You are on page 1of 353

Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

*Imaan*

_By Khaleesat Haiydar_


*All thanks to Allah SWT for giving me the chance, privilege and ability to start
this book, my special greetings goes to my lovely mum Hajiya Hajara and my sweet
aunties (Small mums) my siblings aren't excluded also... I love them all, Ban mance
ki ba Mama dutse ina gaisuwa da fatan anyi sllh lafiya Allah ya amshi ibadunmu,
Hajiya Asabe kema ina gaida ki sosai da maki fatan alkhairi Allah ya raya xuri'a,
Hafsat Oum Ilham I greet you too with respect, and My Sophiee I know you won't see
this but get this.. jiddo Love's you dear, Lovely fans ina maku fatan alkhairi da
fatan gamawa da iyaye lafiya*
1.....
Babban compound ne sosai dake dauke da shuke shuke da bishiyoyi masu daukar
hankali, kai kana ganin tsakar gidan kasan naira ta xauna, makeken tsakar gidan na
dauke da sassa har uku masu fenti iri daya, ko wani sassa kuma akwai tazara mai
tsayi tsakaninsa da wani sassan, sashin farko wanda shi xaka ci karo da bayan
shigowar ka gate din xamanin dake babban gidan ba dai girma ba don sashin duk ya fi
sauran girma, duplex ne babban gaske sai parking space gari guda dake gefe.
Durkushe a bakin tap dake babban sashin farko wata farar budurwa ce da baxata wuce
shekaru sha takwas ba, duk da a duke take hakan baxai sa aki gane doguwa ce ita din
ba, ruwan tap din na ta xuba bucket din da ta tara don ya cika, sai shafa socks din
hannunta take kamar mai tausayinsa, daga ves, huluna sai socks kala uku sune kayan
da take wankewa a wajen amma ta kusa awa daya, kofar entrance da ta ji an bude ya
sa ta kamewa daga inda take durkushe lkci daya ta xaro ido gabanta ya fadi don ita
dai a iya saninta babu kowa sashin banda ita da ke wanki tun daxu, occupant din
bangaren duk sun tafi biki ta kuma ga fitarsu, wanda da ace suna nan tasan ko hauka
take baxata fara xuwa bangaren su tayi wanki ba, a hankali ta juya don ganin wanda
ya fito, wani matashi ne dogo sosai wanda baxai haura shekaru talatin da uku ba
tsaye dai dai entrance din shiga gidan sanye da jallabiya milk color, Ta dauke kai
tana ci gaba da daurayenta, ya rungume hannuwan sa calmly yace "Keee" kamar xata yi
kuka ta juya ta kallesa, yace "Me ya kawo ki wanki nan?" Ta buda manyan idanuwanta
tace "Tap din mu fa ne ya lalace jiya kuma....." Ya katse ta yace "Tashi ki bar
wajen" Tace "To ai na kusa gamawa fa" strictly yana d'an daga murya yace "Kwashe
kayan ki ki bar nan kar ki yarda in iso inda kike" ta dauke kai hade da turo baki
ta mike ta xubda ruwan gaba daya ta hade buckets din bayan ta xuba yan kayan da ta
wanke ciki ta kwashesu gaba daya ta bar wajen kamar xata tashi sama ba tare da ta
sake kallon inda yake ba, ta murguda baki bayan tayi nisa, murya can kasa tace
"Allah ya isa" Dai dai part na biyu da ya kasance wani babban hadadden Bungalow ta
tsaya, shi ma kuma bangaren na da nasa parking lot din da xai dau motoci uku, ta
dinga kallon sauran kayan da bata gama wankewa ba kamar xata yi kuka, to ita yanxu
ya xata yi da su, Ammi na ganin bata gama ba sai ta fara mata fada yanxu tace tun
daxu me take, kallon hanyar da xata bi xuwa part din karshe tayi, ta tabe baki
sanin ba lallai ma mai sashin ta bar ta ta ta6a mata tap ba, tana ta tsaye can kuma
dai ta wuce can bangaren karshen, shi ma sashin bungalow ne sai dai bai kai nasu
ba, tsarin ma ba iri daya bane, a hankali ta ajiye buckets din hannunta dai dai tap
din dake opposite entrance din shiga parlor tana yi tana satan kallon kofar, cikin
dubara ta bude tap din yanda xuban ruwan bazai yi kara ba, ta tara bucket din a
karkace kar ma aji xuban ruwa ta ci gaba da daurayenta, sosai gabanta ya fadi jin
taku duk a tunaninta mai bangaren ce, mutumin daxu ne ke tahowa bata yarda sun hada
ido ba ta ci gaba da wankinta, ko kallon inda take shi ma bai yi ba, bai kuma kai
ga shiga parlon ba suka ji muryar wata tsohuwa tana cewa "Ni wai ya nake jin kamar
ana taba min pampo a wajen nan ne" da sauri ta kashe tap din ruwan xata kwashi
kayanta ta gudu sai ga tsohuwar ta fito, Sake baki tayi tana kallon ta kafin tace
"Waye kuma wannan, meye kike min kusa da pampo?" Budurwar ta turo baki tace "To
inna namu ya lalace..." Inna ta katse ta da sauri tace "Da ya lalace ni na lalata
maku?" Budurwar tace "To wai ma ba daxu kika ce in xo in debo maki ruwa in kai maki
bayi ba, shine fa na zo xuba maki" Inna na mata wani kallo tace "Ke din? Ke din da
na sani ce xaki kai min ruwa bayi munafuka? bayan ba Aisha sunana ba, to wllh ki
kiyaye ni a gidan nan ruwana ba na banxa bane kar ki sake xuwa min nan, kin lalata
naku nima ki xo ki lalata min nawa saboda mugunta koh, to uwar ki ce xata debo mun
ruwan idan na tankin ya kare, haka kawai ki bar ni da diddigin pampo duk tsutsa
cuta ta kama ni in bar 'ya yana da wahala, ke dai wannan yarinya ta Bukar muguwa ce
wllh, shegen barnar ki ta fi karfin ki, to wane 6era ma" ita dai Budurwar sai
kallon ta take kamar xata yi kuka, inna na xaro ido tace "Maxa dau min ruwana ki
tafi ki juye min a bandaki, ni dai a gidan nan duk wanda ya diba da hakkina gaskiya
ban yafe ba tunda abun haka ne, don kowa sai da aka dasa masa pamponsa amma don
mugunta sai ku wani kwaso shegun bokitan ku duk datti kuna kwashe min ruwa mugayen
yara" Ita dai tana tsaye wannan karan ta daure fuska sai kallon ta take, A fusace
inna tace "Baxa ki je ki juye min a bandaki ba ko sai nasa an kira min Bukar ya
taho duk inda yake yanxu?" Daukan ruwan Budurwar tayi fuuuu ta wuce ciki, inna ta
shiga parlor ta dauko wani karamin kwado ta kulle tap din ta wuce cikin parlor tana
cewa "Gwara in ta tsayawa ba ruwan nima da a xo ana ta debe min a cuce ni" Tana
shiga parlor ta kalli matashin dake xaune kan kujera yana danna wayarsa, ta hade
rai ta dau kyallen da take goge goge ta ta fi gun kayan kallo ta ci gaba da gogenta
tana cewa "Ka sake dawowa karasa sauran fitsarar da ka mance baka yi ba kenan, wato
duk wanda kayi jiya bai isheka ba, to ni dai a fita a bar min parlor ba ruwana, ba
katon banxan da zan kula yau ta kaina nake, kaje can kayi ma uwar ka" shi dai bai
tanka ta ba sai danna wayarsa yake, Bayan wani lkci ya mike yace "Dama Abba ne yace
in xo in baki hakuri" daga haka ya nufi kofa fuska daure, da karfi Inna tace "Imaan
tunda mutumin nan ya shigo kinji ya ce min wani abu?? To ni dai ba ni ka ba hakuri
ba wllh, idan kuma ba ka yi hankali ba sae in iya fitar har ofis in sami Ahmadu
ynxu" Imaan ta rufe babban roban da ta jawo daga karkashin gado tana kokarin daure
alkakin da ta cika a leda jin inna ta sake kiranta tace "Gani nan xuwa" window ta
bude a hankali ta jefar da ledan ta shiga bayi ta wanke hannunta da sauri ta fito
ta shiga parlor fuska daure tace "Meye kike kirana" Inna na nuna sa tace "Ke tunda
kika shigo kin ji muryar bawan Allahn can?" Imaan ta tabe baki tace "Wai wa?" Inna
tace "Mujaheed" Imaan tace "To ni na sani? Ni da nake cikin daki" daga haka ta bi
ta gefensa ta fice a parlon, sauran kayan wankinta ta dauka ta xaga baya da sauri
ta dau ledan alkakinta ta wuce part dinsu, a hankali ta bude kofar parlon tana
lekan ciki ganin Ammi bata ciki ta wuce bedroom din ta da gudu ta kulle ta ajiye
buckets din a bayi. Da yamma Ammi ta shigo dakin ta sameta kwance tana bacci, Ammi
tace "Imaan" bude ido tayi a hankali, Ammi tace "Ki tashi daga baccin nan haka,
yamma yayi, kin kwaso socks din naki da kika wanke" tana murxa ido tace "Xan kwaso"
Ammi tace "Ga hijabs din ki da na wanke can clothe line din su Anty ki tafi ki
kwaso su ma sun bushe, don kawai yan gidan basa nan sai ki k'i tafiya makaranta
ko?" Ita dai bata ce komai ba, Ammi ta juya ta fita, xaro ido imaan tayi ta mike da
sauri ta shiga bathroom din ta ta matse socks din da hula da inner wears ta xuba su
a dryer na washing machine ta kunna sannan ta fita, Tana kwashe hijabs din ta a
clothe line da Ammi ta ce mai gadi ya bude gate, wani rantsatsen mota ya shigo
gidan direct parking space dake babban part din ya taho, sai ga wata motar ta biyo
bayansa xuwa parking space din, Mutumin daxu da safe ne ya fito driver seat sanye
da kananun kaya daga cikin motar farko, wata yarinya da baxata wuce Imaan ba ta
fito front seat din motar, sannan wata mata da baxata haura hamsin da hudu ba ta
fito back seat tare da wata yarinya mai shekara ashirin, kana ganinsu kaga yan daki
daya, Imaan ta dauke kai tana ci gaba da abinda take, Bude dayar motar aka yi, wani
mai kama da Mujaheed Sak ya fito sai dai shi ya fi sa haske, Shima dogo ne kuma
Mujaheed ya girme sa da 4 years, mahaifiyarsa ce ta fito bayan motar da kanninsa
duk mata hudu su ma, murmushi mahaifiyar tasa tayi ganin Imaan tace "A'ah wanki aka
yi yan mata" Imaan tayi murmushi tana boye fuskarta tace "Sannu da dawowa Anty"
Anty tace "Sannu Imaan, ya Ammi fa" Imaan tace "Tana gida" Kallon matashin da ke
tsaye kusa da Anty yana kallon ta tayi tace "Ina yini ya Yusuf" yace "Lafiya lau,
Imaan din daddy, sai dai nasan ba ke kika yi wankin nan ba" ta xaro ido tace "Ni
nayi fa" Anty ce "Toh shi xai maki idan baki yi ba banda tsokana, share sa kin ji"
tuni Mujaheed ya nufi entrance din shiga part din su mahaifiyarsa Umma dake satan
kallon Imaan da ta ki kallon ta ta bi bayansa, Anty ma ta wuce Yusuf na biye da ita
yana waigo Imaan yace "In ji yau baki je tsokanan inna ba ta hada ki da daddy"
Imaan tayi dariya tace "Ni ina ruwana da ita ai na daina xuwa part din ta" Daga
haka ta juya ta wuce bangarensu. Da daddare Imaan na kokarin saka kayan baccinta ta
kwanta Ammi ta shigo dakin, tana kallon ta tace "Ki je Abba na kiran ki" xaro ido
tayi tace "Abba kuma Ammi?" Juyawa Ammi tayi ta fita, kamar xata yi kuka ta saka
hijab din ta ta fita tana tunanin kiran me Abba ke mata da daddaren nan. A hankali
ta bude kofar parlon Abba ta shiga bayan ta cire takalmin kafarta, Abba na xaune a
3 seater cikin parlon Mujaheed na xaune shi ma kan lallausan carpet din dake malale
kasa, sai Umma dake xaune kan one seater, Anty ma haka, Imaan ta karasa kanta a
kasa ta xauna kasa kusa da Anty, murya can kasa ta gaida Abba, Abba ya amsa yace
"Ya karatu" tace "Alhmdllh" yace "Imaan discipline din ki kenan rashin gaida na
gaba da ke?" Imaan ta daga kai tana kallon sa, ya daure fuska yace "Ita Hajiya
sa'ar ki ce da ba kya gaisheta a gidan nan?" Shiru tayi bata ce komai ba, ya hade
rai yace "I am talking to Imaan, kuma ki bar kallona my friend" A hankali ta fara
6ata fuska tana jan yatsunta, lkci daya ta fashe da kuka, Abba ya mata tsawa yace
"Daman kuka kika samu don ban xane ki ba yanxu" kuka take yi sosai kamar warce aka
duka, Mujaheed ya mike ya mata wani raxanannen tsawa ta mike da gudu ta nufi kofa,
xai bi ta Abba ya dakatar da shi yace "Rabu da ita M.A, Allah ya shiryeta" Umma
ta tabe baki tace "yaran yanxu da ba a sangarta su ba ma ya aka kare ballantana
wannan?" Anty ta mike ta fita parlon, Abba dai bai ce komai ba, imaan bata xarce ko
ina ba sai sashin inna, tana shiga parlon ta xube kan kujera ta rushe da kuka, inna
ta fito daki da sauri, Yusuf ma dake kwance kan 3 seater ya mike xaune da mamaki
yace "Me ya faru Imaan" jikin inna na rawa tace "Me ya samu Aishar?" Imaan ta ki
cewa komai sai kuka, tuni inna ta nufi kofa, cikin kuka Imaan tace "Ni ba abinda ya
samu Ammina" inna ta dawo tace "Ke dai ki dinga jin tsoron Allah, da yanxu xuciyata
ta buga ya kike son 'ya yana su yi, ya zaki shigo da kuka ki janyo min wata fitinar
ina xaune" Cikin rawar murya tace "Ko ba Umma bace" inna tace "Wacece haka?" Imaan
bata ce komai ba sai kuka, Inna tace "Warcan mata mai kama da zabiya kike nufi wai,
ko ba uwarsu fitsararren yaron nan Mujaheed ba?" Imaan ta hadiye abu da kyar tace
"Ita" Inna ta share wani xufa tace "Toh xata ga barbadin rashin mutunci yau kuwa,
me ta maki?" A hankali Imaan tace "Shine taje ta gaya ma Abba wai ni bana gaisheta
alhalin fa ko na gaisheta bata amsawa, shine Abba ya kirani...." Sai kawai ta fashe
da kuka, inna tayi wani murmushi tana gyada kai tace "Biri yyi shige da mutum, Sai
aka yi ya da ya kira ki" imaan ta kalleta cikin shesshekar kuka tace "Yana min
fada....." Tuni Inna ta fice parlon, Imaan ta saci kallon Yusuf da yyi tagumi yana
kallon ta ta mike tana turo baki ta fita. Inna na isa bangarensu Yusuf kai tsaye
parlon Abba ta wuce, har sannan Abba na xaune da Umma a parlon sae Mujaheed, gaba
daya daga kai suka yi suna kallon ta, inna ta tsaya tsakiyar parlon tana kallon
Abba tace "Yanxu yaro tun da sauran numfashin Bukar a duniya zaka sa ma 'yar sa
ido? Yanxu a kan wannan matar zaka ci mutuncin yarinyar da lafiya ma bai isheta ba
sai dai godiyar Allah? Yanxu Ahmadu duk son da d'an uwanka ke maka xaka rufe ido a
hadu da kai a ci mutuncin yar sa kwaya daya tal..." Kunce ha6ar xaninta tayi tana
matsar kwalla tace "Naga abinda ya isheni bai ishi Allah ba..." Abba kasa cewa
komai yyi da farko, can yace "Haba inna, wannan wace irin magana kike...." A fusace
tace "Ohh yare nake maka da xaka tambayeni wani irin magana nake, to wllh bari ka
ji, a kan Fatima a gidan nan ina iya sa6a ma ko wani mahaluki, kuma baxata gaida
matar taka ba, ita katuwar gaida mutane take?" Mikewa Mujaheed yyi ya nufi kofa
kamar xai tashi sama inna ta bi sa da wani shegen kallo, sannan ta ja tsaki ta
maida dubanta kan Abba dake ta kallonta ta daure fuska tace "Ahmadu yaushe rabon
ita matar taka ta kai kafafuwanta bangarena gaisheni? Lallai... ni a su wa xata je
gaidawa? Ni din banxa xata gaidar?? To hirrrr wllh, kada wanda ya kara sa ma jikata
baki a gidan nan idan ba haka ba sai in sa Bukar ya koma daya gidansa dama shi ya
nace xama waje daya da kai, tunda yar sa xa a takura gwara kawai ya bar
gidan...Dubi fa Mujaheed haushi ya ji yanxu don na ambaci uwarsa, kana gani saura
kiris ya bangaje ni in fadi duk cikin bacin rai, to uwa ta fi uwa ne?? don me kai
ma baxa ka tattala ni haka ba, duk ka bi ka daure mata kugu bata gani na da gashi a
gidan nan, to mu xuba da ita xan ga ko ita ta haifo min kai duniyar, wannan ai
raini ne wllh, wai taji haushi Imaan bata gaisheta ba to baxata gaidata din ba, kar
ta kuskura ta sake sa min jika a baki tayi ta kanta kawai a gidan nan" shi dai Abba
shiru yyi kansa a kasa, Umma ta rungume hannunta daga xaune tana kallon wani
direction din, Abba ya dago yana duban mahaifiyar tasa yace "Kiyi hakuri Inna" ta
maka masa wani kallo tace "Sai dai ka ba matar ka hakuri tunda na 6ata mata rai"
Tana kai wa nan ta fice. Imaan har ta kusa part dinsu taga shukanta na wake da tayi
a babban gwangwani a madadin assignment da aka basu a Agricultural science, a yashe
duk root din ya fita daga cikin gwangwanin, ta xaro ido ta ta fi wajen da sauri,
lkci daya hawaye ya kawo idonta tace "Wllh nasan Rahma ce xata kwabar min da shuka
na" sai kuma ta fashe da kuka na takaici ta durkushe wajen, ba ta lura ba har
Mujaheed ya iso wajen, ta juya hawaye sha6e sha6e idonta tana kallon sa ta sake
rushewa da kuka, ya daure fuska yana kallon kafarta yace "Me ya faru?" Ta mike
cikin rawar murya tace "Yaya kalli fa abinda Rahma tayi ma assignment dina kuma ten
marks ne, xa muyi submitting ranan Friday, kalli fa har ya girma, don nawa duk yafi
nasu sai ta kwabar min" ganin sai hararanta yake ta juya ta wuce tana ci gaba da
kuka, fixgota yyi yana mata wani kallo yace "Shi Abban kika tafi kika yi reporting
gun Inna?" Lkci daya ta tsaida kukan da take bayan ta gane biyota yyi, ta fizge
hannunta ta kwasa a guje, kiris ya rage ya kamata ta shige parlonsu ta banko kofar
tasa key, Ammi dake xaune parlon tana kallo ta mike tace "Meye haka Imaan?" Dariya
ta fashe da ta wuce daki da sauri tace "Sauri nake in xo in kwanta fa Ammi" tana
shiga bedroom din ta ta sa makulli. Har Imaan ta fara bacci wajajen karfe goma Ammi
ta bude kofar dakinta, bude ido tayi Ammi ta hade rai tace "Uban me kika debo ma
inna a dakinta?" Ta mike xaune da sauri tace "Na debo mata abu kuma? Haka ta ce?"
Ammi tace "Kinga na raba ki da xuwa sashinta ki dauko min magana ba ki ji ko? To ki
fito mata da duk ma abinda kika daukan mata gata can bakin kofa" Imaan ta turo baki
ta sauko daga saman gadon ta bi bayan Ammi da ta fita, ido hudu suka yi da inna da
ke tsaye bakin kofa ta tsuke fuska, Imaan ta hade rai tace "Ni me na dibar maki
xaki biyo ni cikin daren nan" Inna tace "Duk cikin jikokina babu mai ta6a min kaya
ban basa ba sai ke, duk kece mai mugun halin nan don haka maxa ki fito min da
alkaki na, don ba a rame na bar sa ba ina sane da abinda nake ba fara haukacewa
nayi ba" Ammi dai ta nemi waje ta xauna, Imaan ta 6ata fuska kamar zata yi kuka
tace "Wai yaushe naje da har xan dibar maki kayan ki ni da ba ci ma nake sosai ba,
to ma ba xaki gansa hannuna da xan fita ba" Wani tsawa Ammi ta yi mata tace "Kin
tafi kin dauko abinda kika diba ko sai na mare ki" Imaan ta harari inna ta wuce
kitchen sai ga ta ta fito da ledan alkakin, Inna ta saki baki ta warce ledan tace
"Naga Ikon Allah ni Asabe, da yake Aisha ce ta xauna ta min tuyar bayan ta kwa6a
dole ki kwaso ki kawo maku ku ci, to ni kar in sake ganin kafafuwanki a bangarena
don halin ki abun tsoro ne, wannan ai ba tarbiya aka maki ba ki shiga har karkashin
gadon mutane ki jawo kwalla ki debe min kayana, yanxu banda jinin ka jininka ne kin
xata idan na ja Allah ya isa baxai bi ki ba, ni wllh darajar d'a na kike ci a gidan
nan gaskiya, kar in sake ganin ki a parlona ni dai dama baki tsinanamin komai sai
dai ki malale kan kujera kina mik'a, duk kin ru6ar min da kujeru" tana kai wa nan
ta juya ta wuce, Imaan bata yarda ta kalli Ammi ba ta wuce daki ta rufe kofa tayi
kwanciyarta tana turo baki.
Maa sha Allah, I am back by Allah's grace... daily update in sha Allah, but if schl
shud resume anytime soon xan dakata da posting for some weeks coz I will be having
exams in sha Allah. Hope you guys will love the *book*, though I know I never
disappoint my fans when it comes to writing in sha Allah....
Khaleesat Haiydar...
[6/11, 12:34 PM] +234 703 570 1601: 🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟

_By Khaleesat Haiydar_✍🏻


2......

Washegari da safe Imaan ta fito parlor shirye cikin well ironed uniform dinta da
beret dake kanta, kitchen ta shiga gun Ammi, Ammi dake juye ruwan shayi flask tace
"Yau ma baki yi combing gashin ba koh" ta jingina da kofa cike da shagwaba tace
"Wllh Ammi xafi, baxan iya ba" Ammi bata ce komai ba ta gama xuba ruwan a flask ta
xuba mata nata a cup dinta ta hada mata shayin sannan ta mika mata, Karba Imaan
tayi ta fita xuwa dinning, Ammi ta kai mata dankali da kwan da ta soya mata ta
ajiye tana kallon agogo tace "Kiyi sauri kar su jira ki don Allah" Imaan ta xaro
ido tace "Ammi kullum fa ni ke jiransu" Ammi tace "Toh kar kiyi saurin" daga haka
ta wuce kitchen don yin wanke wanke, imaan na gamawa ta kai plate din da cup
kitchen, ta dauko jakarta, Ammi tace "Ki duba gaban dressing mirror a daki na akwai
duba daya ki dauka, dakin ta shiga ta dauko sannan ta fito tace " Ammi sai na dawo"
Ammi tace "Ohk Allah ya tsare kiyi addu'a kafin ki fita, and you make sure baki
mance ko wani book ba tunda hankali bai ishe ki ba" dariya kawai tayi ta fita gidan
bayan tayi addu'a, Can parking space din su Yusuf ta tafi ta tsaya don nan take
jiransu, yawanci Yusuf ke kai su wani lkcin kuma Anty ta ajiye su tunda tsohon
driver dinsu ya tafi, Tana ta tsaye jikin mota ta hango plant din su Ummi, Rahma da
Maimoon don duk ajinsu daya wato ss2, kamar xata yi kuka ta dinga kallon waken nasu
da duk ya fito da ganye, ga nata can an lalata mata, kallon entrance din gidan tayi
lkci daya ta nufi wajen da plant din suke da kafa ta haure gaba daya biyun banda na
maimoon don kowa ya sa sunansa, sai da ta tabbatar roots din sun fita sannan ta
koma jikin mota da sauri, Ummi ce ta fara fito sanye cikin uniform irin na jikin
Imaan sannan Rahma sai Maimoon, Babu wanda ya kalleta cikin su banda Maimoon da
tace "Imaan kin gama maths assignment din ki" Imaan tace "Ehh na gama" Maimoon tace
"Toh idan mun shiga mota xan kwafa plss ban yi ba" Imaan tace "Ohk" Mujaheed ne ya
fito rike da makullin mota fuska kamar hadari, Imaan ta xaro ido tana kallon
Maimoon murya can kasa tace "Shi xai kai mu?" Maimoon tace "Ehh ya Yusuf baya nan
ya tafi Zaria daxu, shine Anty tace ya Mujaheed ya ajiye mu, shine yake fushi"
Imaan ta turo baki bata ce komai ba yana bude motar ta shiga back seat tare da
Maimoon da Rahma, Ummi ta shiga gaba, har suka bar gidan babu wanda yace komai
cikin su, Imaan ta bude jakarta ta ciro assignment din ta ba Maimoon, tafiyar minti
ashirin ke kai su makarantar su, amma saboda gudun da yyi cikin few minutes suka
iso, yyi parking dai dai makarantar yana kallonsu da kyau yace "Dama kuna tashi ku
fara trekking din dawowa gida don baxan xo daukan kowa ba" a hankali Ummi tace "Ya
M.A ai soon Abba xai dau mana wani driver fa" yace "Sauka malama" bude motar tayi
ta fita, tuni Imaan da Maimoon ma suka fita suka shige cikin makarantar. Anty ce ta
xo daukan su bayan sun tashi ranan, Anty na kallon Imaan dake ta yamutse fuska tace
"Me ya faru Imaan" a hankali ta nuna mata kanta, Anty tace "Toh idan kin koma gida
kin ci abinci sai ki sha magani ki kwanta ki huta" to kawai imaan tace, ko da suka
isa gida har bacci ya dauketa Maimoon ta tasheta ta bude ido, Anty tace "Toh shiga
gida imaan" kai kawai ta gyada mata ta fita ta nufi part dinsu tana dingishi. Ruwan
xafi Ammi ta hada mata ta shiga tayi wanka sannan ta ci abinci, Ammi ta bata magani
tace "Sai ki daure kiyi shirin tafiya islamiyya it's too early ki fara fashi this
week, today is Monday" Imaan bata ce komai ba, Ammi na fita ta koma kan gado ta
kwanta kamar xata yi kuka, hudu da minti biyar Ammi ta shigo dakin jin shiru bata
fito ba, ganin har bacci ya dauketa ta kai hannu jikinta taji da dumi, girgixa kai
tayi ta juya ta fita, Maimoon ne ta shigo parlorn sanye da uniform din islamiyya,
Ta gaida Ammi sannan tace "Ammi imaan muke jira" Ammi tace "Bata jin dadi ku tafi
Maimoon" a hankali Maimoon tace "Allah ya sauwake" sannan ta fita, Ammi na girkin
dinner a kitchen wajen karfe biyar Imaan ta fito daki, wani internal heat kawai ta
ke ji, kuma tana kunna Ac tasan sauran ta dinga lekan kitchen kamar xata yi kuka, a
hankali ta nufi kofar fita ta bude kofar yanda baxa aji kara ba sannan ta fice xuwa
part din inna don ta je ta kunna Ac, Inna na wanke gun tap dinta da take sa ma
kwado ta daga kai tana kallon Imaan tace "Baki tafi islamiyyar bane yau" Imaan ta
turo baki tace "Ehh" daga haka ta shige parlon, kunna Ac tayi ta kwanta kan kujera
dake kallon Ac din ta lumshe ido, inna na gun tap din har sannan sai ga Mujaheed,
ta mike tana kallon sa tace "Baka ji bayana ba Mujaheed kamar xai balle, ko kai
baka ga yanda wajen pampon yayi haske ba tun daxu nake ta gurza gashi sai kyalli
yake, ai kazanta bata da kyau, yanxu kaga ko tuwo aka xuba a wajen mutum xai iya
xaunawa ya ci" Mujaheed dai bai tanka ta ba ya shige parlorn bin bayansa tayi, ya
ajiye ledan hannunsa yace "Gashi Abba yace a kawo maki" tace "Toh Allah yayi masa
albarka... Dama raina na son kayan marmarin" xai fita Inna tace "Mujaheed kaga
yarinya nan abinda ya kawota kenan ta xo ta kunna Ac wata cutar ta kamata ace ai a
parlorn inna ne, to ni dai ba ruwana ka kashe min kayana taje can ai su ma suna da
shi, duk yanda aka yi kuma uwar hanata kunnawa tayi shine ta taho ta kunna nawa
salon ace parlorn inna to Allah ya fi ki babu me sa ni a bakin duniya" Mujaheed ya
kalli Imaan da tayi rub da ciki kan 3 seater din ya tabe baki xai fita Inna tace
"kai ya ina maka magana xaka fita, idan uwar ka Rukayya ce xaka mata haka
Mujaheed?" Fuska daure ya juyo ya xauna yana kallon ta da kyau yace "Wllh idan kina
sa mahaifiyata a baki Hajiya xa mu kwashi yan kallo dake a gidan nan, komai sai
kice uwata" Inna ta saki baki tace "Kai ni kake daga ma murya" yace "Toh ki daina
sako mahaifiyata a xancen ki idan baki son a daga maki murya, ke kwata kwata
rayuwarki baki son xaman lafiya daga kice wannan yayi maki sai ki ce wannan yayi
maki...." Inna ta gyada kai tace "To ka tara kuma ka samu, xaka san ni ka fada ma
bakar magana" Tana fadin haka ta kashe Ac dinta, Imaan ta mike xaune kamar xata yi
kuka tace "Meye xa ki kashe min inna" Inna tace "Bukar yasa na kashe, na ku
lalacewa yayi xaki taho min nan, ni dai a daina xuwa ana sa ni magana ana min
rashin kunya gaskiya" imaan ta marairaice tace "Don Allah inna ki kunna xafi nake
ji a cikin jikina" Inna tace "Toh baxa ki ji xafi a jikin ki ba ga magani nan an
kawo maki tun daga Nijar kin ki amsa sai yawo kike min da hankali kamar ni xai
amfana, duk tashi fadin da nake a kanki ba ki gani, mutum bai san inda xai dace ba,
idan an baki magani sai kiyi biyayya ki amsa ki sha sai kiga Allah ya yaye maki
wannan ciwace ciwacen da ba a san kansa ba" Imaan tace "Wa yace maki ba a san kansa
ba, to ai da shi aka haifeni kuma ba warkewa...." Inna tace "Oh oh Allah, Mujaheed
kaji irin fitinar da take ja ma kanta da bakinta ko, kai wannan 'ya ta Bukar anyi
doluwa wllh, ke fata kike kar ki warke d'a na yayi ta cacan kudi, duk cikin
jikokina babu mara tunani dama irin ki" Imaan ta hade rai tace "Ehh na ji, ki
kyaleni da ciwo na Babu ruwanki, baxan kuma sha maganin ba don ina da na asibiti da
nake sha, ni bance ki dinga amso min magani ba dama ai" inna tace "Kada Allah ya sa
ki sha, to ni Allah na tuba a haka ma wa xai yi sha'awar aurem ki yau ciwo gobe
lafiya duk tattalin arxikinsa ya kare a asibiti, tun kina mitsitsiyar ki nake
wahala da ke kan maganan magani shi sa ma kika yi kyan gani, ke da kike kamar
kwarangwal da taimakon Allah da taimkona da magungunan da nake amsar maki gun
malamai shine kika marmaro, in dan ta uwar nan taki ce ai sai dai ki mutu tana
kunshe daki ba fita xata yi ta nemo maki magani ba tana jiran na asibiti, Toh wllh
daga yau na fita harkan ku ki ji da ciwon ki nima inyi ta kai na" Imaan ta fashe da
kuka tace "Ehh naji, ki kyaleni tunda ba dole bane shan maganin ki" daga haka ta
fice daga parlorn da gudu, Inna tace "Duk xa ku yi bayani bari iyayen naku su dawo"
Mujaheed ya tabe baki ya mike ya fice mata a parlorn shi ma. Imaan na kwance kan
kujera bayan isha Ummi ta bude kofar parlorn tana tsaye daga bakin kofa tace "Abba
na kiran ki a bangaren Inna Imaan" daga haka ta fita, Ammi dake cin abinci xaune
parlorn ta kalli Imaan da ta wani juya bata dai ce komai ba, bayan kusan minti
biyar Ammi tace "Amma dai kin ji abinda tace Imaan" Ta juyo kamar xata yi kuka tace
"Wllh Ammi kafana ciwo yake min ban san ko xan iya tashi ba" Ammi ta galla mata
wani harara tace "Sai ki rarrafa ai tunda baxa ki iya tashi ba" hawaye cike idonta
ta mike ta sa Hijab ta fita tana taka kafar da kyar. A hankali ta bude kofar
parlorn Inna ta shiga da sallama, Abba ne xaune parlorn sai Inna da Anty, Imaan ta
sunkuyar da kanta ta karasa kusa da Anty ta xauna kanta a kasa ta gaida su, Abba da
Anty kadai suka amsa, inna ta wani tsuke fuska, Imaan dai bata ko kalleta ba, Inna
tace "Wato shi Mujaheed din jira yake kaje ka ciccibo sa da kanka koh?" Abba ya
kalli Imaan yace "Tashi ki tafi can bangaren ki kira min Yayanku" Imaan ta mike ta
d'an harari inna ta gefen ido ta fice a parlorn, tana isa part din su Mujaheed
ganin bbu kowa parlor sama ta haura ta tsaya corridor tana kallon door din dakinsa
har ta mance rabon da ta je kusa da kofar, bude kofar Umma aka yi sai ga shi ya
fito, ta matsa da sauri don kusa da kofar dama take tsaye tace "Abba yace in kira
ka" ko kallon ta bai yi ba ya fara sauka stairs, ta murguda masa baki ta bi
bayansa, har suka isa part din Inna bai juya ba, ya bude kofar ya shiga da sallama,
kusa da Anty Mujaheed ya durkusa kansa a kasa, Abba sai kallon sa yake yana girgixa
kafa, Imaan ta shigo parlorn ganin inda ya durkusa tace "Waje na ne nan" Murmushi
Anty tayi, shi kam ko kallon ta bai yi ba balle ya motsa, Inna tace "Ahmadu na fa
gaji da xama nan kamar warce xa a ma gafara, aji da ni in tashi in shiga ciki in
kwanta" Abba ya kalli imaan yace "Samu wani wajen my friend" ta harari Mujaheed ta
koma wani wajen ta xauna, Abba na kallon Mujaheed
yace "Muhammad ita innar ka mayar abar wasar ka a gidan nan?" Inna ta tabe baki
tana jijjiga kafa, Mujaheed bai dago ba kuma bai ce komai ba, Abba yace "Am I not
talking to Mujaheed" ya dago a hankali yace "Abba kayi hakuri don Allah" Abba yace
"Stupid, ni ma kake ba hakuri?" Ya kalli inna yace "Kiyi hakuri inna" dakatar da
shi tace "A'a malam a gaban ubanka xaka ce min inna kenan, wllh Ahmadu daxu yana
nuna ni da yatsa a can bakin kofar kamar xai make ni Hajiya yace min, ni na ma xata
duka xai kai min bayan ya gama kashedin, to gaskiya da sake, sam yaranka basu da
d'a'a basu da kunya Ahmadu, isuhu ne kadai dama mai gudun bacin raina duk da shi ma
ko aiki xai kashe ni baya taimakona, to ynxu Mujaheed da wani ne da ya xo ya gan ni
durkushe ina faman gurje gun pampo ba amsa xai yi ba ya taya ni, to wllh bai amsa
ba sai xagina ma ni da yayi daga karshe, a xo har sashina a dinga ci min mutunci,
to hirrr don duk ranan da aka isheni tattara kayana xan yi in bar gidan nan kuma
sai anyi shekara duba ana nemana" Mujaheed ya d'an daga kai ya kalleta ta gefen ido
ya maida kansa kasa, Abba dai bai iya yace komai ba, Anty tace "Kiyi hakuri inna, a
yafe masu" Inna tayi kasa da murya tace "Wllh Amina daga nace kai kuwa Mujaheed
haka kake ma Mamarka a gida ina ma magana xaka wuce, kuma fa cikin lallami nayi
tambayar kawai ba sai ya sakar min aradu a kai ba, ita kuma wancan lankwasasshiyar
mai kama da yar tsana bbu abinda ta mance bata gaya min ba daga nace Imaan ga
maganin da na amso maki saboda ciwon ki da ba a san kansa ba ba a san dalilinsa ba,
wllh Ahmadu sae kaga wanke ni da yarinyar tayi tasss har da ce min ba ruwana da
ciwonta kuma ciwon ba me warkewa bane" Imaan ta fashe da kuka har da shessheka,
Abba yyi mata tsawa cikin rawar murya tace "Abba xagina fa ta ke yi wai...." Abba
ya dakatar da ita yace "Keep shut" ta hadiye abinda xata ce tana hawaye, Mujaheed
yace "Kiyi hakuri Inna" Inna tace "Atoh ya xan yi idan ban hakura ba, dama wanda
aka cuta ake ba hakuri, amma daga kai har ita kar in sake ganin kafufuwanku a
bangarena, tunda kun raina ni, Isuhu da Maimuna sun ishe ni" Fada sosai Abba ya
dinga ma Mujaheed da kansa ke kasa, inna sai matsar kwalla take ita a dole an 6ata
mata rai, hakuri Mujaheed ya kara bata, Anty ta sa Imaan ma ta bata hakuri, mikewa
Imaan tayi da sauri ta fice parlorn tana kuka, Inna tace "Sai ubansa na magana yayi
ta sinne kai kamar na kirki alhalin crooo kenan ku ke gani, kar ka sake xuwa min
sashi ni dai na gama magana" Mujaheed bai kalleta ba balle ya tanka ta ya mike ya
fice parlorn, can kusa da wani flower ya ga Imaan durkushe tana kuka, ya dinga
hararanta har ya isa wajen da take, ta mike cikin rawar murya tace "Yaya don Allah
kai kaji na xage ta daxu?" Ba tare da ya tsaya ba yana ci gaba da tafiya yace "Ke
ma ai ba dukan ki naga aka yi ba" Ta bi shi da kallo tana shessheka.
[6/11, 12:34 PM] +234 703 570 1601: 🌟⭐ *Imaan*⭐🌟

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_
3......

Imaan ce xaune kitchen sai faman xuba surutu take ma Ammi dake girkin dinner a
kitchen, yar skirt ne jikinta sai ves da yake ranan alhamis ne babu islamiyya,
Ammi dake ta saurarenta ta tabe baki daga karshe tace "Aikin kenan sai dai ki cika
mutum da surutu ba taimakon fari balle na bak'i" shiru Imaan tayi tana kallon Ammi,
Ammi ta kalleta ganin yanda mood dinta ya canxa tayi murmushi tace "Toh ci gaba ina
jin ki" sunkuyar da kanta tayi bata ce komai ba, Ammi ta karasa kusa da ita tace "I
was joking sweetheart, tafi ciki let me fry some onion and pepper" mikewa Imaan
tayi a hankali xata wuce Ammi ta bi ta da kallo har ta fita, Ammi ta jingina da
cabinet din kitchen din ta sauke ajiyar xuciya, can ta nufi kofa ta fita don bata
son tayi bacci coz shine next abinda xata yi in har ta shiga daki, dakinta Ammi ta
shiga ta sameta har ta kwanta, Ammi tace "Baxa kiyi bacci ba yanxu yamma yayi, je
dakina xa ki ga leda da atamfa a ciki kan dressing chair ki kai ma su Anty kice
ankon bikin Halima" Imaan ta mike xaune tace "Ammi to na mu fa" Ammi tace "Sai ki
kirata ki tambayeta ban san ko an fidda naku ba" Imaan tace "Toh, Anty kawai xan
nuna ma?" Ammi tace "Ehh sai ki ce mata ta nuna ma Hajiya, na dai fita ai" daga
haka Ammi ta fita dakin, imaan ta sa hijab har kasa kan kayana jikinta ta fita ta
dau ledan ankon a dakin Ammi, tun da ta shiga parlonsu Anty take yamutse fuska ta
dalilin yaji dake tashi sosai daga kitchen, lkci daya ta rike numfashinta, har xata
juya ta fita sai ta nufi stairs da gudu don ta shiga dakin Anty, tsarkewa tayi sbda
rike numfashin da tayi ga kuma gudun da take, lkci daya ta fara tari sosai
breathing dinta na sama, dai dai corridor ta fadi tana kokarin jan numfashi,
Maimoon ta fito dakin Anty ganinta ta durkusa gabanta da sauri tace "Subhanallahi
me ya faru Imaan" sound din faduwarta yasa Mujaheed ya fito daga bedroom din sa,
ganinta a kasa ya kalli kofar Ummarsa kafin ya karasa da sauri ya dagata yana
kallon Maimoon da ta rikice yace "Tafi ki karbo inhaler dinta da sauri" da gudu ta
sauka xuwa part din su Imaan, Mujaheed ya bude kofar dakin Anty ya shigar da ita ya
xaunar da ita kasa ya jinginar da ita da gado ya cire Hijab din jikinta, dai dai
nan Anty ta fito daga bandaki, a rude tace "Subhanallahi, Asthman ne, garin Yaya?
Ko in amso inhaler dinta" yace "Maimoon taje amsowa" sosai imaan xata baka tausayi
saboda ynda take struggling da numfashinta, Mujaheed ya mike ya fita don bin bayan
Maimoon suka kusa cin karo bakin kofa, fixge inhaler din yyi ya juya ya koma dakin
ya durkusa gabanta ya kai mata baki, dafe hannunsa tayi tana inhaling, Anty dai na
tsaye sai kallonta take cike da tausayinta, bayan wani lkci numfashin nata ya fara
fita a hankali yana kokarin dawowa normal, Anty ta xauna gefen gado tayi tagumi
tana kallonta, Ummi da Rahma na tsaye bakin kofar suna kallonta su ma, Har sannan
Mujaheed na duke gabanta idonsa a kanta, muryar Umma suka ji tana cewa "Lafiya me
ya faru ku ka tsaya cirko cirko bakin kofa?" Rahma tace "Asthma ne ya tashi wai"
Umma ta leko dakin ganin Mujaheed ta wani xaro ido tace "Me Mujaheed yake a nan?"
Mikewa yyi da sauri, ta wani hade rai tace "Tambayar ka nake, me ka shigo yi, ko
kayi kama da likitan ta ne?" Ya girgixa kai yace "No na xo wucewa ne...." Dakatar
da shi tayi tana masa wani shegen kallo tace "Sai ka tsaya aikin da ba lada koh? To
ka shiga hankalin ka, Ka guji bacin raina, basu da number likitan ta ne ko kuma
neman suna kake?" Shiru yyi bai ce komai ba, Cikin tsawa tace "Xo ka fita malam
bana son shishshigi da kwala kai a faranti, kanwar uwar ka ko ta ubanka?" Bai ce
komai ba ya kalli Imaan da Anty ke kokarin kwantarwa kan gado ya juya ya nufi kofa
xai fita, Anty ta tabe baki tace "Ciwo dai bai wuce kan kowa ba, ita ma ba ita ta
doro ma kanta ba....." Umma ta katse ta da sauri tace "Allah yayi mana tsari da
irin wannan ciwo nata, ya tsari jikokinmu da tatta6a kunne, a rayuwar nan ta ynxu
wa enda ba sickler ba ma ya suka kare, ae irinsu ne ke tsiyata namiji a sintirin
asibiti...." Tsaye Mujaheed yyi bakin kofa yana kallon Umma, Anty ta wani hade rai
tace "Kinga ki daina kiranta da sickler ita din ba sickler bace, Allah kuma yyi
mata tsari da shi" Umma ta wani tabe baki hade da dariya tace "Kwa dinga boye ma
wanda ku ka raina ma wayo, Allah dai ya ba kowa lafiya...." A hankali Mujaheed yace
"Umma ba fa sickler bace, she is just a carrier...." Umma ta maka masa wani kallo
tace "Meye maraban dambe da fada? And did you have any problem with her being a
sickler or not da har kake karyata ni Mujaheed?" Bude kofar yayi ya fita dakin bai
ce komai ba, ta ja tsaki ta fice ita ma. Anty ta girgixa kai ta zauna kusa da Imaan
da ta lumshe ido numfashinta na sauka a hankali tana mata sannu, sai da ta ga
alamar tayi bacci sannan ta mike ta fita, Imaan bata dau lkci tana bacci ba ta
tashi ta dalilin ciwo da kirjinta ke mata, ta dinga juye juye kan gadon hawaye na
xuba idonta, bude kofar dakin aka yi Mujaheed ya shigo, ya karasa kan gadon yana
kallonta, daure fuska yyi yace "Me ya faru kuma?" Kirjinta ta nuna masa ta fashe da
kuka, yace "Toh kukan ne xai sa ya daina ciwo, tashi xaune" mikewa tayi ta xauna da
kyar, sai ga Anty ta shigo dakin, da sauri ta isa gadon tace "Me kuma ya faru
Imaan, are you feeling pain anywhere?" Ta gyada kai tana nuna kirjinta, Anty ta dau
Hijab ta nufi kofa tana cewa "Bari in je in kwaso magungunanta dai" Xaunawa
Mujaheed yyi gefen gadon, ta koma xata kwanta yace "Kar ki kwanta" ta jingina da
gadon tana goge idonta, ba a dau lkci ba Anty ta dawo da ledan maganin gaba daya,
Mujaheed ya amsa yana duba maganin ya cire mata wanda xata sha, still yyi jin an
bude dakin Umma, sai kuma ya ji muryarta tana tambayar inda yake, tashi yyi da
sauri ya tafi bayan kofa ya tsaya, Anty ta tabe baki ta balli maganin ta dau table
water ta mika ma Imaan, bude dakin aka yi Umma ta kare ma dakin kallo kafin ta tabe
baki ta kulle, Shi dai yana tsaye bayan kofar, Anty ta sa Imaan ta kwanta bayan ta
sha maganin sannan ta kallesa tace "Don Allah ka fita min a daki malam, tunda aikin
xumuncin ma ba so ake kayi ba, kai ma kuma tsoron yi kake, yau ko da ace baka san
Imaan ba a matsayin ka na likita ka ganta a wannan hali ai baxa ka ki taimaka mata
ba balle tana yar uwarka halak malak, Allah dai ya shiryi mahaifiyar ka" shi dai
bai ce komai ba, bayan karin mintuna uku ya bude dakin ya fita. Anty na xaune kan
darduma bayan ta idar da magrib Imaan ta tashi daga baccin da ya kara dauketa, Anty
tace "Sannu ya jikin Imaan" a hankali tace "Na ji sauki" Anty tace "Toh shiga bayi
kiyi alwala ki xo kiyi sllh" ba musu ta mike ta shiga bandakin ta dauro alwala ta
fito Anty ta mike kan darduman ta fita, Imaan ta sa Hijab dinta ta hau kai ta tada
sllh, tana ta xaune kan darduman bayan ta idar sai ga Anty ta shigo da plate din
abinci dakin. Imaan na gama ci ta mike rike da plate din tace "Anty sae da safe"
Anty tace "Au baxa ki kwana nan ba" murmushi tayi ta make kafada ta nufi kofa, Anty
tace "Toh baki fada min ko na meye atamfar ba" Ta juyo da sauri tace "Lahh, Ammi ce
tace in kawo maku ankon bikin Anty Halima" Anty tace "Ashe abu ya xo dai, toh ki ce
mata xan shigo gobe" Imaan tace "Toh" Anty tace "Allah ya sauwake Imaan" murmushi
tayi a hankali tace "Ameen" daga haka ta fita, tun da ta sakko downstairs umma ke
mata kallon tsana tana tabe baki, Imaan dai bata ko kalleta ba ta nufi kitchen rike
da plate din, Rahma ce kitchen din ta gama wanke wanke, sai Mujaheed dake tsaye
yana xuba ruwan Lipton daga teapot a cikin mug, Imaan xata ajiye plate din, Rahma
tace "Kinga plate mai datti a wajen ne malama" turo baki tayi ta dau morning fresh
ta bude xata wanke plate din, Rahma tace "Ya M.A in debar maka abincin ne xan
fita?" Ya harareta yace "Abincin da ku ka cika yaji ko wanda ba yaji?" Yar dariya
tayi tace "Ya Mujaheed yajin fa ba yawa" tsaki yyi yace "Ance maki ban yi tasting
abincin bne ku dinga cika ma mutane ya ji a abinci kamar mayyu" Tace "Toh in maka
cous cous?" Yace "I will take tea" Imaan ta gama wanke plate din ta juya ta fita
kitchen din. Kallonta Ammi ta dinga yi bayan ta shigo tace "Ya jikin Imaan" tayi
murmushi tace "Na ji sauki Ammi" daga haka ta nufi dakinta Ammi ta bi ta da kallo.
Karfe sha daya saura Ammi ta shiga dakin Imaan, ganin tayi bacci ta tasheta tana
mika mata wayar hannunta tace "Me ya sa kika kashe wayar ki" Imaan na murxa ido
tace "Kila mutuwa yyi ba charge" Ammi tace "Toh idan kin gama ki maido min wayata
daki" Imaan tace "Toh" sannan ta kai wayar kunne tace "Daddy ina yini" Daga daya
bangaren ya amsa yace "Why is ur phone switched off" ta langwabar da kai tace
"Daddy ban sa a charge ba tun jiya" yace "Toh kiyi kokari ki sa ya jikin?" Tace
"Naji sauki, daddy ina missing dinka yaushe xaka dawo?" Yace "Weekend in sha Allah"
ta wara ido cike da jin ddi tace "Plss daddy ka dawo week end din kar ka daga, wllh
ina son in ganka" kamar xata yi kuka ta kare, yyi murmushi yace "Sure dear, plss ki
daina wasa da shan drugs din ki kinji" tace "Ina sha Allah daddy, har yanxu Dr ma
bai xo ba" yace "Ehh mun yi waya daxu yace bai dawo ba" Imaan tace "Toh" yace
"Sleep tight dear, banda kunna Ac" yar dariya tayi tace "Toh daddy byeee" katse
wayar tayi ta mike ta kai ma Ammi daki sannan ta dawo dakinta ta shige duvet. Yau
Friday Imaan na dawowa schl bayan tayi wanka tana kokarin saka kayanta taji k'aurin
abincin da Ammi ta bar mata a kitchen kan gas don tana shigowa gidan Ammi ta fita
kasuwa yin cefane, da gudu ta fita daure da towel don kashe gas din don dama sae da
Ammi tayi mata kashedi kan cewar kada ta yarda abincin ta ya kone, muryar inna ta
ji a balcony tana cewa "Aa kawai ni dai naga kwana biyu bata shigo bane shine nace
in xo in duba ko jikin ne, tunda haka Allah yyi ta mai laulayi, ni jiya ma ko
abinci basu kawo min ba wllh, in ma ba ta da lafiya ita Aishar baxata iya takowa ta
kawo min abincin ba tunda ba uwarta Habiba bace, abu dai gashi ba tsari da ni
fitinanniyar tsohuwa
ce ba Bukar xan kira ince matarsa ta bar ni da yunwa ba?" muryar Yusuf imaan taji
yana dariya yace "Toh ae an kai maki daga gidanmu naga" da sauri Imaan ta shige
daki ta dau Hijab dinta ta fito ta shige kitchen ta kashe gas din sannan ta bude
kofar kitchen din ta fice tana murguda baki ta sa Hijab dinta da iyakarsa gwiwa, ko
takalmi bbu kafarta ta dinga tafiya har ta zagayo front din gidan, Mujaheed ne
xaune kan farin kujera yana waya, ta turo baki ta wuce sa da sauri, ko minti biyar
ba ayi da wucewarta ba shi ma ya ji muryar inna tana tahowa, mikewa yyi da sauri
tun kan ya bar wajen ta gansa, da karfi ta kwalo masa kira tana murmushi, ya ki
juyowa har ya sha corner, Yusuf sai danne dariyarsa yake, Inna ta bude baki tace
"Wato ni Mujaheed xai walakanta ina kiransa ya min banxa kai shaida ne ko Isuhu"
tana magana tana kunce ha6ar xanin xata goge kwalla, Yusuf ya kasa daurewa ya fara
dariya yace "Ke fa kika ce kar ya sake xuwa bangaren ki..." A fusace tace "To shi
mahaukaci ne bai san bacin rai ba" Karo Mujaheed ya kusa yi da Imaan dake kokarin
lekowa taga ko inna ta taho bangaren, ya hade rai yace "Baki gani ne?" Tana shafa
Inda ya bugeta tace "Ko ba inna bace, ta wani biyoni gidanmu anjima tace ina mata
rashin kunya" tafiyarsa yyi ya bar ta wajen tsaye, ta turo baki ta bi bayansa, jin
tafiyarta a bayansa ya tsaya ya juyo yace "Wai me yasa kike bi na ne" Tace "Ni ba
bin ka nake ba tafiyata kawai nake" Tsayawa yyi ya daure fuska yace "To yi tafiyar
ki, bana son ganin ki kusa da ni" ba ta ce komai ba ta fara tafiya kamar mai
counting steps dinta, yana ta tsaye yana jiran tayi nisa ganin ynda take tafiyar ya
girgixa kai ya wuce ta cikin lokaci kankani, sai a sannan ta kara saurinta har ta
jera da shi, d'an murmushi yyi bai dai ce komai ba bai kuma kalleta ba, sai da suka
kusa entrance din kitchen din part dinsu tace "Yaya ka mance promise da ka taba min
2 years back koh?" Kallonta yayi kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Na me?" Ta
wara manyan idanuwanta tace "Idan nayi saukan al-quran, gashi mun kusa in few
months time" tabe baki yyi xai bude kofar kitchen din yace "I can't recall...." Ta
xaro ido ta rikosa da sauri tace "Wllh nasan baka mance ba" Buge hannunta yyi yana
mata wani kallo yace "Keee" Ta turo baki tana kallonsa, yace "Sakeni kar in mare
ki" sake sa tayi ya bude kofar kitchen din ya shiga ya kulle, tana ta tsaye wajen
bayan few minutes ta murguda baki ta wuce, ta kitchen dinsu ta bi ta kulle kofar
sannan ta wuce dakinta ta sa kayanta. Yau tunda Imaan ta tashi take ta murna, gaba
daya farin cikin ta ya kasa boyuwa, Kitchen ta shiga tace "Ammi da yaushe daddy xai
iso?" Bude baki Ammi tayi tace "Kina kallon agogo kuwa Imaan?" Imaan tace "Ammi wai
yau ma da daddyna xai dawo sai naje islamiyya?" Ammi ta mata wani mugun kallo tace
"Uwar me xa ki xauna ki min ko yace maki da safe xai taso, common kin 6ace min a
nan kin je kin shirya ko sai na 6ata maki rai" a hankali Imaan ta juya a sanyaye ta
koma bedroom dinta ta fiddo uniform dinta ta shiga sa wa, sai da Ammi tayi mata jan
ido ta amince da yin breakfast da ta hada mata, tana xaune dinning tana shan shayin
da kyar Maimoon ta shigo parlon sanye da uniform, Ammi dake goge goge a parlorn
tace "Maimoon ku yi wucewar ku kar ta bata maku lkci ko da kafa ne sai ta je"
dariya kawai Maimoon tayi ta fita, Imaan ta mike don kanta ganin takwas ya wuce ta
dau jakarta ta fita tana matsar kwalla ko ta kan kudin makarantar bata bi, Ammi dai
ko kallonta bata yi ba, Tsaye taga Mujaheed jikin motar banda masifa babu abinda
yake ma kannin nasa, duk kallonsa kawai suke babu wanda yace komai, "Don samun waje
nan nan da islamiyyar ma sai an kai ku a mota ku ga yan gayu ko, to wllh ni ba
driver din kowa bane a cikin ku da xa a dinga cewa in ajiye ku a makaranta, Yusuf
da ya ga xai iya sai yyi, I won't tolerate that shittt" A hankali Ummi tace "Amma
ya Mujaheed kawai don kana nan ne yasa xaka kai mu ai ba kai ke kai mu ba dama,
kuma Abba yace kila Monday xa mu samu sabon driver...." wani kallo ya dinga mata
fuska daure, ta sunkuyar da kanta, Imaan da isowanta kenan ta bude motar xata shiga
ya dakatar da ita yace "Kee, do I look like drivern gidanku da xaki ajiye ni for
the past 15 mins a nan, to ke daga yanxu ma xa ki fara naki trekking din" yana
fadin haka ya nuna mata makeken gate din gidan yace "Bi can ki kama hanyar
makarantar" ta wani gwalo ido tana kallonsa, lkci daya ta juya kamar xata yi kuka
xata koma part dinsu tace "Ni dai ban ta6a tafiya da kafa ba...." Wani tsawa yyi
mata yace "Wllh ki ka yarda na takowa har Inda kike sai na sa ki kuka" tsayawa tayi
tana hawaye don bata mance last abinda ya mata ba, ya nuna mata gate on a serious
note yace "Bi can" Gate din ta nufa tana kuka ya jira ya ga fitar ta sannan ya
shiga motar ya bar gidan har ya wuce ta. Tsaye tayi bakin titi ta rufe fuskarta da
Hijab tana kuka, ta kusa minti sha biyar tsaye a haka taji cikin cool voice ance
"Are you okay" xame hannunta tayi a hankali daga fuskarta tana lekan ko waye ta
cikin hijab dinta, wani dogon matashi ne da baxai wuce thirty two ba, yana sanye
cikin kananun kaya idonsa sanye da bakar spec, dogo ne shi din sosai, sannan shi ba
baki ba kuma baxa a sa shi a jerin farare ba, kuka ya kara taho mata ta dinga
rerawa, yace "Subhanallah, wani abu ya faru da ke ne? Talk to me plss" Cikin rawar
murya tace "Yaya ne ya ce baxan shiga mota ba trekking xanyi kuma islamiyyar mu da
nisa wllh" kallonta ya dinga yi da mamaki, ta sake lekosa ta cikin Hijab suka hada
ido ta yi saurin rufe fuskar tana shessheka, ya d'an yi murmushi yace "Kin masa
laifi kenan" girgixa masa kai tayi, yace "Toh mu je in ajiye ki ga ride dina can,
while going inside the filling station na gan ki tsaye bayan nayi refilling tank na
fito I still saw u the way you were so I decided to check if you are alright" shiru
tayi bata ce komai ba yace "Mu je to" tace "A'a" yace "Ohk in samar maki adai
daita?" Kai ta gyada masa, ya tsayar da adai daitan ta shiga ya basa kudin, a
hankali tace "Nagode" ya mata murmushi kawai mai adai daitan ya ja suka bar wajen,
Yusuf ne ya dauko su daga islamiyyar bayan sun tashi karfe sha biyu, tun a mota ya
dinga tambayar Imaan me ya faru ganin yanda take yamutse fuska, da kyar tace
"Kafana ke min ciwo" yace "Toh sannu, idan muka isa gida sai ki shafa maganin" a
hankali tace "Toh" suna isa gidan da kyar ta fito motar, Yusuf ya kama hannunta ya
rakata har sashin nasu sannan ya bude mata kofa ta shiga ciki, wanka kawai tayi ta
saka doguwar riga Ammi ta shafa mata methylated lotion din da take shafawa a
kafafuwanta sannan ta sa ta kwanta nan da nan kuma bacci ya dauketa, dab da la'asar
Ammi ta tasheta, Ammi bata mata xancen islamiyya ba Imaan ta wara ido ganin irin
girke girken da Ammi tayi tace "Ammi is all this for daddy?" Ammi tace "No it's for
Imaan" murmushi Imaan tayi ta rungumeta ta baya tace "Thanks sweet mum" Ammi tace
"Ki tafi kiyi sllh ko baki ga lokacin hr ya gota ba" da sauri ta koma daki, tana
idar wa ta fito, Ammi tace "Daddy ya kira yana gate, ki fita ki shigo masa da kaya"
da sauri Imaan ta nufi kofa Ammi na kiranta ta xo ta sa hajib don rigar jikinta
karamin hannun garesa amma tuni ta fice, dai dai nan mai gadi ya bude gate sai ga
motar Daddynta, da gudu ta nufi parking space ta tsaya cike da murna, Mujaheed dake
kokarin bude motarsa suka yi ido hudu da daddy da ya fito Imaan ta rungumesa, Daddy
ya sakar masa murmushi, hakan yasa ya nufe sa kamar mai kirgan steps dinsa, daddy
na shafa kan Imaan yace "Ba kya girma koh Mamata" ta kara kankamesa tace "Don Allah
daddy ka daina dadewa haka wllh ina Missing dinka" yyi murmushi yace "To xan daina
mamana" Mujaheed ya risina yace "Sannu da hanya Abba" Wani hade rai Imaan tayi tana
hararansa ta gefen ido, Daddy na murmushi yace "Thanks Son, ka bar mu a birnin
tarayya ynxu koh" murmushi Mujaheed yyi yace "Ae kam daddy" daddy yace "Toh Allah
yayi jagora, ya aikin fa?" Yace "Ae ban fara ba sai Monday Abba" Daddy yace "Allah
ya kai mu" Daddy ya mika ma Imaan da ta turo baki ledan apples dinta da chocolates
don a ko da yaushe tsaraban ta kenan, Mujaheed dai ko kallonta bai yi ba ya dau
jakar laptop din daddy da wasu files ya nufi part dinsu, Murguda baki Imaan tayi ta
jera da daddynta tana ci gaba da gaya masa yanda tayi kewarsa, Mujaheed ya sunkuyar
da kai ya gaida Ammi bayan ya ajiye jakar hannunsa da files, ta amsa ta dau jakar
ta wuce daki, Daddy ya xauna yace "Barrister bai dawo ba ko Mujaheed?" Mujaheed
yace "Ehh bai dawo ba" Daddy yace "Ohk mun yi magana daxu ma" Mujaheed ya dukar da
kai yace "Toh Allah ya huta gajiya Abba" daddy yace "Madalla nagode son" har ya
fara tafiya Daddy ya kalli ledan apples da chocolates da Imaan ta sa gaba tana
dubawa yace "Son baxa ka Debi apples ba" Da sauri Imaan ta jawo ledan jikinta tana
kallon daddy, Mujaheed da har xai ce A'a don he isn't a fan of Apple ganin abinda
tayi yayi kasa da kai yana shafa gashinsa yace "Toh Abba" daga haka ya nufeta, bude
baki tayi tana kallon daddy lkci daya hawaye ya kawo fararen idonta, Mujaheed ya
jawo ledan yana kallonta da kyau ya cire spare leda ya debi apples har hudu a cikin
guda takwas da Daddy ya siya ya xuba a wani ledan yana kallonta har sannan, ya kara
bude ledan chocolates din ma ya debi mai yawa ya xuba a ledan hannunsa, har ya mike
ya sake dawowa ya dau Apple daya ya sa ka a ledan, daddy ya dauke kai yana
murmushi, Mujaheed bai yarda ya kallesa ba yace "Nagode Abba" daga haka ya fice
parlon.
[6/11, 12:34 PM] +234 703 570 1601: 🌟⭐ *Imaan*⭐🌟

✍🏻
_By Khaleesat Haiydar_

4.....

