito zucuyarsa nayi masa wani irin zafi da tukuki,tana magana ya kashe
wayar,take taji hankalinta ya tashi ta zabura ta zauna tace "nashiga uku ya kashe wayar meyasa nafada
masa?"ta jingina da jikin bango take wasu hawaye da batasan dalilinsu ba suka soma zubowa,
shi kuwa kamar mahaukaci haka ya mike ,"an fada masa ni zanzo neman aure wajensa ne?koko an fada
masa zanso yarsa da aurene?be kai matsayin da zanzo in durkusa dan ya bani yarsa ba,babu wanda ya
tabamun wulakanci da kaskanci irin wanda mutumin nan yayi mun,wato sameer ya kai masa kudi ne dan
ya amince damu mu rinka kula yarsa ko mene?"cikin daga murya yake maganar,sameer cikin bacci yakejin
maganar mansoor sama sama idonsa a rufe yaji mansoor na bubbuga sa da sauri ya mike ya zauna "lafiya?
meyafaru?ko an daura aurenka da nabeeha ne?"ransa ya kara baci kiran sunan nabeeha da sameer yayi,

"meyasa kayimun haka sam?meyasa ka siyarmun da mutunci?sam tayaya zaka dau kudi kaba mahaifin
Dina?ka zubar mun da mutunci?yayi tunanin nayi hakan dan in siyeshi ne! yaushe kabashi kudi?"jikin
mansoor har rawa yakeyi yayi fushi sosai,sameer ya nisa ya dafe kansa sam bayason irin maganganun da
mansoor yakeyi akan mahaifin Dina bayan yana tare da yarsa kuma sonta yakeyi dikda ya kasa yarda da
hakan?katse masa tunani yayi "magana nakeyi kayi shiru"sameer yace "yanzun meya faru?"nan mansoor
ya kwashe yadda sukayi da Dina a waya ya fadawa Sameer,

"calm down ni abun arziki nayi,dan ban fada maka bane kawai ya zama laifi,nazo da kudi sosai dayawa da
zan rabawa mutanen garin nan saboda zakka muka fidda hakan yasa na dauka nabawa mahaifinta amma
bada nufin wai in siye bakinsa ba,akan me zan siye bakinsa bayan kaidin kace ba soyayya kukeyi ba"shiru
mansoor yayi be sake cewa komi ba, Sameer ransa ya baci ya koma ya kwanta kawai badan yanajin bacci
ba saidan zafin abinda mansoor yayi masa,yaja tsaki ya gyara kwanciya yaja bargonsa,

kasa bacci mansoor yayi zuciyarsa keyi masa wani irin kuna,gashi ya kashe mata waya batare da sunyi
sallama ba me zata dauka?ko ya kirata ne?wata zucuyar tace kada ya kirata meyasa zai tsanesa haka kawai
dan kawai yana shaye shaye?yaja tsaki ya dubi agogo hudu da rabi ya mike kawai ya shige toilet ya dauro
alwala ya fito ya shimfida dadduma ya tada sallah,.

lamo tayi akan katifarta tana kallon wayar batajin bacci lokaci kankani bacci ya kaurace mata dole zata
sanarwa da mahaifinta waye mansoor dan bataji dadin furucinsa akansa ba,to idan ta fada masa hakan zai
tabbatarda bataji maganarsa ba suna nan tare,dakyar bacci barawo ya saceta gab da asuba,befi baccin
minti arbain tayiba taji innahrta na buga mata kofa.....
*****
"rufaida kin fito?dama yanzun nakeso in tasoku kizo kiga wadanan kayan hajiya basira ce da sassafen nan
tasa driver dinta ya kawosu na dauka zaasa a akwatin nabeeha"rufaida ta zauna tana kallon tsubin kayan
dake gaban momy fuskarta babu walwala Momy tacev"yadai naganki haka ina nabeeha?bata tashi ba tana
nan tana baccin nata"girgixa kai tayi "ko daya matar da batayi bacciba ta kwana tana kuka"momy ta fiddo
ido waje "meyafaru meya hanata bacci?"rufaida ta nisa "momy wanan auren da kuke shirin yiwa yaya man
da nabeeha bafa ya sonta fa?ina zargin akwai wadda yakeso wallahi saboda jiya dik Kiran da takeyi masa
baya dauka call waiting daga karshe yayi diverting calls dinta wanda hakan ne yasa hankalinta ya tashi take
tunanin dawa yake waya kuma kinsam fa dama basu daidaita kansu ba"tana maganar tana kokarin daukar
passport din data gani zube a centre table "wanan fa?"ta bude taga passport din mansoor ne dana
nabeeha wanda aka kai har visa ta fito zasu tafi nan da sati uku,tabdijan "momy dagaske kukeyi dai zaku
daura auren ya man da nabeeha su tafi Cyprus "Momy tayi tsaki tace "da karya kike ganin inayi?eye? to
dagaske nakeyi koma dawa yakeyin waya shi yasani shi ta shafa amma tabbas sai ya auri nabeeha ya tafi da
ita,zamu rabashi da garin nan ne saboda wanan mugun shaye shayen da yakeyi"rufaida ta bata rai tace
"dan shaye shaye?idan kuma yasamu me hanasa fa?"

"tunda sameer be hana mansoor shaye shaye ba babu wanda ya isa dik amintarsu sameer ya gagara tou
kawai bazai bariba amma idan ya tafi can dole zai canja wasu abubuwan sanan akwai company din da suka
gayyaci mahaifinsa wani kasuwanci haakan yasa yasamu damar turasa can din"cije lebe rufaida tayi tace
"zan leka kitchen inga me sukayi inajin yunwa"

"ki taso rufaida tasameni a nan in lallasheta taci abincu bazai yuwu yar mutane ya rinka mata haka ba,nima
ai kinga tunda suka tafi kauyen be kirani ba kila fushi yakeyi tou in fushin ne ma me akayi masa?bayan
besan da wanam labarin ba?"rufaida tayi gaba cikin zuciyatta tace bayan na sanar masa zanga yadda
zaayiwa namiji auren dole,ta shige kitchen momy ta shiga kwalawa nabeeha dake daki kira....

******
cikim sauri baba ya shigo gida har yanacin tuntube,Dina ta tasa kofin kokon da aka zuba mata batasha ba
ta gagarasha burinta kawai tasamu damar fita tasamu su mansoor taji fushin meye yakeyi da ita?jiya ya
kashe waya gashi ita bata iya kiransa ba,"lafiya malam ka dawo haka?"

"inafa lafiya?yanzun aka kirani gidan mai gari naje ance tun jiya baaga su Tasiu ba da abokansa kuma an
tabbatar da cewar angansu tsaye da su sameer yan birnin nan ana zargin da saka hannun Dina ciki"da sauri
Dina ta kalli mahaifinta a furgice ta dafe kirji "ni kuma?tayaya zansa hannu wajen batansu?nibabu ruwana"

"dasa hannunki mana tunda bakison aurensa?tou kisani ko zaki mutu saikin auresa kuma ana ganinsu zaa
daura aurenki da tasiu kodan in huta da masifar nan in rabaki da wadanan bata garin"innahrta tayi
maganar hade da rushewa da kuka,zabura Dina tayi gabanta na faduwa kardai wani wuri su mansoor suka
kai tasiu tabbas tasan jiya yayi furuci akansa gashi an wayi gari baa gansu ba,komawa daki tayi ta banko
kofar cikin tashin hankali tace "nashiga uku innahlillahi yanzun ya zanyi idan innah tace saita auramun tasiu
bayan zucuyata bashi takeso ba?bata damu dashiba ko kadan?"wata zuciyat tace "waye zucuyarki takeso
tadamu dashi da lamarinsa?"ta danne kirjinta dake harbawa take tace "ya man.....shi kadai nadamu
dashi....toushi din ya damu dani?"tace tana jijjiga kai tabbas ya damu dani amma aiba sona yakeyi ba,take
zucuyarta ta kwabeta tou meyasa ya shiga lamarina gashi jiya zuwa yau sanadinsa nakasa cin komi?cikin
zullumin yayi fushi nake?

mansoor na tsaye hannunsa rike da tabar wiwi idonsa jajir yana kallon bishiyoyin cikin gidan cike da
tunaninta tayaya zai hadu da ita?kira nawa yayi mata bata dauka ba?ko wani hali take ciki oho,ya sake
dialing wayarta cike da fargaba,tana tsaye jikin kofa taji vibration da sauri ta wawwaiga sanan ta dauki
wayar ta kara a kunnenta tace "ya man....inasu tasiu?"tambayar da tayi masa kenan kafin yayi
magana,wani abu ne yaji ya caki zuciyatsa ohhh su tasiu take tambaya kenan har sun fahimci be kwana
gida ba?bazama ta gaisheshi taji yadda ya kwana ba?ta sake jefa masa tambayar murya kasa kasa tana jiyo
muryarsu innah da mutanen gari cike da gidansu yayi banza da ita yana sauraren muryarta dake haifar
masa da kasala,marairaicewa tayi muryarta na rawa zatayi kuka tace "Dan Allah ka rufamun asiri ka
fadamun inda suke, idan zakayi fushi dani kayi da nikadai kayimun horo dik yadda ya dace zan jure hakan
amma kayimun magana"a sanyaye ya sauke ajiyar zucuya yace "baki iya gaisuwa bane?"cije lebenta tayi
dan yanzun lallabasa zatayi "ina kwana ya man,antashi kalau?"murmushi yayi yace "village girl,ya
kike"dakyar ta motsa bakinta tace "lafiya lau"shiru sukayi su dukan,karasawa yayi ya zauna a kujerun dake
harabar gidan gonan ya dora kafarsa daya kan daya yana hangen sameer ya fito a shirye,

"tasiu suna nan na kyalesa amma shine ya kawo kansa da kansa"ajiyar zuciya ta sauke tace "kayiwa Allah
da manzonsa ka kyalesa yanzun gashinan ance ka boyesa amma hakan bashi zai hana a auramun shi ba"

"what?mai kikace?aiko sunja masa"zai katse wayar tace "kana ina?"shiru yayi ganin sameer a gabansa
yana cika Yana batsewa yacw "ina gidan gona"ya katse wayar cikin sauri ta turata a wandonta ta kama
window din ta dane ta dire tayi gidan gonar....

"yadai sam sai ina kuma?"sameer yace"gida"da sauri mansoor ya dubesa "karkacemun zaka tafi saboda
abinda ya faru jiya kadaisan daddy bazaiji dadi ba"Sameer yayi murnushin takaici yace"ko daya zan tafi ne
khairatu nasan ganina sanan zan samu momy akan maganar nasamu matar aure"mansoor yayi murmushi
ya jinjina kai yace "good"ya zuki tabar hannunsa ya busar da hayakin?sameer yayi masa wani kallo yacw
"amma kasan abin nan da kakeyi yaudara ce?ko ka manta kacewa Dina kabar shaye shaye?kuma gashi
kanayi?"
"nafada mata ne kawai dan ta amince dani da abotata dan ita din in canjata amma badan wani abu a
rayuwar duniya zai sauyamun raayi daga shaye shaye ba"Sameer yace "really?cin amana kenan ko?koda
yake lets see amma nasan gaba kadan soyayya zata tarwatsa wanan shaye shayen"tabe baki mansoor yayi
bama yason sameer nayi masa maganar wata soyayya da kalubalenta shi dai dayaga zai iya yayi tayi "ka
gaida khairatu"yace a dakile Sameer ya jinjina masa kai ya shiga mota yaja,mansoor yayi cilli da sauran
tabar dake hannunsa ya dafe kai maganganun sameer nayi masa yawo akai "dagaske amanar Dina yaci dan
yayi shaye shaye bayan ya mata karyar dainawa?"

"Ranka ya dade wata yarinya ce gata nan tazo wajenka ta shigo?mai gadi ke tambayar mansoor da yayi
zurfi cikin tunani yadan kallesa yacw "ta shigo "yasan Dina ce da sauri ya shinshina hannunsa da kansa
gabansa ne ya fadi karfa ta gane?ganinta yayi ta shigo sanye take da wani jan hijab iya gwiwa a dinkesa ta
wajen kai cikin sauri har tuntube takeyi,ya tsareta da ido gashi hijab din ya tsufa sosai ya kode amma be
hanasa yi mata kyau sosai ba,saidai fuskarta tayi wani kala babu walwala idanuwanta farare tass kamar
madara da dan hawaye a makale cikinsu ta karaso,tsayawa tayi akansa "yadai.....zauna mana kin tsayamun
a kai"tana waige waige ta juyo tace "ka taimakeni ka fito dasu tasiu inda ka kaisu kafim yan garin nan suyi
muku hukunci domin yanzun haka baasan na diro ba nataho nan nadauki tsautsayine kawai dan in kareka
banason abinda zai taba mutuncinka da alakata da kai"tsareta yayi da ido dikda irin haukarta da kauyanci a
karo na farko tayi masa maganar dayasa jikinsa yayi sanyi,burinta ta tsare mutuncinsa batason damuwarsa
meyasa shi yayi mata karyar daina shaye shaye?,idonta ne ya sauka akan tabar wiwi din dake gabansa
kadan taja da baya tayi wani burki tace "au dama yaudara ce abun?"a kausashe tayi maganar da sauri yace
"yaudarar me?"ta nuna masa da yatsa ,gabansa ne ya fadi tabbas shine yasha tayaya zaifara mata
explaining?tsoro da furgici suka kamasa a karo na farko a rayuwarsa gashi baya karya gashi yana gudun ya
rusa alakar daya samu ta ginu da kyar.....

******
mahaifin Dina ransa a bace yake sosai haka sukayi tawaga kungiya guda su shida ciki harda hakimi suka
nufi gidan gona da niyyar samun sameer yayi magana dashi dan idan mansoor ne bayida abinda zai tsaya
musayar miyaun baki dashi bayan mashayi ne da kwakwalwarsa bata fada masa gaskiya....cikin fushi suka
Shiga dukan gate dim gida,

a zabure Dina tace "kagani ko?kayimun bayanin wanan sanan ka nemi inda zaka boyeni kafin baba ya
yankani"tayi maganar daidai mai gadi ya bude gate kafin yayi magana da wani yunkuri sun soma
shigowa......

*SLIMZY*😍
[11/11, 15:28] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

*GODIYA TA MUSAMMAN GA Y'AR MUTAN NIJAR ANTY HASSANA B.S ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MIKI*

*9*
JAMA'A, INA GABATAR MAKU DA ROYAL EXQUISUTE, GIDAN GYARAN AURE, GIDAN AMINCI, GIDAN GIGITA
MA'AURATA, JAMAA INA AMARE? UWAYEN GIDA? ZAWARAWA? DA KUMA MASU JEGO, INA MATA?
MATAN DA SU KA AMSA SUNAN SU MATA? MATAN DA SUKE SON ZAMA DARAM DAM A ZUKATAN
MAZAJEN SU? MATA ƳAN ƘWALISA? TO WALLAHI ROYAL EXQUISUTE NA KU NE, SUKE DA INGANTATTUN
KAYAN MATA NA GYARA BA WAI TAWULWULBA, BA WAI SHA KA TAFI BA, KAYAN MATA DAKE ƘARA DARAJA
DA ƘIMA WAJEN OGA, GA SAUƘI GA ARHA, GA KUMA AIKI..ROYAL EXQUISUTE ZATA GYARE KU
KI TUNTUBI WANNAN NUMBER 08030644073
Location kano,nationwide delivery

A tsorace ta juya zatabar wajen idonta ya sauka akan mahaifinta dake jifanta da wani irin kallo cike da
mamakin ganinta a wajen,"malam kaga yarka a cikin gidan gona meye ya kawota?"mahaifin Dina kasa
magana yayi suna kallon kallo shida Dina wadda ke tsaye hantar cikinta na wani irin kadawa,tsoro da furgici
ne suka cikata nan da nan taji kamar zata saki fitsari a wurin,mansoor kuwa dakewa yayi dayake namijin
duniya ne dikda ganin mahaifin Dina da wadanan tawagar be hanasa hada girar sama data kasa ba dikda
tsoron abinda zaayi mata yakeyi,"Barkanku da zuwa"abinda yace kenan a takaice yana binsu da kallo,Dina
kuwa sai raba ido takeyi bakinta na rawa ta dubi mahaifinta tace "Baba kayi hakuri ka ganni a nan ko?"daga
mata hannu kawai yayi yana girgixa kai cike da takaici "bana bukatar abinda ya kawoki ko ki fadamun
nagani, tunda ga shedar shaye shaye kikazo ya koya miki ko?"girgiza kai tayi da sauri tace "ba biyo sahun su
tasiu ne da naji kana maganar baa Gansu ba shine nazo basusan da zuwana ba ko zan mamayesu ingansu a
nan"tana maganar bakinta na rawa,wani irin d'aci yakeji a bakinsa miyaun bakinsa ne ya kafe ya kalli
mansoor wanda shi yake kallo yaji wata sabuwar tsanarsa da takaicinsa ya kamasa a karo na farko yayi
sanadiyyar kangarewar yarsa tunda ya haifi Dina bata taba yinkurin bata musu rai ba daidai da seconds
daya,yayi murmushin takaici yace "kayi nasara kaci wanan wasan saura nagaba yaro,kayi nasarar
kangarewar yata ko?ka jirayi hukuncin da zan yanke akanta da kai kanka bazai maka dadi ba sai kayi kuka
da hawayenka a gaba ata dalilin ta"Mansoor ya cije lebe ya dubi sauran da sukayi tsaye cirko cirko "nasan
abinda ke tafe daku akan yaran ku ne ko?"ya zuba hannuwansa a aljihu zucuyarsa na tafarfasa yace "laifi
sukayimun dikda ba lallai ku yarda da hakan ba amma zansa a fito dasu da kuma faifan video a waya
danasa aka dauka suna kokarin bankawa gidan gonar nan wuta na kamasu"nan sauran suka soma salati
Banda mahaifin Dina wanda yace "karya ne, yayi ne kawai dan raba tasiu da Dina jin shine zai aureta"

hakimi yace "tou kai yaro wace alak'a ce tsakaninka da Dina din?soyayya kukeyi aurenta zakayi ka kaita
birni ko yaya?"mansoor yayi shiru gabansa na faduwa ya juya ya kalli Dina wadda ke tsaye kamar an dasata
hawaye ke zuba a idanuwanta kamar am bude famfo ga majina dake zubowa daga hancinta, runtse idonsa
yayi ransa na kuna ganin tana hawaye bayan baya son kukanta ko kadan,"tambayarka mukeyi"hakimi ya
dawo da tambayar dayayi masa,

"Ehh sonta nakeyi da....."kafin mansoor ya karasa mahaifinta ya daukesa da Mari"sonta kakeyi da aure
zakace ko?"mansoor ya dafe kuncinsa yanajin wani radadi a kwakwalwarsa a karo na farko a rayuwarsa da
aka maresa tinda uwarsa da ubansa suka haifesa baa taba marinsa ba yau gashi akan Dina mahaifinta ya
maresa yau da wanine ya maresa bashiba da sai yasa an kashesa har lahira,kallon mahaifinta yakeyi cike da
mamakin yadda ya zabga masa mari be Bari ya jira yaji sonta yakeyi da mene ba? so yakeyi yace sonta
yakeyi da abota amma ya maresa?"karya kakeyi kaso yata dama abinda nakeson ji kenan kuma naji ya
tabbata maganar da innahrta ta fada ta zama gaskiya to kasani bazan taba baka yata ba harabada kuma
yadda ka kangarar mun da ita ka sauya ta kotu ce zata rabamu dakai,kuma ka gaggauta fitomin da yara ka
jira goron daurin auren Dina"idanuwan Mansoor sun kankace tsananin takaici da bacin rai duhu kawai
yake gani a gabansa besan lokacin da dakyar ya motsa bakinsa ya kwalawa Sergent kira ba,cikin sauri yazo
"jeka fito da yaran can"yana gama maganar ya mike ya cigaba da tafiya Dina kuwa ji tayi kamar kasa ta
bude ta shiga menene laifin mansoor dan ya kaunace ta? ashe sonta yakeyi dagaske?ta lumshe idonta ta
soma takawa mahaifinta ya daka mata tsawa "ina zakije?zaki bishi ciki ne ya koya miki sauran iskancin da
be koya miki ba?dawo ki tsaya a nan"jikinta na rawa ta dawo mansoor ya juyo ya kalleta tausayinsa ne ya
kamata ta rushe da kuka ya juyar da kansa idan ya cigaba da tsayuwa a wajen tabbas zai iya illata mahaifin
Dina zai iya kauda soyayya,da Abotar dake tsakaninsu ya bar masa tabon da bazai taba mantawa dashi
ba,suna tsaye aka fito da tasiu wanda dik sun galabaita tasiuu a wuyace yace "dama kina nan?kince ya
daina shaye shaye?tou me yakeyi jiya daddare da yau da safen nan?"cije lebe tayi ta danne zucuyarta da
takeji kamar ta tsunka masa mari tace "karya kakeyi baya shaye shaye ya daina a ta dalilina saidai nasan
rabashi dani zai iya maidasa halin da yake ciki"tasiu zai sake magana baban ya hanasa "rabu da ita idonta
ya makance amma zanyi maganin abun ka kwantar da hankalinka zan aura maka ita cikin satin nan"Dina
jikinta ya soma rawa dakyar take taka kafarta tana biye dasu har gida.....
******
sameer gyara zama yayi a gaban momynsa ya kurbi juice yace "momy nasan kinyi farik ciki sosai da jin
labarin zanyi aure da wadda zan aura ko?"momy ta kara fadada murmushinta sosai tace "kwarai dagaske
kaga zumunci zai kara kulluwa tsakanin mu ban taba kawowa khairatu kakeso ba sameer kayimun ba zata"
murmushi Sameer yayi yace "mansoor nakeso muyi tare dashi amma abun da kamar wuya"momy tace
"kamar yaya bayan hajiyar ta aikomin akan an tsaida lokacinsa da nabeeha?"shiru sameer yayi kamar ya
sanarwa da momynsa maganar Dina amma gudun halin Mansoor yaja bakinsa kawai suna cikin maganar
kiran mansoor ya shigo wayarsa,

"yadai man yanzun muke maganarka da momy Dan halak kaki ambato"momy tana dariya tana kallom
Sameer gyara zama yayi jin yanayin muryar mansoor yace cikin rudewa da damuwa "lafiya meya
faru?"Mansoor muryarsa a shake cikin tsananin bacin rai yace "ka dawo please i need you by my side inaso
ka fadamun alamomin soyayya"hankalin sameer ya tashe yace "yeah dama naso biyawa gidanku na
gaidasu momy ne amma ganinan zuwa yanzun zan kamo hanya kaji?ka kwantar da hankalinka ina tare
dakai kadafa ka damu kaji?"ya mike zumbur "momy zan tafi akwai yar matsala tare da man"momy tace
"tohhh meyafaru inji dai ba ciwonsa bane ya tashi"kada kai yayi"ko daya momy babu komi i will handle
it"momy tace "tou Allah ya tsare ka kula da kanka sanan gobe zan karasa gidan ummahn khairatu din idan
mahaifinka ya dawo zamuyi magana zan kiraka"yace "badamuwa"cikin sauri ya fice hankalinsa a tashe
yake burinsa kawai ya ga mansoor yasan halin da yake ciki....

*****
"Dina kinbani mamaki ban taba zaton wani zaizo ya batamun tarbiyyarki ba, dik irin yadda kikejin
maganata kinsa kafarki kim shure tunda kika hadu da wanan majanunin yaron to kisani babuke babushi
dukkansu kar insake ganinki da daya daga cikinsu,sanan maganar sakaki a secondary da kuma karatun da
kikeso kiyi na sokeshi"da sauri ta durkushe a gaban mahaifinta "kayimun rai baba idan mansoor kakeso na
rabu dashi zan rabu dashi zanyi yadda kakeso amma inaso kayimun uzuri guda daya banaso na zama silar
tarwatsewar rayuwarsa bayan nice nayi silar shiriyarsa mansoor mutumin arziki ne wallahi,kuma yana
so.....n"kasa karasawa tayi ganin yadda mahaifiyarta ke kallonta cike da takaici tace "innah ki sa baki kada
baba ya rabani dashi nasaba dashi sosai naji bazan auresa ba amma inaso ya bari muyi rabuwar mutunci
sanan banason auren tasiu gara ya nemi wani ya auramunshi"innahrta batace komiba saboda takaici baba
kuwa can kasan zucuyarsa kuna takeyi masa shi kansa baasom ransa zai aurawa Dina tasiu ba da wani zai
fito maganar aurenta ko waye zai aura masa ita amma banda mansoor banda abinda ya shafesu,cikin
zucuyarsa yace "Allah ga yata nan a hannunka banason aura mata wanda surukata keson aura mata nabar
komi a hannuka"yana gama adduar ya mike innah ta nisa tace "zakaje wajen mai gari ne akan a kira iyayen
yaran nan subar garin nan kuma su fita a sabgar yarinyar nan ko?"baba yace"ehh can zani akan maganar
ansamu number mahaifin takadirin za kuma a kirasa a fada masa komi sanan ayi masa tsakani da
Dina"Dina idonta jajir take kallon mahaifinta wanda bakinsa ya bushe ya kamata ace yana wajen facin
tayarsa amma yana gida akan maganarta,yunkurawa tayi ta mike zata shiga daki,"ina zaki?"innahrta tayi
mata magana cikin tsawa,cak ta tsaya batare da ta kalleta ba tace"dawo nan ki zauna kusa dani dan idan
kin shiga dakin bansan menene zaki aikata ba kila ya baki siddabarun da kikebi ta jikin bango kike tafiya
wajensa ki zauna ina ganinki a nan sanan ga dan wakenki nan har ya sandare tun safe bakici komiba kokon
da kika kai daki ma kuda ke binsa gashican"ajiyar zucuya ta sauka ta koma ta zauna ta tasa robar dan
waken a gaba tunanin mansoor takeyi tasan bacin rai na saka shaye shaye Allah yasa ba shaye shayen
yakeyi ba,ko wani hali yake ciki oho,taso ace ta Shiga daki ta kirasa ta jadadda masa yadda ta damu dashi
ta fada masa damuwarta amma ba dama saidai akwai dabarar data fado mata wadda zatayi amfani da ita
wajen Yin magana dashi,ajiyar zucuya ta sauke tana tsananin kewarsa ta lumshe idonta shi take gani
lokacin daya dorata akan window yanayi mata tsadadden murmushinsa....

*****
koda Sameer ya iso ya samu Mansoor a buge yasha yasha har ya gaji kwalabe ne a gabansa ga hayaki daya
turnuke dakin,"kai man zaka kashe kanka meyake faruwa haka?ya naganka cikin wanan yanayin?"idonsa
jajir yake kallon sameer dake kallonsa cike da rudani ya fuzge kwalbar daya dauko zai bude ya cillar gefe
yace "wanan itace soyayyar da kakeyiwa Dina?"zuba masa ido mansoor yayi sameer ya cigaba da magana
"tabbas son Dina kakeyi zan fada maka gaskiya ko kaki ko kaso man,saboda haka ka dawo hankalinka mu
nemi mafitar yadda zaayi ka mallaketa"mansoor ya zuba masa ido cike da kunci yace "menene alamomin
so?"sameer ya nisa yace "alamomin so dik sun bayyana a gareka man,abinda nake guje maka tun farko
kenan gashi ya faru saida na tabbatar maka da sonta kakeyi kaki amincewa gashi da kanka kanaso ka gane
haka,alamomin so sun bayyana a tattare dakai,yawan ambato,kulawa, damuwa da damuwat abinda
kakeso,kishi da tausayi"

"duka inayiwa Dina?"ya tambayi sameer a sanyaye,sameer ya jinjina kai "Duka kakeyi mata man,harda
wanda ban fada ba,yanzun fadamun meye ya faru bayan tafiyata in nema maka mafita?"shiru mansoor
yayi bayaso ya tuna yau mahaifin Dina ya maresa akan yarsa a karo na farko a rayuwarsa,nan da nan ya
sake ganin duhu ya mamaye ganinsa ya runtse idonsa gamm cikin takaici yake bawa Sameer labarin abinda
ya faru da furucin da yayi yanason dina da....basu bari ya karasa ba,sosai sameer ya tausaya masa yace
"man inaso ka yarda kanason Dina sosai so bana wasa ba tunda har mahaifinta ya mareka baka aiwatar da
komi ba"mansoor ya jinjina kai yace "na Amince tabbas ina sonta kuma na shiryawa yaki akanta"

"dakyau mutumina"Sameer yace yana murmushi "dan ko akwai yaki sosai a gabanka dan tabbas zaku kara
da mahaifinta sosai da kuma momy da mutanen gidanku,yanzun abu daya nakeso nabaka shawara shine
kayi dik yadda zakayi kafin kabar garin nan ka kafa soyayyarka a zucuyarta"mansoor ya tsurawa sameer ido
yace "tayaya?bayan mahaifinta ya tabbatarmun da zai aurawa wancen jakin ita?ai inaga karshe sace
yarinyar nan zanyi"da sauri sameer ya tarbi numfashinsa "karma ka fara"kiran wayar daddynsa ne ya shigo
wayarsa suka kalli juna "daddy"mansoor yace a dan tsorace ganin kiran daddy a wanan lokacin,sameer
yayi kasa da murya yace "ka dauka mana"shiru mansoor yayi haka kawai gabansa ya Shiga faduwa,dakyar
ya danna recieve,

Daddy dake zaune a babban parlor yasa wayar a speaker dukkansu suna parlorn cike da damuwa da takaici
musamman momy wadda kad'a kafa kawai takeyi "Daddy...barka"yace murya ciki ciki take daddy ya
fahimci a buge yake a kausashe yace "mansoor meye ya hadaka da yar masu garin nan?"damm gaban
mansoor ya fadi a karo na farko,suka hada ido da sameer daya zaro ido waje,

"ina magana mansoor kayimun magana nace wacece kake kokarin gurbata musu tarbiyyarta?"still beyi
magana ba nabeeha idonta ya kawo ruwa wato dama akan wata yar kauye yake wulakantata?daddy yace
"tou ka bude kunnenka da kyau ka saurareni Mansoor,idan nina haifeka na rabaka da wanan yarinyar
harabada,sanan kaje kabawa mahaifinta hakuri"mansoor ya Shiga girgixa kai da sauri sameer ya zunguresa
cikin rad'a yace "kace Toh"mansoor ya girgiza kai yace "Daddy i cant,i want to help her nifa ba"dakatar
dashi daddy yayi "iyyeee nace kayi abu kace bazakayi ba ko? tou dik abinda kakeyi jibi jibin nan ka tattaro
ka baro kauyen nan ka dawo gida idan baka dawoba dik hukuncin dana yanke akanka kaika siya"

"naji"mansoor yace be jira me daddy zaice ba kawai ya datse wayarsa,

"kingani?kashe wayarsa yayi bejira me zance ba dan ubansa ya dawo in tara mutane im daura musu aure
da nabeeha subar kasar nan kafin ya daukomin maganar kauyawa"momy tayi kwafa tace "ninasan baa
banza suke dokin zuwa kauyen nan ba shida sameer ashe da abinda suke shukawa to dukkansu aure zasuyi
mu huta shima momynsa dazun take cemun anyi maganar aurensa,ran daddy a bace yabar parlon,
cike da masifa Sameer yace "meyasa kayiwa daddy musu?ba haka naso kayi ba gashi ka bata komi yanzun
ai"murmushin takaici mansoor yayi yace "haka kake gani?ban bata ba ina sane da abinda nakeyi koda nake
shaye shaye,ba mahaukaci bane ni inada hankalina bazan taba masa karya akan abinda nasan bazan iya
ba,bazan taba rabuwa da Dina ba,kuma bazan taba bawa mahaifinta hakuri ba bayan shine ya mareni
wanda inda kotu zan kaisa sai ya Biyani diyyar marin da yayi mun,abinda nasani shine zanyi masa biyayyar
komawa jibi kamar yadda yace amma kafin inbar garin nan i will fix everything daya shafi Dina da cikar
burinta"

"ciki harda karatunta?da hana aurenta da tasiu bayan shine kudirin iyayenta?"Sameer yayi maganar yana
kallons yace "yess ciki harda daina Shaye shaye da zanyi na gaske bana karya ba'tsura masa ido sameer
yayi yana mamakin yadda mansoor ya sauya,

Dina tana shiga bayan gida ta ciro wayarta daga wandonta jikinta na rawa ta rufe kofar ta leka ta jikin ramin
katangar ban dakin taga innahrta na alwala zata shiga daki hakan ya bata damar Ciro wayarta tana adduar
Allah yasa ta iya kiransa,cikin saa ta danno ta kara dannowa taji kara din din......tayi saurin sawa a
kunnenta tana adduar Allah yasa kiran ne,

yana kishingide yaga wayarsa na haske ya kalli wayar "peace of mind"yayi mata saving ya mike ya zauna
yana murmushi sameer yace "yadai?"