Daddy ya kalli Imaan dake goge hawayen idonta yace "Don yayanki ya debi apples kike
kuka Imaan?" Ta marairaice tace "Toh daddy ai ba shi ka siyo ma ba gashi ya kwashe
min gaba daya kuma wllh baya cin apple" Daddy yyi murmushi yace "Shi yace maki bai
ci" cikin rawar murya tace "Ae nasan baya ci tun da can" Daddy yace "Toh anjima
idan na fita xan karo maki" a hankali tace "Toh nagode" yace "Wai amma me ya hada
ku da yayan naki all of a sudden Imaan" Ammi da ta fito parlon tace "I am still
wondering also, lkci daya aka yi parting" Daddy yace "Ko kin masa wani abun ne dai"
ta turo baki ta dawo kusa da daddy tace "Kawai dai naga ya xama mugu ne shi sa na
daina kulasa" Dariya kawai daddy yayi, Ammi tace "Har nan ma ai baya shigowa yanxu"
Daddy yace "Toh Allah ya kyauta" Imaan tace "Daddy ni dai ka daukan min personal
driver dina plss" daddy yace "Ba Abbanku xai daukar maku driver ba, ai mun yi
magana da shi bayan tsohon drivern ya wuce" Tace "A'a daddy ni dai nawa daban nake
so, kilan ba yanxu driver din ma xai xo ba, yau fa Yaya bai bari na shiga motar ba
don na bata masu lkci da kafata na tafi islamiyya shi sa tun da na dawo duk jikina
ke ciwo sai da Ammi ta shafa min magani na kwanta da na tashi shine naji sauki"'
Murmushi kawai Daddy yayi ya mike yace " Bari in yi wanka daughter " daga haka ya
wuce bedroom dinsa, Ammi tace "Sai ki tashi ki kai ma Inna abinci ko yau ma baxa ki
ba" Ta kalli Ammi da sauri tace "Ammi ca tayi bata son sake ganin kafata a part
dinta fa, kuma in je yanxu ta gaya ma daddy" Ammi tace "Tashi ki dauki abinci ki
kai mata nace" Daga haka Ammi ta bar parlon, mikewa Imaan tayi ba don ta so ba ta
shiga kitchen, kusan duk abinda Ammi tayi ma daddy sai da ta dibar ma inna duk ta
ajiye a basket, Imaan ta dau basket din me dauke da abincin ta fita, har ta isa
part din Inna fuskarta a daure yake irin ko kulata din nan baxata yi ba, ta dinga
kallon takalman dake bakin kofa kafin ta bude kofar ta shiga, Mujaheed na xaune
yana kallon inna dake bada labari tayi mitsi mitsi da ido, banda murmushi babu
abinda yake don da wuya yake dariya, su Maimoon da Rahma kuwa dariya har da
kyakyatawa, Inna ta saita hannu sama tace "Ji kawai muka yi ratatatata.... Ba sai
kakan ku ya shige karkashin gado ya bar ni da halina da 'ya yana ba, lkcn Bukar na
bayana sai tsala ihu yake, Ahmadu kuwa fitsari ya dinga saki yayi sau uku a
wando...." Ganin Imaan Inna tayi shiru ta jawo daya daga apples biyar dake cikin
leda a gabanta ta kai baki, Har sannan su Maimoon dariya kawai suke, imaan ta ajiye
basket din hannunta tana kallo chocolates din da Daddy ya kawo mata a hannunsu
Maimoon, ta saci kallon Mujaheed ta juya xata fita Inna ta tabe baki tace "Ga
dambun naman ki can a daki ni dai na ajiye maki bana bi ta halin ki ba" ba tare da
ta juyo ba tace "Bana ci" inna na ci gaba da cin apple dinta tace "To wa yayi
asara?" Mujaheed yace "Yana ina a dakin?" Da sauri Imaan ta juyo ta shige dakin,
Inna tace "Ya xaka ce yana ina bayan ka ci rabon ka da wanda ma ka dauka ban baka
ba" yace "Haba" tayi tsaki tace "Yana nan cikin roba xa ki gansa a rufe, duk naki
ma ya fi yawa" Imaan ta fito rike da uban dambun naman da inna ta ajiye mata a bowl
mai murfi ta nufi kofa, inna tace "Wannan liyafar hala Bukar ne ya dawo?" Imaan
tace "Bai dawo ba" daga haka ta fita, Inna tace "Duk ta ma fige kamar bata cin
abinci" Rahma tace "Mu dai ci gaba da ba mu labarin da kike yi don Allah inna" inna
ta gyara xama xata ci gaba, mikewa Mujaheed yyi ya fita parlon. Imaan na komawa
bangarensu ta tadda Yusuf ya shigo gaida Daddy, Ya bi ta da kallo ta boye bowl din
hannunta tana wara masa manyan idanuwanta tace "Nasan ka ci naka dai" fitowar Daddy
parlon yasa Yusuf bai ce mata komai ba, daddy yace "Engnr ashe kana gari" Yayi
murmushi yace "Ina nan daddy, da fatan kun iso lafiya" yace "Alhmdllh My son, ya
aikin fa" Yace "Mun gode Allah Daddy" daddy ya xauna kujera yace "Madalla, kowa dai
lafiya koh?" Yusuf yace "Duk lafiya" Yusuf bai wani dade ba ya mike yace xai wuce,
daddy yace "Baxa ka tsaya mu ci abinci ba" Yace "Alhmdllh daddy na ci abinci" Ammi
dake dinning tana jera abincin tace "Anya Yaya Yusuf" dariya yayi yace "Ammi wllh
na koshi" tace "Toh shikenan" sallama yyi ma daddy ya fita. Bayan magrib daddy xai
je gaida inna babu yanda bai yi da Imaan su je ba ta ki, har hakan ya basa mamaki
ya tafi shi kadai, inna na goge tiles din parlonta daddy ya shiga da sallama, ta
mike tace "Amma dai gaskiya Bukar ka dinga kwa6a ma yar ka ta daina karya, ce min
fa tayi baka dawo ba" Ya xauna yana murmushi yace "Sannu inna, ina yini" ta
shimfida tabarma ta xauna tace "Lafiya lau, amma ai karya ba shi da amfani kuma a
gaskiya Imaan ta iya karya" Shi dai bai ce komai ba, tace "Toh ya hanyan?" Yace
"Alhmdllh mun baro hanya" tace "Wannan karan kuma kamar baxa ka sake dawowa ba"
yace "Aiki ne yyi yawa Inna" tace "Toh Allah ya bada sa'a ya tsare mana ku a duk
Inda kuke, ya maka albarka" yace "Ameeen inna" Tace "Toh ya xa ayi, Allah ya
kaddara a can abincin ka yake, banda haka na tabbata da kana gidan nan da ka dinga
share min hawaye daga bakin cikin da nake fuskanta" Daddy na kallonta da mamaki
yace "Bakin ciki kuma Inna?" Inna tace "Yo bakin ciki mana Habu... Kaga yayanka
baxai fito daga masallaci ya tako nan tun asuban ba ya gaisheni sai ina jin wajen
karfe tara xai taho da safe ya duka can bakin kofar ya gaida ni a gurguje ya kara
gaba, bana sake ganinsa Bukar sai ina kokarin kulle kofa ta da daddare shi ma Allah
yasa ya yi minti biyu xaka ga yace sai da safe daga haka ya wuce, Kaga matar nan
tasa Rukayya take ko wa? Uwarsu Mujaheed dai wllh kaji rantsuwar musulmi tafi wata
biyu ina ga bata tako ta xo nan ta gaisheni ba sai ta gan ni a tsakar gida ko a can
bangaren, ita kuma dayar mai kama da fulanin Bararoji wato Amina da suke ce ma Anty
sai ta bushi iskarta xata kwaso kafafuwa ta xo gaisheni, ita wnn farar wa take da
suna? Uwar wannan yarinya Imaan d'an wankin da take min da duk ta watsar sun
xugeta, in kuwa wannan 'ya taka Imaan borinta ya tashi ta ki kawo min abinci to
ranan fa da yunwa xan kwanta a gidan nan, Aisha ta fi karfin ta taso takanas ta
kawo min da kanta, to me yafi wannan bakin ciki Yaro? Gashi gaba daya 'ya yanku sun
rainani sun maida ni ba bakin komai ba, sun maida ni kakarsu tun ma ba wannan katon
Mujaheed ba da ramammiyar 'yar ka, sai wannan kazamar Ummi, ni nasan da sun ga ido
wllh taka ni xasu dinga yi suna wucewa, isuhu kadai ke raga min a gidan nan sai
wannan yarinya Seeyama, Imaan idan ta fara balbale ni wlh shiru nake, haka ma
Mujaheed yaron da aka haifa a gabana, to ina dalili ina da gata na ta ko ina don
dai d'an abincin da ake yarfa min a kwano sai a maida ni bola" Daddy dake ta
saurarenta ya dago kansa a karo na farko yace "Kiyi hakuri don Allah inna" a fusace
tace "Na gaji da jin wnn axxalumin kalman, ayi ta baka hakuri ana cutan ka, ni dai
a fita harkata, don idan tsiyata ta debeni wllh sai an fita har kasashen waje ana
nemana" Daddy yace "Xa a gyara Inna, duk ki yafe masu, ita Imaan xan sameta yanxu,
shi ma Mujaheed din xan gamu da shi" Tace "Atoh, sai ka xaunar da su ka tambayesu
kaji ko xaman gidan ne basa son inyi, ka tambayesu dalilin da yasa basa fitsaran su
a waje sai a cikin gida cikin gidan ma a kan uwarka, kayi masu jan ido ka nuna masu
bacin ranka Yaro" Daddy yana murmushi yace "In sha Allah" nan suka ta6a hira amma
kusan hiran gaba daya na complain ne daga karshe daddy yace mata xai wuce masallaci
don an kira isha. Daddy na dawowa masallaci ya dinga kallon Imaan dake xaune parlor
tana cin abinci, ya xauna yace "Imaan yanxu ita innar kika mayar abar wasar ki a
gidan nan?" Kallonsa ta dinga yi kamar zata yi kuka, ya hade rai yace "would you
take ur eyes off me silly girl, haka kike ma uwar ki? I warned you the last time a
kan haka shine kika sake repeating foolishness din yanxu ko?" Ta sunkuyar da kanta,
ya gyada kai yace "Nasan maganin ki, tashi ki bar min parlor" tashi tayi da sauri
ba tare da ta bi ta kan abincin ba ta shige bedroom dinta ta kulle, ita dai Ammi
bata ce komai ba, Daddy yace "I don't like this nonsense character of her, ita
innar abokiyar wasanta ce, ke kuma Aisha baki taka mata burki, a kan me xata dinga
rainata, I don't like that, and I am going to teach her manners soon" Ammi ta tabe
baki ta mike ta dauke abincin da ta bari ta kai kitchen ta rufe, ta tsaya kitchen
din tana wanke plates da ke sink. Washegari wajen karfe bakwai da rabi Imaan ta
fito sanye da uniform din islamiyya, kanta a kasa ta gaida Ammi dake jera breakfast
a dinning, Ammi dake kallonta tace "Wato ke ba isa a maki fada ba shine kika kwana
kuka ido ya kumbura koh?" Ta fashe da kuka tace "Ni Ammi don Allah kar ki sake ce
min in kai mata abinci kullum sai tayi ta ma mutum sharri alhalin ba abinda nayi
mata" Ammi tace "Ko ban baki abinci kin kai ba ma da kanki naga kike kwasan
kafafuwanki kije can din ko da kuwa koranki tayi" Imaan ta hade rai tace "Yesterday
was the last day da xan je part dinta, har abada baxan sake xuwa ba" Ammi tace "Toh
bari dai ya ji ki gashi can ya fito, ni ba ruwana" shiru Imaan tayi tana juya
shayin da Ammi ta hada mata, Daddy dake tsaye parlon yace "Madam me yasa ba a kai
ma Inna breakfast ne wai?" Ammi tace "Breakfast kuma?" Yace "Ehh ai ya kama ta ne"
tace "A'a don Allah yallabai kar ka hada ni da ita, kullum sai Abba ya tura mata
bread, tana da kayan shayi kuma tana da heater ta iya amfani da shi, meye breakfast
din dama idan ba shayi da bread ba sai kwai wani lkcn, lunch da kanta tace bata so
a daina kai mata wai jagwalgwalon yara ne" Tuni Daddy ya xauna ya sa news channel,
Ammi ta shiga kitchen ta ci gaba da abinda take, Imaan ta gama breakfast din ta
mike ta iso cikin parlor ta durkusa ta gaida Daddyn nata, sau daya ya kalleta ya
amsa ya ci gaba da kallonsa, ta mike ta tafi kitchen ta amshi kudin makarantar ta
gun Ammi ta fito ta dau jakarta bayan ta sa takalmi da safa tayi ma daddy sallama
ba tare da ta kallesa ba ta
fice daga parlon, kiranta daddy yyi ta juyo ta dawo ta sunkuyar da kanta tace "Ga
ni" room freshener har biyu ya nuna mata dake ajiye yace "Dauka ki kai ma Inna
kafin ku wuce" shiru tayi tana kallonsa kamar xata yi kuka, bata dai ce komai ba ta
durkusa ta dauka sannan ta fita xuwa part din inna, Inna na ta goge goge bayan ta
gama share ko ina fesss, banda kamshin turaren wuta babu abinda ke tashi a parlon,
imaan bata kalleta ba ta ajiye abun hannunta fuska daure tace "Ina kwana" xata fita
inna tace "Me ya sami idonki ni Asabe? An umaki wani abun ne" Imaan da har ta kai
kofa ta juyo lkci daya ta fara kuka tace "Kawai sai kije kice ma daddy ina maki
rashin kunya yaushe rabon da in xo nan...." Tana fadin haka ta fashe da matsanancin
kuka, Inna da ta saki baki tace "Shine ya maki me?" Cikin kuka tace "Fada ya dinga
min mana yace zai yi magani na" Inna ta dau dankwalinta ta fita parlon imaan ta bi
ta da kallo tana share idonta, Ko sallama babu inna ta bude kofar parlon, daga
daddy har Ammi suka daga kai suna kallonta, tace "Bukar dama yaro ba lallabasa ake
yi ba a rayuwar nan, daga mun yi magana tsakanina da kai sai ka taho ka far ma
yarinya da bala'i, to ae gwara ita sau dubu a kan sauran, Imaan bar ta da son
jikinta amma wllh wllh bata da matsala, haka kawai ka ja mata wani cutan dama gata
mai cuta iri iri kamar ta kashe d'an mutum, yanxu da kasa ta kwana tana kuka idan
wani abun ya sameta me xa ka gaya ma Allah, kai dai wllh ka cika bala'i, ba haka
yayanka Ahmadu yake ba, ba ruwansa da irin wannan hali, to wai ma me ta min da xafi
haka da xaka sa ta kuka haka, ga abun duka can Mujaheed me nuna ni da yatsa, mai ce
min Hajiya, ni tunda nake wllh xan iya kirga sau nawa Imaan ta mayar min magana
shima kuma duk laifina ne....." Ammi dai tuni ta shige kitchen, Daddy kuma ya kasa
cewa komai, Inna ta juya ta nufi kofa tana cewa "Wannan dai ba yi bane, kamar ba
kai ka haifeta, yar gata daga ita sai ita amma kuma ka takurata, da wanne xata ji
da rashin karo mata kanni da ba ayi ba har yau ko kuma da fitinar mahaifinta, kuma
ka tashi ka kawo min turaren bature da ko kamshi babu wai in fesa a daki, to uwata
bata ce min je ki kya gani ba turaren wuta tsadadde mai kamshi nake nufi, sai ka ba
matarka mai kumewa a daki kamar matar liman ta fita kasuwa ta siyo min" daga haka
ta fice ta kulle masu kofa. Dama imaan direct gun mota ta nufa bata yarda ta ma bi
ta part dinsu ba. Yusuf ne ya ajiye su islamiyyar, karfe sha biyu Anty ta dauko su,
A hankali Imaan ta bude kofar parlonsu tana lekan ciki, babu kowa hakan yasa ta
shiga ta rufe kofar ta nufi bedroom dinta da sauri, tana kokarin cire Uniform dinta
Ammi ta bude kofar, Imaan ta gaisheta kanta a kasa, Ammi tace "Amso min card waje
kafin ki cire uniform din" Imaan ta amsa tana kallonta tace "Ammi daddy fa?" Ammi
tace "Yana daki" Imaan ta marairaice tace "Ni fa ban gaya ma inna ya min fada ba,
kawai taga idona ne haka" Ammi tace "Wannan ya rage naku ke da shi, ni kiyi sauri
ki amso min card din" imaan ta maida Hijab dinta ta fita, kiosk din is just a house
from theirs, ta amso card din ta juyo ta shigo gida, Umma ta gani tsaye parking
space alamar xata fita, Mujaheed ya iso wajen ya bude mata back seat, sannan ya
shiga driver seat, Imaan na hada ido da Umma dama ta dauke kai tayi wucewarta,
Mujaheed ya bi ta da kallo ta madubi, Umma ta shiga cikin motar tace "Wllh duk
ranan da ka gaida uwar yarinyar nn ko da mistake a gidan nan ban yafe maka ba
Mujaheed, duk kanninka ma na karanta masu haka nasan kuma sun dauka...." Yana
kallonta ta madubi yace "Haba Umma kema kin san....." Ta karasa masa da sauri tace
"Baxa ka iya ba ko? tunda ga ta kanwar Ahmad ko kanwata, Mara tunani kawai da bai
san ciwon uwarsa ba, to mu xuba da kai wllh, ba dai makiyana su ne mutanen arxikin
ka ba a gidan nan, ka ci gaba, a ta dalilin munafukar uwar yarinyar nan na bar
gidan ubanka for good 5 years, ta hade kai da kishiyata suka yi ta kulla min
makirci har ubanka ya sakeni, da yake akwai sauran xamana a gidan na dawo few years
back na tarar baka da masoya da ya wuce makiyana, ka maida Aisha uwarka, ka nuna
duk gidan nan baka da kanwa da ya wuce yarinyar Aisha, yarinyar da bata gaisheni a
ynxu ko idona xai makale a nata saboda uwar ta hanata, da kyar da siddin goshi da
rokan Allah na rabaka da su, ni da ba a kan idona na haifeka ba kuma ina haihuwar
ka aka ajiye min kai a gefe na da wllh bbu abinda zai sa baxan ce canjen ka aka min
a asibiti ba, sam baka san mutunci na ba, ace makiyana su ne masoyan ka Mujaheed?
Anya kana son gamawa lfya kuwa?" Shi dai ya kasa cewa komai, ta gyada kai ta bude
motar ta fice tana cewa "Ga ka ga su ai, daga ynxu ma ka tatttara yanaka yanaka ka
koma bangaren nasu" a hankali yace "Umma I have avoid a lot of things a gidan nan
kema kin sani, wllh ko kadan bani son abinda xai bata maki rai, don Allah kiyi
hakuri...." Ko saurarensa bata yi ba ta fice daga compound din ya sauka ya bi
bayanta da sauri. Washegari har Ammi ta gama hada breakfast ta fito daga kitchen
imaan bata fito daki ba, ta kalli agogo ganin bakwai da quarter ta nufi dakin ta
bude ta shiga, kwance ta ganta ta dukunkune cikin bargo, Ammi ta karasa da sauri ta
cire bargon tace "Are you okay Imaan?" Ta bude ido kamar xata yi kuka, Ammi ta
dinga kallonta don jikinta ya dau xafi sosai, a hankali tace "Ina ke maki ciwo
kuma?" Kafafuwanta ta nuna mata da kai, hawaye cike idonta tace "Ammi duka jikina
ciwo, jiya ban yi bacci ba" Ammi ta kamo hannunta cikin sanyin murya tace "Ba ki
sha magani ba jiya da daddare ko daughter" ta nuna ma Ammi magungunanta a side
drawer tace "Na sha Ammi" saketa Ammi tayi ta mike ta shiga bathroom ta hada mata
ruwan wanka ta fito tace "Toh shiga kiyi wanka sai ki kara shan maganin" da
taimakon Ammi ta sauka kan gadon, Ammi na rike da ita suka shiga bathroom, bayan ta
wanke baki Ammi ta taimaketa tayi wanka ta fito, barin ta tayi ta sa kaya ta tafi
hado mata shayi, Daddy na xaune parlor yana dube dube a laptop, ta tsaya bayan
kujerar tace "Yallabai jikin imaan fa kar ya rikice mana ko xa aje asibiti tunda
likitan ma baya nan" daddy ya mike yace "Bata jin dadi ne" Ammi tace "Nima yanxu na
shiga ganin bata fito ba, her temperature is high tace bata yi bacci ba" daddy ya
d'an yi shiru, Ammi tace "Kwanakin baya ciwon ya lafa sosai, as from some weeks ago
yanxu duk sai ya tasar mata ga xaxxabi da ciwon kai kuma tana shan drugs dinta"
Daddy yace "Toh ta shirya mu tafi asibiti" Ammi tace "Toh" komawa yayi ya xauna,
ita kuma ta wuce dinning don hada mata shayi. Kwance ta sameta bayan ta sa abayar
da ta fiddo mata, da kyar Imaan ta sha shayin, Ammi ta fesa mata turarrukan ta ta
bata veil din abayar sannan suka fito parlor, kwanciya tayi kan kujera tana gaida
daddy dake rike da makullin mota yana jiransu, ya amsa yace "Sannu mamana, tashi mu
je to" mikewa tayi ya kama hannunta suka nufi kofa Ammi na masu Allah ya kiyaye
hanya, A hanya daddy ya hadu da Abba ya taho daga part din Inna, gaisawa suka yi,
Imaan ma ta gaishesa a hankali, Abba yace "Jikin ne ya tasar mata?" Daddy yace
"Wllh kuwa, xa mu je asibiti ne yanxu" Abba yace "Subhanallah tana shan magunguna
kuwa" Daddy yace "I think so" Abba yace "Toh likitan ta fa?" Daddy yace "Yayi
tafiya ne" Abba yace "Toh tunda Muhammad na nan ba sai ya dinga dubata ba kafin
likitan nata ya dawo, ko gwara a tafi asibitin?" Daddy yace "Noo in xai dubata
shikenan, dama don likitan baya nan ne xa mu je asibitin" Abba yace "Let me give
him a call, na barsa sashin inna, idan ma asibitin xa a sai ya kai ta kawai" Yana
kokarin kiran Mujaheed suka hangosa yana tahowa, Abba ya maida wayarsa, har
Mujaheed ya isa parking space da suke tsaye kallonsu kawai yake, Ya risina ya gaida
Daddy, ya amsa masa da fara'a, Abba yace "Imaan xaka duba Mujaheed, bata jin dadi"
Sosai gabansa ya fadi ya kalli Imaan dake jingine da mota duk ta wani langwabe.
I appreciate my fan's love always, ina yinku fisabilillah😘😍
[6/11, 12:34 PM] +234 703 570 1601: 🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟

✍🏻
_By khaleesat Haiydar_

5.....

Gaba daya Mujaheed ya daburce ya rasa abin cewa, Abba yace "Ko in kai ta asibitin
kawai" da sauri yace "Noo Abba, naga bani da kayan aiki a gida ne, sai dai in kai
ta asibitin in duba ta a can" Abba yace "Toh hakan na da kyau" Magana yake amma
gaba daya rabin attention dinsa na kan window din dakin Umma duk da baya hango
komai, amma fatansa yanxu ace bata tashi bacci ba duk da yasan da wuya, Ya sunkuyar
da kansa yace "Toh xan dauko makullin mota a ciki" Daddy ya mika masa nasa makullin
motar yace "You use my car, duk yanda ake ciki you let me know" Mujaheed ya risina
ya amsa makullin motar yace "Toh Abba" daddy yayi ma yayan nasa sallama ya wuce ba
tare da ya kalli imaan da ta cika saura kiris ta fashe ba, bayan ya tafi Abba ya
kalleta yace "Sannu Mamana" Ganin hawaye idonta yace "Baki son bin Muhammad din
kenan?" Da sauri ta gyada masa kai hawayen na sakkowa idonta, yace "Kuma baki son
daddyn naki ya huta koh, am sure kila xuwa anjima ko gobe xai koma bakin aiki, shi
Mujaheed din ba yayanki bane?" Ta fashe da kuka tace "Abba ihu xai ta min a hanya
fa" Abba yyi murmushi mai sauti sai dai bai ce komai ba, Mujaheed dai sai kallonta
yake ta gefen ido, Back seat Abba ya bude mata yace "Shiga" a hankali ta shiga ta
jinginar da kanta jikin motar, Abba na kallon Mujaheed yace "You take very good
care of her, ko kallon banxa ban yarda kayi mata ba" Ya sauke idonsa yace "Toh
Abba" Abba ya daga mata hannu ta mayar masa tana goge idonta, ya juya ya wuce ciki,
Mujaheed ya gama warming motar yayi horn ana bude masa gate ya fita gidan, sai da
suka hau saman titi yace "Saboda baki son xuwa schl shine kika fake da ciwon karya
salon ki ba mutane wahala koh?" Jin bata ce komai ba ya kalleta ta madubin motar,
murguda masa baki take, suna hada ido ta turo bakin kamar xata yi kuka sai dai bata
ce komai ba, ya gyada kai yace "Xaki gwammace schl kika yi tafiyar ki yau" ta fashe
da kuka tace "Dama dai Abba yace duk abinda ka min in gaya masa" Bai tanka ta ba
har suka iso asibitin da yake aiki, yana gama parking ya bude motar ya fita ita ma
ta fita, ya rufe motarsa ya dau hanyar entrance din shiga hospital din, a sauri ta
bi bayansa, tsaye ta gansa reception suna gaisawa da nurses dake wajen da fara'a,
Wata nurse tace "Doctor I heard an sake transferring dinka xuwa nan, kuma shiru ba
mu ganka ba" Yace "Sure da yau xan yi resuming, but due to some reasons sai
Wednesday in sha Allah" duk nurses din suka amsa masa da Allah ya kai mu, juyawa
yyi yaga Imaan ta nemi kujera tayi xamanta, wata nurse tace "Dr sister dinka ce?"
Yace "Sure bata da lafiya ne" daga haka ya wuce sama, duk sai da ya shiga office
din doctors dake duty safiyar, Dr Mukhtar na ganinsa ya mike yace "Kaga mara kirki
dama yau xaka yi resuming shine babu sanarwa" Mujaheed ya karasa yana murmushi suka
gaisa yace "Sai Wednesday in sha Allah, na kawo sister na ne bata da lafiya"
Mukhtar yace "Subhanallah Ummi ko Rahma?" Yace "None, cousin dita ce wannan" Dr
Mukhtar ya koma ya xauna yace "Ohk tana ina" Yace "Tana reception" Dr Mukhtar ya
buga waya downstairs ba a dau lkci ba wata nurse ta shigo office dinsa, gaida
Mujaheed tayi da fara'a ya amsa yace "Ya aikin Zainab" tace "Alhmdllh Dr" Dr
Mukhtar yace "Ki taho da patient dake reception" tace "Wanne they are almost 7
patients downstairs" Mujaheed yace "Imaan sunanta" tace "Ohk" daga haka ta fita,
tare suka dawo da Imaan da ta wani yi laushi da kyar take jan kafar, Dr Mukhtar ya
nuna mata kujeran dake kallon wanda Mujaheed ya xauna, ta xauna xata kwantar da
kanta kan table Mujaheed ya mata wani kallo yace "Tashi" kamar xata yi kuka ta dago
kanta, likitan yace "Sannu Imaan, ya kike jin jikinki, like ina ke maki ciwo?" A
hankali tace "Jiya da daddare bayana ya dinga min ciwo har da kai na kuma ina jin
sanyi, ban ma yi bacci ba" likitan yyi murmushi yace "Yau da safe fa" Ta kallesa
murya can kasa tace "Kafafuwana suka fara min ciwo da na tashi, anjima kuma duk
jikina ya fara min ciwo" Ya langwabar da kai yace "Ikon Allah, suna maki haka ne?"
Kai ta gyada masa, yace "Toh kina shan wasu magunguna ne?" Kai ta gyada masa, yace
"Kin san sunan su?" Ta gyada masa kai, yace "Can you write them down for me now?"
Tace "Sure" farar takarda ya ajiye mata da pen, nan ta rubuta masa gaba daya drugs
dinta har da na shafawa ta mika masa takardan ya amsa yana dubawa, bayan few
seconds ya daga kai yana kallon Mujaheed dake kallonsa shi ma, kafin yace komai
Mujaheed yace "Rubuta mata injections taje ayi mata" Likitan yyi yanda Mujaheed
yace, Mujaheed ya amshi takardan yana kallon alluran da ya rubuta mata sannan ya
mika ma Imaan da ta kife kanta da table yace "Karba kije nurses su maki alluran" ta
dago da sauri tace "Yaya allura kuma, ni doctor na baya min allura magani kawai
yake ban" ya jefa mata wani kallo yace "Sai ki jira ya dawo ya ci gaba da baki
maganin, nan kam allura xa a maki, get up my friend" a d'an tsawace ya karasa
maganan, Ta amsa lkci daya hawaye ya cika idonta ta juya ta fita office din, a
hankali Dr Mukhtar yace "Is she a sickled cell patient Mujaheed?" Mujaheed ya
girgixa kai yace "Not at all, She is only carrying the trait, a carrier" da mamaki
Likitan yace "But it's almost mimicking the disease" Mujaheed ya buda hannu yace
"Mu ma haka muka gani" Dr Mukhtar yace "Subhanallah, this is kind of rare, Allah ya
bata lafiya" Mujaheed yace "Ameen" Dr Mukhtar yace "Kasan alluran are strong, ta ci
abinci kuwa?" Mujaheed ya mike da sauri yace "I don't know, bari in tambayeta,
kafin in dawo plss kayi prescribing drugs in addition to hers" daga haka ya fita,
injection room ya shiga bayan nurses din sun sanar masa suna ciki xa a mata
alluran, tsaye take tana hawaye nurse din ma na tsaye rike da alluran sai kallonta
take, tana ganin Mujaheed tace "Yauwa Dr ta ki fa" Mujaheed ya hade rai yace "Are
you a baby? Waye kike son ba wahala, xan maida ki gida da ciwon ki ne idan baki yi
respecting kan ki ba" ta fashe da kuka bata ce komai ba, Yace "Kin ci abinci?"
Cikin rawar murya tace "Na sha shayi kadan amma yunwa nake ji" wani kallo ya dinga
mata, can ya kalli nurse din yace "Nurse let me get her something to take plss"
nurse din tace "Ba damuwa Dr" daga haka ya fita, nurse din ta nuna mata kujera ta
xauna. Rike da malt Mujaheed ya dawo injection room din, ya bude sannan ya mika
mata, Kadan ta sha xata ajiye yace "Wa za ki ajiye ma" ta hadiye na bakinta da kyar
tace "Xan sha idan an gama min" nurse din tace "Aa ki kara kadan" da kyar Imaan ta
kara malt din sannan nurse din tasa ta tashi, ta mike ta fashe da kuka tana kallon
Mujaheed tace "Wllh tsoro nake ji xai min xafi" nurse din tace "Baxai maki ba kuwa"
Mujaheed yace "Xan fa tafi in bar ki a asibitin nan kina bata min lkci" tace "Don
Allah kai ka min plsss" yace "Baxan yi ba, kin tsaya ko inyi tafiyata" da kyar ta
isa kusa da nurse din, ta kallesa ta mika masa hannu jikin rawar murya tace "Don
Allah ka rike min hannu Yaya" bai san lkcn da yyi murmushi ba ya karasa inda suke,
ta kama hannunsa ta runtse ido, nurse din tace "Me yasa baki sa under skirt ba?" Ta
turo baki tace "Ni bana so" nurse din tayi murmushi, ta daga mata abayar jikinta,
rungume Mujaheed tayi ta kwantar da kanta kirjinsa, cikin rawar murya tace "Wayyo
Yaya don Allah kace ta min a hankali, kar ta min da xafi" Mujaheed ya amshi alluran
hannun nurse din yayi mata, xaro ido tayi tana cewa "Yaya ta sa alluran? Don Allah
tayi a hankali, tuni ya amshi dayan alluran yyi mata shi ma, sae da ya cire syringe
din ta sakar masu ihu duk tunaninta lkcn xa ayi alluran, ya turata daga jikinsa, ta
dinga xaro ido, nurse din tayi dariya tace "Toh ba gashi har an gama ba" Imaan ta
zaro ido tace "Da gaske? To ban ji sanda aka cire ba" Mujaheed dai ko kallonta bai
yi ba yyi disposing syringe din ya nufi kofa, nurse din tace "Ki fa danna wajen
sosai idan kun koma gida" Imaan ta gyada mata kai tana goge idonta har sannan tana
mamakin wai har an mata allura don bata ji zafin da take ta jira ba, ta dau sauran
malt dinta ta fita, xaunawa tayi reception ganin bata gansa ba, bayan kusan minti
goma sai gashi ya sakko, yana kallonta ya nufi kofa, da kyar ta mike tace "Yaya na
fara jin jiri" yace "Toh ko in bar ki a nan" da sauri ta girgixa masa kai ta isa
gunsa, saura kadan ta fadi gun fita, ya kalleta sau daya yyi gaba, back seat ta
shiga ta kwanta tana maida numfashi, ya shiga motar ya tada suka bar asibitin, wani
pharmacy ya tsaya xai fita tace "Yaya wllh idona juya min yake" nan ma dai bai
tanka ta ba, drugs dinta da sabbin da Dr Mukhtar yyi prescribing ya siya mata sae
lucozade boost babba biyu, duk ya ajiye bayan motar, har suka isa gida yyi parking
a parking lot din daddy bacci Imaan take, daga cikin motar ya dinga lekan apartment
dinsu gabansa na faduwa, ya juya ya kalleta, sannan ya fito daga motar, ya bude
back seat yace "kee" bude ido tayi da sauri, yace "Sakko" ba musu ta fito daga
motar da kyar, ya dau magungunan da drinks din ya rufe motar, da sauri ya juya
ganin kiris ya rage ta fadi ya kara kallon apartment dinsu, kamo hannunta yyi ta
jingina jikinsa. Har suka isa bangarensu, ya bude kofar ya shiga parlon hade
sallama, Imaan ta kwanta saman kujera ya ajiye drugs din hannunsa da lucozade boost
ya kalleta kafin yace komai daddy ya fito parlon, yace "Har kun dawo kenan?"
Mujaheed yayi kasa da kai yace "Eh mun dawo Abba" dukawa yyi ya dau ledan maganin
ya fiddo gaba daya, ya bude wanda xata sha a lkcn yana kallonta yace "Tashi ki sha
magani" Daddy ya tafi kitchen don dauko table water da cup, Mujaheed daure fuska
kamar tana ganinsa yace "Baxa ki tashi ba?" A hankali ta bude ido ta mike xaune
kamar xata yi kuka, daddy ya iso parlon ya ajiye ruwan da glass cup yace "So how
much is the bill doctor" kallonsa Mujaheed yyi, sai kuma yyi murmushi yace "Bill
kuma Abba" Daddy yace "Eh ba asibiti ku ka je ba, ga kuma drugs ka siyo" ya girgixa
kai yace "A'a Abba, I have settled everything, Allah ya bata lafiya" daddy yace
"Toh madalla, Allah ya yi albarka" Mujaheed
ya debi ruwan ya mika mata tare da drugs din ta amsa, tana runtse ido ta kai baki
sannan ta sha ruwan, mikewa Mujaheed yyi yace "Xan koma daddy Allah ya bata lafiya"
Daddy yace "Ameen thanks Son" daga haka ya fita parlon, daddy na kallonta yace "Toh
tashi ki shiga ciki ki kwanta" ba musu ta mike ta wuce bedroom dinta. Mujaheed na
shiga parlonsu ya kalli mahaifiyarsa dake sakkowa downstairs, kai kana ganin shirin
da tayi kasan fita xata yi, Anty dake parlor tana kokarin sa turaren wuta a burner
ta kalli Mujaheed tace "Har kun dawo kenan, ya jikin nata?" Gabansa ya fadi sosai,
ya hadiye abu da kyar yace "Eh na dawo" Anty tace "Daxu Abban ku ke gaya min ka kai
Imaan asibiti, da naga breakfast dinka baka yi ba" kasa cewa komai Mujaheed yyi,
ya d'an saci kallon Umma da ta tsaya stairs tana kallonsa baki bude, Anty tace "Ji
walakanci ba da Mujaheed nake magana ba" Da kyar yace "Anty ba fa ni na kai ta ba,
Abbanta ne ya kai ta" Shiru Anty tayi ganin yanayinsa, can ta saci kallon inda yake
kallo, d'an tabe baki tayi ta duka ta ci gaba da abinda take, Umma ta juya ta koma
sama, da kyar Mujaheed ya ja kafarsa xuwa dinning, har Anty ta gama abinda take
Mujaheed na xaune bai taba komai a dinning table din ba, tace "Idan baka ci ka kai
min su kitchen a ba almajirai" ya marairaice yace "Anty da baki yi magana a gaban
Hajiya ba" Anty ta maka masa wani kallo tace "tunda uwata ce ita ba" Bai ce komai
ba, bayan wani lkci ya mike ya fita parlon ko a mafarki bai ma son haduwarsa da
Umma, to me ma xai ce mata ta yadda, part din Inna ya nufa, ya sameta xaune kan
tabarma rike da cazbi tana ta xuba gyangyadi, kwanciya yyi kan kujera ya lumshe
ido, inna ta yi gyangyadin ta mai isarta sannan ta bude ido, a tsorace ta koma baya
ganin sa tace "Meye wannan?" Shi dai bai tanka ta ba bai kuma bude ido ba, tace
"Wannan dai ba yi bane ina Lazimi kato ya fado min parlor ba sallama" Ba tare da ya
bude ido ba yace "Kina gyangyadi dai" rai bace tace "Ya xaka ce ina gyangyadi ga
carbi hannuna, ai asararre ne xai yi gyangyadi a wannan lokacin walha fa na gama
ina lazimi ka shigo sadaf sadaf ban sani ba" Mikewa xaune yyi yace "Akwai ruwan
shayi?" Tace "Eh akwai wanda uwarka ta kawo min" ya kalleta bai ce komai ba, tace
"Can din hanaka ruwan shayin suka yi?" Komawa yyi ya kwanta, tace "Sai dai in sa
Aisha ta dafa maka don baxan iya ba, baka ji bayana ba tun safe nake aiki, ko kai
baka ga ko ina fess ba, leka dakina ma kaga yanda yake talli" shi dai bai ce mata
komai ba, tace "Duk na tattara ma yarinyar nan me shigo min daki ta kwanta ta bar
min tsummokaran dankwalayenta idan ta tashi tafiya, suna can baranda na ajiye mata,
sai kaga hasken da dakin yyi wllh, ni dai da xata taimaka ta daina shigar min daki
don Allah, ni tsoron da nake jiye mata idan tayi aure, ko ina fa ta samu barin
kayanta take kamar mahaukaciya, Bukar dai ya haifo abinda ya fi karfinsa" mikewa
Mujaheed ya sake yi ya shiga kitchen, ba a dau lkci ba ya fito rike da cup din
ruwan xafi yace "Ina kayan shayin?" Makulli ta kunce a habar xaninta ta mika masa
tace "Saboda ire iren su Imaan nake adana kayana, ba ruwana" Ya tabe baki ya amshi
makullin ya shiga dakinta, closet dinta ya bude yaga gwangwanin madara manya har
biyu da milo biyu sai kwalin sugar uku, da kwalin lipton girgixa kai yyi ya sauke
madaran da Milo, muryarta yaji a bayansa tace "Da dai ka bari in xuba maka Mujaheed
kada ka min barna" Wani kallo ya mata, ya debi cokalin Madara har uku ya xuba, ta
bude baki cikin tsawa tace "Kai ubanka ne ya siyo min xaka diba haka, Bukar ne dai
mai siyo min kayan shayi, shi Ahmadu sai dai ya jibge min kayan abinci kamar
mayunwaciya, kudin nan fa da wahala ake samun su" shi dai bai tanka ta ba har ya
gama hada shayin sa ya fita, tayi kwafa ta kwashe kayanta ta maida closet din ta
kulle da makullin tana cewa "Ae dai gobe rana ce" Daga haka ta fito parlor. Har
kusan azahar Mujaheed na bangaren Inna, har ya gaji da jin muryarta gashi bai taho
da earpiece balle ya toshe kunnensa ba. Yana kokarin tashi ya je yyi alwala jin an
kira sllh aka bude kofar parlon ya kalli kofar da sauri, Imaan ta shigo parlon rike
da warmer, har ta rame ciwon kwana daya sai manyan idanuwa, Inna ta saki baki tace
"Wacece wannan kuma?" Imaan bata ko kalleta ba ta ajiye warmer din hannunta, inna
ta rike ha6a tace "Ni dai naga abinda ya isheni bai ishi ubangijina ba, yanxu fa
sai ace jikinta ne ya tashi, fisabillah dubi yanda yarinya ta zabge ta koma fiyot
kamar kyanwa Mujaheed, anya iyayenki na son ki kuwa yar nan, haka xasu xuba ido
suyi ta kallonki kina wahala ga magani kasadan na wani malami a Maiduguri ance min
babu ciwon da baya warkarwa, dubu hamsin aka ce xa a basa Bukar ya maida ni ban san
abinda nake ba kamar shi ya haifeni, ta rasulu kawata xata cuce ni ne ake tunani?
ce min fa tayi xata min hanyar samun maganin don can bayan tsauni mutumin yake,
kuma babu kalan iskan da bai warkarwa da ciwace ciwacen da ba na Allah da annabi ba
irin na yarinyar nan, amma iyayenta sun ba tsinannun turawa karfi sun amince masu
dari bisa dari ba saurarana xa su yi ba, dubi don Allah yanda ta fige, lafiya muka
rabu jiya amma ga iskan har ya tashi tunda gashi bata je makaranta ba" Mujaheed
yace "ina kika ce mai maganin yake" Inna ta gyara xama tayi kasa da murya tace
"Wllh a bayan tsauni ta rasulu tace yake, sannan aikinsa yanda kasan yankan wuka,
sha ynxu maganin ynxu, duk xata fitsare ciwon da iskan inji ta rasulu" yyi murmushi
yace "Ikon Allah, boka ne kenan?" Buda baki tayi tace "Kaji salu6a66e ko, ni dai ka
rufa min asiri kar ka ja min kasa Ahmadu ya kafa min sabon babin wa'axi, kai ynxu
fata kake inje wajen boka d'an nan" yace "Atoh, mutumin kirki dai baxai je bayan
tsauni ya xauna ba" tace "Yo ai ni ce gantalalliya ma da nake xancen nan da kai na
mance ashe d'an aiken turawan ne kai ma, Allah wadaran naka ya lalace, ba damuwa ni
da ya xame ma dole xanje samo mata magani kuma kada wani shege ya min maganan
banxa, Allah kuma ya tsine ma turawan nan dai" Imaan dake tsaye bakin kofa har
sannan ta tabe baki tace "Kar ma ki amso ni baxan sha ba, daddy yace min in daina
hada na asibiti da gargajiya" a fusace Inna tace "Kya tsufa a gida ina kallonki
kina kallona don wllh babu namijin da xai auri ciwo da kudinsa ki karar masa da
tattalin arxiki a asibiti, wllh baxan bari a cucesa ba duk sai na xayyane masa
lalurorin ki don ni ba yar cin amana bace, ni yar gaskiya ce, ke ce ciwon kafa,
kece ciwon baya, ke ce ciwon kai, ke ce ciwon mara, kece sanyin k'ashi, kece
xaxxabi, kece ciwon jiki, ga shegen son jiki sannan in rufe masa da cewa duk iska
ne da ba a san kansa ba, ba ruwana wllh" murmushi Mujaheed yyi ya mike ya fita don
yin alwala, Imaan ta mata wani kallo bata son magana saboda daddy ta juya kawai ta
fice mata daga parlonta tana murguda baki.

I am soo grateful for the birthday wishes from families, friends, fans, and love
ones, Allah bar xumunci ya kara mana shekaru masu albarka.
[6/11, 12:34 PM] +234 703 570 1601: 🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟

✍🏻
_By khaleesat Haiydar_
6.....

Hatta islamiyya Imaan bata iya taje ba ranan banda bacci babu abinda take, xuwa
lkcn jikin ya mata sauki sai dai rashin kwari, Daddy dake parlor a study area dinsa
ya kalli Ammi dake parlon ita ma yace "It's almost six madam baxa ki tada Imaan
ba?" Ta kallesa tace "Kafin magrib xan tasheta" yace "Amma jikin ba xafi koh?" Tace
"Ehh ba xafi but she's weak" yace "Allah ya bata lafiya" a hankali Ammi tace
"Ameen" bayan wani lkci ta kallesa tace "Am really disturbed with Imaans health
ailment... She have suffered a lot but always claiming strong, and...." Sai kuma
tayi shiru, a hankali ta ci gaba "I don't want to loose her" Daddy na kallonta yace
"Allah plans best, ke dai ki ci gaba da yi mata addu'a a ko da yaushe wataran sai
labari, Allah xai yaye mata" Ammi tace "In sha Allah" Bayan magrib Ammi na kitchen
taji muryar inna a parlor, fitowa tayi ta gaida ta da ladabi tace "Sannu da xuwa
inna" inna tace "Ina mijin naki?" Ammi tace "Ya fita masallaci" Inna tace "Daxu
Imaan ta xo duk tayi wani fayau fayau da ita, jikin ne ya matsa mata koh?" Ammi
tace "Ehh wllh, amma taji sauki ma yanxu, tana daki xata yi sllh" Inna tayi kasa da
murya tace "Yanxu 'yar nan idan shi mijin nan naki boko ya gama cutarsa ya ratsa sa
ta ko ina ke baxa ki maida hankali ki tashi tsaye kiyi ta kanki da 'yar ki ba?
Fisabillilah meye laifin maganin gargajiya Aisha, komai sai ace sai asibiti ga na
gargajiya kasadan?" Ammi tace "Gaskiya ne inna" Inna tace "Wllh malamin a bayan
tsauni yake" Ammi ta d'an bude ido tana kallonta, tace "Ga aikinsa kamar yankar
wuka, duk xata fitsare jaraban ta dawo kamar mutane, amma ni tsoron magana nake
Bukar da Ahmadu ba kirki ne da su ba sai su karee min rashin mutunci suce boka ne
alhalin ba boka bane kawai Allah ne yyi xamansa a bayan tsauni, ta rasulu ta sha
xuwa can kuma ana kwana daya da rabi a hanya kafin a kai, tunda kika ji haka ai
kinsan akwai kamshin nasara, tafiyar kwana daya har da rabi ai kuwa akwai
nasara....." Shigowar Daddy ya sa tayi shiru, daddy ya gaida ta da ladabi ta amsa
masa sama sama tana kallon Ammi tace "Kina ji 'yar nan bari in koma na bar kofa
bude kada yaran gidan nan su min aika aika ga dambun nama ta can daki, dama
Mujaheed sai xarya yake min tun safe, ko shi ya isa ya kwashe, yanxu dai yaushe
mijin naki xai koma?" Ammi tace "Xuwa gobe in sha Allah" Ammi tace "Toh idan ya
tafi ki taho sashina ki same ni mu karasa maganar a can don sirri ne" daga haka ta
nufi kofa daddy na mata sai anjima ko tanka sa bata yi ba. Bangarensu Mujaheed inna
ta nufa tana cewa "Ita kuma Amina bara inje inji ko lafiya ban ganta yau ba"
Mujaheed ne xaune parlor sai Yusuf, Hajiya na dinning tana jera abinci Rahma na
taya ta, gaba daya Mujaheed bai yarda sun hadu ranan ba sai yanxu da ta riskesa a
parlor ta fito kitchen, Inna na kallon Yusuf tace "Kai ina uwar ka, lafiyarta yau
bata xo gaisheni ba" Yusuf yace "Yanxu da daddaren nan xaki kamo hanyan xuwa nan
inna" Hajiya ta karaso parlon tayi kasa da kai tana daga tsaye tace "An yini lafiya
Inna" Inna tace "Rukayya idan Hadiza ce xa ki gaida ta a tsaye sandandan haka?"
Juyawa Umma tayi ta koma ta ci gaba da abinda take ba tare da ta bata amsa ba, inna
ta kara da cewa "Sannan kiyi min rai ki rufa min asiri ki daina gaisheni kwata
kwata a gidan nan idan kin gan ni, don Allah bana bukata, wnn ae kanki kike
munafurta, kuma Allah ya tsine ma gaisuwar" Wani kallo Mujaheed ke ma inna fuskarsa
daure, inna tayi kwafa tace "Mu xuba dai, xamu ga mai kwashewa, ae kema ga naki
d'an ya isa aure ba don ya tsaya shashanci ba xaki ji ko da dadi ko babu" mikewa
Mujaheed yyi yace "Ke dai ba dai alkhairi ya kawo ki nan ba sai fitina da
complaint, haba don Allah, gaba daya ba a ta6a maki dai dai...." Inna ta bude baki
tace "Ni kake xagi Mujaheed?" A fusace yace "Mu bar sa a hakan" daga haka ya wuce
ta kamar xai tashi sama, Yusuf ya bi sa da wani kallo, tuni Umma ta shige kitchen
ranta fari fat duk da haushinsa da take ji, Yusuf ya mike yace "Yi hakuri muje in
raka ki" Inna ta fara matsar kwalla tace "Isuhu kaga abinda Mujaheed ya min ko? Da
ina kusa da shi babu mai hanasa make ni.... Ina mahaifin ku yake" Yusuf yace "Ke
dai mu je, Abba bai dawo ba" Da kyar Yusuf ya lallabata suka fita parlon tace "Wllh
in har Mujaheed zae ci gaba da xaman gidan nan sai dai ni in tafi" Yusuf ya danne
dariyarsa suna isa part din su Imaan ta bude kofa, daddy dake xaune yana duba
laptop ya mike ganinta tace "Bukar babu abinda Mujaheed ya mance bai gaya min ba
yanxun nan daga nayi ma uwarsa gyara, sai ku xaba ko ni ko shi a gidan nan" daga
haka ta rufe kofar. Yusuf dai tuni yyi gaba, suna isa part dinta ta rushe da kuka
tace "Sai yanxu abun ke min ciwo isuhu, kai kaga wahalar da nayi da Mujaheed kare
baxae ci ba wllh" Yusuf yace "Sai kiyi hakuri, Mujaheed din ki ne fa" a fusace tace
"Mujaheed dinsu dai, bari dai mahaifin ku ya dawo xai gaya min ko shi ke koya masa
ya min rashin arxiki" kiran Isha da ake yasa Yusuf ya bar part din inna, tare Daddy
ya je gun Inna da Imaan bayan isha, Inna ta fito daga daki ta shimfida tabarma ta
xauna tace "Wllh Bukar daga nace ma Rukayya ta daina gaisheni a gidan nan don na
munafurci ne, shi kenan Mujaheed ya hayayyako min yana huci..." Daddy yace "Kiyi
hakuri Inna, ina fita xan je in samesa yanxu" a fusace tace "Oh oh babu xancen
samunsa, kawai ni ba na son ganinsa gidan ne ko kuma ni in tafi ai dama ya isa aure
sai yyi ya koma gidansa baxan xauna tare da shi wataran ya mareni ba, wai ku me
yasa baku san ciwon uwar ku ba, uwarsa fa na yi ma fada shine ya min rashin arxiki
haka, kai ko ga ka xaune sandandan gabana kana bani hakuri, ya fi karfin ka ne
mujaheed din ko kuma uwarsa ta fi naka ne, Ahmadu dai bai ba yaron tarbiyar da ya
ratsa jikinsa ba wllh" Daddy ya mike yace "Xan dawo anjima inna" daga haka ya nufi
kofa tace "Yauwa, ka titsiye sa sai ya gaya maka ko ni sa'arsa ce kafin ya bar
gidan" shi dai bai ce mata komai ba har ya fita, Inna tayi kwafa tace "Xai san ya
ta6a uwar su yau" Imaan dai na kwance kan kujera tana kallonta, Inna tace "Ni na ma
fara tsoronsa tunda abinda ya zama kenan yanxu" Imaan tace "Toh ke me ya kai ki
bangarensu" inna tace "Ya za ki ce min haka 'yar nan, ni da gidan d'a na kuma kice
me ya kai ni?" Imaan dai bata ce komai ba, Inna tayi kwafa tace "Ke kin ga wahalar
da nayi da Mujaheed?" Imaan tayi dariya tace "Ae ke dama kullum sai kice kin yi
wahala da kowa" Inna tace "Kee na Mujaheed k'are baxai ci ba, ni nasan me nake
cewa, ina fa tsaye bakin kofar dakin haihuwa daga safe har dare sannan aka haifesa,
sai kin ga wahalar da ya ba uwar d'an banxan, ai ko aka haifosa lafcece ya kusa
biyun wani jaririn, duk ya cika asibiti da kuka nyaaa ke kina gani kinsan sadauki
aka haifo, gashi jajir da shi fari hulll, gashin kansa kuwa ga bak'i ga cika yanda
kika san d'an balarabe, ke ki bari kawai, nan dai muka koma gida na wanke sa tass,
baki ga uwarsa ba lkcn yar siririya kamar xata karye ba yanxu da ta ci kudin d'a na
iya ci ba ta koma kamar buhun masara, kullum zanyi wanka da sassafe daga gidana in
tafi gidan Ahmadu yi ma fitsararren yaron nan wanka, don babu abinda uwar ta iya
wai tsoron jaririn ma take don bala'i, a haka har yayi wata uku ya koma yanda kika
san bredi wato ya xama wani lukeke, ga kyau tsantsa, ba sai uwar tayi ta cika masa
nono yayi ta tumbudi ba duk k'arni??" Imaan ta fashe da dariya har da kyakyatawa
tace "Shi yayan?" Inna tace "Wllh shi, to ni ko ina xan iya kazanta da k'arni, oh
oh nan na taka mata burki, ga uwar kazama dn har sannan tana tashen kuruciya ni fa
ko abincin gidan bana iya ci da, ana haka har Mujaheed ya kai shekara biyu, ba sai
naga ana neman hallaka yaron ba, ba shi da aiki sai kukan banxa, fitsari a tsaye
kashi a tsaye, ga uban shan yogurt, to da yake ba yanda na raini ubansa ba kenan
bakina a leko na daukesa, kin ji mafarin komawansa waje na kenan, kuma Mujaheed bai
bar gu na ba sai da uban ya biya masa kudin karatun likita a kasashen turai bayan
ya gama sakandari, to ace banyi wahala da d'an banxan yaron ba kuwa, tsakaninsa da
iyayensa fa sai dai bayan kwana biyu yaje ya gaishesu ya dawo, ko k'uda bana yarda
ya ta6a min shi balle shegun kishiyoyina da duk suka mace yanxu, Allah dai ya ji
kansu amma shari'ar mu da su sai a lahira...." Imaan tace "Ni lokacin ma ba a
haifeni ba koh?" Da mamaki Inna tace "Oh oh kaji wata magana kamar na ta6a66u, wa
ke ta ke, ke da aka haifa jiya jiya, a hannuna fa kika fado, ai wannan labarin da
nake baki a lkcn mu duk mun dauka uwar ki juya ce...." Imaan ta mike xaune ta hade
rai tana kallon inna, inna ta gyara xama tace "An auro uwar Mujaheed da shekara uku
fa Ubanki Bukar ya auri bafillatanar uwar ki tana tallan nono a lkcn, a gidan sa fa
tayi wnn karatun da take takama da shi" Imaan ta daure fuska tana kallonta, inna
tace "Bayan an auri Uwar ki Aisha da yan watanni na tursasa Ahmadu ya sake aure
shine fa ya auro Uwarsu isuhu, don a lkcn Rukayya na tashen rashin kunya duk an
hure mata kunne, ga kazanta duk ta bi ta ru6ar min da gidan d'a na, To ita kuma
uwar isuhu lkcn kawar Mamarki ce, kin ji musabbabin rashin shirin Rukayya da
mamanki har yau, Rukayya ta dinga jin haushin Aisha tunda kawarta ta aure mata
miji, Uwar su isuhu na shigowa da wata goma sai gashi ta haifo wannan d'an albarkan
isuhu shi ma dai a gabana aka haifesa ina tsaye, ke ko uwar ki shiru kamar malam ya
ci shirwa, ke in takaice maki har bayan shekaru aru aru sai dai uwar ki ta ci ta
sha tayi kashi duk tayi bake bake a gida babu haihuwa babu dalilinsa, babu yanda
banyi da Bukar ya karo mata ba amma yaron nan ya bijire min to duk ta shanye min
shi ta rarraba min sunansa inda bai kamata ba, ke kinga bafillatani? To wllh kiji
tsoronsa mugwaye ne na kin karawa, ni dai na dage rokon Allah ba dare ba rana don
Allah ya warware abinda tayi ma d'a na, to wllh karshe sai da Ahmadu yayi 'ya ya
shidda sannan uwar ki ta haifo ki, murna gun mahaifinki kuwa ba a cewa komai, duk
lkcn fa ba mu san ba lafiyayya bace ke din, nayi ta xuba
idon xuwan kanninki amma shiru, astagfirullah wa ya sani ma ko sai a lahira idan
ana haihuwar tunda gashi yanxu kin doshi ashirin, kuma tun da kika fara wayo Bukar
ya kulla adashin da ba kwasa da asibiti, shine ake nan har yanxu jiya e yau, ni
yanxu mai kwasan ki ma nake tausayi wllh kada ya kasa rike ki, wannan idan talaka
kika aura ae sai dai mu xo wataran mu dau gawarki muna koke koke, to banda haka
sata xai yi ya kai ki asibiti? abinda Bukar yace min a kalla magungunan ki suna yin
kusan dubu hamsin duk wata, wa xai iya wannan idan ba mai kudi ba irinsu yaran d'an
tata, mu dai Allah ga mu gare ka, ka yaye ma jikata wannan iska da ya sa ta gaba
yake cutan ta, ita kenan gun d'a na" Imaan na hararanta tace "Daga labarin yaya kin
wani dawo bada labarina kamar an tambayeki, har na gaji da jin labarin nan a gidan
nan" inna tace "Toh wa ke ta wani yaya da barin gidan xai yi gaba daya, ai yau sai
ya san ya ta6a uwar masu gida" Da sallama Abba ya shigo parlon, Inna ta daure
fuska, Daddy ma ya shigo parlon Mujaheed na biye da shi a baya, inna na ganin
Mujaheed tace "Ni dai n shiga uku, mutumin nan ya fitar min a parlo don ba ruwana"
Mujaheed ya durkusa d'an nesa da ita ya sunkuyar da kansa yace "Kiyi hakuri inna"
inna tace "Oh oh Allah, ni dai wllh sai naga kamar tsoron yaron nan ku ke Ahmadu,
ni cewa nayi ku taso sa ya bani hakuri? Me xanyi da hakurinsa, idan da amana
Mujaheed zae dinga fifita uwarsa a kai na kuwa? Ni da na ci fitsarinsa na ci
kashinsa ba irin wahalar da ban yi da shi ba, wannan wani irin fitina ne, me yasa
Isuhu baya min haka?" Shi dai Mujaheed bai dago ba, inna tace "Toh ni dai a bar min
parlo na" Daddy yyi murmushi bai dai ce komai ba, Abba yace "Mu dai sai dai mu ce
kiyi hakuri, shi kuma nasan maganinsa" inna ta wani tsuke fuska bata ce komai,
Imaan dai na kwance sai murmushi take, Abba na kallon Mujaheed yace "On a serious
note Mujaheed be careful... you had better respect yourself in this house, and mind
you no matter how she does her things, how she behaves, how annoying she might be,
she is still my motherr, yes she is my mother I can't change her from who she is,
and you have got to respect her to the fullest, you keep that grandma and
grandchild play aside since she doesn't cherish that, she have got all right to
complain of ur mother, let her be entitled to her opinion, today shud be the last
that she will complain of ur attitude toward her Muhammad am I clear" Mujaheed bai
iya ya dago kansa ba yace "in sha Allah Abba" Daddy yace "Maa sha Allah" inna da
sai tabe baki take tace "Oho dai duk a banxa tunda baxa ku iya koransa a gidan ba"
Mujaheed yyi kasa da murya yace "Kiyi hakuri" tace "Tashi ka bani waje, ba dai aure
xaka yi ba wataran, wllh duk sai matar ta rama min abinda uwarka tayi min a duniyar
nan, takanas xan tattara kayana wllh in koma gidanka da xama duk ni xan dinga koya
ma yarinyar, nan Rukayya xata ji ko da dadi ko babu" Mujaheed dai bai ce komai ba,
Abba yace "Leave now" mikewa yyi yana hararanta ta gefen ido ya fice daga parlon,
Imaan ta fara dariya kasa kasa. Ranan juma'ah da daddare Inna na xaune parlonta
Imaan kuma na kwance kan kujera gaba daya ta gaji da labarin da inna ke bata, tana
son tashi ta wuce amma ciwon da kafarta ke mata yasa ta kasa tashi, tun magrib take
wajen bayan ta kawo mata abinci har wajen tara da rabi yanxu, Inna tace "To kin ji
abinda ya raba ni da uwar d'an gwate kenan, kuma fa lkcn kakanku bai san ina xuwa
ba, kai jama'a na xuba farin jini gun masu kudi wllh" Imaan dai bata tanka ta ba,
bude kofar parlon aka yi Mujaheed ya shigo da sallama, Inna tace "Dama shi kadai ne
me shigo min da sallama banda su oh oh" Ta gefen ido Imaan ta kalleta, ya ajiye
ledan hannunsa yace "Gashi" ta jawo ledan tana budewa tace "Lahh kaza ce kamar
yasan ina marmari wllh " Imaan ta mike xaune, inna ta hade rai ta rufe ledan,
mikewa Mujaheed yyi ya dauko plate ya ajiye gabanta, ta mayar gefe tace "Ni dai
wllh kuna takura ni gidan nan kai da Imaan ba haka isuhu da su maimoona ke min ba,
su basu da sa ido" ta hade rai ta bude ledan ta dau cinya daya ta dungura masa a
plate din, dariya yyi ya dauka yace "Ni fa na siya maki kazar ba Abba ba" Inna tace
"Auuu" kara bude ledan tayi ta fiddo tsoka daya ta manna masa kan plate din, Ta
kalli Imaan tace "Naga kina son albasa da kabeji dauko kwanon can da kika ci abinci
in kwashe maki in hada maki da tsoka daya" Imaan tace "Ni nace maki xan ci kaza?"
Inna tace "Toh na sani? Gani nayi kin xabura kin tashi kamar Bukar ya siyo min"
Daga haka ta kai cinya baki tana ci tace "Allah maka albarka Mujaheed duk cikin
jikokina kafi jin k'aina wllh, shi sa ma kana aure zan tattara yanawa yanawa in
koma gidan ka na rantse" ya xaro ido yace "Gidan wa?" Ta kallesa tana washe baki
tace "Gidan ka" yace "A'a wllh ga yar gaban goshin ki nan kice kuma gidana" tace
"Waye yar gaban goshi na?" Yace "Gata nan xaune" inna tace "Oh oh ni gidan ka xan
xauna xai fi min kwanciyar hankali, idan matar ka xata rainani nasan xajka taka
mata burki kai da baka son abinda xai ta6a ni, wannan salubabbiyar kuma ai yunwa ma
kadai ya isa ya koro ni, ni fa ban jin imaan ta iya girki tunda take ko tafasasshen
ruwan xafinta ban taba d'andanawa ba" dariya Mujaheed yyi, Imaan ta wani hade rai
tana kallon inna, Mujaheed yace "Kinga idan tayi aure xaki d'an dana idan kin koma
gidan ta da xama" Inna tace "Ni fa baxan xauna gidan imaan ba gidan ka xan xauna
wllh" yace "Wllh baxa ki xaunar min gida ba sai dai nata" Inna tace "Toh me yayi
xafi haka, wannan satin idan nayi gidan ka wani satin sai inyi a gidan ta duk da
nasan a rame dai xan dawo daga gidan nata amma dole naka naka ne, idan na koma
gidan ka sai in murmure" Mujaheed yyi dariya yace "Inaaa ba wannan xancen gidan
mijinta ko gidan Yusuf xai fi maki kwanciyar hankali amma gida na kam sai dai ki
hangesa daga nisa shi ma kuma a photo, Kinga duk sanda mijin nata ya gaji sai ya
koro ki da ita" Inna tace "Wai tsaya Mujaheed da kake wannan xancen da kudin
asibiti mijin xai ji ko da nawa dawainiyar ka fa san irin cimar da nake ci bana
banxa bane, gwara dai a bar sa ya ji da jinyarta, ni kuma in xauna gidan ka ko
Yusuf koh Maimoon, amma ina ni ina xaman gidan imaan ga yunwa dai kiri kiri tunda
ba girki take ba sai a wani fake da ciwon numfashi kamar yanda uwarta ke cewa" fuu
imaan ta mike xata fita cikin rashin sani plate din da ta ci abinci ta bari wajen
ya xamar da ita sai ga ta rijib a kasa, wani ihu ta fasa da karfi tana cewa wayyo
kafarta, Inna ta xaro ido ta mike da sauri ta bude kofa tace "Ni dai na shiga uku
da jaraba, yi maxa fita da ita Mujaheed, fitar min da ita kar ma ace a parlo na ta
fadi" Mikewa Mujaheed yayi yana mata wani kallo yace "Baxa ki tashi ba" cikin kuka
tace "Wayyo yaya kafana ya rike baxan iya tashi ba" Inna ta gwalo ido tace "Ka ji
ko? Mujaheed ka fitar min da ita kada a sani a bakin duniya" Ganin da gaske ta kasa
tashi Mujaheed ya daga ta, ta zaro ido tana yarfe hannu tana cewa wayyo kafarta,
inna duk ta rude tana ce ma Mujaheed ya fitar da ita, ko fita basu gama yi ba ta
tura su gaba daya, ta kulle kofarta tasa makulli tace "Dama kada a kuskura ace a
parlo na ta fadi wllh don ba ruwana" Mujaheed ya xabga ma imaan harara yace "Baxa
ki tsaya da kyau ba" cikin kuka tace "Wllh ba karya nake ba yaya kafar ya rike min"
kalle kallen wajen ya fara yi, can yayi tsaki ya dauketa kamar yar baby ya nufi
bangarensu da ita, gam ta rikesa tana rera kuka.🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟

✍🏻
_By khaleesat Haiydar_

8.....