"peace of mind ke kirana"cikin rashin fahimta Sameer yace "waye haka?"

"Dina....."ya bashi amsa a takaice,galala sameer yayi yana kallom ikon Allah......

*SLIMZY*😍
07042277401
[12/11, 09:31] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

JAMA'A, INA GABATAR MAKU DA ROYAL EXQUISUTE, GIDAN GYARAN AURE, GIDAN AMINCI, GIDAN GIGITA
MA'AURATA, JAMAA INA AMARE? UWAYEN GIDA? ZAWARAWA? DA KUMA MASU JEGO, INA MATA?
MATAN DA SU KA AMSA SUNAN SU MATA? MATAN DA SUKE SON ZAMA DARAM DAM A ZUKATAN
MAZAJEN SU? MATA ƳAN ƘWALISA? TO WALLAHI ROYAL EXQUISUTE NA KU NE, SUKE DA INGANTATTUN
KAYAN MATA NA GYARA BA WAI TAWULWULBA, BA WAI SHA KA TAFI BA, KAYAN MATA DAKE ƘARA DARAJA
DA ƘIMA WAJEN OGA, GA SAUƘI GA ARHA, GA KUMA AIKI..ROYAL EXQUISUTE ZATA GYARE KU
KI TUNTUBI WANNAN NUMBER 08030644073
Location kano,nationwide delivery
*10*

"Hello.....Dina"yace a sanyaye yana lumshe idonsa,bugun zucuyarsa ne ya sauya jin yadda tayi shiru ta
kasa magana,batasan lokacin da hawaye ya soma zuba daga idanuwanta ba tana sauraren yadda yake
sauke numfashi minti minti,"Dina....ashe kin iya kiran waya"yace cikin zolaya dikda yadda gabansa ke
tsananin faduwa bukatarsa kawai tayi magana,share hawayenta tayi taja majina yace "what kuka kikeyi?
meyasaki kuka?"ya tambayeta cike da kosawa,
"Dole zanyi kuka nasan baa kyauta maka ba ya man...inata tunaninka nasan kayi fushi dani bansan hanyar
da zanbi inzo gareka ba baba yasamun dokoki masu tsauri akanka ni kuma bazan iya jure hakan ba nasaba
dakai dayawa"shiru yayi yana sauraren siririyar muryarta mai zaki,dikda kuka takeyi amma sautin muryarta
kadai ya haifar masa da sukuni da kwanciyar hankali ya lumshe ido ya sake budewa yace"is ok ya isa kibar
kukan banyi fushi dake ba bazan kuma tabayin fushi dake ba kinji?haka bazan taba iya rabuwa dake ba sai
na cika miki burinki,inaso na sauyaki na sauya rayuwarki Dina,hakan yasa nake tunanin yadda zaayi ki fara
karatu dikda nasan mahaifinki ya tsaneni matuka,bansan hanyar da zanbi ba wajen ganin na inganta
rayuwarki kafin na mallakeki"shiru tayi tana saurarensa,hawaye na cigaba da zuba a idanuwanta ta nisa"na
cire rai da samun inganci a rayuwata ya man....domin yanzun haka shirye shiryen aurar dani akeyi ga tasiu
wanda kuka samu matsala,sanan kasani banajin zaka taba mallakata domin bamu dace da juna ba
hasalima ba soyayya mukeyi ba abota ce"..ajiyar zucuya ya sauke yace "mahaifinki ya fada ne kawai yana
barazana amma banajin zai iya mikaki ga wancen mahaukacin yaron jahili wanda besan abinda yakeyi
ba,saboda haka ki kwantar da hankalinki kinji?"ta jinjina kai kamar yana ganinta tace "naji shikenan yanzun
ma boyewa nayi dan in kiraka kar innah ta tanemeni kaji?an hanani zaman daki gudun kada na tafi
wajenka"murmushi yayi yace "karki damu ni zanzo gareki koda zasu tsireni kinji?kinason ganina?"damm
gabanta ya yanke ya fadi tayi shiru ta kasa magana idan tace batason ganinsa tayi masa karya,kuma idan
tace tanason ganinsa yazo kofar gidansu batasan meye zai faru ba hakan yasa batace komi ba yace
"shikenan ba komi zamuyi magana Anjima kinji zansan yadda zanyi na ganki nima jibi zanbar garin
nan"wata irin faduwar gaba ce ta ziyarceta wadda batasan dalili ba nan da nan taji wani jiri na neman
yadda ita, har ya kashe wayar ma bata sani ba dafe kirji tayi tai shiru ta kasa ko motsin kirki dakyar ta tashi
daga kan dutsen datake zaune cikin ban daki ta dauko buta a sanyaye ta fito,

jigum jigum ta sammu innahrta zaune da uwaliya makociyarsu wadda gidansu ke hade tabi Dina da kallo
itama kallonsu takeyi cike da tsoro ta dire butar ta karaso ganin hawaye nabin fuskar innahrta,

"Innah karkicemun nice silar wadanan hawayen dake zuba a idanuwanki Innah meyafaru?mutuwa
akayi?"ta juya ta kalli matar dake zaune gefenta ta rafka tagumi tace "baba uwale lafiya?mutuwa akayi
meyafaru naga innah ta tana kuka"ta zauna dirshan a gaban innahrta tana tambayarta,

dakyar innah ta bude baki tace "burinki ya cika Dina.....burinki ya cika yanzun babarku lubabatu ta aikomin
da sakon cewa tasiu bazai aureki ba dan ana zargin ciwo gareki wadanan yan birnin sun gama dake"wani
abu taji ya caki tsakiyar kanta kamar mashi,gabanta ne ya yanke ya fadi nan da nan ta soma ganin duhu a
gabanta wanda yasata saurin rufe idanuwanta,

"kedai Dina baki kyautawa kanki ba ga abinda kika jawowa kanki nan bacin suna ga iyayenki gareki ke kanki
kaf kauyen nan babu wanda ya kaiki kyau kaf yan matan garin nan samari rububi sukeyi akanki sosai
musamman idan anje dandali yan matan nan babu wadda ta kaiki kasuwa gashinan dik inda ka bulla cikin
garin nan maganarki akeyi hakan ya zama sanadiyyar rabuwar zumuncin innahrki da yar uwarta"Dina kasa
magana tayi tsananin bacin rai da bakin ciki dikda ta gefe daya wata rahma taji ta saukar mata dan babu
yadda zaayi tayi rayuwa da tasiu a matsayin mijin aurenta data aureshi gara ta auri malam salihu mai kasa
kanwa a bakin kasuwa dikda ko wanke baki bayayi amma shi ba dan iska bane,dakyar ta mike batare da
tace komiba ta nufi dakinta da niyyar shiga "ke Dina"sai lokacin innahrta tayi magana a kausashe ta tsaya
"ina zakije?zaki shiga ne ki fita ta jikin bango yadda kika saba?"girgiza kai tayi a raunane tana hawaye tace
"innah babu inda zani kaina ne yakemun ciwo sosai shine nakeso nad'an kwanta ko zai daina"kwafa innah
tayi kawai ta kauda kanta Dina ta shige dakinta ta fada kan yar katifarta tana sauke numfashi wani sabon
kuka ne ya kufce mata wanda batasan dalilinsa ba....
*******
"nabeeha na fada miki ki kwantar da hankalinki idan kinga baayi aurenku da Mansoor ba to numfashi ne
banidashi a doron kasa kuma bazan taba barinsa ya kwaso wata yar kauye ya kawota cikin dangin mu
ba,nina fara zargi ma Allah yasa ba asiri kauyawa sukayi masa ba ganinsa dan birni da mota babu abinda
bazasu iya ba"nabeeha ta share hawayenta tace "momy tunfa daya tafi idan nakirasa bana samunsa tundai
ranan da nakirasa har wajen asuba call waiting kina ganin anya yar kauyen nan ce kuwa suke soyayya da
ita?"momy ta dubi Anty zalli dake ta faman danna waya batace komi ba tace "ke kinki yin magana kodan
saboda mansoor din Dan gidanki ne?tunda kikazo gidan nan ganin kaya bakice komiba kuma kinji abinda
ya aikata"ajiyar zucuya kawai ta sauke tace "me zance?bayan mansoor din be dawoba tukunna?ai kubari
muga isowarsa garin badai gobe bane akace zai dawo?ko jibi?idan ya dawo dik wacce zaayi sai ayi amma
ke nabeeha wanan koke koken da kikeyi ba abinda zai haifar miki sai bacin rai,meyasa ma zaki kuka bayan
dubi nan?"ta nuna gefenta set din akwatuna ne a gefe seto biyu na auren mansoor da nabeeha,ajiyar
zuciya ta sauke ta kwantar da kanta a pillow ta lumshe ido cike da farin ciki can kasan zucuyarta tana
kissima tafiyarsu Cyprus da Mansoor mahaifiyarta ta tabbatar mata da auren mansoor babu makawa dan
akan hakan ta tafi garinsu tunda safe,hangosu takeyi a cikin jirgi ita dashi tasani baya sonta amma da zarar
hakart ta cimma ruwa sai ya manta da wata ya mace a duniya saita maidashi bawanta,sai ya haukace akan
kaunarta ballantana wata yar kauyen banza da zarar ta mallaki man.....ta gama samun duniyarta.....

*******
yana makale da waya daddare suna magana da Dina "kinsan me na gama shirya komi akan sakaki a
makaranta batare da mahaifinki yasan daga wurina bane kingane ko?"ta lumshe idonta tanajin wata
sabuwar kaunarsa na kara shiga cikin jikinta cikin wani irin yanayi tace "idan ka tafi yaushe zaka dawo?"cije
lebensa yayi yace "da inada damar dawowa kauyen nan da zama dana dawo gabaki daya kodan saboda ke
abokiyata Dina"murmushi tayi tace "nidin?har matsayina yakai hakan?"bece komi ba yayi shiru hakan yasa
ta gane yaji haushi tayi yar gyaran murya tace "Afwan nasan kayi fushi amma kasan mene?nasamu kaina
cikin kunci yau din nan, saboda ganin innahta tana kuka da hawayenta saboda fasa aurena da akayi da
tasiu,amma ta wani fannin kuma ina farin ciki da hakan koba komi bazamu rabu ba zamu cigaba da
abotarmu,kasan mene?wallahi da babu wayar nan inaga idan ina kewarla sato hanya zanyi intafi
birni"dariya ya kwashe dashi wadda bemasan ta kwace masa ba ya mike ya zauna "zaki sato hanya kitaho
birni idan kikazo kice wajen waye kikazo?"yayi maganar yana dariya yasa wayar a speaker ganin sameer ya
tsaya da buga karta da yakeyi dukkansu sukasa kunne suji me zatace salati sukaji ta hauyi "meyafaru?lafiya
Dina?meke faruwa?"tace "ina zuwa sautin kukan innah nakeji dama tunda rana nake ganinta kamar batada
lafiya taki fadamun saboda fushi takeyi dani"

"karki kashe wayar ajiye kawai zan ajiye idan kinzo kawai kiyi magana ki fadamun meke faruwa Dan
Allah"yace cike da damuwa,ta dire wayar akan katifarta yana jin karar bude kofarta ta fice,

ya dubi Sameer da yanayinsa ya sauya wanda gaba daya Mansoor ya kasa gane menene damuwarsa ya
tambayesa yaki fada masa saidai yana ganin damuwa a kwayar idonsa "lafiya wai sameer?kanata mun
boye boye kaki fadamun ainihin damuwar ka gabaki daya ka sauya tun dazun ga abincin da muka tura akayi
order nan kakici"sameer ya dauki cup din shayin daya hada kawai ya soma sha mansoor ya tsura masa ido
yana saurarensa bece komiba,

"yaya man....."da sauri ya dauki wayar ya kara a kunnensa ya cireta a speaker"yadai meyafaru"kuka yaji ta
rushe dani , gabansa ne ya shiga faduwa "lafiya?"yace yana saurarenta cikin kuka tace "innah ta ce batada
lafiya ciwom ciki ne yake damunta har suma takeyi na sameta tare da baba dik tayi Amai nashiga uku
banaso na rasa mahaifiyata"a tsorace yace "ganinan zuwa bari nazo mukaita asibiti"

"kada Kazo idan kazo babana zai gane wani abu zansan akwai hanyar da muke magana nida kai,yanzun zan
fita cikin darem nan nemo motar da zata dauki innah mu fita mutafi asibiti"ajiyar zucuya ya sauke yace
"okay nasan mafita "Yana gama magana ya kashe wayar ya diro daga shi sai singlet ya dauki rigarsa ya zura
"ina zakaje a daren nan?"
"waccen golf 3 din motar can nakeso nasa daya daga cikin yaran nan da ke cikin gidan nan suje wucewa ta
inda gidansu Dina yake yadda zaakai mahaifiyarta asibiti"sameer ya mike yace "bazan barka ka fita ba"tare
suka fito cikin saa aka tada motar suka tsaya a wajen gate din gidan har ya karya kwanar hanyar gidansu
Dina,

Dina ba tsunnne a kofar gida tana rizgar kuka mahaifinta na tsaye yana kallon hanya gabas da yamma kudu
da arewa babu kowa sai kukan tsuntsaye,gashi garin yayi bakinkirin da hadari karfe biyu na dare suka
hango hasken mota "Alhamdulillah ga mota nan kila malam dauda ne ya dawo tukin dare"ya Shiga saka
masa hannu,kamar yadda mansoor ya shirya haka ya tsaya mahaifin Dina ya tsaresa da ido kamar ya
ganesa saidai besan a ina bane "baba meyafaru na ganku a nan cikin darem nan?na kawo tumaki ne gidan
mai gari zan dau hanyar birni"ajiyar zucuya baba ya sauke "mara lafiya garemu ka taimakeni mu tafi tare
dakai dan dik garin nan asibiti daya ne kuma kasan yanzun an rufeshi sati guda kenan har suma takeyi"ya
jinjina masa kai ya kashe motar ya fito tare suka Shiga suka fito da innahrt Dina baba ya dauko kudin
dayake shirin maidawa Sameer yasa a aljihu suka dau hanya......
******
washe gari,
"Dina yanzun ya kike gani?wanan kudin dake hannuna bazasuyi ayiwa mahaifiyarki aiki kamar yadda likita
ya fada ba kodarta ce tasamu matsala aiki zaayi mata ai mata dashen koda,sun gwadani akan yadda zaayi a
dauki tawa daya asa mata nima ance bazai yuwu ba gashi bamuda kudin da zamu siyi koda"cikin kuka tace
"baba ni su cire tawa duka indai innahta zata Rayu banida wani buri a wanan duniyat daya wuce ganinku
cikin koshin lafiya,nasani nice silar shigarta cikin wanan halin a ta dalilin bakin cikina ne"baba yasa hannu
yana sharewa Dina hawaye idonsa jajir yace "kaddara ce kawai Dina bake bace fatana tasamu lafiya idan
burinta ki auri tasiu din ne ni zan basu hakuri suxo ayi maganar aure ki aureshi din dikda banason gurbata
rayuwarki hakan yasa na tsani wancen dan shaye shayen,wanan kudin ma so nayi na mayar musu saiga
wanan iftila'in,yanzyn abinda zanyi kawai kauye zan tafi ga wanan ki siyi abinci ku karya insa gidanmu a
kasuwa inyaso sai ayi mata aikin"wasu sababbin hawaye taji suna zubowa daga idanuwanta masu dumi ta
zura masa ido ta kasa magana,

mansoor ne ke jan motar tare da sameer da driver daya kawosu daddare yayi musu jagora har asibitin
daya kawosu yayi parking a harabar asibitin ya dubi sameer yace "bazamu fito ba banaso ya ganmu bazan
lamunci yayi mana tozarci cikin jamaa ba dikda taimaka musu zamuyi amma kasan mutumin kauye da
kafiya"Sameer ya nisa yace "haka ne tabbas amma kamar gashi nan fita zaiyi"ta jikin glass din mota yabi
mahaifin Dina da kallo har ya fita sanan suka firfito,ta mike tsaye tana tunanin yanzun ta ina zata fara?yau
gata a birni amma a sanadin rashin lafiya?"ganinsa tayi tsaye a gabanta ya harde hannuwansa a kirjinsa ya
zuba mata ido fuskarta ta kumbura sosai tayi jajir alamar tasha kuka,

"ya sameer kune?"tayi maganar a sanyaye tana satar kallon mansoor yace "mune"cikin mamaki take
kallonsa yadda akayi yasan asibitin da aka kaisu,ta juya tana hada ido da driver ta gane dama mansoor ne
ya turoshi?a hankali ta sauke ajiyar zucuya a sanyaye ta dubesa tace"nagode"bece komi ba sameer ne yace
"yanzun me ake ciki?"wani miyau mai kauri ta hadiye sanan ta fashe da kuka ta soma yi musu bayani,
dukkansu shiru sukayi cike da tunani,daga bisani Mansoor yace "inaga zanga likitan kawai zan shiga a
gwadani idan k'odata zatayi kawai a cire daya asa mata"zaro ido waje Dina tayi tana kallonsa tana girgiza
kai cikin fargaba da tashin hankali tace "kodarka?zaa cire asawa innah ta?"ya gyada mata kai,

Sameer ya kauda kansa gefe yana wani tunani yace "noo bazaayi haka ba man tayaya zaa cire kodarka asa
ma innahta?bayan ni inada kudin da zan iya Siya mata koda daga naira daya zuwa million dari?"kallonsu
kawai takeyi dan bata fahimci wanam lissafin ba,

daddy ne ya kira layin Mansour ya dauka da sauri "Hello Daddy barka dai"yace yana gyara tsayuwarsa
"ance anga motarku ta shigo gari ina kaje?"ya kalli cikin asibitin sanan yace "ehh nashigo ina dan wani abu
ne zan karaso"
"kazo yanzun yanzun nan"daddy ya katse wayar yace "sameer daddy na kirana i have to go kasan akan
rigimar da muke nasam an fada masa ne so zan barka a nan kayi handling komi"sameer ya gyada masa kai
suka wuce tare da driver,

Dina shiru tayi ta kasa magana,wani irin matsayi mansoir garesa haka da isowarsa keda wuya dik girman
birni ace har anganeshi mahaifinsa yasani?sanan wace irin matsala yake ciki. haka!?shi kuwa sameer tsaye
yayi akanta ta rafka tagumi ya tsura mata ido wanda besan yanayi ba kallonta kawai yakeyi ko kifta ido
bayayi ji tayi a jikinta ana kallonta a hankali ta dago kai taga yadda ya tsareta da ido gabanta ya fadi ta kalli
kanta sanan tace "lafiya?"ajiyar zucuya ya sauke yace "bakomi"ta sunkuyar da kai barinta yayi a wurin
kawai ya shige cikin asibiti wajen likita.......

Page Daya zaku samu yau🫣

*SLIMZY*[13/11, 09:35] 😍Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

*11*

*Assalamu alaikum* ina maiso taga tayi K'IBA jikinta yayi kyau tazama yar lukuta 😘ina maiso taga NONO
yacika yayi kyau ina maiso taga duwawu yafito kinzama cikakkiyar mace ina maza da basacin abinci ina
maza masuso suyi kiba ina yara da basuda kiba ina mai farin cikin sanar daku zumar kiba, zumar kiba
zumace wadda zata saka kiba cikin kwana 7 dayardar Allah zumar kiba zumace mai inganci wadda aka
hadata da magun gunan gargajiya,Bugu da qari har nafdac ta amince da lafiyar zumarmu ta bamu BACH
NO hjy indai kina fama da rama d'an gwada shan zumar mu kisha mamaki indai kasha zuma saika chanza
Maza kinemi mmn khairat domin samun ingantacciyar zumar qiba Mai cike da lafiya with zero side effect🤗
08167453086

Shiru Daddyn Mansoor yayi yana kallonsa ya kasa magana,shi kuwa gogan durkusar da kansa yayi kasa
tunda ya zauna bece masa komiba,momy ce ta shigo da sallamarta dauke da tray na flask da cup da kular
abinci ta dire tana jifan mansoor da wani irin kallo,zata fita yace "dawo ki zauna muyi a gabanki kiji abinda
danki yake fada"gaban momy ne ya fadi ta dawo da baya ta zauna tana fuskantarsa"Alhaji meya fada?
meyace maka?kardai abinda nake zargi ke shirin faruwa"girgiza kai kawai daddy yayi yaja ajiyar zucuya
yace "ya fada miki da bakinsa"yana nuna Mansoor yace "oya fada mata naga kamar sauri kakeyi ko?dan na
fahimci dik maganar da mukeyi hankalinka baa nan yake ba"sai lokacin mansoor ya dago kai suka hada ido
da momy data zura masa ido shi besan meye zai fada musu ba gabaki daya baya cikin hayyacinsa burinsa
be wuce su gama magana ya tafi wajen Dina a asibiti ba ya barota ita kadai dikda yasan sameer na wajenta
amma yasan shima akwai abinda zaiyi a wajen aiki,"kayi mata bayani ga mahaifiyarka na
saurarenka"mansoor ya kara tamke fuskarsa hade da kauda idonsa gefe yace "momy nifa ban taba fada
miki inason nabeeha ba,dan haka banida raayin yin aure yanzun kuma ko inada raayin yin aure bazan
aureta ba dan ba ita bace zabina"wani zabura momy takeyi tace "karya kakeyi mansoor wallahi baka isa ba
karyarka Tasha karya wallahi mu muka haifeka ko kai ka haifemu?yar Aminiyar tawa?tazo gidan nan wata
da watanni zaman jiran lokacin aurenku?amma ka bude baki kace ita ba zabinka bace?sai uban waye zabin
naka eyee?ko yarinyar da kaje kayiwa ubanta rashin kunya akanta zaka aura?yar kauye dangin kazzuwa
zaka auro?",furzar da wata iska yayi daga bakinsa idanuwansa jajir ya kalli agogon hannunsa yace "Daddy
bazan auri nabeeha inbar kasar nan da ita ba da sunan mata,idan maganar shaye shaye kukeyi nabar shaye
shaye"cikin sauri daddy ya dago yana kallonsa cike da mamaki,ya jinjina kai yace "dagaske nakeyi na daina
shaye shaye daddy kamar yadda kaji nafada inhar dan shaye shaye zaayimun aure na daina,nayi mata
alkawarin haka"
"ita wa?"daddy ya tambayesa cike da mamaki ya cije lebe kawai bece komiba ya mike tsaye yana kokarin
fita daddy ya daka mai tsawa "ina zakaje muna magana dakai?kanada wata wadda kakeso shine ka bari
akayi muku baiko da nabeeha?"mansoor ya kada kai yace "Daddy ni bansa ayimun baiko da nabeeha ba
dan haka bazan aureta intafi wata kasa da ita ba, idan dagaske ne maganar kasuwancinka ce kadai zata
kaini zan tafi amma bada aureba idan kuma kuka matsamun akan sai na aureta na tafi da ita tabbas zakuga
ba daidai ba dan bana raayinta"yana gama maganar ya fuzgi labule ya fice cikin sauri cike da bacin rai,

kuka momy ta fashe dashi cikin takaici tace "kana ganin abinda yaron nan yake fada ko?kanajin
maganganun dayakeyi wallahi be isa ya watsamun kasa a ido ba be isa ya shiga tsakanina da Amincun
mahaifiyar nabeeha ba idan an daura mai aure da ita yayi dik abinda zaiyi amma aurensa da nabeeha babu
fashi idan kuma ya dage akan bazai aureta ba to tabbas zai gamu da fushina sanan dik yarinyar daya bullo
da maganar aurenta ko yar gidan uban waye bazai aureta ba bada yawun mu ba"ta fice cike da takaici,
tagumi daddy yayi yana mamakin wanan tashin hankali na hajiya saadatu....
******
yana isa asibitin ya shiga nemanta be sameta ba hankalin mansoor ne ya tashi ya ciro waya daga aljihunsa
to ko ya kirata ne?tou idan kuma ya kirata tana tare da mahaifiyarta fa?idan sukasan tanada wayar salula a
hannunta ansamu matsala wanan wayar ba karamin taimaka masa takeyi ba wajen magana da ita ta
hanyar wanan wayar yake samun natsuwa,

tura kofar doctor yayi da sallama can kasa kasa,yana ganinsa ya ganesa ya fadada murmushinsa yace
"barka da zuwa ranka ya dade"Mansoor ya jinjina masa kai ya nemi kujera ya zauna yace"nazo ne muje
dakin gwaji cikin mintuna goma sha biyar nakeso ka cire k'odata guda daya ka dasawa waccen mara lafiyar
batare da kowa yasan nine na bata ba,inason hakan ya zama sirri a tsakanina dakai likita"galala likita yayi
yana kallon mansoor da yayi maganar babu wasa ko zolaya a cikin lamarinsa shiru yayi ya kasa magana
Mansoor ne dan gidan Alhaji sulaiman Aliyu dan majalisar jiha yazo mikawa wadanan kucakan yan kauyen
koda?"likita magana nakeyi maka inaso kayimun abun nan cikin sauri akwai abinda zani inyi ne"likita ya
sauke ajiyar zuciya yace "Ranka ya dade sameer matawalle Amininnka yanzun yabar asibitin nan yaje don
kawo million sittin din da zaayiwa baiwar Allahn nan aiki har mun tanadi kodar da zaasaka mata yanzun
haka,kudi kawai ake jira"Mansour ya lumshe ido wata kaunar sameer yakeji a cikin zucuyarsa tabbas
sameer Aminine na kwarai yasani ransa ne kawai sameer bazai iya sadaukar masa amma bayaso ya kashe
kudinsa yanaso ya mallakawa mahaifiyar Dina koda ne tsakaninsa da Allah saboda girman kaunar da yakeyi
mata,likita "muje ka cire kodar jikina banaso sameer ya kawo kudin nan ya bannatar da kudinsa"

"yallabai dagaske kakeyi kodarka zaka cire ka mallakawa wad'anan kauyawan?"wani kallo mansoor yayi
masa wanda yasa ya tsuke bakinsa ya mike yace muje,kwankwasa kofar akayi likita ya bude zasu fita sukayi
kicibis da Dina turus tayi ganin mansoor tsaye a bayan likita,kallonta yakeyi cike da tausayawa itama shi
take kallo sosai kayan jikinsa suka burgeta sai yanzun ta fahimci kayan dake jikinsa ta lumshe ido likita ya
wuceta mansoor yace"lafiya na ganki haka meyafaru"girgiza kai tayi idonta ya kawo ruwa tace "dama nazo
fadawa likita innahta ta farka ne amma cikin nata ke ciwo,yanxun haka tanacan tana murkususu"hankalin
mansoor ya kara tashi yace"yanzun zaa shiga da ita bari insamu likita"ya wuceta mamakinsa ne ya kamata
tayaya zaayi mata aiki bayan baaga zuwa babanta da kudi ba?tasa hannu ta share hawayenta,taji mansoor
ya kara shiga ranta bata taba sanin mutumin kirki bane sai da abubuwa ke faruwa dasu illarsa wanan shaye
shayen ga mahaifinta ya tsanesa bataga aibunsa ba.....
bayan awa daya aka fito da innahr Dina daga dakin operation nurses suka gungurota suka kaita daki da
sauri Dina ta tarbesu "innahta innah ki tashi ki farka insha Allahu kin samu lafiya kingama kinji?"tana
maganar tana hawaye tana kuma shafa goshin innahrta cike da tausayawa,da sauri ta fito ta shiga dakin
likita a tunaninta mansoor na ciki likita kadai ta gani a zaune yana rubuce rubuce tace "likita..... yanzun
gashi anyi mata aikin baku jira tukunna an kawo kudin ba babana ya tafi kauye ne ya siyarda gidanmu ko
kudin zaiyi"dariya taso bawa likita tayaya zai siyarda gida a kauye yakai million sittin kudin dashen koda?
wajen zama ya nuna mata,a d'arare ts zauna "ansamu wani bawan Allah wanda yace kada a fadi sunansa
ya bada kodarsa guda daya ansakawa mahaifiyarki"zumbur ta mike ta dafe kirjinta tace "wani bawan
Allah?a ina? wayeshi da zai dauki kyautar koda Rabin rayuwarsa ya bamu? mai muka hada dashi?likita ka
fadamun gaskiya wayene ya bawa innahta kyautar koda kafadamun ko wayeshi sujada ne kadai bazanyi
masa ba likita dan nasan be halarta ba amma daya halarta shi din ma da nayi masa,waye ya sadaukar da
rayuwarsa Dan ganin rayuwata ta inganta?"tana maganar hawaye na zuba a idanuwanta, tausayinta ne ya
kama likita tabbas ya cancanci a fada mata Mansour ne ya bada kodarsa ga mahaifiyarta amma gudun
sanin hali irin na mansoor yasa ya tsuke bakinsa,dakyar taja kafarta ta fito daga dakin likita tayi kicibis da
sameer hannunsa dauke da basket na kayan abinci wasu kuloli ne na alfarma,
ganin tana kuka yasa yace "lafiya?kidaina kuka jikin nata ya matsa ko?nasamu baba a company ne yasa
hannu a bani kudin nazo mu biya"

"ai anyi mata aikin"

"anyi mata?kudin ya rage kenan a biya?"ta girgiza kai tana share hawaye take fada masa abinda likita ya
fada mata,

wata irin faduwar gaba ce ta ziyarci Sameer ya dire basket din dake hannunsa jikinsa na rawa cikin
zucuyatsa cike da furgici yace kardai mansoor ne yasa aka cire masa koda aka dasawa mahaifiyar Dina?.....a
kidime ya dubeta "ina Mansour?yazo asibitin nan?"ta gyada masa kai tace "ehh yazo amma bansan
tafiyarsa ba nima inason ganinsa muyi magana amma ban gansa ba"ajiyar zucuya yayi cikin zucuyarsa yace
tabdijan lallai mansoor cikin mamaki tace "yadai akwai wata matsala ne?"girgiza mata kai kawai yayi yana
jifanta da wani kallo wanda yau ya fara yi mata hakan kuma tsarguwa takeyi,

"ya tafi bangansa ba Dan Allah ka kiramun shi ya dawo ina bukatarsa"ta marairaice murya yana kallon
soyayyar mansoor karara da damuwa dashi a cikin kwayar idonta,gudun kada ta fahimci wani abu yasa ya
fadada murmushinsa yace "Dina na fahimci kin kamu dayawa ko?"batasan lokacin data jinjina masa kai
ba,sanan ta rufe fuskarta da tafin hannunta tana dariya suka jera zuwa dakin da innahrta take....