Yau Thursday Imaan na dawowa schl bayan tayi wanka ta ci abinci ta fito parlor ta
xauna kusa da Ammi dake xaune, ta langwabar da kai tace "Ammi ina son xan je
supermarket in siya pad da turarurruka" Ammi ta kalleta tace "Duk uban turarrukan
da kika kwaso ranan sun kare kenan Imaan?" Yar dariya tayi tace "A'a ba su kare ba
amma sun kai rabi" Ammi tace "Toh sai ki kira babanki bani da kudin da xan baki ki
karo turare" Imaan ta bude ido tace "Ya min transfer din 30k ranan da xai tafi ai"
Ammi tace "Tohhhh har 30k, lallai kam Allah ya taimaka" dariya Imaan tayi ta mike
ta koma daki, Hijab dinta gogagge har kasa ta fiddo ta saka sannan ta dau karamar
jakarta ta sa atm card ta feshe jikinta da turare ta fito parlor, ta durkusa kusa
da Ammi tace "Toh Ammi ba ni kudin transport don Allah" Ammi tace "Ki duba gaban
mirror a daki" tashi tayi ta shiga ta dauko sannan ta dawo parlon, tace "Yauwa Ammi
ina son xan biya ta gidansu Mariya, tun Tuesday bata xo schl ba bata da lafiya"
Ammi tace "Waye kuma Mariya?" Imaan tace "Lahh wannan da ke xuwa dubani wani lkcn
idan bani da lafiya" Ammi tace "Kice min dai gidansu xa ki je ba supermarket ba"
Imaan tace "A'a fa Ammi, kawai tunawa nayi, Ban ma san ko xan gane gidan ba fa
tunda sau daya muka taba xuwa da Maimoon, idan ban gane ba kawai sai in dawo gida"
Ammi tace "Gwara dai ki gane don ki dubota tunda tana yawan xuwa duba ki" Imaan
tace "Toh Ammi" daga haka tayi ma Ammi sallama ta fita Ammi na tunatar da ita tayi
addu'an fita gida, tana isowa part din su Yusuf taga Umma da wata kawarta xaune a
waje kan fararen kujeru, Imaan ta dauke kai duk da sun hada ido har ta wuce su ta
nufi gate, Hajiya Salaha tana kallon Umma tace "Wace fitsararriya ce wannan kuma"
Wani murmushi Umma tayi tace "Yar wajen Aisha" Hajiya salaha tace "Ikon Allah ita
ce ta girma haka?" Tabe baki Umma tayi, Hajiya Salaha tace "Ita Aishar ta sa kar ta
gaishe ki gidan nan kenan?" Umma tayi yar dariya tace "Ga dahir kin gani, ai fa ko
idona xai makale cikin nata shegiyar baxata gaida ni ba uwar ta hanata" Hajiya
Salaha tace "Tabdi ita wannan yar ficicciyar yar?" Umma tace "Ba shine bayan na
dawo gidan nan naga ita da Mujaheed da bai san ciwon kansa ba bai san ciwon
mahaifiyarsa ba tamkar su yi 6ude, ya maida Aisha kanwar uwarsa bashi da tamkar ta
gidan, ita kuma yar mai ciwo yau mai ciwo gobe tunda sickler ce idan kin ga abinda
yake mata ko kanninsa su Ummi bai masu, in takaice maki duk dai Aisha ta bi ta
shanye min shi yanda ta shanye kanin ubansa, yanda kika san xai mata sujjada"
Hajiya Salaha tace "Ikon Allah" Umma tace "Ae tuni na tashi tsaye, nice can nice
nan, da taimkon Allah da taimakon Magajiya na kwato d'a na da karfi da yaji, yanxu
ko ga maciji basa yi a gidan bangaren ma ya daina xuwa, I can't risk that, uban
waye bai san tsafi Aisha take ba, gashi dai ta hana kanin babansa karo matar da
xata haifo masa 'ya yansa duniya ta rufe masa baki ta hada sa da 'ya sickler kullum
ana hanyar asibiti ana kashe Dan banxan kudade, Allah kenan, kuma in dai ina
numfashi a haka yarinyar nan xata kare yau lafiya gobe babu, in Allah ya yarda sai
yar nan sai ta xame masu jaraba duk sai ta tsiyace su muna nan muna gani, kee duk
wanda xata ra6a ma wllh sai ya tsiyace, haka nan kuma xata yi ta xama ba
mashinshini.... to ubanwa xai iya da ita ta kassara tattalin arxikinsa, ni fa duk
duniya billahil azim bani da makiyiya da ya wuce Aisha, wllh xan iya yin komai don
in toxarta ta da yarta, ni ko kishiyata ban jinta yanda nake jin Aisha, kuma yanda
tasa aka toxarta ni aka min kishiya sai na toxarta ta ita ma ko ba jima ko ba dade,
ina nan dai kan bakana lokaci kawai nake jira" Hajiya Salaha tace "Ae ko kar ki
yarda wllh, ki mata fiye da wanda ta maki ma" Umma tace "Yanxu gobe ma akwai inda
xa ni tare da magajiya da sai ki fito mu je tare, wani take take na fara gani nake
son taka ma abun burki tun wuri" Hajiya Salaha tace "Haba na me kuma?" Umma tace
"Ki ji fa don walakanci yanxu sai su yi ta makala ma Mujaheed ita ya kai ta
asibiti, ga uban kudaden da xai kashe wanda nasan ko ance xa a basa baxai amsa ba
to akan wani dalili? Shi ya dauro mata ciwon? Na samu na rabasa da shegiyar
yarinyar suna kara lika masa ita to gwara in kara xage damtse, ba wani ke nemo masa
kudin ba kuma kudinsa ba na banxa bane, su je can su da suka haifeta su karata da
cutan ta" Hajiya Salaha tace "Gaskiya kam Allah ya kai mu goben idan kin fito ki
kirani" Tunda Imaan ta fito Yusuf dake xaune tare da mai gadi da sabon drivernsu ke
kallonta, yyi murmushi yace "Ina xuwa Imaan din daddy?" Rufe fuska tayi tace
"Shopping mana" Ya wara ido yace "Kaji Hajiya Imaan, in taso mu je ki min shopping
din nima" dariya tayi ta make kafada tace "mu je dai ka biya min" yyi murmushi yace
"abun yar haka ne kenan, to wa xai kai ki?" Ta buda hannu tace "Napep xan shiga" ya
bude ido yace "Salon ki kwaso k'ura ki dawo mana da asthma?" Turo baki tayi yace
"A'a bari driver ya kai ki ya dawo dake kawai" Ta wara ido tace "Da na ji dadi" Ya
kalli sabon drivern dake murmushi yace "Toh driver xa a ajiye mana ita a
supermarket" ya mike yace "In sha Allah, bari in fiddo motar" daga haka ya shiga
cikin compound din, Sai a sannan Imaan ta ga Mujaheed dake xaune kan farin kujera
nesa da su yana danna wayarsa, tana kallonsa ya jefa mata wani harara, ta turo baki
ta dawo kusa da Yusuf tace "Ya Yusuf jiya da na fita inna ta debar maka dambun
koh?" Dariya yyi yace "Aa bata ban ba" ta tabe baki tace "Ba wani nan nasan dama
jira take in tafi sai ta xuba maka ita ma ta ci, ni da ba ma cin dambu nake sosai
ba" yace "Ae ko sai kin ji dadin da dambun yyi, cewa tayi ita ma ta rama abinda
kika mata" bata fuska tayi tace "Ai nasan sae ta baka nice dai baxata ba" Driver na
shiga compound din ya gaida su Hajiya da ladabi yana rike da makullin motar ba ta
amsa gaisuwar ba tace "Ina xaka?" Yayi kasa da kai yace "Hajiya karama xa a ajiye a
supermarket" Umma na masa wani kallo tace "Anya kasan wanda ya dauke ka aiki gidan
nan kuwa?" Shiru yyi yana kallonta, tace "Toh ita warcan da kake gani ubanta daban
a gidan nan, kuma ba shi ya dauke ka aiki ba, mai nan bangaren ne ke biyanka don
haka ka maida hankalin ka, ka wuce ka ban wuri nan da 'yan mintuna xaka ajiye
kawata gida" kansa a kasa ya risina yace "Ayi hakuri Hajiya ban sani bane" tace
"Ehh ka sani yanxu ai" hakuri ya kara bata ya juya ya fita compound din, Yusuf na
kallonsa yace "Ya aka yi?" Yayi kasa da kai yace "Hajiya ce tace xa a ajiye
bakuwarta yanxu" Tsaki Yusuf yyi ya mike Mujaheed ya daga kai yana kallonsa, Yusuf
na kallon Imaan yace "jira in dauko mota in ajiye ki" a hankali tace "Toh nagode"
banda hararansa babu abinda Hajiya take don tasan shi xai sa driver ya fita da
imaan, ta ja tsaki bayan ya fita da motarsa waje, Imaan ta bude front seat ta shiga
ya bar layin, sai bayan sun hau saman titi yace "Amma dai baxa ki shanya ni a mota
idan kin shiga shopping din ba" yar dariya tayi tace "Kasan me ya Yusuf kawai idan
ka kai ni ka wuce ba gida xan dawo ba" Yace "Ina xa ki?" Tace "Xanje duba kawata
bata da lafiya" yace "Wani anguwa?" Ta fada masa tana kallonsa yace "Su Imaan an
fara hankali xa a je duba Mara lafiya" dariya ta fara yi, har suka isa Supermarket
din Yusuf na tsokanarta, Bayan yyi parking yace "Kar ki shanya ni Imaan, in har
kika dde to baxa ki same ni nan ba, ga ATM dina kiyi amfani da shi ai kinsan pin
din" tace "Ya Yusuf ka wuce kawai ba gida fa xan koma ba nace, kuma Daddy ya turo
min kudin shopping din" yace "Anya gidan kawarki kadai xaki je kuwa Imaan" ta turo
baki tana kallonsa, yyi murmushi yace "Toh yi hakuri, napep xaki hau xuwa gidan
kenan?" Ta gyada masa kai yace "In ji kin fito da nose mask din ki?" Tace "Ehh yana
jaka" yace "Toh kar dai ki jima gidan kawar don ni baxan iya ba ammi hakuri ba"
tayi dariya tace "Sae ka bata ni dai idan xata dokeni" dubu daya ya mika mata yace
"Sai ki hau napep din tunda Daddy ya baki kudin shopping" ta amsa tace "Nagode"
daga haka ta daga masa hannu ta nufi entrance din supermarket din. Tun a bakin
entrance din yake kallonta har ta shiga mall din yana biye da ita a baya, gun
turarurruka ta nufa, bayan ta dau wa enda take so har shidda, ta tafi gun pad, ta
duka ta dau pad manya biyu kenan sai gashi yana xuwa toward her, suna hada ido
gabanta yyi mugun faduwa don rass ta ganesa, da sauri ta ajiye pads din hannunta ta
dau dettol dake wajen guda biyu, har ya iso kusa da ita kallonta yake daga cikin
bakin spec dake idonsa, ta dauke kai ta dau wani sabulun ma ta sa a basket din
hannunta xata wuxe, yace "Assalamu alaikum" ba tare da ta kallesa ba ta amsa, yace
"Good evening" Tace "Same" yace "Kin gane ni kuwa?" Kallonsa tayi bata ce komai ba
tayi saurin sunkuyar da kanta ta shiga jera kayan basket din hannunta, yyi murmushi
yana kallonta yace "Dama saboda kina tare da yayanki ne kika kafe ni da ido jiya a
airport, yanxu kuma gashi kin kasa" juyawa tayi xata wuce yace "Wait" juyowa ta
kuma yi, ya duka ya dau pads din da ta ajiye ya sa mata cikin basket din, still
tayi a tsaye, ya wuce shi kuma gun counter, turo baki tayi ta bi sa da kallo ta
gefen ido, bayan wasu sakwanni ta bi bayansa, bata yadda ta tsaya gun da xai biya
nasa kudin wines din da ya siya ba a mall din, duk da mutanen da suka fi yawa a
next counter din can ta tafi ta tsaya, ana xuwa kanta ta bude jaka xata fiddo atm
card dinta taga ya mika masu nasa, juyawa tayi tana kallonsa ya saka masu pin dinsa
a pos din, imaan dai ta kasa cewa komai, suka cire kudinsu suka mayar masa card
dinsa ya nufi kofar fita, ledan kayanta ta amsa bayan an mata packaging, gabanta ya
dinga faduwa har ta fita bata fatan ganinsa a waje, ai ko tsaye ta gansa jikin ride
dinsa, da sauri ta dauke kai ta nufi bakin titi, ya bi bayanta har ya isa Inda take
yace "In ji yau yaya bai ce ki taho shopping da kafa ba" bata ce komai ba kuma bata
kallesa ba, yyi murmushi yace "Toh muje in ajiye ki a gida?" Kamar jira take tace
"Nooo" daga haka ta tsayar da adaidaita fuskarta daure
ta shiga, mai napep na tambayarta inda xata je tace "Mu je gaba" bin su yyi da
kallo yana murmushi, sai bayan da suka yi nisa Imaan ta fada ma mai adaidaitan
anguwar da xa ta. Suna isa ta kasa gane gidan, mai napep din yace "Toh kiyi tambaya
mana" a hankali tace "To wa enda ban sani ba xan tambaya? Kamar fa wancan layin ne"
ya juya yana kallonta yace "Duk fa kin sa na xagaye anguwar nan" Shiru tayi tana
kallon layin da suke tsaye ciki banda haushin karnuka baka jin komai ko ina silent"
mai napep din yace "Duk na kona mai na" yana fadin haka ya sakko don samun wanda
xai ma tambaya duk da ba kowa silent layin sai mota daya dake tahowa, kana ganin
layin kasan na manyan mutane ne sosai, ya kalleta yace "Ya kika ce sunan layin?"
Fada masa tayi, mai motar na isowa inda suke ya tsaya ta dalilin tsaida shi da mai
adai daitan yayi, Ya sauke glass mai adai daitan ya kalleta yace "Ya layin ma?" Ta
hade rai don ta gaji da gaya masa sunan layin ta sakko daga napep din tana sake
nanata masa, shiru tayi tana kallon mai motan kamar yanda shi ma ke kallonta, ya
d'an yi murmushi yace "Ashe anguwar mu xa ki xo dama" bata ce komai ba ta wani
hade rai, yace "Gidansu wa kike nema?" Ta sauke kanta kasa tace "Mariya Ahmad" Yace
"I think wancan gidan ne" ya nuna mata gate din gidan, sae a sannan ta gane wajen,
ta kallesa da kyar tace "Nagode" daga haka ta ciro dubu daya ta mika ma mai adai
daitan ya bata dari biyar ta wuce xuwa gate din. Sosai Mariya taji ddin ganin Imaan
ta rungumeta tace "Imaan a gidanmu, lallai yau za ayi ruwa da kankara, taya kika
gane nan" imaan tayi murmushi tace "i just came to check on ur health daga shopping
mall nake" Mariya tace "wllh naji sauki sosai, gobe in sha Allah xan je schl" Imaan
tace "Toh Allah ya kara lafiya" Mariya zata dauko mata drinks a fridge tace "Aa ni
fa baxan sha ba bana shan abu mai sanyi" Mariya tace "Ehh akwai mara sanyi ai"
murmushi kawai imaan tayi Mariya ta tafi dauko mata mara sanyi, sosai Mariya ke son
Imaan sai dai Imaan bata da saurin sabo kuma bata sakewa da mutane duk da kowa
yasan mahaifin Mariya mai kudi ne sosai kuma sananne, har kawance ake son yi da
ita, yawanci Mariyar ce ke xuwa gidansu Imaan dubata idan ta kwana biyu bata je
schl ba, ita ko Imaan tun da suka je gidansu Mariyan duba yayarta da aka ma aiki
tare da classmates dinsu bata sake komawa gidan ba sai yanxu, bayan boko
islamiyyarsu ma daya kuma Mariya ma na da haxaka both schl da islamiyya tamkar
Imaan din, Duk yanda imaan ta so tafiya Mariya ta ki yarda wai sai mamarta ta dawo
sun gaisa, mahaifiyarta na dawowa kuwa ta kai Imaan har parlonta, Imaan ta duka
kasa ta gaisheta da fara, matar mai kirki ta tarbe ta tana tambayarta mamarta,
Imaan tayi murmushi tace "Tana gida" Aunty tace "Ya karatun fa" imaan tace
"Alhmdllh" Aunty tace "Maa sha Allah sai ku yi ta dagewa, Allah ya bada sa'a kin
ji" bude kofar dakin aka yi duk suka kalli kofar, xaro ido Imaan tayi tana kallonsa
gabanta na faduwa, ya mata kallo daya kafin yace komai Aunty tace "Har ka dawo
Sadeeq" yace "Ehh na dawo, ina yini" tace "Lafiya lau" Mariya tace "ina yini ya
Sadeeq" yace "Lafiya lau" Imaan ta sunkuyar da kanta, yana kallon Mariya yace
"Bakuwa kika yi" Mariya tace "Eh yaya, classmate dita ce Imaan" Yace "Oh I see,
sannu da xuwa bakuwa...." Imaan ta kasa dago kanta tace "Ina yini" yace "Lafiya
lau" Daga haka ya juya ya fita, Imaan na kallon Mariya tace "Xan tafi Mariya"
Turaren Humra mai yawa Aunty ta dibar ma Imaan da smart collections, Mariya ta
amsar mata tana godiya, Imaan tayi mata godiya ta mike suka fita tare da Mariya
Aunty na cewa ta gaida ummanta, Bedroom din Mariya Imaan ta shiga daukan jakarta da
ledan shopping dinta, bayan ta dauka tana facing Mariya tace "Waye wannan da ya
shigo Mariya?" Mariya tace "Wai ya Sadeeq? Yayana ne shi" Imaan ta xaro ido da
sauri tace "Da gaske?" Mariya tace "Kin san sa ne?" Da sauri Imaan ta girgixa kai
tace "A'a tambaya kawai nake" Mariya tace "He is my stepbrother, ga bangarensu can,
kina shigowa compound part dinsu xa ki fara gani" Imaan tace "Ayya, ni dai xan wuce
kar Ammi ta fara kirana" daga haka ta fita Mariya na biye da ita, a parlor suka
tadda Aunty da Sadeeq, da fillanci Mama ke ce ma Sadeeq tunda fita xai yi ya daure
ya ajiye Imaan ko bai kai ta har gida ba, Imaan tayi murmushi tace "Aunty ya bar
shi xan hau napep" Mariya ta fashe da dariya, Aunty tayi murmushi tace "Ashe dai
kina ji, kin bar kawar ki a baya, ba abinda ta iya sai shashanci" Imaan ta kalli
Mariya da ta cinno baki tana murmushi, Sadeeq ya mike yace "Toh bari in ajiye ta"
Imaan ta d'an xaro ido, Babu yanda ta iya, bata kuma yi ma mahaifiyar Mariya musu
ba, suka fita tare da Mariya dake rike da ledan ta bayan Sadeeq ya fita parlorn,
Aunty ta bi su har bakin kofa tana ce mata ta gaida ummanta, cikin motar suka tadda
Sadeeq, Mariya ta bude mata front seat Imaan ta sunkuyar da kanta ta shiga ba don
ta so ba, Mariya tace "Byee Friend sai mun hadu schl gobe, nagode sosai" murmushin
karfin hali Imaan ta mata bata ce komai ba, Mariya na kallon Sadeeq da ya tada mota
tace "Ya Siddiq drive my friend carefully fa" wani kallo yyi mata bai dai ce komai
ba yyi horn, Mariya ta koma ciki tana dariya, har suka hau saman titi babu wanda
yace komai cikinsu, bayan wani lkci yace "Wani anguwar xa ki?" Tana wasa da fingers
din ta tace "Malali" bai ce komai ba, sai da suka kusa bayan kusan minti sha biyar
sannan yace "Wani layin?" Ta gaya masa, daga nan kuma ta dinga nuna masa Inda xai
bi har suka shigo gate din layinsu, dai dai gidan ta nuna masa yayi parking ya juya
yana kallonta, bata yarda ta kallesa ba tana daukan ledanta dake kan kafarta tace
"Nagode" yace "Welcm" daga haka ta bude motar ta fita ta rufe masa motarsa ya bi ta
da kallo, Tsaye taga Mujaheed bakin gate da alamar fita xai yi don makullin motarsa
na hannunsa, ya kalleta ya kalli motar ya sake kallonta da wani expression, ta wani
daure fuska duk da faduwan da gabanta ke yi abinda yayi ma Maimoon ranan don an
ajiye ta a mota ya fado mata a rai, turo baki tayi ganin ya ki matsawa daga gate
din sai kallonta yake, ta raba ta gefen sa har tana bugesa ta shige gidan da sauri,
juyowa yyi yana ci gaba da kallonta, tana ganin haka ta kwasa a guje xuwa part
dinsu, sai da ta isa entrance din parlonsu ta tsaya ta juya tana kallonsa, har
sannan kallonta yake, ta turo baki ta bude kofa ta shige ta kulle.

🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟
✍🏻
_By khaleesat Haiydar_
9.....
Bayan magrib Imaan ta je kai ma inna abinci ta hadu da Yusuf a hanya yana dawowa
daga bangaren innan, gaishesa tayi ya amsa yace "Wai ina tsaraban shopping dina ne
Imaan?" Tace "Body spray da turare na siya fa, ka xo sai in baka daya idan yyi rabi
sai ka maido min, rabi kawai xan baka dama" yayi murmushi yace "Toh an gama, yaushe
xaki fito part din inna?" Tace "Ina kai mata xan dawo" yace "Toh idan na dawo
masallaci xan shigo sai ki fiddo min su in xabi wanda nake so" tace "Tohmm ina
jiranka" daga haka ta wuce, Mujaheed ta gani bakin tap din inna yana alwala, taji
muryar innar tana cewa "Mujaheed ka tabbatar ka datse min pampo wllh cutata kawai
Imaan take ta debe min ruwa ta kai ma uwarta" Imaan ta murguda baki tace "Tunda
Imaan kadai ce a gidan ba" Ta gefen Ido Mujaheed ya kalleta daga durkushen da yake,
ta yi watsi da takalmanta nan bakin kofa ta shiga parlon ta dungure mata warmer din
hannunta, inna ta daga murya tace "Har gwara Ita Mujaheed a kan su Ummi da Maimoon
tunda ita tana tambayata kafin ta diba, su dai diba kawai suke da hakkina" Juyawa
Imaan tayi ta fice mata a parlonta, bata ga Mujaheed din a bakin tap din ba kuma
bai kulle mata ba da kwadon da tace Ga, ta yi wucewarta, tayi nisa sosai daga part
din inna xata dauki hanyar part dinsu ta ga Mujaheed a tsaye, xaro ido tayi ta juya
xata gudu ya cafkota, a tsorace tace "Wayyo me nayi maka" yana mata wani kallo yace
"Uban wa ya ajiye ki a mota daxu? Ta 6ata fuska tace "Ni yaushe kaga an saukeni a
mota, kawai fa...." wani wawan mari ya xabga mata, ta dafe kuncinta a rude ta fara
kwala ma Inna kira, yana mata mugun kallo yace "Baxa ki gaya min waye shi ba" Kuka
kawai take tana bubbuga kafa har sannan hannunta na dafe a kuncinta, strictly yace
"Gobe na sake ganin haka wllh sai na faffasa maki jiki, duk gidan nan wa kika ga
ana ajiyewa a mota, yar mitsitsiya dake xaki shiga mota a sauke ki a gida baki
tsoron kowa ke gaki kwai da ake lallabawa" yana kai wa nan ya turata yyi wucewarsa,
da gudu ta koma sashin inna ta shige parlon ta xube kasa tana rusa kuka, Inna ta
mike tace "Ae fa an kwan biyu ba ayi ba, to uban waye ya ta6a min ke?" Cikin kuka
sosai tace "Yaya ne" Inna tace "Waye haka? waye kuma wani yaya?" Imaan ta ki cewa
komai sai kuka, Inna tayi fici fici da ido tace "Shi Mujaheed din ya sha wiwi ne da
xai kai hannunsa jikin ki?" Imaan na shessheka tace "Mari na yayi ya tura ni" inna
ta gwalo ido tace "Mari? Kika sakar masa fuskar ya mara baki ciccijesa kin gudu ba,
uban me kika mashi? Toh ya tara kuma ya samu, ba a ta6a ki ba ma ya aka kare da
ciwace ciwacen ki balle an mareki a fuska, to mu je ki nuna ma ubansa fuskar" tana
fadin haka ta daga Imaan suka fice parlon, inna na tafe tana kunduma masa duk xagin
da ya xo bakinta, Imaan dai sai ajiyar xuciya ta ke saukewa tana biye da ita, inna
ta tura kofar parlon Abba bayan ta shiga main parlor, Umma ce duke tana sa turaren
wuta a parlon, Inna ta wani hade rai tace "Ke ina mijin ki?" Umma ta dauke kai tana
ci gaba da abinda take tace "Bai dawo masallaci ba, ina wuni" inna ta xauna saman
kujera tace "Ina wuni kuma, dama da ban wuni ba kya gan ni Rukayya" Umma dai bata
ce komai ba, Inna na kallon Imaan dake tsaye tace "Toh ai sai ki xauna mu jira
ubansa koh" Imaan ta xauna kasa tana goge hawayen idonta, Abba ne ya fara shigowa
parlon, yayi still ganin Inna, ta kafesa da ido tana girgixa kafa, yace "Lafiya
kuwa inna?" Mujaheed dake bayan Abba har ya sako kai jin abinda Abba yace xai koma
baya da sauri suka yi ido hudu da inna, da sauri cikin daga murya inna tace "Rikosa
Ahmadu rikosa, abu ya lalace idan ya gudu kar ka bari ya fita, xamansa muke a nan"
Abba ya juya yana kallon Mujaheed da ya wani hade rai ya fasa komawan, Abba ya
karasa cikin parlon ya xauna yana kallon Imaan da ta hade kai da gwiwa sannan ya
kalli Inna, Mujaheed na satan kallon Umma ya shigo ya nemi waje ya xauna a kasa,
duk ya fi jin ummar tasa a kan inna, banda faduwa babu abinda gabansa ya ke, Abba
yace "Me ya faru kuma inna" Inna ta kalli Umma dake tsaye tace "Toh Malama xa ki
iya ba mu waje in yi sirri da d'a na koko mu koma daya parlon" Umma bata ce komai
ba, Inna tace "Atoh ke kadai ce bare, nan d'a na ne da jikokina" Umma ta nufi kofa
fuskar nan nata a murtuke, Mujaheed ya sauke ajiyar xuciyan samun relieve daya wato
fitar Ummarsa, Inna ta mike da kanta ta rufe kofar har da sa makulli ta dawo, Abba
dai sai kallonta yake, ta xauna tayi kicin kicin da fuska tace "Ahmadu daxu Imaan
taje kai min abinci bayan ta ajiye ta fita ba sai wannan yaro Mujaheed ya kamata a
hanya ya daddage ya kwada mata wani mahaukacin mari a fuskarta ba" tana fadin haka
ta dago kan Imaan tana nuna ma Abba fuskar tace "Yanxu fisabilillahi meye wannan
Ahmadu, yau ko dabba Mujaheed ya samu xai maresa haka balle d'an mutum, d'an mutum
din ma 'yar kanin ubansa, to wllh ka dau mataki yanxun nan, Sam baxai yiwu ba,
yarinyar da ake kaffa kaffa da ita saboda lalurorin da Allah ya saukar mata, yanxu
gobe ba abun mamaki bane a ga fuskar ya salu6e wannan irin bugun da yaji, tunda ga
irin yanda Allah yayi ta ko ina ba kwari sae laushi, to wllh ka san abun yi Ahmadu,
shegiya nake idan na yadda" Mujaheed dai ya kasa dago kai sai kallonsa Abba yake,
fuska daure Abba yace "Kai..." Ya dago da kyar, Abba yace "Uban me tayi maka ka kai
hannu fuskarta?" Inna ta gyara xama ta hade girar sama da ta kasa tana kallonsa,
Mujaheed yyi kasa da murya yace "Abba gani nayi an sauketa a mota daxu...." Abba ya
kalli Imaan yace "Mota kuma?" Inna ta buda ido sosai tace "Mota?? Ina kika samo
mota Imaan?" Imaan ta ki cewa komai ta fara hawaye, Abba yace "Baxa ki bude baki ki
ma mutane magana ba, wa ya sauke ki mota Imaan?" Inna tace "A'a dakata Ahmadu kada
a wani fake da an sauketa a mota a shashantar da xancen mari, kai ko daukanta aka
yi a hannu aka sauketa a kofar gida bai kai katon d'an ka ya xabga mata mari har
haka ba, a kan me? To an sauketa a motar, ita yarinya ce ko ba ta isa a ajiyeta a
mota bane? Idan sabon saurayi tayi fa, ko dama haka xata yi ta xama ba saurayi?"
Daga Abba har Mujaheed kallon inna kawai suke, ta ja tsaki tace "Wannan ai abun
farin ciki ne ni dai a gu na, to da a mashin roba roba ku ka so a sauketa idan ba a
mota ba, ko kuma idan tayi ta xama ba saurayi Mujaheed din ne xai aureta? Yau naga
abinda ya isheni bai ishi Allah ba, kawai yaro ka tattakure ka kama yar mutane ka
falle da mari ga ka mugun tantiri ko? sannan na taso takanas na kawo kara gun
ubanka ya wani fake da wa ya sauketa a mota salon maganar marin ya bi iska, To
Allah ya Isar mata" daga haka ta mike tana kallon Imaan tace "Tashi mu je, Allah
dai ya isa" Tashi Imaan tayi ba tare da ta yarda ta kalli Abba ba inna ta ja
hannunta ta nufi kofa tana cewa "Ka ci gaba da daure masa kugu wllh duk randa
xuciya ya kwasheni idan ban sa k'attin anguwar nan sun tare sa a lungu sun nakada
masa shegen duka na biya su ba kace ba uwata ta haifeni ba" da karfi ta rufo masu
kofar bayan sun fita, Abba ya sauke ajiyar xuciya yana kallon Mujaheed, lkci daya
ya hade rai yace "Does that warrant you to slap her Muhammad?" Mujaheed ya kasa
cewa komai, Abba ya masa tsawa yace "Ba da kai nake ba malam?" Da kyar yace "Abba
kayi hakuri, I was only trying to do what I thought was right, duk gidan nan nasan
you don't tolerate yarinya ta shiga motar saurayi" Abba yace "Not to the extent of
slapping her, if she proved to be stubborn why not report her to me? Kasan halin
grandmother din ku, kuma kasan dole sai taje ta gaya mata" Mujaheed yace "Kayi
hakuri" Abba yace "Stupid ba ni xaka ba hakuri ba, ita da ka mara da innan xaka ba
hakuri, kuma kada ka sake wannan wawancin" yace "In sha Allah Abba" Abba yace "Idan
ba hauka ba ma kawai ka daga hannu ka mari mace?" Shiru Mujaheed yyi, Abba yace
"Tashi kaje kayi abinda na ce maka, ita kuma Imaan din xan hadu da ita" mikewa
Mujaheed yyi ya kara ba Abba hakuri sannan ya fita parlon. A hanya Inna ta kalli
Imaan tana washe baki tace "Ke kice saurayi me mota kika yi Imaan?" Imaan ta turo
baki bata ce komai ba, Inna tace "Toh baki ce masa kakarki na nan da rai bane naga
bai shigo ba, ko yaushe yace maki xai shigo gaisheni?" Imaan tace "Ni fa ba saurayi
na bane, driver din gidansu kawata ne naje dubota bata da lafiya shine mamansu tace
ya maido ni gida" sake baki inna tayi a sanyaye tana kallonta tace "Ba lafiya...
Direba kuma?" Imaan bata ce komai ba ta shige balcony dinsu ta bude kofar parlor ta
shiga sai a sannan ta kalli inna dake tsaye baki sake har sannan tace "Sai da safe"
daga haka ta kulle kofar ta sa makulli. Washegari da ya kasance Friday tun da Imaan
ta dawo schl take xaune balcony dinsu tana assignment dinta na maths, Ammi ta kwalo
mata kira for the second time ta ajiye pen din ta amsa, Ammi tace "Idan baxa ki ci
abincin ba ki shigo ki mayar min kitchen nace" Tace "Ammi fa na kusa gamawa saura
biyu" Daga haka ta ci gaba da assignment din, kamar ance ta daga kai taga wata
budurwa da baxata wuce shekaru ashirun da biyu ba tana tahowa, xaro ido tayi ta
ajiye pen din ta mike ta fito tace "Lahh Anty Farida" murmushi kyakkyawar budurwar
tayi tace "Imaan ta mance ni" Rungumeta Imaan tayi tace "Wllh ban mance ki ba Anty
farida, yaya ne yanxu baya bani waya mu gaisa" Farida tace "Toh ke ba sai kice ya
ba ki ba" Imaan ta tabe baki tace "Ai to yanxu babu ruwana da shi shima ba ruwansa
da ni" dariya Farida tayi tace "Toh saboda me" Imaan na murmushi ta amshi ledan
hannunta tace "Ae yanxu yaya ya xama mugu, wajen inna xa ki?" Farida tace "Ehh na
xo layin kusa da wannan ne nace bari in shigo yau dai mu gaisa da inna" Imaan tayi
dariya tace "Amma yaya yasan xa ki xo?" Farida tace "A'a bai sani ba" Imaan tace
"Last time da kika xo gaida inna ai tare ku ka je da shi to me yasa yau ma baxa ki
bari ku je tare ba?" Tayi murmushi tace "Na fa ce maki bai ma san na xo anguwar ba,
Ammi tana ciki?" Imaan tace "Ehh tana ciki" Farida tace "Toh bari mu gaisa" daga
haka ta nufi parlon Imaan na biye da ita, Da fara'a Ammi
ta tarbeta tace "Kin guje mu Anty Farida" banda murmushi babu abinda take tace
"Ammi karatu ne wllh, kinga yanxu ma hutu na xo" Ammi tace "Allah sarki, Allah ya
bada sa'a, ya kuma bada abinda aka je nema" Farida tace "Ameen Ammi" daga haka tayi
mata sallama tace "Xan je mu gaisa da inna" Ammi tace "Toh idan xa ki wuce ki biyo
ta nan mu yi sallama" tace "Toh Ammi" daga haka ta mike imaan na kallon Ammi tace
"Ammi ni dai xan rakata gun inna, idan na dawo xan ci abincin" Ammi tace "Ai shi
kenan" tare suka fita da farida tana rike da ledan ta, farida budurwar Mujaheed ce
babu wanda bai sani ba a gidan, 2 years back kafin Ummarsa ta dawo gidan farida kan
xo ta gaida Ammi da Anty, idan ko xata je gaida inna dama shi xai rakata kuma ko
minti biyar baya yarda su yi a parlorn kafin inna ta fara xance yake janta su fita,
sosai farida ke son Imaan tun lkcn da take xuwa gidan lkcn ma bata kai haka ba,
suna isa bangaren inna imaan ta bude kofar ta shiga da sallama, Maimoon da Rahma na
parlon xaune tare da inna, Farida ta shiga da sallama, inna dake xaune kan tabarma
ta amsa tace "Wacece wannan kuma?" Maimoon tace "Lahh Anty farida sannu da xuwa"
farida tana murmushi tace "Yauwa Maimoon, ykk" durkusawa tayi kasan rug tana kallon
inna tace "Ina yini Inna" Inna tace "Lafiya lau ni dai ban gane ki ba" Maimoon tace
"Inna faridar ya Mujaheed ce fa" Inna tace "Ayyoo farida ce, sannu da xuwa, kai ku
kawo mata ruwa da sauran ayaban nan" Imaan ta mike ta dauko mata ruwa, Inna tace
"Allah sarki, da yake sau uku ya ta6a kawo ki a gurguje shi sa ban gane ki ba, ya
iyayen naki?" Tana murmushi tace "Sun ce a gaida ku inna" Tace "To madallah muna
amsawa, Mujaheed din ne ya kawo ki kenan?" Farida tace "A'a ni kadai na xo" Inna
tace "Atoh ba dole ki xo ke kadai ba, ni ma duk yau ban gansa ba ko gaisuwar
Juma'ah ma bai xo ya min ba daga na kai kararsa kan ya doki yar kanwar nan ta sa,
ko ke haka yayyinki ke cutar ki?" Murmushi kawai farida tayi, Inna tace "Toh
Mujaheed kam cutan nasa kannin yake, kawai daga an sauke yarinya a babban mota ya
daddage ya kwada mata mari ba laifin fari balle na baki wai ashe ma gantalallen
direba ne ya sauketa, to kin san sa da xuciya sai dai kiyi ta hakuri kawai, dama
tun da aka haifesa na ji irin kukan da yake a asibiti nasan akwai bala'i gaba, baki
ji ba duk ya cika asibitin da muryarsa ga shi wani lafcece" Imaan ta fashe da
dariya har da kyakyatawa Maimoon na taya ta, Rahma dai ta6e baki kawai tayi, Farida
kam sai murmushi take kanta a kasa, Inna tace "Wllh ba xancen dariya ba nasan
abinda nake fada, kuma a yunwace aka haifesa, kilan dai uwar bata ci abinci ba taje
haihuwarsa, mu dai haka muka koma gida na wanke sa tass, baki gansa ba jazur da shi
ba yanxu da ya kode ba, ke kinga wahalar da nayi da Mujaheed wllh k'are baxai ci
ba, tun fa yana tsummarsa nake wahala don sai da nayi kwana hamsin ina kai komo a
kansa, to ba abinda uwar ta iya har na koma gidan mijina, daga nan kuma sai dai in
kai masu ziyara duk sati, lkcn baki ga uwarsa ba yar siririya doguwa kamar dai
yanda kika ga wannan yarinyar Imaan" Inna na yamutse fuska tace "gashi uwar tayi ta
cika masa nono yayi ta bulbula tumbudi duk k'arni malam, duk jikokina babu wanda
yyi tumbudi kamar Mujaheed, ni ne ma nace uban ya sa masa Mujaheed" Imaan dai an
samu abinda ake so don har wani kwanciya kasa take don dariya, Maimoon kawarta na
taya ta, Farida dai ta kasa dago kai, Rahma ta wani hade rai tana hararan Inna ko
Kadan bata ga abun dariya a wajen ba, Inna ta gyara xama tace "Lkcn yana da shekara
daya da wata bakwai uwar ta yayesa, shi ma fa da kyar, ai duk cikin 'ya yan Ahmadu
babu wanda ya sha nono irinsa, ya tsotsi uwar ba kadan ba, ko ke baki ga bakinsa
d'an tsiyot kusan a tsuke ba? Ai duk tsotso ne yaja haka, sai yaje gantalinsa ya
dawo ki ji yace Nono, uwar sai ta fiddo ta basa ya sha yyi nak sannan ya mayar, ke
in takaice maki da kyar kanwar uwar ta yayesa don ni dai nace baxan iya wahala ba
cikin kishiyoyi, ae ko sai kinga tashin hankali gunsa, bayan an yayesa kuwa idan
Mujaheed ya daga maki roban yoghurt to bai direwa sai ya kwankwade tass, ga katon
ciki yanda kika san an kifa masa kwarya, Sai uban kukan banxa da shagwaba, ni dai
ba komai yasa na daukesa gaban uwar ba sai ganin xai hallaka, yo hallaka mana katon
yaro haka yayi fitsari a tsaye kashi a tsaye uwar sai dai ta kwashe ta rabu da shi,
duk ta dau son duniya ta daura masa, Shi kuma lkcn kaninsa isuhu na cikin tsumma an
haifesa wani fiyot da shi kamar kyanwa ni na ma xata bakwaini ne" Shiru Inna tayi
tana kallon Imaan, can ta xaro ido tace "Auzubillahi... Ke meye haka kike yi?"
Maimoon ta tsayar da dariyar da take tana kallon Imaan, da sauri ta dagota tana
xaro ido tace "Me ya faru Imaan?" Farida ma ta tashi da sauri ganin yanda
numfashinta ke sama, inna ta mike a rude tace "Kun ga xata ja min jalala ina xaman
xamana ko, to ita nake ba labari da xata dinga dariya haka taje ta mutu a banxa a
buga ni a jarida? kai ku fitar min da ita kar ace a parlo na ne, meye kuma numfashi
na neman daukewa daga ina ba yarinya da ta xo gaisheni labari? Ni dai ba ruwana a
kai ta gun uwarta, ni wllh ba ita nake ba labari ba" Da gudu Maimoon ta mike xata
je dauko mata inhaler suka kusa cin karo da Mujaheed xai shigo parlon, ya turata
yace "Baki da hankali ne" kamar xata yi kuka tace "Ya M.A Asthma din Imaan ne...."
daga haka ta fita, Da sauri ya karasa yana kallon Imaan yace "What happened" inna
da har ta fara matsar kwalla tace "Ka fita da ita Mujaheed idan ma asibiti ne ku
tafi, wllh ba ita nake ba labari ba xata sa ni a bakin duniya ni ban ma san lkcn da
ta shigo parlon ba" Mujaheed ya kalli farida da mamaki, inna tace "Ka rufa min
asiri ka fita da ita Mujaheed, meye kuma dariya haka kamar mahaukaciya, ban san
meye abun dariya a xance na ba" dagata Mujaheed yyi suka fita parlon, can kusa da
wani flower ya xaunar da ita yana kallonta yace "Relax now" da kyar take numfashin
kamar xai dauke, Maimoon ta iso kusa da su ta durkusa ta mika ma Mujaheed inhaler
din, budewa yyi ya kai bakinta da sauri, bayan wani lkcn ta dinga sauke ajiyar
xuciya, maimoon dai sai kallonta take cike da tausayi, Ta jingina da flowern tana
ajiye numfashi a hankali hawaye na sauka idonta cikin tsarkewar murya tace "Yaya
xan sha ruwa" mikewa Maimoon tayi ta tafi dauko mata ruwan da sauri, shi dai
kallonta kawai yake, bayan wani lkci ta daga kai suna hada ido ta kamo hannunsa ta
kwashe da dariya, ya daure fuska yace "kina da lafiya kuwa?" Tana dariya a hankali
tace "Wllh yaya babu abinda inna ta mance bata gaya ma Anty farida ba yau" ya wani
xaro manyan idonsa yace "Kamar me?" Imaan ta kara fashewa da dariya hawaye na sauka
idonta, ya hade rai yace "Baxa ki daina wannan dariyar mahaukatan ba" ta hadiye da
kyar, har wani ciwo kirjinta ke mata cike da karfin hali tace "Labarin ranan da aka
haifeka har sanda aka yaye ka take bata da yanda...." Ganin yanda Mujaheed ya bude
baki da idanuwa yasa ta kara kwashewa da dariya tace "Wllh yaya har da tumbudi da
fitsari da kashi duk ta fada mata" Mujaheed ya kasa rufe baki, Ganin irin dariyar
da take ya sauke boyayyen ajiyar xuciya yace "Toh dariyar ya ishe ki haka" Mikewa
yyi fuska daure xai koma part din Inna ya hangota tana tahowa da gudu, tsayawa yyi
har ta iso yace "Gaskiya Hajiya ki daina abinda kike yi a gidan nan, ke dai magana
magana magana baya kare maki, wanda ya kamata da wanda bai kamata ba haba don
Allah, ni bana son irin wannan abun, ki shekara kina bada labarin kowa amma banda
nawa, ba ruwanki da rayuwata da yanda aka haifeni ke kenan kowa kice xaki ba labari
baki san bako ba, kawai ke dai kiyi ta magana babu naxari haba don Allah" sake baki
tayi tana kallonsa, mikewa Imaan tayi tana hadiye dariyarta sum sum xata bar wajen
inna tace "Ke dai wannan 'ya ta Bukar anyi munafuka wllh, to da kika gaya masa
dukana xai yi ko ko, ina ce yarinyar da xai aura ce, kuma laifi ne don na bata
labarinsa? Me yasa ban samu masu gadi na basu labarin ba? Saboda bai shafesu ba,
komai fa da ku ke gani a rayuwar nan kamawa yake, yarinya ta xo gaisheni sai in
xauna muna kallon kallo da ita??" Imaan ta turo baki tace "Ba wani nan, yaya har ce
mata ta yi da yunwa aka haifo ka duniya kana ta ihu a asibiti, kuma saboda shan
nono bakin ka ya xama d'an karami haka, wai sai kaje yawo ka dawo sai ce ma Umma
nono sai ta baka ka sha, shi ma ya Yusuf sai na gaya masa tace an haifesa fiyot
kamar kyanwa kamar bakwaini" Girgixa kai Mujaheed yyi ya bar wajen a mugun fusace
Imaan ta bi bayansa da gudu tana kyalkyala dariya, Inna ta share kwallar idonta
tace "Ni dai ba don gabana aka haifi muguwar yarinyar nan ba wllh sai ince ba
jininmu bace, don gulmarta ya wuce hankali ya dauka, banda haka yaya xa ta dinga
hada mutane fada a gida haka, shi kenan ni kuma bani da Ikon bada labari, ni daga
yau ma kar ta sake xuwa min na yafe abincin, yarinya dai guda daya sai hada bala'i
a gida, gashi ta hadani da Mujaheed xata tafi ta hada ni da isuhu kuma, ni dai bari
Ahmadu ya dawo a ja mata kunne kar ta sake xuwa min, Bukar dai ya Haifi jaraba"

🌟⭐ *Imaan* ⭐🌟

_By khaleesat Haiydar_

10.....

A fusace Mujaheed ya juya ganin Imaan na bin sa yace "Kee Why are you following
me?" Ta xaro ido tace "Ni ba gidanmu xan tafi ba toh??" kwafa yyi ya ci gaba da
tafiyarsa tana kai wa bangarensu ta shiga tana dariya kasa kasa. Sai kusan karfe
biyar Farida ta fito bangaren inna bayan ta cikata da abun arxiki, su sabulai, omo,
malt har da bottle water duk ta xuba mata a leda, Inna ta rakota har bakin kofa
tana cewa "Toh sai ki gaida iyayenki kinji, Allah maki albarka, nagode nagode, naji
dadin turaren da kika kawo min duk da dai ba mai tsada bane, sai ayi ta hakuri da
Mujaheed dai, Allah kuma ya nuna mana lkcn abun arikin nan" murmushi kawai Farida
take ta wuce tare da Maimoon dake rike da ledan da inna ta bata, sai da suka isa
bangaren su Imaan tace "Bari na shiga in duba imaan" Tare suka shiga parlon da
Maimoon, imaan dake kwance tana kallo ta mike xaune tana murmushi tace "Har xa ki
tafi Anty farida" farida tace "Eh xan wuce ya jikin fa?" Imaan tace "Ae na ji
sauki" Farida tace "Toh Allah ya sauwake xan fito daxu inna tace kun tafi asibiti
da Mujaheed" dariya imaan tayi tace "Ni dai naji sauki" farida tace "Toh ki dinga
yawo da inhaler din ki amma" Imaan tace "Toh nagode" Ammi ta fito daga daki tace
"Har xa ki tafi Farida" farida tace "Ehh Ammi yamma yayi" Ammi tace "Toh mun gode
da ziyara, ki gaida mamarki da mutan gidan kin ji" farida tace "In sha Allah xa su
ji" body spray uku Ammi ta sa mata a leda, ta amsa tana godiya suka fita tare da
Imaan da ta sa hijab xa ta rakasu, xaune suka tadda Mujaheed a part dinsu kusa da
parking space a kan farin kujera idonsa a kan wayar hannunsa, farida na daga inda
take ta gaishesa ya kalleta sannan ya mike yace "Why did you come without telling
me?" ta d'an buda ido tace "Saboda baka son inna ta bani labarin ka? To yau duk
naji komai" Dariya Maimoon tayi har da imaan ya watsa masu wani kallo fuska daure,
Farida tayi murmushi tace "Kawai na xo anguwar ne shine nace bari in karaso in
gaida inna" yace "But da rana ai mun yi waya kuma baki ce kina anguwar ba" tace
"Noo ban taho ba lkcn, nima fa ban san ma xan fito ba, I came on an errand for my
mum" Kamar ance Mujaheed ya daga kai ya ga Ummar sa tsaye a balcony na sama tana
kallonsu keenly, farida ta kalli sama ita ma, ganinta ta sunkuyar da kanta, murya
can kasa yace "I think you have to go in ku gaisa tunda ta gan ki" Tace "Toh" imaan
tace "Toh Anty farida sai wani lkci xan amshi number dinki gun yaya idan xai bani"
ta gefen ido ya harareta, farida tace "Toh shi kenan imaan na gode sosai" Daga haka
ta wuce Maimoon tayi leading din farida xuwa parlon Umma, Umma na xaune wayar ta a
hannu suka shigo, Farida ta durkusa kasa tana kallonta tace "Ina yini Umma?" Murya
can ciki umma tace "Lafiya lau" Farida na wasa da fingers dinta tace "Ya aiki umma"
umma tace "Alhmdllh" shiru farida tayi, Maimoon dai na tsaye sai tabe baki take,
Umma tace "Ya 'yan gidan naku?" Farida tace "Suna lafiya" Umma tace "To yayi" bayan
kusan minti biyu farida ta mike tace "Toh xan koma umma nagode" umma tace "Toh a
gaida gida" daga haka ta fita Maimoon na biye da ita, dakin Anty suka shiga, Anty
taji dadin ganin ta, bayan sun gaisa ta tambayeta mamarsu farida tace "Suna lafiya
Anty" Da ta tashi tafiya Anty ta bata dubu daya kudin transport, Maimoon ta amsar
mata don kin amsa tayi suka fita dakin Anty, Mujaheed na tsaye parking space suka
fito gidan, bayan sun iso inda yake yana kallon farida yace "Gida xa ki koma
yanxu?" Tace "In sha Allah" yace "Ohk mu je in ajiye ki" har ya bude mota wayarsa
ya fara ring, ya duba yaga umma ce ke kiransa, a hankali ya daga ya kai kunne, Umma
tace "Ina jiran ka parlor yanxu" yace "Toh" daga haka ta katse wayarta, ya kalli
Farida a hankali yace "Bari in baki transport kawai dear, akwai aikin da xan yi
yanxu" daga haka ya fiddo dubu biyu ya mika mata, ta girgixa kai tace "A'a ka bar
shi I have transport thanks" ya mika ma Maimoon yace "Ki bata plss" Maimoon ta
amsa, yana kallon faridar yace "Sai mun yi waya dear" daga haka ya wuce ciki.
Maimoon ta tabe baki tace mu je Anty farida. A hankali Mujaheed ya bude kofar
parlon Ummarsa ya shiga da sallama, tsaye ya sameta ta rungume hannu tsakiyar
parlon wandering about, ya karasa yace "Umma gani" kallon da ta dinga masa ya sa ya
durkusa ya sauke kansa kasa, tace "Mujaheed dama ban raba ka da wannan yarinyar
ba?" Ya kalleta da kyar yace "Umma ni ban fa san da xuwanta gidan ba, kuma...." Sai
yayi shiru, Fuska a murtuke tace "Kuma me?" Yace "Umma don Allah me yasa baki so na
da farida?" Tace "Ra'ayi! Wato dai har yanxu kuna tare duk jan kunnen da na maka
kwanaki koh? To wllh ka kiyaye bacin raina Mujaheed, ka kiyaye ni a gidan nan, uban
me xaka yi da diyar talakawa ka ja min bala'i, in xama abun magana gun kawayena,
duk fadin kaduna ka rasa budurwar da xaka nema sai wannan yar, warce iyayenta ke
xaune a ghetto ? Haba Mujaheed are you even alright?" Yace "But Umma I see nothing
wrong with that, arxiki fa na Allah ne, beside suna da rufin...." Umma ta dakatar
da shi rai bace tace "Da ca nayi arxikin na kanin ubanka Sadeeq ne? Ni xaka ma
wa'axi? To wllh in dai kana son kwanciyar hankalin ka a rayuwa ka fita harkar
yarinyar nan, su je can su samu wani kuma, abubuwan alkhairi da ka dinga masu a
baya da ciyar da su da ka dinga yi Allah ya saka maka da alkhairi, ina ji ina gani
baxa ka auri yarinyar nan ba ka xama mai bada charity su talautar min da kai,
yarinya dai dai class dinka in sha Allah xan samo maka tunda naga ba saiti gareka
ba, ba abun mamaki ba wataran ma ka xo min da yar talla kace ita kake so, kai ko
kunyan kanka ma baka ji, dubi yarinyar da Yusuf yake nema xar sha'awa yar masu kudi
ta ma fi ubansa kudi shi ne kai xaka makale ma yar ghetto ko, to wllh ka guji bacin
raina a gidan nan, sannan don munafurci da kinibibi ta shigo sumui sumui ta nufi
gun alakakan kakarka da ba so na take ba a gidan nan salon duk ta bata ni gunta ta
hure mata kunne, don wllh da ban ganta a sama ba dama bata yi niyyar shigowa gaida
ni ba, ta kama ta tafi gun kakarka da kanwar uwarka Aisha tunda ita ta haife ka,
Allah kadai yasan me kakar taka ta k'itsa mata, wato Mujaheed tarayyar ka da
yarinyar ba abu bane mai yiwu wa samm kayi ta kanka tun wuri, daga this very moment
na raba ka da yarinyar na har Abadan abidina, tashi ka ban waje mara tunani kawai"
mikewa yayi bai ce komai ba ya nufi kofa ta bi sa da harara har ya fita ya kulle
mata kofar ta. Xaune yake cikin Lafiyayyen motarsa nesa da gidan, abokinsa dake
gefensa yace "Look ni fa na gaji da xaunar da ni da kayi cikin mota tun daxu
Sadeeq..." Sadeeq ya shafa cute Beards dinsa a hankali yace "You just chill
Fahad... jikina na bani xata fito soon" Tabe baki abokin yyi yace "Have you changed
ur mind about loving and dating only whites?" Sadeeq ya xaro ido yace "Of course
No, wannan fa yar yarinya ce.... I think she is not even up to 18, she is....." Sai
kuma yyi shiru yana murmushi, Fahad da ya saki baki yana kallonsa yace "Sweet
eighteen kenan" Yar dariya Sadeeq yyi a hankali underneath his breathe yace "she is
beautiful" Fahad yace "and why didn't you callect her digit?" Wani kallon gefen ido
yyi masa yace "Sai kace nine kai? How on earth xan amshi numberta bata ce in bata
nawa ba" Bude gate da suka ji aka yi yasa duk suka daga kai da sauri, Mujaheed ne
ya fito, walking majestically ya nufi motarsa da yyi parking a waje. Imaan na xaune
bakin kofar kitchen tana ta yi ma Amminta dake girkin dinner hira, Ammi tace "Daxu
inna ta xo fa wai tana nemanki idan kin dawo schl" Imaan ta xaro ido tace "Ni??? Ba
ruwana baxan je ba, ce ma Abba tayi fa kar in sake xuwa mata ina kwasan
maganganunta ina yadawa a gidan nan, ita gaskiya xata gudu ta bar gidan idan naje
mata" Ammi tayi murmushi tace "Toh tace kwana biyu bata gan ki ba ko jikin ne"
Imaan tayi dariya tace "Xa ma ta fadi gaskiya ne, ba inda xanje ta sake cewa na
mata laifi gwara dai Maimoon ta ci gaba da xuwa tana kai mata abinci" Ammi tace
"Toh ke xa ki kai yau, kina ajiye mata ki gaisheta sai ki fito ba shi kenan ba"
imaan ta bata fuska kamar xata yi kuka tace "Ni dai Ammi nayi alkawarin baxan sake
xuwa part dinta ba fa" Ammi dai bata ce mata komai ba. Bayan magrib Imaan na Idar
da sllh Ammi ta tilastata kai ma inna abinci sabanin Maimoon da ta dinga xuwa tana
kai mata kusan kwana uku kenan, Imaan ta dau abinci ta fita fuska daure kamar mai
shirin yin kuka, tana isa bangaren inna ta tura kofar ta shiga, Yusuf ne parlon
suna hira, Inna na ganinta ta washe baki tace "A'a takwara ce" imaan ta ajiye
abincin ba tare da ta kalleta ba tace "Ina yini?" Inna tace "Lafiya lau, ni kwana
biyu ban ganki ba nace to ko jikin ne? Duk hankalina ya tashi na tafi sashin ku
daxu Aisha tace ai kin ma tafi boko" Imaan ta tabe baki tace "Lafiya ta qlau kawai
dai umarnin Abba nake bi" inna tace "Umarni kuma? Umarnin me ya maki?" Imaan ta
buda ido tace "Ba ce masa kika yi kar na sake xuwa bangaren ki ba baki son ganina,
shine ai na daina xuwa" Inna ta kalli Yusuf tace "Oh oh Allah, isuhu kaji wata
magana irin na Ahmadu ko, dama an san babba da hadin fada, ni yaushe muka yi haka
da shi, daga nace yayi mata fada ta daina haka gidan aure xata kuma ba halin xaman
gidan miji kenan ba, shine xai ce nace kar ta sake xuwa min? To ina da masu xuwa ne
idan ba ita ba ko shi xuwa yake yi ya xauna min, ni dai a dinga jin tsoron Allah
gaskiya" Yusuf yyi murmushi yace "Toh ba ga ta nan dai ta xo ba" Inna na kallon
imaan tace "Ni ban yi haka da shi ba gaskiya, ga soyayyen naman ki can na ajiye
maki tun jiya a daki, naki ne da na Mujaheed shima kwana biyu ban gansa ba sai ki
diba naki ki bar masa nasa" Imaan ta turo baki ta wuce cikin dakin, daukan bowl din
tayi ta bude taga soyayyen naman cow din sai kamshi yake ta xubawa, ta xauna gefen
gado ta kirga gaba daya taga yanka sha takwas ne, murmushi tayi ta fita don dauko
leda a kitchen, Inna tace "Kin diba naki" tace "Leda xan dauko a kitchen" daga haka
ta shiga kitchen din ta dau leda biyu ta boye
daya, tana rike da daya ta fito ta koma cikin dakin, equal ta raba naman ta debi
nata, cikin sauran da ya rage ta debe guda hudu ta xuba a daya ledan ta ajiye
sauran, ta window ta jefar da guda hudun da ta dauka sannan ta fito parlor, inna na
kallon hannunta tace "In ji baki kwashe naman ba nace naki da na Mujaheed ne, don
gaskiya nasan halin ki" ta xaro ido tana nuna mata ledan tace "Duba ma ki gani,
guda sha takwas ne na kirga na dau tara na bar masa tara" Inna tace "Yauwa kinyi
dubara" Yusuf da ke ta kallonta yana murmushi yace "Are you sure imaan" da mamaki
ta kallesa tace "Me that don't even like eating meat sef" murmushi ya kuma yi yace
"Eh naga alama" Inna ta tabe baki bata dai ce masu komai ba, Ummi ce ta shigo
parlon rike da abinci ta kawo ma inna, inna ta bude warmer din ta girgixa kai tace
"Mayar masu, ce masu aka yi xaman abinci nake a gidan nan shekaranjiya a ban
shinkafa da miya jiya a ban dafaduka yau kuma a ban koren shinkafa, maida baxan ci
ba" Yusuf yace "Toh ae ba iri daya bane wannan fried rice ne fa" Inna tace "Toh
Isuhu ni kenan a cin shinkafa xan kare, wlh na gaji da kaddararren shinkafar nan,
Ahmadun baya ajiye abinci ne" tana fadin haka ta jawo warmer din da Imaan ta kawo
ta bude, shinkafa ce da miya sai salad a gefe shi ma, Yusuf ya fara dariya, Imaan
ma ta kyalkyale da dariya, inna tace "Toh Allah ya mana tsari" tana fadin haka ta
kalli Ummi tace "Ke Mujaheed ya dawo ne ko yana can yana siyar da abinda ya kasa a
titi?" Ummi tace "Ya dawo, tare muke tahowa kuma ya tsaya yana waya " Bata rufe
baki ba sai ga shi ya shigo da sallama, farar 3 quatre ne jikinsa da bakar riga,
Inna ta tura kulolin gabanta tace "Mujaheed don Allah irin wannan tuwon da ka taba
siyo min nake so ni dai" ya karasa parlon ya ajiye ledan fruits din hannunsa yace
"Ae sun tashi masu siyarwan" tace "Ni dai don Allah ka rufa min asiri ka tafi, su
tashi su je ina?? Bayan ga maza masu fita titi cin abinci ta dalilin rashin iya
girkin matansu" Yace "Ki tambayi Yusuf da karfe shidda suke tashi" yana fadin haka
ya bude warmer din abincin kusa da ita yace "Wannan kuma fa" tace "Haba Mujaheed
shinkafa dai shinkafa dai inje basir ya cafke ni, wa nake da shi da xai nema min
magani, wllh baxan ci shinkafa jiya in ci yau ba, wannan ai mugunta ce ma" Mujaheed
ya tabe baki yace "Toh ai sai ki sha tea ki kwanta" Ta maka masa wani kallo tace
"Kai xaka gaya min abinda xan yi ko raini?" Yusuf ya mike yace "Toh bari a samo
maki tuwon idan basu tashi ba" daga haka ya fita, Inna tace "Toh Allah yayi maka
albarka, Ya baka abinda kake nema duniya da lahira, to dama? idan ba kai ba waye,
Allah dai ya ma albarka" Mujaheed ya kalleta ta gefen ido xai fita inna tace "Ga
namar ka can a daki, baxan biye ta halin ka ba ni dai" Ya juyo yace "Nama na me?"
mikewa Imaan tayi ta nufi kofa ta fita sum sum, inna ta bi ta da kallo baki bude
tace "Toh kuwa idan ba wani ikon Allah ba ta kwashe rabon naka, Ummi tafi daki ki
dauko min roban naman, ai ni naga abinda ya isheni bai ishi ubangijina ba" Ummi ta
tafi dakin ta dauko bowl din naman inna ta amsa ta bude tana kallo ta saki salati
ta ajiye ta rike ha6a, Mujaheed ya dau roban yana kallon sauran naman, inna ta
sauke ajiyar xuciya tace "Ta kwashe wllh, gaskiya dai wannan 'ya ta Bukar bata da
hali, muguwa ce ta innanaha, ni wllh da xaka burgeni Mujaheed ka bi ta har gaban
uwarta ka kwato min namana gaba daya na fasa badawa" Ya ajiye bowl din hannunsa bai
dai ce komai ba, Inna tace "Idan kuma baxa ka ba ni sai in tashi inje, ya xata
kwashe min nama gaba daya bayan na mata bayani, naman fa yyi yanka kusan ashirin
shine ta bar maka hudu, ni dai rabona da a sani magana haka tun kwana uku da suka
wuce, to bata xuwa.... yau kuma ban san uban me ya kawota ba" Yace "Sai da safe"
bai jira cewar inna ba ya fita parlorn, motsin da yaji a bangarensu Imaan yasa ya
tsaya duk da bai yi niyyar tsayawa ba, durkushe ya ganta a balcony dinsu tana
tattara shoes dake wajen xata shigar da su ciki, yana kara taku daya xata gansa
saboda hasken dake wajen hakan ya sa ya tsaya, mikewa tayi ganin alamar xata fito
ya koma baya da sauri ya tsaya jikin flowers, socks dinta da ta shanya take
kwashewa, da sauri ya nufeta tana ganinsa ta saki takalman hannunta da socks ta
gudu xuwa balcony dinsu, Amma tuni ya kamata ta xaro ido kamar xata yi kuka tace
"Yaya me nayi kuma?" Ya daure fuska yace "Ina naman da kika kwashe" tace "Yaya nama
kuma, ni fa guda shidda na dauka" yace "Dauko shiddan" tace "Toh ai rabona ne fa"
ya mata wani kallo yace "Na fara wasa da ke gidan nan koh?" Kamar xata yi kuka tace
"Toh tasan ba bani xata yi ba kuma ba ni ta ajiye ma ba meye na sa min rai, baxan
sake xuwa parlonta ba ma" yace "Eh dauko naman" durkusawa tayi ta dau kayan da ta
saki, tace "Mu je parlor in baka" yace "Baxan shiga ba ki dauko min" tace "Toh ni
dai idan baka shiga ba baxan baka ba" ya wani daure fuska yace "Ke wai yaushe na
xama mate din ki a gidan nan?" Tace "Toh xaka tsammin plss" ya fixgota yana mata
wani mugun kallo har tana jiyo numfashinsa, Bata sake cewa komai ba yace "Tafi ki
dauko min" a hankali tace "Toh" sannan ta nufi balcony din ya bi bayanta ya tsaya
yana kallonta, ta bude kofar ta shiga sannan ta juyo tana kallonsa, wani murmushi
tayi ta wara masa ido tace "Good night yaya" daga haka tayi banging kofar da sauri
ta sa makulli, sosa kansa yyi bayan kusan second goma ya juya ya fita balcony din
yana murmushi. Imaan ta fito daki jin Ammi na kiranta, da mamaki tace "Ammi ina xa
ki kuma?" Ammi na rike da flat shoe dinta tace "Kin manta yau xa a kawo lefen
Seeyama" Imaan tace "Ohh na manta, to ni Ammi baxan je in gani ba" Ammi tace "Toh
girkin da na daura fa?" Shiru tayi kamar xata yi kuka, Ammi tace "Toh idan
shinkafar ya nuna ki kwashe sai ki taho" Imaan ta washe baki tace "Toh" Ammi na
fita parlon ta tafi kitchen da sauri tayi ta tsaye tana jiran dahuwar shinkafar,
daga karshe da sauran ruwa a ciki ta kwashe a warmer ta fita da sauri, Hijab ta sa
har kasa ta bar gidan xuwa part dinsu Maimoon, har an kawo akwatunan ta tarar masu
kawo wa ma har sun tafi, Anty ce da kawayen Umma uku suka shiga buda tsadaddun
akwatuna set shidda da aka kawo, Ammi dai na xaune parlon, parlon cike yake da
mutane duk yawanci yan uwan Umma da Kawayenta, Imaan ta nufi inda Maimoon ke xaune
duk suna jiran a bude akwatuna su fara ganin kaya ta durkusa, Umma dai fuskar nan
babu yabo babu fallasa tana tsaye, Kanwar Umma Hajiya Mariya ce tace "Imaan fa an
xama yan mata" Imaan tayi murmushi ta sunkuyar da kanta tace "Ina yini Mama" Umma
ta wani daure fuska tana kallon kanwartata, Hajiya Mariya tace "Lafiya lau Imaan ya
schl ko kun gama secondary din?" Imaan ta girgixa kai tace "A'a Mama muna ss1"
Hajiya Mariya tace "Maa sha Allah, Allah ya baku sa'a" Umma na kallon hajiya mariya
tace "Ban ga amfanin ki xaune nan ba Mariya da ki tashi ki bar nan kawai" Murmushi
kawai Hajiya Mariya tayi ta mike nan suka dinga fiddo kayan akwatunan, Ammi dai
bata tashi ba, Maimoon ta ja Imaan kusa da boxes din wai su ga kaya, Imaan na daga
kaya taga wani arnen kallon da Umma ke mata, sunkuyar da kai tayi bata sake
yunkurin matsawa kusa da boxes din ba, kaya maa sha Allah sunyi kyau sannan masu
tsada, Hajiya Laraba tace "Kai maa sha Allah lallai Seeyama tayi goshi, Allah ya
sanya alkhairi ya sa gidan xamana, Allah kuma ya nuna mana na sauran yan matan
gidan haka" Umma tace "Toh Ameen amma kuma lafiyayyun yan matan gidan dai koh?"
Kawayenta suka kwashe da dariya Anty ta daga kai ta kalli Umma, Wata kawar Umma
tace "Gaskiya kam irin wannan kaya ai sai mai lafiya, Mara lafiya kam yyi fatan
samun mijin kafin ya sa ran kaya haka" Umma tayi wani dariya har da shewa, Hajiya
Mariya da mood dinta ya canxa ta dinga kallon yayartata, ita dai Ammi kallon kayan
da suke ta fiddowa kawai take, Umma ta kalli kawarta Hajiya Shafa tace "Ya haka
hajjaju naga baki tashi duba kaya ba ko kema kina cikin sahun yan yi ma 'ya ta
bakin ciki ne naga dai duk kin aurar da naki yaran" dariya sosai Hajiya Shafa tayi
tace "Masu bakin ciki sun san kansu, ni ko in rasa Wanda xan ma bakin ciki rayuwar
nan sai ke, jira nake duk a bar wajen In duba kayan a tsanake" Umma ta bata hannu
suka tafa tana dariya, maganganu marasu dadi Umma da kawayenta suka dinga saki a
parlorn, Anty da abun ya isheta ganin sai xancen mara lafiya suke
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