*******
Babu wanda yasan shigowarsa gida Yana shiga sashensa ya haye sama sai zaheed dake buga game a
parlor yaga wucewarsa,
momy ta fito daga kitchen tana waya tana fadin "look zaliha ke kadaice zaki iya tankwara Mansour yaji
maganarki ya auri yarinyar nan nabeeha idan baiji da lalama ba ta dole zan aura masa ita ko yaki koya so ya
fita gidan yanzun haka ina zargin akwai abinda yake shiryawa "zaheed ne ya rugo yace"momy naga ya
mansoor ya shigo ya hau sama "
"tou kinji ma kamar yazo ya haye sama bari in tura nabeeha ta kai masa abun karyawa dan banajin sun
karya suka baro kauyen akwai abinda suke shiryawa zan nemi sameer nasan zai sanar mun da koma
menene kinsan mansoor ko kashe mutum yayi Sameer zai sani,kuma mamakina ma yadda wai ya iya furta
indan shaye shayene ya daina ta hanasa"cikin kwantar da hankali kanwarta ta soma magana"ki kwantar da
hankalinki Dan Allah Insha Allahu komi zaizo da sauki idan kuma ya dage akan bazai aureta ba idan yanada
kudurin auren wata kubarsa ya aura kawai inyaso ya hadasu su biyu "shiru momy tayi tana tunanin
shawarar kanwarta dakyar suka karasa maganar ta kashe wayar ta shiga dakinsu nabeeha "jeki kaiwa
yayanku breakfast ni bansan shigowarsa gidan bama"nabeeha ta mike cikin sauri jikinta har rawa yakeyi
tace "tou momy Bari na shirya masa na kai"tausayinta ya kama momy ita kuwa nabeeha dama ta samu ta
bude drawer ta ciro siririn gyale ta fito da maganin da ummahnta ta bata akan tasa masa da yaci magana
ta kare ta makale tana kallom yadda rufaida ke zuba murmushi har takai kofa tace "Amarya yar
shagali"cike da zolaya tayi maganat "mai kike nufi? nifa kin rainani koda nake saarki dai yayanki zan
aura"dariya ce ta kusa kwacewa rufaida dam tasan zaa kwashi artabu da yaya man,

yana makale da waya a kunnensa a kishingide hannunsa rike da iPhone 14 dinsa yana kallon hotonta yace
"common wai ba nace miki zan dawo ba?meyasa kike magana kamar bazaki sake ganina ba"tsaye nabeeha
tayi tana kallon yadda yake zuba murmushi murya can kasa yake magana,tanaso tasan dawa yake maganat
ta kara kasa kunnenta ta dire tray din ta zauna gefen gado cike da kissa tace "ga abinci nan momy tace a
kawo maka"wani kallo yayi mata wanda yasa ta mike tana kallonsa da idanuwanta da suka canja kala suka
rine cike da kishi take kallonsa kirjinta na harbawa burinta da fatanta ta zama surukat dan majalisar jiha ta
zamo daya daga cikin manyan mata na garin,

"fita"shine abinda yace ganin ta tsaresa da ido kamar zata cinyesa,ya yunkura a hankali yana lullube da
bargo bayaso taga inda akayi masa aiki,ganin haka yasa ta fice cikin zucuyatta tace "kanacin abincin nan ka
gama yawo".....

saukowa yayi ya bude flask din farfesun kayan ciki ne,ya hude dayan fankasau ne daya soyu sosai, favourite
dinsa ne saidai bazai iyaci ba sakamakom likita yace kada yaci komi sai abu mai ruwa,da badan ya matsa
bama sai ya zauna a asibiti na wani lokaci zaa sallamesa,suna waya da Dina yaga kiran sameer na shigowa
ya kalla,bazai iya ajiye wayarta ba dik yadda yake cikin damuwar preasure din momy muryarta kadai ta
haifar masa da natsuwa,haka suka cigaba da waya da Dina ganin mahaifinta na shigowa asibitin sukayi
sallama ya kashe,

tunanin mafita kawai mansoor yakeyi,tabbas yasan dole zaijewa Daddy wanan harkar ta
kasuwancinsa,amma bazai taba amincewa akan ya auri nabeeha ba tunani yakeyi nan da nan yasamu
mafita sawa zaiyi a canja masa visa kawai yayi tafiyarsa, idan ya dawo yasan zuwa lokacin maganar
nabeeha ta kwanta lokacin ne zai fuskanci mahaifin Dina da nasa kudirin,ko be aureta ba babban kudirinsa
shine tayi karatu ya wayar da ita kafin nan ya kara tabbatarwa da kansa soyayyarta dan har yanzun be
Amince da maganar cewar sonta yakeyi dagaske ba.....

****"""
"amma sameer meyasa zakace a dakata da maganar turawa gidansu khairatu?bayan nayi magana da
ummahnta da mahaifinka mungama shirya komi so nakeyi a hada aurenka dana abokinka rana daya"

"momy mansoor bazaiyi aure yanzun ba dan bashida wadda yakeso,yanzun haka momynsa kirana tayi
akan na lallashesa ya Amince da auren nabeeha amma yaki,na kira wayarsa yana waya yaki picking call
dina ni bama akan maganar nabeeha nake nemansa ba akan wata magana ne amma samm yaki daukar
wayata"momy tayi shiru ta sauke ajiyar zucuya tace "tou shikenan yanzun kaje gidan nasu ka samesa ka
lallabasa ayi abun nan tare da naka"sameer ya jibjina! kai ya mike kenan tawagar gidan yayan mahaifinsa
suka shigo ciki harda khairatu wadda ta biyosu murmushi yayi mata itama tayi masa ya kashe mata ido
alamun zai fita ta turo baki yana dariya ummah matar uncle dinsa tace "dama kin biyomu ne dan kigansa?"
"ehh fa momy gaba daya ta zauce akan maganar yaya sameer fa kawai daga ta kirasa yace mata yaje asibiti
shine ta rude"shidai ficewa yayi momy tace "asibiti kuma?ah ah badai asibiti ba kamfani dai yaje wajen
daddynsa, maganar ma mukeyi yanzun kuka shigo"khairatu ta zauna ta sunkuyar da kanta kasa wani irin
shaukin son sameer takeji a cikin zucuyarta burinta data samesa su kadaice tasamu ta rungumesa ta saba
dashi dayawa ga wutar shaawarsa dake ruruwa a zucuyatta bata taba tunanin sameer zai aureta dagaske
ba bayan yasanta a waje......

******
"look sameer ka fahimceni ka boyemun wanan sirrin banaso Dina tasan ninaba mahaifiyarta koda kodan
mahaifinta kar yayi tunanin dan neman sulhu dashi nakeyin hakan ko kadan nayi ne saboda kaunar da Dina
takeyimun na saba da ita sosai ban fada mata komi akan barina kasar nan ba yanzun haka na canja Visa
batare da sanin daddy ba sau nakeyi sai gobe kawai in kama hanya,na tabbatar idan nadawo komi ya lafa
lokacin zansan menake ciki lokacin zan karanci zucuyata dagaskene ina sonta? dikda na shaku da ita
sosai"sameer zura masa ido yayi kawai yana kallonsa ya kasa magana "kana nufin tafiya zakai bazaka auri
nabeeha ba?kuma kake tunanin idan ka dawo zasu barka ka mallaki Dina? mahaifinta zai Amince
dakai?"mansoir yayi murmushi yace "wai kai waye yace maka aure zamuyi da Dina?"Sameer yayi
murmushi kawai ya cije lebensa ya sauya hirar "zanyi kewarka sosai wallahi ji nakeyi kamar na bika mutafi"

"idan muntafi khairatu fa? ta angwance dawa?kayi hakuri Aminina dalili yasa zan tafi dan tserewa
hukuncin momy naso ace dani zaayi aurenka"sameer yayi murmushi bece komiba kawai ya cigaba da wasa
da makullin motarsa.....

******
washe gari,

"yaya man yanzun ina zaka tafi kabarni?"Dina tayi maganar muryarta na rawa tana kallonsa ta bayan inda
ake ajiye motoci cikin asibiti yace "karki damu dik inda natafi zucuyata na makale dake karfa ki manta kece
peace of mind"ta turo baki gaba tace "kai kasan wani wanan abun ni bazan ma iya fada ba"

"ina nufin natsuwar raina"yace ta kallesa tace "dagaske?yanzun idan katafi yaushe zaka dawo?"ya lumshe
idonsa bazai fada mata inda zaije ba gudun kada tayi masa rigima yace "jibi zan dawo kinji?"ta jinjina masa
kai ta harde hannuwanta a kirjinra,bugun zucuyarta ne ya sauya ta tsura masa ido cike da shauki da
kaunarsa tace "haka kawai nakejin tsoro"cije lebensa yayi yace "tsoron me?"

"kada in rasaka?"

"Dina wanan tafiyar da zanyi itace zata zama silar da bazaki rasa ni ba zamana kuwa zai haifar da
matsala,yauwa ya kukayi da baba?" nan da nan fuskarta ta sauya cikin wani irin yanayi tace "baba ya kasa
yadda da cewar wani ne nadaban yaba innah kyautar koda gani yakeyi kaine ka biya akasa mata"lumshe
ido yayi cikin zucuyarsa yace "nasan zaayi hakan,idan yasani komi na iya faruwa"a zahiri kawai bece komi
ba tanaso tayi wata magana ta kasa kawai suka danyi hira sukayi sallama dakyar ya lallasheta ya baro
asibitin......

"yanzun mansoor tafiya zakayi batare da ka cika burin mahaifiyarka ba?ka zabi ka bakanta mana rai?dama
abinda ka shirya kenan?"Mansoor bece komiba ya sunkuyar da kai nabeeha kuwa koka sosai take rizga cike
da takaicinsa,

"shikenan ka shirya katafi aikin idan kadawo zuwa lokacin ka shirya sai ayi"momy tayi maganar a
sanyaye,murmushin nasara yayi yace "kafin nadawo kun huce dana dawo zan sauya muku tunani kafin nan
na raba nabeeha da gidan nan "sameer na tsaye sukayi sallama dasu momy ya ja akwatin mansoor suka
nufi mota dukkansu suka firfito harabar gidan suna daga masa hannu sameer yasa akwati a boot din
mota,ya Shiga mansoor yaja excort suka shiga tasu motar suka take musu baya zuwa Airport.......

Page daya kullum Insha Allah....

*SLIMZY*😍
07042277401
[14/11, 08:41] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33
*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

*Masu Bukatar A tallata musu hajarsu ku nemeni ta 07042277401*

*12*

Slm ina maiso taga tayi K'IBA jikinta yayi kyau tazama yar lukuta 😘ina maiso taga NONO yacika yayi kyau ina
maiso taga duwawu yafito kinzama cikakkiyar mace ina maza da basacin abinci ina maza masuso suyi kiba
ina yara da basuda kiba ina mai farin cikin sanar daku zumar kiba, zumar kiba zumace wadda zata saka kiba
cikin kwana 7 dayardar Allah zumar kiba zumace mai inganci wadda aka hadata da magun gunan
gargajiya,Bugu da qari har nafdac ta amince da lafiyar zumarmu ta bamu BACH NO hjy indai kina fama da
rama d'an gwada shan zumar mu kisha mamaki indai kasha zuma saika chanza Maza kinemi mmn khairat
domin samun ingantacciyar zumar qiba Mai cike da lafiya with zero side effect🤗 08167453086

Mansoor kallon sameer yakeyi gabaki daya yanayinsa ya canja daga shekaran jiya zuwa yau ya rasa
menene matsalarsa kamar akwai abinda yake boye masa,sameer ajiyar zuciya ya sauke yace "am gonna
miss you friend "mansoor ya jinjina kai "nasani kaima kasan zanyi kewarka sosai na zabi tafiyar nan ne a
wanan lokacin yadda dana dawo zan san matakin da zan dauka wajen ganin na ingata rayuwar
Dina"sameer ya dafa kafadarsa "haka kayi nisa akan soyayyar Dina?lallai kayi zurfi man a tsananin kaunarta
tunda ka dauki Rabin rayuwarka ka mika musu dikda irin tsanar da mahaifinta yayi maka"mansoor
murmushi yayi yace "well i dont care da tsanar da yayimun tunda nasan na kafa soyayyata da kulawata a
cikim zucuyarta ai shikenan,babban farin cikina be wuce yadda wancen dan kauyen ya janye daga maganar
aurenta ba komi zaizo mun da sauki nayi mata alkawura kala kala a daren jiya muna waya da ita wanda
dana dawo zam cika mata shi kota wani hali"sameer tsura masa ido yayi kawai yana gyad'a kai yace "good
luck inaso naje nasamu daddy a company yana jirana sanan akwai maganar da nakeso muyi dashi mai
muhimmanci"rungume juna sukayi mansoor na bubbuga bayan sameer cikin sigar lallashi ya rada masa a
kunne "i can see you are already missing me"sukayi sallama sameer ya juya ya shiga motarsa mansoor na
daga masa hannu har ya bar cikin Airport din,

a reception mansoor ya zauna kusa da wata budurwa wadda tun shigowarsa ta ganesa shi be ganeta ba
hakan ya bata damar kawar da kanta gefe guda bugun zucuyatta ne ya tsananta ta lumshe ido cikin
zucuyarta tace "tarko na ya d'anu a daidai tare zamu tagi cyprus dakai mamsoor bazaka taba barina kasha
a banza ba sainasan yadda nayi nashiga rayuwarka ka koma shaye shaye wanda inada labarin sanadin
daina shaye shayenka wata yar kauye ce,kafin ka dawo ka mance da ita"wayarsa ya ciro daga aljihunsa ya
shiga hoton Dina ya fito dashi wanda yayi mata da kayan fulani bakin nan yasha jan baki jajir kamar zai
d'igo yayi murmushi ya shafa fuskarta a screen din wayar yace"bansan yadda zanyiba da rashinki peace of
mind banso wanan tafiyat tazo a wanan lokacin da nake tsaka da bukatarki ba"tunanin kiranta yakeyi a
wanan lokacin yasan likita ya sanat masa da an sallamesu tunda safe to ko suna gida?tambayar da yayiwa
kansa kenan ya kwantar da kansa a jikin kujerar da yake zaune ya lumshe idonsa,

"Dina lafiyanki?tun dawowar mu daga Asibitin nan nake ganinki kamar bakida lafiya"cikin taushin murya
innahrta ke tambayarta tana daga kwance,

tsaki kakarta baba kulu tayi tace "lafiyanta kalau mana akwai abinda ke damunta banda ya wuce tunanin
yan birnin can?nifa nafara zargin wani abu akan wanan yarinyar dan hatsabibiya ce ban yarda cewar wani
bane ya baku kyautar kodat da aka sa muku kila wadanan yan birnin ne sun samu abinda sukeso suka biya
muku kudin aikin"innah cikin rashin fahimta tace "kamar yaya sun samu abinda sukeso?"

"ya wuce sun gama lalata da ita?"innah ta dafe kai taji takaicin wanan kalmar data fito daga bakin baba
kulu da badan mahaifiyarta bace da babu abinda zai rabasu yau sai Allah, innah ranta ya bacu ta juya ta
kalli Dina wadda ta rafka tagumi batasan ma me sukeyi ba hankalinta baya kansu,hamdala tayi da Dina
batajiba tasan zataui bakin ciki kuma bazata kyale baba kulu ba,

vibration wayar Dina ta somayi ta zabura da sauri innah tace "ke lafiya?"wani miyau ta hadiya jikinta na
rawa tace "kamar cinnaka ne ya cijeni innah Bari in duba ta fada dakinta ra bugo kofa da sauri jikinta na
rawa ta ciro wayarta,

"yaya man...."tace a sanyaye cikin siririyar murya data daki zucuyatsa yaci wani sanyi a cikin ransa
yacev"ashe zan sameki nadauka kina tare dasu innah inata tunani gashi inaso naji muryarki kafin na shiga
cikin jirgi"

"jirgi?"tace tana dafe kirji cike da mamaki ya jinjina kai yana dariya kamar tana ganinsa yace"ehh wanda
kike gani a sama din nan?"ta kwashe da dariya tace "haba kai zanso in ganni cikin jirgi zani Makka"dariya
sosai ya hauyi maganarta cike da wawta yace "ke ba dik wanda zai aureki zaisha fama da wawtarki da
dramer"ta lumshe ido ta turo baki tace "ba kai zaka aureni ba"wata faduwar gaba yaji be taba tunanin
Dina zata fada masa wanan maganar ba ,shiru yayi batare da yayi magana ba tace "yi hakuri tunda ka fasa
auren nawa"tayi maganar muryarta na rawa kamar zatayi kuka,jin haka yasashi sarkewa yace "sorry Dina
zan aureki nina isa ince bazan aurekiba?"ta share hawayenta tace "ya man bazan iya auren wani ba idan ba
kaiba,kaga idan mukayi aure sai mu cigaba da abotarmu babu mai rabamu ko?"murmushi yayi fararen
hakoransa suka fito ya fahimci maganarta bataso tayi aure su rabu su daina abota hakan yasa ta yanke
hukuncin aurensa badan tasan meye aure ke nufi ba,

sanarwa aka somayiwa matafiya masu shiga cikin jirgi,ya cije lebensa yacev"Zan shiga cikin jirgi Dina ki
zama kusa da wayarki koda yaushe yin waya dake shine zai samun kwarin gwiwar yin dik abinda zanyi har
nadawo gareki sanan karki Bari kowa yasan kinada waya kinji?idan banjiki ba komi zai iya faruwa dani"ya
kashe wayar ,ya mike yaja akwatinsa,

bin wayar tayi da kallo haka kawai jikinta yayi sanyi ta kasa koda kwakkwaran motsi ta lumshe idonta tace
"ina sonka yaya man....."mari taji an sauke mata,da sauri ta bude idonta suka hada ido da mahaifinta dake
tsaye akanta Yana kallon wayarta,gabaki daya sandarewa Dina tayi tai mutuwar zaune cikin tsananin tashin
hankali da rudewa ta cillar da wayar gefe ta tarwatse a wajen baba yace "sannu Dina.....lallai wuyanki yayi
kwari Dina kuma yaron nan ya cuceni ya cuci rayuwata wato har wayar salula ya siya miki?"ta girgiza kai
bakinta na rawa a kidime tace "bashi bane ba yaya man bane "ya kara sauke mata mari yace "idan har kika
Kara cemun bashi bane saina fasa miki baki "innah ce ta mike ta lallabo ta shiga dakin ta samesu,

"lafiya malam? yaushe ka shigo?"

"nashigo tun dazun nazi da cefane ta bayan gida na biyo kawai nakejin magana ta cikin dakin Dina gabaki
daya na tsorata yasa na dauke kafata dan insan meke faruwa a dakin nata ko barayi ne kwatsam ina
shigowa na bude kofar batasaniba tayi nisa wajen yin wayar salula"

"wayar salula?"innah ta dafe kirji tace "waye yabaki wayar salula Dina?"

baba ya karbe "wancen Dan iskan yaron mashayi mana?har tana fada masa shi zata aura dan su cigaba da
Abotarsu?dan tasan idan ta auri wani bazasuyi abota ba?tou ko zaki mutu bazaki auresa ba bari kiji koda
tasiu ya fasa aurenki ina muawiyya wanda yake sonki da aure gobe goben nan idan an sauko masallacin
jumaa zaa daura aurenki dashi"ya duka ya dauki wayar ya hada ya zura a aljihunsa ya fita cike da takaici
sabuwar tsanar mansoor ce ta kara darsuwa a cikin zucuyarsa,

"Dina baki kyautawa kanki ba ga abinda kika jawowa kanki nan ai"ta juya ta barta nan durkushe dafe da
kumatunta hawaye na zuba a idanuwanta ta dora hannunta akai tace "shikenan nashiga uku dik wani
mafarkina da nakeyi na ganin yaya man ya zama nawa ya kare kenan?shikenan bazanyi karatu ba haka zan
kare rayuwata?"ta fad'a kan katifarta hawaye masu zafi ne suka soma zubowa daga idanuwanta nan da
nan idanuwanta suka rufe wani irin zazzabi ne mai zafi ya lullubeta ta soma rawar sanyi tunsnin yadda
zaayi tayi magana da mansoor takeyi gashi bata haddace number wayarsa ba,tayaya zatayi taga sameer ta
sanar masa da halin da take ciki?bazata taba iya zama cikin kauyen nan batare da yaya man ba,ya zatayi da
kaunarsa data daskare a cikin zucuyatta tayi Mata riga da wando da mayafi?jikinta ne ya soma
karkarwa,aure?ita da wani a cikin kauyen nan bazata bari ta auri kowa ba idan haka ne gara ta gudu ta
mutu data auri wani ba Mansoor ba idan tayi aure bayanan taci Amanarsa.....

******
suna zaune da daddy da sameer a dining bayan sun dawo daga company suna cim abinci daddy ya dubi
sameer yace"kace akwai maganar da kakeso kayi dani naga akwai magana a bakinka amma ka kasa
fadamun kanada wani wanda ya fini ne sameer?"ajiye cokali sameer yayi gabansa na tsananin faduwa
dikda yasam dik abinda yakeso a duniya Shi mahaifinsa yakeyi da mahaifiyarsa kasantuwar shine dansu
daya tilo yasa kome yakeso sukeyi masa,shiru yayi ya kasa magana,

momynsa ce ta fito sanye da wani jan material mai flowers golden an mata dinkin doguwar riga ya karbi
jikinta sosai yasha ason stones sai walkiya takeyi tace "yadai naganku haka Sameer? lafiya kanada damuwa
ne?"shiru yayi ya kasa magana momy tace "kodai kaida khairatu ne kuka samu matsala?yanzun nan suka
bar gidan nan da ummahnku hajara ai kagansu lokacin da zaka fita ko?meyafaru?akwa damuwa ne?"

gyada kai yayi daddy ya ruko hannunsa cikin sigar lallashi yace "nasan damuwarka bata wuce Amininka
daya bar kasar ba ko?nasan da kasan da tafiyar nan tare zakuyi visa kutafi amma idan kaga bazaka iya
zamaba ka shirya zan kira waya yanzun insa ayi maka visa ka bishi"sameer yaja ajiyar zucuya ya girgiza kai
yace "daddy kayi hakuri aure nakeso nayi gobe goben nan"momy tace "aure?gobe goben nan kuma? shine
dik ka Shiga damuwa wanan ai Mai sauki ne saina kira ummahn khairatu na sanar mata da su shirya komi
gobe in ankai sadaki sai a daura kawai"girgiza kai yayi yace "momy ba khairatu zan aura ba akwai wadda
zucuyata keson na aura bansamu damar hakan ba sai yanzun"zaro ido tayi cike da mamaki take kallonsa
daddynsa ma kallonsa yakeyi "ehh daddy dama nasamu wanda idan har baku taimakamun na mallaketa ba
zaku rasani"da sauri momy ta rukosa yana kokarin tashi daga kujerar dayake zaune "mu rasaka kuma?
meyayi zafi da zamu rasaka sameer?ai zaka iya hadasu duka ka aura tunda Allah ya hore mana dukiyat yin
hakan kuma hakan bazai taba zumuncin mu ba "girgixa kai yayi yace "aurenta nakeso nayi badan
soyayyarta tayi karfi a zuciyata ba saidai kawai in mallaketa inkawota gidana,ku taimakamun inyi hakan
idan har bansameta ba tou tabbas zan rasata"Ajiyar zucuya daddy ya sauke yace "yat wacece a garin nan a
ina suke?waye mahaifinta?"

"a kauye suke"dafe kirji momy tayi tace "kauye?dama abinda ke kaiku kauye kenan kaida mansoor?biri yayi
kama da mutum shima mahaifiyarsa ta shedamun yaki amincewa da auren nabeeha ne saboda yanada
wadda yakeso a kauye "gaban sameer ya fadi Allah yasa mansoor be fada musu cewar yana son Dina ba
dan shine yake sonta bashi ba,

"tunda yar kauye ka zabi kwasowa ai shikenan bazamu hanaka ba dan mu bama kyamar talakawa zan kira
mahaifiyar khairatu in sanar da ita"sameer cikim sauri yace "ah ah momy kibari a nemomin auren Dina
goben tukunna idan an dauro auren sai ki sanar musu"gabaki daya momy kallom sameer takeyi yanayinsa
ya sauya kamar wanda zaiyi auren rashin gaskiya?bata sake cewa komiba ta mike ta barsu nan zaune da
daddynsa,
"zan kira alhaji sulaiman Aliyu mahaifin Mansoor mu hadu goben da wuri mukama hanyar kauyen "gumi
ne ya karyowa sameer bayaso daddyn Mansoor yaje wajen karbo masa aure idan yasani Mansoor zaiji
kuma bayaso yasan komi harabada,dabara ce ta fado masa yaja daddy da hira......

*******

karfe sha daya na dare cyprus....

mansoor zaune akan carpet ya hada shayi Yana sanye da kayan baccinsa yana rike da remote yana canja
tasha aka buga masa kofar daki,shiru yayi waye zai buga masa a wanan lokacin?ko maaikatan hotel ne?
shiru yayi yace "yess come in"a hankali aka turo kofar,wacce ya ganine yasa ya mike a rude yana kallonta
cikin wani irin yanayi "fatima Dan maliki,waye ya kawoki kasar nan?"

"ohh really you are asking?okay akwai course din danazo ne daga nigeria tare muka shigo jirgi nidakai ai"ta
karaso tana sanye da wata riga iya gwiwarta mara hannu ta dame mata jiki tare da waiter suke yana dauke
da tray na kayan shaye shaye datasa aka sako musu,ya dire ya fice,

"meye wanan!"yace cikin tsawa yana kallonta "na kawo ne muyi hira mud'aj taba"ya kalli kwalaban,gabaki
daya favourite dinsa ne ya ja numfashi ya sauke take Dina ta fado masa a rai dik yadda yakeso yasha
wadanan abubuwan bazai iya sha ba idan ya tuno da alkawarin da yayi mata na daina shaye shaye idan
yasha tamkar yaci amanarta ne,teemah dan maliki ta shiga budewa a hankali tana gantsaro nonuwanta da
auka cika suka batse cikin riga,bata ankara ba kawai ya kwashi wayoyinsa taga ya fice daga dakin ya bugo
mata kofar,tsaki tayi tace "zaka dawo bazamubar garin nan ba saida danka dik yadda zanyi insamu cikinka
saina samu"ta karbi daya daga cikin kwalaben ta lumshe ido,

wani waje ya samu ya zauna a harabar hotel din turawa ne kowa ke shaaninsa kamar ba dare ba ya Shiga
kololuwar tashin hankali kiran Dina da yakeyi bata shiga,ya kira wayarta yakai sau goma ge sameta
ba,hankalinsa ya tashi yanzun yasan dare ne sosai a nigeria daya kira sergent na gidan gonarsu dik yadda
zaayi ya hadasa da Dina yayi ,saidai bazai yuwuba saida safe,

hada kansa yayi da table din dake gabansa cikin damuwar rashin jin muryarta yake yanaso ya fada mata
shima ita yakeso ya aura karta bari ta yarda a hadata da kowa har ya dawo kasar,

sameer ne ya fado masa a rai cikin sauri ya mike yw zauna idanuwansa sun kara kankacewa tsananin
damuwa ya shiga kiransa,

yana kwance beyi bacci ba suna video call da khairatu wayarsa ta shigo hamdala yayi dan dama ya gaji da
maganar da ita,bayaso ta fahimci wani abu yasa yace zai dau wayar mansoor sanin wayeshi yasa bata
damuba kawai ta katse ya dauka,

"ya sam.....bakayi bacci ba?inata adduar Allah yasa bakayi bacci ba sam"sameer ya gyara zama yace "yeah
banyiba muna waya da khairatu ya akayi ya ka sauka?"

"lafiya ba lafiya ba,banasamun wayar Dina"gaban sameer ya fadi yayi shiru,bece komiba "ya zaayi kaje
kauye gobe ka dubomin ita?"sameer ya runtse idonsa cikin zucuyarsa yace "zani kauye Mansoor.....amma
zani ne in mallaki Dina"a fili yace "anything for you zanje goben zan dubota"

"da safe please"Mansoor yayi maganar cikeda damuwa,sameer yace "okay zanje ka kwantar da hankalinka
karfe sha daya ma inacan"farin ciki ne ya lullube mansoor najin sameer zai je ya hadasa da Dina hakan yasa
ya samu natsuwa ya mike ya nufi masaukinsa.......
*Wata sabuwa inji d'an caca🧐haba sameer matawalle*

*SLIMZY*😍
[15/11, 08:51] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

*Mai Bukatar a tallata masa hajarsa ya tuntubeni ta 07042277401*

*13*

Slm ina maiso taga tayi K'IBA jikinta yayi kyau tazama yar lukuta 😘ina maiso taga NONO yacika yayi kyau ina
maiso taga duwawu yafito kinzama cikakkiyar mace ina maza da basacin abinci ina maza masuso suyi kiba
ina yara da basuda kiba ina mai farin cikin sanar daku zumar kiba, zumar kiba zumace wadda zata saka kiba
cikin kwana 7 dayardar Allah zumar kiba zumace mai inganci wadda aka hadata da magun gunan
gargajiya,Bugu da qari har nafdac ta amince da lafiyar zumarmu ta bamu BACH NO hjy indai kina fama da
rama d'an gwada shan zumar mu kisha mamaki indai kasha zuma saika chanza Maza kinemi mmn khairat
domin samun ingantacciyar zumar qiba Mai cike da lafiya with zero side effect🤗 08167453086

"Dina idan bakida lafiya ne ki fad'a dubi yadda kika fita hayyacinki kamar wadda tayi ciwon wata da
watanni indai akan mahaifinki zai aurar dakene kinsan babu fashi kamar yadda ya fad'a"innahr Dina ta juya
ta kalli babanta dake Alwala fuskarsa babu walwala ya gyada kai yace "gara in aurar da ita tunda abu har ya
kaiga dan shaye shaye ya dauki wayar salula ya bata batare da munsaniba?mai suke aikatawa da wayar?
kafin ya karasa lalatata gara in mikawa wanda nayiwa alkawari dan yau da safe mun hadu a wajen sallahr
asuba na kuma tabbatar masa da daurin aure ita dashi babu fashi"wasu hawayene masu d'umi suke
zubowa daga idon Dina gabanta ne ya yanke ya fadi tayaya zata fara rayuwa da wani ba mansoor ba?yaya
abotarsu zata kasance idan ya dawo daga kasar waje yazo kauye ya tarar an aurar da ita?tasani mai kayan
miya bazai taba bari ta cigaba da abota dasu ba bayan dama kowa a kauyen ya tsanesu,kuka sosai ta fashe
dashi ta mike ta nufi daki tana ganin wani irin jiri,

"Assalamu Alaikum,Baban Dina wai ana sallama dakai a waje wasu mutane a motoci guda biyar
sukazo"yaron yayi magana cike da farin ciki,kallon juna mahaifina Dina yayi da innahrta dake tsaye rike da
buta,tace "motoci kuma?su waye zasuzo wajenka a mota a wanan lokacin ana gab da sakkowa
masallaci?"girgiza kai yayi yace "nima abun ya bani tsoro amma bari naje na samesu inji meke tafe
dasu?"dafe kirji innah tayi cike da furgici ta soma kiran Dina daga inda take tsaye,

Dina na kwance tana kallon sama idanuwanta a lumshe hawaye kebi ta gefen fuskarta gabanta ne ya
tsananta faduwa,tayi wani juyi ta gefe daya ta bude idonta, idanuwanta ne suka sauka akan sim card din
dake cikin wayarta,wani zabura tayi da sauri jikinta na rawa wata irin yunwa takeji jikinta har rawa yakeyi
saidai bata da kuzari da karfin da zata iya cin abinci a halin yanzun babu abinda take bukata samada
magana da mansoor ko Sameer wanda dukkansu batasan yadda zaayi ta samesu ba ta dauki sim card din
tana jujjuyawa cike da ko kwanto ta lumshe ido "menene wanan?"ta furta a fili muryarta na rawa tanajin
yadda numfashinta yake sarkewa tsananin yunwar da takeji tabbas yanada amfani a cikin wayarta yake,ya
zaayi tasan me akeyi dashi?take tayi shiru tana tunani shafiu ne ya fado mata mai kunna solar a kauyen
taga yawanci masu salula suna zuwa wajensa bazai rasa sani ba,mikewa tayi dikda irin jirin da take gani be
hanata zura hijab dinta ba ta kama window ta haye dan tasan baba da innah bazasu taba barinta ta fita ta
kofa ba,ta dire ta nufi wurin shafiu mai shagon salula.....

"Innahr Dina wadanan mutanen kina ganin in Amince da bukatarsu?wanan yaron ne Sameer dan gidan
matawalle yake sonta na birni ashe sameer yaron matawalle ne kuma shine mutumin da yake gina
masallatai a cikin kauyen nan yake taimako ake yawan maganarsa,saidai ina tsoron in mallaka masa Dina
yazo gadar zare yayimun bashi zai aureta ba dan iskan nan ne abokinsa dan shaye shaye"Innahr Dina rik'e
habarta tayi tai shiru cike da rudani da tashin hankali ta kasa magana Dina ce zatayi aure a birni gidan
matawalle?tambayar da tayiwa kanta kenan Baban Dina ya katse mata tunani "ke inata magana kin kasa
magana shawara nake nema kema kinada hakki akan yarki Dina kina ganin yadda ake zagin mu a gari akan
Dina dan shaye shaye ya lalatata babu mai aurenta hatta d'an yar uwarki cewa yayi ya fasa kina ganin
mubar yarinyar nan taki auruwa?inajin tsoron abu biyu innahr Dina,kar yaron nan ne ya turo aurenta da
fuskar sameer"innah ta nisa tace "ina ganin bazasuyi hakan ba tunda ai da iyayensu akazo ko?ni ina ganin
kawai na Amince matukar ka yadda da ingancin iyayen shi sameer din koba komi shi ba irin Abokinsa bane
kace"baba ya sauke ajiyar zucuya yace zanyi magana da sameer din kafin ayi komi ina zuwa "ya fice innahr
Dina ta bishi da kallo,

Sameer na jingine jikin mota sanye da farar shadda kansa babu hula hannunsa rike da waya a kunnensa
Mansoor ne,cikin damuwa mansoor yace"sameer narasa meyasa zuciyata take rawa,tunanina yake
tsayawa cak ba,hankalina ya gaza kwanciya tun daren jiya,dana kwanta bacci sai mafarke mafarken Dina
nakeyi, please me kake boyemun kacemun da sassafe zakaje kauyen nan ka dubomin ita kaga wani hali
take ciki amma na kiraka sau biyu a na uku ka dauki wayata,karka boyemun komi wani hali Dina take
ciki?"Yana maganar ne muryar mansoor tana rawa gabaki daya sautin muryarsa yasa jikin Sameer yin sanyi
kalamansa sun karyar masa da zuciya saidai bayajin zai fasa kudirinsa na auren Dina,dikda irin son da
yakeyiwa Aminin nasa yasan yadda mansoor ya damu da Dina sosai amma yasan Dina bata dace da
mansoor ba dashi ta dace dikda kasancewarsa amininsa,lumshe idonsa yayi ya bude ya nisa yace "calm
down man ina kauyen yanzun haka maganar da mukeyi dakai nasa a bincikomin Dina din ne kasan
mahaifinta bayason muamalarku da ita so banaso kowa yasan nazo balle a fada masa anganmu da
ita"ajiyar zucuya Mansoor ya sauke a sanyaye yace "it's okay don't hide anything for me idan kun hadu da
ita kaji?na nemi wayarta tun jiya shiru nasan mahaifinta zai iya kwance wayarta saboda ni idan har ya
kamata dashi please ka kirani ka hadani da ita idan babu waya a hannunta kuma ka siya mata wata Dan
Allah baxan iya abinda najeyi ba sam idan har banji muryar Dina ba kasani she's my peace of mind"sameer
ya lumshe idonsa bugun zucuyarsa ne ya tsananta ganin mahaifin Dina a kusa yasa ya katse wayar ba tare
da yace komiba,yaja gauron numfashi ya sauke cikin zuciyarsa yace "sorry friend.....Dina ta koma tawa"ya
durkusa ya gaida baban Dina sanan ya mike suna fuskantar juna,baba yace "Sameer inajin tsoro kada
kuyimun angulu da kan zabo"

"Baba ban fahimceka ba kafadamun mai maganarka take nufi "yayi maganar yana sosa keya,shiru mahaifin
Dina yayi sanan yace "tou ina tunanin kar Mansoor ya turo ka ka aurar masa Dina tunda yasan nace bazan
bashi ita ba"sameer yayi murmushi ya girgiza kai yace "ko daya baba nine kawai nakeda muradin
hakan,inaso na cika maka burinka na cika burin Dina wajen inganta rayuwarta da karatu kamar yadda
kakeso"baban Dina farin ciki ne ya lullubesa ya gyada kai yace "na baka Dina"ya juya kawai wajen mahaifin
sameer sukai magana suka kama hanyar masallacin garin dan gudanar da sallahr jumaa da daura auren
Dina da sameer.....

Dina tagumi ta rafka cikin tashin hankaki tace "kace kanata kiran wayarsa yana shiga amma yana waya
ko?"ya jinjina mata kai yace "ehh waya yaketayi be dauka ba daga baya ma yanzun wayar bata shiga
Dina,amma kibar layin a wurina idan ya kira zan sanar masa da kece kikeson magana dahi inyaso sai kizo ko
anjima daddarene kuyi Magana "Dina tayi shiru cikin faduwar gaba ta kasa magana, tayaya zatazo bayan
yau mahaifinta yayi alkawarin aurar da ita ga mai kayan miya idan ya kira lokacin kuma lokaci ya kure fa?ta
juyo ta marairaice murya tace "idan ya kira kasamu yaro kawai yazo gidan mu ya fadamun zan fito kota
wani hali muyi magana"ya jinjina mata kai yace "Dina kenan yar innah"yana dariya ta wuce zucuyarta
cunkushe da tsananin takaici,

mansoor ya tasa takadda a gabansa gefensa wasu turawa ne da suke tattaunawa gabaki daya hankakinsa
baya jikinsa dik maganar da sukeyi masa ya dafe kansa,meyasa Sameer ya sauya masa?ya kasa fada masa
gaskiyar meke faruwa?tou kodai beje kauyen bane yayi masa karya?girgiza kai yayi yace "kai sameer bazai
mun karya ba"ya dauki wayarsa ya dubi daya daga cikinsu yace "excuse"furkarsa ya daure idanuwansa jajir
ya koma can gefe ya tsaya ya bude wayarsa misscalls goma ya gani,nan da nan bugun zucuyarsa ya sauya
yana danna wayar dan ganin waye jikinsa na rawa yana gani jikinsa ya soma rawa kamar mazari yace
"Dina....why meyasa sai yanzun kike kirana?kin wahalarmun da zucuyata? Insta tunanin halin da kike
ciki"ya gyada kai yayi murmushi yace "nasan kila sun hadu da Sameer ne"yana murmushi yaja ajiyar
zucuya yayi dialing,bugu daya aka dauka gabansa ne ya yanke ya fadi jin muryar namiji yayi shiru ya kasa
magana wani jiri ne yake neman daukarsa,ya dake yayi gyaran murya yace. cike da isa da izza yace "ba mai
wayar wayarta"shafiu yace "ai mai layin dai nine mai wayar Dina ce"bakinsa har rawa yakeyi yace "ina
take?ina wayar tata?kace mai layin?"shafiu yace "ehh layi ta kawomin tace nasa mata kuyi magana munata
kiranka kuma baka dauka ba shine ta tafi gida"ji yayi kamar ya caka masa wuka a kahon zucuya,nan da nan
idanuwansa ke neman rufewa da duhu ,a sanyaye yace "ya zaayi inyi magana da ita?ka taimakeni zan baka
dubu dari ka hadani da ita Dan Allah"

"tayaya zaka ganni kabani dubu dari malam banason karya ban taba rike dubu goma bama ballantana
dubu dari" Mansoor yace "look zan baka wallahi zansa har inda kake a kawo maka matukar zaka hadani da
Dina muyi magana"shafiu ya washe baki yace "Angama zan aika yanzun a kirata"ya kashe wayat wata ajiyar
zucuya mansoor yayi sai lokacin ya samu sassaucin yadda yakejin faduwar gaba wanda besan dalilin hakan
ba....

********
khairatu na kwance ta kifa cikinta wasu hawaye masu d'umi kebi ta gefen idanuwanta yayinda kanta ke
wani irin sara mata wanda ya haddasawa idanuwanta yin nauyi ta kasa budesu saidai hannunta daya na
rike da wayarta wadda taketa trying number sameer tun safe bata samu,turo kofar dakin akayi da karfi
wanda ya haddasa mata tsananin tashin hankali da furgicin da take ciki mai tsanani ta bude idonta tana
kallon ummahnta wadda ta harde hannuwanta a kirjinta tana kallonta cike da damuwa da tashin
hankaki,ganin yanayin ummah yasa khairatu saurin mikewa ta zauna tana kokarin saita natsuwarta cike da
tsoron kar ummah taga lokacin da mai gadi ya kawo mata abun awon ciki,

"Khairatu kardai abinda aka sanar mun a waya ne kema kikaji ya haddasa miki wanan tashim
hankalin?"damm gaban khairatu ya yanke ya fadi cikin zucuyarta tace dik girman tashin hankalin da kike
ciki be kai wanda zakiji daga gareniba ummah idan har kikasan ina dauke da cikin sameer matawalle
wanda ake gab da yi mana baiko dashi,

"kinyimun shiru bakice komi ba khairatu,ko bazakice wani abuba nasam wata damuwar tana haddasawa
harshe kasa motsi ballantana ya furta abinda ke cikin zucuya,nasan kinada labarin wai sameer sunje an
daura masa aure yanzun nan da wata?"damm gaban khairatu ya yanke ya fadi wanan kalmar ce ta haddasa
mata wani irin mummunan hankali wanda yasa zucuyarta ta tsaya cak yayinda numfashinta yake kai komo
daga kirjinta zuwa cikinta wanda hakan ya haddasa mata wani irin gumi da ya soma karyo mata,

bakinta na rawa ta soma magana "ummah dagaske sameer aure yayi?ya auri wata ne ya dawo ya aureni ko
kuma ya aureta ne ni ya watsar da tawa soyayyar"hawaye ya soma zubowa daga cikin idanuwanta kamar
am bude famfo,
"yanzun nakira hajiya zinariyar matawalle(mahaifiyar Sameer)nake tambayarta akan maganar zuwan nasu
dikda abun dik na gida ne amma ya kamata na sanarwa da kannen mahaifinki shine take sanar mun akam
muyi hakuri dama zatazo akan wata magana,na nemi ta sanar mun abinda yake faruwa shine take
fadamun yanzun haka sun tafi nema masa auren wata yarinya daga can aka daura auren zasu taho da ita
ma"dafe kirji khairatu tayi ta koma da baya ta fadi jagwab akam gado cikin mummunan tashin hankali
tayaya zata fuskanci iyayenta da nasa ta sanar musu da cewar tana dauke da juna biyu na sameer?wanda
shine ya bukacu ta boye soyayyarsu kada su sani sai ya nemi aurenta? tayaya zasu yarda da hakan?"

zama ummah tayi gefen gado ta dafa kafadarta cike da takaici tace "nasan ciwon abinda kikeji khairatu
akan sameer,nadade da sanin kina sonsa dan nasan hakan a kwayar idonki dik zuwan da yakeyi gidan nan
kika boyemun dikda be furta yana sonki ba amma ke kina sonsa,dan haka ki kwantar da hankalinki dik
wata hanya da zanbi sainabi wajen ganin kin shiga gidan daular matawalle kota wani hali kuwa"khairatu ta
kalli mahaifiyarta da jajayen idonta ta gyada mata kai kawai ita kadai tasan masifar da take ciki,ummah ta
mike tace "yanzun zan shirya zan nufi gidan su kafin nan gidan Antynku zan fara zuwa sanan muje gidan
wajen tarbar amarya Inga wace kalar amarya ce wadda tafi tawa yar? Asali kyau koko dangantaka?"kuka
kawai khairatu takeyi cikin tashim hankali ta koma ta kwanta wani zazzabi ne mai zafi ya lullubeta
idanuwanta sukai mata nauyi......

********
Gidansu Dina cike yake da jamaa ganin komi takeyi kamar a mafarki yadda gari ya dauka Dina tayi aure a
birni tana jingine da bangon dakin mahaifiyarta ta lunshe idanuwanta,ko mansoor ya kira shafiu mai shago
oho?cikin tsananin mamaki ta kara duban mahaifiyarta tacev"innah nakasa yadda akan cewa aure zanyi
kuma a birni dikda kunki sanar mun da wanda zan aura mai hakan yake nufi?"dafa kafadarta innahrta tayi
tana murmushi "zakiso wanda zaki aura Dina nasani tunda dama kuna son junanku"lumshe ido Dina tayi ta
bude tace "innah munason juna kuma?waye haka wanda muke som juna yazo da maganar aurena lokaci
daya?"tana kallon innahrta cike da rudani zucuyarta na wani irin bugawa tou kodai Mansoor dinta ne ya
turo a aura masa ita kafin ya dawo daga kasar waje?tou idan mansoor ne mahaifinta zai amince da auransa
bayan yana ikirarin cewar mashayi ne?irin tsanar da mahaifinta yayiwa mansoor batajin zai Amince da
aurensa lokaci daya,

shiru Dina tayi gabanta na tsananin faduwa innah ta dubi kanwarta baba lubabatu da baba kulu tace "muje
daga waje mu tattauna wadanda zasu raka Dina din tunda sunce tarw da ita zasu tafi basa bukatar komi"

baba kulu ta tabe baki tace "kundai siyar da yarku kawai a birni hankalinku ya kwanta shiyasa kuka kulla
abinda taki auren tasiu niban yarda cewa yau ne akazo da batun auren Dina ba wallahi koma menene zai
kare muku keda mijin naki"innah murmushi kawai tayi ta fita,

yaro ne ya tsaya daga bakin kofar dakin babu kowa sunata hayaniya a tsakar gida yace "Dina shafiu ne ya
aikoni wai wanda kika kira waya ya kira"wani zabura Dina tayi ta mike jikinta na rawa tace "ya baka wayar
ka kawomin ne?"ya girgixa mata kai yace "ah ah yace wai kizo kuyi magana yanzun yana jiranki yamma tayi
zai rufe shago tun dazun yake aikowa a kiraki baa sameki ba"ta gyada masa kai cikin tashin hankali tanason
jin muryar yaya man tanaso zucuyarta ta samu natsuwa tanaso taji shin shine ya aiko da maganar aurenta
batare da mahaifinta yasam shi bane?tayaya zataje tayi magana dashi?gashi an daura mata aure,tana
tsananin kewarsa sosai dikda jikinta ya bata shine mijin tasani sunyi alkawarin auren juna kodan su cigaba
da abotarsu gashi Allah ya amsa,tayaya zataje suyi magana?lumshe ido tayi tace "ko banje ba nasan zanyi
magana dakai muna isa birni aka kaini dakinka,kila ma dama yana gari yace baya nan dan yayi mata bazata
ya aureta ne"dariya ta somayi tana hawayen farin ciki lokaci daya,gud'a taji an rangada gidan ya kara cika
mahaifinta ne ya bude labulen ya shigo yace "taso Dina"gabanta ne ya fadi a karo na farko tumda akace an
daura aurenta bata shiga tashin hankali irin yanzun ba tasan tafiya zatayi tabbas zata rabu da iyayenta da
innahrta da take tsananin so,rungume innahrta tayi ta kankameta tana wani irin kuka mai ban tausayi,
Sameer na tsaye a jikin kofar gidansu yana kallonsu tausayinta ya kamasa ta wani bangaren kuma ya tsinci
kansa cikin tsananin faduwar gaba shin yaya Dina zata amshesa a matsayin mijinta na aure idan tasan
shine ba mansoor ba?bude idonta tayi suka hada ido da sameer take ta tsaresa da wani irin kallo mai cike
da tambayoyi,saidai ya boye hakan a cikin xucuyarta idanuwanta ne suka nuna masa hakan,tabbas tunda
taga sameer tasan aiken mansoor ne tasani yaya man dinta ne ya turo sameer ya lallashi mahaifinta ya
aura masa ita, farin ciki ne ya lullube dina wanda yasata rufe Ido cikin dukunkunannen hijab dinta shi kuwa
kiran waya ne ya shigo da sauri ya duba man ne.....wata ajiyar zucuya ya sauke ya koma wajen motoci
driver ne ya bude masa ya shiga gidan baya ya zauna,

sameer cikin sarkakkiyar murya yace "yane man mutanen Cyprus ya ake ciki ya kunsamu magana da Dina
kuwa?"tsaki mansoor yayi cike da damuwa yace "tayaya bayan na nemi abu a karo na farko a wajenka
bakayimun ba?haba sameer ka taimakeni dazun da muke waya da kai Dina ta kirani ashe mahaifinta ne ya
karbe wayar luckily takaiwa wani layin ya kirani bansaniba saida tabar wajen nakira,yanzun inata fama
dashi ya hadamu abu ya gagara"kwantar da kansa sameer yayi a jikin seat din mota yace "ka kwantar da
hankalinka kayi aikin da daddy ya turaka man ka raba hankalinka biyu yarinyar da kacemun ba sonta kakeyi
ba meyasa barinka kasar zaka shiga damuwa rashin jin motsinta?"

"sameer ina son Dina so mai tsanani ko ka manta manufarmu?ta ina dawowa zam aureta?look Dina itace
rayuwata sameer ina dawowa ko ana ha maza ha mata i most marry her,nadaina shaye shaye saboda Dina
ban taba tunanin zan iya daina shan wani abuba akanta sameer,kaima kaki hadani da itane saboda kana
bayansu momy?tou kasani bazan sake kiranka ba"yana gama maganar ya katse wayar,

sameer ya lumshe ido yace "am sorry Aminina.....bazan iya hadaka da Dina ba dan tazama mallakina
yanzun" motar da yake ciki aka shigar da Dina,mahaifin sameer kuwa cikin farim ciki yake rabawa jamaar
kauyen kudi wanda hakan yasa labarin auren Dina ya zagaye kauyen da kewaye.....Dina kuwa minti minti
take sauke ajiyar zuciya tanajin radadin rashin iyayenta saidai babban burinta da sun isa ta hada idonta da
angonta mansoor......

*ku cigaba da bina wanan tafiyar mai zafi ce.....*

*SLIMZY*
✍🏻
*07042277401*
[16/11, 09:32] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

*14*

ADADE ANAYI SAI GASKIYA 💯✅💯


Ina masu Neman data Mai 'karko Mai da'dewa? Ki Da'de kina amfani da abarki cikin kwanciyar hankali
Kuma cikin farashi Mai sauki da rahusa ? Toh Maza ku garzaya kada abarku abaya AHZUK DATA services &
all ONLINE payments
MTN ><><
🛜500mb = #150
🛜1GB = #250
🛜 2GB =#500
🛜 3GB =#750
🛜 4GB = #1000
🛜 5GB = #1300
🛜 10GB =#2600
To check balance ♎ dail for MTN (CG)= #460*260#
MTN(SME)=*461*4# OR *323*3#
MTN(Direct &Datacard)= *323*4#

AIRTEL ><><
🛜500MB =#150
🛜1GB =#280
🛜2GB =#600
TO check balance ♎ dail AIRTEL (CG& Direct)=*140#

GLO ><><
🛜500MB =#150
🛜1GB =#280
🛜2GB =#560
🛜3GB =#900
🛜5GB =#1500
To check balance ♎ dail GLO(CG& Direct)=*127*0#

9MOBLIE ><><
🛜500MB =#140
🛜1GB =#250
🛜2GB =#500
🛜3GB =#750
To check balance ♎ dail 9MOBLIE (CG&Direct)== *228#

UNIVERSAL CODE (FOR ALL NETWORK)==*323# OR *323*4#


ALL DATA SERVICES VALID 30 DAYZ
PAYMENT DETAILS BELOW 👇👇👇
223878120 UBA Muhammad sabo Ahmad
8068616274 Palmpay
Muhammad sabo Ahmad
EVIDENCE 🧾 VIA 08035182984
07015399345

Parlorn gidan matawalle cike yake da jamaa wanda cikin awanni sukaji labarin auren Sameer da wata
sabanin khairatu,momy ce ta fito sanye da qani tsadadden lace maroon mai ado baki baki da golden
wuyanta sanye da dankarariyar sarkar zinarw wadda ta kwanta ta karawa adonta kyau,ummahn khairatu
ce ta dago ido cikin jamaar dake zazzaune a parlorn tacev"Tabarakalla kaga uwar Ango"tayi maganar
muryarta na shakewa,wadda ke gefenta tayi saurin dagowa tayi kasa da kai wadda matace wajen yayar
matawalle hajiya Rumasa'u suna kiranta Momy rumah tacev"keko harda yaba kwalliyar uwar Ango kuda
akayiwa dan waken zagaye?ai harda son ganin kalar matar da sameer ya auro ya kawoni gidan nan dama
daga nan tafiya zanyi gidanki mu tattauna"ummahn khairatu cije lebenta tayi tace "Hajiya zinariya wanan
alkyabbar ta hannunki fa?"momy ta kalli alkyabbar dake walkiya a hannunta golden da amy green tacev"ta
tarbar sirikarku ce dan kinga auren babu shiri kingane tou dazun na aika aka karbomin wanan alkyabbar
aka siyoya naira million daya kenan"wani kululun bakin ciki ne ya tsayawa ummahn khairatu tana bin
alkyabbar da kallo cike da tsananin takaici tace cikin zucuyarta zamuga kalar yarinyar da zaasawa alkyabbar
million daya,alkyabbar nan zatayi matukar yiwa khairatu kyau sosai dole zan rama kota wani hali"horn din
motoci ne ya karade kunnuwansu nan take dukkansu suka mummuke tsaye momy kuwa faraa kawai takeyi
hamida da khadija yaran Momy Rumah sukace "laaa gasunan ankawo amaryar yaya Sameer bari mutashi
muyi tarba muga kalarta ita kuma "momy murmushin yak'e takeyi dan tasan dij tsammanin matan dake
cike da parlorn nan yar wata hamshakin mai kudi sameer ya auro basusan daga kauye zaa kawota ba,nan
da nan gida ya rud'e aka soma rangad'a guda ta ko ina suka firfito harabar gidan ummahn khairatu suna
hada ido da sameer kallon da ta tarbesa dashi yasa gabansa ya fadi take khairatu ta fad'o masa a rai wata
irin faduwar gaba da baisan dalilin ta ba ta ziyarcesa ya cije lebe, cikin zuciyarsa tunanin yadda akayi momy
ta sanar musu aurensa yau yakeyi,wayarsa ce ta soma ruri cikin sauri ya zarota daga cikin aljihu a
tunaninsa mansoor ne dikda yasan yayi fushi dashi akan be hadasa da Dina ba sai yaga khairatu ce,tsurawa
wayar ido yayi yana kallo ya dago ya kalli ummahnta data kafesa da kallo cike da tuhuma,

Baba kulu,da innah lubabatu ne suka fito daga cikin mota,wani ja da baya Baba kulu tayi a rude ta koma
gefe tana bin harabar gidan da suka iso da kallo cike da tsoro,innah lubabatu ta matso tana satar kallon
jamaar dake harabar gidan sanan tace "Baba kulu ya naga kinyi baya da sauri kema kinji irin tsoron da naji
ko? kinga inda aka aiyar da Dina ko? wanan wani irin gida ne mai shegen kyau haka? kalli wata rumfa can
gefe mota a karkashin rumfa?"baba kulu ta daga kai ta kalli dalleliyar motar ta juyo tace "Allah dai ya fitar
damu daga gidan nan lafiya kwana zanyi ina zikiri da salati"katse musu magana sukaji anyi, ummahn
khairatu ce cike da kissa Tana satar kallon kafar innah lubabatu wadda tasha lallen gargajiya bayan yayi ja
yayi bakinkirin har saman diddigenta wata blue din atamfa ce a jikinta wadda tayi fari tasss tsabar kodewa
tace "barkanku da zuwa sannu ku da zuwa"washe baki baba kulu tayi jajayen hakoranta ne da suka dafe da
goro suka bayyana tace "yauwa yar nan"ummahn khairatu tayi musu iso,sameer yana gefe ya harde
hannuwansa a kirjinsa kusa da Dina dake tsaye wacce gabanta ya tsananta faduwa taji an ruko hannunta
"Amarya ni bari na tarboki"da sauri hamida ta karaso "Barka da zuwa Amaryar yaya sameer barka da zuwa
iyalin Gidan matawalle"dammm gabanta ya yanke ya fadi kadafuwanta taji suna neman kasa daukarta
sunan waye taji an kira a matsayin mijinta?sameer fa taji ance ba yaya man ba?wani irin fitsari taji yana
neman kufce mata,ta kasa motsa kafarta saida ummah ta sake magana tace "muje mana Amaryar
danmu"momy ce ta karaso cike da faraa rike da alkyabba a hannunta "ke ummahn yara inata jira ki karbi
alkyabba daga hannuna sai kiyi shiru?"ummah ta tabe baki tana bin jan hijab din dake jikin Dina da kallo
wanda yasha dinki ta gefensa da saman kanta babban burinta shine Dina ta bude fuskarta suga kalarta,cike
da takaici ta karbi alkyabbar tasa mata dik yadda taso a shiga da Dina batare da alkyabba ba hakan be
yuwu ba?dan tsaki taja wanda ita kadai taji sai Dina datake rike da ita suka taka cikin gidan babban parlorn
gidan aka sakata a tsakiya,

momy rumah kuwa baki bude take kallon yadda innah lubabatu da baba kulu suke kallon cikin parlorn
waddda basuma san ana kallonsu ba, momy rumah tace "zinariya yanzun wadanan mutanen sune
surukanku a garin nan?wadanan mutanen su sameer ya zabi ya auro mana mata wajensu?"momyn
Sameer ranta yadan baci tace "mai sukayi mutanen Rumah?su din ba mutane bane ko dabbobi ne su din
da kike wanan maganar?"ummahn khairatu ta zunguri momy rumah alamar tayi shiru hakan yasa tayi shiru
momy ta kwalawa masu aiki kira ta basu umarni da akai abinci da ruwan sha da lemo dayan sashen da
sameer zasu zauna dan acan zaa saukesu hakan kuwa akayi,

Hamida ce ta wuce mutane tazo gaban Dina taja hijab dinta,take fuskarta ta bayyana,fara ce soll da ita mai
manyan idanuwa farare tass dikda kukan da tayi besa idanuwanta sun canja kala ba suna nan kamar
madara,da yalwar gashin gira gazar gazar kasantuwar tanada masifar gashi,bakinta sanye da jan janbaki
kamar zaiyi magana ga katon digon india da akayi mata a goshinta wanda da zasu fito innah lubabatu tayi
mata wanan kwalliyar,wata dariya hamida ta kwashe da ita tacev"yanzun wanan itace Amaryar yaya
sameer"tsawa Momy ta daka mata Wanda take parlorn yayi shiru wanda da surutu kakeji kasa kasa tace
"karki wulakantamun suruka kinji nafada miki ko?wani irin iskanci ne wanan wai?ohh dama kunzo kutaru
ne dan munafunci?"khadija kuwa dake zaune a dining tana fuskantar Dina ta kashe mata hoto take ta
turawa khairatu,

Ran Dina ya baci sosai wani sabon kuka ne taji yana neman kwace mata hakan yasa ta runtse idonta cike
da tsananin takaici babban burinta be wuce ta ganta a daki suyi magana da Sameer ba shin dagaske shine
mijin daya aureta ba mansoor Amininsa ba?shin ko bashida labarin mansoor shine muradin zucuyarta?tou
kodai Mansoor din ne ya turosa dan ya aureta kafin ya dawo daga tafiyar da yayi?zucuyarta cunkushe take
da tambayoyi wanda sameer ne kadai zai amsa mata su,babban damuwarta da burinta ya kasance
mafarkinta ya zama gaskiya cewar yaya man ne mijinta ba sameer ba......

*******
Bayan sallarh ishai bayan kowa ya watse sameer ne ya shigo sashen gidan bangaren momynsa babu
kowa ya tsaya jimm a parlorn yana daddana waya yana matukar kewar Mansoor sosai yayi fushi dashi
saboda yaki hadasa da Dina ya kamata ya kirasa ya lallashesa,dan hadasa da Dina a waya yasan cewar ya
aureta babbar matsala ne yana tsananin son mansoor so mai tsanani hakan yasa dik yadda yaso kyale Dina
ya kasa dikda bayajin soyayyarta nada karfi ko wani tasiri a zucuyarsa haka kawai yakeson kasancewa da
ita,zama yayi yana kallon Tv amma gabaki daya hankalinsa na wajen mansoor,,

Mansoor kuwa ya shigo dakinsa kenan daga wani babban shagon Hoto na kasar cyprus dauke da manyan
hotuna wanda ya tura musu akayi masa manyan enlargement na hotunan Dina,wanda rashin jin muryarta
ya haifar masa da tsananin damuwa da rashin ganinta idan yana ganin hotunanta zai rage masa radadin
rashin ji daga gareta,zama yayi ya kunna side lamp hasken dakin ya sauya ya koma blue ya tsurawa hoton
Dina ido ko kiftawa bayayi,yanajin yadda wayarsa kw ringing sarai yasan daga nigeria ake kiransa ko waye
bazai dauka ba,yayi tagumi "Dina......ko wani hali kike ciki yanzun oho?nakasa daina faduwar gaba yau din
nan,zucuyata tayi rauni nakasa daina tunaninki,babban fatana ya kasance kina cikin koshin lafiya"ya
lumshe ido yana jin wayarsa na cigaba da ringing,dakyar ya bude idanuwansa da suka sauya kala sukayi
jajir ya zabura tunowa da yayi ko shafiu ne na kauyensu Dina,zai hadasa da ita?ya karasa ganin mai kiran
yasa yayi dan guntun tsaki kadan sanan ya dauka cike da isa da izza mansoor yace "waye ya Baka iko da
damar kirana sam.....?inace burinka shine kaga son Dina ya kasheni ko?"gyara zama sameer yayi yadda
Mansoor yayi maganar yasa jikinsa ya soma rawa yace"look tayaya zanso ka mutu?meyasa sonta zai
kasheka?rashin Dina sai sonta yayi ajalinka?mansoor kamar bakai ba gabaki daya ka canja"mansoor ya
sauke ajiyar zuciya yace,

"she changed me.....Dina ce ta kawomin sauyi a cikin rayuwata sam.....ina mai tabbatar maka idan kana
tamtama akan yadda nake jinta a zucuyata tabbas ka daina domin rashinta zai iyasani na rasa komi ciki
kuwa harda numfashina"sameer yaji mansoor kamar ya caka masa mashi a kirji,haka mansoor ke tsananin
son Dina da bukatarta?ya ja gauron numfashi ya cije lebensa yacev"Be a man mana mansoor wallahi gaba
daya ka koma kamar wani sauna"murmushi kawai mansoor yayi ya hadiyi wani miyau mai daci yace"ka
shirya hadani da ita gobe ko inbar aikin da nakeyi indawo naganta batare da kowa yasani ba sanan in
koma?"gaban sameer ya yanke ya fadi bakinsa na rawa yace"no no....man karka dawo daddy zaiyi fushi
dakai i promise zan hadaka da ita goben"besan sanda yayi maganar ba dan bayason Mansoor ya dawo a
tsakanin nan yasan Dina tayi aure kuma shine ya aureta idan ya dawo komi zai iya lalacewa yafiso sai Dina
ta mance da Mansoor sanan zai dawo dik yadda zaiyi ya boyeta da ganin mansoir zaiyi har yasamu damar
mantar da ita Shi,

momy ce ta fito daga kitchen rike da gorar ruwa a hannunta ta tsaya cak ganin sameer zaune a parlor yana
waya tace "ah ah sameer kaine?kaida waye kake waya a wanan lokacin?ina kabar amaryar?"

"momy nida mansoor ne"momy ta karaso ta fuzge wayar ta kara a kunnenta ta soma magana "Mansoor
yanzun kunyi amaryar ma bazakuyi hankali ba?ko be sanar maka da cewar anje neman aure an dauro mai
aure daga nan ba?"da sauri ya karbi wayar hannun momy yana fadin "ina ya barni in sanar masa momy
bayan yana nan yana yimun rigimarsa ta daban?kai an daura mun aure yau fa,"mansoor yayi wani ihu cike
da farin ciki yace "great katayani da addua nima dana dawo su momy su yarjemun auren Dina"wani miyau
mai kauri Sameer ya hadiye yace "see momy na tsaye ta kasa ta tsare sai naje dakin Amarya muyi magana
gobe"ya katse wayar momy ta dubesa tace"kun fiye sakarci shima ya dawo muji a wani kauyen zai dauko
mana in kuma ya amince sa nabeeha to"Sameer yayi murmushi yace "momy zani dakina in kwanta"..
"ka isa?ai baka isa ba sole kaje sashenka ina kallonka daga nan,"tana maganar tana kallon kofar da zata
sadaka da matakalar da zaka hau sama bangaren Dina,yace "kamar ya momy"

"Dakin Dina zakaje bazata kwana ita kadai ba,iyayen nata nasa an kaisu guest house din dake kusa damu
gobe da sassafe zasu shirya sutafi bayan sun karya nasan yanzun tana can tsuru ka taimaka mata tayi
wanka ta rage kayan jikinta,wancen akwatunan set biyu zaa kai sashenta bayan kwana biyu sai a karo mata
wasu ta cire kayan jikinta"gaban sameer ke tsananin faduwa ya jinjina mata kai bayaso momy ta fahimci
damuwa a fuskarsa tayaya zai sanarwa da Dina shine mijinta na gaskiya? momy ta tsaresa da ido,dakyar
yaja kafarsa yace "saida safe"tana tsaye tana kallonsa yana haye matakala kamar Wanda kwai ya fashewa a
ciki ta girgiza kai tace "shashasha"ya haye sama,

ya dade tsaye a kofar dakin yanajin sautin shasshekar kukanta wanda yasashi tsananin faduwar gaba,a
hankali ya murda kofar dakin ya bude da sauri ta zabura ta zauna tana kallonsa tana bin dakin da kallo
Wanda ko ina hotunansa ne a manne a bangon sashen parlor da dakunan,kallon tuhuma takeyi masa
wanda hakan ya haifar masa da mummunar faduwar gaba,saidai kasantuwar yasanta da wawta da rashin
wayau yasa ya saita natsuwarsa dan karta gane rudanin da yake ciki,"yaya Sameer"ta kira sunansa a
sanyaye ya washe baki kamar yadda ya saba mata yace "naaaammmmm Dina yar innahrta"gabansa na
tsananin faduwa,cikin wasa yayi mata maganar yaga sabanin haka,

"ina yaya man?dagaske kaine mijin dana aura ba yaya Mansoor ba?karka cemun dagaske haka ne,Dan
Allah idan wasa kukemun ka shigo dashi ina tsananin bukatar son ganinsa inaso nayi magana da
abokina,nasan bazai taba sabamun alkawarin da mukayi na zamuyi aure dan mu cigaba da abota ba "rassss
rasssss gaban sameer ke faduwa ya kalli yadda ta tsaresa da manyan idanuwanta wadda suka kashe masa
jiki,take taga fuskarsa ta sauya ya canja daga sameer din da tasani zuwa wani na daban,zaiyi magana tex ya
shigo wayarsa,

da sauri ya bude wayar ya Shiga tex din,

*INA MAKA MURNA DA ZUWAN SABUWAR AMARYA KAMAR YADDA NAKE MAKA MURNAR SAMUN
KARUWAR JINJIRI DAGA WURINA NANDA WATA BAKWAI DA SATITTIKA DOMIN INA DAUKE DA CIKINKA NA
SATI BAKWAI DA KWANA BIYAR KUMA KA SHIRYA TSAF DOMIN TARE ZAMU RENI ABINDA KE CIKINA DAKAI
A GIDAN MATAWALLE KAKANSA*.....gumi ne ya shiga karyowa sameer cikin tashin hankali yake kara
karanta tex dun duhu ya soma gani kafafuwasa suka kasa daukarsa yayi baya kamar zai fadi kasantuwar
namiji ne da kafarsa ta kama kasa yasa be fadi ba ya kalli Dina da idanuwansa da suka kankance tace "kayi
shiru kayimun magana kaine mijina ko yaya man"

a fusace yace"nine mijinki Dina....."gabanta ne ya yanke ya fadi wani irin lugude kirjinta yakeyi kamar ana
buga mata ganga yayinda taji numfashinta yana sarkewa da miyaun bakinta,idanuwanta suka kafe akan
kallon sameer ko motsi batayi kamar gunki......