tace "Ai kuma Hajiya abun fa ba daga nan yake ba, sai a ga kuma mara lafiya ya
samu abun arxiki a rayuwa fiye da mai lafiya, so nawa kuma aka yi hakan" wani
dariya Umma tayi tace "Toh ayi mu ga ko basilin xai toya kosai" Anty tace "Kwarai
kuwa xai toya sai dai a dau lkci kawai" Hajiya Laraba tace "Toh ni duk wannan abun
fa har yanxu ban ga amarya ba" Umma tace "Ohh tana can makaranta, gobe xata taho
sun ma kusa gama jarabawa" Hajiya Laraba tace "Ayya tana Zarian kenan" Umma tace
"In sha Allah" Mikewa Ammi tayi tace "Toh Hajiya Allah ya sanya alkhairi xan je in
ci gaba da abinda nake yi" a dakile Hajiya tace "Oh toh madallah, ban ma san an
gayyato ki ba da ina da niyyar tura Ummi ta kira ki sai ga ki" Ammi bata tanka ta
ba tana kallon Anty tace "Anty Amina, bari inje in ci gaba da girki, kaya sun yi
kyau maa sha Allah, Allah ya sanya alkhairi yasa ayi da mu" Anty tace "Toh ameen
Ammi sai na shigo" Mikewa Imaan tayi xata bi Ammi Anty tace "Au har xa ki tafi don
gulma" murmushi tayi ta shige gaba, daga Umma har kawayenta suka bi su da kallo ana
tabe baki. Sai bayan da suka kusa part dinsu Imaan tace "Ammi yaushe ne bikin?"
Ammi tace "Me ya hanaki tambayarsu a can" Imaan bata ce komai ba har suka shiga
gidan. Da magrib Imaan taje kai ma Inna abinci taga akwatunan jere a parlonta, Inna
tace "Kinga akwatunan yar uwar ki kuwa?" Imaan ta girgixa kai tace "A'a ban ga
kayan ciki ba" Inna ta mike ta shiga sakko da su tace "Taho ki fiddo su ki gani, ni
sai naga kamar ma mijin rufin asiri kawai garesa, ji fa na yarinyar nan Khadijah
guda takwas aka kawo har da gwal biyu a ciki wannan kuwa ko axurfa ban gani ba sai
dankunnayen kauye" imaan ta rufe baki xata yi dariya inna ta tabe baki ta xauna
tace "Toh naga duk sai saurayin ya wani xo ya cika mana kofar gida da katuwar mota,
ga kaya nan kuma duk abun kunya, anya ba gudunmawar da dangi suka dinga basa ya
xuxxuba mata a akwatunan ba kuwa, ji fa har da man mai gurguwa na gani a ciki, man
da aka yi yayi tun lkcn haihuwar Mujaheed" Imaan ta fashe da dariya har da
kyakyatawa, Inna tace "Ni daga ganin dankunnayen da sarakuna dama jikina yyi sanyi,
atamfofin kuwa har da na roba guda biyu idan dai ba idona ne yyi min karya ba, ga
wani uban lace duk nauyin tsiya, sannan jallabiyoyin irin Wanda na taba siya a
makka tun ina goyan Ahmadu da naje, bari in fiddo ki gani, ni da dai a kira min
yaron inji muguwar da ta hada ma jikata wannan kayan" tana kokarin fiddo jallabiyar
Yusuf ya shigo parlon tare da Mujaheed, Inna ta juya tace "Kun ga kayan yar uwar ku
kuwa?" Yusuf yace "Na gani sai dai ko M.A" inna ta mike tace "Toh kai isuhu baka ga
irin kayan ba, dama katuwar motar karya yake kawo mana kofar gida ya paka?" Yusuf
ya bude baki yana kallonta, ta tabe baki ta xauna ta rungume hannu tace "Ni dai ba
ruwana, sai kace xa a basa baxawara" Yusuf yace "Haba inna ina laifinsa duk fa
kayan masu tsada ne wllh" a fusace Inna tace "Amma kai dai mugu ne wannan yaro, kai
ka yarda ka hada ma figalalliyar budurwar nan ta ka wannan kayan, kai kana ganin
idan mun kai masu xa su amsa, mutanen da suka jik'a cikin kudi gidansu gari guda
motoci ta ko ina, Kai in takaice maka Idan basu koro mu da kayan ba kace ba ni ba"
Imaan ta fashe da wani dariya har da kwanciya inna ta fiddo jalabiyyar ta watsa
masu kamar xata yi kuka tace "Ku ji fa kayan da na taba siya lkcn ina goyan ubanku
a makka" Ganin dariyar da Imaan take Mujaheed ya daure fuska yana kallonta yace "Ke
waye kike ma dariya a nan wai" a fusace Inna tace "A'a bar ta tayi wannan ae abun
dariya ne, har da fa mai gurguwa da basilin irin na tale tale, bar min ita tayi
dariyarta" Tsaki Mujaheed yyi yace "Toh Allah ya sa ta samu hakan ita" A rikice
inna ta mike tace "Auxubillahi... Bakin ka ya tsari danyen kashi Mujaheed, kai ka
so a kawo ma Imaan irin wannan tarkacen, ai da na shiga uku wllh, bari kaji duk mai
auren Imaan sai ya shirya a duniyar nan, idan na amshi akwatunan ta babu gwal na
dan kunne, sarka da awarwaro da zobe kace ba ni bace, sannan atamfa idan na amshi
na kasa da dubu ashirin kace ba nice Hajiya patu ba, kai in takaice maka idan ba
akwatuna sha biyu ba dama kada shegen da ya xo yace xai aureta don xai ga barbadin
bala'i" Mujaheed da ke gyada kai ya tabe baki yace "Ae sai ku yi ta xama, kinga sai
ki jik'a ta ki shanye ko kiyi kwadonta ki cinye" daga haka ya fice a parlon, Yusuf
ya girgixa kai ya fita shi ma, inna tace "Gantalallu kawai yan hassada wanda basa
son ci gaba na, a haka xa ku yi ta gantali a titi."

Alhamdulillah, Thanks to all those that patronize the book *Imaan* Allah bar ku da
iyayen ku, My book Imaan is for sale coz I am done with free pages tun friday, ni
nasan it will go round as usual, I can't prevent that, but if you should come
across it it's not for free, i repeat it's not for free, na siyarwa ne, wllh I am
too grown up to say Allah ya isa, but have the fear of Allah SWT in u, don't forget
it's my property, hakkina ne, wahalata ce, pay before reading, pay before reading,
or you just over look it and smile, have a very good conscience plss, and a good
conscience won't read happily without paying, if you want any favor pertaining to d
book contact me and let me know, the book is 300 via..... Fcmb 3276052019
Hauwa Bello Jiddah

07087865788 and then u contact me through this digit to be added in the payment
groups. Thanks once more for patronizing.

For those saying xa su same shi a banxa yana yawo to gashi... amma fa ba a banxa
yake ba wllh, there is power in the tongue, Karamin hakkin da ka raina..... 😃😃

11. 🌟⭐ *imaan* ⭐🌟

Kasancewar ranan Alhamis ne Imaan na dawowa schl bayan ta yi wanka ta fito ta d'an
cito abinci kadan ta koma bedroom ta saka kayanta ta sake fitowa parlor, Ammi dai
sai kallonta take don tun daga ganin d'an abincin da ta ci ta san da matsala, Ammi
tace "What's wrong with you?" A hankali tace "Ammi cikina xai fara min ciwo ne"
Ammi tace "Toh Allah ya sauwake abincin ya ishe ki?" Kai ta gyada mata ta xauna
kusa da ita tace "Ammi na dade fa ban je gidan gwaggwo in gaisheta ba" Ammi tace
"Jiya ma ta tambaye ki da muka yi waya, ran Saturday idan kin dawo islamiyya sha
biyu sai ki tafi, before four ki taho gida saboda islamiyyan yamma" Imaan tace "Toh
Ammi me yasa gobe baxan je ba" Ammi tace "A'a xan je xa mu duba ma Halima kaya an
kawo daga dubai, idan kin dawo schl ma baxa ki sameni" Imaan tace "Toh, Ammi ankon
mu fa?" Ammi tace "Idan kin je sai ki tambayeta" Imaan tace "Ammi bikin na Anty
Seeyama xa a fara yi ko Anty Halima?" Ammi tace "Na Seeyama saura two weeks, Halima
kuma saura sati hudu" Imaan tace "Toh Ammi na Seeyama baxa a mana anko ba?" Wani
kallo Ammi tayi mata tace "Kin ishe ni kuma haka" Shiru Imaan tayi, can ta mike
tace "Ammi xan je wajen inna" Ammi tace "Toh sai ki dauko magana idan kika tashi
dawowa" dariya kawai tayi ta sa takalminta ta fita parlon ta rufe kofar. Inna na
share waje Imaan ta sameta, Inna ta mike tace "Baki ji bayana ba Imaan tun daxu ban
xauna ba wllh, aiki dai aiki dai, to kuwa idan mutum bai yi aiki ba ai sai kazanta
ta ra6e sa, to ni ko yaushe xan yarda hakan ta faru???" Imaan tace "Toh me kike
sharewa a nan din, naga ba datti" inna ta xaro ido tace "Toh k'uran dake yashe a
kasa kuma uwaki ce ba datti ba?" Imaan ta yi dariya tace "Toh ai sai kiyi ta
sharewa" daga haka ta shiga ta bar ta a wajen, bayan minti goma inna ta shigo
parlon ganin yanda Imaan take yatsine yatsine ta hade rai tace "Me kuma ya faru?" A
hankali tace "Wllh cikina ne xai fara min ciwo" Inna tace "Toh tashi ki tafi gidan
ku ba ruwana da wahalan ki, ko ba jini bane" Imaan tace "Toh ai bai xo ba kawai dai
yana min ciwo ne" inna tace "Toh kiyi maxa ki tafi uwar ki ta kai ki asibiti, haka
wancan karan kika cuce ni kika daga min hankali, ni dai da xaki dinga rufa min
asiri duk kika ji baki da lafiya ki daina taho min nan sai kin ji sauki, a gaskiya
kina shiga alhakina" Imaan bata tanka ta ba, Inna tace "Kin ko ji abinda nace"
Imaan ta daure fuska tace "Sai nan da kwana biyar ko shidda ma xai xo, ni dama haka
yake min ba shi bane" Inna ta tabe baki ta mike ta nufi dakinta tace "Ni dai ba
ruwana kar a xo a dameni a gigita ni" Imaan ta gama juye juyenta bacci ya dauketa.
wajajen karfe shidda Inna na daki duk ta fiddo da kayan closet dinta tana masu
linkin guga jin an bude kofa ta ajiye kayan xata fita parlor, ta labule ta hangi
Mujaheed tsaye cikin parlorn, kana ganinsa kasan daga aiki yake don ko tie din
wuyarsa bai cire ba kan farar shirt din jikinsa, kallon Imaan dake bacci ya tsaya
yi sannan ya kalli kofar dakin Inna, can dai ya karasa kusa da ita ya duka ya kai
hannu a hankali kan goshinta yana feeling temperature dinta, sauke hannunsa yyi kan
wuyarta ta bude ido tana kallonsa, yace "What's wrong?" Cikinta ta nuna masa kamar
xata yi kuka, daga cikin dakin ya ji muryar inna tana cewa "Don Allah a dinga
kyakkyawan xato dai, Shikenan ita kuma a rashin lafiya xata kare kamar warce ta
kashe mai rai ka wani kai hannu kana tattaba jikinta kaji ko da xafi ko babu, to
babu, kuma lafiyar jikata qlau ka matsa wajen tunda fatan ciwo kake mata, dama
likitancin hauka ne" Mujaheed ya dinga kallon kofar dakin, inna ta fito tace "A dai
ji tsoron Allah a dinga kyakkyawan xato fisabilillahi, lafiyarta lau wllh,
al'adarta ce kawai ke kan hanya shine ta langwabe haka, ka shigo kana wani tabe
taben jikinta salon a ja mata wani ciwon tunda a haka ake so ta kare" Shi dai kawai
tsayawa yyi yana kallon inna fuskarsa daure, can ya juya ya nufi kofa, inna tace
"Toh Ina yini... yanxu ka dawo daga aikin kenan" bai tanka ta ba har ya fice
parlon. Kafin magrib Imaan ta watsake gaba daya, bata shirya barin part din Inna ba
sai kusan karfe goma na dare tare da Yusuf, Inna na kallon Yusuf tace "Isuhu wai
daga na fadi ma Mujaheed gaskiya daxu shine har yanxu bai tako nan ba, to me xai
bani da Allah bai ban ba, banda ma magana da yake sa ni idan ya xo, ni dai kai da
Imaan kun isheni ni kar ma ya sake xuwa" Yusuf yyi murmushi bai dai ce komai ba ya
fita yana kallon Imaan dake tsaye gaba daya hankalinta na kan film da ake yace "Ko
dai in tafi ne Imaan" tace "A'a ya Yusuf jira ni, ynxu xa a gama" yace "Toh ki
kwana nan mana" da sauri ta fice a parlon har tana tuntube, Yusuf ya fara dariya,
Inna ta ja tsaki tace "Toh banda ki yamutse min gado ki bar ni da aiki amfanin me
xaki min idan kin kwana Imaan?" Yusuf ya kulle mata kofarta suka wuce, a hanya yace
"Me yasa baki son kwana wajen inna imaan?" Ta make kafada tace "Karfe uku idan ta
tashi sai tasan yanda tayi ta tashi mutum, tayi ta masa surutu har sai baccin ya
fita idonsa" Yusuf yyi dariya yace "Dole ma gobe ki kwana can tunda Friday ne"
Imaan tace "Sai dai kai ka kwana" daga haka ta shige balcony dinsu tana daga masa
hannu yyi murmushi yana kallonta yace "Good night" yana wucewa ta shiga ciki ta
kulle kofarsu.
"Wannan iskancin da kike ki tafi exams babu karatu baxa ki min shi a gidan nan ba
wannan karan" Cewar Ammi kenan tana kashe kayan kallon parlon gaba daya, Imaan ta
dinga kallonta kamar xata yi kuka bata dai ce komai ba, Ammi ta nemi waje ta xauna
tana danna wayarta, A hankali Imaan tace "Ranan Monday fa ne exams din Ammi, i
still have Saturday and Sunday sannan Monday da safe" Ammi tace "Ki tashi ki dau
abincin Inna ki kai mata baxa kiyi kallon ba, kuma I promise you har ku gama
jarabawan nan baxa ki kunna kayan kallo a gidan nan ba, ko yaushe kika xama
dedicated da kallo haka ban sani ba" da mamaki Imaan ke kallonta, can tace "Amma
ammi ban taba daukan sama da second position ba fa a schl" Ammi tace "Ur silly
First position ba karatu? I want to see ur grade idan kika yi karatu this time
around" Imaan ta dauke kai kamar xata yi kuka tace "Ni da ma ba wani kallo nake ba
sai lkci lkci kuma da ace 5th nake dauka shine sai ki ce in daina kallo fa Ammi"
Ganin kallon da Ammi ke mata ta mike ta sa hularta ta wuce kitchen ta dau abincin
inna dake ajiye tun daxu ta fice gidan, har ta isa part din inna ji take kamar ta
fashe da kuka, ta bude kofar ta shiga, xaune ta tadda inna da bowl din fura a
gabanta ta daura kafa daya kan daya, Yusuf na xaune parlon shi ma da cup din furan
a hannunsa, sai Ummi dake shan furan ita ma, Mujaheed dai idonsa na kan tv ga nasa
cup din furan a kusa da shi, Inna na ganin Imaan ta daure fuska ta rufe furan
gabanta ta mayar bayan ta tace "Ni dai wllh ya kare, ba ruwana sai kun ga mutum da
abu ku wani dinga tururuwan xuwa, to duk na rabar..." Imaan ta ajiye abincin
hannunta tace "Toh ni ina ruwana da furanki ce maki nayi xan sha?" Inna ta kalli
Ummi tace "Ke tashi ki shigar min da abina ciki" Ummi ta mike ta dau furan ta kai
daki ta fito, imaan ta turo baki tace "Sai kace nace xan sha" Inna tace "Toh ai sai
ki juya ki tafi koh?" Imaan ta ki fita don har ranta take son fura da nonon barin
idan inna ce ta dama kuma ita tayi furan da kanta, inna ta kalli na Mujaheed tace
"Dama ga wannan Boss din ya ji sha, ko raina wanda na tarfa masa yayi Oho, da yake
Rukayya ce tayi min wahalan aikin furan Ahmadu kuma ya siyo min nonon, cewa ma yayi
baxai sha ba ki dauka ki sha, Allah yayi da rabon ki" Yusuf yyi yar dariya yana
kallon Imaan, Imaan ta saci kallon Mujaheed dake kallon TV har sannan, ta kalli
rabin cup din furan kusa da shi, inna tace "Tunda fa aka ji yace baxai sha ba fa
baxai sha ba, kawai ki dauka rabon ki ne, don ni bani da wanda xan baki in kwana da
yunwa" Imaan tace "Toh wai ni nace maki xan sha ne?" Tana magana tana kallon kofar
parlon lkci daya ta suri cup din tayi waje a guje Yusuf ya kyalkyale da dariya don
yasan abinda xata yi kenan, Inna ta washe baki tana kallon Mujaheed tace "Allah ya
kara" mikewa Mujaheed yyi fuska daure ya bi bayanta, Inna ta rushe da dariya har da
kyakyatawa tana kallon Ummi tace "Da dai ki tashi ki kulle min kofa da makulli
tunda sun fita" Kafin Imaan ta kai rabin hanya dama gaba daya furan duk ya xube
saboda gudun da take, Mujaheed ya cafketa daga karshe ta fasa ihu ta sake cup din
hannunta ta kama hannunsa tace "Wayyo Yaya don Allah kayi hakuri inna ce tace in
dauka" da mamaki yake kallonta yace "Yaushe na fara wasa da ke gidan nan amma?"
Jikinta na rawa tace "Don Allah kayi hakuri Yaya" fuska daure yace "Kiyi providing
min furan nan yanxun nan idan ba haka ba wllh kinji na rantse sai na sa ki kuka" ta
fashe da kuka amma ba hawaye tace "Yaya bayan kana gani duk ya xube nima ban sha
ba, don Allah kayi hakuri xanje waje in siyo maka wllh" ya wani hade fuska yace
"Wannan nake so ba na waje ba" ta marairaice tace "Toh yanxu yaya a ina xan samo
maka wani, nima fa kaga bata bani ba" ya kalli part din Inna sannan ya kalleta,
murya can kasa yace "Kinsan abinda xa ayi yanxu?" Ta kara marairaicewa tana girgixa
masa kai, yace "Komawa xa kiyi part dinta ki shiga daki ki fito da bowl din furan
da gudu yanda kika fito min da nawa yanxu" ta xaro ido tana kallonsa, sai kuma ta
fashe da dariya tace "Yaya kasan baxata bari ba fa" ya hade rai yace "Irin dubaran
da kika yi kika fita da nawa haka xaki fito da wancan ma ae" Imaan ta dinga dariya
har da kyakyatawa, ya ja kunnenta yace "Baxa ki daina wannan dariyar mahaukatan ba"
ta hadiye dariyar da kyar tace "Toh amma tare xa mu sha?" Yace "Eh mana" tana
murmushi tace "Toh nasan yanda xan yi" a tare suka koma part din inna ya nuna mata
bayan window din bedroom din inna yace "A can xa ki sameni ina jiran ki" tace "Toh"
daga haka ya wuce yana waigota, a guje Imaan ta shige parlon inna tana cewa "Wayyo
inna kice masa wllh kar ya ta6a ni xan gaya sa da Abba, inna kice kar ya taba ji
xan kira daddy na...." Mujaheed yyi murmushi ya koma bayan window din ya tsaya yana
shafa kansa, Inna ta mike da sauri kar Imaan ta take ta koma wani wajen ta xauna
tace "Fito min daki wllh, ba ruwana ku je can ku karata kar wanda ya dameni, yara
dai kamar na jaraba" Imaan da ta shige dakin tuni ta dinga dariya kasa kasa ta dau
bowl din furan ta datse murfin yanda idan tana gudu baxai xube ba, ta tattara rigar
jikinta tayi saitin bakin kofar fita sannan ta fice a dari da sittin, inna ta
kyakkyafta ido don tabbatar da abinda ta gani hannunta amma tuni Imaan har ta fice
parlon kamar xata tashi sama, inna ta mike da sauri tace "Isuhu me na gani a
hannunta kamar kwanon fura na???" Ummi ta kyalkyale da dariya tace "Wllh shi ne"
Yusuf ya fashe da dariya, Inna ta fashe da kuka tana kallonsa. Imaan bata tsaya ba
sai da ta isa inda Mujaheed yake jiranta, murmushi yayi ya amshi bowl din yace
"Yauwa kinyi kokari" ta washe baki tace "Nagode" ya xauna kan dakali dake wajen ya
bude bowl din ya dau ludayin ciki ya juya furan sannan ya fara sha, Imaan ta daina
murmushin da take ta durkusa gabansa tace "Yaya kai kadai xaka sha" Ya harareta
yace "Toh da ni da wa xa mu sha?" Ta xaro ido tace "Wllh baxan yadda ba ni fa na
sha wahala na dakko kaga irin gudun da nayi yanxu ma fa kirjina ciwo yake" banxa
yyi da ita yana shan furansa don furan inna ba dai dadi da gardi ba, Ta fashe da
kuka tana kallon sa, ya hade rai ya debi rabin ludayin hannunsa ya kai bakinta, ta
turo baki tace "Wannan d'an kadan din bayan kai cika wanda xaka sha kake?" Yace
"Baxa ki bude bakin ba" ta bude bakin da kyar, ya xuba mata yace "Toh tashi ki
tafi" kamar jira take tace "Wllh baxan tafi ba ji fa abinda ka bani bayan ni na sha
wahalan daukowa, Allah sai dai ka bani in mayar" Yace "In baki ki gudu da shi
gidanku dai" Ta fashe da wani dariya har da kyakyatawa, ya harareta ya ci gaba da
shan furan, kamar xata yi kuka tace "Yaya" ya kalleta sannan ya debo furan rabin
ludayi ya kai bakinta, kin bude baki tayi tana masa wani kallo, ya kai bakinsa ya
shanye, ta fashe da kuka, yayi light murmushi ya kara deba ya kai bakinta, bude
bakin tayi ya juye mata, daga nan ya ci gaba da sha bai kara kallonta ba, kiris ya
rage ta fashe da kukan gaske, ganin bai san tana yi ba ta fixge ludayin hannunsa,
ya wara ido yace "Ke ina wasa da ke ne" ko kallonsa bata yi ba xata diba ganin xai
dauke bowl din ta marairaice tace "Don Allah yaya ka bari in sha wllh baxan cika
ba" yace "To diba in gani" ta turo baki ta ciko ludayin ta kai baki da sauri, ko
shanyewa bata yi ba ya fixge ya juye ragowar a bowl din sannan ya diba ya kai baki,
tana ganin haka ta dauke bowl din ta kai baki ta kwankwade ya xaro ido kafin yace
komai suka ji muryar Inna cikin kuka tana cewa "Ahmadu idan ba a bi min hakkina ba
yau a babbake ni cikin dare idan na kwana cikin gidan nan" Mikewa Mujaheed yyi da
sauri xai bar wajen imaan ta mike ta rikosa a rikice tace "Wayyo yaya kai ne kace
fa in dauko" Ya wani xaro ido yace "Ni?? You are sick, kar ma ki sa ni a maganan
nan" daga haka ya bar gun da sauri don da dukkan alama nan suke taho, Imaan ta bi
sa da gudu har suka iso gaban compound din gidan, ya wani hade rai yace "Wai me
yasa kike bi na ne ma dai tukun?" Ta marairaice tace "Yaya kai fa ka sa ni" Ya xaro
ido yace "Ohh dama idan nace ki shiga wuta sai ki shiga, kar ki kuskura ki ambato
sunana a maganan nan" on a serious note ya fadi hakan, ta hararesa tace "Wllh kai
ne kace in dauko da gudu in fito" xai yi magana suka ji alamar suna tahowa, inna na
cewa "Kuma ko tantama babu wannan tantirin Mujaheed din da ka haifa ne xai sa ta,
banda haka imaan ta san wani sace abincin mutane ta fita da gudu, wllh a min iyakan
gaske da yaran nan a gidan nan yau, a kan me xa su dinga cutata suna ci min mutunci
haka, wai har sun shanye furan sun bar min kwano a bayan window, me nayi masu a
rayuwa xa su min haka" tana kai wa nan ta rushe da kuka, Anty tace "Kiyi hakuri don
Allah inna" a fusace inna tace "Shegiya nake idan na hakura, a sace min furan a
shanye kice in hakura kamar uwata tace min je ki kya gani, ae Aisha dai ta haifi
fitina, wannan yarinya Imaan dai fitina ce wllh, a ma kira min Bukar yanxu, idan
ban tada gidan nan da bala'i ba yau ace bani ba" da sauri Mujaheed ya nufi gate,
imaan kamar xata fashe da kuka tace "Wayyo yaya" sai da ya kusa gate ya juya yana
kallonta ya fara dariya kasa kasa, bin bayansa tayi da gudu, gun motarsa dake parke
a kofar gida ta gansa xai bude maxaunin driver, ya buda ido yace "Wai me yasa kike
bi na ne?" Ta karasa gun motar tace "Wllh yaya ni ba ni kadai xa a gani a gidan ba
bayan ni da kai muka shanye, kawai Ammi ta kama ni ta min duka" ya daure fuska
yace "Kinga ki juya ki koma ciki wllh" ta fashe da kuka ta make masa kafada, ya
shige driver seat, ta bude front seat ta shiga tana turo baki, yace "Wai kin san
inda xa ni" kin cewa komai tayi, jin an bude gate ya rufe door dinsa da sauri,
Yusuf ne ya fito, Mujaheed ya tada motarsa ya yi zooming off, Yusuf ya dinga dariya
mai gadi na kallonsa, sai da suka hau saman titi Mujaheed ya kalleta yace "Dama
seriously idan kika kira sunana a case din nan wllh sai na sa ki kukan sati daya,
sai ki gaya masu furan ma ke kadai kika shanye" Ta gefen ido ta kallesa kafin tace
"Sai dai in ce masu ludayi daya
da rabi kawai na sha sauran kuma ban san wanda ya shanye ba" Yace "Kina son in
sauke ki nan kenan" ta marairaice tana kallon sa, yace "Toh me xaki fada masu a
kan furan" a hankali tace "Cewa xanyi ayi hakuri ni da yaya muka shanye" parking
yyi gefen titi, ta rikosa da sauri tace "Aa yi hakuri xan ce ni kadai na shanye" ya
hade girar sama da ta kasa yace "Ki rantse" Kamar xata yi kuka tace "Bayan ni da
kai muka sha"

Alhamdulillah, Thanks to all those that patronize the book *Imaan* Allah bar ku da
iyayen ku, My book Imaan is for sale coz I am done with free pages tun friday, ni
nasan it will go round as usual, I can't prevent that, but if you should come
across it it's not for free, i repeat it's not for free, na siyarwa ne, wllh I am
too grown up to say Allah ya isa, but have the fear of Allah SWT in u, don't forget
it's my property, hakkina ne, wahalata ce, pay before reading, pay before reading,
or you just over look it and smile, have a very good conscience plss, and a good
conscience won't read happily without paying, if you want any favor pertaining to d
book contact me and let me know, the book is 300 via..... Fcmb 3276052019
Hauwa Bello Jiddah

07087865788 and then u contact me through this digit to be added in the payment
groups. Thanks once more for patronizing.

For those saying xa su same shi a banxa yana yawo to gashi... amma fa ba a banxa
yake ba wllh, there is power in the tongue, Karamin hakkin da ka raina..... 😃😃
12. 🌟⭐IMAAN⭐🌟

Gidan wani cin abinci Mujaheed yyi parking, yace "Ki jira in fito..." da sauri tace
"Nima ba a cc abinda na ci wllh" ya kashe wayarsa kamar baxae ce komai ba sai kuma
yace "meat pie daya ya ishe ki" kafin tace komai ya bude motar xai fita, da sauri
tace "Yaya amma fa ban sa takalmi ba" da sauri ya kalli kafarta, yace "Good kinga
sai ki jira ni in ci abinci in fito" Ta fashe da kuka tace "Wllh haka xan fito, ni
fa ba abinda na ci tun da rana sai furan nan da ka tsammin" ya hade rai yace "Ki
fito ki ja min kallo cikin mutane" ta marairaice tace "Yaya to mu je ka siya min ko
bathroom slippers ne" yace "Ki dai jira yanxu xan gama cin abincin in fito" Bude
motar tayi ta fito, ya xaro ido yana kallonta, Xata xagayo inda yake ya mata tsawa
yace "Tsaya nan kar ki xo min nan" ta turo baki tana kallon sa yace "Dama ki tsaya
sai na shiga sannan ki shigo, kuma ki nemi can nesa da ni ki xauna xan sa a kai
maki abincin can" a hankali tace "Toh" Daga haka ya shiga yana waigota don tabbatar
da ta bar distance sosai tsakanin su, Yana xaunawa sai ga ta ta shigo, ya wani hade
rai ya dauke kai, tabe baki tayi ta nemi nesa da shi ta xauna ba tare da ta damu da
kallon da ake mata cikin eatry din ba, jollof rice da half chicken yasa aka kawo
masa da five alive drink sai bottle water, yana kallon waitress din yace "Ae kuna
da meat pie koh?" Tace "Ehh har da burger da pizza with sausage roll duk akwai"
yace "Good kinga wancan matar dake xaune at that far end?" Waitress din ta kalli
inda yake nunawa ganin imaan tace "Ehh na ganta" yace "Ki kai mata meat pie daya da
table water, ni xan biya bill din" tace "Ohk" daga haka ta wuce ta dau meat pie din
da table water ta nufi gun Imaan tana ajiye mata a gabanta imaan ta kalli Mujaheed
da ya dauke kai yana cin abincin gabansa, waitress din ta juya ta wuce, satan
kallonta Mujaheed yyi suna hada ido ya juya kujerar sa yayi backing dinta yana
murmushi yana cin abincin sa, Imaan ta dinga kallon sa amma ya ki juyowa, bayan
kusan minti uku ya sake juyawa a hankali, kawai ganinta yayi a gabansa tana kallon
sa kamar xata yi kuka, da sauri ya fara kalle kallen eatry din ya ga kallonsu kawai
ake, ya xaro ido kafin yace komai ta ajiye masa meat pie da ruwan a gabansa ta jawo
plate din abincin da drink ta dauka ta koma inda take ta xauna ta fara ci, Mujaheed
bai ce komai ba ya dauke kansa, bayan kusan minti goma ya mike ya tafi ya biya
kudin abincin da snack sannan ya dawo ya dau meat pie din da ruwa yana satan
kallonta ita ma kallonsa take, mamaki ya cika sa ganin har ta kusan cinye shinkafar
nama kuwa ta ma gama da shi, ya dauke kai ya nufi kofar fita, imaan ta mike da
sauri ta dau sauran five alive din ta bi bayansa, a tare suka iso gun motar, ya
bude driver seat ya shiga ita ma ta shiga gaba yace "Fita ki koma ki cinye abincin"
tayi yar dariya tace "Dama fa nasan wucewa xaka yi ka bar ni shi sa nake ta kallon
ka" ya hade rai yace "Fita nace" tace "Ai na koshi baka ga na cinye naman ba" tada
motar yayi ya bar eatry din, bayan sun hau saman titi yace "Xan maida ki gida
yanxu, wllh kika kuskura kika ce nasan komai a kan furan inna Allah xan sa ki kuka"
da mamaki tace "Kai ina xa ka yanxu?" Yace "Gidana" ta fashe da kuka tace "Toh
shine ni xaka maida ni gida, wllh kar ma ka kai ni don baxan fita daga motar nan
ba" ya buda ido yace "Toh ina xan kai ki?" Ta turo baki tace "Mu tafi gidan ka
tare" ya gyada kai yace "Tunda ke mahaukaciya ce ni ba mahaukaci bane" ta kallesa
tace "Toh da ba ina xuwa ba" ya jefa mata wani kallo yace "Da ba yanxu bane" Shiru
tayi ganin ya dau hanyar gida ta kamo sa tace "Don Allah yaya kar ka maida ni gida
yanxu, wllh Ammi xata iya dukana don dama tace kar in dauko mata magana" yace "Toh
ina xan kai ki?" Hawaye ta fara yi, yayi murmushi yace "Gobe baxa ki dauke ma
tsohuwa furanta ba, ni dama ba ruwana" ta hade kai da gwiwa tana kuka a hankali,
bayan few minutes yace "Abinda xai faru yanxu ina maida ki gida sai ki shige dakin
Anty da sauri, ki kwana a can" ta dago tana goge hawayen idonta tace "Don Abba ya
gani ko, kasan Ummi xata ce ma Abba ina nan" Ya daga kafada yace "Ae shi Abba baxai
doke ki ba, fada kuma baya nuna wa a jikin mutum" parking yyi yace "Oya fitar min a
mota sai da safe" wasu hawaye na xubo mata ta bude motar ta fita tana kallon sa
tace "Duk abinda ya faru daga farko har karshe xan gaya ma Abba baxan boye masa
komai ba, tare muka shanye furan kuma kai ka sa na shiga dakin Inna in dauko saboda
ta xuba maka kadan" daga haka ta bar wajen da sauri tana kuka ya bi ta da kallo
baki bude, tuni ta shige gate ta dinga rabe rabe har ta isa parking space din su
Yusuf, a haka har ta shige parlour rufin asirinta ba kowa da gudu ta wuce dakin
Anty, Anty dake xaune gaban madubi ta bude baki tana kallonta, Saman gadonta Imaan
ta hau ta rufa da duvet, Anty tayi murmushi tace "Ina Mujaheed din?" Imaan ta cire
duvet din ta mike xaune kamar xata yi kuka tace "Yace baxai dawo ba yau kuma wllh
Anty shi yasa in dauko mata furanta sai ma kinga abinda ya tsammin duk ya shanye
sauran" hawaye cike idonta take maganan, Anty tayi dariya tace "Ae ko kun sha
jaraba yau, don har yanxu Abba da Ammi na can ana ba Inna hakuri, nima gajiya nayi
na taho" Imaan ta turo baki ta koma ta rufe kanta da duvet. Washegari Saturday
Imaan na xaune gaban madubin Anty tana shafa mai don har tayi wanka, Anty kuma na
xaune kan darduma hannunta rike da hisnul Muslim aka bude kofar dakin, Abba ne
tsaye bakin kofar, Imaan ta kusa faduwa saboda rudewa, Abba ya kalli Anty yace
"Amina amma baki ce min yarinyar nan na nan ba" Anty tace "Ni ma har na yi bacci na
ganta jiya da daddare" Abba ya kalli Imaan yace "Ki sameni parlona yanxu" kamar
xata yi kuka tace "Abba to shi yaya fa?" Dakuwa Abba yyi mata yace "Stupid girl,
yayan banxa ai duk xa ku gane kuran ku yau" daga haka ya juya ya fita, Imaan ta
fashe da kuka tana kallon Anty tace "Kinga ni kadai xa a ma fada yaya ya gudu koh"
Anty tace "Ni dai ba kin sani nayi karya ba, maxa fita ki tafi ki samesa ba ruwana"
da kyar Imaan ta bar dakin sanye da Hijab dinta, Abba dake parlonsa ya mike ganinta
yace "Mu je" bin sa tayi tana goge hawayen idonta suka nufa part din inna, tun daga
nesa suka hango Mujaheed yana share mata frontage, Yana ganin Abba ya mike tsaye,
Ya gaida Abba da ladabi Abba ya masa banxa ya shiga parlon inna, inna ta fito
kitchen tace "Ahmadu ne da sassafe haka" Abba ya xauna ya gaisheta ta amsa, ganin
Imaan ta hade rai tace "Ya xaka shigo min da ita parlor Ahmadu, ni da dai ta tsaya
daga bakin kofa, tsoronta ma nake ji wllh" Abba ya kalli Imaan yace "Koma can"
komawa tayi bakin kofar ta tsaya, Abba yace "Shi yaushe Mujaheed din ya xo nan?"
Inna ta xauna tace "Ko minti biyar ba ayi ba, Ashe jiya na shiga alhakin yaron bai
ma san me ke faruwa ba baya gidan yana asibiti, sai yanxu da ya shigo nake basa
labarin abinda yarinyar ta min, ya taya ni jimami sosai yayi mamaki ainun, shine ya
ga xan share waje ya amshi tsintsiyar yake sharewa yanxu duk da dai nasan ba
sharuwa wajen xai yi ba amma ai dai ya fi babu" Abba ya sunkuyar da kai yana
murmushi, Inna tace "Yanda yarinyar nan ta sa na kwana da yunwa jiya gaskiya Ahmadu
idan ba a dau mataki ba xan tafi inje duk inda Allah yayi ko kasar waje ne kuwa,
don na gaji da cutata da take, jiya mun dade muna magana da Bukar a waya a kan
yarinyar tasa yana ta bani hakuri ni dai ban hakura ba" imaan ta fashe da kuka tace
"Wllh yaya ne yasa in dauko masa kwanon furan fa" Abba ya kalli inna da ta bude
baki tana kallonta, yace "Ke sai kika yarda da yace maki bai san me ke faruwa ba
dama?" A hankali Mujaheed ya ajiye tsintsiyar hannunsa xai bar wajen Abba yace
"Don't try that, come in now" Inna ta mike tace "Toh amma ko gaskiya Ahmadu ka
haifi abinda ya fi karfin ka, ka haifi tashin duniya, yanxu duk dadin bakin da ya
shigo ya min da sa hannunsa a sace min fura da nono, Haba da walakin goro a miya,
dama wani Mujaheed ne xai amshi tsintsiya ya min shara, ko da kuwa aiki xai kasheni
baxai yi ba wllh, wato xuwa yayi ya yaudare ni ya cuce ni to akwai hisabi ai, ni
dama nasan ina imaan ta koyi wani sata idan ba sa ta aka yi ba, ilai ga maganata
nan, kuma wllh kaji rantsuwar musulmi ko, to baxan yadda ba sai sun san yanda suka
yi aka min furata mai kyau mai kamshi da tsafta irin tawa sannan a siyo min
kindirmo mai kyau idan ba haka ba gaskiya abinda xai biyo baya a gidan nan har kai
sai ya shafa Ahmadu" Mujaheed ya shigo parlon kansa a kasa, inna na kallonsa da
kyau tace "Mugu katon banxa kawai, wllh yau idan na maku Allah ya isa kai da
figaggiyar yar nan sai ya bi ku don kun ci da hakkina, ku ka bar ni na kwana da
bakar yunwa, to amma ya xanyi, sai dai ku ci albarkacin Ahmadu da Bukar don ni ba
abinda na hada da ku, ba dangin iya balle na baba, kawai sai dai ku ci albarka cin
'ya 'yan da na haifa tunda su suka haifo ku duniyar, to banda 6are ma wa xai maka
haka, ai 'ya yana baxa su min haka ba, amma kuma Ahmadu ka min iyaka da su kar kato
ko figaggiyar da ta sake xuwa bangarena bana bukata Isuhu ya ishe ni rayuwar
duniya" Imaan sai hararanta take ta gefen ido, Mujaheed dai kansa na kasa, Abba
yace "Toh bana son sake ganin kai ko Imaan a bangaren nan" da sauri Inna tace "Har
abada kuwa, don gaskiya idan suka xo sun ja ma kai da Bukar fitina, ita ta tsaya
iya bangarensu, shi ma ya tsaya iya nasu, kada wanda ya tsallaka ya yo min nan don
xan gudu in bar gidan" Abba yace "Hope u both are apprehending?" Mujaheed yace "In
sha Allah" Inna tace " Kuma kafin gobe a kawo min furata da aka yi a kuma siyo min
kindirmo nah" Abba yace "Xa su san yanda suka yi in sha Allah" inna ta kalli Imaan
tace "Ke kin ma ci halas ya kika kare da ciwace ciwace balle kin dau hakkin mutane,
jarababbiya kawai" Imaan ta fashe da kuka Inna tace "Fita can kije ki ma uwar ki
Aisha, fitar min a parlor" Juyawa tayi da gudu ta fita tana rusa kuka, Inna ta
kalli Mujaheed tace "Kai ma fita, har abada kada ka sake tako min nan, kaje can ka
saci furan uwar ka idan ta yi" ta gefen
ido ya harareta ya fice a parlon, Abba yace "Ki kara hakuri xan sake ja masu
kunne" tace "A'a ni ba ruwana ba dai na gama yanke hukuncin da nake so ba suje can
su karata, sai kuma ko wannensu yyi ma uwarsa rashin mutunci ba dai Inna ba" Abba
yyi murmushi bai dai ce komai ba. A hanya Mujaheed ya tadda imaan tana kuka bakin
rai kamar xata shide, ya tsallake ta yayi wucewarsa. Mujaheed na komawa part dinsu
dakin Ummarsa ya nufa, tun da ya shigo take kallonsa ya xauna yace "Ina kwana
Umma?" Tace "Ban kwana ba, yanxu duk abinda xaka janyo a xageni a ci min mutunci
baka gudunsa ko Mujaheed? Wannan kakar taka wai dole ne sai kaje inda take tunda
ita jarababbiya Allah yayi ta, sannan kuma yunwa kake ji da ka dau shegen furanta
jiya ta daga mana hankali a gidan nan, ni duk wannan bai wani dameni ba, babban
damuwata a nan shine yaushe har ka fara shiri da yarinyar nan Imaan da ku ka dauke
furan a tare ku ka sha?" Mujaheed ya bude ido sosai yana kallonta yace "Shiri kuma
Umma? Ni bamu wani sha fura tare da ita ba, nine ma na dauke furan na sha" Umma
tace "Toh naji tana cewa kai ka tura Imaan daukan furan ku ka raba" ya girgixa kai
yace "A'a ba haka bane" Umma tace "Sannan da ake nemanka jiya ina ka tafi, ita
yarinyar ma bata gidan a jiya da daddaren" Yace "Ni fa eatry na tafi cin abinci
karfe sha daya ya wuce na shigo duk kun yi bacci" tana masa wani kallo tace "Toh
ita imaan din ina ta tafi?" Yace "Ban sani ba gaskiya" Umma tace "Mujaheed?"
Kallonta yayi tace "Mujaheed?" Yayi Shiru yana dubanta tace "Sau nawa na kira ka?"
Ya sauke idonsa kasa tace "Toh wllh idan baka kama kanka gidan nan ba xan sa6a
maka, ita kanta innar daga yau na kashe xuwa sashinta, kar ka sake tunda ba kanwar
uwata bace ita din, idan kana son gaida kakarka ne sai ka shirya ka tafi katsina
uwata na can da ranta" murmushi kawai Mujaheed yyi, tace "Dama tun shekaranjiya
akwai maganar da nake son mu yi to da ka dawo gun aiki sai ka tare gun alakakan
matar can sai nayi bacci xaka shigo min nan" ya daga kai ya kalleta yace "Toh ina
ji Umma" tace "Kasan Hajiya Mansura kuwa?" Ya girgixa kai yace "A'a" tace "Ka santa
mana, wata warce ka taba kai ni gidanta a Marafa, ka koma dauko ni da yamma ruwa ya
tsuge har tace ka shigo ka ci abinci ka ki ci?" Yace "Ohh na tuna ban san sunanta
ba ai" tace "Toh ita ce Hajiya Mansura, dama tana da wata budurwa yar shekara
ashirin da daya tana karatu a Malaysia, to ina jin last week suka dawo hutu, baka
ganta ba kyakkyawa fara doguwa ga hankali da nutsuwa, shine nake baka shawaran don
me baxa ka neme ta ba" Shiru Mujaheed yyi bai ce komai ba, Umma tace "Sunanta
Safeena, nasan ma xaka so ta ne coz she have all the qualities, uwa uba ga ubanta
mugun attajiri abokin ma d'angote ne aka ce" Murmushi Mujaheed yyi bai dai ce komai
ba, Umma tace "Ba batun murmushi bane wannan, dama gashi saura wata hudu ta kare
karatun, last week da naje gidan na ganta ta kwanta min har nayi ma Hajiya Mansurar
magana ita ma ta ji dadin tunanin nawa don ta yaba da hankalin ka, yanxu abinda
nake so da kai ka shirya kaje gidan ko xuwa Sunday tunda baka xuwa aiki da safe,
dama xan baka sako ka kai ma Hajiya Masurar nasan xaka ga Safeenar" Murya can kasa
Mujaheed yace "Toh, Allah ya kai mu" Umma tace "Ameen son, Allah maka albarka" yace
"Ameen, xan je in yi breakfast Umma" tace "Toh shikenan" mikewa yayi ya fita dakin
ya kulle mata kofar. Karfe takwas Mujaheed ya fito xai fita kofar gida yaga imaan
tsaye jikin mota tana jiran fitowarsu Maimoon su wuce islamiyya, idonta ya kumbura
kana ganinta kasan ba karamin kuka ta ci ba, tunda ya fito take kallonsa ta wani
cika kiris ya rage ta fashe, Mujaheed ya saci kallonta suna hada ido ya dauke kai,
ta fashe da wani matsanancin kuka, da sauri ya kalleta kafin yace komai ta shige
gidan da gudu, direct parlon Abba ta nufa, ta samesa kuwa yana kallon news shi
kadai, ta xube nan tsakiyar parlon ta dinga rusa kuka kamar xata shide, ya mike da
sauri yace "Subhanallah, me ya faru mamana?" Tana kuka sosai tace "Abba Yaya ne ke
min dariya, Wayyo Abba" da mamaki yake kallonta, yace "Dariyar me yake maki" ta
kara fashewa da kuka tace "Nima ban sani ba wllh Abba" komawa yayi ya xauna yace
"Xo nan" mikewa tayi ta koma kusa da shi tana kuka sosai, yayi murmushi ya
rungumeta yace "Ya isa haka mamana kiyi hakuri kinji" ta kasa cewa komai yace "To
baxa ki daina kukan ba?" Da kyar tace "Xan daina" Ya dau handkerchief ya mika mata
yace "Toh goge idon ki kiyi Shiru" tana sauke ajiyar xuciya ta amsa tana goge
idonta wasu hawayen na sakkowa, Umma ce ta shigo parlon rike da mug din ruwan
Lipton yana turiri, tun da ta shigo take kallon Imaan dake rungume jikin Abba har
sannan ta dinga kallonta da wani expression a fuskarta, Umma ta dai ajiye mug din
hannunta xata xauna Abba yace "Nemo min Muhammad" Umma tace "Muhammad kuma, lafiya?
Ina jin dai ya fita uxurin gabansa ba gwanda a kai ta asibiti ba idan ma ciwon nata
ne ya tashi" Abba ya dau wayarsa yayi dialing number Mujaheed, Mujaheed dake xaune
gun mai kiosk dake 2 houses away bayan ya siya card ya dinga kallon screen din
wayarsa ganin Abba ke kira, ya daga ya kai kunnen kafin yace komai Abba yace
"Muhammad ka sameni parlona yanxu" Daga haka ya katse wayar, Umma ta tsaya kallon
Abba fuska daure, ba a dau lkci ba Mujaheed ya shigo parlon da sallama, sosai
gabansa ya fadi ganin Imaan kusa da Abba ga Umma ma tsaye a parlon, ya sunkuyar da
kai ya duka kasa a hankali yace "Abba gani" Abba na kallon Imaan yace "Me kika ce
ya maki mamana" cikin rawar murya tace "Dariya ya min ban san ko ya san Ammi ta
doke ni bane" Abba yace "Subhanallah ta doke ki kuma, me kika mata" ta fara kuka
tace "Wai na sha ma inna fura shine ta mareni ta kuma dokeni a bayana" Abba yace
"Aa bata kyauta ba xan je In sameta yanxu kuwa, kai kuma Mujaheed dariyar Uwarka
kake mata" Umma ta dinga ma Abba wani irin kallo, Mujaheed ya girgixa kai yace
"Abba ni ban fa ganta ba balle in mata dariya" Imaan tace "Wllh ya gan ni ya dinga
kallona a sace" tana fadin haka ta fara share hawayen dake sakko mata, Mujaheed
yace "To tayi hakuri tunda tace na mata dariya amma ni ban mata ba" Imaan ta turo
baki ta dauke kai, Abba yace "Ai kin hakura koh" kin cewa komai tayi Abba yace "Toh
kiyi hakuri mamana Aisha kuma zan je in sameta yanxu, maxa tashi ki tafi makarantar
kar ki makara" Umma ta fice parlon rai a bace, a hankali Imaan tace "Abba nasan su
Maimoon sun tafi yanxu" Abba yace "To mu je in ajiye ki" yana fadin haka ya mike ya
dau makullin mota, Mujaheed ya mike yace "Bari in ajiyeta Abba" Abba ya dau dubu
biyu ya bata yace "Toh ga kudin lunch din ki" ta rusuna ta amsa.

Alhamdulillah, Thanks to all those that patronize the book *Imaan* Allah bar ku da
iyayen ku, My book Imaan is for sale coz I am done with free pages tun friday, ni
nasan it will go round as usual, I can't prevent that, but if you should come
across it it's not for free, i repeat it's not for free, na siyarwa ne, wllh I am
too grown up to say Allah ya isa, but have the fear of Allah SWT in u, don't forget
it's my property, hakkina ne, wahalata ce, pay before reading, pay before reading,
or you just over look it and smile, have a very good conscience plss, and a good
conscience won't read happily without paying, if you want any favor pertaining to d
book contact me and let me know, the book is 300 via..... Fcmb 3276052019
Hauwa Bello Jiddah

07087865788 and then u contact me through this digit to be added in the payment
groups. Thanks once more for patronizing.

For those saying xa su same shi a banxa yana yawo to gashi... amma fa ba a banxa
yake ba wllh, there is power in the tongue, Karamin hakkin da ka raina..... 😃😃