*SLIMZY*
✍🏻
07042277401
[16/11, 20:08] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*
*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

*15*

Slm ina maiso taga tayi K'IBA jikinta yayi kyau tazama yar lukuta 😘ina maiso taga NONO yacika yayi kyau ina
maiso taga duwawu yafito kinzama cikakkiyar mace ina maza da basacin abinci ina maza masuso suyi kiba
ina yara da basuda kiba ina mai farin cikin sanar daku zumar kiba, zumar kiba zumace wadda zata saka kiba
cikin kwana 7 dayardar Allah zumar kiba zumace mai inganci wadda aka hadata da magun gunan
gargajiya,Bugu da qari har nafdac ta amince da lafiyar zumarmu ta bamu BACH NO hjy indai kina fama da
rama d'an gwada shan zumar mu kisha mamaki indai kasha zuma saika chanza Maza kinemi mmn khairat
domin samun ingantacciyar zumar qiba Mai cike da lafiya with zero side effect🤗 08167453086

Kallonta yakeyi dikda irin tashin hankalin da yake ciki be hanasa dakewa ba,yasan yadda zaiyi da khairatu
dan wanan message din be yarda dashi ba tayaya zatayi ciki bayan sau daya takk ya kwanta da ita?
hawayene ke zubowa a idon Dina a sanyaye tace "kaine mijina kuma?"hawaye na cigaba da zubowa daga
idanuwanta ya gyada mata kai yace "ehh nine na aureki Dina ba mansorr ba"gabanta ya sake faduwa,wani
abu taji ya soketa a bangaren kirjinta na hagu ta koma da baya ta jingina da jikin gadon tace "meyasa ka
aureni bayan kasan yadda zuciyoyin mu suka makance da tsananin kaunar juna nida Amininka?meyasa ka
aureni bayan kasan yadda zucuyata ta shaku da soyayyar mansoor da kulawarsa?ko ka manta a halin
yanzun banida wani buri daya kasance wanda ya wuce ya dawo ya zama abokin rayuwata yaya sameer?
kaine ka koyamun kula abokinka tun zucuyata bata aminta dashi ba har ta sake ta rayu da tsananin
kaunarsa da shakuwarsa?tayaya zaka mallakeni bayan kasan cewar nida Amininka muke kaunar juna da
abota?"kalamanta ne suke neman hargitsa masa lissafi,ya juya yana fuskantar kofa ya harde hannuwansa a
kirji yace "Dina kisani dik wanan kulawar da soyayyar da mansoor keyi miki yayi miki ita ne kawai dan ya
tabbatar ya cusa miki kaunarsa dan ya rama rashin jituwar da kukayi a baya, kisani mansoor ba sonki
yakeyi dagaske ba ko kinga wasu alamu da suka nuna kedashi kun dace da juna?"gabanta ne ya yanke ya
fadi wani irin jiri takeji yana neman kada ita nan da nan gumi ke karyo mata ta ko ina yayinda kirjinta da
zucuyarta sukeyi mata lugude da barazanar tarwatsewa?....ta rushe da kuka tace"ka tabbatar kalaman da
kake fadamun akan yaya man gaskiya ne?menene ingancin kalamanka idam gaskiya ne? inaso nayi magana
da mansoor ina tsananin bukatar jin muryarsa a halin yanzun inaso ya fadamun cewar dagaske ba sona
yakeyi ba wasa da zucuyata yayi,idan har be dace dani ba meyasa kai ka aureni bayan nidakai din bamu
dace da juna ba?"ya juyo da sauri yana kallon Dina idanuwansa suka kankance yace "ni kike fadawa wanan
maganar?mansoor ya bata miki suna a kauyenku yadda babu wanda zai aureki,iyayenki mutanen arziki ne
da dattako wanda tsananin tausayin mahaifinki yasa na yanke shawarar aurenki dan na inganta rayuwarki
dikda nasan dani dake bamu dace da juna ba kamar yadda kike fada,sanan koda mansoor dagaske yake
sonki yakeyi iyayensa bazasu taba barinsa ya aurekiba,koda sun barsa kuma mahaifinki ya lashi takobin ko
mutuwa mansoor zaiyi bazai aura masa ke ba,tsananin tausayinki yasa na aureki Dina bawai dan zucuyata
na sonki ba,dan haka kisani bakya cikin rayuwar Mansoor a halin yanzun ya manta dake,wanan yasa nake
gargadinki nake so kisani na aureki ne na ajiyeki a cikin gida,dan haka ban baki umarni ko kasan matakala
ki sauka kije parlor ba,indai bada umarnina ba ballantana ki kaiga fita waje kinji ko bakiji ba?"jikin Dina
tsuma kawai yakeyi ganin komi takeyi kamar a mafarki anya maganganun sameer gaskiya ne?idan gaskiya
ne meyasa mamsoor bazai sanar da ita ba sai shi?wata zucuyar tace kin manta Aminan juna ne basa
boyewa juna komi?lumshe idonta tayi wasu sababbin hawaye ke zubo mata mansoor ya barta da tabo a
zucuyarta wanda bazata taba gogesa ba,zucuyarta jaririyar zucuyace wadda dashi tafara soyayya batasan
meye so da shakuwa ba sai akansa,tayaya zaiyi mata haka?baxata taba yafe masa wanan ciwon daya dasa
mata a kahon zucuyarta ba,ta dafe kanta dake barazanar tarwatsewa,nan da nan taji zazzabi mai zafi ya
rufeta,
ganin haka Sameer ya tsura mata ido ya runtse idanuwansa mansoor ne ya fado masa yadda yakeyi masa
magiyar son magana da Dina,ya bude jajayen idonsa yasa hannu ya kashe wutar dakin ya koma can gefen
makeken gadon ya kwanta yasa pullow ta bayansa ya rufe idanuwansa ba bacci yakeyi ba,tunanin tex din
khairatu yakeyi babban burinsa shine safiya tayi yaje ya sameta yasan be kyauta mata ba yana sonta amma
ya rasa dalilin dayasa yake bukatar Dina a kusa dashi dikda Dina bashi takeso ba mansoor Amininsa takeso
amma dik irin kauna da amanar dake tsakaninsa da Mansoor bazai taba barin masa Dina ba,yasani tabbas
idan mansoor ya dawo yasan Dina tayi aure zai Shiga mawuyacin hali yasan irin kaunat da mansoor yakeyi
mata amma yasan nadan lokaci ne zai mance da Dinar sanan bazai taba bari yasan waye matarsa ba.....
shasshekar kukan Dina yakeji a cikin Duhu tana sauke wani irin numfashi,da sauri ya kunna side lamp na
gefen gado dakin yadanyi haske,can kasan makoshinsa yace "ke lafiya kikeyimun kuka?kukan me
kikeyi?"yadda taji muryarsa yasa tadanji tsoro kamar ba sameer mai wasa da dariya idan suna tare duka da
mansoor ba ya sauya mata gabaki daya,tsittt tayi tana sauke ajiyar zucuya ya zauna dakyau yana
fuskantarta ta cikin sigar lallashi muryarsa can kasan makoshi yace "Dina menene laifina dan na tallafi
rayuwarki na aureki?shine kikeyimun kuka dan nafada miki kudirin mansoor akanki?"girgiza masa kai tayi
jikinta na rawa alamun jin sanyi,remote din AC ya dauka ya kashe AC din dakin sanan yakai hannunsa ya
rukota,wani abu yaji kamar shocking yayi saurin cirewa yace "ki kwanta kiyi hakuri kinji zanyi magana da
mansoir Din"kwanciya tayi kamar yadda ya bata umarni tayi lamo akan gado sabbin hawaye masu d'umi ne
ke fitowa ta gefen idonta yayinda zuciyarta ke hasko Mata fuskar mansoor.....

******
Mansoor na daure da farin towel ya fito daga wanka ya tsaya a gaban babban hoton enlargement na Dina
wanda yasa akayi masa,ya daga kansa ya kalli agogo karfe goma da minti sha biyar na dare,yayi murmushi
yakai hannu ya shafa daidai fuskarta a sanyaye yace "Dina.....nakasa daina tunaninki,ashe haka so yake?da
kinsan yadda soyayyarki ta haukatani da bakiyi bacci ba,nasan yanzun kinacan kin saki wanam bakin kina
bacci"ya sunkuya daidai lips dinta a jikin hoton ya bashi light kiss yace"am coming for you zanyi dik yadda
zanyi in kammala ayyyukan daddy da nakeyi yadda idan nakoma zai Amincemun da aurenki,zai shigemun
gaba koda momy bata Amince ba,i cant wait gobe zanji muryarki"ya karasa ya zauna gefen gado ya zuba
tagumi yana kallon hotonta yana murmushi,sakarcinta yake tunawa da tsananin tsiwa da bakinta,ya shafi
sajen fuskarsa yana murmushi,wanda shi kansa besan dalilin murmushinba......motsin mutum yaji ya daga
kansa,tee Dan maliki ce ta shigo,kayan dake jikinta yasa gabansa yankewa ya fadi yana bin ta da wani irin
kallo mai cike da mamaki,juyi tayi pant da brezia ce a jikinta jajaye ,nonuwanta sun cicciko a ciki yayinda
hips dinta suka baje kamar zasuyi magana tayi wani irin juyi ta fado jikinsa ta kankamesa tana goga masa
nonuwanta cikin kunnensa take rad'a masa "kana nan kana kallon hoton wanan yarinyar wadda batada irin
wadanan?ina sonka man.... please ka mance DA yarinyar nan tunda naji Daddynka suna waya da Abbah na
akan zakazo cyprus na nemi visa nataho saboda in debe maka kewa duba,"ta zaro nononta daya daga cikin
brezia yana kallon nipple dinta ya lumshe ido wata irin shaawa yakeji tana bijiro masa take zucuyarsa ta
tuno masa Da Dina da alkawarin da yayi mata cikin sauri ya bude idosa yasa hannu ya hankadata yayi baya
da sauri yana nunata da dan yatsa "idan ke yar iska ce niba dan iska bane kingane?kije can ki nemi wanda
zakiyi iskancinki dashi bazaki samuba a nan,kinyi hakan ne dan ki mallaki zucuyata in taba jikinki?kisani
mutum daya ce ta mallaki zucuyata itace Dina dana koma gida zan aureta dan haka ki kama kanki kafin in
miki cin mutuncin da baki zato ba'yana maganar muryarsa na rawa ya kauda kansa gefe,wani irin kallo
teema dan maliki takeyi masa "kaine zakace kai ba dan iska bane?ko ka manta lokacin da muke shaye
shaye nidakai muyi rawa tare?mu kwanta tare har kissing dina ka tabayi ko ka manta?yanzun ne ka tuno da
maganar wata banza kucaka can Dina?kila ma batasan kanayi ba jaka"a fusace mansoor ya tsinka mata
mari,ya kara tsinka mata mari jikinsa har rawa yakeyi hannunsa daya na rike da towel dinsa dake neman
kwancewa yace "idan kika kara kiranta da wadanan sunayen saina datse harshenki keda magana
harabada,idan kina maganar lokacin da mukayi wadanan abubuwan lokacin bansan meye rayuwa ba
bansan meneneso ba,yanzun sanadin soyayya na sauya bazan taba komawa rayuwata ta baya ba matukar
ina tare da Dina "a fusace ya janyota kiiiii ya bankade kofa ya hankadata waje ya koma ya rufe kofarsa yana
maida numfashi yasa bayansa ya jingina da jikin kofar"Alhamdulillah ban karya miki alkawari ba Dina na
daina dik abinda kika hanani fatana idan na koma gida mahaifinki ya Amincemun da aurenki"ya karasa
gaban hotonta ya sumbata,ya dauki kayan baccinsa riga da wando ya zura ya kashe wutar dakin ya kwanta
yana kallon ceiling idanuwansa a rufe yana murmushi minti minti yakan sauke ajiyar zucuya yace
"Dina ...gobe zanji muryarki"ya gyara kwanciyarsa ya ciro wayarsa misscals dayawa ya gani nabeeha
ce,tsaki yayi ya jifa da wayar ya rufe idanuwansa......

*******
khairatu na rike da wayarta ta tasa soyayyen irish da miyar hanta da cup din tea mai kauri mahaifiyarta ta
fito shirye tana rike da jakarta zata fita,tsaye tayi tana kallonta "yadai?tunanin mai kikeyi haka?"ummah ta
tambayeta yasa tadan zabura,tayi saurin daukat cokali ta dibo ruwan tea ta kai bakinta,karnin ne ya daki
hancinta ta yatsina fuska da sauri ta toshe hancinta da hannunta tanajin amai na taso mata ta mike cikin
sauri tayi toilet din dake kusa da dakinta,cikin sauri ummah tabi bayanta "lafiya khairatu?wai meke
damunki tun jiya ina kallon yanayinki tun kafin na fita gidan nan natafi taryar amaryar sameer naganki cikin
wani irin yanayi,tun jiya kin kasa cin komi nasan takaicinki be wuce yadda sameer yaci amanarki ya auri
wata bake ba"khairatu ta cigaba da yunkuri tana kwara amai,ummah ta riketa harta gama ta wanke
bakinta, idanuwanta jajir take kallon ummah a galabaice,wani irin kallo ummah keyi mata cike da tuhuma
ta rukota suka Shiga kuryar daki ta zaunar da ita gefen gado ta cire gyalenta ta wurgar gefe daya sanan ta
koma tasawa kofar makulli,khairatu na ganin haka gabanta ya fadi jikinta ya soma rawa tana raba ido a
cikin daki,ummah ta matso kusa da ita sosai ta tallabo habarta tasa hannu ta bude idonta ta kara budewa
sanan jikinta ya soma rawa kamar ana watsa mata ruwan sanyi taja da baya muryarta na hardewa tace
"khairatu?kardai kicemun ciki gareki kika boyemun,nashiga uku na lalace khairat ciki?"girgiza kai khairat ta
shigayi hawaye suka soma zubowa daga idonta "ummm ummah...na rantse"ummah ta wanka nata wani
gigitaccen mari tace"idan kikace tak a dakin nan saina shakeki kin bakunci lahira in kasheki in kashe banza
dan babu wanda zaisan nina kasheki tunda nina haifeki"take khairatu ta hadiye kukanta ta toshe bakinta
tana jinjina kai,cikin tsawa ummah tace"ciki?waye yayi Miki ciki khairatu?kodai dama Sameer ya fahimci
ciki gareki yasa ya fasa aurenki ya auro wata? haba biri yayi kama da mutum dik irin son da sameer yakeyi
miki haka nan bazai fasa aurenki ba ashe da walakin goro a cikin miya kin cuceni khairat, nafasa zuwa
gidan boka tunda na fahimci kece kikaso cin amanarsa ki auresa da cikin wani"cikin kuka khairat tace
"wallahi ummah shine yaci Amanata,ban taba sanin wani da namiji ba sai akansa,cikinsa ne ummah sanin
yasanni a waje yasa ya ci amanata ya fasa aurena"wani kallon rainin wayau ummah ke yiwa khairatu "har
yaushe kuka fara soyayya da sameer dim da har yayi miki cikin?inace cikin sati biyun nan ne baa rufe na
uku ba yace zai aureki yana sonki"khairat tayi murmushin takaici "ummah mun dade nida sameer muna
soyayya yana abubuwa dani batare da kunsaniba"jiri ummah taji yana neman daukarta tayi zaman y'an
bori a kasa tana fuskantar khairat wadda take bata labarin komi tana kuka cikin takaici da kunar rai ta
karasa maganar da "ummah ki taimakeni ki kwatar mun hakkina abinda ke cikina gudan jinin sameer
matawalle ne,banaso kice komi inaso kibani goyon baya wajen haife masa dan dake cikin cikina"gumi ne
kawai yake karyowa ummah cike da takaici wata irin tsanar sameer ce ta darsu a cikin zuciyarta tace "ohh
wato yaci moriyar ganga ko?shiyasa ya kama gabansa ya gwammaci ya auro kidahuma yar kauye ko?tou
wallahi bazai taba zaman lafiya shida ita ba,kuma wanan cikib sai kin haifesa a cikin gidan ubansa,nasan ta
inda zan bullowa lamarin"khairat ta ruko hannun mahaifiyarta da sauri tace "tayaya zaki bullo?ummah ya
auri wata ni kuma ina dauke da cikinsa ummah gashi ina tsananin kaunarsa dik girman laifin da yayimun da
cin amanata da yayi ummah har yanzun kaunarsa na nan dashe a cikin zucuyata dikda inada kudurin saina
rama abinda yayimun anma ina sonsa ina tsananin kishinsa ummah "tana maganar ne tana kokarin janyo
wayarta dake gefenta ta cire key ta fito da hoton Dina da khadija ta turo mata tace "ummah dubi yarinyar
da Sameer matawalle ya aura yarinyat da ko darajar yar aikin gidansu bata kai ba,sameer yaro matashi mai
class maiji da daloli"ta fashe da kuka ummah ta rungumeta tace "kiyi shiru yanzun idan nafadawa
mahaifiyarsa cikin dake jikinki nasa ne zasuce munyi hakan ne kawai dan munga yayi aure zamu bata masa
suna dan sameer macijin kaikayi ne sam beyi kama da wanda zai aikata hakan ba,zan kirata zan roketa
akan ta rikemun ke ta boye mun ke a gidan da zummar babu wanda nasani nasan hajiya zinariya macece
mai kirki da karamci zatayimun zamanki a cikin gidan wani makami ne babba a garemu wanda zamu kaiwa
nasarar abinda mukeso khairatu"kuka khairatu takeyi amma jin shawarar mahaifiyarta yasa taji wani sanyi
yana ratsata batasan lokacinda murmushi ya subuce mata ba ta kara rungume mahaifitarta cike da farin
ciki,

"kin sanar masa da maganar cikin ne?"khairatu ta jinjina mata kai "ehh nayi masa tex a daren jiya har
yanzun be biyo ba nasan zuwa zaiyi da kansa nasamu makamin da zan yakesa har saina mallakesa".
"dakyau"ummah tace,sanan ta mike ta yafa gyalenta tace "zan biya ta gidan hajiya ruma tukunna"

"tou ummah a dawo lafiya"ummah ta fice khauratu ta kwanta rigingine tana shafa cikinta tanajin wani
farin ciki yana kara lullubeta tayi kwafa tace "sameer matawalle kenan ka dauka kaci bulus?tou karya
kakeyi".....

******
wanka Dina tayi ta bude akwatunan da aka zube mata a cikin daki ta zauna gefe dirshan bayan tayi
kwalliyarta bakin nan yasha jan baki sosai kamar zai d'igo ga dugo da tayi a goshita ta zagayesa da bakin
kwalli,taja skirt dinta saman kirjinta,nonuwanta da suke a tsaitsaye kamar bulan bulan suka fito,turo kofar
sameer yayi yana makale da waya,da mamsoor ya tsurawa Dina ido fuskarta kadai tasa yaji wani takaici ya
lullubesa ya kalli jikinta fara ce tass babu ko digon baki, gyaran murya yayi yasa ta zabura da sauri ta tsaya
tana hararsa kallonta yakeyi cike da mamaki wato sam bazata daina tsiwar nan tata ba"ya zaka shigo mun
daki babu sallama?"da sauri yasa hannunsa ya toshe bakinta ya zaro mata ido cikin kasa da murya yace
"shhhhhh karki kuskura kiyi abinda zaki batamun wasa"ya zare mata ido ta watsa masa harara tana kallon
yadda ya saci kallon breast dinta tayi tsaki tace "iskanci"can kasan makoshi,

mansoor ne daga cikin wayar yace cike da zumudi"sam kace zaka hadani da peace of mind har yanzun ko
baku hadu bane?"kallon gefensa yayi yadda yaga ta natsu tana sauraren wayar yasa yace "gani ga ita"farin
ciki ne ya lullube mansoor yace "nagode"sameer ya mika mata waya yace "ga man...."kallonsa takeyi ido
cikin ido cike da mamaki "mansoor kuma? meya hadata dayi masa magana bayan ya mance ya fada mata
cewar yaudararta yakeyi"harara ya watsa msta yasa ta karba ta kara a kunnenta bugun zucuyarta ne ya
tsananta tace "yaya man...."muryarta na rawa tayi maganar tana saurarensa lokaci daya taji komi yana
neman rikice mata jin yadda yace "Dina.....ya kike?"tasa hannu ta share hawayenta "lafiya lau
kaifa?"muryarta na rawa hawaye na zuba a idanuwanta,

"Dina meyafaru?ya naji kina kuka?ko shagwaba ce?"a rude yake maganar,wani irin takaici ne ya lullubeta
da wata sabuwar kaunarsa da taji tana taso mata,can kasan zucuyarta zafinsa takeji yadda yayi wasa da
zucuyarta har yanada damar cewa a bata waya?tayi saurin mikawa sameer yana ganin haka ya karba dama
addua yakeyi kar Dina tayi abinda mansoor zai gane abinda yake faruwa "Dina.....menene meyafaru ya naji
kinayimun magana kamar kinajin haushina? fushi kikeyi dani natafi nabarki ko?zan dawo zamuyi aure mu
cigaba da abota"sameer na saurarensa ne zucuyarsa na bugawa "look ta fa bani wayar ta tafi abinta"yana
fadan haka ya fice Dina ta zauna dirshan gefen gado ta fara rera sabon kuka meyasa zai kira yace a bata
bayan ya fama mata ciwon da takeji a cikin zuciyarta tun daren jiya?,

"Sam dole zan gama abinda nakeyi in dawo dik yadda zaayi ayi in mallaki yarinyar nan in aureta "sameer
yayi murnushi yace "yanada kyau,nadai hadaku ko kaji dadi?"

"naji dadi sosai muryarta ta ragemin radadin rashinta da nayi wanda da hotunanta nake kwana nake
tashi,saidai nashiga damuwar jin yanayinta, Dan Allah ka lallasar mun ita kafin n dawo nanda kwana uku
zan dawo zanje gareta ina isowa zan tafi kauye inganta nayi kewar kyakkyawar fuskarta"sameer ya katse
wayar ya jefa cikin aljihu yace "sorry friend bazaka sake ganin Dina ba domin a halin yanzun matar
Amininka ce"ya lumshe ido ya shiga saukowa daga matakala,suna hada ido da ummah gabansa ya fadi ya
kalli momynsa wadda yaga ta fadada murmushinta tace "ah ah sameer ina Dina?"

"ta kwanta"yace a takaice,

momy ta dubi ummah tace "wanan bakomi bane hajiya khairatu ta dawo nan ai rufin asirin mu ne kinyi
dabara da kikace bazaa zubar da cikinba kinga idan kika bari aka haifesa zamu gano wanda yayi mata cikin
kinga lokacin sai mu dauki mataki"ummah ta cije lebe cikin zucuyarta tace "a cikin gidanki zaa reni dan
shegen da danki yayi"a zahiri kuwa godiya ta somayi mata,
"hajiya zinariya nagode sosai da wanan rufin asirin da kikayimun yadda kika rufamin Allah ya rufa miki"

"Ameen"sameer na tsaye yana saurarensu ya kasa fita,kafafuwansa ne sukayi masa nauyi ya kasa motsi
wato khairatu dagaske takeyi gidansu zatazo ta reni cikin jikinta?tabdijan intasan wata batasan wata ba
yasan yadda zaiyi da itam....

Sako Daga *SLIMZY*

Ina Alfahari daku masoyana kuma inajin dadin yadda kuke bani Hadin kai akan wanan tafiyar ina kuma
fatan zakuyi gangami wajen ganin an cigaba da tafiyar nan daku ina mai Alhini sanar daku cewar labarin
nan a 20 pages zai tsaya muku free....ina mai fatan zaku bani goyon baya dari bisa dari ta Hanyar siyan
cigabam labarin nan akan 500 naira kacal domin jin yadda turka turkar zata kasance yadda zata kaya ina
mai baku tabbacin bazakuyi danasani ba wadanda sukasan labaraina irin *KADANGARUWAR* da su
*RUD'ANI* da sauransu sun sani zaki tura 500 Dinki ta wanan account number din

*2255398727*
*ZENITH BANK*
*AMINA JIBRIL*

Tare da tura shaida ta 07042277401 ko 08036953516 ina matukar alfahari saidaku masoya......

*SLIMZY*
✍🏻
[17/11, 09:34] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

*ASSALAMU ALAIKUM SAKO ZUWA GA MAKARANTA LITTAFIN MAZA BIYU INA MATUKAR ALFAHARI DA
YADDA KUKA NUNAWA WANAN LABARIN SOYAYYA DA KAUNA INA KUMA MAI TABBATAR MUKU DA DIK
WADDA TAKE BIN LABARIN NAN BAZATAYI DANASANI BA LABARI NE MAI CIKE DA ABUN MAMAKI SOYAYYA
DA SARKAKIYA.....SHIN KINASO KI CIGABA DA SHAN ROMON LABARIN NAN?KINADA LABARI PAGES NA GAB
DA TSAYAWA?HANZARTA KI BIYA 500 KACAL DOMIN CIGABA DA SHAN ROMON LABARIN GA MAI BUKATAR
VIP 700 ZATA BIYA TA WANAN ACCOUNT NUMBER*

*2255398727*
*ZENITH BANK*
*AMINA JIBRIL*

*SHAIDAR BIYA TA 07042277401 KO 08036953516*

*16*
Gidansu Mansoor ya nufa bayan fitarsa dan bai kyautu ace tun tafiyar mansoor a matsayinsa na Amininsa
beje gidan ba,a harabar gidan yayi parking motarsa ya fito securities suka sara masa yayi musu
murmushi,zaheed ne ya rugo da gudu da ball dinsa yana fadin "oyoyo yaya sameer munyi missing dinka
jiya inaji momy tana fadawa daddy tun tafiyar yaya mansoor baka zo gidan nan ba"murmushi Sameer yayi
ya shafa kan zaheed suna kokarin shiga yace "magananne kila ma kaine kayi tsarin maganarka"dariya
momy keyi tana jiyosu daga parlor "oyoyo ango kasha kamshi dama yau nakeso naje gidan naga Amarya
tunda dai baa fada mana ba babu gayyata ko?tunda abokinka ya tafi ka kasa leko mu gashi inaso muyi
magana dakai"daddy ne ya fito sanye da farar shadda cikin sauri ganin Sameer ya tsaya "ja'irin kaya ashe
daga kai kudin aure aka daura maka aure ko?saura abokinka dikda yana can ya dameni ya kosa yanaso ya
dawo ni bansan meye matsalarsa ba"momy ta gyara zama tace "zauna sameer dama inada magana da
kai"sameer ya zauna daddy ya zauna kusa da kujerar dake kusadata momy,nabeeha ce da rufaida suka
shigo daga waje "ahh barka da zuwa yaya sameer yau kaine a gidan namu?"cewar rufaida cike da zumud'i
tace "dama zan kiraka dan inaso nazo naga amaryarka"ya dab furgita yace"amaryata Kuma?keda zatazo ta
gaisheki har gida aike inlaw dinta ce"dariya sukayi duka nabeeha ta hada ido da Sameer tace"hi...."shima
yayi waving dinta yana murmushi suka shige da rufaida,

"sameer na fahimci zumudin da abokinka yakeyi akan wata yarinya yakeyi sameer kuma inada tabbas a
kauye take,ya kasa sukuni dazun nan ya kira mahaifinku yace gobe ko jibi yakeson dawowa koda bai gama
abinda yakeyi ba, tayaya ga yar Aminiyata da tadade a gidan nan sabodashi hankalinsa na can kan wata yar
kauye?ni dama nadade ina zarginku akan tafiya kauyen nan da kukeyi sameer ashe ashe budurwa mansoor
yayi a can yanzun kamar mansoor da mutuncunmu a gari ace wai ya rasa inda yake neman mace sai kauye
dik wulakancin da yakeyiwa matan garin nan?"sameer yayi shiru yana sauraren momy,gumi ne kawai yake
karyo masa tabbas bayason mansoor ya dawo kasar nan yanzun saboda Dina,dan gaskiya ya rigada ya
aureta bazai iya sakinta ba idan ya saki Dina mai mahaifinta zai daukesa?ita kanta ya rigada ya shawo kanta
da cusa mata kalamai a zucuyarta?"ya kayi shiru sameer nasan bakason laifin mansoor saboda karfin
kaunar dake tsakaninku wanda tun kuna yara kuke a haka amma ya kamata ka fada masa gaskiya bazan
Amince masa da auren wata a kauye ba,
.daddy ya karbe "kedai kibi a hankali kinsani mansoor yanada murdadden hali dik wanan surutun da kikeyi
idan har ya dawo bai gadama ba babu wanda ya isa ya sauya masa raayi kinsani"shiru momy tayi cike da
takaici ta kasa magana dik maganar da daddy sukeyi da sameer akan mansoor ta kasa tsoma baki shiru
kawai tayi cike da takaici,sameer yayi musu sallama akan zai kawo amarya har gida su gaisa.....

******
wani zabura khairatu tayi ganin Sameer a tsaye a cikin parlorn ya zura mata idanuwa ko kiftawa bayayi
itama shi take kallo cike da takaici ta juya baya ganin yadda zucuyarta ta karaya gabaki daya yasa ya cije
lebe yace yess nayi nasara yasan yadda khairatu ke tsananin kaunarsa hakan yasa ya tako ya karaso ya
tsaya ta bayanta tanajin kamshin turarensa ta lumshe ido kukan da take kokarin boyewa ne ya kwace
mata,ta durkushe a kasa ta soma rera kuka "nasani damar idan aure bai kawoka ba saki zai kawoka nasan
tun daren jiya da kaga sakona akan cikinka da yake jikina nasan ka kasa bacci amma dayake kanada karfin
hali shine sai yanzun zakazo dan ka tabbatar?tou kasani danka ne a cikin cikina Kuma wallahi bazan ciresa
ba Sameer dan ina sonsa kamar yadda nake sonka dikda zucuyarka bata tare dani tana tare da sabuwar
Amaryarka wadda kuka kwana kuna amarci kana sheke ayarka da ita"murmushi yayi yasani a fusace take
saidai kalamanta ya kara tabbatar masa da tsananin sonsa da takeyi da wanan damar zaiyi amfani wajen
ganin ya kwantar mata da hankali,dagota yayi ya rugumeta a kirjinsa yana sauke wani irin numfashi,ya
dagota sosai ya kara mannata a jikinsa ta kankameta sosai dikda kici kicin kwacewa da takeyi,"kin
gama?"yace cikin wata shu'umar murya wadda tasa jikin khairatu ya sandare nan da nan ta nemi
natsuwarta ta rasa ta juyo da idonta da sukayi jajir ta zuba masa su, shima kallonta yakeyi da narkakkun
idanuwansa ya cigaba da magana "kina tunanin zan baki goyon baya ne ki zubarmun da cikina dake jikinki?
ko kina tunanin bana sonki khairatu?ina sonki ina tsananin khaunarki kinsani soyayyarki tasa nazo ganawa
da abinda ke cikinki"yana maganar yana shafa mararta wani yarrrrr takeji a jikinta ya dora bakinsa a gefen
wuyanta yayi mata wani light kiss,ta juyo da ita sosai tana fuskantarsa yacev"kalli kwayar idona khairatu
kisani ba saina fada miki ba kingani da idanuwanki ina sonki so mai tsanani ki yadda Dina dana aureta
kawai ita din kaddarata ce Allah ya rubuta auran mu ne amma so daya ne ke kadai nakeyiwa shi,hakan yasa
nazo gareki in nemi gafararki in kara jadadda miki kaunar da nakeyi miki kisani kina haihuwa zan aureki"ta
lumshe idanuwanta ta bude ta sauke sassanyar ajiyar zucuya a raunane tace "i trust you Sameer please
dont break my trust for the second time,dik yadda na dauki fushi dakai nakasa banyi tunanin zan saurareka
ba"yayi yar dariya yace "zaki saurareni kodan symbol of love"ya tabo cikinta tayi murmushi yace"naji
conversation dinsu momyna da ummah yanzun"ta durkusar da kai tana wasa da yan tsunta yace "seee ba
dole bane sai kinzo gidan mu kin zauna khairatu dik inda kike ina tare dake ina tsananin kaunarki dakeda
wanan"yana maganar yana kokarin hade bakinsu wuri daya shida ita ta kauda kanta gefe wasu hawaye
suka fara zubo mata "kanaso muyi abinda zan kasa bacci ko?in kwana ina tunaninka bayan kanacan
rungume da wata?"wani kallo yayi mata yace "look wanan yarinyar kaddarata ce amma babu ta yadda
zaayi na rungumeta bayan inadake pure heart ke kadai nakeso ke zuciyata ke mararin so bazan taba son
Dina ba na aureta ne kawai badan ina sonta ba"sakin baki tayi tana kallonsa cike da mamaki kwayar idonsa
take kallo tana so ta gano gaskiyar kalamansa dagaske sameer ya auri wanan yar kauyen ne badan yana
sonta ba?"zatayi magana sukaji sallama da sauri ya dan saketa daga rungumar da yayi mata yaja da
baya,kawar khairatu ce ta shigo tana jifan Sameer da wani irin kallo wanda yasa gabansa faduwa yasani
sarai yasan Halin surayya tanada masifar wayau tasan kan duniya dik yadda zai taushi khairatu saita ruguza
masa shiri beso ace surayya tazo a wanan lokacin ba,ya kauda kansa gefe khairatu ta tabosa tana
murmushi "bakaga surry bane ya sameer?naga ka kauda kanka gefe"wani murnushi yayi irin na yan Duniya
ya zuba hannunsa a aljihu yace "hajiya surayya....kece?idon gari"tayi wani murnushi tace "Ango kasha
kamshi,ya akayi naganka a wajen khairatu a wanan lokacin daya kamata kanacan manne da
Amarya?"gabansa ya fadi gumi ya karyo masa yace "ga Amaryar zuciyata nan wancen ita kuka gani a
zahiri"ya janyo kafadar khairatu ya hadata da jikinsa,ta kwantar da kanta a kafadarsa cikin shagwaba tace
"surry nice Amaryar sameer ba waccen kucakar kauyen ba"surayya tace "tabbas nagani aiga Amarci nan
kunayi a zahiri"tayi maganar cike da rainin wayau ta dire jajarta a gefen kujera ta zauna ta dora kafarta
daya kan daya tana wa sameer wani kallo wanda ya harzukasa sosai yasan wacece surayya tabbas dik
yadda zaiyi ya lallaba khairatu ta zubar da cikin jikinta batare da tazo gidansu zama ba saita wargaza
shirinsa sam beso zuwanta a yanzun ba dole zaibi dik hanyar da zaibi wajen ganin ya rusa dik wata alakar
abota a tsakanin khairatu da surayya dan ganin ya cika burinsa batare da mahaifiyarsa da mahaifinsa
sunsan shine yayi mata ciki ba "pure heart am going zan dawo daddare"yace yana kashe mata ido ta gyada
masa kai yaja dogon hancinta ya rada mata a kunne cike da yaudara "ki kulamun da symbol of love"tayi
murnushi ya fice,

surayya ta zabura "amma yau na tabbatar dake wawuya ce jaka khairatu ban taba tunanin kwakwalwarki
ta juye idonki ya makance akan soyayya ba sai yau kin kasa gane so da kuma yaudara,idonki ya rufe guy din
nan yayi aure ya barki amma nazo da niyyar mu shirya masa ramuwar gayya kawai na tarar daku rungume
da juna kila ma ya gama biyan bukatarsa dake ta hanyar kara hura miki wutar soyayyatsa da petir din
yaudara irin tasa,to bari kiji karya yakeyi wallahi be isa yaci bulus ya barki ba kinga shedar tantiri ne daya
gama matseki da lalataki sai yaje kauye yayi aure ya auro wadda batasan komi ba yadda shi zai koyar da ita
komi yayi tarbiyyarta da kaunarsa,tou karya yakeyi ummah ta kirani ta shedamun komi dake faruwa hakan
yasa nazo dan mu shiryawa yaki da sameer"jikin khairatu yayi sanyi kalaman surayya sun daki zucuyarta
tabbas sameer ya gama raina mata wayau batasan hakan ba saida surayya ta zaro wadanan maganganun,

"yanzun menene abunyi surayya?"khairatu tayi maganar a sanyaye tana kallon surayya cike da
takaici,idanuwanta sun kada sunyi jajir.....

"matso kiji yadda zaayi"ta gyara zama kusa da surayya tana saurarenta....

*******
Dina na tsaye a gaban tankamemen hoton sameer da mansoor wanda yake parlornta ta tsura masa ido ko
kiftawa batayi girar tasha gazal bakinkirin jan baki kuwa kamar kamfanin ta shafa a bakinta tana rike da
kwankwasonta,batasan lolacinda wasu siraran hawaye ke zubowa daga idanuwanta ba ta karasa ta hau
saman kujera zata shafa fuskar mansoor kenan Sameer ya daka mata wata razananniyar tsawa "ke Dina are
you mad? halan kin haukace kina matar aure zaki shafa fuskar wani kato wanda ba muharraminki ba"a
razane ta juyo tana kallonsa cike da tsananin mamaki,jikinsa ne ya kama rawa idanuwansa suka rufe ya
karaso ya fuzgota tayo kasa zata fadi yayi saurin tareta a jikinsa,ta cire jikinta daga nasa taja da baya tana
kallonsa "yaya man din ne wani kato?ohh Amininka abokinka wanda zaka iya sadaukar da farin cikinka
akansa Shi kake kira da kato?koda yake banga laifinka ba tare kuka yaudareni kaidashi,kuka hakamun rami
mai zurfi na fada ciki a sanadin soyayyar abokinka,wanda idanuwana suka rufe banaji bana gani akansa har
sabawa iyayena nayi daga karshe ka aureni Shi yaki aurena,kayi hakuri a matsayina na matarka ka sameni
na shagala da kallon wani sabanin mijina,zucuyata ta kasa daurewa da cire sonsa a cikinta,ina son yaya
man....baxan boye maka ba yaya sameer inason ganinsa koda shine ganin da nayi masa na karahe, nasan
yana nan babu tafiyar da yayi ya kawai gujeni ne yayi ramuwar gayya akan dama yanada wani kudiri a
kaina amma nakasa cire sonsa"tana maganar hawaye na zuba daga idanuwanta,wani radadi sameer yakeji
a cikin zucuyarsa kalamanta na tafasa masa rai meyasa?dikda bayajin digon kaunarta a zucuyarsa meyasa
ya kasa barwa Mansoor ita har ya dawo?idanuwansa sukai ja ya nemi kujera ya zauna ya dora kafarsa daya
kan daya batare da yace mata komi ba,ganin haka yasa ta juya cikin sauri ta nufi bedroom dinta ta kullo
kofar ya sauke ajiyar zuciya ya ciro wayarsa tayaya zai hana mansoor dawowa nigeria?babban tunaninsa da
damuwarsa kenan shine ya zauna a can dan tabbas yana tsananin kaunar Aminin nasa amma yasani akan
ya auri Dina inhar yasani zasu iya samun matsala Shi kuma bazai iya rabuwa dashi ba,kamar an tsikaresa ya
mike wani irin tukuki yakeji a cikin zucuyarsa har zai fita yake jiyo sautin kukan Dina daga bedroom a fusace
ya nufi dakin ya ingiza kofar ya jita a rufe ya dawo da baya wato ma da mansoor ta damu?ya dage
kafadarsa abinda yasani bazata taba ganin Mansoor ba shima koda ya dawo kasar bazai taba bari su hadu
ba,ya juya ya fice ya rufe kofar da makulli ya sauko daga sama cikin sauri, turus yayi ganin khairatu da
surayya a parlorn mahaifiyarsa gabanta dauke da trolley da wata jaka "ki saki jikinki khairatu kinji ki
kwantar da hankalinki har Allah ya saukeki lafiya sanan saimu nemi uban dan dake cikinki mu makasa a
kotu"turus sameer yayi tsaye yana kallon khairatu wadda ta sakar masa wani murmushi mai kamada na
mugunta ta nunasa da yatsa,gabansa ne ya yanke ya fadi take yaji wani jiri na daukarsa kamar zai fadi,
momy da sauri ta kalli sameer "yadai khairatu kike nuna sameer?"wayancewa tayi tana Sosa kanta tana
murnushin mugunta tasan saida gabansa ya fadi ai tayi masa alkawarin renom cikin dake jikinta a
gidansa,gidan metawalle kakan shegen dake cikinta,ya dauka zata fadawa momy zinariya cewar shine yayi
cikin?kashe masa ido tayi sanan tace "au momy nibanmasan yaya sameer bane"momy ta sauke sassanyar
ajiyar zucuya ta kalli sameer "ya na ganka cikin wani yanayi kuma?ina Dina? wai kaikam sameer lafiya
tunda ka auro yarinyar nan kake boyeta a sama kamar wanda yayi auren rashin gaskiya?meyasa kake
boyeta ta sauko kasa mana ga jamaa nan ita kadai a sama?"ya girgiza kai cikin zucuyarsa yace momy bazaki
gane yadda zanyi yakatsantsan da boye Dina ba gudun kada Mansoor ya dawo yasan nine na aureta,a
zahiri kuma cewa "tayi bacci ne bata dan jin dadi ne"wani kishi khairatu taji ya caki zucuyatta wato
dawowa yayi wajen matarsa ya tarairayeta?shiyasa yake boyeta?ya saci kallom khairatu yayi mata wani
kallo cike da shu'umancu take taji komi nata na kokarin kwarkwancewa ya fice ya barsu nan tare da
momy....

*******
idanuwa jajir Mansoor ke kallom likitan wanda ya kasance bature ne suna magana cikin harshen turanci,
cikin kulawa likitan yake tambayarsa da harshen turanci,

"meyasa ka bada k'odarka guda daya?bayan kasan kanada matsalar numfashi?sanan gashi na duddubaka
naga kana cikin matsananciyar damuwa akwai abinda kakeso?"mansoor ya ja numfashi bece komiba saidai
maganar zuci"damuwata bata wuce na koma Nigeria nasamu Dina na aureta ba,rashin ganim Dina shine ya
haddasamun damuwa"likitan ya tsaresa da ido yana karantarsa ya sake magana "tunanin mai kakeyi?
kanaso ka mutu ne?"mansoor ya girgiza kai yace masa cikin harshen turanci "Bazan mutu ba saina auri
Dina,damuwata kuma da kake tambaya itace damuwata,itace peace of mind na rayuwata gabaki daya nayi
nisa da ita dole nashiga damuwa"likitan yayi murmushi ya jinjina kai sanan yayi wasu rubuce rubuce ya
dago ya kallesa "dole ka kiyaye dik wata damuwa kasantuwar rayuwarka tanada rauni a halin yanzun"shiru
mansoor yayi batare da yace komi ba,ya rubuta masa magunguna ya karba ya fito take ya karasa pharmacy
ya karba sanan ya fito harabar asibitin ya tsaya,

tunanin maganganun likita yakeyi wanda suka dan caja masa kai,yaja gauron numfashi ya ciro wayarsa ya
kira sameer,ya kana tafiya ya karasa jikin wata mota ya tsaya,
sameer na zaune a garden cikin tashin hankali yaga kiran mansoor "Hello Man....yane How are you"sameer
yace muryarsa na sarkewa,

"Da dama dai"sameer ya jinjina kai "what the problem"ya tambayesa cike da kulawa,jimmm mansoor yayi
sanan yace "Banida lafiya ne sameer naje asibiti"sameer da sauri ya razana cikin damuwa da kulawa yace
"meyasameka?me sukace yana damunka man are you ok?"a rude yake tambayarsa,

mansoor yace "common sam ka kwantar da hankalinka nasan yadda ka damu dani kake tsananin kaunata
nasani hakan yasa nakiraka na fada maka"sameer ya natsu gabansa na faduwa yace "me sukace ina
saurarenka?"nan mansoor ya fada masa komi abinda likita ya fada da wanda shima ya fada masa ya dora
da,

"sameer idan ban dawo nasamu Dina ba zan iya rasa rayuwata bansan haka nayi nisa akan soyayyar
yarinyar nan ba,amma nasan inada kalubale a gabana kafin in mallaketa saidai nayi tarko guda daya wanda
dik duniya babu wanda yasan kodar dake jikin mahaifiyarta tawa ce sai kai,saboda Allah nayi saboda
insameta man inason Dina sosai kasani"dishi dishi sameer ke ganin gabansa tsananin rudewa haka
mansoor yayi nisa akam son Dina?gabansa ya fadi to tayaya zaiji idan yadawo ya tarar Dina tayi aure?dikda
bazai taba sanin shine ya aureta ba?mansoor katse masa tunani yayi "sameer ka kwantar da hankalinka
nasan inada Kai zaka tayani yaki dasu momy da mahaifin Dina har in mallaketa nasan zakayimun
wanan,dan haka kasa ran ganina a nigeria ko wani lokaci from now am coming for her na shiryawa dik
wani yak'i,sanan yauwa ka cewa Amaryarka idan nadawo a wajenta zanci Abinci"dam gaban sameer ya fadi
ya kasa magana zaiyi magana ya juya yaga khairatu a gefensa ta zuba masa manyan idanuwanta sai kawai
ya katse wayar ya mike a zafafe zaibar wurin tasha gabansa.......

*ASSALAMU ALAIKUM MASOYANA MUTANEN ARZIKI WANAN TAFIYAR PAGES NA GAB DA TSAYAWA
WADDA KE BUKATAR SIYAN LITTAFIN NAN MAZA BIYU....500 KACAL ZATA TURA SINGLE GROUP 700 VIP TA
WANAN ACCOUNT NUMBER*

*2255398727*
*ZENITH BANK*
*AMINA JIBRIL*

*SHAIDAR BIYA TA 07042277401 KO 08036953516*

*SLIMZY*😍
*07042277401*
[18/11, 09:12] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

*17*

Slm ina maiso taga tayi K'IBA jikinta yayi kyau tazama yar lukuta 😘ina maiso taga NONO yacika yayi kyau ina
maiso taga duwawu yafito kinzama cikakkiyar mace ina maza da basacin abinci ina maza masuso suyi kiba
ina yara da basuda kiba ina mai farin cikin sanar daku zumar kiba, zumar kiba zumace wadda zata saka kiba
cikin kwana 7 dayardar Allah zumar kiba zumace mai inganci wadda aka hadata da magun gunan
gargajiya,Bugu da qari har nafdac ta amince da lafiyar zumarmu ta bamu BACH NO hjy indai kina fama da
rama d'an gwada shan zumar mu kisha mamaki indai kasha zuma saika chanza Maza kinemi mmn khairat
domin samun ingantacciyar zumar qiba Mai cike da lafiya with zero side effect🤗 08167453086

"ina zakaje?ko ganina ne bakaso?idan nice bakason gani dole zakaso ka shaki numfashin abinda ke cikina
Daya kasance mallakinka sameer?ko kanaso kace baka sona yanzun waccen bagidajiyar daka kulle a cikin
daki itace muradin zuciyarka sameer?karya kakeyi kayi karya kaso wata bayan ni ina sonka soyayyarka ce
tasa na zabi haihuwar shege a gidan kakansa"maganganunta suna tafarfasa masa zucuya cikin tsananin
fushi ya kalleta ga mamakinsa hawaye yagani suna zuba a idanuwanta hakan yasa jikin sameer yayi sanyi
ya tsareta da manyan idanuwansa wanda kallo daya zakayi masa ka hango tsananin furgici da
rudani,kallonta yakeyi cike da mamakin karfin hali irin na khairatu tana tunanin zuwa gidansu da cikin
shege zaisa ya aureta?yayi murmushi yasa hannu ya share mata hawaye yace "ya isa haka kinsan banason
kukanki ko a da ballantana yanzun da kike dauke da gudan jinina"cike da dabara da lallashi yayi maganar ta
fada kirjinsa yayi saurin tallabota tana sauke ajiyar zuciya yana bubbuga bayanta yana waigawa gefe da
gefensu bugun zucuyarsa ne ya tsananta daga idanuwansa yayi saman bene ta bangaren dakin Dina yaga
window dinta a bude ya tsare window dun da idanuwa gabansa na tsananin faduwa yake hangen tamkar
inuwarta a tsaye jikinsa na rawa ya janye jikinsa daga nata tayi saurin kallonsa ya sunkuyo da kansa daidai
kunnenta yace"come on so kikeyi a fahimci wani abu?kinsan momy fa tana gidan nan kuma naga alamar
kamar motar daddy"yana maganar yana waigen sama cikin dabara khairatu ta kalli inda yake kallo
windown Dina ne a wajen yake facing garden din tayi ajiyar zucuya tace "ko kuma kana gudun matarka
tasan halin da muke ciki ko?kana jin tsoronta ne?"girgiza kai yayi ya shafa gemunsa cikin sauri yadan ja da
baya ganin momy daga nesa tana magana da masu yankan flowers,tasha wani tsadadden lace red mai
flowers baki fa gyalenta da takalmi da jakarta duk bakake,kamar ance ta waigo ta gansu,nan da nan momy
ta sauya fuska ta watsawa Sameer harara yayinda ta karaso idanuwanta dauke da tambayoyi gabansa ne
ya shiga masa lugude "mai kukeyi ku biyu a nan?"tace a kausashe ya sosa keyarsa yace "naga khairatu ita
kadai a nan tana kuka ne"ya kalli khairatu ya kashe mata ido ta sunkuyar da kai momy tace "kukan mai
kikeyi khairatu?ba nace kidaina koke koken nan naki ba?ko ba nayi miki fada akan abinda ya sameki
kaddara bace?kiyi hakuri ki kwantar da hankalinki har Allah ya saukeki lafiya kigani dik wanda yayi miki
cikin nan sai mun karbar miki yancinki sanan sai ya dandana kud'arsa"khairatu ta saci kallon sameer wanda
ya basar tamkar babu wata damuwa a tattare dashi tace "wuce ciki kije ki kwanta zan dan fita ne yanzun
zan dawo"khairatu ta jinjina kai tana waigen sameer ta baya tabi,kasa tafiya tayi samun kanta tayi da son
sauraren mai momy zata fadawa sameer,taga alamar taji haushin ganinsu tare,hmmm matar nan batasan
cikin dake jikinta na danta bane ko? har take wani zare musu ido ganinsu tare?sai ta wayi gari ta gansu
kwance a gado daya a daki daya sanan zucuyarta zata buga ita sameer zai yaudara yayi aure?ta kasa
kunnenta ta bayan flowers,

"sameer kada in sake ganinka da khairatu kun kebe ku biyu kaji nafada maka ko?idan nasake ganinku kaida
ita tabbas saina bata maka rai, kasani ciki take dauke dashi wanda baasan na waye ba Allah ne yasa ma
bazaka aureta da cikin wani ba dayake Allah yaga zuciyarmu ashe tagama zubar da mutuncinta a
waje"sameer ya jinjina kai gumi ya karyo masa khairatu shine ya fara saninta a waje kuma shi kadai ke taba
jikinta,shiru yayi ya kasa cewa komi momy tace "yadai naga dik yanayinka ya sauya?"ya girgiza kai yace
"bakomi bari nashiga ciki nasamu Dina"momy ta jinjina kai tayi murmushi tace "abinda boyonta kakeyi
yarinyar nan ko hira baka bari ta fito muyi"suna maganar suna tafiya a tare,ya sosa kewayarsa cikin
zucuyarsa yace "tayaya zanbari Dina ta fito momy?Dina bazata taba fitowa ba banason kaddarar da zata
hadata da mansoor domin yanzun nine mallakinta"a zahiri yace"batason yawan magana ne kawai inacewa
ta sauko bataso"momy ta bude mota tace "yauwa wai kaji mansoor jirgin rana zai biyo da yamma zai sauka
ko?naji dazun suna magana da daddynku yace bayaso a fada maka ne surprise zaiyi maka saidai ya kiraka
yace ka daukoshi a Airport kawai nafada maka ne dan ka shirya gashi nasan nan zaici abinci ya kenan?kaga
dai Dina bata iya irin abincinmu na birni ba"tana maganar ne amma gabaki daya gumi ya jika sameer
tashin hankali wani irin damuwa yakeji a ransa gashi yana tsananin bukatar mansoor Amininsa a tare dashi
gashi ya auri Dina ya kenan?tayaya zai kaucewa haduwar Dina da mansoor?"tsaki momy tayi "kai kasani
kag driver ja muje ina magana yana can yana wani tunani na daban"karar rufe kofar motar ne ya dawo
dashi daga tunani yace "momy...."ta watsa mai harara driver yajata ya soma horn gefe ya koma ya lumshe
idanuwansa Amininsa zai dawo gari yasan yana dawowa zai bukaci Dina,lumshe idonsa yayi ya hasko
fuskarta dazun sosai take burgesa yadda take magana,kunnuwansa ne suka tuno masa da sautin kukanta
da barota da yayi a daki tana kuka,cikin sauri ya nufi hanyar da zata sadashi da cikin gidan dole ya lallabata
ta bashi tausayi yasan yadda take tsananin son mansoor dole dik yadda zaiyi ya mantar da ita mansoor
kota wani hali....

*******
"Ah Ah su Anty nabeeha Kenan anata shiri kinji yadda dakin nan ya kaure da kamshi kamar a maiduguri?
kamar wata amarya"cikin sigar tsokana rufaida tayi maganar ta zauna gefen gadon da nabeeha ke shiryawa
"kin manta ni Amarya ce?ko kin manta yaya Mansoor nadawowa zamuyi aure?na tabbatar yanzun ya
mance da wanan yar kauyen "rufaida ta jinjina kai ta sauke gauron numfashi tace "Allah yasa
kam"nabeeha tayi farrr da ido "kinga nasa su Asama'u su fara shirya abinci kafin na fito nashiga kitchen din
na tayasu Dan dani zaayi abincin da yaya man zaici"rufaida tace "dakyau Amaryar yaya man aimu yan biki
ne Allah dai ya dawo dashi lafiya,kenan ke yaya sameer zaizo ya dauka yaje daukoshi?ya kamata ace yayi
tozali da wanan kwalliyar daya sauko daga jirgi"nabeeha tace "kinsan bazai yuwu ba yaya sameer nasan shi
kadai zaije kila da matarsa zasuje taryar yaya mansoor"rufaida ta yatsina fuska"Allah yasa da ita din tinda
bata fitowa fa koda mukaje gidan da momy jiya yin Allah ya sanya Alheri bamu ganta ba "nabeeha tace
"boyonta yakeyi yafiso abokinsa ya soma ganinta"rufaida batace komiba ta mike tsam tausayin nabeeha
takeyi dan koda sukayi waya da yaya mansoor ya tabbatar mata yana isowa kauye zaitafi wajen Dina tasani
su momy sunyi haka ne dan su mantar dashi auren yar kauye basusan yar kauye soyaytarta tayi dashe da
jijiyoyi da rassa a zucuyar yaya man ba,

nabeeha na ganin fitar rufaida cikin sauri ta bude wardrobe dinta ta fito da kwalin da ummah ta karbo
mata wajen boka ta tsaya a gaban madubi tasa shi da kyau ta fito da turare ta dangwalo ta zana a koshinta
kamar cros ta lumshe ido tace "idona idonka yaya man ka tashi aiki babukai babu wata yar kauye nice zan
mallakeka nikadai na dace dakai"ta fada kan gado cikin farin ciki,momy ta kwala mata kira cikin sauri ta
mike ta fice sukai karo tanata faraa tace"ah ah nabeeha dik wanan murnan ganin mansoor ne?"nabeeha ta
sunkuyar da kai cike da kunya,momy tace cikin zuciyarta Allah yasa dai ya mance da waccen kucakar
bakauyiyar"a zahiri tace "tou muje ku shirya masa dining nasan yanzun sun kusa sauka"tace "Toh
momy"tayi gaba momy na bin ta da kallo cike da tausayawa,momy ta lumshe ido tace "ai nayi shiri akamsa
ke nakeso ya aura da zarar yaci abincin can nasan zucuyarsa zata cire masa son wata tsinanniya nan"tabi
bayan nabeeha cike da sake sake....

*******
sameer na rungume da Dina a kirjinsa ta kwantar da kanta ta gefen idonta hawayene ke zubowa wanda
batasan dalili ba tarasa dalilin dayasa zucuyarta ta kasa mantawa da mansoor dikda ya yaudareta ya cusa
mata soyayyarsa daga karshe yayi tafiyarsa amma ta gagara mance amon sautin muryarsa a kunnenta,ta
gagara mance kyakkyawar fuskarsa da shanyayyun idanuwansa dama karya yayi mata da yace ya daina
shaye shaye?....wayar sameer ce take ruri idanuwansa a rufe ya janyo wayar dayan hannunsa na cikin
gashin kan Dina yana yawo da hamnunsa ciki wata irin natsuwa yakeji ta musamman yau kasancewarsa
tare da Dina "Ranka ya dade aiki nata tafiya yanzun haka an kusa kammalawa sirikin naka baban Dina yace
ayi maka godiya"abinda Dina taji kenan ta dago kai ta tsaresa da ido,wani abu yaji ya tsarga masa ganin irin
kallom da takeyi masa ya hura mata iska a ido ya kashe a raunane tace "aikin me akeyi wanda baba yakeyi
maka godiya?"yayi murmushi besan sanda ya sunkuya ya mata light kiss a bakinta ba tayi saurin janyewa
yace "gidanku nasa ayi renovating"tayi shiru tana kallonsa bata gane ba yace "sorry na mance nasa a rushe
gidanku ne a sake muku sabon gini irin na birni na zamani ya kirani yana shedamun an kammala karashene
zuwa da safe zasu gama"farin ciki taji ya lullubeta ta soma dariya fararen hakoranta suka bayyana tana
kallonsa lokaci daya taji ya samu wani girma a idonta mahaifanta?ya kyautatawa?ya dage mata gira yace
"kinji dadi?"ta daga masa kai ya janyota jikinsa sosai hannunsa na kokarin shiga breast dinta ta ture
hannun ta zumburo baki "nifa banayin iskanci"dariya sosai ta bashi ya kyalkyale da dariya ya rinka
dariya,khairatu na labe a jikin kofar tanajin dariyarsa wani kishi ne ya taso mata ya rufe mata idanuwa ko
gani batayi ta soma bubbuga kofar iya karfinta, Sameer da Dina suna can ciki basu saniba ganin bazaa bude
ba yasa a haukace ta nufi daki neman wayarta dole yau ya kwanta da ita ko yaki koyaso dan tana kewarsa,

yace "au wanan iskanci ne?"ta watsa masa harara wani irin burgesa ta karayi ya janyota yace"kinga"ta
fuzge ta rufe kirjinta tana bubbuga kafafuwanta kamar yarinya karama hakan yasa ya shagala da kallonta
yanajin zucuyarsa cikin wani shauki wanda besan daliliba,wayarsa ce ta soma ruri cikin sauri ya dauko
ganin number mansoor ta kasa nigeria gabansa ya fadi ya kalli Dina wanda itama kallonsa takeyi samun
kanta tayi da jin wani irin faduwar gaba wanda tanajin hakan ne dik lokacin da take waya da yaya man
dinta....

mansoor yace "yane sam....i know you are happy ganin numberta ta nigeria,surprise?"mansooor yana
maganar yana murmushi sameer kamar an dasashi ya kasa gane wani yanayi yake ciki farin ciki ko bakin
ciki?"ohh my god i cant believe man...."fadin kalmar man yasa gaban Dina faduwa da sauri ta karaso ta
zauna a gefen gado jikinta a sanyaye yaya man ya dawo kenan?zataso tagansa da wani ido zai kalleta
yaudararta da yayi Sameer ya saci kallon Dina yace "on my way yanzun nan"

Mansoor yace "cant wait to see you i miss you soo much,akwai maganganu na shiryowa yak'i kaidai kawai
kayi sauri idan dare beyiba kauye yau zamuje naga Dina"be gama jin me zaice ba sameer ya datse wayar,

Mansoor ya lumshe ya sauke ajiyar zucuya Yana jin wani irin nishadi ya dawo nigeria babban burinsa be
wuce ganin Dina ba yanaso yaga ta sauya?ya shafa sajensa "nayi kewarki Dina nayi kewar shirmenki"....ya
runtse idanuwansa yana hasko kyakkyawar fuskarta da gashin girarta masu tsawo da yadda take turo baki
tana magana....

dafa kafadar Dina sameer yayi yace cikin rad'a"mansoor ya dawo"tayi saurin kallonsa yana hango damuwa
da tsananin soyayyar mansoor a kwayar idonta yace "kiyi hakuri nasan ya yaudareki nasani dik abin nan da
nakeyi bana burgeki saboda shi zucuyarki takeso ko?"ya marairace idanuwansa suka kankance "ah ah"tace
a sanyaye ta share hawayenta tace "ina sonsa ne ina tsananin kaunarsa bansan meye kulawa da soyayya
ba sai akansa hakan yasa nakasa ciresa daga zucuyata,yaya sam.....ka taimakeni ka mantar dani yaya
man"ta fashe da kuka ya rungumeta yayi shu'umin murmushi cikin zucuyarsa yace "yesss nasamu
dama"yana shafa kanta yace "zan mantar dake shi ciki kuwa harda bazan taba bari kwayar idonki su hadu
da nasa ba yadda hakan bazai fama miki ciwon dake cikin zucuyarki ba yayi miki"ta jinjina kai zucuyarta na
cigaba da bugawa,ajiyar zucuya Sameer yayi dama neman yadda zai raba haduwarsu yakeyi bayaso Dina ta
hadu da mansoor dan tana haduwa dashi zata gano gaskiya komi zai iya lalacewa,yayi kisshing dinta a
cheeks dinta ta zumburi baki yayi murmushi"am sorry"ta fahimci wanan kalmar ya kura mata ido ya kalli
jan bakinta,ya karasa gaban mirror ya ciro tissue paper yazo daf da ita suna shakar numfashin juna ya soma
goge mata"banason kina irin wanan kwalliyar ta yan kauye a hakan ne zan kaiki makaranta kina irin
wanan"take tace "dagaske zaka kaini"ya gyada mata kai yana goge mata yana murmushi yace"zan rinka
kaiki daddare inda zaa koya miki kwalliya da gayu irin na yan birni"tayi murmushi tausayinsa ya kamata
yana sonta amma zucuyarta na wajen abokinsa tayi masa adalci?jan hancinta yayi yace "saina dawo"tace
"toh"ta sunkuyar da kai ya fice,

a harabar gidan yayi karo da khairatu ganin yanayinta saida gabansa ya fadi "yaya dai?"ta watsa masa wani
kallo tace "kagama?"ya hade rai yace "look sauri nakeyi zani dauko mansoor a Airport"da sauri tace "zan
bika"ya girgiza kai yace "bazaki wahalar mun da baby ba beyi kwari ba"ta cije lebe tace "yau danka yana
bukatarka daddare dan saika zuba masa ruwan da zaisa yayi kwari,idan ba haka ba kakanninsa zasusam
waye ubansa"gabansa ya yanke ya fadi wani jiri yaji yana daukarsa ta barsa nan tsaye mai khairatu ke nufi?
barazana takeyi masa?ya cije lebe yace "cikin da kike amfani dashi wajen damun dama a wajena idan
nagadama zan barar dashi batare da kinsaniba"ya furzar da iska mai dumi ya wuce ya shiga mota yaja...
WAI NIKAM DIK INA SOYAYYAR LITTAFIN MAZA BIYUN NE?😩😩