13.🌟⭐imaan⭐🌟
A hankali Imaan tace "Abba nasan idan muka fita kilan xai min fada a hanya"
Mujaheed ya kalleta bai ce komai ba Abba yace "Toh ya maki fadan mu ga" Murmushi
kawai Mujaheed yayi ya fita parlon, Abba yace "Maxa ku tafi kar kiyi latti mamana"
Imaan ta bi bayan Mujaheed tana share idonta, tunda Mujaheed ya fito parlon Abba
gabansa ya dinga faduwa, xaune ya ga Umma a main parlor fuskar nan nata a tamke,
Mujaheed ya karasa inda take, ita ko bata fasa kallonsa ba, kofar fita Imaan ta
nufa, Mujaheed yyi kasa da murya yace "Umma dama Abba...." Katse sa tayi tace "Bana
son jin komai, Ban baka izinin fita parlon nan ba in har ni na haife ka Mujaheed,
ko da kuwa me xai faru yau" Kallonta Mujaheed ya tsaya yi ba tare da yace komai ba,
Anty ta fito kitchen da breakfast a hannunta tayi wani dariya tace "Su haihuwa
manya...." Umma ta kalleta ta dakatar da ita da sauri tace "Ke in kina cin k'asa ki
kiyayi ta shuri, ki daina min shisshigi a lamari na, ki yi mai fissheki kawai a
gidan nan" Anty ta tabe baki tace "Anya akwai wanda ya kai me shiga lamarin d'a da
ubansa shisshigi kuwa, kuma naga duk wanda xai ce d'a kada ya bi umarnin mahaifinsa
shine mai babban shisshigi a rayuwa kuma bai dauko abinda xai fishshesa ba" Umma ta
mike rai bace tace "D'an ki ko nawa? tunda ba wata shegiya ce ta haifa min d'an ba
sai kiyi ta kanki ki, ki kuma cire min ido kan d'a na" Anty tace "Na wuce in tsaya
ina xance irin na yara da ke, amma bari in baki shawara, domin kin haifi Muhammad
ba yana nufin ke kadai ke da iko da shi ba duk ki bi ki takura ma yaro sai abinda
kike so xai yi a gidan nan, kina amfani da advantage din ganin yana maki biyayya
dari bisa dari...." Cikin tsawa Umma tace "Da ke da shawarar taki Allah kwashe maku
albarka..." Dai dai nan Abba ya fito parlon jin hayaniya, ya kalli Mujaheed dake
tsaye, ya kalli Yusuf dake tsaye stairs yana kallon su shi ma sannan ya kalli su
Umma yace "Me ke faruwa nan?" Rai bace Umma tace "Ka ja ma matar ka kunne Alhaji ta
fita harkata kada abu ya bace tsakanin ni da ita a gidan nan, ta cire ido kan d'a
na, ta kuma yi ta kanta..." Abba ya dakatar da ita yace "I asked what happened kina
min warning madam" Anty ta tabe baki tace "D'an ta da ka aika yanxu... ta hana shi
xuwa saboda isa da gadara, to ni kuma bana gani inyi shiru...." Abba ya kalli
Mujaheed da ya kasa dagowa ya mika masa hannu yace "Bani makullin motar...." Da
kyar Mujaheed ya dago yana kallonsa sannan ya kalli Umma, ta watsa masa wani kallo
alamar ya basa, a hankali Mujaheed yace "Abba ai bance fa baxan je ba" yace "Eh
baka ce ba, amma ba ni" Mika masa makullin Mujaheed yayi, Abba ya kalli Yusuf yace
"Here, ka tafi ka ajiye Imaan a makaranta" Yusuf ya karasa saukowa stairs da yake
tsaye ya amshi makullin sannan ya nufi kofa ya fita, Juyawa Abba yyi ya koma
parlonsa, Mujaheed ya wuce sama a sanyaye, Anty ta tabe baki ta wuce saman ita ma,
wani ajiyar xuciya Umma ta sauke ta koma ta xauna ranta fess. Sai bayan da suka bar
gidan Imaan ta kalli Yusuf tace "Ya Yusuf Umma ce tace yaya kar ya kai ni koh?"
Yusuf na driving yyi murmushi yace "Toh dama ya xa ayi ta bari ya kai ki?? salon ku
je ya d'an rankwashe ki ki dawo kina mana ihu kina kuka" xaro ido Imaan tayi tana
kallonsa, Ya ki kallonta sai murmushi yake, ta hade rai tace "Toh an doki mutum
kuma baxai yi kuka ba" Yusuf yace "A'a xai yi kuka abunsa" Turo baki tayi bata ce
komai ba, shi ma bai kuma cewa komai ba har ya iso islamiyyarsu ya tsaya bakin
gate, ya kalleta yace "Kin fa yi latti sosai" tace "Ae xa su ga idona kuma cewa
xanyi bani da lafiya, dama ban da lafiyan" daga haka ta bude motar ta fita, D'aga
masa hannu tayi, yayi mata murmushi ta shiga cikin makarantar. Imaan na dawowa
islamiyya karfe sha biyu kashegari lahadi ta fara shirin tafiya gidan gwaggonta
wato Mahaifiyar Ammi dake unguwar rimi, Tun da ta fito daki Ammi dake xaune parlor
ke kallonta, tsadadden atamfa ne jikinta sai dan kunnenta na gwal, babu abinda ke
fuskarta banda eye pencil da chappete da ta goga a lips, sosai tayi kyau duk da
haka, da mamaki Ammi tace "Ina xa ki?" Imaan ta xauna kusa da ita tace "Gidan
Gwaggwo mana Ammi" Ammi ta mata wani kallo tace "Kin gaya ma Daddy ne?" Ta
marairaice tace "Daddy baxai hanani ba fa na sani" Ammi tace "Baxa fa ki fita gidan
nan ba sai da saninsa don ba ruwana" tashi Imaan tayi kamar xata yi kuka ta shiga
dakinta kiran Abba, wayarta da bata damuwa da ta dauko ta yi dialing number sa,
bayan wani lkci ya dauka, ta amsa sallamarsa sannan ta gaishesa, yace "Ya kike
Imaan" tace "Lafiya Daddy ya aiki?" Yace "Alhmdllh, har kun dawo islamiyyar?" Tace
"Ehh daddy dama gidan gwaggwo nake son in je in gaisheta shine Ammi tace sai na
gaya maka" yace "Ae kina da islamiyya da yamma mamana" kamar xata yi kuka tace "Ae
kafin karfe hudu xan dawo" yayi shiru kafin yace "Toh waye xai kai ki?" Tace "Ni
kadai Daddy ai ina xuwa ni kadai" yace "Kai ma Ammin ta ki waya" fita dakin tayi ta
kai ma Ammi waya, Ammi ta amsa ta kai kunne, daddy yace "Why not drop her plss bana
son tana fita ita kadai" Ammi tace "Sai kace wata yar shekara goma yallabai, she do
go out her self...." Daddy yace "Toh minti nawa ne kin ajiyeta ki dawo" Ammi tace
"I told u for the past two month ban shiga motar nan ba, sai dai ta bari next week
mu je tare idan Allah ya yarda, ina da aikin da xan yi yanxu, ko jiya fa naje gidan
gobe ma xan je, yau kuma sai na kai Imaan?" Daddy yace "Bata wayar" Ammi ta mika
mata, daddy yace "Mamana ki bari next week ku je da Ammin ki idan Allah ya kai mu"
imaan ta fashe da kuka tace "Bayan na shirya daddy, na fa san hanya ba yau xan fara
xuwa ni kadai ba" Daddy ya dan yi shiru kafin yace "Shikenan to kije, but go with
ur nose mask, and inhaler, Allah ya kiyaye hanya" tana goge idonta a hankali tace
"Toh daddy na gode" Ammi ta shiga kitchen ta dauko dambun naman da tayi ma
mahaifiyarta tace "Ki kai ma gwagggo ina gaisheta sai na xo goben" Imaan ta amsa
tace "Toh" dubu Biyu Ammi ta bata ta bar gidan bayan tasa gogaggen Hijab dinta har
kasa, a dai daita Imaan ta samu da xai kai ta har gidan, bayan sun isa ta sauka ta
basa kudinsa sannan ta shiga gate din gidan, babban gida ne sosai da su Ammi suka
siya ma mahaifiyar tasu, Ammi ce ta biyu gun gwaggwo bayan babban yayansu Umar, sai
maxa biyu da mace daya Anty Murja, duk sun yi aure da 'ya yansu, yar Anty Murja ta
biyu Halima ce ke gaban gwaggwo kuma ita xa ayi aurenta kwanan nan, Sosai Gwaggwo
tayi murnar ganin Imaan, duk cikin jikokinta ko da bata nunawa ta fi jin Imaan har
ranta, Imaan ta rungumeta cike da jin dadin ganinta ita ma, Gwaggwo tace "Kin guje
ni Fatima" Imaan tace "Toh Gwaggwo kinga idan naje boko da safe da yamma muna
dawowa xan wuce islamiyya, ranan asabar kuma islamiyya safe da yamma, yau ma kawai
dai na taho ne kuma da wuri xan koma saboda islamiyya" Gwaggwo tace "Toh Allah ya
maki albarka ya baki sa'a a karatun ki, ya Ammin ki fa?" Imaan tace "Tana gaishe
ku, tace in kawo maku wannan" Gwaggwo tace "Toh nagode Allah mata albarka, fatan
mutan gidanku duk suna lafiya" Imaan tace "Duk lafiya lau" Ammi tace "Mujaheed ya
daina xuwa min kwata kwata yanxu yana kasar kuwa?" Imaan tace "Yana nan" Gwaggwo
tace "Ikon Allah, shi kuma d'an farin fa, duk da shi baya ma gaida mutane dama"
Imaan tayi dariya tace "Shi ma yana nan" Gwaggwo tace "Toh Allah maku albarka, in
ji kakarku tana lafiya" Imaan ta turo baki tace "Ehh" Gwaggwo tace "Toh Allah ya
kara mana lafiya, ki dauko lemo fridge ki sha" Imaan ta gyara xamanta tace "Anty
Halima bata nan ne?" Gwaggwo tace "Taje kai anko" Imaan tace "Toh ni ba a ban ankon
ba" Gwaggwo tace "Xa ta kai maki naki har gida tace" Imaan ta washe baki tace "Toh"
mikewa tayi ta dauko malt daya ta dawo ta xauna ta fara sha tana cin dambun naman
da ta kawo, Gwaggwo tace "Inji yanxu ciwon ki yana sauki sosai kamar yanda
mahaifiyar ki ke gaya min idan na tambaya" Imaan tace "Ehh da sauki" Da damuwa
Gwaggwo tace "Allah ubangiji ya yaye maki wannan cutar Fatima, in sha Allah xaki
samu lafiya gaba daya muna nan muna gaya ma Allah" Yar dariya Imaan tayi tace
"Gwaggo ya Salim yana xuwa?" Gwaggwo tace "Yauwa kwanaki yayanki Muhsin ya kawo min
karar ki wai baki gaida mutane" Imaan ta hade rai ta daina cin naman da take tace
"Ni kullum sai yace bana gaishesa, to ma a ina nake ganinsa balle in gaishesa"
Gwaggwo tace "A'a Fatima ga wannan dai waya da ta kawo komai da sauki, ko shi kika
dauka ai xa ki kirasa ku gaisa" Imaan ta turo baki tace "Toh shi ma fa ba kulani
yake ba wllh" cike da damuwa Gwaggwo tace "Ni dai ku rike xumunci don Allah, ba kya
ganin yanda iyayenku ke yi ne, ubansa ya sha nono ya bar ma uwarki, wllh baki da
yan uwan da ya wuce su don mutan gidanku ba son ke da uwar ki suke ba duk an sa
maku ido, ga kakarku fitinanna, kiyi ma kanki fada ki rike xumunci da yan uwanki na
nan, duk suka xo gaisheni sai sun tambayeni ke ba Usman ba, ba Muhsin din ba, ba
Salim ba ga matan su ma gaba daya, ke sai kiyi shekara baki xo nan ba baki je
gidajen nasu ba shi sa bakwa hadu duk da ba laifin ki bane laifin uwar ki ce don
ita ya kamata ta sa ki a hanya ta kuma sa maki ido" Imaan dai sai cin namanta take
tana shan malt, sallama aka yi bakin kofa Gwaggwo ta amsa Muhsin ya shigo tare da
abokinsa, Gwaggwo tace "Sannun ku da xuwa, yanxu nake xancen ka Muhsin" Muhsin yayi
murmushi yana kallon Imaan da ta ki kallonsa yace "Wannan fitsararriyar ce ta xo
ashe" Gwaggwo tayi dariya tana kallon abokinsa tace "Sannu da xuwa Sadeeq kwana
biyu ka gujeni" murmushi yyi ya cire glass din idonsa ya karaso Inda take ya
durkusa yana kallon Imaan da taki dago kai sai cin namanta take yace "Sannu Kaka
ina yini" Imaan ta daga kai don muryar sounds soo familiar, Gwaggwo tace "Lafiya
lau Sadeeq ya mutan gidanku? Ya kuma aiki da kujuba kujuban rayuwa" ya sauke kansa
kasa yace "Alhmdllh mun gode Allah Kaka" Gwaggwo tace "Toh Allah yayi maku albarka
ya kare ku sharrin makiya, ya tsare ku da tsarewarsa" a hankali yace "Ameen" ya kai
idonsa kan Imaan that was so uncomfortable,
Muhsin yace "Ina yini Anty Imaan" boye fuskarta tayi da kujera yace "Ke yanxu kin
girma kin daina kula kowa kin mance lkcn da kike kuka sai an goya ki, kiyi ta bamu
wahala muna goya ki a anguwa koh" kamar xata yi kuka tace "Ya Muhsin bana so ni
yaushe nake kuka a goya ni" yayi dariya yace "Tunda kin girma kin manta ai
shikenan, gashi nan ma kin daina gaida kowa" kamar xata yi kuka tace "Ya Muhsin kai
ma fa ba magana kake min ba, ni da bani da lafiya ka tambayi Ammi ma, kuma ni ina
dadewa ban hau whatsapp ba, wayar ma ba amfani nake son yi da shi ba" yace "Yaushe
ne baki da lafiya?" Gwaggwo tace "Kai ma dai Muhsin sai kace baka san dawan garin
ba, sai kayi mata addua da fatan samun lafiya" Muhsin yace "Toh Allah ya sauwake
Imaan amma ai kina shan magani koh?" Ta gyada masa kai ba tare da ta dago ba, yace
"Sannu lil sis" ta turo baki a hankali ba tare da ta dago ba still tace "Ina yini"
ya xaro ido yace "Toh boye fuskar ta meye, Kunyata kika fara ji ko na abokina" ya
fadi haka yana muna sadeeq dake kallonta, kin dagowa tayi ta kuma ki cewa komai,
shi dai Sadeeq sai kallonta yake, Gwaggwo tayi dariya tace "Fatima kenan, to tashi
ki shiga ciki" kamar jira take ta mike ta wuce dakin Gwaggwo da sauri, Muhsin yayi
murmushi yace "Imaan Daru" mikewa Gwaggwo tayi ta dauko ma Sadeeq ruwa da lemo yace
"Da kin bar shi Gwaggwo daga gida mu ke ai" Gwaggwo tace "A'a idan baka son inyi
fushi to ka sha, ga dambun nama yanxu Imaan ta kawo min" murmushi yyi ya dau bottle
wata daya ya bude, Muhsin yace "Wai ban ga Amaryar gidan nan ba?" Gwaggwo tace
"Taje kai anko, nasan tana hanyar dawowa yanxu" Muhsin yace "Da alama dai duk
Halima ta kagu ta bar ki" Gwaggwo tace "Don bata nan shine xaka mata wannan
sharrin, to bari dai ta dawo" Muhsin yyi dariya yace "A'a ni dai ba ruwana rufa min
asiri Gwaggwo" Sadeeq dai sai murmushi yake yana danna wayarsa, hira suka dinga yi
gaba daya a parlon har kusan Asr, Muhsin yace "Gwaggwo bari mu je masallaci mu dawo
yanxu" Gwaggwo tace "Toh Allah maku albarka" Muhsin ya mike tare da Sadeeq suka
nufi kofa, tashi Gwaggwo tayi tana kiran Imaan da bacci ya dauke tun daxu a dakin.
Suna fita compound Sadeeq na kallon Muhsin yace "Wacece yarinyar nan Muhsin?"
Muhsin ya wara ido yace "Ko dai kana ciki ne Abubakir?" Sadeeq yace "Na santa ne
shi sa nake tambayarka" Da mamaki Muhsin yace "Haba, amma ban ga ta nuna alamar ta
san ka ba" Murmushi Sadeeq yyi yana shafa sajensa yace "Ni na nuna alamar na santa
banda yanxu da na fito?" Muhsin yace "Toh ina ka santa?" Sadeeq yace "Baka fada min
relation dinka da ita ba" Muhsin yace "Cousin dita ce, mum dinta ita ce immediate
sister din Abbana" da mamaki Sadeeq ke kallon sa yace "You mean you two are this
close?" Muhsin yace "Sure" Sadeeq yace "That's Amazing, she is Mariya's school
friend kaga dalilin da ya sa na santa" Muhsin yace "Maa sha Allah, amma bata gane
ka ba ko?" Murmushi Sadeeq yayi yana maida glass dinsa yace "Ta gane ni sarai, that
was why she was uncomfortable" Muhsin yyi dariya yace "Ohh I see, there is
something a kasa kenan" Sadeeq yace "Let not miss jam'i plss" daga haka suka shiga
masallacin don yin alwala. Imaan na idar da sllh tace ma Gwaggwo xata wuce don xata
islamiyya, Gwaggwo tace "Baxa ki ci abincin ba kenan, shinkafa ce da miya fa" Imaan
tace "Bana jin yunwa fa Gwaggwo" Gwaggwo tace "Toh shikenan ki duba siff a daki
xaki ga wani sabon hijab da na dinka maki da takalmi ki dauka," Imaan tace "In ji
me hannu ne Hijab din?" Gwaggwo tace "Ae nasan me hannu kike sawa, shi nayi maki"
Bude kofar parlon aka yi Muhsin ya shigo tare da Sadeeq, Muhsin yace "Har kin fito
kenan yan matan Ammi" Imaan tayi murmushi tace "Ehh wucewa xan yi saboda islamiyya"
Muhsin yace "Mu ma yanxu xa mu wuce ai" Gwaggwo tace "Toh sai ku ajiye min ita don
Allah a gida kar ta kara bin k'uran nan ta koma a samu matsala" Dariya Muhsin yayi
yace "Wa yaga imaan baturiya" Imaan ta boye fuskarta, dubu biyar Sadeeq ya ajiye ma
Gwaggwo yace "To kaka xa mu koma sai wani lkcn kuma, ba yawa wannan ki siya goro"
Gwaggwo tace "A'a gaskiya ka dau kayan ka Sadeeq, matsalata da kai kenan idan ka xo
gidan nan kai baka gajiya ne" murmushi kawai yayi, Muhsin yace "Shikenan dama ban
fito da kudi ba ya fanshe ni, sai ki raba, nawa da nasa" Gwaggwo tayi dariya tace
"Allah sarki, Toh Allah dai ya maku albarka ya ba ku mata na gari kuyi aure ku bar
xaman nan da ku ke" Muhsin yace "Toh Ameen Gwaggwo" Tare Imaan suka fita da Muhsin
don Sadeeq har ya fita, ta bude back seat ta xauna, Sadeeq ne xaune driver seat din
Muhsin ya shiga front seat suka bar anguwar. Hira suka ta yi a motar, ita dai danna
wayarta kawai take, amma da ta daga kai xa su hada ido da Sdeeq ta madubi, sai tayi
maxa ta sauke kanta, bayan tafiyar kusan minti sha biyar ta ji Muhsin yace "Ajiye
ni nan man" parking Sadeeq yyi, Muhsin ya fita yana kallonta yace "Toh anmata sai
mun yi waya ki gaida Ammi, abokina xai ajiye ki gida" ta xaro ido tace "Ya Muhsin
nima nan fa sauka xan yi dama" Muhsin yace "Inaaa... bayan amana Gwaggwo ta ba mu
mu kai ki gida kada kura ya taba ki, nima akwai abinda xan yi anguwar nan ne amma
da tare xa mu tafi" Imaan ta dinga kallon sa kamar xata yi kuka, ya daga mata hannu
yana danne dariyarsa yace "Sadeeq drive her carefully plss sai mun yi waya" daga
haka Sadeeq ya ja motar suka hau saman titi, Imaan dai sai wasa take da fingers
dinta, bayan wani lkci ta dago a hankali tana kallon gaba suka hada ido ta madubi,
da sauri ta sunkuyar da kanta, yayi murmushi yace "Kina tsoron kada in sace ki ko?"
Kin cewa komai tayi, bayan kusan minti biyu taji cikin cool voice dinsa yace "I am
Abubakar Sadeeq Ahmad, was born and bred up here in Kaduna, first son of the
family, my primary and secondary education all in Kaduna, before I proceed to UK
where I had my degree and msc, I am a medical practitioner....." Kallon sa kawai
Imaan take ta madubi, yyi murmushi yace "Mariya is my step sis, I have six siblings
altogether, ranan kinje gidanmu amma part din stepmum dita, namu part din yana
cikin gidan though very far away, soo you've known almost all about me... Yes I am
still single and searching..." daga haka yyi shiru ya kalleta yana murmushi yace
"Do you mind telling me about ur self" shiru tayi da farko, can a hankali tace
"Sunana Fatima Abubakar amma ana kirana Imaan" ta kallesa don a hankali yake
driving din kasancewar bbu motoci sosai titin, ya gyada mata kai alamar yana ji,
yana murmushi, murya can kasa tace "I am the only child of my parent" Da mamaki ya
dinga kallonta, ta sunkuyar da kanta tace "I am In the same class with Mariya both
School and Islamiyya, muna xaune tare da Daddy na da Ammi, with my paternal
grandmum, and my Uncle with his family, i mean my father's senior brother" Sadeeq
ya gyada kai a hankali yace "That's nyc, Allah maki albarka ya sa ki xamo the Apple
of ur parent eyes" Murmushi tayi murya can kasa tace "Ameen" ganin sai tafiya yake
ta bude manyan idonta tace "To ai baka san inda xaka kai ni ba" ya kalleta ta
madubi yace "Kin manta ranan da Antynmu ta sa na ajiye ki gida kenan?" Ta wara ido
tace "ohh na tuna" ya d'an yi murmushi, suna kusa layin yace "Toh baki fada min
samarin ki nawa ba?" Ta xaro ido tace "Samari kuma?" Yace "Yeah" tace "Tabb, ni
bani da Samari" yace "Sai dai frnds kenan" ta turo baki, yayi murmushi yana
kallonta, tace "A school bani da male frnds, a islamiyya ma haka, a gida ne kawai"
yace "Toh su waye?" Tace "Cousins dina" yace "Really?" Ta gyada masa kai, yace "Can
I know them" murmushi tayi tace "Ya Yusuf ne sai yaya.. Ohh yaya yusuf ne ma kadai,
mun daina shiri da yaya yanxu" yace "Can I know the Yusuf?" Tace "Yea he is my
cousin, an engineer yana aiki a nan yana yi a Kano yana yi a zaria" yana parking
kofar gidan su yace "Shi dayan fa?" Tace "Yaya?" Ya gyada mata kai tace "Shi wani
lkcn yana Abuja wani lkcn yana nan, yanxu yana nan" Sadeeq yace "Maa sha Allah, to
me yasa bakwa shiri?" Tace "Yanxu ya fiye mugunta baya kuma kulani kamar da" tana
magana ta bude kofar motar tace "Nagode" ba karamin daure ransa yyi ba yace "Wait
ara min fone naki pls, I want to confirm ko Muhsin ya tafi da nawa cos I can't find
it here" komawa tayi ta xauna ta basa wayarta ya amsa ya gama danne dannensa sai ga
ring din wayarsa, ya mayar mata yace "ohhh thanks yana nan ashe" ta fita motar tace
"Thanks" yayi murmushin da ya bayana dimples dinsa yace "You are welcm" Xaune ta ga
Mujaheed gun mai kiosk a kofar gidan yana kallonta, duk da yanda gabanta ya fadi ta
dauke kai da sauri ta wuce cikin gida ta rufe gate.

*I want to use this medium to bring this to the notice of my Fans, akwai wani
namiji mai amfani da information dina gaba daya both Facebook and WhatsApp, a lot
suna chatting da shi a tunaninsu ni ce, to bani bace ba wllh, masu nemana Facebook
idan sun yi searching xa su ga account biyu iri daya, to ni nawa account din daga
followers kadai ma mutum xai gane it's real me bcos the followers are much, idan
mutum ya duba post na timeline dina ma xai gane account dina ne, duk da ko wani
update nayi shi ma sai ya sata yayi, ga lambarsa kamar haka masu chatting da shi ta
WhatsApp 09031263639.... Billah namiji ne kuyi ta kanku, har card wasu na tura masa
da sunan xa su siya littafin Imaan to bani bace, da yawa na cewa sun biya Noor
Hayat ban sa su group ba ban basu littafi ba to shi suka ba kudinsu ba ni ba.
Beware fans katon namiji ne yake claiming khaleesat Haiydar kuma ni na bar sa da
fitowar rana da faduwarsa, duk da ban ma yarda shi din Muslmi bane, Allah ya Isar
min, a yanda ya fara a gantale haka xai kare a gantale*

Littafin Imaan is 300 via... Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah

Show ur evidence of payment through my WhatsApp digit... 07087865788, subscribe and


read happily without feeling any guilt.

_Su ma masu editing min novel su sa abinda ban yi niyyar sawa ba, bayan fitar da
shi da suke ban yi complain ba... we shall meet in the hereafter in sha Allah_ 😇

14. Imaan

Mikewa Mujaheed yyi ya bi bayanta, tunda Imaan ta shiga gidan daman take waigen kar
ya biyo ta, ido hudu suka yi da Umma da ta fito tare da wata bakuwa, ta dauke kai
ta ci gaba da tafiyarta da sauri, Mujaheed na ganin Umma dama ya canxa direction
dinsa, Umma na kallon sa tace "Daga ina kake?" Yace "Ina xaune a waje, xan wuce
wajen aiki ne yanxu" Umma ta bi Imaan da kallo sannan ta kara kallon sa, ya d'an
buda ido yace "Umma ni ban gane kallon nan ba, ki tambayi mai kiosk din can tun
daxu nake wajen a xaune wllh" Kawar Umma tace "Yi wucewan ka kaji Muhammad"
Murmushi Mujaheed yyi ya wuce ciki, tafiya suka ci gaba da yi Umma tace "Gani nayi
kamar tare suke da warcan mai laluran da ta wuce yanxu" Hajiya Saude tace "A'a da
xan shigo daxu fa na gansa xaune inda yace maki, to minti na nawa a ciki ko minti
sha biyar fa ban yi ba" Umma ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Da kin san irin k'i
da tsanar da nake ma uwar yarinyar nan har cikin raina ko Hajiya Balaraba, wllh
abun ba kyau, xan iya komai a duniya don ganin na walakantata, yanda nake jin
tsanarta a rai ko kishiyata Amina ban jin ta haka, sai in ki cutar Amina amma ita
xan iya cutar ta, sai ga tsanar har ya shafi wannan figaggiya irin ciwon da ta
haifo duniya, duk na tsane su kamar yanda na tsani mutuwata, bayan na dawo gidan
nan da kyar fa na raba Mujaheed da yarinyar, sai da na tashi tsaye kyamm" Hajiya
Balaraba tace "Ikon Allah to sonta yake shi din?" Umma tace "Auzubillahi kaji wata
magana wai so, ni na haifi Mujaheed na san halinsa, wllh ba so bane kawai shakuwa
ce tsantsa da shisshige masu da yake, sannan yarinyar ta yi mugun sabo da shi, kuma
a da kafin in dawo shi ke tsaye kan bata magunguna da dai abubuwa da ya shafi
lalurorinta, kin san sickler ce sosai...." Hajiya Balaraba tayi dariya tace "Ba fa
a shaidar d'an yau Hajiya, ke kin shiga xuciyarsa ne kika ga ba sonta yake ba?"
Umma tayi wani murmushi tace "Kin san akwai wani abokinsa Ibrahim iyayensa
hamshakan masu kudi ne, shi ma yaron ya jike jagab da naira, da ban yi da gaske ba
wllh ita Imaan din ya so hadawa da yaron wai ya nemeta, ga yaron mai hankali da
nutsuwa, wllh sai da na masa jan ido sosai, don in dai ina raye abun arxiki baxai
taba xuwa inda Aisha da 'yar ta suke ba, baxan bari ba in sha Allah ina nan ina sa
ido in ga wanda xai jajibe yarinyar da gwara babu da ita, kullum fa ana hanyar
asibiti kamar 'yar da aka sama ta mugun hanya, to fa da nayi da gaske da Mujaheed
shine ya hada yaron da kanwarsa Ummi, yanxu ana gama bikin Seeyama xa a fara xancen
na Ummin, Uban yaron fa abokin gwamnan garin nan ne na kut da kut" Hajiya Balaraba
tace "Toh Allah dai ya kyauta" Umma tace "Sannan shi Mujaheed din akwai wata yar
talakawa da yake mutuwar so wai farida, ni a bincike na ma cewa aka yi idan ban
tashi tsaye ba wllh sai ya aureta don yayi mugun kwallafa rai a kanta, baki ga
hidimar da yake mata da iyayenta ba, duk ya talike a kansu har haya na samu labarin
yana biya masu don nasa mutane su sa masa ido a anguwar, in sha Allah na kusa cire
masa yarinyar a ransa gaba daya sai dai idan ba ni ce na haifesa ba, sa'anninsa na
neman 'ya yan masu kudi shi ya buge da neman talauci salon su mallake min shi su
tsiyace shi, iyayen fa matsiyata ne na gaske wllh" Hajiya Balaraba tace "Toh shi
ina ya samota?" Umma tace "Wllh wai ya dawo daga Abuja ranan, kin san wani lkcn
jirgin kasa yake biyowa ta a nan anguwar ya ganta dai dai layinsu wai xata Unguwar
sanusi, shine fa ya rage mata hanya daga nan kuma ta makale masa ina jin, ni dai
ina nan ina kokarin cireta a ransa gaba daya" Hajiya Balaraba tace "Gaskiya kam,
Allah dai ya mana tsari" Umma tace "Ameen" sallama suka yi Umma ta koma ciki. Bude
kofa Imaan tayi ta fito misalin karfe tara na dare don kwashe socks da kananun
kayan da Ammi ta wanke mata a cloth line, da kyar take tafiya don ji take kamar
xaxxabi xai rufeta ga ciwon kai, tun bayan Isha Mujaheed ke xaune kan farin kujera
ta wajen parking space dinsu, yana jin fitowarta kuwa ya mike ya tsaya kusa da wani
flower dake opposite cloth line din, bbu wuta gaba daya a wajen hakan ya ba Imaan
mamaki sai tayi tunanin mutuwa bulb din yayi, nan ko shi ya cire bayan ya dawo
masallaci, sai da ya jira ta fara kwashe kayan nata sannan ya cafkota ta baya,
yasan next action dinta hakan yasa ya rufe bakinta da sauri, tayi mugun tsorata
wanda hakan yasa ta fara numfashi da sauri, yayi freeing bakinta yana kallonta don
gaba daya ya ma mance da laluran nata, ya dukar da ita da sauri yace "Ke relax now,
nine fa, stay still and relax" kasa yin hakan tayi babu bata lkci kuma Asthma dinta
ya tashi a wajen, daga ta yayi ya shiga apartment dinsu da ita, Ammi ta mike tana
kallonsu, ya xaunar da ita kasa, Ammi ta wuce dakinta ta dauko inhaler dinta ta
mika masa ya amsa ya bude cap din ya kai mata baki, sai da Ammi ta ga numfashinta
ya fara dawowa steady sannan ta juya ta wuce bedroom dinta. Kwanciya Imaan ke son
yi ya dagota yana kallonta yace "Ina ke maki ciwo" Hawaye cike idonta ta nuna masa
kafarta, yace "Kin sha magani?" Ta girgixa masa kai, yace "Ina magungunan?" Ta nuna
masa bedroom dinta, dagata yayi suka wuce dakin nata, ya dau magungunan ya bude su
sannan ya fita xuwa kitchen ya dauko ruwan gora da glass cup ya koma dakin, bata
maganin yayi ta karba ta sha, ya mike ya dauko na tube da take shafawa a kafanta da
bayanta, dawowa yayi kan gadon ya durkusa kusa da ita ya daga rigar baccin jikinta
xuwa thigh dinta, ta bude ido tana kallonsa, duk ta wani langwabe tana sauke
numfashi a hankali, shafa mata man xafin ya shiga yi, kamar xata yi kuka murya can
kasa tace "Wayyo Yaya yana min ciwo" hararanta yyi bai dai ce komai ba, ta runtse
ido ta kama hannunsa tace "Ni wllh ciwo yake min ka min a hankali" Buge mata hannun
yyi ta janye da sauri, haka ta dinga yarfe hannu har ya shafe mata maganin daga
thigh har fararen toes dinta, gaba daya jikinta ya dau xafi wanda at anytime
xaxxabi zae iya rufeta, a hankali tace "Yaya saura bayan" yana kulle tube din yace
"Baxan yi ba" da kyar ta mike xaune ta sauke rigan jikinta xuwa waist dinta ta koma
tayi rub da ciki, yace "Ki shafa da kanki baxan shafa ba" a hankali tace "Baxan iya
ba ae, don Allah ka shafa min" da kamar baxai shafa ba sai kuma ya bude tube din ya
matso methylated cream din ya fara shafa mata a bayan a hankali, lumshe ido tayi
cikin sanyin murya tace "Yaya kai na ciwo yake min sosai, kamar xaxxabi xan yi" ya
hade rai yace "Ina kika tafi daxu?" Ta bude ido da sauri tace "Gidan Gwaggwo naje"
yace "Waye ya ajiye ki a mota?" Ta xaro ido sai kuma ta turo baki bata san duk yana
kallonta ba, yace "Ba tambayar ki nake ba" kamar xata yi kuka murya can ciki tace
"Ya Muhsin ne fa" mintsilinta yyi a bayanta yace "Ni xa ki ma karya?" Ta yi wani
kara ta mike xaune da sauri tana shafa wajen, ganin kallon da yake mata ta xaro ido
tayi wani karan ta koma tayi rub da ciki tace "Wayyo bana so yaya" yace "Nace wa ya
ajiye ki daxu?" Ta rufe idonta tace "Ya Muhsin" yace "You are still lying koh?
Wannan yayi kama da motar Muhsin?" Ta turo baki tace "Ya canxa mota" yace "Ohk,
idan kika bari na fita dakin nan baki gaya min ko waye ba, this case will pend har
ki gama langwabe langwaben ki kuma I promise i will deal with you" kamar xata yi
kuka tace "Yaya abokin ya Muhsin ne fa, tare muke da shi sai ya sauka a wani anguwa
xai yi wani abu shine abokin ya ajiye ni shi, ka kira ya Muhsin din ma ka tambayesa
wllh" yana gyada kai yace "ke yanxu kin girma baki da aiki sai shiga motar karti
suna ajiye ki kofar gida koh?" kallonsa take kamar xata fashe da kuka ya mike ya
ajiye tube din xai fita, a hankali tace "Yaya baka gama shafawa ba" wani shegen
kallo ya mata ya fice dakin. A stairs ya hadu da Umma xata sauko parlor, ya jira ta
wuce tana kallonsa tace "Mura kake nake jin kamshin aboniki?" Ya wara ido yace "Oh,
eh daxu naji kamar xan yi muran shine fa na shafa a kirji" Umma tace "Toh Allah ya
sauwake" daga haka ta wuce shi ma ya wuce sama ya shiga dakinsa, gun injections
dinsa ya nufa ya dau pcm da syringe yasa a aljihunsa sannan ya sakko parlor, Umma
tace "Ga fa abincin ka can ka bari yana galallawa a dinning" Mujaheed yace "Ohk xan
ci Umma" tace "Yanxu ina xa ka?" Yace "Card xan amso waje" daga haka ya fita, sanin
halin Ummar tasa, hakan yasa ya fita gidan gaba daya, bayan kusan minti bakwai ya
dawo ciki ya nufi part din su Imaan, Ammi na kitchen tana wanke wanke jin an bude
kofar parlor ta leko suna hada ido yace "Allura na dauka na pcm naga tana xaxxabi"
yana magana yana ciro alluran a aljihu Ammi bata tanka sa ba ta koma kitchen
Bedroom dinta ya bude ya shiga ya sameta yanda ya bar ta har ta fara bacci, ya isa
kusa da ita ya xauna bakin gadon ya fara hada alluran yana gamawa ya juya yana
kallonta yace "Kee" tayi nisa baccin dama gata mai nauyin bacci, sanin haka ya ja
hancinta yace "Imaan" bude ido tayi da kyar xata kara rufe idon yace "Baxa ki tashi
ba?" A hankali tace "Yaya me xan yi kuma" Ta bude ido sosai ganin abinda ke
hannunsa ta mike xaune da sauri tana jan rigar ta xuwa chest dinta tace "Yaya wa
xaka ma alluran?" Yace "Gado" kamar xata yi kuka tace "Ka mance na sha magani ne"
yace "Kar ki bata min lkci my frnd" ta fashe da kuka tace "Na shiga uku Ammi ni ban
ce a min allura ba" Tana fadin haka xata mike ya fixgota ya kwantar da ita ya daga
rigar jikinta ya mata alluran ya mike ya fice daga dakin, sai da Ammi ta shigo
dakin tana mata mugun kallo sannan ta hakura da kukan ta koma ta kwanta nan da nan
kuma bacci ya dauketa. Imaan na dawowa schl ranan litinin taga calls har biyu da ta
yi missing, bayan ta idar da sllh tana xaune kan darduman ta dau wayar tayi dialing
number din, har ya katse ba a dauka ba, few seconds later sai ga call din ya shigo
wayarta, dagawa tayi ta kai kunne, sallama aka yi daga daya bangaren cikin cool
voice, tayi shiru da farko, can kuma tace "Waye ne?" Yace "Baki amsa sallama ne?"
Tace "Not a must in amsa a fili, who are you" yayi murmushi yace "Ohk then, how are
you?" Tace "I
asked who are you first?" Yace "Tsoro kike ji?" Tace "Sorry i think it's a wrong
call" yace "Why do you say so?" Tace "Because without any doubt I know it's only my
dad, mum.... and very few dat have my contact" yace "Ohk... Muhsin ya sa in kira
in ji ko kin shiga gida lafiya" ta d'an bude ido da mamaki amma ta kasa cewa komai,
yyi murmushi a hankali yace "How are you Imaan?" Murya can kasa tace "Alhmdllh"
yace "I guess yanxu kika dawo schl?" Tace "Sure" yace "Alryt, sai islamiyya ko?"
Tace "Eh" yace "Ohk then Allah ya kiyaye hanya, amma tare xa ku yi sauka da su
Mariya?" Tace "In sha Allah" yace "Saura wata nawa?" Tace "Two months" yace "Maa
sha Allah, we will talk later kar kiyi latti" tace "Sai anjima" daga haka ta katse
wayar ta mike ta fara shirin Islamiyya. Bayan Magrib Mujaheed na xaune parlon
Abbansa da duk yan gidan, Yusuf ma dake xaune wayarsa kawai yake ta dannawa a
parlon, Anty duk ta fiddo ankon bikin Seeyama suna nuna ma Abba, Umma dai na xaune
ta hade rai don gani take kamar Anty shishshigi kawai take mata, Anty tace "Toh
Abba ga kaya nan, gaba daya kala uku ne" Mujaheed yace "Toh duka kala ukun xa su
yi?" Anty tace "Ehh ko kana da damuwa da hakan??" murmushi yyi bai ce komai ba,
Yusuf ya daga kai yace "Amma fa Anty yayi yawa sai kace su ne..." Mugun kallon da
mahaifiyar tasa tayi masa yasa yyi shiru ya ci gaba da danna wayarsa, Abba yace
"Kice expenses ne ba na wasa ba, to da wanne ku ke son mutum ya ji, ina laifin ma
kala biyu?" Umma tace "Haba Alhaji, abu dai na rana daya lkci daya, ni fa da cewa
ma nayi kala hudu hudu Amina tace a bar shi a kala uku kawai" Abba ya gyada kai bai
dai ce komai ba, Anty tace "Idan ma baxa ka siya masu ba ga yayyinsu sai su masu"
Umma tace "Atoh dai" Yusuf yace "Mu dai sai dai muyi masu kala bibbiyu" Anty tace
"Toh ka rike kudin ka" Dariya yayi yace "Shikenan ni sai in ma Rahma da Ummi M.A
yayi maku sannan yayi ma Maimoon" Umma tace "Sai kayi ma Kakarku ko kala biyu ne
ita ma, shikenan it's settled" Yusuf ya dinga kallon Umma bai ce komai ba, Abba
yace "Toh mamana fa?" Anty ta buda ido tace "Ai kuwa Imaan... kaga na ma mance
wllh, shikenan sai Mujaheed yayi mata kaga hakan ma is settled" Abba yace "Ehh sai
Mujaheed yayi mata" Umma ta yi ma Anty wani kallo tace "Wani Mujaheed din, shi
Yusuf me ya hanasa yi mata?" Anty tace "Saboda kince yayi ma Kakarsu, kinga
Mujaheed sai yayi ma Imaan" A fusace Umma tace "Toh an ruguje wannan tsarin kowa
tayi ma 'yar ta, Inna kuma Alhaji ko baban ita Imaan din su yi mata" Abba yace "Ba
tsarin da ya ruguje Hajiya, Mujaheed yayi ma ke, Amina... da maimoon sai Imaan,
Yusuf kuma yayi ma Ummi, Rahma da Inna, kuma a cire ma imaan nata a kai mata yanxun
nan" Anty ta cire ma Imaan kala uku, Abba ya kalli Mujaheed yace "Dauka ka kai
mata" Mujaheed ya kalli Umma da ranta idan yayi dubu a lkcn ya baci, Anty tace "A'a
jira, yi min transfer din kudin Imaan din yanxu tukun, sauran ko daga baya ne sai
ka yi" Mujaheed ya kasa cewa komai, Anty tace "Malam ka min shiru ina maka magana
m" ya dau wayarsa gabansa na faduwa sai dai bai yadda ya kalli Umma da ko ba a
fada masa ba yasan kallonsa take, ya gama danne dannensa yace "Anty ina jin ba
network...." Ta mike ta isa kusa da shi ta amshi wayar tace "Baxa ka raina min
hankali ba" sanin Gtb yake amfani da lkci daya ta danna transfer code dinsu tayi
komai ta sa har account number dinta bayan ta sa amount sannan ta mika masa tace
"Sa min pin" Karba yyi ya sa pin din ta amshe wayar, duk ya kasa kallon Umma, sai
da Anty ta ga transfer din yayi sannan ta basa wayarsa ta koma ta xauna, lkci daya
aka turo masa debit ya bude ya ga 30k ta yi transfer, Abba yace "Toh ka dau kayan
ka kai mata sai kace mata kai ka siya mata" Kasa tashi yayi, Abba ya hade rai yace
"Are you stupid ina maka magana kana xaune, wato abinda kake nufi shine baka jin
maganar kowa gidan nan sai na uwar ka koh, ina fa lura da kai kuma nake sharewa"
Tashi Mujaheed yayi ya dau ledan kayan ya nufi kofa, Umma ta mike fuu ta wuce sama,
Anty tayi wani murmushi a ranta tace "da sauki ai tunda ba bin sa xa ki yi ba" A
hankali Mujaheed ya murda kofar apartment dinsu Imaan ya shiga da sallama murya can
kasa, Imaan ce durkushe parlon da yar ves sai skirt iya cinya, nose mask na
hancinta tana goge gogen kayan da ke daukan k'ura a parlon, ta mike ta cire abun
bakinta tana kallonsa, Ammi ta fito parlor jin an shigo, yyi kasa da kai ya ajiye
ledan hannunsa kan kujera yace "Abba yace a kawo mata" daga haka ya juya ya fita ya
kulle kofar, Imaan xata bude ledan Ammi ta mata tsawa, dakatawa tayi da sauri,
fuska daure Ammi tace "Kina ganin ya shigo amma kika ki wucewa daki da wannan
shegun kayan jikin ki koh, tun daxu nake maki magana ki nemi kayan arxiki ki sa ko
don saboda ciwon ki sannan kada wani ya fado amma kin maida ni mahaukaciya, ke kam
wace irin yarinya ce Allah ya bani, in ji hankalin ki ya kwanta da ya shigo ya
ganki a haka?" Imaan sai kallonta take da mamaki tace "Ammi yaya ne fa" Bude baki
Ammi tayi tana kallonta, can tace "Sai aka yi ya don shi ne?" Tace "Toh Ammi shi ne
fa ba wani ba ya shigo, dama dai ya Yusuf ne kin san baxan tsaya haka ba" Ammi ta
kasa daina mata kallon mamaki tace "Shi yayan muharramin ki ne Imaan?" Imaan ta
xaro ido tace "Ammi yaya fa har wanka ya taba min ina karama, kuma da ba shi ke sa
min kaya ba ma idan ban sa ba, ni dai bana jin kunyarsa wllh, dama dai yaya Yusuf
ne shi ko dankwali bana tsaya kusa da shi ban sa ba, shi kuma yaya ni xan ma iya
cire kaya a gabansa, toh har yau ba yana shafa min magani a kafana da bayana ba, ko
wajen inna idan yana nan ina....." Ammi taga bude baki fa ba nata bane ta dau daya
daga pillows na kujera ta jefa mata a mugun fusace tace "Ban taba sanin ke
shahararriyar mahaukaciya bace sai yau, wato iskanci yasa kike cewa ya shafa maki
maganin xafi koh, to in sake gani sai na ci uban ku ke da shi, kuma kar ki fasa
cire kaya gabansa tunda ke shashasha ce, sai kace warce bata taba shiga ajin
islamiyya ba wai kina cire kaya gaban namiji da ba muharramin ki ba" Imaan ta nufi
daki kamar xata yi kuka tace "Ni fa ba yanxu nake cewa ba Ammi, da da nake nufi,
kuma naga ai yayana ne shi tunda ba ni da wani yayan" ganin Ammi ta yo kanta ta
shige dakinta da gudu ta sa makulli tana turo baki kamar xata fashe da kuka.

15..

*Imaan* is not free subscribe and read hankali kwanceIt's 300 via Fcmb 3276052019
Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included
in the payment group

Ammi ce xaune parlon inna ta sanadin aikawa da innar tayi a kirata, ta fi minti sha
biyar parlon amma inna bata ce da ita komai ba sai goge gogen kayan kallonta take,
Ammi ta bukaci ta yi mata goge gogen inna tace ta bar shi, bayan wani minti biyar
din Ammi tace "Inna na daura girki ne wllh...." Inna tace "Kin daura girki?
Tabdi... Toh ita warcan 'yar da kika bari meye amfaninta da baxata dinga duba maki
girkin ba, ina ce yau alhamis babu islamiyya" Ammi tace "Barci na baro ta tana yi"
Inna ta tabe baki tace "A haka dai kullum, Allah dai ya mana tsari ya fidda d'a na
kunya, amma gaskiya ni tunda nake tafasasshen ruwan Imaan bai taba shiga baki na
ba, toh uwar me xata je ta dafa ma mijin ma idan tayi aure, kullum ayi ta laka ma
yarinya ciwo ana daure mata kugu wai bata da lafiya, to ni dai ba ruwana ba wanda
xai xagi d'a na, idan ma an samu to Allah ya isa" Ammi dai bata ce mata komai ba,
Inna ta xauna tace "Tana yar yarinya da ita tayi ta langwabewa, tana abu salalo
salalo, ana ma ciwo sharri to ni dai ba ruwana, dama magana nake son yi mama ke da
Amina, to Aminar bata ga damar xuwa ba har yanxu, tana can sai ta mula ta mulmule
sai kace xata ma Maryam haka....." Inna bata rufe baki ba Anty ta shigo da sallama,
Tace "Sannu inna..." Inna ta tsuke fuska tace "Yauwa" Anty ta xauna tana kallon
Ammi tace "Uwar Imaan kwana biyu" Ammi tayi murmushi tace "Ae kam duk mun buya"
Mikewa inna tayi ta ci gaba da goge gogenta, Anty tace "Goge goge kike Inna" a
fusace Inna tace "Toh baxan yi goge goge ba in mutu cikin wari yar nan, ko ke baki
ga ko ina tsaf ba, ko hancin ki bai ji kamshin dake tashi parlon ba, wllh tun safe
ban xauna ba ina ta aiki baki ji bayana ba kamar ya balle in huta, ke hatta
simintin da kika tako kika shigo nan sai da na goge sa fess yau, ai kazanta bata da
kyau, ni dai in sha Allahu cikin kamshi xan mutu ba ruwana, kuma tirr da kazami, ai
ina lura duk cikin jikokina babu wanda ya dauko tsafta ta sai Mujaheed" Anty da
Ammi dai sai kallonta suke, ta xauna tace "Yo Mujaheed mana, shi kadai ne Allah ya
ceta ta wannan fannin, duk inda kazanta take ma shi bai xuwa, kullum tsaf xaka
gansa abunsa, baxa ku yarda da xance na ba sai kun shiga dakinsa, ko don raino na
ne shi din oho, ga shegen kyankyamin tsiya.... shi kuma wannan katon Isuhu ba shi
da aiki sai saka gogaggun kaya da fesa turare amma duk kika basa abinci to wllh a
nan xai bar maki kwanon ya tsallake ya wuce, to ina tsafta a nan, ai ta nan ake
gane kazami, dakinsa kuwa karkari ya kakka6e gadon ya kara gaba, ita ko wannan mai
laluran Imaan ga dai gashi har gashi amma ba gyara malam, kullum gashin nan a kume
xa ki gansa sai ta fi sati da sattuka bata sharce ba, to ina tsafta a nan, da an
mata magana sai tace xafi yake mata, ai duk mace ta gashi ake gane kazantar ta ni
kwarkwata ma nake guje mata wllh, sannan babu tattali kullum sai ta bar min
adikonta a nan idan ta xo, ga su can na tara yafi kala dari yanxu, Ko uwarta xan ci
da su oho, ni ce ma Bukar xan yi ma ya daina siya mata turmin atamfa gwara a siya
falle a mata riga da sket banda dankwali, Atoh shi kenan yayi ta asaran dukiya
atamfa dai masu tsada amma tayi ta walakanta adiko, Maimoon kuwa dama kayan datti
sai ta tara ta tara taga babu sarki sai Allah, babu wanda xata saka sannan xata
kwashesu ta hau wanki duk su cika gida, to ina mace a nan, babu kazantar da ya fi
wannan wllh, sauran yan matan kuwa ni wani lkcn ma sai in ji kamar wari suke
wllh...." Murmushi Anty tayi, Inna tace "Wallahi ba batun dariya ba, to dai kowa
tasa ta fishshesa a gidan nan ba ruwana da kowa ta kaina nake, yanxu dai abinda
yasa na kira ku ba wani abu bane...." sai kuma ta yi shiru, su dai kallonta kawai
suke, tayi kasa da murya tace "Ku lissafa min daga ranan asabar xuwa yau kwana nawa
kenan" Ammi tace kwana shidda" Inna tace "Toh yau kwana shidda rabon Mujaheed da
Imaan su xo min nan su gaisheni, yanxu fisabillahi daga sun min ba dai dai ba na
nuna bacin raina sai su kullace ni, meye laifina don nace ban yarda shanye min fura
da suka yi ba" Anty ta bude baki tace "Gaskiya basu kyauta ba har kwana shidda"
Inna ta fara matsar kwalla tace "Ni fitinata har ya kai Mujaheed ya ki takowa nan
yau har kwana shidda, daga gyara kayanka sai ya xamo sauke mu raba? Ke Amina na
kira ki ne a matsayin uwarsa don ba ruwana da wancan katuwar da ta haifesa, ke kuma
Aisha saboda Imaan yar ki ce" Anty tace "Amma Inna ca nake kince kada su sake xuwa
maki idan ba haka ba xaki bar gidan" Inna xaro ido tace "Oh oh Allah kaji wata
magana don Allah, to Amina idan na bar gidan nan ina da gidan uban da xanje in
tsugunna, duk ba xance bane dai da tsorata mutane, bacin rai ai babu abinda bai
sawa, don nace kada su sake xuwa kowa yasan fada kawai nayi, me suka min da xan
hanasu xuwa nan?? Allah ya tsine ma fura da nonon in dai saboda shi xan kori
jikokina, meye kuma wani fura da nono kamar mayyar bafillatana" Anty na danne
dariyar ta tace "Ahh to gaskiya basu kyauta ba" Inna ta kalli Ammi tace "Ke kuma
Aisha kinyi shiru kina kallona ko baki da abun cewa ne?" Ammi tace "Kiyi hakuri
Inna, ina komawa xan sameta" Anty tace "Nima Mujaheed na dawowa aiki xan samesa In
sha Allah" Inna ta gyara xama tace "Toh, sai ku ji dalilin da yasa xa su min haka
su kaurace min, yanxu duk saukin kai na su basa gani, ni ba mafadaciya ba, ni ba
fitinanna ba, ni ba mai sa ido ba, ni ba mai kwadayi ba, ni ba mai mita ba, toh
meye xasu wani dauke kafa daga magana dai ta fahimta, to sai dai idan Ahmadu ne ya
hure masu kunne ya masu hudubar tsiya, banda haka su har wani wayo garesu da xasu
dauke kafa daga xuwa inda nake" Anty ta fara dariya, Ammi kam murmushi kawai tayi,
Inna tace "Aa don Allah ku duba xancen da kyau, wllh xuge su aka yi, kuma ba kowa
xai yi hakan ba sai mutumin nan Ahmadu don Bukar baya haka shi, ni gaskiya na ma
daina sa Ahmadu a lamarina daga yanxu tunda tsanata yake cusa ma yaran a rai,
anjima kuma xan sa kira min Bukar yaji abinda ake ciki, kwana daidai har shidda fa"
Ammi ta mike tace "Ki yi hakuri Inna ina komawa xan mata magana bari in je in duba
girki na" Inna tace "ke ta girki ma kike ga maganar al'ajabi ana yi a nan Ahmadu ya
xuge yara, haba don Allah abinci dai abinci dai kamar ana yunwa Amina" Ammi ta nufi
kofa tace "Toh sai dai anjima inna" Inna tace "Toh Allah bamu alkhairi, ki dai
tsitsiyeta kiji dalili" fita Ammi tayi parlon bayan ta ma Anty sallama. Inna ta
tabe baki tace "Kinga bafillatanin mutum, kinga agwai?? Wllh ki ji tsoronsa, barin
idan kika ga ya fiye shiru shiru banda haka ki ga fa babu abun kirki da tace har ta
bar parlon nan, Bukar dai na ganin boni, mata kamar kurma, ni kwanciyar hankali na
ma Imaan bata dauko halinta ba, Imaan xata iya kwatar kanta a ko ina da bakinta,
tun daga ranan da na karanta mata ta daina gaida Uwar Mujaheed gashi har yau bata
gaisheta, gashi har Ahmadu da Bukar sun gaji sun kyaleta, kusan ma Imaan ce kadai
ta dau halina a gidan nan wlh, banda haka ya xata dinga gaida katuwar mata bata
amsa mata, da ta fi ta iskanci kuwa kinga ta daina gaishetan gaba daya" Anty dai
dariya kawai take, Inna tace "Toh ni dai ki taimake ni Amina ki rufa min asiri,
Mujaheed na dawowa ki titsiyesa a daki kiji me na masa da ya dauke kafa a nan" Anty
tace "In sha Allah Inna, bari in je nasan ma ya dawo yanxu tunda biyar har ta yi"
Inna tace "To yi maxa" tashi Anty tayi ta mata sallama ta fita inna ta mike ta ci
gaba da goge gogenta tana cewa "Ahmadu dai ya lalace, da dai ba haka yake ba"
Dariya sosai Imaan ta dinga yi bayan Ammi ta bata sakon inna, tayi mai isarta ta
mike daga kwancen da take tace "Ba Inda
xanje Ammi, tun Sunday kinji ta kai karana gun Abba, to haka ya fi, ita da bakinta
tace wannan time din ba wasa take ba Abba ya ja mana kunne sosai don muna xuwa part
dinta xata tsallake ta gudu ta bar gidan" Ammi tace "Toh nace bayan magrib kije ki
gaisheta, kina gaidata ki juyo" Imaan ta fashe da kuka ba hawaye tace "Ammi don
Allah ni baxan je ba, ina xuwa xata ce na mata wani abu" Ammi ta mike tace "Toh
idan na baki abincin ki kai mata kar ki kai" daga haka Ammi ta bar parlon, Imaan ta
fara kukan gaske, har ranta bata son xuwa gun inna. Anty na gama girkin dinner dab
da magrib ta fito kitchen, ganin Mujaheed xai fita masallaci tace "Dr idan ka dawo
mosque ka sameni bedroom" Yace "Toh" daga haka ya fita parlon, tare suka dawo
masallacin da Yusuf, bayan sun haura sama Mujaheed ya shiga dakin Anty, Yusuf ya
shiga dakinsa, Anty na xaune kan darduma ta shafe addu'o'in da take ta mike ta
dauke pray mat din ta linke tana kallonsa tace "Toh ka tsaya min kamar soja a kai
ka xauna" murmushi yayi yana shafa kansa ya xauna gefen gadon, tace "Yanxu M.A idan
kowa ya guji inna kai ma sai ka gujeta" ya d'an buda ido yace "Inna kuma?" Tace "Eh
mana" yace "Ban gane ba Anty" tace "Kirana tayi daxu wai kwana shidda rabon da kaje
bangarenta kai da Imaan" Mujaheed yyi murmushi bai ce komai ba, Anty tace "Toh ka
gama murmushin ka tashi ka ta fi ka gaisheta" mikewa yayi yace "Wa?? Ai har abada
ni da xuwa apartment dinta, beside irin warning da Abba ya min ma is not funny don
haka..." Anty ta karasa masa tace "Baxa kaje ba koh?" Yace "Allah Anty kinga kwana
biyu shiru bata ce an mata komai ba hakan bai fi ba?" Anty tace "Toh ni dai nace ka
tashi ka je" ya mike xaune yace "Anty ki bari kawai ba inda xanje" Anty tace "Wato
ban isa da kai ba kenan, idan Hajiya ce tace kaje xaka ce mata ba xa ka ba?" Yayi
murmushi yace "Anty Hajiyan ma hanani xuwa bangaren tayi gaba daya" Anty tace "Toh
tashi ka fita ka ban waje" ya marairaice mata yace "Wllh Anty ina iya xuwa yanxu
tace nayi mata wani abun" Anty ta hade rai tace "Cewa nayi ka gaisheta kawai ka
juyo" Ya lumshe ido ya bude yace "Wllh da ba don ke bace ni ba inda xanje Anty"
Anty tace "Naji din tashi ka fita, idan ka dawo kuma ka xo ka gaya min, gobe da
safe kuma xan je in ji ko ka je" Murmushi yyi ya mike ya fita dakin. Tun da Imaan
ta fito parlonsu rike da warmer din abinci take tsaye jikin wani flower taki
tafiya, kiris ya rage ta fashe Inda take tsaye, daga nisa ta hango Mujaheed yana
tahowa waya kare kunnensa, labewa tayi ta koma bayan flower din ta tsaya da sauri,
sai da ya d'an wuce inda take ta fito tayi wani kara a bayansa, still yyi na few
seconds, ta fashe da dariya ya juya yana kallonta, ya wani hade rai yace "Kee" Ta
wara manyan idonta tace "Toh ai baka ji tsoron ba ma" Wani kallo ya dinga mata, ta
turo baki ta wuce sa, sai da ya ga tayi nisa sannan ya bi bayan ta, tsaye ya ganta
tana lekan parlon inna don kofar ba duka aka rufe ba, ya cire takalmansa outside
the balcony yayi tiptoeing har bayan ta, fingers dinsa ya kai gefen cikinta yayi
tingling dinta, ihu ta fasa ta sake abincin hannunta, tuni ya janyeta wajen don
gaba daya tuwo da miyar dake warmer din ya tarwatse a kasa, ta xaro ido a rikice
tace "Innalillahi yaya ka xubar" daga cikin parlor inna ta dinga cewa "Me aka
6arar??" Ummi ta bude kofar, Imaan dai sai kallon abincin take kamar xata yi kuka,
Inna ta mike ta taho wajen tace "Meye hakan?" Kamar xata yi kuka tace "Yaya ne ya
xubar da abincin da na kawo maki" Inna tace "Toh sai ki kwashe ki mayar mata ta
canxa min wani ba ruwana" Imaan ta shige parlon ta xauna ta rungume hannu tace
"Salon Ammi ta doke ni ba ga abinci nan Ummi ta kawo maki ba" Inna tace "Aa wllh
kinga ina cin wani abu banda tuwo, Ummi maxa kwashe ki kai ma Aisha kice yar ta ta
xubar ta xubo min wani" Ummi tace "Mu ma fa tuwo muka yi" A fusace Inna tace "To ni
ina ruwana da tuwon ku? Ku tuwon ku har wani dadi garesa miya kamar an wanke kai,
ki min abinda nace kada ran kowa ya baci a gidan nan" Ummi ta mike a fusace ta
kwashe tuwon ta mayar cikin warmer din, Imaan tace "Dama kice yaya ne ya xubar na
ni ba" Inna tace "Haba dai, dama ina xa ki iya xubar da wannan abincin ai sai dai
shi" Tsallake miyar Mujaheed yyi ya shiga parlon ya xauna, Ummi ta tafi da abincin
da ta kwashe part din su Imaan, gyaran wajen inna ta dinga yi duk suna xaune, bata
gama ba Ummi ta dawo da wani abincin ta ajiye ma inna tace "Imaan Ammin ki tace xa
ki dawo ki sameta" Inna tace "Sai me xai faruwa idan ta sameta, bakin cikin kara
min abinci take komai, ina laifin ma tace xata gamu da Mujaheed din, Imaan ce ta
wani san xubar da abincin mutane, bata ta6a ba tunda take, lafiya take kawo min
abinci ta koma to yau da yake ta hadu da wnn mutumi a hanya" tana kai wa nan ta
shiga parlon tana kallon Ummi tace "Don Allah ki rufa min asiri ki taimakeni ki
karasa goge wajen baki ji bayana ba kamar xae cire" Ummi tace "Toh su da suka
xubar...." Kallon da Mujaheed ke mata yasa tayi shiru ta mike rai ba dadi ta fita
ta ci gaba da gyaran wajen. Inna ta shiga daki sai ga ta ta fito da bowl na dambun
nama, tace "Tun ranan litinin nake ta ajiya amma ban gan ku ba na nace to ko
lafiya, na ba kowa nasa...." Mujaheed ya amsa yace "Na waye wannan din?" Tace
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

"Na kai da takwara ta" Ya saci kallon Imaan, da sauri Imaan tace "Inna ni dai ki
raba mana da kanki" Mujaheed yace "Toh samo leda sai ki raba mana" komawa daki Inna
ta yi, Mujaheed ya mike kafin Imaan ta ankara har ya fice parlon, kwalo ma inna
kira ta yi, ya saka takalminsa ya kara gaba, inna ta leko parlon tace "Lafiya!"
Imaan ta fara kuka tace "Ya tafi da naman gaba daya" inna tace "Maxa tashi ki bisa
in ya kama ki je parlon Ahmadu ki tafi" Imaan ta mike ta fita parlon, bata son gudu
saboda laluranta, hakan yasa kafin ta iske sa har ya shige part din su, ta goge
hawayen da ya cika idonta a ranta tace "Allah ya isa" daga haka ta wuce apartment
dinsu kawai, Sai da ta tsaya Ammi ta gama fadanta na xubar da abinci da tayi sannan
ta shiga bedroom dinta. Bayan isha tana saka kayan baccinta wayar ta ya fara ring,
duk tunaninta Sadeeq ne don kullum sai ya kira ta da daddare sun gaisa duk da basa
waya mai tsawo iyaka gaisuwa shikenan amma har wani murna take idan ya kirata,
Daddy ta ga ke kiranta, ta daga a hankali tace "Ina yini daddy" yace "Lafiya lau
Mamana, ya gida?" Tace "Alhmdlh ya aiki?" Yace "Da godiya, kina karatu sosai dai
koh?" Tace "Ehh ina yi" yace "Maa sha Allah, daxu kafin magrib inna ta kirani wai
sati daya kenan baki je gaisheta ba, why is that?" Imaan tace "Daddy na fa je yau"
Daddy yace "All those days me ya hanaki xuwa?" Tace "Cewa tayi kar mu sake xuwa ni
da yaya fa" yace "That's because kuna mata rashin kunya ke da shi, wato warning da
na maki kafin in tafi went in vain koh?" Shiru tayi bata ce komai ba, yace "Toh kar
ki sake skipping one day baki je gaisheta ba, idan Ammin ki ce don ta maki fada xa
ki k'i xuwa gaisheta, she is my mother Imaan you have to respect her much, shi ma
Mujaheed na kirasa ban samesa ba ki kai masa waya yanxu" Kamar xata yi kuka tace
"Toh" daga haka ya katse wayarsa, Hijab ta sa har kasa ta fita, Ammi dake parlor
tana kallo ta bi ta da ido, Imaan tace "Daddy yace in kai ma yaya waya" Ammi tace
"Shi me ya samu wayarsa?" Bude hannu tayi alamar bata sani ba, Ammi ta ci gaba da
kallonta, hakan yasa ta nufi kofa ta fita. Babu kowa babban parlon nasu don hatta
kayan kallo ma a kashe suke, ta haura sama ta na kallon direction din dakinsa don
har ta manta rabon da ta je wajen, takawa tayi har bakin kofar sannan ta bude tana
lekan cikin bedroom din, wani sanyayyen kamshi me hade da sanyi ya doki hancinta da
fuskarta, shiga dakin tayi ta kulle kofar, ko ina fes har kan gadon dake dauke da
farin bedsheet, Ko ba a fada mata ba tasan wanka yake jin saukan ruwa da kamshin
sabulu da ya hadu da kamshin dakin, xaro ido tayi tana kallon sketches dinta dake
bangon dakin kusan gudu hudu, tun tana Jss3 tayi drawing din mai kyau coz she is
more than perfect a zane, turo baki tayi ta dau kujeran dake gaban mirror ta kai
jikin bangon ta hau ta dinga cire hard carbon paper din a hankali kar ya yage. Bude
kofar bathroom Mujaheed yyi ya fito da short yana goge gashin kansa da karamin
towel, xaro ido yyi yana kallonta da mamaki, ta juya jin an bude kofa suna hada ido
ta turo baki tace "Yaya daddyna yace in kawo maka waya" Tana magana wayarta da ta
ajiye kan gado ya fara ring, sakkowa tayi da sauri ta dau wayar tace "Ga shi nan ya
kara kira" daga haka ta nufesa ta daga kiran ta kai kunne tace "Daddy ga shi nan"
mika masa wayar tayi ya amsa ya kai kunne hade da sallama, Kamar ance ta juya taga
bowl din dambun naman da ya dauke ajiye a gaban mirror dinsa, yana magana da daddy
amma duk hankalinsa na kanta kuma yana lura da ita, ganin ta nufi gun mirror din ya
fixgota, xaro ido tayi xata yi magana ya rufe bakin, sai ce ma daddy yake toh don
ya kagu ya katse wayar, kamar kuwa daddy ya shiga ransa yace "Shikenan we will talk
tomorrow sae da safe" da sauri yace "Allah ya tashe mu lafiya Abba, mun gode, sae
da safe" daga haka ya katse wayar ya juyota yana mata wani irin kallo yace
"Drawings din da kika cire nake so ki hau kujeran ki maida su yanxu kafin ki fada
min sanda na fara wasa da ke da xaki shigo min daki kai tsaye" ta 6ata fuska tace
"Toh ba waya na kawo maka ba" Jan kunnenta yayi yace "Baxa kiyi knocking idan kinji
ba a amsa ba kiyi wucewar ki" muryar Umma suka ji a corridor tana ma Maimoon masifa
wai ta share datti ta kai bakin kofarta lkci daya kuma tana tambayarta ko Mujaheed
na dakinsa, Maimoon da ta hade rai tace "Yana ciki" Mujaheed ya xaro ido ya ja
Imaan ya bude kofar bathroom dinsa suka shiga ya kulle kofar, dai dai nan kuma Umma
ta shigo dakin tana kiran sunansa, Irin tsoratan da imaan tayi ba a cewa komai,
Mujaheed ya dukar da ita kasan bayin murya can kasa yace "Kee you better relax now
kar in mare ki, ance maki xata shigo nan ne" kai kawai take gyada masa numfashinta
na sama, ya cire Hijab din jikinta yace "Nace maki ba fa shigowa xata yi ba, breath
in and out gently now" jingina take son yi da bango ya jawota jikinsa ya rungumeta
yana shafa bayan ta a hankali to calm her down, tuni Umma ta fice dakin ganin
Mujaheed bai ciki, bayan kusan minti biyar jin tana fitar da numfashin a hankali
kuma a nutse ya dago kanta yana kallonta, hawaye ne makale idonta, ya daure fuska
yace "What?" A hankali ta nuna masa kirjinta, ya mike ya fita bathroom din ya sa
makulli kofar dakin sannan ya dawo ya fito da ita dakin, wajen da yake ajiye drugs
da allura ya bude yana dube dube, can kasa ya hango inhaler dinta da take bari a
dakinsa a da idan ta xo, ya juya ya kalleta ya ga kwanciya tayi kan gadonsa ta
takure waje daya, ya mayar da inhaler din ya mike, ya dau gogaggen jallabiyarsa ya
saka don tuni jikinsa ya bushe, ya feshe jikin sa da turare, ya dau drawings da ta
ciro ya fara maidawa jikin Bangon, Imaan ta mike xaune tana turo baki xata ce masa
don me idonta ya kara sauka kan dambun dake gaban mirror, tashi tayi a hankali har
sannan hannunta na kirjinta ta isa gaban mirror din ta dau bowl din, karan bude
kofar da yaji ya sa ya juya, xata fita da gudu ya bi bayanta da sauri yana cewa "ke
har kin manta abinda ya same ki a bathroom ynxu koh, ba ruwana fa idan...." Tuni ta
fara sauka stairs, sai da ya tabbatar ba kowa corridor sannan ya bi bayan ta da
sauri, amma har ta fita gidan, can ya hangota a durkushe kusa da apartment dinsu,
karasawa yyi kusa da ita a hanxarce, ya durkusa kusa da ita yace "Ba nace kar kiyi
gudu ba..." Dagata yyi ganin Asthman ne ya tashi ya amshi bowl din, ya wuce da ita
cikin apartment dinsu, Ammi ta tabe baki ta mike ta dauko inhaler ta jefa masu, sai
da ya ga numfashinta ya dawo dai dai sannan ya mike ya dau bowl din naman ya ajiye
a kafarta yana mata wani kallo ya fita parlon, a hankali take sauke numfashi ta
bude bowl din ta fara cin naman.

*The book Imaan is not free, it's for sale, you read for free ur cup of coffee*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included


in the payment group.

16.....

Ranan Friday Imaan suka gama exams din first term ss2, suna tsaye tare da Mariya a
bakin gate din makarantar tasu ko wannensu na jiran driver, Ummi da Rahma ko fitowa
cikin schl din ma basu yi ba, Maimoon dai na tare da wata Kawarta a waje ita ma,
Mariya na ganin motar Sadeeq tace "Lahh ya Sadeeq ne ma ashe shi sa ya bata mana
lokaci" Imaan dai bata ce komai ba, tunda yayi parking idonsa ke kan Imaan, suna
had a ido gabanta ya fadi, siblings din sa duk suka shiga motar, Mariya bata taba
sanin Yayan nata na interacting da Imaan ba don Imaan din bata gaya mata ba, Mariya
tace "Mu je ku gaisa da shi, shine ya ta6a ajiye ki gida ko baki gane sa ba" Imaan
ta d'an yi murmushi kawai, Mariya ta kama hannunta suka nufi gun motar, Mariya tace
"Ya Sadeeq frnd dita da ka taba ajiyewa a gida..." Ya cire glass din idonsa Yace
"Yea na gane ta" Imaan ta sauke idonta kasa tace "Ina yini?" yace lafiya lau, fatan
an gama exams lafiya" tace "Alhmdllh" yace "Toh Allah bada result mai kyau" ta daga
kai tana kallonsa tace "Ameen" lallausan murmushi ya sakar mata ta dauke kai da
sauri gabanta na faduwa, yace "Let drop u mana" ta girgixa kai tace "Aa yanxu
driver din mu xai xo" Yace "Ohk then" ta saci kallonsa ya kashe mata ido daya, ta
daga ma Mariya hannu ta juya da sauri ta tafi gun Maimoon, Sadeeq ya tada motar ya
bar wajen, Ya Yusuf ne ya xo daukansu bayan tafiyar su Sadeeq da kusan minti
bakwai, Maimoon na turo baki tace "Ya Yusuf driver din fa?" Yusuf yace "Ya kai su
Umma kasuwa, M.A aka ce ya dauko ku tun daxu ya ki, ni kuma ynxu na dawo aiki"
Maimoon ta kyabe baki tace "Da dai Anty Farida aka ce yaje ya dauko, jiya fa da
yamma har Hayin d'an bushiya muka je daukota taje gidan aunt dinta, baka ga uwar
wahalan da muka sha ba ga hold up sai kusan shidda da rabi muka dawo gida" Yusuf
yace "Au suna tare har yanxu kenan?" Maimoon tace "Tab, sosai ma, gobe xata koma
schl sai kaga tulin shopping da yayi mata" Yusuf ya sake baki yana kallonta,
Maimoon ta kyalkyale da dariya tace "Amma fa wllh ya Yusuf kar ka ce masa komai,
dama yace kar in fadawa kowa" Yusuf yace "Ae ko kin fada ma kowa tunda kika fada
gaban Imaan da Ummi" Imaan ta hade rai tana kallonsa ta madubi tace "Ya Yousuf
kamar ya?" Ya wara ido yace "Ke sai ki kwasa ki kai ma inna, Ummi kuma ta gaya ma
Umma, saukin abun dai idan magana ya fita an san it's either Imaan or Ummi sae M.A
ya ji dadin jibgarku da kyau" Imaan ta xumburo baki tace "Naji dai" Ummi kuwa yi
tayi kamar bata ji sa ba dama, suna isa gida Maimoon tace "Dama ya Yusuf ka ja masu
kunne ba ruwana idan suka fada ma kowa" wani kallo Imaan ta watsa mata ta fice daga
cikin motar tana turo baki ta kara gaba. Satin da aka shiga banda shirye shiryen
bikin Seeyamah babu abinda ake a gidan, tun ranan lahadi yan uwa suka fara xuwa
daga nesa gida ya fara cika da jama'a, kowa ya xama busy a gidan barin Umma da
Anty, Ammi kam baya baya ta dinga yi, tun a ranan lahadin dama ta kai nata
gudunmawarta na tsadaddun manyan bedsheets biyu, da set din food warmer shi ma biyu
masu kyau sosai, a walakance Umma ta dubi kayan aka bar su a nan parlorn. Ranan
laraba Abba ya ba su Maimoon kudin gyaran gashi da lalli a kai su Saloon, Har xa su
fita ya dakatar da su ya ciro wani dubu biyar din yace "Na mance ban bada na mamana
ba, gashi nan ta shirya ita ma ta je" Fita suka yi su hudu Ummi na cewa su yi
wucewansu kawai don Imaan ba xuwa xata yi ba, Maimoon tace "Ba ruwana Abba cewa yyi
mu je mu kira ta" A balcony suka tadda Anty tana magana da wa enda xa su yi girkin
biki a biya su, Mujaheed ma na xaune balcony din sai Yusuf dake tsaye, Anty tace
"Saloon din xa ku yanxu" Maimoon tace "Anty Abba yace mu je da imaan" Anty tayi
wani dariya tace "Wace Imaan din tab, amma ku je dai ku ji abinda xata ce" Imaan na
dakinta Maimoon ta shigo parlor, nan ta sanar ma Ammi abinda Abba yace Ammi ta kira
Imaan, tana fitowa Ammi tace "sai ki dau Hijab ku wuce saloon" sosai gabanta ya
fadi ta marairaice tace "Saloon kuma Ammi, aa ni dai xan wanke gashina da kai na"
Ammi tace "Kee! dau Hijab ki fice min parlona, dama idan baki gyara gashin nan ba
yau kar ki dawo min gidan nan" Imaan fa fashe da matsanancin kuka tana kallon uwar
tata, ganin Ammi ta mike ta shiga daki da sauri ta dau Hijab dinta ta fita, Maimoon
ta bi bayan ta tana dariya kasa kasa, Anty na ganinta tace "Subhanallahi me ya faru
Imaan" cikin kuka tace "Anty ni fa gashina bashi da wani datti kawai combing dinsa
ne bana yi" Anty tace "Toh mu ga gashin" tana shesshekar kuka ta cire Hijab din ta
cire hulan kanta, Yusuf ya dauke kai bai son dariya ta fara wani sabon kukan, ga
dai gashi har gashi amma duk an cukuikuye shi waje daya, Anty tace "When last kika
wanke gashin" a hankali tace "Ranan nan" Anty tayi murmushi kafin ta ce komai
Mujaheed ya mike fuska daure yace "Mu je in kai ku saloon din" Ta fashe da sabon
kuka xata koma bayan Anty ya ja ta sai gun motarsa, Yusuf yayi murmushi yace "Da
yake Umma bata nan ba" Su Maimoon duk suka shiga motar bayan ya tura Imaan ciki,
Suna isa saloon din Imaan ta hadiye kukan da take barin da taga yan mata kala kala
cikin saloon din, Ita Mujaheed yasa a fara gyara ma gashin, da ruwa mai dumi sosai
yace a wanke mata gashin nata bayan an sa mai, banda turo baki bbu abinda take tana
runtse ido don ba daman kuka ga yan mata kar su mata dariya, lkci daya gashinta ya
dawo sak na Indians sai sheki yake, ganin an kusa gama mata ya kalli kannin nasa
yace "Sai ku samu napep da xai maida ku gida, coz I am a driver to none of you"
daga haka ya fice saloon din, duk suka bi sa da kallo. Sai bayan magrib suka shigo
gidan don har da lalle suka yi, dama Imaan direct part din inna ta nufa tun daga
bakin kofa ta cire Hijab din jikinta ta shiga tana murmushi tace "Inna..." Inna
tayi mitsi mitsi da ido tana kallon gashin nata tace "Ikon Allah kin ganki kin fito
sak mace ko?" Imaan ta xaro ido tace "Toh da ni na miji ne?" Inna tace "Idan ba
kallon isuhu nake maki wani lkcn ba shegiya nake" Imaan ta fashe da dariya har da
kwanciya kan kujera, Inna ta kalli Mujaheed dake cin abinci tace "Ko kai baka gani
ba Mujaheed?" Imaan ta hararesa ta gefen ido ta mike xata shiga daki Inna tace
"Dawo nan ana ma yar uwar ki gyaran jiki tunda can bangarensu ya dawo kamar wajen
cin kasuwar laraba" Imaan tace "Anty Seeyama" Inna tace "Ehh kema da dai Allah ya
fiddo maki da mijin nan kiyi aurenki da wuri ki haifi kanninki da uwarki taki haifo
maki" Imaan ta hade rai tace "Yar karama da ni xaki ce min aure?" Inna ta kalli
Mujaheed tace "Don Allah Mujaheed Imaan bata isa aure ba yarinyar da ke al'ada? Ga
kirjinta cike da dukiyar fulani" Murmushi Mujaheed yyi kansa a kasa yana cin
abincinsa, Imaan ta harari Inna ta juya ta nufi kofa inna tace "Ke kika sani, ni ba
ruwana wllh, Allah na tuba lalurorin ki na duniya ma ai tsaye yake da kafafuwansa
gun d'a na, ba gwara kiyi auren ko Bukar xai huta da kashe kashen kudi kije can
kuma mijin shi ma ya d'an dana ukubar" Washegari alhamis Imaan ta tashi da ciwon
ciki ga bak'i a part dinsu balle tayi raki yanda ranta ke so, duk magungunan da ta
sha ba wanda taji ya mata, ta lallaba da kyar ta tafi bangaren inna, ita din ma dai
parlon nata duk tsofaffin kawayenta ne a xaune, imaan ta gaishesu da kyar ta shige
bedroom dinta ta kwanta, lkcn Azahar nayi dama inna ta lallabo ta shigo dakin ta sa
ma bandakinta makulli don ba wanda xai shiga balle ya mata kazanta duk me son yin
alwala ga pampo can ta bude, idan kuwa xai kama ruwa ne to yaje sashin masu biki,
ganin juye juyen da Imaan take duk ta hada xufa duk da iskan fankan dake dakin ta
wani xaro ido tace "Ke lafiya meye hakan, ni fa ba ruwana idan baki da lafiya ne ki
tafi bangarenku kada a gigitani a nan, meye wani juye juye kamar macijiya a kan
gado na" Imaan ta fashe mata da kuka tace "Wayyo cikina ke min ciwo" Inna tace
"Auzubillahi, to rufa min asiri ki sakko ki tafi gun uwarki ba ruwana" Cikin kuka
tace "Akwai mutane a can" a fusace Inna tace "Mutanen banxa ina ruwanki da su, idan
wani abu ya sameki maganin me mutanen xa su yi banda su cika mu da surutu, dama ba
komai ya kawo su ba sai kwadayin d'an shinkafar da xa a raba a kwano da kaji banda
haka wani ma anyi shekara goma ba a gansa ba, ki tashi ki tafi tasan yanda xata yi
dake idan ma asibiti ne ta kai ki, idan ko ba haka ba idan ban sa an dage bikin ba
ace bani ba, biki ya fi rai ne" da kyar Imaan tace "Ni fa marana ke min ciwo" Inna
tace "Wai jini?" Imaan ta gyada mata kai, Inna tace "Toh shi kuma wanda kika yi ko
sati ba ayi ba fa?" Tace "Ba shi bane kawai alama ne" Inna ta xabga tagumi tace "Ke
kam kina ganin jarabawa iri iri a rayuwa na lalura, banda haka jinin ma idan xakiyi
sai kin ta fama, anya kuwa ba a sa maki hannu ba imaan?" Imaan ta xamo daga kan
gadon tace "Wayyo ni dai ki kira min yaya " Inna tace "Waye kuma yaya?" Hawaye na
sakko mata tace "Ni dai ki kirasa" Inna tace "Toh su wa encan tsofaffin duk tsami
sun cika min parlor kamar ni xan aurar da 'ya sun ki tafiya, ni dai na gaji wllh
ana damuna, wata ma ni nafi shekara talatin ban gan ta ba, ni dai gaskiya sun
isheni suje can bangaren da ake biki kuma sun ki, duk parlona ya gauraye da warin
tsofaffi, wannan fitina da mai yayi kama" Imaan na son yi dariya amma ciwo yaki
barin ta tayi, Inna ta fita fuska daure ta kashe TV da ke aiki tace "Kada TV ya
buga in ja ma Ahmadu asara gwara a bar shi haka nan ya huta" daga haka ta dau
wayarta ta fita don neman me kira mata Mujaheed, wata ta samu a tsakar gida ta
nufeta tana kallon mata yan gayu xaune tsakar gidan, tace "Toh dai gida ba na
bitilman bane duk wanda ya xubda ko kwayar shinkafa yyi hakuri ya share
fisabillahi, kar a tafi a bar mu cikin wari cuta ta kama mu" mika ma matar wayar
tayi tace "Gashi Idan kin iya karatu ki duba lambobi xa ki ga ansa Dakta, lambar
Mujaheed ne shi ya sa mun shi a haka, sai ki kira min idan kuma baki iya ba don
Allah kar ki rikita min wayar in shiga uku" murmushi matar tayi ta nemo number tayi
dialing ta mika ma inna, ta amsa
ta kai kunne, sai da yayi ringing sau uku sannan Mujaheed ya daga, inna tace
"Mujaheed??" Mujaheed yace "Ina ji, ya aka yi?" Inna tace "Toh ga yar uwar ka nan
dai rai a hannun Allah, duk inda kake ka rufa mana asiri ka juyo ka dawo, ni sae in
iya cewa a daga bikin ma wllh don idan ta mutu ni nayi asara...." Da mamaki yace
"Wacece?" Inna tace "Wacece banda Imaan, tun safe Ashe tana dakina babu inda bata
mirgina ba don ciwo, tun daga kan gadon har kasan tass, wai yanxu na shiga dakin
don kulle bandakina saboda marasu hankali masu shiga bayin mutum suyi kaca kaca da
shi kawai naga yarinya duk ta hada xufa a kan gado kai kana ganin ta kasan...."
Mujaheed ya katse ta yace "Ina hanya" daga haka ya katse wayar, Inna tace "Atoh
haka kawai, bikin banxa bikin hofi..." Daga haka ta nufi part dinta, tana durkushe
bakin kofa tana watsi da takalman jama'a can gefe ganin duk ya cika mata bakin
kofar ta ji muryar Mujaheed a bayan ta ta mike, tace "Wannan uban sauri haka kamar
wanda ya biyo jirgi, to ka shiga tana can ciki ban san isilinta ba" Shiga parlon
yayi ganin mutane ya sunkuyar da kansa ya gaishe su ya wuce dakin Inna, karasawa
kan gadon yayi yana kallonta yace "Me ya faru?" Ta fashe da kuka sosai tace "Yaya
cikina" hannu ya kai cikin yace "Tun yaushe?" Ta cire hannunsa tace "Ni ba cikin
bane ke min ciwo, period ne" ya daure fuska yace "Toh me xan maki, ba kin sha
magani ba" da kyar tace "Bai yi ba, doctor Habib allura yake min" yace "Toh me ya
hanaki kiransa?" Tace "Yana Lagos" yace "Toh bani da allura a nan sai na koma
asibiti" ta kamo hannunsa cikin rawar murya tace "Toh ka tafi da ni asibitin plss"
tana fadin haka ta fara kokarin sauka kan gadon, bude baki yyi ganin yanda tayi ma
inna stain din kan gado, bai san lkcn da ya dauke kai yana murmushi ba don har ya
hango inna, ita ma xaro ido tayi tace "Na shiga uku yaya" yace "Aa sai ta gani xaki
ki shiga ukun ai, yanxu kina daya ne" ji tayi gaba daya ba ciwon ta sauko kasa da
sauri jikinta na rawa tace "Wayyo yaya ya xan yi" Tana fadin haka ta nufi bathroom
ta murda ta ji a rufe, tsayawa kallonsa tayi kamar xata yi kuka tace "Yaya ta sa
makulli" parlor ya koma gun inna yace "Inna xata shiga bayi ina makullin" inna ta
mike da sauri tace "Auzubillahi, wani bayin? Aa ta fito ta tafi nasu idan ma baxata
iya tafiya ba ka goyata, haka kawai bayina fess ta shiga ta sa min k'arnin jini"
Kunya ma yasa Mujaheed ya kasa cewa komai don mutanen dake parlon sun kai shidda,
ganin inna xata shiga dakin ya rigata shiga da sauri, ya dau dankwalinta ya rufe
saman gadon da shi, Imaan ta marairaice tana kallon inna da ta shigo tace "Don
Allah ki ban makulli wllh xan wanke maki bayin" Inna tace "Ai uwata bata ce min je
ki kya gani ba, don haka ba bayina xa a shiga a min kazanta da jini ba, ki daure ki
tafi can bangaren ku idan ma tafiyar ne baxa ki iya ba sai Mujaheed ya goya ki"
Kuka Imaan ta fara yi tace "Na fa ce xan wanke maki wllh" a fusace Inna tace "Kai
ku fita ma ku bar min dakina kuje can bangaren ku karata, da na bar ki ma kika
kwanta min saman gado duk da ban san al'ada kike ba" Mujaheed yace "Toh ki bata xan
wanke maki bayin da kai na" Inna kamar xata rushe masu da kuka tace "Yau naga
abinda ya isheni bai ishi Allah ba, wai ana dole ne, hypo uku na xuba bayin nan
daxu da safe da nake wankewa, a kan wani dalilin xa aje a bata min da karni...." Ya
katse ta yace "Ni kuma xan xuba maki hypo biyar" da kyar da kyar da sidin goshi
inna ta bada makullin shi ma sai da aka yi yarjejeniyar baxa a bude mata drum din
ruwa ba kada a xuba kazanta, Mujaheed ya dau buckets biyu ya fita debo ruwa a waje,
Ita dai imaan na tsaye sai satan kallon saman gado take, Mujaheed na ajiye ruwan a
bayin ta bi sa ciki tace "Wayyo yaya pant da pad da xan canxa fa?" Ya kalleta da
mamaki yace "Ni ma kike tambaya?" Ta marairaice tace "Plss ko xaka je dakina...."
Ya jefa mata wani kallo yace "You are stupid" fitowa bayin tayi ta bude gun kayanta
a wardrobe din inna, ai ko taga panties dinta na nan, tace "Yaya toh saura pad"
Yace "Bari in xama pad din ki sa" Bata ce komai ba ta turo baki ta shiga bandakin
ta rufe, juyawa yayi ya fita, ya tafi gun mai kiosk dake layin ya amso always daya
ya dawo, inna dai na xaune ta daura kafa daya kan daya tace "Allah ni dai ya dubeni
ya rabani da k'arni, komin xuba hypo da xa ayi a bandakin nan" Mujaheed bai ko
kalleta ba ya shiga dakin, yana ta tsaye har Imaan ta fito daure da towel din inna,
ya jefa mata pad din kan gado, ta turo baki tace "Thank you" komawa bandakin tayi
ba a dau lkci ba ta fito, yace "Sai ki cire xanin gadon ki wanke" ta xaro ido tace
"Yaya ya min nauyi fa" bude baki yyi yace "Toh ki bar shi haka nan" kamar xata yi
kuka ta isa kan gadon ta shiga cire xanin gadon bayan ya dauke pillows din kai,
Muryar inna suka ji tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, jinin ta xuba min a
kan gado ni Asabe????" Inna ta fashe da kuka tace "Me na maki xaki saka min da haka
Imaan" Mujaheed ya dauke kai yana kokarin danne dariyarsa, imaan duk ta gigice,
inna tace "Toh sai ki Kwashi xanin gadon don ubanki ki Bukar kai ma Aisha ta wanke
min, kai kuma ka fitar min da katifar waje ka sa min shi a setin rana, Allah
ubangiji ya saka min, daga taimako sai ta xuba min al'adarta a xanin gado k'arni ya
kashe ni" Inna ta kara rushewa da matsanancin kuka tace "Sannan d'an walakanci tana
yoyon xata dau tawul dina ta daura salon ta goga min gaibu, ni dai na shiga uku da
wannan 'ya ta Bukar, tana cutata a gidan nan" Imaan ta wani hade rai kamar xata yi
kuka, Mujaheed ya cire xanin gadon ya wuce bathroom da shi, Inna na matsar kwalla
ta daga hannu biyu sama tace "Allah kaga xuciya daya nake xaune da kowa gidan nan,
duk mai nufina da sharri ka min iyaka da shi" Tana fadin haka ta share idonta ta
fita tace "Bari xanje inji ko Aishar ce ta sa ki xo ki cuce ni yau" Imaan ta
murguda baki ta fiddo kayanta a press ta saka, bude kofar bathroom din tayi ta ga
Mujaheed yana aikin wanke xanin gadon.

17....

Imaan dai na tsaye har ya gama wankin bedsheet din tana rike da kayan da ta cire,
ya saka xanin gadon a bucket ya fito, a hankali tace "Yaya to wankin bayin fa?"
Wani mugun kallo ya watsa mata ya dau wayarsa da makullin mota da ya ajiye kan gado
zai fita ta xaro ido tace "Yaya don Allah ka tsaya, baxan iya shanya bedsheet din
ni kadai ba ai" ko juyowa bai yi ba balle ya tanka ta, a bakin kofar parlor ya hadu
da Inna, Inna ta gwalo ido tace "Har an wanke min bayin?" Yace "A'a xan fita in
amso Hypo ne" yana magana ne yana kokarin fita, inna ta cakumosa tace "Sai dai ka
raina ma Bukar ko Ahmadu hankali, ce maka nayi bani da hypon?" tana fadin haka ta
ja sa xuwa bedroom din fuskarta daure, yace "Toh ki sakeni mana" ko saurarensa bata
yi ba har suka shiga dakin, Imaan dake labe bayan kofar dakin tana jin sun shigo
dama ta fito da sauri ta fice a dakin, Har bandakin Inna ta turasa ta dauko Hypo
biyu ta jefa masa, yace "Biyar fa kika ce Inna" a fusace tace "Toh ai ni ba
asararriya bace Mujaheed, Ko sisin Bukar da Ahmadu babu a Hypon, Isuhu ne na roka
ya siyo min" tana fadin haka ta dau ledan omo babba ta jefa masa tace "Har jikin
tiles ni dai a gurje min ba ruwana, kuma daga yau gaskiya idan Imaan ta sake shigo
min daki xa a ga bala'i, wato kawai fasa bomb din bala'i xanyi a gidan nan, naje
yanxu uwar bata nan, da sai in ji ko ita ta turo min ita ta cuce ni ta xuba min
al'adarta, banda ma kazanta irin na yaran ynxu duk sai sun bari kowa ya san suna
al'ada, gantalalliyar duk ta tashi ta kazance min kan gado da bandaki, to hirrr
dinta kada ko da wasa ta sake leko min daki ta tsaya iya falo, idan kuwa dama bata
da tsarki kar ta yo min nan xan koreta don parlona na tsarkakakku ne" Mujaheed dai
bai tanka ta ba ya nade sleeve din shirt dinsa ya fara wanke bayin bayan ya kada
kumfa da hypo, inna tace "A'a bana son aikin al'gus malam, ka kara barbade bandakin
da omo lungu da sako sai ka juye dayan hypon" ya jefa mata wani kallo yace "Toh wai
ni na bata maki bandakin daga taimako kawai" Inna tace "A'a ba ruwana saboda kai na
bude, in don ta wancan matar ce ai sai dai ta tafi bangarensu jage jage da jini don
wllh baxan bude ba, haka kawai" ko kallonta bai yi ba ya ci gaba da wankin bayin da
babu abinda ya samesa, haka inna ta dinga basa wahala tana tsaye daga bakin kofa
tace can tace nan, har daga karshe aka gama wanke bayin, ya wanke hannunsa ya fito
fuska daure, tace "Toh don Allah ni dai kar in kwana cikin k'arni yau ka taimakeni
ka fidda min katifar can ka ajiye dai dai idon rana" yace "Wannan kuma sai dai ki
kira Yusuf baxan iya ba gaskiya" Tace "Toh wllh baxa ka fita dakin nan ba sai tare
da katifar nan, haka kawai in kwana cikin najasa, kafar ka kafar katifan" tana
fadin haka ta sa makulli a dakin ta tsaya bakin kofa, kallonta ya dinga yi fuska
daure, inna tace "Oho dai duk kanwarka ta ja maka, ita yanxu ba gashi ta gudu ta
bar ka da aikin jini ba, yarinya sai mugunta fal cikinta" Babu yanda ya iya haka ya
cire katifar ta bude masa kofa tace "Saitin rana xaka ajiye duk ya kona abinda ya
xuba kai" fita yyi da katifar ya ajiye inda tace, ya dawo dakin don daukan wayarsa
da makulli, ganin babu su a inda ya ajiye ya kalli inna dake tsaye tana kallonsa
kyarr, bucket din xanin gadon ta nuna masa tace "Idan ka shanya wnn sai ka dawo ka
amshi wayar ka da makulli ba ruwana, yarinya dai ta cuce ka kawai, sae dai sakayyar
Allah" tana fadin haka ta koma parlor, Mujaheed ya fi minti uku a tsaye, yasan ko
me xai ce mata baxata basa ba, hakan ya sa ya ja tsaki ya dau bucket din fuska
daure ya fice dakin, yana gama shanyawa a nan parlorn ya ajiye mata Bucket din yace
"Bani wayana in wuce" ta jefa masa makullin siff dinta tace "Ka bude ka dauka ka
rufe min kayana" daukan makullin yyi ya koma daki ya bude yana daukan wayarsa da
car key ya bar mata siff din a wangale ya fice kamar xai tashi sama, inna tace "Oho
dai....." Dab da Magrib Ammi ta shiga tada Imaan dake ta bacci tun bayan da ta kara
shan magani, Ammi tace "Ya jikin?" A hankali tace "Da sauki, Ammi Daddy ya dawo?"
Ammi tace "Ehh ya dawo" wara ido tayi ta sakko kan gado ta sa Hijab har ta isa kofa
ta tsaya ta juyo tace "Ammi hope bak'in duk sun tafi?" Ammi tace "Ina kuwa xa su
gobe biki?" Imaan tace "Toh daddy yana bedroom dinsa ne?" Ammi tace "Aa ina jin
suna can tare da Abba" Imaan na sa takalminta bakin kofa aka bude kofar parlon,
d'aga kai tayi taga Inna ce, Inna tace "Ya jikin, na ji shiru tun daxu baki leko ba
shine nace bari in lallabo in xo in duba ki, kun je asibitin ne?" Imaan da ta hade
rai ta ki kallonta tace "Ni na ji sauki" inna ta amsa gaisuwar masu gaisheta a
parlon sannan ta kalli Imaan tace "Tohhh, Allah dai ya sauwake, amma wannan wahala
ba gwara Bukar ya aurar da ke ba kowa ma ya huta kema ki huta" Ammi dake tsaye tana
jin su ita ma ta gaida inna, inna tace "Lafiya lau Aisha, in ji mai gidan ya dawo
lafiya?" Ammi tace "Alhmdllh" Inna tace "Toh da kyau, duk da dai ni ko tsinke ba a
kawo min a tsarabar da yake yowa, sai dai ke da yar ki ku cinye, to duk ba wannan
ba don bai dameni ba wanda Ahmadu ma ke bani Allah ya amfana, yanxu dai xuwa nayi
in duba jikin Imaan, ta xo daxu tana ciwon mara ban kai ga jik'a mata ararra6i ba
na nemeta na rasa" Ammi tace "Ta ji sauki yanxu, sai dai ko ta bi ki ta amsa ta sha
a can" inna ta gwalo ido da sauri tace "Ta bi ni ina? A'a ta xauna xan lallaba in
koma in jiko mata in kawo yanxu, ta bi ni kuma ana xaune kalau? Taje ta min me kuma
ban da abun ki Aisha yarinya na fama da kanta, Aa bari inje in dawo yanxu, dama na
bar sauran tsoffin da basu tafi ba kada a min barna" daga haka ta juya ta bar bakin
kofa murya can kasa tace "Haka kawai ta sake koma min ta min wani aika aikan da
kazantar ta a gida ta cuce ni, wa gareni da xai bi min hakkina ban da Allah" Imaan
ta turo baki ta fita parlorn ko da wasa bata fadi ma Ammi abinda ya faru daxu ba,
part din su Maimoon ta nufa, kasa shiga parlon tayi ganin mutane a ciki, ta fi
minti biyar tsaye bakin kofar taji muryar Yusuf yace "Me kike yi nan Imaan"
kallonsa tayi tace "Toh akwai mutane a parlon ta ya xan shiga" tana magana tana
kallon Mujaheed da ya wani hade rai don tare da Yusuf suke, dauke kai tayi bata son
tayi dariya, can ta turo baki ta bar bakin kofar ya shiga ciki, Yusuf yace "Toh ko
in maki jagora?" Dariya tayi tace "Daddy na yana parlon Abba?" Yusuf yace "Eh mana"
tace "Toh oya ka shiga gaba sai in bi ka a baya" a haka suka shiga parlon tana
boyewa a bayansa wanda hakan yasa few kawayen Umma dake parlon suka dinga kallonta
har suka shiga parlon Abba. Da gudu ta tafi ta rungume daddy tace "Daddy sannu da
dawowa" Daddy yace "Baki gaida Abba ba" kallon Abba dake kallonta tayi, ta boye
fuskarta tace "Ina yini abba" yyi murmushi yace "Lafiya lau daughter" Daddy yace
"Toh baki gaida yayanki ba shi ma" ta kalli Mujaheed dake parlon tace "Ai mun hadu
a waje" Daddy yace "Toh maa sha Allah" Tace "Daddy baxan je gombe Hutu ba tunda mun
yi holiday?" Abba yace "Wajen wa a gombe" murmushi Daddy yayi yace "Kanwar mamarta"
Abba yace "Ohk If I recalled well last holiday ma can kika je ko" Kai ta gyada
masa, Abba yace "Kuma babu canji, ga gwaggon ku Suleja ma ba sai ki je can ba ko da
su Maimoon, dama bata da lafiya" Daddy yace "Gaskiya ne ya kamata" Imaan ta xaro
ido tace "Kauye?" Abba yace "Of course, you will have more experience.... Shi
kauyen ba wuri bane" Ta dauke kai bata ce komai ba ta cinno baki gaba, Abba yace
"Nasan inna xata ji dadi idan taji xa ku je, kinga sae Mujaheed ya kai ku a mota
tunda ya sha xuwa tare da mu" Da sauri Mujaheed ya kallesa yace "Abba... ai ba
lalle xan gane wajen ba fa" Abba ya kallesa yace "Last time ma ba kai ka kai mu a
mota ba" da kyar yace "Abba kusan shekara daya fa" mikewa Imaan tayi ba tare da ta
kallesu ba tace "Xan je ina taya Ammi aiki" bata jira cewarsa ba ta fice, Abba yayi
dariya yace "On a serious note dole su je riga suyi hutu bari dai a gama bikin nan
lafiya" mikewa Mujaheed yyi yace "Xan je ana kirana can waje" daga haka ya fice a
parlon, Daddy ya gyada kai yana murmushi yace "Su masu wayo wai, gaskiya ne ya
kamata su kai ma Hansatu ziyara tunda gashi bata samu xuwa biki ba ba lafiya" Abba
yace "In sha Allah I will see to that on Tuesday if everything is settled" Daddy
yace "Alhmdllh, Allah ya kai mu lafiya" Washegari Friday bayan an sakko juma'ah aka
daura auren Seeyama da angonta Abdul, throughout shagalgulan da ake a gidan imaan
na dakinta tana bacci ko ankon bikin bata sa ba, Ammi bata takurata ta shiga jama'a
ba sanin cewar bata wani jin dadi, kuma dama bata son tayi stressing kanta ta
jogana masu wani ciwon, sai dab da xa a tafi da Amarya Ammi ta tasheta don tun daxu
Inna ke cigiyarta, sai a sannan imaan ta shiga bayi tayi wanka ta wanke baki ta
fito ta shirya cikin daya daga ankon da suka yi, ta d'an shafa powder tasa eye
pencil da chappette, sannan ta dau farin hijab har kasa ta saka ta dau wayarta,
ganin missed call ta tsaya ta duba, Sadeeq ne ya kirata, komawa tayi ta xauna tayi
dialing, katsewa yyi ya kirata, bayan sun gaisa yace "Ina kika shiga yau" tayi
murmushi tace "Bacci" yace "Uhm baki da damuwa, ya su mama?" Tace "Alhmdllh" yace
"Daxu Mariya tace min kuna biki gidanku" tace "Ehh haka ne" yace "Shine ba
gayyata?" Tace "Uhmm" yace "Toh kin kyauta" a hankali tace "Kayi hakuri, next time"
yace "Toh waye next din auren? Ko ke?" Ta xaro ido sai kuma tayi dariya tace "Ni
kuma, yar yarinya da ni" yace "Haba?" Tace "Ehh mana" yace "How old are you?" Ta
langwabar da kai tace "Na kusa 19 soon" dariya yayi yace "Ehh gaskiya ne, ke
yarinya ce sosai ma" tace "Toh kaga" yace "Ko aure aka maki yanxu ma baxa ki haihu
ba ai" ta xaro ido sai dai bata ce komai ba tayi murmushi, yace "Yeahh" tace "Xa mu
je raka Aunt dina dakinta yanxu" yace "Wani anguwa ne?" Tace "Ban sani ba dai" yace
"Toh idan kun je gidan ki kirani" tace "Toh in sha Allah" sallama yayi mata ya
katse wayar. Inna ce tsaye tsakar gida ta cakare cikin atamfa England an mata
dinkin
su irin na tsoffi, ga katon gyalenta ta yafa, ga mutane duk ana ta shirin xa a
wuce da seeyama gidanta, motocin dake compound din sun fi shidda duk na daukan yan
kai amarya, tun daga nisa Imaan ke jiyo Inna ta tana cewa "Naga abinda ya isheni
bai ishi Allah ba, duk an wani yi cirko cirko a gaban motoci ku ja baya mana kar ku
gurje masu dukiya in shiga uku, ni wllh saboda bala'in mata ma duk xafi ya isheni
abu kamar maita dai, ke Maimuna ba ca nayi ki dubo min Imaan ba ko har yanxu jinin
bai dauke ba ne, duk yau ban ganta cikin jama'ah ba ko bakin ciki take ma yar
uwartata ban sani ba" Imaan ta turo baki bayan sun hada ido da Innar, inna ta ja
tsaki tace "Kai ni dai ko limamin babban masallacin Habuja ne Bukar yau dai baxai
hanaki sa gyale ba, duk yan uwanki ga su fess cikin gyale ke ko kin maka hijabi uwa
xamu je xaman makoki ba amarya xa mu kai ba haba imaan, ni dai na gaji da maganar
ki a gidan nan" Imaan ta dauke kai har ta iso gun motar, wata kawar Umma ce ta xo
tayi announcing wai Umma tace wasu su fara tafiya kafin a fito da amarya, nan aka
fara kokarin shiga motoci, inna ta bude baki ta gwalo ido ganin wata katuwa cikin
shiga ta alfarma da gwalagwalai na kokarin shiga daya daga motocin, cikin daga
murya tace "Wayyo meye wannan kuma... Kee don Allah ki bar sirara su shiga, banda
neman magana da tsokanar fada ina xa a dake a haka, kisa kike son yi cikin motar
fisabillahi, wannan ai sai dai idan ke kadai xa aje a ajiye a dawo to ina kuma
hakan xai yiwu tunda motar ba taki bace, fito don Allah mutane su shiga" Imaan ta
boye fuskarta da Hijab kar tayi dariya, mutanen wajen wasu sai dariya suke kasa
kasa, matar ta fito kamar warce ruwa ya cinye kanta a kasa, inna ta karasa kusa da
ita tana kallonta tace "Haba baiwar Allah... ke ba kya tsoron Allah ne wannan abu
haka kinyi wani bake bake bayan motar mutane, ina kike son a xuba sauran jama'a, ko
ke baki ga irin ki bane" Wata mata ta karaso kusa da Inna tayi kasa da murya tace
"Hajiya babban kawar uwar amaryar ce fa" inna ta bude baki tace "Babban kawar uwar
amarya kuma sai a sa mata ido ta latse hanjin 'ya yan mutane a bayan mota, dama
kisan kai ya kawota ba biki ba, wannan abu kamar giwa kice ta shiga mota, amma
bakya tsoron Allah wllh" sum sum matar ta bar wajen, Inna ta ja tsaki tace "Kai
sirara su shiga a wuce, ba ruwana a aje a tatse hanjin mutane daga kai amarya ace
bikin jikata ga abinda ya faru, to banda gwalagwalan ma duk karya ne ya xa ayi
kamar ta ace bata da mota, ke kuma imaan ga motar da xa mu shiga can da Seeyama
nace ban son tukin kowa sai na Mujaheed haka kawai mahaukatan abokan angon su ja mu
su watsar da mu a rami" Bude motar Imaan tayi ta shiga back seat tana murmushi,
Maimoon xata shiga inna tace "Toh ina kuma wancan figaggiyar xata shiga ni patuu,
ba ga motoci can ba" Maimoon ta sauka da sauri, Imaan ta dinga dariya har da
kyakyatawa, Kamar yanda inna tace Mujaheed ne ya ja su, ita, Seeyama da kawayenta
biyu sai Imaan, suna hawa main road inna tace "Toh yau dai Seeyama gashi xa mu kai
ki dakin ki, duk da dai mijin naki wani ga6o ga6o ne kiyi masa biyayya iya yanda xa
ki iya, ni baxan ce kiyi hakuri yaje ya kashe mana ke ba gaskiya, bbu xancen xaman
hakuri, mu dai da aka cuta da hakan aje a haka, amma duk kika ga abinda baxa ki iya
dauka ba yafa gyalenki ki dawo gida, ko ki tafi sashin ubanki ko ki tafi sashin
kaninsa ko kuma ki yo sashina sai iya Inda karfin mu ya kare na kwatar maki hakkin
ki, ni fa tun daga lefen da ya hada maki dama na raina masa aji...." Mujaheed da
takaici ya ishesa yace "Haba inna yanxu fada kike mata ko hudubar tsiya?" Inna ta
hade rai tace "Ka ji min yaro da aka haifa ina tsaye bakin kofar asibiti daga safe
har dare, kai xaka koya min xaman duniya Mujaheed, ko ance maka ban san abinda nake
bane, to bari kaji ko kai yau aka daura ma aure iyakar abinda xan gaya ma matar
kenan don ni yar gaskiya ce, akan me xa ayi ta wani ce ma mace tayi hakuri gidan
miji ana cutarta ana musguna mata, Allah kadai yasan me yasa ya halitto ni a mutan
da ba na yanxu ba, kuma ai bance kada tayi masa biyayya ba kawai idan taga xai
takata ta gudo gida, ina laifin wannan shawara tawa??" Kawayen Seeyama dai sai
kallon inna suke k'asa k'asa, inna ta ja tsaki tace "Tun da shaidan duk na makale
gefen xuciyar ku ba dole kaji haushin abinda na fada ba, maxa dai sun xama masifa
yanxu, duk halinku daya dama, yo banda halinku daya ya wuce idan yace xai walakanta
maka kanwa ka matse gantalalle ka nakada masa duka tunda ga irin sa kamar tsinken
sakace, wllh xaka iya dukansa" Seeyama dake hawaye cikin gyalenta ta fashe da
dariya, imaan na taya ta, shi dai Mujaheed bai ce komai ba yana mamakin warce Allah
ya basu matsayin kaka.....

*The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee wllh*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included


in the payment group.

18....

Suna isa gidan bakin inna ya mutu murus sai 'yan idanuwa ganin gida ne ba na wasa
ba, ni ko nace dama Umma ce xata yarda 'yar ta ta auri mai rufin asiri kawai?? Inna
ta fito cikin motar tana cewa "Fito da kafar ki ta dama in sha Allah gidan xama ne,
yi nayi bari na bari, aure kuma da kike gani d'an xaman hakuri ne duk shi muka yi
muka kawo yanxu da rai da lafiya, Allah ya maki albarka yasa gidan ki ne ke kadai
don na xauna da kishiyoyi ban ji da dadi ba, kishiya masifa ce" Wani kallo Mujaheed
ya dinga mata, inna na washe hakora tana kara kallon katon gidan tace "Toh kai
Mujaheed baka da abinda xaka ce mata ne ka tsaya wani sandandan kana kallonmu,
wannan ai ya ma fi gidanka girma wllh" Yace "Kece baki mata nasihar tun a gida ba
amma ni nayi tun a can" Kuka kawai Seeyama take, inna ta hade rau tace "Ji
shashanci don Allah, to ki bude ido ki ga gidan mana idan ba sae kin daina shegen
kukan nan ba" Mujaheed ya karasa kusa da ita yana kallonta yace "Be the best wife
you can be lil sis, wishing you a peaceful married life" rungumesa tayi tana kuka,
shi ko ya dinga kallon imaan da ta ja can gefe tana 6a66aka dariya har da rike
ciki, ganin kallon da yake mata ta shige cikin gidan da sauri bata kuma fasa
dariyar ba, cike da damuwa Inna tace "Ni dai wllh wannan 'ya ta Bukar gani nake
kamar ciwace ciwacen ta ya shafi kwakwalwarta, to banda haka taya xa a kawo yar
uwarki dakinta tana kuka, ke baki bata hakuri ba kina dariyar mugunta, to Allah dai
ya kai mu naki kiga iskanci wllh" tana fadin haka ta janye seeyama tace "Mu shiga
ciki kiyi kukan a tsanake kin ji jikalle, kai kuma Mujaheed bayan isha ka xo ka
daukeni, idan kuma ya kama a nan xan kwana to shikenan" daga haka suka wuce ciki
shi kuma ya fita compound din da motarsa yana girgixa kai. Bayan Magrib da rashin
arxiki inna ta sallami duk kawayen Umma yan kawo amarya, Aunty da Ammi dama basu
dade ba suka bar gidan, tsaye inna tayi bakin kofa rai bace tana cewa "Wannan ai ba
yi bane, sai kace baku da maxaje baku da mafada, amarya dai ga ta an kawota lafiya
har ta hakura ta daina kuka, to ai kuma sai kowa ya kama hanyar gidansa sai kuma
wata shekarar idan ta haihu, amma duk kun wani ja6e ba niyyar tafiya, a dai dinga
jin tsoron, ni ma nan da ku ka ga ban tafi ba kakar ta ce, ni na haifi ubanta
Ahmadu, bai baci ba ko da cewa nayi xan kwana, amma mutane karere kawai ku cika
gidan yarinya kun ki tafiya, ko ita Rukayyar ce tace ku kwana tare da su bani da
labari? To ni dai ba ruwana" Wa enda suka fita iskanci yi suka yi kamar basu ji
abinda take cewa ba, wasu kuma haushi yasa duk suka bar gidan, a fusace inna tace
"Mata wasu katangala kawai rai ba ga ta sun xaune ma yarinya a gida, ni ban taba
ganin haka ba tunda uwata ta haifeni, ku barta daga ita sai kawayenta su ma a xo a
sallamesu su kama gabansu mana" Inna na kallon imaan dake kokarin fita ta gefenta
tace "Ke kuma ina xaki sanyi ya kare maki ki cuci d'a na da kashe kudi?" Imaan ta
turo baki tace "Ina xuwa ni dai" inna tace "Toh kar dai kiyi nisa don Mujaheed ya
kusa xuwa yanxu, ba ruwana in kwana su Ahmadu su min fada" imaan bata ce komai ba
ta fita, tana ganin motarsa ta gane don layin tamkar rana saboda hasken fitilu, ta
karasa gun motar ya bude ya fito yana kallonta, Ta sunkuyar da kai tace "Ina yini"
yace "Lafiya lau Imaan, nan ne gidan sistern naki?" Kai ta gyada masa, yace "Maa
sha Allah, Allah ya basu zaman lafiya" tace "Ameen" yace "Amma ba nan xaki kwana ba
dai koh?" Ta xaro ido tace "In kwana kuma?" Murmushi yyi ya rungume hannu sa yace
"Shi na gani ai, Idan kika kwana ai xaki yi inconveniencing amarya da angon" turo
baki tayi tace "Toh ni dama ta ya xan kwana" yar dariya yayi yace "Gaskiya ne,
yaushe xa ku koma gida?" Tace "Muna jiran yaya ne, xai maida ni da Maimoon da
Grandma dinmu" yace "Ohk yayanku kenan" ta gyada masa kai, yace "Idan bai taho ba
let me drop you people mana" ta xaro ido tace "Bayan ma yana hanya yanxu, ai shi ya
kawo mu" Yace "Ohk then...." Bata kuma cewa komai ba, shi kam yyi shiru yana
kallonta, a hankali yace "Kin yi kyau" Dauke kai tayi tana murmushi, shi dai bai
fasa kallonta ba, murya can ciki tace "Kai kuma baka sa glasses dinka yau ba" wara
ido yyi yace "Ya 6ata.... sai dai ki siya min wani" ta kallesa tace "Da gaske?"
Yana murmushin sa mai kyau yace "Yea" Sunkuyar da kanta tayi, yace "Ko baxa ki siya
min ba" Ta d'an kallesa tace "Xan siya" yace "Toh yaushe xan xo amsa?" Tace "Idan
na siya" yace "Toh gobe nake so, I can't do without it" da sauri ta kallesa sai
kuma ta dauke kai tana murmushi tace "Toh Allah ya kai mu" yace "Ameen... Da yamma
xan xo amsa" ta girgixa kai tace "A'a kawai ka bar shi next tomorrow" Shiru yyi
yana kallon bayanta.... Can yace "Or wancan ne yayan naku?" Imaan ta juya da sauri
taga motar Mujaheed yayi parking, ta gyada masa kai a hankali, tunda Mujaheed yyi
parking d'an nesa da su dama yake kallonsu, Sadeeq yace "Tunda ya gan mu bari in je
mu gaisa" shiru tayi da farko, ganin yanda yake kallonta a hankali tace "Is it
necessary?" Yayi murmushi yace "Baki son yan gidanku su san ni kenan?" D'an bude
ido tayi tace "Toh kaje ku gaisa ni xan shiga ciki in kira su Maimoon" yace "Ohk"
gate ta nufa tana satan kallon Mujaheed da ya bi ta da kallo gabanta na faduwa,
Sadeeq kuma ya nufesa, sauke glass Mujaheed yyi ya bude motar ganin sadeeq, ya fito
yana kallonsa directly cikin ido, sadeeq ya masa sallama hade da mika masa hannu,
sai bayan kusan seconds biyar Mujaheed ya mika masa nasa yana d'an murmushi wanda
iyakarsa lips, nan suka gaisa... Cikin cool voice Sadeeq yace "I am Dr Abubakar
Ahmad" Mujaheed ya gyada masa kai kamar baxae ce komai ba, sai kuma yace "Muhammad
Ahmad" Sadeeq yace "Maa sha Allah it's nice meeting you" Mujaheed yace "Same"
Sadeeq yace "Alryt xan koma, sae da safe" Mujaheed yace "Ohk... kun yi sallama ne"
Sadeeq yace "Sure" daga haka ya nufi motarsa ya shiga ya wuce. Inna bata fito
parlon Seeyama ba sai da ta kada kan sauran mutanen dake parlorn, har Mujaheed ya
gaji da jira cikin mota, Inna ta fito gate tare da Maimoon da Imaan ta shiga bayan
mota tana cewa "Mujaheed kaga Gantalallu kila da so suka yi su kwana a gidan, don
da ban masu jan ido ba baxa su tafi ba, ni dai ba ruwana" Maimoon ta bude front
seat ta shiga, imaan ta shiga back seat gun inna, Mujaheed dai bai kulata ba yyi
reverse, Inna tace "Ni bikin Imaan da na Maimoon ma gaskiya sae na xabi wa enda xa
su raka su daki, iyaka kawai in xauna bayan mota ni da su don ina fatan ya xamo
rana daya, Mujaheed ya ja mu in kai su dakunan su ya maida ni gida idan Allah ya
yarda, ba katuwar da xata bi mu" Mujaheed dai driving yake har ya bar layin ya hau
saman titi, lkci lkci ta madubi yana kallon imaan da ta ki yarda ta kalli gaban
motar, inna tace "Mujaheed kaga kawayen uwar ka kamar mayu kuwa, wllh da kyar na
kora su, duk sun ban wahala, ita ina ta samo su haka wasu lafta laftan mata ba kyan
gani kamar aladu? kaii Rukayya dai shahararriyar mahaukaciya ce wllh" taka brake
Mujaheed yyi bayan ya tabbatar bbu motar dake bayansa ya gangara gefen titi, inna
ta saki salati tace "Lafiya Mujaheed, me ya sami motar" ya bude motar ya fita ya
bude side dinta yana kallonta yace "Ita uwar tawa ce mahaukaciya?" inna ta bude
baki tana kallonsa, sai kuma ta kalli Imaan tace "Ga reshen bishiya can, sauka ki
karyo ki kawo masa...." Imaan ta hade kai da kafarta tana dariya kasa kasa, a
fusace inna ta kunduma masa xagi tace "Na ce mata mahaukaciyar sharri na mata, da
hankalinta ina ita ina gunduma gunduman matan da ta ajiye matsayin kawaye, wasun su
idan suka xaune kanta shegiya nake idan bata suma ba bayan sun latse ta" yace "Ku
saukar min a mota ku samu wanda xai kai ku gida Hajiya" kamar jira Inna take ta
sauka da sauri tana kallon Imaan tace "In dai kin san motar ba ta Bukar bace ki
sakko ki bar masa tsiyar sa" Imaan ta hade rai tace "Inna bai ce har da mu ba fa"
Irin kallon da Mujaheed yyi mata yasa ta sauka da sauri don ya dade bai mata irin
kallon ba, Inna ta kalli Maimoon tace "Ke kuma idan ba ta Amina bace motar ki sakko
kema" Maimoon ta bude front seat ta sakko, inna ta fara matsar kwalla tace "Ku sama
min Adaidaita sahu" ko kallonta Mujaheed bai yi ba ya rufe back seat dinsa ya shige
motarsa ya kara gaba, inna ta bi motar da kallo tace "Allah dai ya isa, kuma sai
Ahmadu ya min iyaka da Mujaheed yau, ni xai toxarta ya walakanta a bakin titi a kan
Rukayya" Imaan ta tsayar da adaidaita ta fada masa inda xai kai su, Mai adaidaita
yace "Ba can xan yi ba" bai gama rufe baki ba inna ta shige adaidaitan ta xauna,
Imaan da Maimoon suka saki baki suna kallonta, Mai napep din ya juya yana kallonta
yace "Baaba nace ba can nayi ba" a fusace tace "Dalla can mu je d'an nan, ko baka
ganin dare yyi ne xaka ce min ba can kayi ba, jika na ne fa ya watsar da mu a titi
yanxun nan yyi wucewarsa daga nayi ma katuwar uwarsa gyara, banda haka yaushe xaka
gan ni bakin titi tsaye da gata na, motocin 'ya yana sun fi biyar wllh, ko da yake
in mun je gidan ma xaka gane abinda nake nufi, ko kai so kake inyi ta tsayuwa kamar
yar iska bakin titi?" Shiru yyi bai ce komai ba, Inna ta kalli su Imaan sannan ta
kallesa tace "Yaro idan baxa su shiga ba ja ni ka kai ni gida, su kuma Allah ya
kawo masu mafita, mu je ni dai" murmushi mai napep din yyi, Imaan ta turo baki ta
shiga Maimoon ma ta shiga, inna tace "Atoh da kun tsaya jiran d'an sahun da xai je
ku kwana a wajen" suna isa gida dama inna ta sauka napep din ta nufi gate tana
gyara yafin mayafinta, Maimoon ta kalli Imaan dake dariya ta ja tsaki ta bude
jakarta ta fiddo dubu daya ta basa ya bata canji ta wuce ciki, can suka ga inna har
ta shige parlon su Maimoon, Imaan ta nufi part din su Maimoon ta bi bayan Inna,
babu kowa parlon Abba hakan yasa inna ta dawo main parlor tana kallon mutanen da ta
wuce da farko tace "Ahmadu baya nan ne" Daga kitchen Aunty ta leko tace "Bai shigo
ba inna, kun dawo lafiya?" inna bata tanka ta ba ta fice parlon, bata tsaya ko ina
ba sai part din su Imaan, ba kowa
parlon sai kamshi dake ta tashi, cikin daga murya inna tace "Salama alaikum" Imaan
ta bude kofar bedroom dinta tana lekowa, Inna tace "Ina Bukar din?" Daddy ya fito
daga daki yace "Har kun dawo inna" karasawa cikin parlon tayi ko takalmanta bata
cire ba ta xauna saman kujera tana share guntun hawayen idonta, Ammi dama na jin
irin sallamar da inna tayi tasan ba lafiya don haka bata fito ba, duk xaton ta
k'aran imaan ta kawo, Imaan da har ta cire kayanta ta sa Hijab kawai ta fito da
sauri, Daddy na kallon inna a hankali yace "In ji dai lafiya inna" a fusace tace
"Ina fa lafiya Bukar, shegen d'an ku ya watsar da ni tsakiyar titi gefen jaji yayi
wucewarsa, daga nayi ma Rukayya gyara" Shiru Daddy yyi yana kallonta da mamaki, ta
fashe da kuka tace "Gaskiya Bukar idan ba a bi min hakkina ba yau duk a station xa
mu kwana gwara in kai karar can a bi min hakkina, da girmana da matsayina da
martabata Mujaheed xai juye ni tsakar titi yyi wucewarsa?? Ae wannan babban magana
ce wllh" Daddy ya sauke ajiyar xuciya yace "Subhanallah me ke damun Mujaheed haka"
Inna ta tsaida kukan da take tace "Toh ai ba ni xaka ma tambayar ba, waya xaka
dauka yanxu ka kirasa, kada ma ka nuna masa ina nan, kawai ce masa xaka yi ya xo
xaka aikesa yanxun nan, daga nan sai kaji me ke damunsa ko wiwi ya fara sha bamu
sani ba" Daddy ya kara sauke ajiyar xuciya, inna tace "Sae wani sauke sauken ajiyar
xuciya kake Bukar, ko tsoron sa kake ne inyi ta kai na?" Yar dariya kawai daddy
yayi ya dau wayarsa, inna ta tsuke fuska tace "Wllh yanda ya min tijara a kan
uwarsa kai ma haka xaka masa tijara akan taka uwar, kuma idan baka ce masa aikensa
xaka yi ba wllh baxai xo ba nan kuma xa mu kwasa mu tafi police station " Daddy dai
bai ce komai ba yayi dialing number Mujaheed ba a dau lkci yana ringing ba ya daga,
Daddy yace "Muhammad kana kusa ne?" Daga daya bangaren Mujaheed yace "Eh Abba"
daddy yace "Toh ka xo parlor na yanxu" Mujaheed ya d'an yi shiru, kafin yace "Toh
Abba" Daddy yace "Don't keep me waiting fa naji kayi shiru ko baka kusa ne?" Yace
"Ina nan" Daddy yace "To ina xaune ina jiranka yanxu" Mujaheed yace "Toh" daga haka
daddy ya katse wayar, inna tace "Kai xaka kwana a ciki wllh idan yaron nan bai xo
ba Bukar" Daddy dai bai ce komai ba, Mujaheed ba don yanda yake jin kunyar daddy ba
da fa ba xai je ba don yasan sarai inna na can, kuma da Abbansa ne ma ya kirasa ba
lallai yaje ba, jallabiyarsa kawai ya xura ya fita dakinsa, banda girgixa kafa babu
abinda inna take, da sallama ya shiga parlon, ba tare da ya kalli Daddy ko ita ba
ya tafi ya xauna kasan lallausan carpet din parlon yace "Barka da dare Abba" Daddy
yace "What happened between you and ur grandma yanxu?" Mujaheed ya daga kai yana
kallonta yaga yanda ta wani tsuke fuska tana kallon sa, ya maida kansa kasa, inna
na nuna Imaan dake kwance kan kujera tana kallonsu tace "Idan sharri na masa ga
'yar ka kwance kusa da kai ka tambayeta ka ji ko ba tsakiyar titi ya juye mu ba"
Daddy ya juya ya kalli Imaan, a fusace Inna tace "Ke tashi xaune ki basa labarin
abinda ya faru, ba tsakiyar titi Mujaheed ya sauke mu ba, naga kamar tantama Bukar
yake" Imaan ta mike xaune tace "A'a ba fa tsakiyar titi bane inna, gefen hanya
ne....." Rai bace Inna tace "Amma wannan anyi shegiyar 'ya... Dama akwai bambanci
tsakanin gefen titi da tsakar titi, ke dai munafuka ce wllh" Imaan ta harareta ta
gefen ido tana turo baki ta koma ta kwanta, Inna tace "Wllh Bukar gefen hanya yayi
watsi damu, kuma kafin ya sauke ni don Allah mai yace min Imaan" da sauri Imaan ta
daga hannu tace "A'a ba ruwana nima ban sani ba" Bude baki inna tayi tana kallonta,
daddy yace "Yanxu dai ki tashi ki tafi ki bar ni da shi inna" inna tace "In tashi
in tafi ka basa hakuri shima ya tafi xaka ce min" Tana fadin haka ta mike tace "Tun
farko ma ban san me ya kawo ni gun Bukar ba, duk inda Ubansa ya tafi ai ya ci ace
ya dawo yanxu" daga haka ta fice parlon fuska daure. Daddy ya hade rai yana kallon
Mujaheed yace "Saboda baka da kirki xaka ajiye su bakin hanya Muhammad?" Mujaheed
yyi kasa da kai bai ce komai ba, Daddy yace "Yanxu ka kyauta kenan, idan Hajiyar ka
ce ko min abinda tayi maka xaka mata haka?" Yace "Kayi hakuri Abba" Daddy yace
"Haba Muhammad, I am highly disappointed at you, this is very rude and stupid of
you, she is our mother fa, no matter how she behaves baxa mu canxa ta ba" Mujaheed
bai iya cewa komai ba, daddy yace "Ka tashi ka bi ta ka bata hakuri yanxu" yace
"Toh, ayi hakuri Abba" Daddy ya kalli imaan yace "Ke kuma I've warned you times
without number ki daina fada mata magana anyhow amma baki ji ko, xan fara sa6a maki
soon wllh idan baxa ki canxa naughty attitude din nan ba, will you dare talk to ur
mother that way?" mikewa xaune tayi kamar xata yi kuka, Mujaheed ya tashi yace
"Xan je in sameta yanxu Abba" daga haka ya fita parlon. Washegari da safe da kyar
imaan ta tashi tayi wanka tayi breakfast da Ammi ta ajiye mata a dinning, Ammi tace
"Idan kin gama ki dau magungunanki ki sha kada in tuna maki, kuma da Ac kika kwana
ko?" Ta xaro ido tace "Ammi wllh A'a" Ammi tace "Toh ga mura nan na shirin kama ki"
Ta langwabar da kai tace "Jiya fa da daddare a napep muka dawo, kin ji sanyi kamar
xanyi freeze a hanya" Ammi ta fiddo kindirmo a fridge yayi sanyi sosai ta ajiye
mata a dinning din tace "Gashi ki kai ma inna inji daddyn ki, you make sure kin
goge min dinning table idan yayi stain" Ta marairaice tace "Ammi my legs are aching
me fa" Ammi ta harareta ta wuce dakin ta, Imaan na gama breakfast ta tashi ta dau
kindirmon ta tafi kai ma inna, Tana shiga parlon bayan ta ajiye tana kallon inna
dake ta kukkula dubulan da cin cin a leda sai ga Umma ta shigo parlon da sallama,
Inna ta kalleta ta ci gaba da abinda take ta amsa sallaman ba yabo ba fallasa, Umma
ta dafa kujera tace "Ina kwana inna" inna tace "Lafiya lau" Umma tace "Ya gajiyan
taro" inna tace "Bana tare da gajiya duk ya bi lafiyar gado" Umma tace "Toh
Alhmdllh Allah ya saka da alkhairi yaji k'an mahaifa" inna tace "Ameen" karasawa
tayi kusa da inna ta ajiye ledan hannunta tace "Ga wannan dai ba yawa" inna na
kallon ledan tace "Meye wannan din? Ke imaan xo ki bude" imaan dake xaune ta mike
ta karasa kusa da Inna, Umma ta bi ta da kallon gefen ido, durkusawa tayi ta bude
ledan ta ciro atamfa da pack din sabulu guda biyu da turare mai tsada" Inna ta bude
atamfar tana kallo da kyau, tace "Holland ce wannan din?" Umma tace "Ehh" inna ta
tabe baki tace "Toh, da dai basirar ki ce hakan da sai ince Allah yyi albarka, amma
wannan ko kaffara baxan yi ba Ahmadu ya sa ki, Allah ya masa albarka ya kare min
shi duk inda xai shiga, Allah ya ci gaba da hada kansu da d'an uwansa Bukar ya raya
mai 'ya yansa yayi masu albarka, ita kuma wannan da ya aurar Allah xaunar da ita da
mijinta lfya, ke kuma nagode da isar da sako" Umma ta dinga kallonta ko kiftawa
babu, Imaan sai danne dariyarta take, Inna ta ci gaba da kulla dubulan dinta a
leda, Umma tace "Sai anjima" inna tace "Mu jima da yawa" daga haka ta nufi kofa,
inna na kallon Imaan tace "To ke sai kiyi ta kanki, don wllh jiya Mujaheed ce min
yyi xai kakkarya ki ya xane ki, wai ya ganki da wani mai mota a tsaye a kofar gidan
seeyama, imaan ina kuma kika samo mai mota kike ta boye min ban sani ba ni Asabe??"
Umma ta d'an dakata bakin kofa jin abinda inna ke cewa, Imaan ta turo baki tace
"Shi sa ma xan tashi in tafi yanxu kar ya xo nan, to har kun shirya ne inna?" Inna
tace "Haba dai sai kace wata yarinya, to me yyi min da baxa mu shirya ba, wai na ce
ma Rukayya mahaukaciya, ke ki ji fa? to me ta min xan xageta banda abunsa ma dai,
kawai daga ina mata gyara? Ni fa na yarje ma Ahmadu ya aureta wllh, baki ganta ba a
lkcn yar siririya yanda kika ganki, kamar iska xai hure 'yar banxa ta fadi, gashi
iyayenta basu da komai basu kuma ba wani ajiya ba, wani d'an akurkin gida fa gare
ubanta a lkcn, to ni ban masu bakin ciki ba don xuciya ta fess mai kyau ne na yarda
Ahmadu ya auro mana ita a haka, ke kinga wahalar da nayi da ita kuwa? Wllh kare
baxai ci ba, gashi ba abinda ta iya a lkcn, har girki ni ke sa ta kan hanya ina
koya mata, kishiyoyina su yi ta jin haushi yanda nake ji da ita bana son ko k'uda
ya ta6ata har dai ta samu cikin wannan yaro Mujaheed, sai kin ga wahalar da nayi
mata sbda laulayin da ta dinga yi ba kakkautawa, to ni duk ba wannan ba don nasan
sakayya ta dai na gun Allah, to don kuma yanxu Rukayya ta xama abinda ta xama sai
me xai dameni ni patuu? ga dai Amina na bina sau da kafa ga Aisha, ni dai abinda na
sani shine Mujaheed ai xai yi auren, to nan xata d'an dana ko da dadi ko babu,
abinda duk abinda ka shuka shi xa ka girba, tsaf xan karance ma yarinyar xaman da
xata yi da ita, muna nan da ku sai an dinga xuwa daukata shari'a a mota...." Imaan
har wani kwanciya tayi kan kujera tana dariya amma ba mai sauti ba, Umma da ta
makale jikin kofa ta fita ta sa takalmanta, inna ta tabe baki tace "Wllh Mujaheed
da gwiwowinsa bibbiyu ya durkusa ya dinga ban hakuri tun ban kai ga gaya ma ubansa
ba, to tunda naga yyi nadama kawai sai na yafe masa don ba halinsa bane gaskiya bai
taba juye ni a tsakiyar titi ba tunda mu ke" Imaan ta fashe da dariya tace "Jiya
dai ya juye ki ai"

*The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included
in the payment group.