*DIK WADDA KESON LITTAFIN MAZA BIYU DAGA YAU ZUWA JIBI A GAMA FREE PAGES TA TURA 400
MEMAKON 500 IDAN VIP TAKESO TA TURA 600 MEMAKON 700,WAI NIKAM DIK INA SOYAYYAR LITTAFIN
NE?HANZARTA MANA KI BIYA A JEFAKI A PAID GROUP KIGA YADDA WASAN ZAI KASANCE?*

*2255398727*
*ZENITH BANK*
*AMINA JIBRIL*

*SHAIDAR BIYA TA 07042277401 KO 08036953516*

*SLIMZY*🥰😍
07042277401
[19/11, 09:56] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

*mai Bukatar a tallata masa hajarsa ya tuntubeni ta 07042277401*

*18*

Slm ina maiso taga tayi K'IBA jikinta yayi kyau tazama yar lukuta 😘ina maiso taga NONO yacika yayi kyau ina
maiso taga duwawu yafito kinzama cikakkiyar mace ina maza da basacin abinci ina maza masuso suyi kiba
ina yara da basuda kiba ina mai farin cikin sanar daku zumar kiba, zumar kiba zumace wadda zata saka kiba
cikin kwana 7 dayardar Allah zumar kiba zumace mai inganci wadda aka hadata da magun gunan
gargajiya,Bugu da qari har nafdac ta amince da lafiyar zumarmu ta bamu BACH NO hjy indai kina fama da
rama d'an gwada shan zumar mu kisha mamaki indai kasha zuma saika chanza Maza kinemi mmn khairat
domin samun ingantacciyar zumar qiba Mai cike da lafiya with zero side effect🤗 08167453086

Tuki sameer yakeyi cikin shaukin ganin Amininsa mansoor dake zaune a gefen mai zaman banza ya jingina
hannunsa rike da wayarsa yana kallon hoton Dina,jin shirun yayi yawa sameer yace "yadai shugaban yan
miskilanci na kasa?koda yake naga sauyi ka canja sosai komi naka ciki kuwa harda yanayin maganarka tun
kafin kabar kasar"murmushi man yayi yayi zooming hoton Dina ya dagowa sameer yace "dole kajini shiru
ina kallon madubina,kuzari na sanan peace of mind Dina i cant wait to see her nayi kewar ta dayawa"cije
lebe sameer yayi take fuskarsa ta sauya wani irin kishi yaji ya daki zuciyarsa wanda yasa ya dauke wuta na
wasu yan dakiku mansoor yace "yadai naji kayi shiru?wai nikam tunda nabar kasar nan kaje kauye ka
ganomin Dina kuwa?"ya danne zucuyarsa dakyar ya seta natsuwarsa yace "naje mana koka manta na
hadaku a waya saidai baku gama maganaba mahaifinta ya bullo shine dalilin datse wayar"mansoor ya
gyada kai yace "amma kasan zamuyi rikici da mutumin nan?domin ba saboda kowa nadawo kasar nan ba
sai saboda Dina bansan haka so yake ba saida nayi nisa da abinda zuciyata ke mararin so,kawai sai gani ina
rashin lafiya a Cyprus?tsananin son da nakeyiwa Dina yasa koda shedaniyar nan tee dan maliki ta bini kasar
nan dan tasamu kaina nakasa ,gues what kasan rabona da shaye shaye har na manta a sanadiyyar soyayyar
Dina?ban taba tunanin akwai abinda zai sauyani ya rabani da kayan mayeba sai soyayyar Dina "a nutse
yake jero kalaman wadanda ke barazanar tarwatsa zuciyar sameer wanda ya cika fam da kishi nan da nan
idanuwansa suka kada sukai jajir yanajin yadda amininsa ke tsananin son matar da ya aura?ya mansoor
zaiyi idan yasan Dina tayi aure?take zuciyarsa ta bashi amsa da dole ya hakura,

mansoor ya bugi kafadar Sameer wanda yayi zurfi cikin tunani yace "kai wai meyake damunka ne haka?
kamar baka farin ciki da dawowata"da sauri ya girgiza kai cike da kulawa yace "nayi matukar farin ciki nayi
kewarka sosai man....look tunda katafi ko aiki bana fita babu inda nake zuwa"cike da zolaya mansoor yace
"kana makale tare da Amarya ko?"ya shafi sajensa, Sameer yace "aure akwai dadi"mansoor ya gyara zama
"really?woooow har nakosa naje muyi wacce zamuyi dasu momy dan Wallahi bazan auri Nabeeha ba Dina
itace muradin zuciyata"Sameer yace "kaidai ka kwantar da hankalinka yanzun ka shigo kasar fa?ko gida
bamuje ba"mansoor ya janyo wayarsa ya kalli agogo karfe shida da minti talatin yace "yanzun yamma tayi
ko?ya zaayi mu shiga kauye yau sameer?bazan iya bacci ba idan banga Dina ba"ran sameer a Dan bace
yace "kai kadameni da zamcen Dina Dina kai ko hirar kewar juna bamuyi ba zaka ganta ka kwantar da
hanlalinka"mansoor ya kwantar da kansa a jikin seat ya lumshe ido yanajin wani iri haka kawai ya samu
kansa da rashin natsuwa burinsa be wuce yayi tozali da muradin zuciyarsa ba,meyasa yake ganin sauyi a
tattare da sameer ne?kodai akwai abinda sameer yake boye masa ne?"ya bude idonsa daidai sameer ya
karya kwanar shiga layin gidansu "yadai kai nayiwa momy alkawarin a gidanku zanci abinci fa Kuma abincin
Amarya"sameer ya ja gauron numfashi cike da faduwar gaba ya kalli mansoor yaga ya kafesa da ido bayaso
ya fahimci akwai abinda yake boyewa,tayaya zai bari suje gidansu cin abinci bayan Dina tana nan?"momy
batanan sun fita wallahi sunje gidan momy rumah hamida batada lafiya ta kwanta a asibiti har an
sallamota"mansoor yace "its okay no problem ko gobe idan munje kauye mundawo sai muje naga amarya
ko?"sameer ya cije lebe yana murmushin yake ya danna horn,

A guje momy da su rufaida suka fito daga ciki zaheed kaninsu sai tsalle yakeyi daddy na tsaye ya harde
hannuwansa a kirjinsa yanata murmushi,cikin farin ciki mansoor ya bude kofar mota da sauri rufaida tayi
huging dinsa "nice ta farkon ganinka nice ta farkon hugging dinka welcome back yaya man"yaja hancinta
yana murmushi zaheed ya rungumesa ya karasa "barka da yamma momy da daddy"momy sai kallon dan
nata takeyi cike da farin ciki saidai yadan rame yayi baki,

"mansoor meyasameka haka naga ka rame?"daddy ya tambayesa yana rukosa suna kokarin shiga yace
"nadanyi rashin lafiya ne kwana biyu"tare suka Shiga duka kowa ya zauna a parlor, Sameer ya dubi
nabeeha wadda keta zuba murmushi yace "ke baki hugging din nasa ba"ta sunkuyar da kai momy tace"to
rasa kunya a gabanmu zata rungumesa"sukayi dariya sai lokacin mansoor ya dago suka hada ido da
nabeeha,wata faduwar gaba yadanji cikin zucuyarsa yace "hasbunallahu wa niimal wakeel"ita kuwa farin
ciki ne ya lullubeta dan sun hada ido tabbas kwallin da ummah ta bata ta tabbatar mata sunan kwallin
idona idonka da zarar sun hada ido zai makance da kaunarta zai manta da wata yar kauye,"Barka da zuwa
yaya man"tace cikin siririyar muryata ,yayi shiru tamkar baiji ta ba momy tace "mansoor bakaji nabeeha
tana maka sannu da zuwa bane?"ya juyo suka kara hada ido ya wurga mata wani kallo wanda yasa ta
saurin sunkuyar da kai yace "Barka"yayi mata kyau sosai ya kara kwarjini ramar da yayi tayi masa kyau
daddy kare ma mansoor kallo yayi cike da mamaki yace "sameer bakaga abokinka ya canja ba?yayi kamala
ya zama kamili tamkar bashi ba injidai an ajiye shaye shaye an dawo da shirin aure?"mansoor yayi
murmushi masu aiki keta jera kuloli akan katuwar daddumar da aka shimfida,mansoor ya nisa yace "daddy
sauyi kam kaga sauyi canji kuma na canja ciki harda gudunmawar Dina"momy tace "Dina kuma?waye
wanan sabon aboki kayi"mansoor ya girgixa kai yace "ko daya Dina....matar da zan aura kenan wadda itace
silar sauyin danku,itace silar daina shaye shayena,tabbas daddy na dawo da shirin aure kamar yadda kace
ina fatan zaka bani goyon baya yadda na kammala maka wanan aikin nadawo"nabeeha sandarewa tayi a
zaune jikinta ya soma tsuma nan da nam taji wani abu ya sara mata a kai kamar gatari duhu ya soma gani a
wurin,yanzun dik kwallin da tasaka da turaren data murza a goshinta yadda ummahnta tace hankalinsa da
tunaninsa suna wajen wata yar kauye wai ita Dina?Dina?ta maimaita a cikin zuciyarta nan da nam
idanuwanta suka cicciko da kwalla ta d'ago kanta suka hada ido da mommy wadda tausayin nabeeha ya
kamata tace "nabeeha yi serving din yayyin naki abincin da kikayi musamman dansu?"girgiza kai nabeeha
tayi "momy kaina ke ciwo zanje in kwanta"tanayi tana satar kallom mansoor wanda ko kallonta beyi ba
idonsa nakan wayarsa hoton Dina ne a fuskar wayar ta wuce jikinta har rawa yakeyi a fusace momy tace
"yanzun mansoor ka kyauta abinda kayi kenan?daga dawowarka ka dawo dasaka yarinyar nan kuka?a
gabanta kake fadin kanada wadda kakeso?"Mansoor ya dago kai babu ko tsoro yace "au momy kunyarta
zanji?wai dama Zaman jirana takeyi indawo ta aureni? she's not serious dama ta tattara tsummokaranta
tabar gidan nan Dan wallahi babu mai hanani auren Dina"daddy yayi gyaran murya yace "ya isa haka sauka
ga abinci nan Kaci,sameer ga abinci kuci"mansoor ya mike yace "bazanci ba tunda ance itace ta hada
abincin zamuje gidansu sameer muci idan bamu samuba zamu eatery"yana gama magana ya wuce abunsa
sameer ya girgiza kai yaja gauron numfashi yace "kuyi hakuri momy zai canja tunda ansamu sauyi sosai
akansa bari nasameshi, rufaida dafo mana indomie nasan zaici bazai yuwu isowarsa kenan ya zauna beci
wani abuba"yabi bayan mansoor,

daddy ya nisa yace "meyasa kikayi magana?aida kin kyaleshi keda kike lallabimsa akan ya aureta?ai a
hankali zakibishi matukar kinaso yayi abinda kikeso"momy rai a bace tace "yanzun yayi cim fuska sai inkasa
masa magana?ita Dina din yar gidan uban waye?jakar kauye zai kwaso mana?"daddy yace "look hajiya
bana bayanki a wanan fadam gaskiya,bazai yuwu ayiwa namiji auren dole ba idan kin matsa ya aureta you
will end up jin kunya ni yanzun ganinsa da samun sauyi yasa naji inaso ya auri yarinyar wallahi ki duba kiga
yadda ya zama mutumin kirki idan har besamu yarinyar nan ba zai koma shaye shayensa da yawon club da
bin mata kinason haka?babu abinda mansoor ya taba nema a rayuwarsa ya rasa banaso a karo na farko a
rayuwarsa ya rasa abinda yakeso"shiru momy tayo cike da tashin hankali yanzun da wani ido zata kalli
ummahn nabeeha?babbar damuwarta kenan dakyar takai cokali daya na abinci ta mike ta nufi daki wajen
nabeeha.....

********
zama mansoor yayi ya dafe kansa kirjinsa nayi masa zafi da radadi sameer ne ya turo kofar ya shigo dakin
"Daga dawowarka? kafara batawa da iyayenka akan Dina?wanan shine yakin da kace zakayi ka mallaketa?
duba ko abinci fa bakaciba Ranka ya soma baci daga isowarka haba Man ka kwantar da hankalinka mana
koka manta kana tare da Amininka ne?"cikim sigar lallashi sameer ke maganar ya zauna gefen masoor ya
dago kansa da hannunsa yace "kasani tun muna yara banason ganinka cikin damuwa kamar yadda kaima
bakason ganin bacin raina ko damuwata man,meyasa ni zan ganka cikin damuwa nabarka"ajiyar zuciya
mansoor ya sauke "I know na fahimci kun kasa fahimtar irin soyayyar da nakeyiwa yarinyar nan ko kasan
saboda ita nabaro Cyprus nadawo?"sameer ya jinjina kai idanuwansa suka sauya ya shiga damuwa ganin
soyayyar Dina karara a kwayar idon Amininsa tabbas yanason Dina so mai tsanani ya zaiji idan yasan Dina
tayi aure?kuma shi ta aura?bazai iya barwa mansoor Dina ba dikda irin kaunar da yakeyiwa Amininsa zai
iya sadaukar da komi na rayuwarsa ga mansoor amma banda Dina yau kadai daya kasance da ita ya fahimci
irin nishadin da mansoor yasamu lokacin da suke communicating,yana tare da mansoor ne amma
hankalihsa gaba daya Yana wajen Dina da badan mansoor zai fito dauka bama da be fito ba yaji dadin
kasamcewa da ita sosai"sameer ya naga kamar kanada damuwa ko kai bazaka tayani yakin da zan mallaki
Dina ba"sameer ya tsaresa da ido cikin zuciyarsa yace "sorry friend narabaka da Dina domin nima tawa
zucuyar in mallaka mata abinda takeso"a fili yace "yeah inada wanda ya Fika ne?kaima bakada wanda ya
fini man dan haka ina tare dakai dari bisa dari"suka rungume juna mansoor ya sauke ajiyar zuciya yace "am
hungry amma bazanci abincin da waccen jahilar yarinyar tayi ba"be karasa magana ba rufaida ta turo kofar
bakinta dauke da sallama da tray da plate da cokula akan kamshi ne ya gauraye dakin cikin sigar tsokana
sameer yace "anya bazan daukeki aikin zuwa ki koyawa amaryata girki da kwalliya ba"rufaida ta tabe baki
tace "abinda munje gidan da momy"gaban sameer ya fadi bakinsa na rawa yace "kunje kun
ganta?"mamaki ya kashe rufaida ganin yadda sameer ya firirice tace "ehh munje amma tana kulle a daki
har muka fito bamu samu ganinta ba rowar ganinta kakeyi mana yaya sameer"ajiyar zuciya ya sauke da
basu ga Dina ba dan yasan da rufaida ta ganta Tabbas zata tambayeta sunanta zataga kamanninta zata
fadawa mansoor,bayason rushewar abokantakarsu yana tsananin son mansoor bayaso akan mace su sami
matsala,rufaida taja kofar ta rufe mansoor yace "wai tunanin mai kakeyi haka ne?ka sauko mana muci
abincin dakasa ayi"sameer ya sauko ya dauko cokali yana danna waya ya bude datarsa sakon khairatu ya
gani take ta fado masa da bukatar ta nason kwana dashi ya dubi mansoor cike da damuwa yace
"man....kasan cewa ban auri khairatu ba"da sauri mansoor ya hadiye abinci jin Yana neman sarke masa
yace "meyasa?meyafaru?"sameer ya cije lebe dan dole ya sanar masa idan be fada masa be auri khairatu
ba zasuje gidan kuma zai ganta a gidan zata iya baro masa aiki yace "ehh saida mukazo aure akayi test
akaga tanada ciki"mansoor ya ajiye spooon yace "what?ciki?cikinka kardai kacemun wanan soyayyar da
kukesha kasanta q waje sameer karka fadamun kayi zina da khairatu"jikinsa na rawa yake maganar yana
kallon kwayar idon Sameer,sameer ya nisa ya seta natsuwarsa yace"ba cikina bane ita dai tasam wanda
yayi mata tana nan a gidanmu momy tana rukonta harta haihu a gano wanda yayi mata cikin,kuma kasan
har yanzun maitar sona takeyi?"tsaki mansoor yayi yace "har naji na tsaneta dama dik koke koken da
takeyi maka akan soyayyarka kuyi aure karyane mazinaciya ce?tou waye ka aura?"gaban sameer ya yanke
ya fadi tambayar da mansoor yayi masa ta gigitasa waye ya aura?idan yace masa Dina fa?ya cije lebe
idanuwansa jajir yana kallon mansoor ya kasa magana mansoor yace "umhmmm talk waye ka aura?a iya
sanina baka da budurwa sai khairatu kamar yadda a iya saninka kasan babu wadda zucuyata keso sai
Dina"shiru sameer yayi ji yayi idonsa sun cicciko da hawaye tabbas yayiwa abokinsa laifi na aure masa Dina
da yayi amma yaya shi zaiyi da son nata da yakeyi?

*********
Dina kuwa bayan ta idar da sallahr magriba zama tayi akan dadduma tayi shiru ta hada kanta da gwiwa
tunanin mansoor takeyi shikenan soyayyar dayakeyi mata ta tabbata ta karya ce,tunda ai yasan cewa
sameer ita ya aura amma ya kasa koda cewa su gaisa ita dashi,kenan itace take haukar sonsa amma shi
bayabi ta kanta?wasu zafafan hawaye suka soma zubo mata tabbas tasan mansoor be dace da itaba amma
zuciyarta ta makance akan tsananin kaunarsa ta mance da itadin ba kowa bace daga karshe yayi tafiyarsa
ya manta da ita,yayinda tata zucuyar takasa mancewa dashi,sai Sameer ne ya tallafi rayuwarta ganin irin
gararin da ya hango zata Shiga ya aureta dan sama mata ingantacciyar rayuwa,idan har ta cigaba da son
mansoor batayiwa sameer adalciba duba da yadda yake tarairayarta da bata kulawa anya tayi masa adalci
tana matarsa zuciyarta na makale da soyayyat Amininsa?ta mike tsaye kamar wadda aka tsikara nan da
nan wani irin takaici ya lullubeta meyasa tayi wawtar yarda da Mansoor ta manta takun sakar da sukayi
kafin ma sufara shiri?dama yayi hakan ne dan yayi mata ramuwar gayya,idan haka ne kuwa tabbas zata
koyawa zucuyarta son mijinta sameer sanan saita nunawa mansoor karshensa saita rama abinda yayi mata
indai tana numfashi,saita nuna masa dama zucuyarta bashi takesoba sameer takeso,wani irin tsanar
mansoor ce sabuwa ta darsu a zucuyat Dina cikin mintuna goma,ta waiga tayi toxali da hoton sameer da
mansoor cikin kunar zicuya ta mike ta taka gadonta ta fuzgo hoton ta tandarashi da kasa ji kake tassssssss
tasa hannu ta toshe kunnenta hade da rushewa da kuka tace "natsaneka.....na tsaneka mansoor na
tsaneka bana fatan idanuwana da naka su sake haduwa da juna"ta runtse idanuwanta ta cigaba da rera
kuka cikin sambatu tace "yaya sam....kayi kadawo ina sonka zan sanar maka da nafara sonka sabanin son
da nakeyiwa Amininka"ta fada kan gado ta Shiga rera kuka mai ban tausayi....

******
sameer mikewa tsaye yayi jikinsa a sanyaye yace"wata ce na aura baason rainaba sabanin su momy sun
rigada sunsaka ranar auren shiyasa na amince da aurenta daga baya naji ta kwantamun a zucuya shiyasa
naso ace ka amince da bukatar momy ka mance da Dina"mansoor ya girgiza kai yace "nidakai ba daya bane
ta wanan fannin sameer sorry naji zafin abinda khairatu tayi maka amma bazan iya amincewa da auren
Nabeeha ba bayan idan nayi hakan naci amanar Dina mun kulla alkawarin zamuyi aure dan mucigaba da
kawance da ita har karshen rayuwarmu,tabbas idan narasa Dina mutuwa zanyi sameer dan haka ka shirya
gobe zamuje kauye da sassafe ko breakfast bazanyi ba ita nakeso nafara gani"jikin Sameer ya kara mutuwa
yanajin tausayin mansoor na ratsa sassan jikinsa tabbas yasan akwai kura tayaya zai rakasa kauye neman
Dina bayan yan kauye sunsan shine ya auri Dina kuma harda mahaifinta?gumi ne ya karyo masa yana
kokarin bude handle din kofa yace "saida safe kayi wanka ka kwanta ka huta"mansoor ya jinjina kai yana
murmushi yace "ka gaida Amarya sai mundawo kauye zamuje na ganta take care"dakyar Sameer ya motsa
kafarsa cike da damuwar yadda zai bullowa mansoor akan zuwa kauye ga khairatu tana jiransa......

*INA MASOYA LITTAFIN MAZA BIYU MAI KUKE JIRA BAKU TURA KUDIN SHIGA PAID GROUP BA?MAZA
HANZARTA KI BIYA 400 KAFIN FREE PAGES SU KARE KI BIYA 500 JIBI ZAN DATSE BAYARDA FREE PAGES
HANZARTA KI BIYA TAFIYAR DA BABU NADAMA VIP 600 MEMAKON 700 ZUWA JIBI....*

*2255398727*
*ZENITH BANK*
*AMINA JIBRIL*
*SHAIDAR BIYA TA 07042277401 KO 08036953516*

*SLIMZY*😍
*07042277401*
[20/11, 11:45] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

*19*

Slm ina maiso taga tayi K'IBA jikinta yayi kyau tazama yar lukuta 😘ina maiso taga NONO yacika yayi kyau ina
maiso taga duwawu yafito kinzama cikakkiyar mace ina maza da basacin abinci ina maza masuso suyi kiba
ina yara da basuda kiba ina mai farin cikin sanar daku zumar kiba, zumar kiba zumace wadda zata saka kiba
cikin kwana 7 dayardar Allah zumar kiba zumace mai inganci wadda aka hadata da magun gunan
gargajiya,Bugu da qari har nafdac ta amince da lafiyar zumarmu ta bamu BACH NO hjy indai kina fama da
rama d'an gwada shan zumar mu kisha mamaki indai kasha zuma saika chanza Maza kinemi mmn khairat
domin samun ingantacciyar zumar qiba Mai cike da lafiya with zero side effect🤗 08167453086

Jiki babu kwari sameer ya shigo babban parlorn momy inda ya sameta ta shimfida dadduma zata tada
sallah ta tsaya tana kallonsa"yadai ina mansoor din?ya naganka kai kadai bayan yacemun a nan zaici
dinner?"sosa keya sameer yayi muryarsa a sarke yace "gida muka tafi dashi yaci abincin a can amma
yacemun idan anyi sallahr isha'i zaizo ku gaisa ya naganki ke kadai ina khairatu?"tace "suna ciki itada
hamida wadda naje gaisarwa na tarar taji sauki shine muka taho tare gashi yamma tayi inaga dai kwana
zatayi"ya jinjina kai zai wuce tace "wai ya naganka kamar bakada kwari?meke faruwa kake boyemun
sameer?"sameer yayi shiru ya kalleta idanuwansa sun kankance yace "babu komi momy bari na haura
sama indan watsa ruwa jikina babu dadi"tace "amma meyasa kake kulle yarinyar nan a sama ita kadai idan
wani abu ya sameta fa?ka kyauta kodai akwai wani abu da kake boyewa?"sameer ya girgiza kai cikin
zucuyarsa yace "momy bazaki ganeba yanzun ne lokacin da zan tsaurara boye Dina sakamakon mansoor ya
dawo bazan taba bari yasan tana tare daniba dan ban shirya tarwatsewar abokantakarmu ba ban shirya
rabuwa da ita ba yanzun ne nakejin wani abu mai girma akanta nafara sonta sosai"momy ta saki baki tana
kallon yadda fuskarsa ta sauya ya zurfafa cikin tunani,"idan kagama tunanin saika haura kaga ni sallah
zanyi"yadan furgita daga tunanin da ya fada ya soma takawa a hankali ya fice daga parlorn yana kokarin
fara taka matakalar benen da zata sadashi da sashen Dina yaji an ruko hannunsa "ina zakaje kake sand'a
kamar mara gaskiya?bakaso na ganka ko"tayi maganat cike da kissa cikin sigar rad'a take maganar ya juyo
da sauri suka hada ido da khairatu cikin wata arniyar riga iya gwiwa babu bra a jikinta bakar riga ce wadda
ta karbi jikinta sosai idonsa ya sauka akan hips dinta da suka baje,tayi murmushin keta tace "nashirya ma
zuwanka ai bakaga rigat danasa ba babynka dake cikina yana bukatar babansa"tana maganar tana shafa
cikinta,wani miyau mai kauri ne ya taru a bakinsa dakyar ya hadiye,tana kokarin hada jikinsa da nata yadan
tallabota yana waigawa "meyasa kikeso sai momy ta fahimci akwai wata alak'a tsakanina dake
khairatu?"cikin mamaki ta ware ido tace "Alak'a kam akwaita tunda cikin dake jikina naka ne sanan kana
nufin soyayyarka dake dankare a cikin zucuyata inyi yaya da ita?hmmm sameer yanzun ne nake kara sonka
nake kara kwadayinka tunda ka lasamun zumarka"ta damko bananarsa tana wani irin murzawa tana hada
kirjinta da nasa take abar ta mike tsaye tana kokarin hade bakinsu taja da baya yace "idan momy tazo ta
ganmu a nan fa?"murmushi tayi tace "zanso hakan kaga shikenan sun samu amsar da suke nema ta wanda
yayi mun ciki sun gano waye uban dan dake cikina kaga shikenan sai ayi mana aure na haifi dana a gidan
ubansa"ran sameer ya baci jim motsin momy yasa jikinsa ya soma rawa cikin sigar lallashi yace "kiyi hakuri
karki tonamun asiri khairatu kinsan ina sonki kaddara tasa na auri Dina badan zuciyata naso ba"tayi
murmushin keta ganin dik yadda ya rude yasa ta sakesa ta hada rai tace"kaje komi dare ina jiranka a dakina
ina bukatarka tsananin shaawa nakeji sosai sameer kuma shaawarka dan haka da zarar momy tayi bacci
wanan kucakar yar kauyen daka aura ta fara jan munshari kazo ka zubamun zumarka idan ba haka ba nayi
maka alkawari da safe zan sanar musu da cewar cikin dake jikina naka ne"tana gama maganar ta barsa
tsaye a wajen ,sandarewa yayi ko motsi ya kasayi meyasa ya fada cikin fitunu?anya ba alhakin mansoor da
Dina bane ya soma kamasa?har khairatu zata rinka yi masa barazana shi sameer matawalle?ya cije lebe
yace "zanyi maganinki zan kawar da matsalarki inji da matsalar dake gabana"ya haye sama cikin sauri ya
tsaya a jikin kofar sautin numfashin Dina yakeji tun daga kofar,nan da nan yasa key ya bude kofar jikinsa na
rawa ya karasa ganinta kwance a kasa jikinta ya dauki zafi sai rawar sanyi takeyi fuskarta tayi jajir yayinda
wasu siraran hawaye kebin gefen fuskarta,

"Dina Dina menene meye yasameki?"ya tallabota jikinsa yaji yadda jikinta ya dauki zafi sosai jikinta sai
rawa yakeyi yace "ya ilahi Dina kiyimun magana"yayi maganar kamar zaiyi kuka,a hankali ta bude
idanuwanta ta saukesu akansa ganin yadda fuskatsa ta sauya ya shiga matsananciyar damuwa yasa dakyar
ta bude baki tace "yaya sameer.....ina sonka kaji zan soka na tsani yaya man....kayi hakuri kaji zan soka
kamat yadda nake sonsa zafin yaudarar da yayimun ne yasa nayita kuka jikina yayi zafi kaji"tausayinta ya
kamasa tabbas Dina tana tsananin son mansoor kamar yadda yake fada da iyayensa akan tsananin son da
yakeyiwa Dina shi mansoor saidai a yanzun bayajin akwai abinda zaisa ya rabu da Dina ya barwa Amininsa
ita,ya bata light kiss a baki sanan ya shafa fuskarta yace "baxaki taba danasanin mallakamun zucuyarki
ba,kamar yadda kika bukata bazan taba barin abinda zai hadaki da mansoor ba duk runtsi dan ni aminina
ne kinga babu yadda zaayi mu rabu ko?"ta gyada masa kai,wani sanyi yaji a cikin zucuyarsa tabbas zuwa
lokacin da kaddara zata hada mansoor da Dina tayi nisa a tsanarsa kuma kome zai fada mata bazata
sauraresa ba,kamar yadda yasan idan mansoor yaje kauye nemanta akace tayi aure dole zai hakura da ita
ya auri nabeeha shikenan yasamu nasarar mallakar Dina na har abada"ya kara rungumeta sosai a jikinsa
yana kara jin wata sabuwar kaunarta a cikin zucuyarsa yanzun zaiyi iya kokarinsa wajen ganin ya mantar da
ita mansoor wajen ganin ta saba dashi koda kaddara zata hadasu gaba....ya ciccibeta ya kwantar da ita a
kan gado yace "ina zuwa"ta gyada masa kai ya tafi kitchen jikinsa na rawa dik tausayinsa ya kamata tabbas
sameer shine kesonta da gaskiya,jim kadan ya dawo da wata pink din roba da sabom towel a hannunsa ya
bude bathroom ya shiga ya dibo ruwan mai sanyi ciki ya fito ya ajiye a gefe ya tallabota yana kokarin cire
mata kaya ta rike hannunsa "yaya samm me zakayimun?"tace idonta cikin nasa,wani abu yaji yarrrr yace
"Dina zan danna miki jikinki ne zaki bar jim zazzabin kinji?ni mijinki ne koda naga jikinki babu komi kuma ai
ba iskanci bane ai ko?"yayi maganar cikin sigar lallashi tayi jimm kadan gabanta na cigaba da tsananin
faduwa yayinda zucuyarsa ke harbawa sauri da sauri yanajin wata irin shaawa na taso masa tana
fuzgarsa,yasan khairatu tasan lagonsa tasan dik inda zata taba a jikinsa ta motsa masa shaawa mugunta
tayi masa yadda ko bayaso dole ya bita,muryar Dina ta dawo dashi daga guntun tunanin da ya soma dakyar
take magana "malamar mu ta kauye tace namiji indai mijinka ne shine halalinka ko?ko hannu baaso wani
ya rike maka"sosai ta bashi dariya yace "haka ne shiyasa nakeso na cire kayanki na goge miki jiki na
rungumeki a jikina kiyi bacci ko?"ta jinjina kai sanan cike da shagwaba tace "umhmmm umhmmmm
ummmm nidai ka rufe idonka karka ganinmu nono na"dariya ce ta tasowa sameer cikin zuciyarsa yace
yarinyar nan kamar tasan abinda yafi daukar hankalina a jikinta kenan?ya runtse idonsa yana murmushi
yace cikin ransa yarinya dole ne in matsa wadanan abubuwan,a hankali yake shafa jikinta da ruwan da yasa
towel ciki tsirara yayi mata cikin kunkuni tace "nima na rufe idona"yana jin haka ya bude idonsa yaga
yadda take saida ya hadiyi wani miyau ya tsurawa surar jikinta ido.....