19. Imaan

Umma na komawa bangarensu kallo daya tayi ma Mujaheed dake xaune dinning yana shan
coffee tace "Ka sameni daki yanxu" sosai gabansa ya fadi ya bi ta da kallo har ta
haura sama, bai iya ya karasa shanye coffee din ba ya mike ya bi bayan ta, tsaye ya
ganta tana safa da marwa a dakin, Yace "Gani Umma" ta juya tana kallonsa fuska
daure tace "Mujaheed ina son sanin meye matsalar ka don kaga shegiyar yarinyar nan
da mai mota jiya har kake ikirarin hukuntata" ya xaro ido yace "Ban gane ba Umma"
Ta masa wani mugun kallo tace "Bana son ka gane dama ai, warce kaje ka ba sakon
take fadi yanxu naji, dama baka raba kanka da makiyan nan nawa ba har ynxu
Mujaheed? Mujaheed ka gaya min meye hadin ka da yarinyar nan Imaan?" Yace "Haba
Umma, ke yanxu maganar inna kike dauka, kila ma don ta ganki yasa ta kirkiri haka,
ni a ina na ganta har muka yi wannan xancen da ita?" Shiru Umma tayi tana kallonsa,
a ranta kuwa tunani take kila hakan ne ma, ganin Umma tayi surrender, Mujaheed yace
"Kawai ta fada haka ne don ki sa a rai, ni yaushe nake da wannan lokacin ma a gidan
nan yanxu" Umma ta sauke ajiyar xuciya tace "Sae ma kaga rashin mutuncin da ta min
kayan da na kai mata, ni na ma ji dadin da ta gane cewar in don ta nine baxan bata
ko tsinke na ba, basirar Abban ku ne kamar yanda ta fada" Mujaheed yyi murmushi bai
ce komai ba, Umma tace "Gobe xan baka sako ka kai ma Hajiya Mansura ta marafa, bata
samu xuwa bikin ba amma ta bada gudunmawarta dubu dari, cin cin da su alkaki xaka
kai mata daga nan nasan xa ku hadu da Safeenah, tana nan ba ta koma makaranta ba,
ni so nake nan da 'yan watanni a fara xancen naka bikin" shi dai Mujaheed bai ce
komai ba banda kallonta da yake, ta xauna gefen gado tace "Kar fa kace min ka manta
gobe kayi ficewarka, xuwa sha biyu in sha Allah xaka kai masu, tunda gobe lahadi"
ya shafa kai yace "Allah ya kai mu" daga haka ya nufi kofa ya fita. Imaan ta kara
leka samirar dake cike da cin cin da dubulan da alkaki da inna ta basu su kai ma ta
rasulu aminiyarta, ta tabe baki tace "Wllh duk kin kwashe ma tsohuwar, mu fa har
ynxu ba mu ci ba" inna ta tsuke fuska tace "To ina ruwana da rashin cin ku, ni na
aurar da 'ya ko ko? Kaji min dai, Dubu talatin ta rasulu ta bada a kawo min
gudunmawa, kuma ace baxan cika mata samira da kayan flawa ba, ni ta ma fi min Aisha
kiji in gaya maki" Imaan tace "Kice ma ta fi maki har daddy mana" Maimoon tace "Toh
ina dubu talatin din?" Inna ta kalleta da sauri tace "Amina aka ce in ba wa da xaki
tambayeni dubu talatin Maimuna? Ko ko kin ban ajiya ne? Ni dai ku daina sa min ido
a gidan nan, idan ba haka ba mugun alkaba'i ba shi da kyau amma to xance kowa ya ci
kansa gaskiya" Imaan ta kalli Maimoon tace "Maimoon karbo kudin motar mu wuce" Inna
ta kunce ha6ar xaninta ta fiddo naira dari ta ajiye masu tace "Hamsin xai kai ku ya
dawo da ku, nan nan kabala dai" Imaan ta ajiye samirar ta xauna tace "Tabdi ko
naira dari dari ma baxa a yarda a kai mu ba balle hamsin" Inna tace "Barawo ne mai
adaidaitan da baxai kai ku a hamsin ba, ko ya sha wiwi ne, wllh kullum a hamsin ake
kai ni a dawo da ni" Maimoon tace "Saboda ke tsohuwa ce ai" A fusace inna tace "Oh
oh Allah, idan baxa ku ba ku ajiye min kayana ku fita, Xan kira Bukar ko Ahmadu
cikinsu wani ya kai mun, ku fitar min a parlor" Kin fita suka yi jin abinda tace
wai xata kira daddy ko Abba, Maimoon tace "Toh wai don Allah mu muka siya masu
adaidaitan da xasu kai mu a hamsin su dawo da mu a haka, ki kara mana kudin mu tafi
mana" Inna ta jefa masu wani hamsin tace "Aniyar ku ta bi ku dai" Maimoon ta dau
kudin tana gunguni tace "Ae sai dai mu cika da kudin mu" Imaan ta tabe baki ta dau
samirar tace "Sai dai ke ki cika, sisina baxan kara a kai ba tunda ba ni xan ci cin
cin ba" daga haka ta fice parlon, inna tace "Shi sa har yau aka kasa gano cutar da
ta sa ki gaba, saboda mugun xuciyar ki da rashin kunya, ni dai Allah ya saka ma
d'ana, Allah ya saka masa kan kudaden da yake kashewa a kan tsadadden ciwon nan
naki, Allah kuma ya raba shi dake lafiya, ya aurar dake ya huta ma ransa mijin ma
ya d'and'ana ukubar, ba a taba jin alkhairi ya fito bakin ki sai sharri, to meye
kuma don kin cika kudin mota" Maimoon ta bi bayan imaan ta kullo mata kofarta tana
turo baki. Suna tsaye bakin titi suna jiran adai daita da xai je kabala, Imaan tace
"Ko da yake nasan tsohuwar da xa mu kai ma baxa ta bar mu haka nan ba, kila ta ba
mu kudin mota" Maimoon tace "Wllh da ba dan Abba da tace xata kira ya kai ba ba
inda xanje ni dai, kullum fa idan xata aiki mutum sai ta raba kudin motar xuwa
wajen kashi uku ta baka daya" Imaan tayi dariya tace "Kawai so take ayi ta mana
fada shi sa tace xata aiki daddy ko Abba" motar Mujaheed da suka gani yasa suka yi
shiru suna kallon motar, shi ma daga gida ya fito, ya sauke glass yana kallon
Maimoon, Maimoon ta marairaice tace "Ya M.A inna ce ta aike mu kabala kuma ba mu
samu adai daita ba har ynxu..." Ya gyada kai yace "Toh Allah ya kawo adai daitan"
xai dage glass da sauri tace "Wait... Kai ina xaka plss?" Yace "Marafa" tace "Toh
ka rage mana hanya mana don Allah" ya mata wani kallo yace "Me ya hada Marafa da
kabala?" Tace "Yaya ai duk hanya ce mu dai ko ina ma ka ajiye mu nasan xa mu samu a
can gaba" yace "Toh shiga" Imaan ta bude back seat ta shiga ya dinga hararanta ta
madubi fuska daure, dama tun da suka hada ido taga kallon da yake mata bata sake
yarda ta kalli madubin ba, Maimoon na kallon fancy nylon dake gaban motar ta dauka
tace "Ya M.A wa xaka kai ma cin cin da dubulan?" Yace "Anty" dariya tayi bata sake
cewa komai ba, sai da suka yi nisa yace "Gidan Baaba ta rasulu xa ki kenan?" Tace
"Xa mu dai, ai ba ni kadai bace, ni da Imaan ce" ya watsa mata wani kallo ta xaro
ido tana yar dariya ta rufe bakinta, har kofar gidan aminiyar inna ya kai su,
Maimoon sai murna take tace "Ya M.A mun gode, ko mu raka ka marafan mu ma?" Shiru
ya d'an yi da farko yana shafa kansa a hankali, lkci daya yace "Toh kar ki dade a
ciki idan ba haka ba inyi wucewata" bude motar tayi ta fita tana kallon Imaan da ta
fita tuntuni tana cinno baki suka shiga gidan, dari biyar ta rasulu dake ta sa masu
albarka ta basu kudin mota, tace "Ina gaida Hajiya Asaben, kuyi mata godiya sosai,
ita kuma amarya Allah ya basu xaman lafiya da mijinta, ku kuma Allah ya maku
albarka ya fiddo maku maxaje na gari" suka amsa mata da Ameen, sannan suka mata
sallama suka fita da samirar don juye kayan ciki tayi a nata samiran. Maimoon na
kallon imaan tace "Wai Imaan me yasa baki gaida ya Mujaheed yanxu?" Imaan tace
"Saboda baya gaida Ammi na sai ya ga Daddy" Maimoon ta xaro ido tace "Da gaske?"
Imaan tace "Ehh mana" Maimoon tace "Toh saboda me" imaan tace "Oho" bude back seat
tayi ta shiga Maimoon ta shiga gaba ya tada motar yayi reverse ya bar anguwar.
Tafiyar kusan minti sha biyar suka yi suka iso gidan Hajiyan Marafa, Dai dai gidan
yayi parking daga kusa da flowers yana kallon Maimoon yace "Xan yi sllh kafin in
shigo" ya mika mata ledan yace "You take this in with you" tace "Amma yaya bamu san
kowa a gidan ba fa" yace "Sai ki ce Hajiya ce ta aiko ki, ina nan shigowa nace idan
nayi sllh" daga haka ya fita motar, Imaan dai na tsaye ta rungume hannu jikin motar
bayan ta fita, Maimoon ta fito ya kulle motarsa da lock, ya wuce masallacin da ya
gani a layin, Maimoon ta kalli Imaan tace "Mu je" bin bayan ta Imaan tayi suka
shiga gidan, bayan sun sanar da mai gadi gun Hajiya suka xo, duk girman gidansu
haka suka saki suke kallon gidan, Maimoon tace "Ni dai baxan shiga ba gwara mu jira
sa a nan, kawai mutum yaje yana ta introduction ana masa wani kallo" Imaan ta yi
dariya tace "Sai kice Hajiya Rukayya ce ta aiko mu" Maimoon ta buda ido tace "Bari
ya Mujaheed ya jiki, wai Hajiya Rukayya" Imaan ta tabe baki suka shiga babban
balcony din dake dauke da kujeru sannan ga babban rug a shimfide kasa, kan rug din
suka xauna suna kara k'are ma gidan kallo, sai bayan da aka idar da sallah Mujaheed
ya shigo gidan, kallonsu ya tsaya yi ya hade rai yace "What did I tell you
Maimoon?" Ta marairaice tace "Yayanmu mun yi sallama kamar basa parlor" hararanta
ya dinga yi kafin ya danna bell, ko minti daya ba ayi ba mai aiki ta bude kofar, ta
gaishesa ya amsa yace "Hajiya tana nan?" Tace "Wa xa ace mata" Yace "Dr Muhd, Kice
Hajiya Rukayya ce ta bada sako a kai mata" Murya can kasa Imaan tace "Toh ba gashi
shi ma cewa yayi Hajiya Rukayya ba" Maimoon ta yi murmushi bata dai ce komai ba,
Mai aikin tace "Toh ka shigo" bin bayan ta yayi xuwa cikin parlon da sauri imaan ta
mike ta bi bayansa, Maimoon na yar dariya ta tashi ita ma ta shiga parlon, wata
yarinya da baxata wuce ashirin da daya bace ta shigo parlon daga dinning kallo daya
tayi masu ta wuce sama, tsaki imaan ta ja Mujaheed ya kalleta ta cinno baki ta
dauke kai, mai aikin ta kawo masu drinks da bottle water ta ajiye, bayan wani lkci
sai ga Hajiyar ta sakko cikin shiga ta alfarma ganin Mujaheed tace "A'a ashe kai ne
doctor" yyi kasa da kai yace "Ina yini Hajiya" tace "Lafiya Alhmdllh, ya Hajiya
Rukayyar, fatan an watse taro lafiya" yace "Alhmdllh" xaunawa tayi tana kallo su
Maimoon da Imaan dake gasiheta tace "Wannan kamar kanwar khadijah da tayi aure Us
koh?" Ta fadi haka tana nuna Maimoon, Mujaheed yace "Ehh kanwarta ce" tace "Maa sha
Allah ga kamanni na gani, to ita wannan fa" Mujaheed ya kalli Imaan da ta nuna, da
sauri yace "Yar uwarsu ce" tace "Allah sarki shi sa ban santa ba" Maimoon ta mike
ta ajiye abun hannunta kusa da ita tace "Gashi Hajiya tace a kawo maki" Hajiyar
tace "To maa sha Allah, nagode kwarai Allah ya basu xaman lafiya" Bude kofar parlon
aka yi, wata yarinya ta shigo parlon cikin English wear bata ko kalli wa enda ke
xaune parlon ba xata wuce sama Hajiya tace "Safeenah lafiya na ga ranki a bace" Jin
sunan da Hajiyar ta kira Mujaheed ya daga kai yana kallon yarinyar, ita ba doguwa
ba kuma ba gajera ba, farin ta har yayi yawa and she is beautiful, lkci daya ya
dauke kansa, Maimoon da Imaan kuwa kamar sun samu TV imaan har da juyawa gaba
daya tana facing dinta, rai bace Safeenar tace "Wai ki ji mum ashe birthday din ma
wani local waje xa ayi, sai kinga yanda raina ya bace bayan duk shirin da nayi,
wllh Saleema koluwa ce I don't know what's wrong with her, ni ko gaya masu na tafi
ma ban yi ba" Mujaheed dai sai danna wayarsa yake, Hajiya tace "Atoh gaskiya basu
kyauta ba, to why not baki ce masu a canxa hall din ba, ko ke ba sai ki biya kudin
hall din ba" Tsaki Safeenah tayi tace "Ni duk raina ya baci wllh Mumy" xata wuce
sama Hajiya tace "Toh ga doctor ku gaisa" Juyowa tayi tana kallon cikin parlon taga
Mujaheed da ya ki dago kansa, ta fi second goma tana kallonsa, kafin ta karasa
cikin parlon ta xauna hannun armchair da uwarta ke xaune cikin sanyayyen murya tace
"Ina yini" sai a sannan ya daga kai yace "Lafiya lau, ya kike?" Tayi wani sanyayyen
murmushi tace "Lafiya lau" Ta kalli su Imaan tace "Sannun ku" Imaan dai tace
"Yauwa" Maimoon kuma ta gaisheta, Hajiya ta kwalo ma mai aiki kira ta fito da
sauri, Tana kallonta tace "Pepper chicken da ku ka yi daxu xa ki kawo masu tun da
ba ku gama lunch ba" Mujaheed yace "Daga gida muke yanxu Hajiya, we ate before
leaving, so we are okay" tun da ya fara magana Safeenah ke kallonsa ko kiftawa babu
har ya dasa aya, Hajiya tace "Wannan ae is more or less a dessert, daxu yara suka
ce suna son pepper chicken, shine nasa su yi, kuma da yawa sosai suka yi don nasan
baxa a cinye gaba daya yau ba sai dai a ba masu gadi da almajirai" Mujaheed ya d'an
yi murmushi yace "Ni dai I am okay" Imaan tace "Ni dai xan ci" kallonta yyi da
sauri, Hajiya tace "Yauwa, bar sa yayi ta fulako dama yayi kama da fulanawan, ke ma
ai xa ki ci ko" Hajiya ta fadi tana kallon Maimoon, Murmushi kawai Maimoon tayi ta
sunkuyar da kanta, mai aiki ta dawo rike da tray da plates uku a kai, ko wanne
dauke da kaxa da aka yi garnishing sai kamshi da turiri yake, Mikewa Safeenah tayi
ta dau plate daya ta karasa kusa da Mujaheed ta ajiye masa, hada ido suka yi yace
"I said I am okay baxan ci ba" tace "Kaci ko kadan ne pls" Daga haka ta koma ta
xauna, a hankali Imaan ta xamo kasa ta fara cin kazar, sai kallonta Mujaheed yake
ta gefen ido, Maimoon ta dau tsoka daya daga kan kujerar tana ci a kunyace, Hajiya
tace "To ya aikin doctor, Hajiya Rukayya tace min ka dawo Kaduna da aiki gaba daya
yanxu koh?" Yace "Ehh" tace "To da kyau, Allah yayi albarka" yace "Ameen" idonsa na
kan wayarsa amma da ya dago sai yaga kallonsa Safeenah take, Hajiya ta mike tace
"Toh bari in d'an shiga ciki...." Mikewa yyi da sauri yace "Wucewa xa mu yi ai, xan
je gun aiki" tace "Da wuri wuri haka, ka dai ki shan ko ruwa ne kuma ban ji ddi ba"
yace "Am sorry bana jin cin komai ne yanxu" Tace "Toh ai sai ka jira kanninka su
gama tukun na ko?" Yace "Bana son in makara xuwa gun aiki ne Hajiya" tace "Toh
shikenan, bari a masu take away da shi" Imaan tace "Toh" wani kallo Mujaheed ya
dinga mata, Hajiya ta kwalo ma mai aiki kira ta sanar da ita tayi masu takeaway din
kajin, Imaan ta mike tace "Ina xan wanke hannu" Safeenah ta nuna mata hanyar
dinning ko kitchen, tare suka tafi da Maimoon suka wanke hannu suka dawo, Hajiya ta
basu dubu biyar Maimoon ta amsa da kyar, tuni Mujaheed ya fice gidan suka bi
bayansa, Hajiya ta kalli Safeenah tace "Baxa ki raka su ba" bin bayan su tayi ita
ma. Mujaheed har ya shiga mota sai ga ta tare da su Maimoon, tana kallonsa tace "I
don't even know ur name" ba tare da ya kalleta ba yace "I am Mujaheed" tace "That's
nyc, I am Safeenah" kai kawai ya gyada mata, Tace "Toh sai yaushe?" Yace "Watarana"
yar siririyar dariya tayi tace "Do you mind sharing your digit with me pls?" Yace
"Ohk" mika masa wayar hannunta tayi ya amsa ya sa mata lambarsa da bai fiye amfani
da ba ya mika mata, tace "Thank you" yace "You are welcm" Daga haka ya tada motarsa
ya wuce, haka ta bi motar da kallo har ya fita layin, da sauri ta koma ciki tana
kallon uwarta tace "Wllh Mum naji ina son sa sosai" Uwar tace "Haba, to ai shine
wanda na maki magana a kai kwanaki kika ce ke ba ruwan ki da hade hade in rabu da
ke, uwarsa ce dama ta kawo shawarar ba ni ba tunda nasan kina da samari iri iri" ta
marairace tace "Mum ai ban san haka yake ba, ni wllh mum ina son sa har raina"
Hajiya tace "To ai shikenan, bari anjima sai in kira mahaifiyar tasa dama kwanaki
duk ta dameni da kira a kan hakan bana daukan kiranta" Safeenah ta sauke ajiyar
xuciya ta xauna tace "kaiii... Ya hadu wllh, his beards are damn cute, his lips so
sexy with those catlike eye, gashi dogooo, I guess he have got six packs daga
ganinsa yana workout, dama kuma ni bana son namiji fari pau, wllh Mum gayen ya hadu
sosai, kuma naga sai wani basarwa yake yana shan kamshi, to ai irinsu nake so" Tun
da Imaan taga irin kallon da Mujaheed ke mata bayan sun dau hanya ta kagu su isa
gida ta fice daga motarsa tayi ta kanta, gashi dama so take suna komawa gida ta dau
Atm card ta tafi supermarket siyo ma Sadeeq abinda ta masa alkawari jiya, a kofar
gida Mujaheed yayi parking tana jin ya bude lock din motar ta bude ta fita da
sauri, fitowa yayi shi ma bai kai ga bin ta ba tayi tuntunbe bakin gate sai ga ta a
kasa, d'agata yyi ta fashe da wani matsanancin kuka tana cewa "Wayyo yaya kafana ya
gurde wllh" maidata gun motar yayi fuska daure ya daga kanta yace "Waye kika fita
wajensa shekaranjiya da daddare" k'in cewa komai tayi sai kukan da take tana kiran
daddy a tsorace, ya wani hade rai cikin tsawa yace "Ba tambayar ki nake ba?" Still
taki cewa komai xuciyar ta Sai bugawa yake, murda kunnenta yyi da karfi yace "Are
you daft" ta kara rushewa da kuka tace "Don Allah kayi hakuri" yace "Waye shi"
cikin kuka tace "Nima ban san shi ba yaya" Ji yake kamar ya sauke mata mari ya
dinga mata wani kallo xuciyarsa na tafarfasa, he is just trying hard to control his
temper, strictly yace "Toh daga yau Imaan, I mean daga yau.... na sake ganin ki da
wani a tsaye wllh sai na kusa sumar dake a gidan nan I promise you that, ba ciwon
jiki ko Asthma ba, idan ma jini ke xuba ko ina na jikin ki wllh sai nayi abinda na
maki alkawari, ke har guda nawa kike xaki ke tsayawa da namiji jikin mota? How old
are you??" Kuka kawai take tana kallonsa duk jikinta na rawa don ta dade bata gansa
cikin yanayin nan ba, ya mata tsawa yace "Baxa ki bani amsa ba sai na gaura maki
mari?" Cikin rawar murya tace "Ba na kusa 18 ba...." Rankwashi ya kai mata ta dafa
wajen tana kiran inna a rikice, yace "In sake ganin ki da wani a waje, sai kin
raina kanki wllh" daga haka ya saketa ya rufe motarsa, ta wuce ciki da sauri bata
xame ko ina ba sai part din inna, xubewa tayi kan kujera tana rusa kuka, Inna ta
fito daki da gudu tace "Na shiga uku me ya same ku a hanya, ko hatsari ku ka yi??"
Imaan ta mike xaune cikin kuka tace "Yaya ne ya rankwashe ni kuma ya ja min kunne
ni ban masa komai ba innaa" Inna ta xauna kan kujera tayi tagumi a hankali tace
"Naga abinda ya isheni bai ishi Allah ba, Wannan yaro dai ya isheni a gidan nan
wllh, innalillahi wa inna ilaihi raji'un, A kan wani dalilin kuma ya cuce ki, me
kika masa?" Xata yi magana sai ga shi ya shigo, kin cewa komai tayi sai shessheka
take hawaye na bin kuncinta, inna tayi mitsi mitsi da ido tace "Mujaheed kana manta
cewar akwai hisabi koh, kana mance akwai lahira koh, ni ina jiye maka kada wataran
ka karasa gawar da ba taka ba a gidan nan, idan abu ya sami yarinyar nan gaskiya
xan rufe ido in mance ni na haifi Ahmadu in maka tijara kotu ta raba mu Mujaheed,"
Yace "Toh yanxu ma ki tashi a tafi kotun mana, duk ke ke karanta mata tsayawa da
samari tun bata kai ko ina ba a titi, idan aure take so ae sai ta sanar da Abbanta
ayi mata ba ta dinga tsayuwa da maxaje ba tare da saninsa ba, ita har nawa take, ni
nasan wlh Abbanta bai sani ba, halan Ummi bata bata labarin abinda na mata kwanaki
ba" Inna ta saki baki tana kallon imaan dake shessheka a hankali, can tace "Amma
gaskiya ke munafuka ce Imaan, samm baki da hali, banda munafurci ya xa ayi kiyi
sabon saurayi amma kiyi ta nuku nuku kina boye min?? me xai bani da Allah bai ban
ba, shi kuma gantalallen bai san kakarki na da rai bane da bai taba cewa xai shigo
gaisheni ba? Ko uwar ki ce tace ki boye min ban sani ba" Mujaheed ya dinga kallonta
da mamaki, rai bace inna tace "Toh ni dai ba ruwana, dama ana boye abun arxiki irin
wannan Ashe, me na maki da xaki boye min sabon saurayin ki Imaan?"
20. Imaan

Juyawa Mujaheed yyi ya fice daga parlon, Imaan ta kyabe baki tana share idonta tace
"Shi fa bai san ko waye doba xai wani dinga ce wa saurayina, ni dai wllh inna ku ce
masa ba ruwansa da ni a gidan nan" inna tace "Atoh dama meye hadin ki da shi, kawai
ni dai nasan ubansa wan ubanki ne kuma duk ni na haifesu, to bayan wannan bbu
abinda ya hada ki da Mujaheed ba dangin iya balle na baba, ke dai kawai ki rabu da
shi ya ji da wawancin sa kiyi ta kan ki, banda fitina ma ina ruwansa da lamarin
rayuwarki, idan ma saurayin kika yi baki isa ba ne, ko idan kin rasa mijin aure
astaghfirullah shi xai aure ki ne?? kar ki sake saurarensa duk saurayi ya kira ki
shirya ki fesa turare ki tafi, wa xai xauna biye ta Ahmadu da Bukar ga d'an su ma
ya dauko hanya, bokon jaraba kawai ni wllh kina gama sakandari aurar da ke xance
ayi mijin yaji da lalurorin ki d'a na ya huta haka shi ma" imaan ta mata wani kallo
ta mike tana goge guntun hawayenta ta fice a parlon. Da yammacin ranan daddy ya
gama shirin komawa Abuja ya tafi yi ma Inna sallama, ta gama goge gogen da ta ke ta
dawo ta xauna tace "Tafiyar na nan yau din kenan" yace "Ehh, jirgi xan bi kada
jirgin ya tashi ba ni" inna tace "Toh Allah ya tsare, amma xaka tafi kuma ya xancen
da ku ka min kai da Ahmadu jiya?" Daddy yace "Na me fa?" Inna tace "Tafiyar yaran
nan su je gaida Hansatu mana" Daddy yace "Ehh Barrister yace xuwa satin da xa a
shiga sai su tafi" inna tace "Ehh gwara su je, duk da dai uwarta axxaluma ce amma
ina mata fatan Allah ya ji kanta na kuma yafe mata, amma gaskiya shari'ar mu sai a
lahira, don ta cutar da ni...." Daddy yace "Haba inna, bayan kuma kin ce kin yafe"
a fusace inna tace "Toh ai Allah ba axxalumin bawansa bane, don na yafe ai a duniya
nake nufi ba a can ba, kai baka san komai ba wllh, kaga irin abinda uwarta tayi min
ne, kishi dama hauka ne, ni dai kawai albarkacin marigayin uban ku yasa nake barin
ayi xumunci da 'ya yan da ta mutu ta bari ma, kuma duk yaran ba xuwa gaida ni suke
ba" Daddy yace "Ke fa kika ce kin yafe xuwan, kowa ya xauna inda yake" Inna tace
"Toh idan bance haka ba ya kake so ince, kai so kake su xo su sa ma kai da d'an
uwanka ido, yanxu da ake nisa nisa ba ya fi ba, babu wanda yasan halin da wani ke
ciki, sai ku dinga wata magana kai da Ahmadu don ba ku aka cuta ba, yanxu
kishiyoyin da bani da hakkinsu ba gashi duk sun mace sun bar 'ya ya duk a gantale
ba, to me xa su xo su min bayan ga nawa 'ya yan... Ku uku wllh kun isheni xaman
duniya ita ma Hadiza tace ta kusa dawowa kasar nan gaba daya, to me xai dameni, a
hada masu goma ta arxiki aje dai a gaishesu, har shi wancan katon Balan dake Abuja
su karasa su gaida shi, ba komai Allah ya ba mu lada su kuma aniyarsu ta bi su"
Daddy yace "Bari in je inna, Mujaheed xai kawo maki sako anjima" tace "Toh Allah ya
tsare, yayi maka albarka, ya kare ka duk inda xaka shiga" yace "Toh Ameen nagode"
daga haka ya fita parlon, part dinsa ya tafi suka yi sallama da Ammi yace "Gobe dai
Imaan ta tafi islamiyya, xuwa Wednesday nasan xa su yi tafiyar, before than Dr
dinta xai kawo mata drugs dinta coz ya dawo" Ammi tace "Toh Allah ya kiyaye hanya
ya tsare, ko in taso ta?" Yace "A'a bar ta" daga haka ya nufi kofa ya fita, Yusuf
ne ya kai sa airport. Mujaheed ya daga kai yana kallon Abbansa bayan ya gama
maganar da yake, a hankali yace "Abba kaga ba a dde da transferring dina nan ba da
har xan fara daukan leave gun aiki...." Abba yace "You are just lookin for excuses,
na lura gaba daya baka son tafiyar Muhd" ya sunkuyar da kai yace "A'a ba haka bane
Abba, kawai naga...." Abba ya dakatar da shi yace "Toh xan ma boss din naka magana"
da sauri ya dago yana kallon Abba amma bai ce komai ba, Abba yace "Beside idan ku
ka tafi Wednesday xuwa Friday ai kun dawo, nan nan sulejah dai" Mujaheed bai ce
komai ba still, jin Abba ma yyi shiru yace "Toh Abba kasan yanayin jikin Imaan, har
da ita xa mu je?" Abba yace "Toh ba ga ka ba, you just go with first aid box"
Mujaheed yace "Toh shikenan" Abba yace "And ina son dama muyi wata magana Mujaheed"
Mujaheed yace "Ina ji Abba" Abba yace "Its high time you think of settling down
with a family Muhd, naga baka san shiru ba kai, idan na kyale ka a haka xa ayi ta
tafiya, duk abokanka sun yi aure with kids, not even kid, to kai me kake jira son?"
Ya shafa kai a hankali yace "Abba warce nake nema tana karatu ne, amma ta kusa
karewa nan da 'yan watanni in sha Allah" Abba yace "Yar ina ce?" Ya d'an yi
murmushi yace "Nan Kaduna, a hayi iyayenta suke amma tana gun yayarta a Unguwar
sanusi" Abba yace "Toh maa sha Allah, hakan yayi kyau sosai, but I think it's
better a fara magana tun yanxu...." Muryar Umma suka ji tace "Babu maganar da xa a
fara Alhaji" duk suka daga kai suna kallonta ta karaso cikin parlon, bacin rai
karara fuskarta tace "Yanxu ni xaka munafurta Mujaheed, haka muka yi da kai, to
kasani wllh idan ina numfashi a doron kasa baxa ka auri yarinyar nan bar, idan kuma
kana son ganin ba dai dai ba a lamarin ka kaci gaba da alaka da matsiyaciyar
yarinyar, ina zamana ka dauko mun talauci a matsayin surka, to wllh kayi kadan
gwara kayi ta xama ba auren ya fi, ga yarinya mai hankali mai natsuwa Safeenah yar
wajen Hajiyan Marafa can na nema maka yarinyar kuma tayi mugun na'am da kai xaka
toxarta ni ka maidani karamar mutum a idonsu???" Abba yace "Abinda nake son in fara
fahimta a nan shine, la6e kike min Rukayya?" Umma ta tabe baki tace "Idan ma la6en
nayi Allah ne yasan bani da hakkin kowa shi sa har ya bani ikon labewan in ji
komai, Alhaji wato idan Kasan talauci to a kan yarinyar da iyayenta ya kare, can
wani ghetto fa suke, to idan ba toxarta mu Mujaheed ke son yi a idon jama'a ba ina
shi ina yarinyar nan, Kyan banxa kyan hofi, yo ina ma take da kyan ita ba wai fara
ba, gaskiya kayi min iyaka da Mujaheed kada in nuna masa 6acin raina a gidan nan,
sam baxai ji da dadi ba, shi baya koyi da d'an uwansa Yusuf, dubi fa yarinyar da
yake nema yar attajiri gashi har magana yayi nisa, sai ni ce Mujaheed xai cuta ya
kwaso min yar talakawa" Abba ya girgixa kai yace "Halan ke ke raba talauci da
arxikin Rukayya?" Umma tace "Ba ruwana da wannan xancen ni dai gaskiya idan
Mujaheed bai yi hankali da ni ba xai sha mamaki, kuma in dai baxai bi ni sau da
kafa ba xai dinga ganin ba dai dai ba a lamarin sa ni dai ba ruwana" tana kai wa
nan ta fice fuuu, Abba ya girgixa kai yace "Look son, ba ruwanka da wannan uwar
taka, ba isasshen hankali gareta ba am giving u my words, ka ci gaba da neman
yarinyar, Allah ya shige mana gaba" A hankali Mujaheed yace "Ameen" Abba yace "You
can go" ya mike yace "Nagode Abba" daga haka ya fita parlon. A hankali Ammi ta bude
kofar dakin Imaan tana kallon ciki jin dariyar da take cikin duvet, da sauri Imaan
ta katse wayar ta tura karkashin pillow jin kamar an bude kofa, Ammi ta kunna wutan
dakin tace "Da wa kike waya Imaan?" Bude duvet din tayi kamar mai bacci ta mike
xaune tace "Na'am" Ammi ta mata wani kallo tace "Baxa ki amsa min tambayata ba, da
wa kike waya nace?" Shiru tayi tana kallon Ammi kamar xata yi kuka, Ammi ta karasa
kusa da gadon tace "Bani wayar" ba musu ta ciro wayar ta mika ma Ammi, Ammi na
kallon call log tace "Number waye wannan din" murya can kasa Imaan tace "Abokin ya
Muhsin ne" Ammi tace "Me ya hada ki da abokin Muhsin, a ina kika san sa?" Tace
"Ammi yana xuwa gidan gwaggwo kuma kanwarsa classmate dita ce, yanxu ma kawai
tambaya ya kira ni yake min ba wani abu ba" Ammi ta dinga mata wani kallo, ta
sunkuyar da kai, Ammi tace "Ke dai kin iya munafurci" kamar xata yi kuka tace "Ammi
ni wllh dai ya kira ni ne amma ba komai fa" Ammi tace "Toh yayi kyau, ki bude kunne
sosai ki saurareni, kada ma ki nuna nasan kina waya da wani a gidan nan don ba
ruwana, duk ranan da Daddyn ki ya kama ki dama ki tanadi abun gaya masa don't
involve me in this" tana kai wa nan ta fice dakin. Washegari da rana Ammi na xaune
parlor Imaan ta fito sanye da Hijab sai karamar jakarta da ta rataye, Ammi na
kallonta tace "Ina xa ki?" A hankali tace "Ammi xan je in siyo cream a supermarket"
Ammi na kallonta da mamaki tace "Yaushe na siyo maki da har ya kare Imaan?" Shiru
tayi tana kallon Ammi kamar munafuka, Ammi tace "Shan cream din kika fara?" Tace
"Ammi shafawa kawai nake yi fa" Ammi ta tabe baki tace "Toh ni kam bani da kudin
cream yanxu" tace "Ai ina da kudi a account dina" Ammi tace "Toh Hajiya mai kudi, a
dawo lafiya" yar dariya tayi ta sa flat shoe dinta ta fita parlon, kamar mai
tausayin kasa ta taka har bakin main road inda xata samu adai daita, jin wayarta na
vibrate a jaka ta fiddo, Sadeeq ta ga ke kiranta, ta daga ta kai kunne, Cikin cool
voice dinsa yace "How r you Imaan?" A hankali tace "am fine ina yini?" Yace "Lafiya
lau, kina hanya ne?" Tace "Ehh" yace "Ina xa ki?" Ta d'an yi shiru kafin tace
"Xanje supermarket" yace "Wanda muka hadu ranan?" Tace "Ehh" yace "Tell me what you
want to get sai in siyo in kawo maki yanxu" da sauri tace "A'a bana so" a hankali
yace "Why?" Tace "Ni dai bana so, yanxu ma xan hau adai daita ai" yace "Toh
shikenan, we will talk later, Allah ya tsare" tace "Ameen thanks" daga haka ya
katse wayar ta samu adai daita ya kai ta har mall din, wani babban boutique dake
opposite mall din ta shiga, gun eyeglasses ta tsaya tana duba glasses masu kyau
shigen irin wanda yake sa wa, ta wara ido ganin the prices are waoww, wani da ya
mata kyau sosai ta dauka tana dubawa kafin ta tafi gun da ake biyan kudin kayan ta
basu atm suka cire kudinsu suka mata packaging din eye glass din ta fita ta
tsallaka ta shiga cikin mall din, gun body creams ta tafi ta dau cream da take
shafawa duk da akwai mai yawa a gida, kawai dai ta juye a wani container ta boye ne
sanin Ammi na iya shiga daki ta duba bayan ta taho, bayan ta dau cream din xata
juya ta kusa cin karo da mutum, komawa baya tayi da sauri da nufin basa hakuri, sai
kuma ta xaro ido da mugun mamaki tana kallonsa, murmushin da ya bayyana dimples
dinsa yyi yace "Sorry" ta sunkuyar da kanta yace "Har kin gama shopping
din ko yanxu kika fara" ta dauke kai tace "Na gama" yace "Toh mu je ki rakani I
want to get somethings" Daga haka ya fara tafiya, bin bayansa tayi kamar munafuka,
gun kayan ciye ciye su chocolates, biscuits sweets da dai sauransu ya tafi, yana
kallonta yace "Kanwata xata yi birthday gobe, so nasan dai ku mata babu abinda ku
ke so da ya wuce wannan, am asking for a favor duk abinda kika san kina so ki
daukar mata nasan ita ma xata so" Murmushi tayi tace "Ohk then" nan ta dinga jidan
duk abinda ya kwanta mata take mugun so kuma, ya dinga tura trolley din yana biye
da ita, xaro ido yyi yace "Anya imaan wannan banda mugunta kuwa, yanxu duk wannan
abubuwan da kike dauka kina nufin kina son su?" Ta juya ta wara masa manyan idonta
tace "Ai duk abinda kaga na dauka a nan I love it with all my heart, baka san yanda
nake son chocolates da sweets ba koh" murmushi yyi yace "Toh mu bar mata su a haka"
tace "A'a jira ga wani chocolate can..." Da sauri ta tafi ta debo har biyar ta xuba
a trolley, ta kwaso wasu biscuits ma ta xuba, ta dau wani sweet ta xuba shi ma, ta
juya tana kallonsa tana murmushi tace "Toh ni dai ina mugun son teddy in daukar
mata" ya langwabar da kai yace "Kawai so kike account dina yayi kuka yau koh??" Ta
hade rai tace "Just guda biyu ko uku fa, Is she not ur sister? And is it not her
birthday" daga haka ta tafi gun teddies ta debo uku masu tsada da kyau ta jefa
cikin trolley din tace "Tunda kana complaining account dinka, mu bar mata su a haka
kawai" Yar dariya yyi yace "Noo ci gaba har sai kin gaji" tace "A'a I have
conscience" dariya yyi ya bi bayanta ganin ta nufi gun counter, cream dinta ta
ajiye xata bada ATM card ya riga ta mika nasa, juyawa tayi tana kallonsa sosai
gabanta ya fadi bayan sun hada ido tayi saurin sunkuyar da kanta, nan aka cire
kudin aka bata receipt dinta, ta taya sa ciro abubuwan cikin trolley din shima ya
bada atm card aka cire aka masu packaging, barinsa tayi da kayan gaba daya ta dau
teddies din suka fita. Bayan ya xuba ledojin a bayan mota ya rufe motar yana
kallonta kafin yace komai tace "Yau ne birthday din?" Gyada mata kai yyi smiling,
ta boye fuskarta a hankali tace "Toh ni dai ina son kaza ko xaka siya mata" Wara
ido yyi yana kallonta, sai kuma yyi dariya yace "Ina kika ga kaxa imaan?" Ta turo
baki ta nuna masa inda ake gashin kaji, yana murmushi ya tafi, ya siyo kajin
gasassu biyu ya dawo ya sa a mota, ya juya yana kallonta pleadingly yace "Let me
drop you plss" da sauri tace
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

"Nooo thank you" tana fadin haka ta bude karamar jakarta ta fiddo glass din dake
leda tana kallonsa ta mika masa, a hankali ya sa hannu ya amsa yana kallon kwayar
idonta, hakan yasa tayi saurin sauke nata idon, bude ledan yyi ganin glass din
underneath his breathe yace "Waow..." Murmushi tayi xata juya masa baya ya riko
hannunta cikin sanyin murya yace "Thanks Imaan, I love it..." Bata ankara ba sai
gani tayi yyi pecking hannunta, ta kwace hannun da sauri tana xaro ido a tsorace,
shi ma daburcewa yyi yace "I... Sorry I.. I am just happy imaan, I love the
glasses" ta kirkiri murmushi har sannan tana jin warm lips dinsa a hannunta, xata
juya yace "Wait Imaan" tsayawa tayi gabanta na faduwa, ya bude front seat yace
"Plss let me drop you home" kasa ci gaba da kallonsa tayi ta kuma kasa cewa A'a, a
hankali ta shiga motar yyi murmushi ya rufe, ya xaga ya shiga driver seat suka bar
mall din, bata yrda yaje dai dai gate din su ba tasa ya ajiye ta few houses away
from theirs, ta bude motar ta sauka shi ma ya sauka ya xaga ya bude back seat, ya
fiddo gaba daya ledojin siyayyar da suka yi da teddies da kajin duk ya ajiye kusa
da ita ya wara ido yana mata murmushi yace "Dama duk naki ne" bai jira cewarta ba
ya xaga ya shiga driver seat ya tada motar ya bar ta da zare ido ya bar layin,
kallon ledojin ta dinga yi kamar xata yi kuka, yanxu ya xata yi da kayan nan....
Kwasa tayi ta boyesu cikin flowers ta dinga dauka da daddaya da daddaya tana kai su
part din inna, duk a mugun tsorace take, Inna ta saki baki tana kallon kayan, imaan
ta tafi dauko last ledan, Yusuf dake ta kallonta tun shigowarta na farko ya mike ya
isa kusa da ita da mamaki yace "Daga ina kike wannan saurin hakan Imaan, what's all
this u are taking in" kin tsayawa tayi tana kirkiran murmushi ta wuce sa da sauri,
tsoronta daya kar ta gamu da Mujaheed, har dai ta isa parlon inna, Inna dake tsaye
bakin kofa har lkcn ta sake baki tana kallon uban ledojin ta bi ta da kallo har ta
ajiye na hannunta, Inna tayi kasa da murya tace "Imaan ina kika samo wannan kuma?"
Imaan ta kwashesu gaba daya ta kai dakinta da sauri duk ta ajiyesu sanin Yusuf xai
iya biyota, Tana fitowa dakin tace "Ni dai kawai kiyi shiru inna kar ya Mujaheed ya
sani wllh duka xai min" Inna ta hade rai tace "Duka?? da kuwa ya dokar ma kansa
fitina da bala'i, kuma da karshen xamansa ya kama a gidan nan" Imaan ta xauna saman
kujera har sannan gabanta bai daina faduwa ba, Yusuf ne ya shigo parlon, inna ta
wani tsuke fuska, yana kallon Imaan yace "Daga inna kike Imaan?" Inna tace "Yau
naga jaraba, to ina ruwanka isuhu ko ka aiketa ne? Ku dai 'ya yan Ahmadu ku daina
sa ido wllh, meye kuma wani daga ina take kamar xamanka take a gidan, ni dai ba
ruwana, ku dinga tsoron Allah kuyi mai fishshe ku a gidan nan" juyawa Yusuf yyi ya
fita parlon, inna ta kulle kofarta ta sa makulli, ta kalli imaan tana murmushi tace
"Kar dai sabon saurayin ne yyi maki uban siyayyar nan takwara" Imaan tace "Wllh kar
ki gaya ma kowa idan ba haka ba kazar ma baxan tsam maki ba" Inna tace "Ke ma dai
da wata magana wllh, sai kace wata yarinya?? Wa xan gaya ma ni patuu, wannan ai
sirri ne tsakaninmu" Imaan ta shiga ta fiddo ledan kajin guda biyu tace "Toh idan
yaya ya shigo fa?" Inna tace "Oh oh Allah, waye kuma wani yaya, ina ruwana da shi,
ko me xai xo ya min? Ko ya xo ma ni baxan bude kofata ba bbu ruwana, idan ma ya xo
damuna yake ba abinda yake tsinana min"

*The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included


in the payment group.

21.....

Ammi ta bi Imaan da kallo ganin xata shiga daki tace "Kee" juyowa tayi tana kallon
uwarta ta, Ammi tace "Ajiye min plate din kika yi kika fito?" Imaan tace "Ammi na
wanke wllh" Ammi tace "Toh ki tafi ki sha maganinki ki daina min wannan yatsine
yatsinen da kike yi" a hankali tace "Na sha Ammi, kai na ke min ciwo da bayana"
Ammi tace "Allah ya sauwake" Har Imaan zata shiga daki sai kuma ta fasa ta dawo ta
xauna kusa da Ammi murya can kasa tace "Ammi don Allah idan na gaya maki abu baxa
ki min fada ba?" Ammi na kallonta tace "Idan ya kama in maki fada ae dole in maki"
Shiru tayi tana kallon Ammi, Ammi tace "Ina jin ki" Sauke idonta kasa ta yi tace
"Dama..." Sai kuma tayi shiru, Ammi tace "Dama me?" Murya can kasa tace "Wannan
mutumin da kika ji ina waya da shi da daddare shine da naje shopping mall daxu muka
hadu" Marairaicewa tayi tace "Ammi wllh ban san ma ni ya siya ma ba" Ammi tace "Me
ya siya maki?" Ta ja baya kadan tace "Chocolates, da abubuwan ci...." Ammi ta dinga
kallonta, kafin tace "Ina suke?" Imaan na kara matsawa daga kusa da ita tace "Na
kai part din inna, ina tsoron kar ki min fada" Ammi tace "Ni xa ki ma karya baki
san xai siya maki ba koh??" Kamar xata yi kuka tace "Wllh Ammi ban sani ba, we just
met at the supermarket" Ammi tace "Toh shi yaron a ina kika san sa?" Tace "Ai na ce
maki abokin ya Muhsin ne kuma Yayan Classmate dita Mariya ce, a gidan gwaggwo muka
hadu" Ammi tace "Toh yyi kyau, you had better be careful Imaan, kin san Abbanki
won't take it likely with you if he should find out, ni dai kar ki ja min matsala
bbu ruwana, banda shashanci ya maki yawa you ought to have known ur left from right
now" shiru Imaan tayi bata ce komai ba, can ta mike a hankali ta wuce dakinta.
Mujaheed na zaune parlon inna bayan ya dawo aiki ran Tuesday ita ko tana can tana
shara, Imaan na kwance tana bacci kan 3 seater, tun da ya kalleta sau daya bai sake
kallonta ba, bayan wani lkci inna ta shigo parlon, kakkabe kujeru ta dinga yi tana
cewa "Ni dai gaskiya wannan yarinya ta Bukar tana takurani duk ta kare min kujerun
sun lotse, sai dai naji kunya idan nayi manyan baki, yarinya dai kamar kyanwa
kwanciya baya karewa, gashi yau laluran ciwon kafar ya tashi bata je islamiyyan ba
ma, Allah ka dubi jikata ka yaye mata wannan bala'in da ba a san kansa ba, ni bari
ma kwanan nan xan shirya inje in samu ta Rasulu in ji yanda xa ayi, sai dai duk
abinda Ahmadu da Bukar xa su ce su ce, ai dai ba gun boka xa mu je ba" ganin ruwan
kumfa inna ke kokarin kadawa Mujaheed yace "Ni dai magana na xo mu yi, ki bar
wannan aikin naki da baya karewa ki saurareni" ta kallesa ce "Toh idan aiki ya kare
ae kazanta ta tabbata kenan, ni ko ina xan yarda in daina aiki in mutu cikin dauda,
ko kai baka ji dadi da kamshi da ka shigo parlon ba" yace "Abba nake son ki yi ma
magana inna, wllh bana son tafiyar nan, ruwan garin ma ba iya sha nake ba balle
abinci, kwanaki da muka je da ku har muka dawo ni ban ci abun kirki ba fa" Inna ta
saki baki tana kallonsa, can tace "Toh yanxu ya kake son ayi?" Tace "Kawai ce ma
Abba za ki yi xa ki aikeni kano in kai maki wani sako sai Yusuf ya kai su gaskiya"
inna tace "Tohhh, yanxu kiransa xan yi kenan?" Yace "Ehh ki kirasa, sae kice masa
ya min magana don kinsan in kece kika min ba xuwa maki aiken xan yi ba" Inna ta
mike ta dauko wayarta tace "Toh kirasa" Dialing number Abba yyi ya sa a speak on ya
mika mata, imaan sai tsaki take tana turo baki ita a dole an hanata bacci, sai dai
ba wanda ya tanka ta, Abba na d'aga kiran inna tace "Yaro??" Abba yace "Ina yini"
Tace "Toh lafiya lau, sae dai wuni nayi ina aiki wllh har bayan window na duk na
share, na goge gilashin windon" Yace "Alhmdllh, fatan dai lafiya?" Ta gyara xama
tace "Ina fa lafiya, wato kai dai ka haifa ma kanka fitina da abinda ya fi karfin
ka ne baka sani ba har yanxu Ahmadu, wai dama don Allah ina ne asalin ko wani
mutum dai bahaushe?" Abba yace "Ban gane ba inna" a d'an fusace tace "oh oh Allah,
Asalin kowa nake tambayarka, ina ne asalina da na Ubanka?" yace "Asalin kowa kauye
inna" Inna tace "Toh Alhmdllh, yanxu wannan mutumi Mujaheed ya xo ya sameni, ko
gaisuwar kirki ba mu yi ba, ya fara bani sako in baka, wato cewa yyi ince maka shi
baxai je kauye ba gaskiya, don kwanaki ma da mu ka je a gantale ya dawo ba abinci,
har yana koya min karyar da xan maka na cewa xan aikesa kano ko uban wa gareni kano
oho, wai sai Yusuf ya kai su kauyen, bai san ni yar gaskiya bace, ba a cin amana da
ni, yanxu fisabillahi Ahmadu in ji kaga abinda yasa tun suna yara nake cewa ka
dinga kai su can koh?" Mikewa Mujahedin da ya bude baki yyi yana kallonta, imaan ta
sauko kasa ta dinga 6a66aka dariya, Abba yace "Toh yayi kyau ki kyalesa kawai, sae
su tafi da Yusuf din" inna tace "Atoh, ni dai ba ruwana, ka tashi tsaye da rokan
Allah kan Mujaheed" daga haka ta katse wayar ta tayi kasa da murya tana kallon
Mujaheed tace "In dai ranka bai kwanta xuwa kauyen ba kada kaje gaskiya, duk
bambamin da Ahmadu xai yi xuba masa na mujiya, haka kawai kaje ka cutu, don gaskiya
ko ni bana cin abincin gidan hansai, to idan na ci na tsuge da xawo ya za ayi da
ni???" Mujaheed ya juya a mugun fusace xai fita jin dariyar da Imaan take ya juyo
ya haureta da karfi ya fice, wani ihu ta fasa ta rike kafar, inna ta mike da sauri
tace "Fita ki bisa ni ba ruwana kada a dameni ya xa mu dinga magana ki mayar da mu
mahaukata kina dariya" Imaan ta mike tana kuka sosai ta fita parlon tana dingishi
ta wuce part din su, Ammi ta fito kitchen da sauri, Tace "Lafiya, me ya faru?"
Cikin kuka tace "Yaya ne ya haure min kafar dake min ciwo da karfi gashi yanxu ya
rike Ammi, Wllh ban masa komai ba" tana fadin haka ta xube kan kujera tana kuka
sosai, Ammi ta karaso tana kallon kafar, har gun ya tashi yyi ja, Hijab dinta ta
dauka ta sa ta fita parlon bata xame ko ina ba sai bangarensu, Yana xaune dinning
takaici ya ishesa Anty kuma na kitchen da su Maimoon. Nan parlon Ammi ta tsaya tace
"Mujaheed me Imaan tayi maka ka haureta a kafa?" Kallonta yyi ya dauke kai bai ce
komai ba, ta karasa dinning din fuska daure tace "Tambayar ka nake malam, ka fara
hauka ne xaka haureta a kafa, to Wllh even by mistake kada ka sake don zan dau
mummunan mataki a kanka" Anty ta fito kitchen da sauri tace "Lafiya Hajiya Aisha?"
A fusace Ammi tace "Wllh ku ja masa kunne ya fita harkar Imaan a gidan nan, duk
ranan da ya sake gangancin ta6a lafiyarta xa ayi tashin hankali a gidan nan, haka
kwanaki ya mareta na kai xuciya nesa ban ce komai ba, to this shud be the last,
kada ya sake idan ba haka ba wllh sai na rama mata" Hakuri Anty ta dinga bata,
Mujaheed ya mike ya wuce sama ba tare da ya sake kallonta ba, Ammi ta nufi kofa
xata fita suka kusa cin karo da Umma xata shigo sun dawo anguwa da Rahma, ko
kallonsu bata yi ba ta fice, tana komawa dama daki ta shiga ta dauko man xafi ta
fito ta shiga shafa mata a gun, Imaan ta dinga yarfe hannu tana kiran daddy, bayan
Ammi ta daina shafa wa a hankali tace "Ammi xuwa kika yi gun yaya?" Ammi tace
"Baxan je ba ko shi ya haifa min ke?" Imaan na kallonta tace "Fada kika masa" Ammi
tace "Abinda ya fi fada ma" imaan ta zaro ido tana kallonta, can tace "Ni da baki
je ba Ammi ni ne fa nake ta masa dariya...." Da gudu ta mike bayan ta kauce marin
da Ammi tayi niyyar sauke mata, ta wuce daki tana turo baki ta kulle kofar ta sa
key, tana jin Ammi na cewa "Xaki fada min ko kanin ubanki ne yayan, daga yau ma
kika sake xaunawa inda yake wllh sai na kakkarya ki a gidan nan" Inna ta saki baki
tana kallon Mujaheed har ya gama, tura tuwon gabanta tayi tace "Ba lafiya, ita
Aishar? To yaushe ta xama haka, atoh gaskiya imaan dai ta zama yar jaraba tunda
akan ta uwarta taje tana maka bala'i, wato Allah kadai yasan abinda yarinyar ta
tsara ma uwar, saboda irin wannan halayyar tata yasa aka rasa gane kan ciwonta fa
har yau, to meye kuma yarinya karama da hada gurmi a gida, ae da sai kace ma Aishar
A'a ni ba ruwana baxan yi fada da ke ba don kin haifeni, ai ke kusan sa'ar uwata
ce, to kawai kuma sai ka tsaya kallonta kayi shiru" Mujaheed yace "Ni baxan ce mata
komai ba ko sbda daddy, amma ta sake min haka a gidan nan gaskiya sae dai duk
abinda xae faru ya faru" Inna tace "Ni ko sai naje na sameta wllh" da sauri
Mujaheed yace "A'a kar ki ce mata komai" Inna ta ja tsaki tace "Ba dole in sameta
ba xata sa ka gaba tana jaraba a kan figaggiyar yarinya mai hada gurmi" tana fadin
haka ta fice parlon, Ammi na shafa ma Imaan man xafinta a kafa Inna ta shigo ba ko
sallama, Ammi ta mike tace "Sannu da xuwa inna" inna tace "Aa ba wani sannu da
xuwa, yanxu Aisha a kan yar ki xa ki sa Mujaheed gaba kina masifa inda kike shiga
ba nan kike fita ba kamar xa ki make sa, to ma ina ruwanki kina 6are xa ki shiga
harkan 'yan uwa, ubansa fa wan ubanta ne uwa daya uba daya, to ke kuma a wa Allah
na tuba, Ba kunya ba tsoron Allah xaki shiga fadan 'yan uwa, abinda ma ina xaune
parlon d'an shafa kafar nata yyi ya fita shine munafukar nan ta dinga ihu tana min
birgima ni kuma na koreta, ni dai ba ruwana kar ki lalata mana xumunci gaskiya, ko
xane Imaan Mujaheed yyi yau kanwarsa ce kuma yana da ikon yin haka, to banda shi da
ya tsaya mata kan lalurorinta shekarun baya da ba sai dai ta mutu ba, ni dai a
dinga jin tsoron Allah, gashi nan dai albarkacin Bukar bai kula ki ba, toh ni dai
kada a sake sa min jika a baki ba ruwana, banda ma bifillatani agwai da wauta ina
shi ina shiga sha'anin family" tana kai wa nan ta fice a parlon, Ammi ta rufe man
hannunta tana kallon Imaan tace "Wllh na sake ganin ki xaune inda Mujaheed yake a
gidan nan sai na kusa sumar da ke" Imaan dai ba ta ce komai ba. Misalin sha daya
Imaan ta mike daga kwancen da take da kyar xata shiga daki ta kwanta, duk jikinta
ciwo yake mata ga wani xafi da jikin yayi, Ammi dake xaune parlon tace "Kina ji na"
imaan ta juyo tana kallonta, Ammi tace "Dama gobe kice masu baki jin dadi baxa ki
iya tafiyar ba, don babu inda xa a dake, ina xaman xamana a kwaso min wahala a bar
ni da jiyya" Imaan tayi
shiru tana kallonta, can tace "Toh" daga haka ta wuce cikin daki ta kwanta.
Washegari karfe tara su Maimoon, Ummi da Rahma suka gama shirin su na tafiya, kaya
kala biyu ko wannensu ya dauka Abba duk ya basu kudin kashewa, Yana kallon Ummi
yace "Tafi ki duba ko mamana ta gama shirya wa" Ummi ta fita parlon xuwa part din
su Imaan, Ammi ta fito daga bedroom din Imaan kenan rike da cup din shayi don da
mugun xaxxabi ta tashi safiyar ranan, Ummi ta shigo parlon da sallama, gaisheta
tayi tace "Abba yace Imaan ta fito" Ammi tace "Ae kam yau ta tashi babu lafiya"
Ummi na komawa ta fada ma Abba haka, Abba yace "Subhanallah ba lafiya kuma" mikewa
yayi ya fita, a dai dai part din su Imaan ya hadu da Mujaheed ya dawo daga bangaren
inna, Abba yace "Imaan wai bata da lafiya yau" Mujaheed yace "Subhanallah" Abba
yace "Let me check on her" Mujaheed bai ce komai ba kamar ya juya yayi tafiyarsa
sai kuma dai ya bi bayan Abba, Ammi suka gaisa da Abba, Mujaheed yayi kasa da kai
ya gaisheta, Ita ma ba tare da ta kallesa ba ta amsa bbu yabo bbu fallasa, Abba
yace "Toh ya jikin nata?" Ammi tace "Toh da sauki, tun jiya dama bata jin dadi"
Abba yace "Ikon Allah" Ammi tace "Tana ciki" Abba ya nufi dakin nata, Mujaheed ya
bi bayansa kansa a kasa, kwance suka sameta cikin duvet amma still sai shivering
take, Abba ya cire duvet din yace "Sannu mamana" Bude idanuwanta da suka rina tayi
a hankali, Abba yace "Ina ke maki ciwo" girgixa masa kai kawai tayi, Mujaheed ya
duka kusa da ita a hankali ya kai hannunsa jikinta, Abba na kallonsa yace "Ko dai a
tafi asibiti" Mujaheed xai yi magana aka bude kofar dakin inna ta shigo a rikice
tace "Ahaf, ni dama nasan xa a rina, ba ayi hauri ba ma ya aka kare balle anyi,
wllh Ahmadu da ya tattakure ya tattakure kawai sai gani nayi ya haureta"

*The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included


in the payment group.

22. Imaan

Abba ya juya ya kalli Mujaheed jin abinda inna tace, Imaan ta mike xaune da kyar
tace "Ba fa kafana ke ciwo ba" Inna tace "Toh ina ke maki ciwo" Komawa tayi ta
kwanta bata tanka ta ba, Ammi dake tsaye bakin kofar dakin sai kallonta take, Abba
na kallon Mujaheed da ya kasa cewa komai yace "Amma me yasa xaka haureta jiya?" Ya
sunkuyar da kai yace "It wasn't intentional" Abba ya gyada kai yace "It wasn't
intentional, OK that's good kayi kokari" Daga haka ya juya ya kalli Ammi yace "Ta
shirya ta fito mu je asibiti" daga haka ya fita dakin, Mujaheed ya harari Inna
fuska daure xai fita tace "Oho dai ta rufa ma ka asiri amma ko tantama babu haurin
da ka mata ne ya ja mata wannan ciwo" Ammi ta basa hanya fuska daure, kansa a kasa
ya fita dakin, Inna tace "Kyansa duk inda imaan xata ga Mujaheed daga yanxu ta gudu
tayi ta kanta, ni dama tun da naga yanda yake laftar 'ya yan jama'ah a anguwa yana
d'an yaye bai fi shekara 3 ba nasan akwai bala'i a gaba wllh, duk ya bi ya addabi
'ya yan mutane da cizo da yakushi a anguwa, kowa ya gansa sai ya adana d'an sa,
lkcn d'an Hansai Garba na kamarsa kullum sai ya ciji garba yakushesa, Hansai tayi
ta jin haushi don ta xo jegon Huraira a gida, in takaice maki kafin Hansai ta bar
gidan idan aka bude jikin garba duk ta6on cixon Mujaheed ne, to kuma meye baxai yi
ba yanxu?" Imaan na daga kwance sai dariya take da kyar, Ammi dai ko kallon Inna
bata yi ba tana fiddo ma imaan kayan da xata sa, inna tace "Toh Allah dai ya kiyaye
gaba yyi maki tsari da shi, amma gaskiya imaan ki guji duk inda Mujaheed yake,
idan kun dawo asibitin xan xo dubaki idan Allah ya yarda, tafiya dai ta sha ruwa"
daga haka ta fita dakin, Ammi tace "Kin tashi kin shirya ko xaki kwanta nan kina
dariyar walakanci ne?" Imaan ta tashi ta saka kayan da Ammi ta fiddo mata, Inna na
fita taga Abba tsaye a waje, tace "Ahmadu tafiya dai ta sha ruwa koh?" Yace "A'a xa
su wuce tare da Yusuf yanxu, shi Mujaheed xa su je asibiti da Imaan" inna tace "Toh
madallah, hakan ma yayi, to ko in bisu asibitin ne" Ta gefen ido Mujaheed ya
kalleta da sauri, Abba yace "Ehh to xa ki iya bin su" Tace "Toh bari in kulle
dakina kada a barsa a bude gaskiya" daga haka ta wuce sashin ta, Mujaheed ya nufi
motarsa don fitar da motar waje, Abba ya bi sa da kallo har ya isa parking space ya
shiga motar, Imaan ta fito sanye da Hijab har kasa, da kyar take tafiyar, Abba yace
"Sannu mamana, Allah ya sauwake" a hankali yace "Ameen" yace "Mu je can kofar
gidan, ban gane fita da motar da yayi ba" tare suka fita compound din, Ya bude ma
Imaan front seat ta shiga, Abba na kallonsa yace "Inna na tahowa yanxu, tare xa ku
tafi" yace "Ehh na sani" Daga haka Abba ya koma cikin gida, Mujaheed na ta kallon
gate har sai da yaga inna ta fito tana washe baki sannan ya ja motarsa yayi zooming
off, Imaan ta xaro ido tana kallonsa, yana isa titi ya kashe wayarsa ya ajiye ya
dau hanyar asibitin da yake aiki, Sai da suka yi nisa fuska daure yace "Ni kika je
kika hada da mamarki koh?" Tace "Ko dai ita taga ina kuka" ya gyada kai yace "Xa ki
gane kuran ki" Ta turo baki ta jinginar da kanta da kujera, Suna isa asibitin bayan
yayi parking ya juya yana kallonta yace "Sauko min a mota" Bude ido tayi da sauri,
ya bude door din motar ya fita, a hankali ta ta bude side dinta ta saukar da
kafafuwanta kasa, xagayowa yyi ganin bata fito ba yace "Baxa ki sauka ba" kamar
xata yi kuka tace "Wllh jiri nake ji yaya" Wani harara ya watsa mata yace "To
daukan ki xan yi?" Bata ce komai ba ta sauko motar, ya rufe ya kama hannunta suka
shiga cikin asibitin. Yana xaune office misalin sha daya bayan ya kunna wayarsa
kiran Abba ya shigo wayar, murmushi yyi ya daga ya kai kunne, Abba yace "What's
taking you people too long Mujaheed" yace "Drip aka sa mata Abba, jikin da sauki
sosai, she is fast asleep now" Abba yace "Toh Allah ya sauwake, why did u left inna
behind?" Yace "Abba Kasan yanda take abinta, xuwa xata yi tayi ta fada every slight
mistake" Abba yace "Haka ne, da yaushe xa ku dawo kenan" yace "Nan da azahar in sha
Allah" yace "Toh Allah ya kai mu" Mujaheed yace "Ameen" daga haka Abba ya katse
wayar, Mujaheed ya juya yana kallon Imaan dake kwance kan gadon duba pregnant women
tana bacci, mikewa yyi ya isa kusa da ita yana kallon ruwan da ya kusa rabi, Hannu
ya kai forehead dinta yaji da dumi har sannan, ta bude ido a hankali, daure fuska
yyi yace "How are you feeling now?" Yamutse fuska tayi tana son mikewa xaune yace
"Lie still and answer my question" murya can kasa tace "Kai na yana min ciwo" yace
"Shi kadai?" Tace "And am hungry" ya kalli abincin da ta ki ci da yawa daxu kafin a
mata alluran a sa mata drip ya dauka ya bude ya ajiye kusa da ita ya daga ta xaune,
xaro ido tayi tace "Yaya abincin daxu kuma??" yace "Kin taho da abinci daga gida
ne" ta hade rai tace "Ni dai baxan iya ci ba bayan ya huce kuma an ajiye k'ura ya
gama shiga ciki" wani kallo ya mata yace "Toh sai ki tsaya da yunwar ki ai, wannan
abincin dake rufe meye ya samesa da baxa ki ci ba, Bayan har ynxu ma da dumi
abincin" yana fadin haka ya dau cokalin ya debi abincin ya kai baki, ta tabe baki
ta dauke kai tace "A'a ni dai bana so, tun da safe fa, ko ta gefe gefe ai dust xai
iya bi ya shiga, sai dai kai ka cinye a kawo min wani" Yace "Toh xaki ga wani kuwa"
daga haka ya kai abincin table dinsa ya xauna ya fara ci, ta dinga kallonsa kamar
xata fashe da kuka, ganin ko kallonta bai yi ba tace "Ni dai ka bani waya in kira
Ammina ta kawo min abinci" yace "Baxan bayar ba" komawa tayi ta kwanta ta fara kuka
har bacci ya sake xuwa mata, mikewa yyi ya rufe sauran abincin da bai cinye ba ya
fita office din. Wani takeaway din ya fita ya siyo mata na abinci, yana dawowa ya
tasheta ya ajiye mata abincin a gabanta sannan ya juya ya fita, ta mike xaune ta
bude abincin ta fara ci a hankali, har ya dawo dakin bata gama cin abincin ba, ya
xauna kan office chair dinsa, tana kallonsa tace "Yaya ni baxan iya cinyewa ba" bai
tanka ta ba hankalinsa na kan laptop din gabansa, ya gama abinda yake sannan ya
juya yana kallonta ya ga ta ajiye abincin ta kwanta, mikewa yyi ya karasa kusa da
ita ya dauke abincin ya ajiye ta bude ido tana kallonsa tace "Yaya ina son xan yi
magana da Ammina" yace "Baxa kiyi ba" yana fadin haka ya koma table dinsa, ta turo
baki ta juya masa baya. Karfe biyu Imaan ta bude ido jin an kama hannunta, ya
karasa cire mata drip din yace "How are you feeling?" Ta mike xaune da kyar tace
"Da sauki, I want to go home" Yyi disposing roban ruwan ta sakko saman gadon, da
sauri ya rikota ganin xata fadi duk da ita ma ta kama gadon, kamar xata yi kuka
tace "Wllh jiri nake ji yaya" Ya saketa yace "Toh ni nace ki sakko?" Komawa saman
gadon tayi ya fita dakin, ba a dau lkci ba ya dawo ya dau wayarsa da car key yace
"Mu je" ta xaro ido tace "Idan na fadi fa?" Yace "Sai ki tashi" daga haka ya nufi
kofa, sauka tayi saman gadon ta tsaya na kusan minti daya har ta ji ba jirin kuma
sannan ta nufi kofa a hankali kamar mai counting steps dinta ta bude kofa ta fita,
tsaye ta gansa yana jiranta, ya mata wani kallo yace "Da kin bari na sake shiga
office din ki gani" daga haka ya wuce ta bi bayansa, sallama yyi da co workers
dinsa suka fita asibitin, a Wani pharmacy ya tsaya ya sauka ya siyo mata drugs da
aka mata prescribing sannan ya dawo ya shiga motar suka bar wajen, sai da suka kusa
gida a hankali tace "Yaya baxa ka siya min kaza ba plss" yace "A'a sai dai in siya
maki akuya" murmushi tayi tace "Toh siya min" A waje yyi parking yace "Sauka..." Ta
bude motar ta fita sai da ta shiga gate ya ga ledan maganin da ya siya mata" fitowa
yyi motar rike da ledan ya wuce ciki da sauri, ganin har ta kusa apartment dinsu ya
wuce nasu bangaren kawai, Babu kowa parlon, ya haura sama dai dai fitowar Anty
dakinta tace "Ya jikin Imaan din?" Ya saci kallon kofar Umma kafin yace "Da sauki,
Umma bata nan ne?" Anty tace "Ehh tun da ta ji kai ka kai Imaan asibiti ta fice
gidan tun safe bayan ta gama bambaminta" Mujaheed ya xaro ido ya jingina da bango
yace "Wa ya gaya mata Anty?" Anty tace "Abban ku, tunda ba tsoron ta yake ba" Ji
yayi xufa na keto masa, Anty ta wuce ta bar sa wajen tsaye, da kyar ya ja
kafafuwansa ya wuce dakinsa. Ammi ta hada ma imaan ruwan xafi a bayinta ta fito
tace "Ga ruwan ki shiga, saura ki salance ruwan" Tashi Imaan tayi ta wuce dakin
nata. Wanka Mujaheed yayi ya shirya jin lkcn Asr yyi yayi alwala ya fita gidan,
yana dawowa masallaci dama part din inna ya nufa don Allah yasan yana tsoron
haduwarsa da mahaifiyar tasa Inna ta fito daga daki jin an bude kofar parlor
ganinsa tace "oyaa Alale, fitar min parlor kada in tara maka jama'ah, uban me ka xo
min??" Mujaheed yayi dariya yace "Haba dai mai gidan kuma kike kora yau inna?" A
fusace tace "Yana kabari, tun raina bai baci ba Mujaheed ka fita" Mujaheed yace
"Abba ne fa yace kada mu tafi dake Inna" ta buda baki tana kallonsa tace "Kai
haba?" Yace "Xan maki karya ne" xauna wa tayi tace "Ikon Allah, shi Ahmadun yace ku
tafi ku bar ni kenan, to ya ma kansa kuwa, shine har da shi a bani hakuri da masu
gadi a tsakar gida daxu, har hawaye fa sai da na xubar" Mujaheed yyi murmushi ya
kwanta kan kujera, Inna tace "Toh ae shikenan, ya jikin Imaan din?" Yace "Da sauki"
inna tace "Kuma da gasken bata da lafiya Mujaheed? Naga kamar don kar aje kauyen da
ita yasa ta langwabe fa" Mujaheed yace "Ni dai akwai abinci?" Tace "Gashi can wanda
Aisha ta kawo min ne daxu, bai wuce shinkafa da miya ba, Idan kuma biskit xa ka ci
ga su can iri iri a daki wanda aka kawo ma Imaan, Kazan ma daxu na dumama na karasa
cinyewa..." Mikewa xaune Mujaheed yyi yana kallonta na kusan second goma, can yace
"Wa ya kawo mata?" shiru Inna tayi kanta a kasa, can ta saci kallonsa suna hada ido
tace "Yo wa gareta banda Bukar??" tana fadin haka ta mike ta shige daki.... Imaan
ta fi minti biyu tsaye bakin kofar bedroom din Ammi ta kasa shiga don bata san me
xata ce mata ba, bude kofar dakin aka yi ta ja baya da sauri, Ammi ta dinga
kallonta tace
"Meye haka kike yi a bakin kofa ta?" Ta fara kame kame ba tare da ta kalli Ammi
ba, Ammi tace "Imaan" daga kai tayi ta kalleta kamar xata yi kuka, Ammi tayi kasa
da murya tace "Tell me what you want" tana jan fingers dinta a hankali tace "Ammi
dama... Dama Sadeeq ne yace min yana waje ya xo gaisheni" Ammi ta dinga kallonta
tace "Waye Sadeeq" ta sunkuyar da kai tace "Abokin ya Muhsin" Ammi ta yi shiru, can
tace "Toh kar ki dade" Ta d'an yi murmushi tace "Toh nagode Ammi" daga haka ta saka
Hijab dinta ta fito don tun da aka yi la'asar Sadeeq ke waje amma ta rasa yanda
xata sanar ma Ammi ta fita, sosai hankalinta ya kwanta ganin ba motar Mujaheed a
parking space, kamar mai tausayin kasa ta fita kofar gida, Tsaye ta ga Sadeeq jikin
motarsa ya rungume hannunsa, as usual sanye da spec dinsa, dogon hancinsa da cute
millionaires belt dinsa shine first abinda xaka fara noticing a fuskarsa daga nisa,
Ta sunkuyar da kanta har ta isa inda yake tsaye, kallonta yake daga cikin glass din
idonsa ko kiftawa babu, murya can kasa tace "Ina yini?" Yyi murmushin da ya bayyan
dimples dinsa ya cire glass dinsa yace "Lafiya lau Imaan ya jikin?" A hankali tace
"Na ji sauki" yace "Sure??" Ta gyada masa kai, yace "Toh Allah ya kara lafiya, hope
kin sha dosage na afternoon, I mean ur drugs?" Ta gyada masa kai tace "Na sha" yace
"Good, ya mama fa?" Tace "She's inside" ya langwabar da kai yace "Yaushe xan xo
gaisheta pls" ta xaro ido tace "A'a xan ce kana gaisheta" cikin sanyin murya yace
"Ke dai baki son yan gidanku su san ni koh?" xata yi magana aka bude gate, Inna ce
tsaye bakin gate din tana kallon mai gadi tace "Kai iliya kake ko ilu, Kasan kan
waya kuwa? Hadiza xa a kira min duk ba kowa gidan sai mai laluran can kuma nasan
tana can tana bacci yanxu haka, yaran duk sun tafi kauye sai gobe xa su dawo" Imaan
tayi stiff inda take bayan gabanta yayi mugun faduwa jin muryar inna, Mai gadin ya
mike da sauri ya amshi wayar yace "Toh Hajiya...." Buda baki inna tayi tana
kallonsa tace "Eh lallai baka da da'a, banda barbada kace ma matan gidan Hajiya
nima kace min Hajiya, to bari kaji ko wa enda suka dauke ka aiki ma inna suke ce
min balle kai, bar gani na haka xuciya mai kyau da rikon gaskiya da amana yasa ka
gan ni har yanxu da kyau na, amma wllh da kyar idan ban girmi wanda ya haifi
kakanka ba ma" yayi kasa da kai yana murmushi sosai yace "Yi hakuri Baaba tuba
nake" inna tace "Kaji min yaro dai" Imaan dai ta kasa tsaye waje daya tayi backing
din inna xuciyarta sai bugawa yake, murya can kasa Sadeeq yace "Ur grandmum?" ta
gyada masa kai a hankali, kamar ance inna ta daga kai ta gan su, sake baki tayi ta
kalli mai gadin tace "Kai wancan ba Imaan bace nake gani a tsaye?" Yace "Ita ce
Baaba" Sadeeq yace "Let me go and greet her tunda ta gan mu" imaan dai kasa cewa
komai tayi, ta ji kamar ta fashe da kuka, ae kuma shikenan.... Sadeeq na isa gun
Inna dake ta kallonsa ya risina ya gaidata da ladabi, tace "Kai ne sabon saurayin
nata?" Murmushi Sadeeq yyi ya kasa cewa komai, Inna tace "Ikon Allah, Kai ni fa na
haifi ubanta Bukar, jikata ce fa, ita kenan Allah ya ba Bukar fa, a hannuna fa aka
haifeta wllh, yanxu d'an nan da ban fito na gan ku ba shikenan, kai a garin ku haka
ake yi?? ko bata ce maka kakarta na da rai bane, ita tunda bata da hankalin cewa ka
shigo ka gaisheni kai baxa ka yi tunani ka shigo ba, dubi fa yanda ta ji kunya ta
kasa juyowa kamar warce ruwa ya cinye" Sadeeq dai sai murmushi yake yace "Dama ai
xan shiga in gaida ki kaka, kiyi hakuri" inna tace "Ni dai ba ruwana a dinga abu
saboda Allah, tunda dai na kama ka mu je ciki" Yana murmushi ya bi bayanta suka
shiga compound din ta rufe gate, tana nuna masa bangaren su Mujaheed tace "Kaga
wancan katon ginin?" Yace "Na gani kaka" tace "Toh na wan ubanta ne, barrister suke
ce masa, a India yayi karatun lauyancin sa, matansa biyu sai 'ya ya bakwai,
Mujaheed shine d'an sa na fari, ina tsaye bakin kofar asibiti aka haifesa, yana nan
xaka gansa wani lafcece dogo, da yake ada yana daga wannan karafunan turawan, to da
kyar dai Ahmadu ya raba sa da su, nima na dinga rokon Allah har ya daina, a gabana
fa ya girma, tun yaye yake wajena iyayen suka bar min, yana gama sakandari dama
babansa ya biya masa kudin karatun likita a turai, ai ko in gaya maka babu irin
fitsarar da bai koyo a can ba gaskiya, ni dai lkcn da ya dawo ma tsoron sa nake ga
wani uban gashi da ya tara, buduwar da xai aura ma yar hayi ce, to sai kaninsa
Yusuf, xaka gansa shi kuma wani lagwai lagwai kamar ya karye malam, da ma muka samu
ya d'an yi kauri yanxu, sai kaga yanda aka haifesa d'an fiyot, to sauran kuma duk
mata ne" Murmushi kawai Sadeeq ke yi yana bin inna, inna ta nuna masa part din su
Imaan tace "Toh kaga wannan bangaren na su Imaan ne, Ubanta a can Habuja wajen
neman abincinsa yake, ita kadai Allah ya basa a duniya, to dai ya fi babu d'an
agwai da bak'in da, uwarta na nan wata bafillatana sai kirki, toh ni kuma kaga
akurkin da suka gina min nake rayuwa ciki" ta fadi haka tana nuna masa nata part
din.