*******
juyi mansoor yayi ya kalli agogo karfe tara saura na dare ya lumshe idonsa ya bude "ko meyasa lokaci
baya sauri oho,shi ya kosa dare ya tsala gari ya waye yaje yaga Dina ya Kosa yaga sanyin
idaniyarsa,rigingine yayi akan gado yana kallon fankar dake kadawa a cikin dakinsa yayi murmushi yace
"nasan har yanzun kina nan da shiriritarki ko Dina"dik maganar da yakeyi besan momy ta bude kofa ta
shigo ba,mamaki ne da al'ajabi ya kasheta ta tsura masa ido irin kyau na sameer da aji hade da asali
zucuyarsa ta rasa dawa zata kamu da so sai yar kauye? ta girgiza kai dole zata kwantar da kanta ta lallabesa
tayi masa wayau yadda zai Amince da auren Nabeeha daga baya ya auri yar kauyen da yake kira da Dina,ta
karaso tana murmushi shima kallonta yayi yace "ah ah momy "ganin tana murmushi yasa ya sauke ajiyar
zuciya sai kuma baiji dadin yadda yayi mata ba dazun gashi dikda haka ta biyosa koda yake uwa uwa ce,

"Mansoor zuwa nayi da wata shawara muyi magana bansaniba ko ita zatayi maka tunda naga alamar dik
abinda nakeso kai baka sonsa"cikin sigar lallashi take maganar,mikewa yayi ya zauna bece mata komiba sai
manyan idanuwansa daya zuba mata,tasan halinsa beson magana yasa tace "Dama cewa nayi tunda Daddy
shima ya amince da aurenka da yarinyat da kakeso zamuyi yadda kakeso mansoor me zaisa bazaka amince
ka auri nabeeha ba ita kuma waccen ayi bikinku daga baya?"tsareta yayi da ido yadda take maganar cikin
lallashi da tarairaya yasan halin momy babu yadda zaayi ta Amince kai tsaye da auren ba kauya yar
talakawa yadda dik duniya babu wanda take kyama kamar talaka,yasani sarai wayau takeso tayi masa dan
haka yace "tou shikenan na Amince amma da sharadi daya"cikin sauri momy tace "fadi sharadinka koma
menene zanyishi tunda zaka fitar dani kunya ka auri yarinyar nan nabeeha"mansoor ya girgiza kai yace
"zanje kauye gobe idan naje nadawo sai daddy yaje ya tambaya mun aurenta yakai sadaki idan nadawo sai
a fara shirin aurena da nabeeha da anyi sai waccen a dauramun aure da ita"momy kamar ya mike tayi
tsalle tace "na amince mansoor"mansoor yayi murmushin mugunta,momy itama murmushin tayi cikin
ranta tace "koda an kai sadaki tsaf zaa warware mubar musu sadakin da zarar ka auri nabeeha"ta mike
shima ya bita da kallo yace "idan na tabbatar ankai sadakina dole zaku auramun Dina baxan amince da
auren nabeeha ba,momy ta fice mansoor ya janyo wayarsa cike da zumudi dole zai kira sameer ya sheda
masa momy ta amince da aurensa da Dina,yadda sukayi dole ya fada masa dik duniya bashida Aminin daya
wuce sameer matawalle....

Sameer lumshe idonsa yayi yasa bakinsa akan nipple din Dina ya soma tsotsa cike da kwarewa jikinta ne ya
soma rawa tana kokarin janye kansa"ni banaso ni banaso yaya sam....banaso kaji "ya dago kansa
idanuwansa jajir har dishi dishi dishi yake gani tsananin shaawar ta da yakeji cikin rada yazo daidai
kunnenta yakai hannunsa kan breast din yana dan kamawa"nace miki a hankali zanyi miki kuma ni mijinki
ne zakiji dadi nima zanji kuma zamu shiga aljanna ko bakyasi"ta jinjina kai "zamu Shiga aljanna?inaso
kayimun a hankali"muryarta na rawa tayi maganar kiran wayarsa ne yasa yadan bude idonsa,tsaki yayi
waye wanan yake kiransa a wanan lokacin dayasamu dama?ya fuzgo wayar yaga mansoor ne,bazai iya
kyale kiransa ba ya dauka muryarsa a dashe Mansoor bedamuba yace "sam....kasan momy ta amince da
aurena da Dina?"cikin sauri sameer ya rage volume kar Dina taji me mansoor ke fada ya lalata mai ginin da
yayi yace "good lets talk in the morning nafara bacci"mansoor be damuba yace "okay"ya kashe wayar
sameer kara rungumar Dina yayi cikin salonsa da yake kashe khairatu dashi ya soma tafiyar da ita yadda
yake shafa jikinta yasa gaba daya jikinta ya mutu sarrafata yakeyi yadda yakeso haka ya bude kafarta yasa
bakinsa ya soma mata wani gigitaccen sucking wanda yasa tayi yar kara da dan nishi wanda hakan yasa
sameer haukacewa ya tabbatar da Dina najin dadin abinda yakeyi mata,ya mike jikinsa na rawa ya karasa
gaban dressing mirror ya dauko olive oil ya shafa a bananarsa yadda yasan bazaiyi hurting dinta ba yazo
yana kokarin turawa jikinta na rawa ya hade bakinsu waje daya hannuwansa a kirjinta ya soma
bidirinsa,wani irin dadi yakeji da be taba jinsa ba a rayuwarsa har cikin kwakwalwar kansa yakeji nishi
yakeyi yana kiran sunan Dina.....

******
khairatu na zaune gefen gado ta fito da sakon ummah ta dauki wayarta ta bugawa mahaifiyarta jimmm
kadan ummahnta ta dauka tace "ya naga kiranki a wanan lokacin?ai nadauka kinsamu kan Sameer
kingama dashi"khairatu ta cije lebe tace "zaizo dolensa dan na gindaya masa Sharadi idan bezo ba zan
sanarwa matawalle cewar cikin dake jikina nasa ne"mahaifiyarta tayi dariya tace "dakyau dole kuma dan
yazo duniya ni Allah yasa yayi kama da kakansa yadda zaici sunan matawalle dakyau mu gaji arziki"khairatu
ta girgiza kai tace "ummah dolene in koyawa Sameer hankali kodan amanata dayaci ya rabani da budurcina
yayimun ciki sanan ya bar ni ya auri wata,na tabbatar wanan abun matsin da kika bani da zarar yayi amfani
dani koda ya kusanceta bazaiji dadinta ba tunda mai aikin gidan nan ta tabbatarmun be taba kwanciya da
waccen jakar ba"ummah tayi ajiyar zucuya tace "dakyau yanzun ne muka samu dama ai wanan cikin ma
alheri ne"khairatu tayi murmushi tace "nasa a gabana na kuma sha wanan na sha din yanzun shi kawai
nake jira yazo dan dole nasan zaizo nasan bacci yake jira tayi bari nakirasa"sukai sallama da ummah ta
kashe ta soma laluben kiran sameer,

ya fito wanka daure da towel wayarsa ta soma haske,gabansa ne ya fadi ganin kiran khairatu ya kalli Dina
wadda ke bacci sosai ya taba jikinta yaji babu zazzabi,ransa ya baci yaso ace ya kwana tare da ita wanan
zumar daya lasa wata sabuwar shaawarta yakeji amma yasan khairatu zata aikata abinda take nufi saidai
shima zuwa safiya zaiyi maganinta dan tabbas abinda take tutiya dashi cikin jikin nata zai salwantar dashi
sanan zai rabata da gidan harabada,kara kiransa tayi yasa hannu ya dauka yace "umhmmm
what?"murmushin keta tayi tace "ina jiranka yanzun"

"momy tayi bacci ne?"ya tambayeta muryarsa kasa kasa tace "yeah i think so "

"okay am coming"ya katse wayarsa ransa a bace ya zura jallabiya ya nufi wajen khairatu cike da bacin
rai.....

*******
wajen asuba dakyar khairatu tabar sameer ya baro dakinta wadda dik abinda sukayi tasa hamida da tayi
kamar tana bacci ta dauka a wayarta ya fito cikin sauri daidai momy ta gifta jikinsa na rawa ya boye momy
ta dawo da baya a fili tace "waye nagani kamar sameer ya fito daga dakin khairat"ta lalleka bataga kowa ba
ta leka dakin khairatu ta gansu kwance da hamida suna bacci sanan ta wuce,

Dina tayi wanka tana zaune kan dadduma ya shigo yadda tayi da fuska yasa yadan tsorata kardai ta farka
daddare bata gansa ba? ya shigo ya zauna gefenta yayi tagumi yana kallonta ta turo baki gaba ya tsura
mata ido burgesa tayi sosai "yadai nayi laifi nasani ko?"ta jinjina masa kai yace "tou ayi hakuri wanan shine
auren ai ko?kin gasa jikinki da ruwan zafi?"kawai yaga ta fashe da kuka ta fada jikinsa,"ni ka daina
tambayata nidai banida lafiya ka zauna tare dani"a rude yace "yau tare zamu wuni kinji?ba jnda zani inason
shagwabar nan"ta fada jikinsa yana bubbugata,gabansa ne ya fadi tunowa da mansoor fa zai nemeshi suje
neman Dina kauye bayan gashi tare da ita gashi yau din nan jinsa yake sabon ango dan haka ya ciro
wayarsa a aljihu yaga karfe shida da minti arbain,

ya tura masa message *Hey Man good morning sorry please zuwa kauyen nan i cant make it madam ba
lafiya zamuje asibiti idan ka dawo zamu hadu kawai inji ya kukayi idan kaje ka gaida Dina* ya tura masa
sanan ya kara rungumeta ya dagota sosai ya haye gado da ita,

jim kadan Mansoor ya shirya tsaf yaga message din sameer yace "ooohhhh bakomi ciwo nagaba da
komi"yayi masa reply

*idan nadawo zamu hadu mu tattauna*

Sameer na gani farin ciki ya lullubesa dan yasan babu yadda zaayi yaje kauye tare da mansoor wajen
neman Dina bayan yan kauye kowa yasan shine ya aureta....

Mansoor tunda ya dauki hanyar kauyen gabansa ya tsananta faduwa wanda ya rasa dalilin hakan,ya rasa
meke masa dadi ya rasa dalilin dayasa yakejin wani sauyi a bugun zuciyarsa kodan zai hadu da Dina ne?......

kunada labarin gobe free pages zasu kare?mai kike jira ki hanzarta ki tura 400 memakon 500 garabasa
zuwa gobe normal group vip 600 memakon 700 two pages a rana
2255398726
zenith bank
Amina jibril

shaidar biya ta 07042277401 ko 08036953516

*SLIMZY*😍
[21/11, 09:43] Slim girl❤️: 💥 *MAZA BIYU....*💦

*NA:SLIMZY*
✍🏻
Wattpad@slimzy33

*Marubuciyar:*

*K'ADANGARUWA*🦎
*RUD'ANI*💥
*DUHU...*

*INA MASOYA LITTAFIN MAZA BIYU?MAI KIKE JIRA A WANAN TAFIYAR?KINADA LABARIN WANAN SHINE
LAST FREE PAGE? HANZARTA KI BIYA 400 NAIRA PROMO A MAIMAKON 500 DA MARUBUCIYAR TAYIWA DIK
WANI MASOYIN LITTAFIN MAZA BIYU MASUSON VIP 600 MEMAKON 700 INA MASOYA?*

*2255398727*
*ZENITH BANK*
*AMINA JIBRIL*

*SHAIDAR BIYA TA 07042277401 KO 08036953516*

*20*

Hameeda mamakin khairatu takeyi tana jujjuya wayar da videon da sukayi na dik abinda ya wakana daren
jiya itada sameer tace"zan tura masa wanan videon amma sai yayi yunkurin bijirewa bukatuna na dik
abinda nace masa inaso ko kuma yayi yunkurin aiwatar da wani abu akaina zan nuna masa shi karamin dan
cin Amana ne,dan waccen kucakar da yake makale da ita a d'aki ita zan fara nunawa wanan videon dan
tasan abinda ta aura dan inada tabbacin kwadayi ne yasa ta aureshi"hamida ta jinjina kai tace"ki tura
videos din ban dik inda kikasan zaa ajiye mikishi ki turawa surayya kawarki"khairatu tace "yess correct
nasan idan natura mata tarkon da nayiwa sameer matawalle sai tafi kowa farin ciki domin a halin yanzun
babu abinda takeda bukata irin nayi ramuwar gayya akan cin amanar da yayimun"hamida tace "kamar na
Allah sai gashi yanata numfarfashi kamar wanda aka dorawa kaya"suka kyalkyale da wata mahaukaciyar
dariya suka tafa,momy ce ta kwankwasa kofar yasa sukayi tsit ta tura kofar tana tsaye tana binsu da kallon
tuhuma tace"nikam wai dararrakun mai kukeyi haka ne?kundaisan daddy na cikin gidan nan hai fita ba
kuma yayanku yana sama shima nasan bai fita ba in zakuyi ku rage murya banson iskanci"momy na cikin
magana sameer ya sauko hannunsa rike dana Dina a karo na farko da Dina ta sauko daga sama tun
zuwanta gidan shima shagwaba tasa masa akan lallai saita sakko ta gaida momy,momy na ganinsu ta fad'a
d'a murmushinta"ah ah idonki kenan tunda kikazo gidan nan ko saukowa bakyayi?"hamida da khairatu
karo sukayi wajen lekowa suga Dina dan rabon da Hamida ta ganta tun ranan da aka kawota,Dina ta
durkusa har kasa tana sanye da wata bakar abaya mai stones golden a jiki sai walkiya yakeyi ta yane kanta
da gyale yadda sameer ya nuna mata kallo daya zakayi mata ka dauka balarabiya ce yadda tayi wani mugun
fari ta kara kyau fararen idanuwanta ta zizara musu kwalli sun kara fitowa da ita sai walkiya takeyi momy
kanta cewa tayi "Tabarakallah y'ata kinyi kyau sosai"wani irin kishi ne ya tasowa khairatu irin yadda taga
Dina tayi matukar kyau dik irin kyau nata da haske sai taga kanta baka kirin akanta,mamaki ne ya cikata
ganin yadda ta sauya bayan hoton da aka turo mata yar kauyece tantagarya,momy ra ruko Dina ta dagota
ta rike hannunta"muje yau tare zamu karya"gaban sameer ne ya fadi bayaso Dina ta dauki wasu mintoci a
kasa tsoronsa kada mansoor yazo gidan idan har bai tafi kauye neman Dina ba ya ganta,bakinsa na rawa
yace"sama zamu hau momy can zamuyi breakfast kisa akai mana"khairatu na tsaye tana kallonsu tamkar
ta sokawa Dina wuka tsananin takaici, cikin zuciyarta tace"zaki zama yar kallo kamar yadda kikazo daga
kauye haka zaki koma ki auri bakauye ki koma saka badani jaka jar hodar nan mai kama da jar kasa ita ta
dace dake da zarar na nuna miki videon mijinki yana kwanciya dani hade da sambatu"tayi guntun tsaki
wanda ya fito fili yasa momy juyowa da sauri ta kalleta itada Hamida wadda tuni ta sandare a tsaye
tace"au kuna ganin yayanku da matarsa bazaku gaisat dasu ba"kallon da khairatu tayiwa sameer yasashi
Hadiyar wani miyau mai kauri yace"sun gaishemu bakiji bane momy Bari mu karasa sama Dina batajin dadi
yanzun ma ta matsa ne mu sauko ta gaisheki"yana maganar yana kokarin ruko hannun Dina a gaggauce
babban tsoronsa da tashin hankalinsa shine kada mansoor yazo gidan dan su tafi kauye dikda ya fada masa
bazaijeba,"meyake damunta kuje asibiti mana ka kira...."kafin momy ta karasa ya tarbi numfashinta yasan
mansoor takeso tace sam bayaso a ambaci sunan mansoor kada Dina taji a fama mata ciwon dake cikin
zuciyarta yasan cewar bawai ta hakura da son Aminin nasa bane"momy taji sauki jiya kin kwanta lokacin
danasa aka duba ta"Dina ta kallesa jin yayi karya yasan tsaf zata karyatasa yasan wawtarta yasa ya hada rai
yana kallon irin kallon da takeyi masa a gaggauce yaja hannunta sukayi sama,momy ta bisa da kallo tana
murmushi a fili momy tace"kila an samu karuwa ne"tana yar dariya khairatu ta ce cikin ranta "kina gab da
maraba da jikoki da dan sunnah da dan shege"momy ta wuce parlor khairatu cike da kishi ta kasa sukuni ta
soma sunturi a cikin dakinsu hamida tace "wai kinga yadda yar kauye tayi clean wallahi nadauka balarabiya
ce"khairatu ta toshe kunnuwanta cikin daga murya tace "ya isa Hamida"Hamida ta kama bakinta ita ta
kosa taje gida ta shafawa momy Ruma badakalar da akeyi a gidan matawalle......

*******
Anty zali kanwar momy na zaune suna fuskantar juna da momyn Mansoor tace"niko inaga wanan dabarar
da kikayi akan mansoor kin amince da aurensa da Dina yar kauye tamkar yaudara ce kinsan halin mansoor
sarai idan har baku amince da aurensa da muradin ransa ba to wallahi koda kun aura masa nabeeha zai iya
sakinta dan ya kunsa muku takaici,inaga gara ku lallabasa ya auri Dinar daga baya saiya auri nabeeha kinga
bazaiyi musu ba tunda yasan cewar kunyi masa abinda yakeso sanan ina mai tabbatar muku idan har kuka
hanasa Dina to tabbas wanan shaye shayen daya bari zai koma kuma babu wanda ya isa ya hanasa"shiru
momy tayi tana sauraren kanwar tata jiki a sanyaye tace "zaliha kin kawo shawara dan tabbas mansoor zai
iya bijiremun ya rabu da yarinyar nan kina ganin farin cikin da takeyi yau tunda ta wayo gari da labarin ya
Amince da aurenta"Anty zali ta gyada kai tace"idan ya dawo kauyen zan kirasa zamuyi magana zan
lallabesa yadaina wulakanta nabeeha kema kuma karki nuna masa kiyayyar da kikeyiwa abinda yakeso
gudun kasa ya bijirewa bukatarki tunda idonsa ya rufe akan wanan yarinyar"momy tace"haka ne,yanzun
zan fara shiri amma wallahi niba wani d'okin auren sa da yar kauyen nan nakeyi ba"Anty zali tayi murmushi
tace "koma menene dai ayiwa yarona abinda yakeso,yanzun zan biya kasuwa zan duba wasu abubuwan
afara siyayyar ita waccen ko?"momy ta tabe baki tace"me zaa siya mata banda dangwali yab'a da bad'ani
jaka hodarsu ta kauye ai komi daidai da ita zaayi tunda already nabeeha an rigada anyi siyayyar aurensu
tun kafin tafiyarsa cyprus"dariya kawao Anty zali tayi ta dibi makullin motarta tace "koma dai menene komi
kauyancinta surukarmu ce haka zamu karbeta"ran momy ya baci ji takeyi tamkar ta kashe tsinanniyar
yarinyar nan idan mansoir ya aurota yadda taki jinin talaka?talakar ma ta kauye?batasan wace kalar
yarinya bace mansoor ys susuce akanta a kauye,tayi tsaki suka jera suka fito daga sashenta suna tafe suna
kara tattaunawa....

******
Mansoor mamaki ne ya kashesa gabansa sai faduwa yakeyi yana kallon tankamemen gate din dake kofar
gidansu Dina,kofar gidan daya bari da falefale akayisa? gidan kasa da akayi masa yab'e da sumunti?murza
idanuwansa yakeyi yana sake kallon bakin gate din yayinda wasu kauyawa ke zaune gefe akan benci sun
zubo masa ido yana tsaye ya harde hannuwansa a kirjinsa tunani yakeyi kodai ba gidan bane?tou kodai sun
tashi ne daga wanan gidan sun siyar?dakyar ya janyo kafarsa yana takawa jikinsa a sanyaye yace "Assalamu
alaikum barkanku da war haka"yayiwa mutanen dake zaune a kofar gidan sallama,daya daga cikinsu ya
ganesa yace "D'an birni yau kaine a gari mutumin Dina"wani farin ciki ne ya lullube mansoor jin sunan Dina
wato har ansan shidin mutuminta ne?kenan Dina tana sonsa haka?gabansa be daina faduwa ba yayi
murmushi,zaiyi magana yace "ya wajensu Dina?"yana maganar yana washe jajayen hakoransa mansoor
yayi tsaye kamar an dasashi mamakin ya wajensu Dina kuma kafin ya tambayesa ya sake magana "ai
mutumiyar taka nasan tanacan yanzu. ta canja ko?ai infada maka tou kodai bakada labarin Dina tayi aure
ne?"yace yana murmushi ,mansoor take yaji wani abu mai kama da guduma ya daki tsakiyar kansa,nan da
nan wata kibiya ta caki kirjinsa yayi baya da baya kamar zai fadi ya tsaya da kafafuwansa,jikinsa ne ya soma
rawa kamar mazari yayinda zufa ke karyo masa ta ko wace gaba ta jikinsa kamar an kwara masa ruwa,cak
yaji numfashinsa na kokarin tsayawa,ya rufe idonsa na seconds sanan ya bude tare da adduar Allah yasa
mafarki yakeyi ba gaskiya ba,Allah yasa kunnensa beji masa daidai ba"yadai bawan Allah meyafaru?"suka
hada baki suna tambayarsa ganin yadda jikinsa ke rawa yana tangal tangal,"ya ya ?kodai bakasan Dina tayi
aure bane?ai Dina tayi aure sati uku zuwa hudu kenan"take mansoor ya durkushe a kasa idanuwansa yaji
suna kokarin rufewa dakyar ya motsa labbansa ya bude idanuwansa dake rufewa suna budewa yace "tayi
aure?tayi aurefa kace?kasan wace Dina nake magana?"murmushi sukayi suka hada baki "dik garin nan
Dina guda daya ce kuma tayi aure wanan gidan da kake gani gidansu ne canjin rayuwa suka samu"

"Innahlillahi wainnahilaihi rajiun kawai mansoor ke maimaitawa can kasan makoshinsa domin maganarsa
bata fita sosai besan lokacinda hawaye suka fara zubo masa ba,a karo na farko a rayuwarsa hawaye na
zuba a idanuwansa?kuma akan mace?ya dafe kansa garin ke juya masa wata irin hajijiya ce ke kokarin
kayar dashi,yasa hannunsa ya dafe kasa,kirjinsa keyi tamkat ana soka masa allura ,nan da nan ya soma
ganin Duhu wanda idanuwansa ne suka rufe ya yanke jikinsa ya fadi a nan,da sauri suka karasa kansa
"innahlillahi wainnahilaihi rajiun akawo ruwa"daya daga cikinsu ya Shiga bugun gate din gidansu
Dina,mahaifiyarta ce ta bude yace "innahr Dina taimakemu da ruwa wancen ne ya suma"ta dan leka sanan
ta koma cikin sauri ta dibo ruwa a dan jug na roba ta miko masa daidai an tallabo mansoor,tana tsaye tana
lekensa idonta ne ya sauka akan mansoor wanda yasa ta waro ido tana kallonsa,tabbas ta ganesa wato
wanan dan shaye shayen ne kenan?"ta tura kofar gida cike da furgici to meye ya kawosa kauye bayan
abokinsa sameer ne ke auren Dina?har ya suma?tou kodai wani abu yasamu Dina ne?gabanta ya fadi jiki
babu kwari ta zauna akan kujerar robar dake kofar dakinta ta jingina tana sauke nunfashi tana jiyo
hayaniyar mutane,

cika sosai akayi kowa na leken dan birni wanda babu alamar rai a tattare dashi dikda wasu daga cikin
jamaar sunce yana numfashi,daya daga cikinsu ne yace"mukaisa gidan gonarsu inaga zaifi tunda dama
akwai masu kula da gidan gonar"suka daukesa suka nufi gidan gona dashi,

sameer ya fito ya shiga mota kenan ya zauna mansoor ya fado masa a rai tou kodai ya tafi kauyen ne?ya
zaro wayarsa daga aljihunsa ya kamata ya kirasa yaji halin dayake ciki,jikinsa a sanyaye yasan tabbas akwai
matsala,ya soma kiran layin wayarsa,har ta tsinke baa dauka ba gabansa ke tsananin faduwa ya soma kira a
karo na biyu har ta kusa tsinkewa sanan sergent na gidan gona ya dauka "Hello sir"sameer hantar cikinsa
ce ta kad'a a sarke muryarsa yace"ina man din?naji kamar sergent ka dauki wayarsa?"

"ehh sir muna hanyar shigowa gari dama dole zan kiraka domin gashi nan baisam inda kansa
yakeba"sameer yace "what?meyafaru meyasames"

"tou ance wai yarinyar nan ce Dina tayi aure sir shi kuma yazo wajenta ne aka sanar masa shine ya fadi
yanzun muna tahowa inaga ka kira gida ka sanar musu mu hadu a specialist hospital"sameer sandarewa
yayi tausayin mansoor ne ya lullubesa tabbas yasan Amininsa ya kamu da tsananin son Dina yana kaunarta
fiye da komi,shima kuma yanzun ya kamu da sonta Fiye da baya,sameer idanuwansa ne suka cicciko da
hawaye yace "am sorry friend dik halin da kake ciki ka Shiga nine sila sakamakon aure Dina da nayi dan
nima ina bukatarta a rayuwata ina sonta bazan ita sadaukar maka da itaba a halin yanzun,nasan ciwo da
radadin da kake ciki nadan lokaci ne zaka mance da ita koda kaddara ta hadaku ka gano nine na aureta
nasan zaka yafemun"yana maganar muryarsa na rawa hawaye na zuba a idanuwansa,yayiwa motar key
sanan yaja yana kokarin kiran layin daddy ya sanar masa da halin da mansoor ke ciki ciki gaba daya a rude
yake driving,
Daddy yana kokarin shiga parlor kiran sameer ya shigo yace "sameer mutanen kauye nasan kunje zance
ko?"shiru daddy yayi jin yanayin sameer da abinda yake fada yasa yace "Innahlillahi wainnahilaihi rajiun
yanzun ina Mansoor dun?"dukkansu dake parlorn mikewa sukayi tsaye a rude momy tace "yayi hatsari ko?
meyasamesa ya fadi a mota ne?nasan yadda ya kosa yaga almurar yarinyar nan nasan sai wani abu ya
samesa nashiga uku"ta rushe da kuka a rude take maganar rufaida kuwa kuka ta fashe dashi "daddy meye
yasamu yaya man?"

"ku kwantar da hankalinku,yana asibiti ne bashida lafiya ashe batare da sameer sukaje ba shikadai ya tafi
yanzun sameer ya kirani yake sheda masa akan ankirasa Mansoor babu lafiya ya yanke jiki ya
fadi"sandarewa momy tayi a tsaye tace "meyasa zai fadi? meyasamesa ko iyayen yarinyar sun hanasa yarsu
ne?yar gidan uban waye da bazasu bashiba babansa yana dan kasuwa dan majalisa"

"ki kwantar da hankalinki yanzun kuzo mutafi asibitin muga halin da yake ciki"a rude suka firfito sukayi
motoci biyu dana excort suka nufi asibiti....

sameer na Shiga idonsa ya sauka akan mansoor wanda aka sakawa oxygen a hancinsa yana numfashi a
hankali,kasa motsi yayi balle ya taka daga inda yake likitan dake duddubasa yace "kaine sameer?"gaban
sameer ya yanke ya fadi ya jinjina masa kai yace "ehh"dakyar maganarsa ta fito ,doctor yace "bismillah ya
ka tsaya daga nan ka karaso tunda aka kawosa yake kiran sunanka yaki magana"sameer jiki na rawa ya
karaso ya zauna gefen gadon ya ruko hannun mansoir yana murzawa "mansoor calmdown ka kwantar da
hankalinka zaka samu sauki kaji ka farka ka farfado i really need you friend please "yana maganar muryarsa
na rawa,tawagar su momy ce ta iso suka shigo dukkansu sun kadu da ganin yanayin mansoor cikin
kankanin lokaci ya fita hayyacinsa daddy yafi kowa shiga tashin hankali ganin babban dansa daya tilo cikin
wanan halin yace "Doctor meye yasamu dana me akayi masa?idan na rasa Mansour zan dauki mataki
akam kowa ciki harda kai meke damunsa?"Mansoor a hankali ya bude idanuwansa yana kallonsu yayinda
hawaye ke cigaba da zuba a idanuwansa,kallon kowa yakeyi har idonsa ya sauka akan sameer,cikin ikon
Allah dakyar ya bude bakinsa daya kafe ko miyau babu sai wani irin d'aci dake tasowa daga kirjinsa yace
"sameer....sun aurar da Dina,narasa Dina wallahi mutuwa zanyi idan har ban samu Dina ba daddy"a rude
Daddy yace "bazaka mutu ba mansoor zani in nemo maka Dina bazan taba bari na rasaka ba wacece Dina
yar gidan uban waye a kauyen?ko waye mahaifinta zani garesa,zan zube masa kudi sanan zan ajiye mulkina
da komi nawa na durkusa a gabansa ko wa aka aurawa ita a rabasu ta auri Dana bazai yuwuba mansoor bai
taba neman abu ya rasa ba"sameer yaji wani yarrrrrr idan daddy yaje kauye tabbas yasan zaa sanar masa
da shine ya aureta,wace hanya zaibi wajen ganin ya Hana daddy zuwa wajen mahaifin Dina dan kashe
mata aure a aurawa mansoor ita?momy ce cikin kuka tace "Alhaji ka taimakeni yaron nan ya samu yarinyar
nan bansan soyayyar da yakeyi mata tayi zurfi haka ba a nemo wanda ya aureta ya saketa mansoor ya
aureta"gaban sameer ya yanke ya fadi cikin zucuyarsa yace bai shirya rabuwa da Dina ba dan shima yanzun
ya fara sonta yanzun ya fara shaukin kaunarta shima rabuwa da ita tamkar zare masa rayuwa ne,dik yadda
yakeson mansoor bayaji zai iya sadaukar masa da Dina bayan ya rigada ya aureta,

lumshe ido mansoor yayi rufaida tana jijjigasa "yaya man kayi magana kaji"tana jijjigasa dakyar ya bude
rinannun idanuwansa yana kallonta saidai sam ya kasa magana dik yadda suke magana bakinsa yaki
budewa,

Daddy ya kalli agogo yace "koda dare ya tsala ne haka nan zan nufi kauyen nan wajen ganin nasamawa
yaron nan farin cikin rayuwarsa da mu rasashi"momy zatayi magana likita yayi gyaran murya ya dauki file
din da aketa bincike akan mansoor,wata nurse ta shigo ta kawo masa takardar scanning ya dubesu yace
"Tabbas rayuwar mansoor tana cikin hatsari dan inhar baisamu abinda yakeso ba idan bai rasa rayuwarsa
ba to zai zama ga rai babu anfani,domin munyi bincike sosai akansa,zuciyarsa tadan samu matsala sanan
abu mafi muhimmanci a rayuwarsa a jikinsa guda daya ne wanda ko wani dan adam dake rayuwa nasa biyu
ne,idan daya tagaji tabar aiki sai dayar ta dauka to tasa guda daya ce wanan ma babbar matsala ce"momy
da daddy kallon likita sukeyi cikin rashin fahimta kamar hadin baki sukace "meye a jikinsa guda daya?"da
mamaki likita yace "zakuce bakusan kodar dake jikinsa guda daya bace?"dafe kirji momy tayi a rude tace
"kodarsa daya ce?ya akayi kodarsa ta zama daya?"daddy ya kalli mansoor wanda idonsa ke kallom gefe
daya sai hawaye ke zuba Dina kawai yake gani a kwayar idonsa muryarta keyi masa yawo a kunne maganar
da sukayi a waya "zamuyi aure yadda zamu cigaba da abotarmu harabada"ya lumshe idanuwasa bugun
zucuyarsa ya tsananta dik maganar da sukeyi mansoor baya magana a rude daddy yace "ya akayi kodar
mansoor ta zama guda daya?"tambayar da daddy ya jefawa sameer kenan wanda yake zaune gumi na
karyo masa kamar an ana watsa masa ruwa,

momy ta ruko daddy tana kuka "nidai ka tafi kauye wajen mahaifin yarinyar nan a nemi wanda ya aureta ya
saketa mansoor ya aura banaso na rasa dana"momy ta durkusa tana rizgar kuka daddy ya dagota yace "is
okay zanje yanzun nan zani mansoor zai tashi bazai mutu ba kinji"nabeeha kuka kawai takeyi ta hada kai da
jikin bango tsananin tausayi da kaunar da takeyiwa Mansoor,

har daddy ya fita sameer ya kasa motsawa tsananin tashin hankalin dayake ciki ga mansoor kwance kamar
gawa ga Dina a gidansa a matsayin matarsa bayajin akwai abinda zaisa ya rabu da Dina a halin da yake
ciki.....

*Toh fa ga Mansour ya dawo ga Dina a gidan Amininsa ya aureta,sanan gashi kodar dake jikin mansoor
daya na jikin mahaifiyar dina,ya makomar soyayyar mansoor da Dina?shin sameer matawalle zai hakura da
ita ya barwa amininsa yadda yakejin shaukin sonta?ya zata kasance da cikin dake jikin khairatu na sameer?
ya mansoor zaiji idan yasan sameer ne ya aure muradin zuciyarsa?......*

*HANZARTA KI BIYA 400 PROMO DA NAKEYI TUN SHEKARANJIYA ZUWA GOBE MEMAKON 500 IDAN
KINASON VIP 600 MEMAKOM 700 MAI KIKE JIRA LITTAFIN MAZA BIYU ZAI KAYATAR DAKE ZAI ILIMANTAR
DAKE SANAN ZAI NISHADANTAR DAKE INA MASOYAN NE?*

2255398727
ZENITH BANK
AMINA JIBRIL

SHAIDAR BIYA TA 07042277401 KO 08036953516

*SLIMZY*😍

You might also like