*The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah
Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included
in the payment group.

_23. Imaan

Am bringing this to the notice of my fans, idan xaku biya book din *Imaan* in dai
ba digit din nan 👉🏻 07087865788 wato lambata kuka yi ma magana ba to Wllh ba ni
kuka biya ma kudi ba, lambata guda daya ne kacal kuma gashi can a sama na rubuta,
sannan ni bana amfani da wani kati idan ba Airtel ba, don haka duk wanda ya biya ta
wani lamba daban wllh ya karanta hakkina without paying coz every page sai na sa
number na da account number amma sai ku tsallake ku tafi kuna biya a gun wa enda
ban sani ba ban san da su ba, ni kadai nake harkata a bangaren rubutu bni da wani
xae ce ku tura masa xai turo min, talk to me directly through my WhatsApp digit 👉🏻
07087865788, su kuma masu siyar min da littafi har da hada document Billah na bar
su da Allah, we shall surely meet in the hereafter in dai hakkina ne in sha Allah.
Sannan masu *forwarding* ma su ci gaba there is power in the tongue_

Dariya Sadeeq yayi yace "Haba wannan ai ba laifi kaka" ta tabe baki tace "Mu je dai
tukun" suna isa bakin kofa tace "To dai ka gani..." yana murmushi ya shafa kansa
yace "Wannan ai ya fi duk sauran kyau kaka, ga shi ba hayaniya ba komai" Inna ta
kara tabe baki ta bude kofar tace "Toh Allah ya masu albarka da suka gina min ai
dai yafi babu" bin bayan ta yayi cikin parlon dake ta kamshin turaren wuta ta bude
fridge ta dauko masa malt biyu da ruwan gora ta ajiye masa yace "Nagode sosai kaka"
xaunawa tayi tana washe baki tace "Madallah, to ya sunan jik'an nawa?" Yyi kasa da
kai yace "Sunana Abubukar Sadeeq" Inna ta gwalo ido ta saki wani kabbara da ya sa
ya dago da sauri yana kallonta, tace "Yo ai sunan mahaifinta kenan Bukar, wllh shi
ya haifeta, ai ko baka gansa ba mutumin kirki mai dattako da sanin ya kamata, sam
yaron bai son 6acin raina, yo Ashe ma d'a na ne kai, to ka sha kurumin ka in dai
wannan yarinya Imaan ce to wllh ka sameta ka gama ko taki ko ta so in dai ina
numfashi kai ne mijin ba ruwana, don gaskiya ka kwanta min sosai, naga kana da
hankali da nutsuwa" murmushi kawai Sadeeq yake, yace "Toh kaka idan ita bata ra'ayi
fa?" Inna ta xaro ido tace "Wannan kuma ita ta jiyo ni dai ba ruwana, sunan ubanta
fa gare ka kuma duk masu sunan an sansu da rikon aure, dubi fa yanda ubanta ya rike
uwarta duk da rashin haifa masa yara da yawa da bata yi ba, to ni ko ina xan yarda
ka kubce mata, A'a baxai sa6u ba wai bindiga a ruwa" Sadeeq yace "Toh nagode kaka
naji dadi sosai" Tace "A'a ba xancen godiya, sunan d'a na fa gareka, ni dai ko yau
kace xaka turo magabatanka kofa a wangale yake, to me xa mu ci da ita?? duk da dai
ko sati ba ayi da aurar da yar uwarta ba amma idan ma iyayen nata sunce baxa su iya
ba ni xan mata gado da kambodi da dirowa, Ina ce suna kenan kayan auren dai?"
Sadeeq couldn't help it but laugh, tace "Kai ba xancen dariya bane, ni wlh sai in
sa a siyar da filina guda daya in mata kayan daki, dama ni tsinannen bokon nan da
ake yi yanxu ba d'ad'a ni da kasa yyi ba" Sadeeq ya sakko kasa yace "Da xa a ban
ixinin turo magabatan nawa ba da jimawa ba da naji dadi sosai kaka" Inna tace
"Wannan ai ba wata matsala bace bari Ahmadu ya dawo tunda kaga shi uban nata na
Habuja" yace "Toh naji dadi sosai kaka" Inna tace "Kai don Allah... ai kuma an xama
daya godiya ta me kuma, in ji iyayen ka a nan garin suke su ma?" Yyi kasa dai kai
yace "Ehh suna nan" Inna tace "Toh dan siyasa ne uban naka?" Yana murmushi ya
girgixa kai yace "Aa d'an kasuwa ne, Alhaji Ahmad Bulasawa ne Abba na" Inna ta xaro
ido tace "Bulasawa?? Bulasawa dai da na sani na garin nan?" Bai dago ba still yace
"Ehh shi" Inna ta bude baki tana kallonsa da kyau, can tace "Ikon Allah, ashe d'an
babban mutum ne gabana ni Asabe, waye bai san Bulasawa ba duk garin nan da ma duk
kasashen arewa, ba ance gidansa na nan nan GRA ba?" Yayi murmushi yace "Ehh" inna
ta rike ha6a tana kallonsa tace "Ehh lallai ga kamanni kawai hanci ka fisa wllh,
amma matansa aka ce biyu, to wacece uwarka a ciki, ko uwargidan? Don dai Bulasawa
bai wuce Ahmadu na ba" Yace "Ehh ita" Inna tace "Atoh Alhmdllh, Allah na gode maka,
kai abu sharr... bari Ahmadu ya dawo ko cikin watan nan ma ni gaskiya sai ka turo
su Bulasawan, wa xai xauna" shi dai bai ce komai ba, Inna tace "Kai.... Allah mai
iko, amma xan so kada wannan abun arxikin ya dau lkci gaskiya, ai aure abun arxiki
ne" a hankali yace "Toh Allah ya sa haka kaka" tace "In sha Allah ya ma sa, ai abun
arxikin xa a hada" Mikewa tayi tace "Bari in debo maka dambun namar da na ajiye ma
Mujaheed" Da sauri yace "A'a xan koma ne kaka" Tace "Da wuri haka? Ni dai ka tsaya
ko a leda ne sai in kulle maka" bata jira cewarsa ba ta shiga daki ba a dau lkci ba
ta fito da gaba daya dambun naman a leda ta juye, ya xaro ido yace "Kaka wannan ai
yayi yawa" tace "A'a ba ruwana ka amsa, dama Mujaheed da Imaan na ajiye ma to
gaskiya ba rabonsu bane ynxu" dariya yyi ya karba yace "Toh ngd kaka, Allah ya kara
girma" tace "Don ma dai duk sun cinye min cin cin din, kuma nasan ba kowa ya aikata
min haka ba sai Maimoon da Ummi, ita Imaan bata daukan abu ba a bata ba sam ba
halinta bane, gashi yarinyar bata da fitina tun tana jaririyarta, ga rashin yarda
da kowa, lkcn ma ni har fargaba nake kada a kawota wajena don idan ta fara tsala
ihu duk sai ta tara min munafukan anguwa an shigo min ana tambayar lafiya, me ya
sameta?? dama Mujaheed kadai ne bata yi ma kiwa ba lkcn da take tashan kiwan, idan
kuwa ta makalkalesa a lkcn bbu mai banbareta sai uwarta Aisha, ita ce ma ta makala
masa yaya tun bata da wayo, in ko ba shi ya bata abinci ba dama abincin sai dai yyi
ta galantoyi ba ci xata yi ba, in gaya maka lkcn Bukar na siyo mata wani runtumemen
alawa idan ta saka a baki bata yrda ta ba kowa don rowa sai dai Mujaheed, shima din
d'an dangwala masa xata yi a baki tana makale jikinsa, kai har goyata Mujaheed ya
sha yi fa ta saki fitsari jikinsa sai dai ya canxa kaya, gaskiya ta takura ma
Mujaheed ba kadan ba tana karama, shi sa in har yana gida uwar ta kawo ta bani da
fargaba in kyalesu can su karata inyi ta kaina, to idan ban kyaleta ba ya xan mata
tunda bata yarda da ni ta sa iyayenta su fara wani mugun tunani a kai na in shiga
uku? A'a ba ruwana wllh" Murmushi kawai Sadeeq yake yana kallon inna, ta tabe baki
tace "Toh gashi dai Imaan an girma kamar ba ayi ba, bari dai in bar ka haka naga
kamar sauri kake, to sai yaushe kuma xaka sake shigowa??" yace "Ae ko da yaushe xan
dinga shigowa gaida ki in sha Allah" Tace "Kai toh nagode yarona, Allah maka
albarka, ya kare ka sharrin mahassada" ya mike ya ajiye mata dubu goma a gabanta
yace "Ba yawa kaka a sa katin waya ayi xumunci" ta kauda kai da sauri tace "kai
kai.... Ayi haka kuma Bukar??" Ya nufi kofa yana murmushi yace "Sai na kuma dawowa
kaka" ta mike tana washe baki tace "Toh Allah maka albarka ka gaida min uwarka
kaji?" Yace "In sha Allah xata ji" daga haka ya fita parlon just smiling, inna ta
koma ta dau kudin tana kirgawa tana murmushi. Dama tunda inna ta shiga ciki da
Sadeeq imaan ta wuce part din su ta fashe ma Ammi da kuka, Ammi ta mike tace
"Lafiya?" Cikin kuka tace "Ko ba inna bace ta wani fito ta gan mu shine ta sa suka
shiga ciki tare da shi, yanxu ban san dame dame xata fada masa ba, wayyo na shiga
uku Ammi, nasan komai ma yau sai ta gaya masa" Ammi ta sake baki tana kallonta, ita
kanta hango irin maganganun da inna xata juye ma Sadeeq yau ta dinga yi, can tace
"Ae ko sai ki tashi ki tafi bangaren nata, idan ta ganki xata kama bakin ta" Imaan
na girgixa kai tace "Ammi baxan iya ba, tun fa a gate ta fara basa labari" Ammi
tayi jigum, can tace "Toh Allah ya kiyaye, ban san kuma me xan ce ba" daga haka ta
bar parlon, Imaan ta dinga hawaye duk jikinta yyi sanyi babban damuwarta ma kada
inna tace masa ai gashinta na nan bata son a gyara mata shi. Sadeeq na fita
compound din yayi dialing number imaan yana murmushi, da sauri ta mike xaune tana
kallon wayar, ta fashe da kuka a hankali ganin shi ne, da kyar ta daga kafin ya
katse ta kai kunne, yace "Toh ai xaki fito mu yi sallama amma?" Tayi gathering
courage tace "Me grandma dita ta gaya maka?" Yayi yar dariya yana wara ido yace "Ai
babu abinda bata gaya min ba, she told me everything" Ta xaro ido kawai ta katse
wayar ta fashe da kukan takaici, duk kiran da ya dinga yi kin dagawa tayi daga
karshe ta shige daki ta kwanta kan gado bata fasa kuka ba. Bayan Isha jin ana
knocking Ammi ta sa Hijab ta nufi kofar ta bude, Abba ta gani tsaye da Mujaheed ta
ba su hanya tace "Ina yini Alhaji?" Ya shiga parlon Mujaheed na biye da shi ya
xauna yace "Lafiya lau Aisha, ya mai jikin?" Xaunawa tayi ita ma tace "Da sauki
Alhmdllh tana daki" Mujaheed bai yarda ya kalleta ba yace "Ina yini" tace "Lafiya"
Abba yace "Ko bacci take?" Ammi ta mike tace "Anya kuwa...." Mujaheed dake tsaye
dama bai xauna ba yace "Bari in dubata" Har xata dakatar da shi sai ta ji kunyar
Abba, ta dai bi sa da hararan gefen ido don ko kadan bata so tafiyarsa dakin ba,
murda kofar bedroom din yyi ya shiga ciki, tana xaune gaban mirror daga ita sai
towel tana shafa lotion a duk jikinta, duk tunaninta Ammi ce ta bude kofar don bata
ko kalli direction din kofar ba, jin shiru ta daga kai tana kallon kofar ta madubi,
tsaye yake yana kallonta, suna hada ido yayi saurin dauke kansa, ta xaro ido tana
gyara daurin towel din tace "Yayaaa" Mikewa tsaye tayi ta juyo tana kallonsa kafin
tace komai calmly yace "Abba na jiran ki a parlor" bai jira cewarta ba ya fita
dakin ta bi sa da kallo tana turo baki, Mujaheed na duban Abba yace "Tana xuwa
abba" Abba yace "Ohk" Hijab ta sa har kasa ta fito parlon, ta gaida abba da
murmushi fuskarta yace "Ya jikin mamana" tace "Abba ai na ji sauki" yace "Toh
Alhmdllh, Allah kara lafiya" tace "Ameen" Abba yace "Ga watermelon nan you take
much of it kin ji" a hankali tace "Toh nagode Abba, but...." Sai kuma tayi shiru,
yace "But what?" Ta boye fuskarta tace "Abba ina son cin suya" Abba yace "Toh
Mujaheed xai siyo maki yanxu" Mujaheed ya kalleta ta gefen ido irin kallon harara,
Tana murmushi tace "Toh nagode Abba" daga haka Abba yyi ma Ammi sallama Mujaheed ma
yyi mata suka fita. Abba yace "Idan mun fito part din inna sai ka tafi ka siyo
mata, there is still time ai" Mujaheed yyi kasa da murya yace "Abba yanxu tare xa
mu gun innan?" Yace "Of course, ban san urgent kiran da take min ba, it might even
be something that isn't worth the call" Mujaheed yyi yar dariya yace "Dama xaka ga
it's nothing that important...." Abba yyi murmushi yace "But we still have to
listen, gudun matsala" Suna shiga parlon Inna ta shafe addu'ar da take kan darduma
tace "Har ka iso kenan Bukar, to shi kuma wannan jelan da ya biyo ka fa?" Dariya
Abba yyi ya xauna yace "Aa mun shiga duba mamana ne shine muka karaso nan din tare"
tace "Atoh na gansa wani sandan sandan kamar basamude a bayanka" Mujaheed dai sae
hararanta yake k'asa k'asa, tayi kasa da murya tace "Kana ji na Ahmadu?" Abba yace
"Ina jin ki" tace "Kaga kujeran
can da Mujaheed ya xauna?" Kai ya gyada mata yace "Na gani" tace "To wllh tllh a
kai Bulasawa ya xauna" da mamaki Abba yace "Bulasawa kuma?" Tace "Eh, amma d'an sa
ba shi din ba" Abba yace "Tohhhh.... a ina ya san ki?" Ta daga hannu da sauri tace
"A'a ni bai san ni ba, a titi muka hadu yau kuma muka fahimci juna kwarai da
gaske..." daga Abba har Mujaheed kallonta suka tsaya yi without blinking, can
Mujaheed ya girgixa kai planning to get up and leave the parlor yaji tace "Ashe wai
saurayin 'yar ka ce Imaan, amma algungumar bata ta6a sanar da ni ko da wasa ba, a
wajen na gansu tsaye jikin santalelen motarsa, in gaya maka taji kunya tsamo tsamo
da ta gan ni, ni dai ban kulata ba bakina a leko na taso keyarsa muka shigo cikin
gida, d'an wajen Amadi Bulasawa mai gidajen man fetur sun fi dubu a arewa fa
Ahmadu" dakatawa Mujaheed yyi da sauri ya juya yana kallonta, Abba na gyada kai
yace "Tohh da kyau hakan" Inna tace "Kai fa kasan da kyau yaro, wato idan Allah yyi
auren har kasan waje fa sai an fitar da ita an juye duk gurbatattun jinin jikinta
dake ja mata lalura a sauya mata sabo, sannan kasussukan jikinta su ma duk sai an
ce xa a sauya su ta rabu da ciwace ciwace na har abada, kasan fa bbu abinda turawan
nan basa iyawa in dai da naira, to ga naira dai faca faca ta samu, ae ni bayan
fitarsa sai da nayi ya ma ake kiran sujjadar nan na godiya ga Allah?? To ni dai
nayi wllh kuma na dade goshina a kasa" Dariya kawai Abba yake yana kallon
mahaifiyar tasa, Mujaheed dae sai juya counter din hannunsa yake, inna ta
marairaice tace "Ahmadu ka rufa min asiri ba abun dariya bane wannan, sannan yaron
fa duk ya damu wai xai turo magabatan sa nan ba da dadewa ba ayi xancen aure, kasan
su kuma manyan mutane basa son kwalo kwalo kada a bari wannan yaron ya kubce ma
jikata in shiga uku gaskiya" Juyawa Mujaheed yyi ya dinga kallonta, Abba yace "Haba
maganar aure kuma Inna, ko secondary fa bata gama ba" Inna ta wani tsuke fuska
cikin d'aga murya tace "Allah ya tsine ma sakandarin, sakandarin banxa ga abun
arxiki kana xancen sakandari, ko a gidansa wllh xai bari ta karasa, baka gansa ba
dogo yanda kaga wannan mutumin dake kusa da kai a xaune, shi ma da kyar idan baya
daga karafunan nan na turawa don kirjinsa duk a tale, kana ganinsa kaga d'an boko
don gilashi ne ma a idonsa, toh irin wannan ne baxai bari ta karasa sakandarin
jaraban ba idan anyi aure, gaskiya Ahmadu ku maida hankalin ku sosai a kan maganar
nan da nake gaya maka, wllh kullu yaumin fargabana mijin da Imaan xata aura tunda
ga yanda Allah ya halitto ta, mai rufin asiri kadai baxai iya da lalurorinta ba sai
hamshakin mai kudi, da yau ace Bukar ya tara yara kamar yanda ka tara to fa da
imaan bata kai labari ba don nasan ba xai tara uban kudin da xai dinga kashewa kan
ciwonta ba, to astagfirullah kaga amfanin haihuwan kadan ba da yawa ba, to yanxu
dai ga yaro matashi kyakkyawa d'an masu kudi ya fito, bari ma kaga abinda ya ban
Ahmadu"

*The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included


in the payment group.

24....

*Just funny... Earlier this morning nayi post a kan masu siyar min da littafi nace
na bar su da Allah, da kuma masu forwarding min especially wa enda ba wai siya suka
yi ba fa, su dai aikinsu kawai suyi ta forwarding, ni ban ma yarda sun san da Allah
ba tunda basu tsoron a hada su da shi ma.... amma the kind of messages da suka
dinga shigo min was funny wai ni nayi Allah ya isa a kan littafin Imaan.... har na
gama Noor Hayat ban daga kai na kalli masu fitar min balle masu karantawa for free
ba, But Imaan is totally different don wannan karan don anga ina shiru ina kauda
kai har da masu creating group na musamman mutane su basu dari ko dari da hamsin su
saka su a ciki su dinga masu update, is this fair plss??? Kuma ace kar in bar su da
Allah ni da hakkina, sannan idan masu forwarding waje basu yi forwarding ba hakan
xai faru??? No way! wllh domin kin siya littafi kin ba kawarki ko yar uwarki ta
private ko a jikina it's ur property, I 100% agree to that, but not to the extent
of sharing it to groups wannan kashe kasuwa ne, idan wani na da niyyar siya ya
gansa a group yana galantoyi wllh ya fasa siyan kenan and this isn't fair, shi sa
duk end of page nake reminding masu karantawa a groups it's not for FREE amma ban
taba cewa Allah ya isa ba, ni kunya ma nake ji in rubuta haka wllh, sai dai ince ur
cup of coffee, to masu cewa Allah ya isan fasa fitar masu da books aka yi? Of
course noo, to yau kam masu siyar min da littafi sun kai ni bango ne shi sa na
rubuta hakan, I wrote 8 good books for free online kar ku manta😕, kuma duk sun samu
karbuwa wajen ku, ku ma sai ku min halacci kuyi patronizing, writers da suka fara
rubutu of recent ma siyarwa suke balle mu first online writers da ake tare tun tale
tale?? Wasu kuma na ganin lambata ina sawa karshen page amma su tsallake suje su
siya gun masu ci da hakkin mutane, kun ga kuwa ba ni suka biya ma kudi ba, kuma
hakkina suka karanta without paying, plss understand me here, su wa enda na bari da
Allah sun san kansu, yo wa gareni da xan hada su da shi ban da Allahn dama, ni dai
ba ruwana* 😃
_Sorry for the longggg surutu but I have to explain my self pls, I felt soo bad
saboda wa enda suka siya littafin ne suke nuna rashin jin dadin post din, afuwan a
yafe min pls, anyi na farko anyi na karshe in sha Allah, ba sai na sake cewa komai
ba ma coz I know I have Allah_😍

Mikewa inna tayi ta dauko kudin da Sadeeq ya bata a daki tana murmushi tace "Dubu
goma ce ciff, babu yanda banyi da yaron ya bari ba ya ki, toh ni ko xan tsaya muna
jayayya da shi ne, haka dai na hakura na amsa" Mujaheed ya kasa daina kallonta ko
kiftawa babu, Abba ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh Allah ya saka da alkhairi" inna
tace "Toh ya xancen turo magabatan nasa fa?" Ya d'an yi shiru sai kuma yace "Inna
da dai a jira Sadeeq ya dawo koh?" A fusace inna tace "Oh oh Allah waye kuma
Sadeeq?? dole sai Bukar din yana nan? kai ba mahaifi kake wajenta ba, Bukar da idan
ya tafi Habuja kamar baxai sake dawowa ba, ni ba ruwana ka kirasa a waya ka gaya
masa komai in ma ya kama ya taso ne ya taso kawai, to nasan bayan shekara nawa xai
dawo idan muka tsaya jiransa??" Abba ya dinga gyada mata kai nan ko neman abinda
xai ce mata yake, can dai yace "Toh ko xa ki kirasa da kanki Inna??" ta tsuke fuska
tace "Baxan kira ba idan baxa ka kira ba a bar kiran, iyaka in shirya in tafi kano
gun kawun ku ya amshi gaisuwa da kudin auren kawai, ai ba ku kadai ke da iko da ita
ba" cikin low voice Mujaheed yace "Meyasa baki maganan wa enda suka girmeta a gidan
sai ita??" Inna ta masa wani kallo tace "kana nufin su ku kenan masu tambadewa a
titi, wato kai da Isuhu, to ni meye ruwana da rayuwarku fisabilillahi? Da ku yi
aure da kar ku yi duk daya wllh tunda baku da mafada, ko ni na ajiye ku da xan maku
magana idan ba rainin wayo ba, ko me na hada da ku? Ga dai iyayenku suna kallonku
basu ce komai ba sai ni bare? Imaan dai Allah ya fiddo mata zankadeden miji in sha
Allah, to ni na ajiye ku da xan maku magana idan ba rainin wayo ba, ko me na hada
da ku??" Abba ya mike yyi kasa da kai yace "Toh ina fita ynxu xan kira Sadeeq din"
Inna tace "Gwara haka dai, kana kiransa ka zayyane masa duk abinda nace tass, kace
masa yaron ma takwaransa ne shi ma Sadeeq ake ce masa, baka gansa ba Ahmadu
kyakkyawa ga hanci kamar an xana biro, ga idanuwa maa sha Allah" sai da safe Abba
yayi mata ya nufi kofa Mujaheed ya bi bayansa, inna ta bi Mujaheed da harara tace
"Oho dai bakin cikin ka xai kare maka Mujaheed, daga jin kanwarka tayi miji sai
bakin ciki ya bayyana karara a fuskar ka? To aniyar moda ta bi randa, imaan dai nan
gani nan bari" Shi dai bai tanka ta ba har ya fita ya kulle kofar. Abba na fita ya
shiga kiran d'an uwan nasa, daddy na dagawa ko gaisawa basu yi ba yace "Toh tsohuwa
dai ta 6aro mana wani babban aikin Sadeeq" Daddy yace "Tohhh, Me kuma ya faru" Abba
yace "Wai aure take son ayi ma Imaan" Daddy ya wani bude ido da mugun mamaki yace
"Aure kuma Barrister?" Abba yace "Wllh, and she is damn serious, kawai kirana tayi
daxu tana nemana shine na taho and this is what she said" cike da confusion Daddy
yace "Aure fa kace Barrister, toh ita tayi mata mijin?" Abba yace "Na dai ji tana
ta xancen d'an gidan Bulasawa, ban san ko ita Imaan din ta ma san sa ba, I tried
telling her she is too young ko secondary bata gama ba but inda inna take shiga ba
nan take fita ba, she didn't even give me a listening ear, she so mean it, so ko
xaka kirata yanxu??" Daddy yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un me yasa inna
take haka" Abba yace "Kaga gobe Friday if you can squeeze up things ka taho sai mu
san yanda xa mu yi koh? Ni bana son in ja xancen ne ranta ya baci kasan yanda take
abubuwanta, shi sa mata sallama kawai na fita" Daddy yace "But ka fa san idan tayi
deciding abu it's hard ta canxa barrister" Abba yace "Don't worry, ka dai taho
goben sai mu san abun yi in sha Allah" Daddy yace "Toh Allah ya kai mu" sallama
suka yi Abba ya kalli Mujaheed da kansa ke kasa yana tafiya absentmindedly, Abba ya
dafa shoulder dinsa yace "Are you okay son?" Kallon Abba yyi da sauri, sai kuma ya
d'an yi murmushi yace "Sure Abba, kawai dai har yanxu I am surprise at what grandma
is planning" Abba ya sauke ajiyar xuciya yace "Imaan din har nawa take ma banda
abun inna, ga shi ba wani lafiyan kirki gareta ba, inna dai kam abun ta gaba yake
ba baya ba, ita kawai ayi auren saboda d'an mai kudi ne, Allah ma kadai yasan
abubuwan da ta fada ma yaron, tun tasowar mu muke fama da ita a haka muna ta
lallabawa dai, gashi bbu abinda ya canxa har yanxu, abu kuma ya xo ya hade da
tsufa, sai dai mu yi ta mata addu'a, Allah kuma ya rabamu da ita lafiya, amma
abinda ya ban mamaki shine ta yanda ta san yaron, kuma anya Imaan ta ma san sa
kuwa?" Mujaheed dai bai ce komai ba sai pressing din counter dinsa yake a hankali,
Abba yace "Kai kasan yaron Bulasawan da take fadi?" Mujaheed ya girgixa kai, bayan
few seconds yace "But ina ga Yusuf baxai rasa sanin sa ba don yana mingling da irin
su" Abba yyi murmushi yace "I will call and ask him" suna isa sashinsu, Abba yace
"Don't forget ka fita ka siyo mata naman da tace" a hankali yace "Toh" motarsa ya
bude don makullin na hannunsa ya shiga, Abba kuma ya shiga cikin gida, Mujaheed ya
ja motar ya fita compound din. Mujaheed na dawowa daga siyo Tsiren da Abba yace ya
nufi part din su Imaan, a hankali ya kwankwasa kofar sannan ya murda yaji a bude,
shiga parlon yyi, ya sauke idonsa bayan sun hada ido da Ammi yace "Gashi Abba yace
a kawo mata" Ammi ta kwalo ma Imaan kira don tana bedroom dinta, ko me ta tuna sai
kuma ta mike xata amshi ledan sai ga Imaan ta fito sanye da kayan barcinta, xata
shigo parlon Ammi ta dinga mata wani kallo, da sauri ta juya ta koma dakin ta rufe
kofar, Ammi ta karbi ledan ta nufi dakinta ba tare da ta amsa sai da safensa da ya
mata ba, juyawa yyi ya fita parlon ya kulle kofar. Washegari daga Imaan har Ammi
suka yi mamakin xuwan Daddy ba notice, Bayan Daddy ya shiga bedroom Ammi ta bi
bayansa, xaune ta samesa gefen gado tace "Yallabai xuwa babu notice, hope lafiya
dai" Yace "Ehh I came for something urgent, xuwa lahadi xan koma in sha Allah" tace
"Allah ya kai mu" shiru yyi hakan yasa tace "A kawo maka breakfast ne?" Yace "Noo,
Ina son maki wani tambaya, Imaan tana da wani ne dake nemanta?" Ammi tayi shiru
tana kallonsa a bit shocked, can tace "Lafiya Yallabai?" yace "I am asking you..."
girgixa kai Ammi tayi, she have got no option then to protect her daughter, a
hankali tace "Not at all, ita da bata xuwa ko ina daga boko sai islamiyya, is there
any problem" yace "Ohk" mikewa yayi ya shiga bathroom ita kuma ta fita a sanyaye
tana mamakin tambayar, to me kuma ya faru, tana fita parlor tayi still don sai a
sannan ta tuna abinda Imaan tace inna tayi jiya, wato har inna ta kirasa kenan ta
gaya masa, daki ta tafi gun Imaan, tana kallonta tace "kin ga abinda nake guje maki
ko, to ina jin inna ta kira Daddyn ki har ta fada masa xancen yaron jiya, without
any doubt abinda ya dawo da shi kenan" Imaan ta xaro ido a tsorace tace "Daddy ya
maki maganan ne?" Ammi tace "Dama tun ba yanxu ba nace maki ba ruwana kar ki ja min
matsala, gaskiya sai ki san abinda xa ki ce ma Daddyn ki, don't involve me in this"
daga haka ta fita dakin, imaan ta kasa xaune waje daya gabanta ya dinga faduwa
hawaye cike idonta, daga karshe ta fice a dakin, direct part din inna ta nufa
hawaye cike idonta.... shigar Mujaheed parlon kenan ya je gaisheta daga inda yake
tsaye, ko amsa gaisuwarsa bata yi ba tana kada shayi a kofi tace "Ni fa Mujaheed
tsabar yanda nasa maganar jiya a rai har mafarkinsa sai da nayi wlh, wai ga Imaan a
daula iya daula babu abinda babu a runtumemen gidan na more rayuwa, har naje masu
sati biyu, in gaya maka yau... a kawo min kaji, gobe.... a kawo xabee, gata... a
kawo kwayakwayay, citta... a kawo tika tikan Kifaye, ga gwangwanin madarana da
bournvita da suga an min dak'en da shi a daki, nayi wani jazur da ni sai sheki nake
malam, Shi ko bulasawan kullum xai fita sai ya ajiye min dubu biyu in sa kati, wllh
tllh ba karya nake maka ba Mujaheed" Mujaheed dai na tsaye daga bakin kofa yana
kallonta, ta tabe baki ta yagi bread ta kai baki tace "Ni dai ba ruwana, Ahmadu ya
shigo in san yanda suka yi da Bukar din" Jin an bude kofa Mujaheed ya juya, imaan
ta shigo ko takalmi bata cire ba, tana kallon inna kamar xata fashe da kuka tace
"Inna me kika ce ma daddy na?" Inna tace "Waye kuma Daddyn ki?" Imaan tace "Wai ni
nace maki wanda kika gan ni da shi jiya saurayina ne??" Inna ta kyabe baki tace
"Kya ji da shi, ni dai baxan kula ki ba ki xageni, na riga na gama maganata, wllh
Mujaheed baka ga yanda ta ji kunya ba jiya da ta gan ni kamar fa ta nutse, ni dai
ban bi ta kanta ba ban kuma kulata ba bakina a leko na ja Bulasawan muka shigo
ciki, to kuma meye xata shigo min ta tale baki kamar wata agwagwa? Ni dai ba
ruwana" Mujaheed ya juya ya fice daga parlon... imaan ta durkushe wajen tana kuka
sosai tace "Wllh idan kika sa Daddy ya min fada ko ya dokeni ni dai Allah na kallon
ki Inna, ni ban ce naki saurayina bane, abokin yaya Muhsin ne ni ban san shi ba"
Inna dai na ta cin bread dinta tana shan shayi, Imaan ta gaji da kukanta ta mike
xata fita inna tace "Toh aniyar ki dae dama ya bi ki a baya, ba ruwana. Ni nasan
wani yaya Muhsin" imaan bata tanka ta ba ta fice hankali tashe. Tsaye Imaan ta ga
Mujaheed dai dai inda xata sha corner xuwa part din su, xata gudu ya kamo hannunta,
a tsorace tace "Wayyo yaya don Allah kayi hakuri inna sharri take min...." Fingers
biyu ya daura kan lips dinsa yana mata wani kallo, haka yasa tayi shiru tana
kallonsa gabanta na faduwa, ya nuna mata dakalin dake wajen fuska daure yace
"Xauna" Ba musu ta xauna kamar xata fashe da kuka, yace "What did I tell you about
standing outside with guys?" Hawayen dake makale idonta ya gangaro tace "Don Allah
kayi hakuri yaya" yace "Me yasa baki jin maganata?" Tace "Ina ji fa yaya" yace "Toh
meye tsakanin ku da mutumin?" Ta girgixa kai da sauri tace "Ba komai, abokin yaya
Muhsin ne?" Yace "Me yake xuwa yi wajen ki?" Ta sunkuyar da kai ta rasa abun cewa,
strictly yace "Answer me now before I give you an unclean slap" Ta fashe da kuka a
hankali tace "Ba komai fa yaya, kayi hakuri plss" dauke kai yyi na few seconds, sai
satan kallonsa take, ganin yanayinsa gabanta ya tsananta bugawa, can ya kalleta ya
durkusa gabanta calmly yace "Abba da daddy xa su kira ki su tambayeki what's
between you and the guy, me xa ki ce masu?" Ta sauke idonta a hankali tace "Xance
masu abokin yaya Muhsin ne" Ya wani hade rai yace "No, kalleni da kyau" Daga kai
tayi tana kallonsa, sosai gabanta yyi mugun faduwa, a hankali yace "You tell them
babu komai tsakanin ki da shi, kin ji ni?" Ta gyada masa kai kawai, yace "Good, ko
baki son ki gama karatu kamar Seeyama? Baki son ki tafi university" Ta turo baki ta
boye fuskarta da hannunta murya can kasa tace "Ina so mana yaya" Jin bai ce komai
ba ta xame hannunta a hankali ta ga kallonta yake, dauke idonsa yyi murya can kasa
yace "Idan ma yace son ki yake kice masu ke baki sonsa" Yar dariya tayi, ya jefa
mata wani kallo xai yi magana sai ga Abba da Daddy xa su part din Inna, mikewa yyi
da sauri, Daga Abba har daddy kallonsu kawai suke, Mujaheed yyi kasa da kai yana
gaida daddy, daddy ya amsa da murmushi yace "Ya aiki Muhammad" Mujaheed yace
"Alhmdllh" Abba yace "I called ur line baka daga ba" Mujaheed yace "Na bar wayar
can daki naje gaida Inna ne" Abba yace "Ohk" a hankali Imaan ta gaida Abba ba tare
da ta yarda ta dago kanta ba, Abba ya amsa daga haka suka wuce tare da Daddy da ko
kallonta bai sake yi ba, mikewa Imaan tayi tana kallon Mujaheed, yace "Kin ji
abinda nace maki koh?" Kai ta gyada masa a hankali, daga haka ya wuce ya bar ta
wajen a tsaye, Mujaheed bai karasa part din su ba mota ta shigo gidan, Driver na
parking Umma ta fito, suna hada ido gabansa ya fadi sosai ya juya da sauri to make
sure Imaan bata biye da shi a baya, driver ya sakko motar ya xaga ya bude booth,
set biyu na boxes masu d'an karen kyau da tsada ya fiddo a booth din yyi cikin gida
da su, Tuni Umma ta wuce ciki ita ma, Mujaheed ya bi su da ido. Tare Abba suka
shigo parlon da Daddy, Inna tace "Naji dadi da ka ba lamarin nan muhimmanci ka taho
Bukar, ina fatan kuma kayi murna da jin wannan abun arxikin?" Daddy yace "Ina
kwana" tace "Lafiya lau, ya ka xo?" Yace "Alhmdllh" tace "To madallah" Daddy yace
"Jiya Barrister ya min bayanin komai...." Ta washe baki tace "Toh Alhmdllh" yayi
kasa da murya yace "Amma inna, Imaan yarinya ce sosai sannan ga ta ba lafiyayya
ba...." Inna ta katse sa tana kallon Abba tana nunasa tace "Kai dai wllh Ahmadu
baka yi ba, yanxu sai da ka xugesa sannan xaku shigo min nan?" Daddy yace "Aa baki
fa jira na kai aya ba inna" mikewa tayi a fusace tace "Babu wani xancen kai aya
Bukar, ni kai da d'an uwanka xaku munafurta daga taimako, ni xa ayi ma cin
dunduniya, waye baya son nasa ya huta a xamanin nan, koko xan ma Imaan xa6in da xae
cuceta ne ko ance maku ban san abinda nake bane, ku kuka haifeni ko ni na haifeku,
to wai ma ku tsaya tukun, wai idan aka yi auren nan tare za mu tare gidan da ita??
duk girman gidan naga dai nata ne ita kadai ba tare da ni xata more rayuwar xaman
gidan ba, iyaka bai fi a sati inje sau biyar ko shidda ba, to idan baku aurar da
ita ba jik'a ta xa kuyi ku shanye ko enlargement xa ku yi da ita kuna kallo a
parlor, yau naga abinda ya isheni bai ishi ubangijina ba" Daddy yace "Kiyi hakuri,
bai kai haka ba inna, sai ki hada mu da yaron ayi magana ta fahimta" Inna ta goge
xufan da take yi tace "To yanxu naji batun kirki, sai dai kuma ban san inda za a
samo sa ba, amma ita imaan din ai baxata rasa lambarsa ba, ku kira ta ta taho a
kwashe min a wayata in kirasa" Abba dai sai kallon mahaifiyar tasu yake, Daddy ya
ciro handkerchief din aljihunsa ya share xufar goshinsa, Abba ya sauke wani
boyayyen ajiyar xuciya yace "Toh xa a amshi lambar nasa a gunta in sha Allah" Inna
tace "Toh idan kun kirasa me xa ku ce masa?" Abba ya d'an kalli daddy, Daddy yace
"Ce masa xa mu yi ya turo magabatan nasa" Inna ta xauna kan kujera tana murmushi
tace "Toh Allah maku albarka, ya buda maku" mikewa Abba yyi, daddy ma ya mike yace
"Toh anjima xa mu shigo in sha Allah" tace "Toh shikenan amma kar fa ku ce xa ku ja
lokacin don yaron yace a matse yake yyi auren" Babu wanda ya tanka ta cikinsu har
suka fita parlon.

*The book Imaan is not free*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included


in the payment group.

Imaan. Page 25

Abba na kallon Daddy yace "Kada kayi ma Imaan magana tukun, I want to confirm who
the guy is from Yusuf, Mujaheed yace baxai rasa sanin sa ba" Daddy yace "Toh
shikenan, amma I will so deal with her, ita har nawa take xata fara kula samari can
you imagine?" Abba yace "Nace kar kace mata komai tukun, ni nasan abinda xan yi"
Daddy bai iya yace komai ba, don gaba daya ransa ya gama baci, suna isa part dinsa
ya shiga, Abba kuma ya karasa nasa part din. Direct bedroom din Mujaheed Abba ya
tafi ya bude kofar, Mujaheed na xaune tare da Umma a dakin ya sunkuyar da kai yana
saurarenta, Umma na ganin Abba tayi shiru daga abinda take cewa, Abba yace "Ka
sameni parlor Muhd" a hankali Mujaheed yace "Toh Abba" daga haka ya rufe kofar,
Umma tace "Wai me ke faruwa, jiya naga mood dinsa gaba daya sai a hankali, halan
tsohuwarsu ce ta tada wani fitinar?" Murmushi Mujaheed yyi yace "Ehh.." Umma ta
buda ido sosai tace "Wai me take so?" Kamar Mujaheed baxai ce komai ba sai kuma
yace "So take ayi ma Imaan aure" Umma ta xauna da kyau da mamaki tace "Aure kuma?
imaan din saurayi gareta da xa a mata aure? Ko tana da yaron da xata hada ta da shi
ne?" Mujaheed ya d'an yi shiru sannan yace "Ban sani ba Umma" Umma ta hade rai tace
"Baka sani ba duk kusancin ka da inna, ko dai gaya min ne baxa ka yi ba??" Ya
girgixa kai yace "Umma ni bata gaya min komai a kai ba" Tuni mood din Umma ya
canxa, Mujaheed dai kallonta kawai yake, Tabe baki tayi tace "To ma gani ai, yanxu
dai xaka yi transfer din ne ko Safeenar xaka ma?" A hankali yace "Anjima xan maki
Umma" ta mike tace "Toh ina jira" daga haka ta nufi kofa ta fice dakin, Dafe kansa
yyi na kusan minti daya, can dai ya tashi ya tafi parlon Abba. Abba na kallonsa
yace "Mun gama magana da Yusuf yanxu a waya yace bai san yaron ba, so what I want
you to do now is ka samo min number sa a wajen Imaan, but ita kanta bana son ta san
ka dau number yaron, do it wisely" Shiru Mujaheed yyi, Abba yace "Yea just get his
digit by any means without her knowledge" Yace "Toh Abba" Abba yace "I want it
before the end of today" yace "I will do that in sha Allah" Abba yace "Xaka iya
tafiya if u have anything doing" mikewa yyi ya fita, Umma ya gani sanye da Hijab ta
rike purse ta nufi kofa, ko lura da shi bata yi ba har ta fita, ya bi ta da kallo
sannan ya wuce sama . Imaan na xaune kitchen tana kallon Ammi dake kwashe girkin da
tayi a warmer, Ammi tace "Kafin Magrib idan ban dawo ba sai ki kai mata" Imaan dai
bata ce komai ba, bayan Ammi ta gama tana kallonta ta marairaice tace "Ammi amma me
yasa baxan bi ki ba plss" Ammi tace "Nace ki bari lahadi idan kin dawo islamiyya
kije, yanxu akwai mutane da yawa a gidan you will be uncomfortable" a hankali tace
"Toh Ammi" Ammi ta fita kitchen din ta mike ta bi bayanta, Hijab Ammi ta sa ta
shiga parlor gun daddy tace "Yallabai xan je xa mu amshi lefen Halima" Daddy yace
"Ohk xan je cikin gari dama, let me drop you" Imaan ta turo baki ganin ita kadai xa
a bari gida, kamar xata yi kuka tace "Daddy in raka ka?" Wani kallo da ya tsorata
ta ya maka mata yace "You are stupid" sunkuyar da kanta tayi ta juya ta wuce daki,
Ammi ta hade rai tace "Ni ban gane haushinta da kake ji ba tun daxu, ka kuma ki
gaya min me ke faruwa" Yace "Madam dauko min makulli a daki and stop questioning
me" daga haka ya fita parlon, tabe baki tayi ta tafi ta dauko masa makullin, dakin
Imaan ta leka ta ganta xaune gefen gado tace "Ki tashi kiyi sllh sai ki sa kallo ko
a daki ne kiyi" daga haka ta rufe mata dakin, kusan tare suka Isa parking space da
Mujaheed, kansa a kasa ya gaida Daddy, daddy ya amsa yace "Ya aikin?" Yace
"Alhmdllh, xa ku fita ne Abba" Daddy yace "Ehh xan je cikin gari ne" Ammi ta hade
rai ta bude front seat ta shiga, Mujaheed dai bai yarda ya kalleta ba dama, daddy
yace "Toh sai na dawo" Mujaheed yace "Toh a dawo lafiya Abba" daga haka ya bar
wajen yana d'an murmushi, dama tun safe yake tunanin yanda xai hadu da Imaan har ya
dau lambar Sadeeq, kan farin kujera ya tafi ya xauna har Daddy ya fita gidan, bayan
kusan minti biyar ya mike ya nufi part din nasu, murda kofar yyi a hankali ya shiga
ciki yana kallon parlon ya ga bata ciki, ya jawo kofar ya rufe ya nufi bedroom
dinta, tsaye yyi bakin kofar kafin ya murda gently ya tura kofar, bai ganta dakin
ba ya d'an yi jim, running tap ya ji a bathroom ya gyada kai, ya tafi gaban madubi
ya dau wayarta dake ajiye xai yi silencing wayar yaga ma a silent yake, ya xura a
aljihu sannan ya karasa kofar bayin ya makale jikin bango, Imaan ta gama alwalan
da take ta bude kofar bathroom din ta fito, ji tayi an cafketa ta baya, ta fasa
wani ihu a raxane ya jawo ta jikinsa ya riketa gam, kafin ma ya kai ga cewa komai
ta gane shine saboda scent dinsa, k'asa cewa komai tayi ta dinga numfashi a tsorace
don tayi mugun tsorata, bayan few seconds numfashinta ya dawo dai dai, juyo da ita
yyi yana kallonta yace "Anjima Abba xai kira ki, kin dai ji abinda nace maki daxu
koh?" Kin cewa komai tayi, ya hade rai yace "Ba magana nake maki ba" tace "Naji
mana" Saketa yyi ya nufi kofa, ta murguda baki tace "After all he is just a frnd,
and he is...." juyowa yyi da sauri yana kallonta, tayi maza ta shige bathroom ta sa
key.
Mujaheed ya koma inda yake xaune ya fiddo wayar nata a aljihu ya shiga call log,
bai ga wasu calls ba sai na Daddy sai wani number da bata yi saving ba, ya dinga
kallon Number kafin yyi dialing, katsewa aka yi sai gashi an kira, ya daga ya kai
kunne yyi shiru, daga daya bangaren Sadeeq yayi sallama, Mujaheed ya cire wayar a
kunnensa ya katse kiran ya ciro wayarsa ya kwashe number sannan ya danna ma number
block ya goge log din kiran a wayar gaba daya. Imaan na idar da sllh ta debo
chocolates ta xuba su kan gadon ta sannan ta kunna kallo ta kwanta tana shan
chocolates tana yi, ta fi minti talatin tana kallo ta tuna Sadeeq ya kira ta tun
daxu bata dauka ba, mikewa tayi xaune da sauri tana kallon gaban madubinta don nan
ta ajiye wayar, da mamaki ta karasa wajen mirror din idonta a kan inda ta bar wayar
ganin babu shi, lkci daya Mujaheed ya fado mata, ta xaro ido tana fatan ba shi ya
dauka ba, duba dakin ta shiga yi amma ba alamar waya, kamar xata yi kuka ta dau
Hijab ta sa ta fita, bata tsaya ko ina ba sai part din su, Babu kowa parlon gidan
tsit don har sannan su maimoon basu dawo ba duk da ta ji alamar akwai mutane a
kitchen, ta wuce sama cikin sanda tana waige waige, tana ta tsaye corridor tana
kallon kofar dakinsa, karasawa tayi ta murda kofar a hankali ta tura, ba kowa dakin
sai kamshi me dadi dake tashi, ta karasa ciki da sauri tana kalle kallen dakin,
wayarsa ta gani gefen gado amma bata ga nata ba, dauke wayar tayi ta boye cikin
Hijab ta fita da sauri, da gudu ta karasa part dinsu ta shige parlor ta sa makulli
tana turo baki, xaunawa tayi tana kallon wayar ta bude taga ba lock, gallery ta
shiga ta ci karo da hotan Farida a WhatsApp images, ta shiga wajen, duk yawanci
hotunan farida ne ta ajiye wayar ta kunna TV nan parlor ta kwanta kan kujera ta ci
gaba da kallonta. Mujaheed na kallon agogon wrist dinsa yace "Aunty xan wuce aiki
yanxu..." Aunty dake hada stew tace "Toh Allah ya kiyaye" fita yyi daga kitchen din
ya wuce sama ya shiga dakinsa, makullin mota ya dauka ya kara feshe jikinsa da
turare, ya juya xuwa saman gado xai dau waya yaga babu, da mamaki ya dinga kallon
inda ya ajiye wayar, ya fito ya duba dakin Aunty ko ya mancesa a ciki ne yaga babu,
fitowa yyi daga dakin yana sauka stairs yyi still a zuciyarsa yace Imaan, to yaushe
ta shigo?? karasa sauka yyi ya fita parlon dai dai shigowar daddy compound din da
mota, a hankali yace "Shit" Ya tsaya har Daddy ya fito daga motar, ganin leda a
hannunsa ya karasa da sauri ya amsa yana masa sannu da dawowa, daddy yace "Thanks
Muhammad, Barrister ya dawo?" Mujaheed yace "A'a bai dawo ba" a tare suka karasa
apartment din Daddy dake amsa call da ya shigo wayarsa, Daddy yyi knocking, Imaan
dake kwance ta mike xaune da sauri tana xaro ido tace "Waye wannan?" Daddy yace
"Open the door" tashi tayi ta bude kofar, Daddy ya ci gaba da wayar da yake, ta
wani xaro ido ganin Mujaheed ta juya da sauri ta koma ciki, Mujaheed ya saci kallon
Daddy sannan ya shiga, Har ta dauke wayar nasa da ke ajiye kan kujera xata gudu ya
fixgota, ba daman tayi ihu hakan yasa ta gatsa masa cixo a hannu da duk strength
dinta, ba shiri ya saketa, da gudu ta nufi dakinta, sai a kan idon Daddy da ya
shigo ya dinga kallonta da mamaki yace "Zo nan Imaan, whats wrong with you?" Kamar
xata yi kuka tace "Daddy yaya ne" Mujaheed ya kasa daga kai ya ji kamar ya nutse a
wajen, Yyi saurin ajiye ledan hannunsa yace "Abba xan wuce gun aiki" bai jira cewar
daddy ba ya nufi kofa ya fita. Da Magrib imaan ta tafi kai ma inna abinci bayan ta
sake boye wayar Mujaheed da kyau, duk kiran da aka dinga masa na Farida kawai ta
daga, tun da ta fito compound dama gabanta ke faduwa, da sauri sauri ta karasa part
din Inna, Yusuf ta gani xaune, ta wara ido ta ajiye abincin hannunta tace "Lahh ya
Yusuf yaushe ku ka dawo?" Ya kalleta ya d'an yi murmushi yace "Daxu..." Inna tace
"Baki ga da ya shigo ba daxu duk a kode wllh, ai yanxu ya washe a haka, Allah ya
rufa ma ke da Mujaheed asiri ba ku je ba, baku da rabon wahala, amma wannan garin
ae ba wajen xuwa bane tirr" Imaan ta duka kusa da shi tana dariya tace "Toh me ka
kawo min ya Yusuf" ya shafa kansa bai ce komai ba, Inna tace "Yauwa ina maka xancen
kirki kafin wannan mata ta shigo..." Ya sauke ajiyar xuciya a hankali yace "Ae ina
ji" tace "Ko kai ya ka gani, wannan ba shawara mai kyau bace na kawo?" Da kamar
baxae ce komai ba sai kuma yace "Da dai kiyi hakuri a bar xancen inna...." Ta katse
sa da sauri tana gwalo ido tace "Xancen auren?" Calmly yace "Ehh" inna ta saki baki
tace "Ehh lallai kai da Mujaheed kun xama abun tsoro, yanxu har kai isuhu bakin
ciki kake ma yar uwar taka? Anya 'ya yan Ahmadu xa ku ga annabi kuwa? Ba kunya ba
tsoron Allah ku fito kiri kiri kuna nuna ma yar uwar ku bakin ciki" Shi dai
kallonta kawai yake, imaan ma sai kallonta take don bata gane kan xancen ba, Inna
na tabe baki tana girgixa kai tace "Har abada in dai ni yar halas ce ba ni ba
shawara da gantalallu irin ku, tun da haka ku ka xama gwara in yi ta kaina, to wai
tsaya idan aka ki gabatar da ita jika ta xa mu yi mu baku ku shanye?" Nan ma dai
bai ce mata komai ba, ta rike ha6a tace "Ai ni na shiga uku, lallai 'ya yan Ahmadu
mugaye ne, sam ba alheri a ranku, to wai tsaya... ku xa ku aureta idan aka bar
xancen?" Ya kalleta yace "Kika sani?" Imaan da ta fara dago xancen ta wani hade rai
xata mike ta bar parlon Inna ta riga ta, tana kallon Yusuf cikin rashin hankali
tace "Ku har kuna da kudin da xa ku rike min jikata? Ku a su wa kuma Allah na tuba,
lallai kun cika marasa tsoron Allah, me kuma Imaan xata yi da kai ko Mujaheed Idan
ba sa6o kake son yi ba, ka ja mana fushin ubangiji...." Murmushi kawai Yusuf yake,
imaan ta nufi kofa xata fita, still tayi jin kamshin Mujaheed, juyawa tayi da sauri
ta nufi dakin inna tana cewa "Kar ku ce masa ina nan" Mujaheed ya shigo parlon
bayan few seconds, inna ta xauna tace "Imaan dai bata nan idan ma ita ka xo nema"
Mikewa Yusuf yyi ya nufi kofa ya fita. Bedroom dinta Mujaheed ya nufa direct, inna
tace "Da dai ka kinkimota ku fito don na share dakina tasss ba ko kwayar datti,
kada a bata min a cuce ni ba uban wani ke min gyaran ba" Imaan na jin dama inna
tace masa bata nan tasan dole xai shigo dakin, ta shige bayi da sauri ta sa
makulli, Mujaheed ya murda kofar bathroom ya ji a kulle, juyawa yyi ya dawo parlor
yana kallon inna yace "Kiyi mata magana ta ban wayata kada in sa ta kuka" Inna tace
"Ikon Allah ya fi gaban haka, lkcn da wayar ya fita hannun ka ya shiga nata sani
nayi Mujaheed? Kaji min raini dai, ni dai ta fito min daki gaskiya don ba Aisha
bace ta share min" ya gyada kai ya juya ya fita parlon, Da kyar Imaan ta yarda ta
fito bayan tafiyarsa da kusan minti goma, Inna dake tsaye bakin kofar bathroom din
tace "To uwar me kike masa da wayar sa ya taba ki ya taba alakakai ya taba jaraba,
ke dai ki daina tsokanan mutane kiyi ma kanki fada Imaan" Imaan ta fice a dakin,
inna tace "Da dai ya kama ki ya nakada maki shegen duka da xai gigitaki in ga me ce
masa don me a gidan nan, yarinya kawai kamar yar aljanu, wannan iri ta Bukar Allah
ka raba mu da ita lafiya, duk da dai lkci ya kusa" A hankali Imaan ta bude kofar
parlorn inna ta fita, ta gwammace tayi xagaye da ta bi normal route, da gudu ta
shige parlon su ta sa makulli tana murmushi. Karfe tara da wani abu Ammi ta shigo
dakin Imaan, Imaan dake xaune gaban madubi ta fito wanka kenan tace "Na xaton fa
kinyi bacci" Ammi tace "Ki ji da ni kwanciya xan je inyi" mikewa tayi ta hau saman
gado Ammi na kallon wayar kan gadon tace "Wayar waye wannan?" Imaan tace "Na yaya
ne" Ammi na mata wani kallo tace "Me wayarsa yake a nan?" Kamar xata yi kuka tace
"Ammi to ya dauke min nawa wayar ya ki ya bani" Ammi na kallonta da kyau tace "Kin
san Allah idan baki kame kanki gidan nan ba kin raba kanki da Mujaheed sai na sa6a
maki Imaan, yaushe ke da shi ku ka fara shirin da har xa ki dauke masa waya?" Imaan
dai bata ce komai ba, Ammi ta hade rai sosai tace "Let me make it brief, daga yau
na datse sabon alakar ku na gulma da Mujaheed, duk kika kuskura naga sabanin abinda
nace wllh sai kin sha mamaki na, ko dama kin hada wani abu da shi ne ban sani ba?
Kuma maxa ki kai ma inna wayar ta basa kayansa, naki kuma idan ya ga daman baki
toh, idan kuma bai baki ba ki bar sa, hope am clear?" Kai kawai Imaan ta daga mata
a hankali, Ammi tace "Shegantaka kawai, wai wani yaya, A'a ba yaya ba yayo, in sake
ganin kin kalli inda yake a gidan nan idan ban tsole maki idanuwa ba" daga haka ta
shafa mata lotion din maganinta sannan tace "Ki rage fan din, sai da safe" daga
haka Ammi ta fita ta kulle mata kofa, Imaan ta saka kayan baccinta ta koma mirror
tana shafa lotion a kafarta taji ana bude window, mikewa tayi da sauri tana kallon
window din, ido hudu suka yi da Mujaheed ta dauke kai, strictly taji yace "Bani
wayata" Ta make kafada tace "Nima ka bani nawa first" Yace "Na fara maki wasa a
gidan nan koh?" Ta ki cewa komai ta daura kafarta kan stool dake gaban mirror tana
shafa lotion dinta, jin shiru ta juya, kallonta taga yana yi da lumsassun
idanuwansa, ta hade rai tace "Yaya yanxu idan sauro ya cije ni na fara rashin
lafiya fa? Dubi yanda ka bude min window fa, ni dai ba ruwana idan na fara ciwo"
calmly yace "Kar ki bari in shigo gidan nan, wllh xan sa ki kuka, give me my phone
I want to use it" yar dariya tayi ta dau turare tana fesawa, yace "OK kina xaton
baxan iya shigowa bane?" Ta wara ido tace "Toh ai bance maka kar ka shigo ba" Tana
fadin haka ta karasa saman gado ta kwanta ta rufe da duvet, rufe window din yyi
yana gyada kai ya bar wajen. Mujaheed xai shiga parlon su suka hadu da Daddy, gaida
sa yyi da ladabi daddy na tambayarsa ya aiki yace "Alhmdllh" yana tsaye har daddy
ya shiga gun Abba, ya d'an yi jim, can ya tafi apartment din su imaan, ya fi second
goma tsaye ya kasa bude kofar, A hankali ya murda kofar ya shiga yana kallon cikin
parlon, babu kowa sai tv dake kunne, dakin Imaan ya nufa ya bude kofar, kwance ya
ganta har ta yi
bacci, ya dinga bin dakin da kallo ya karasa kusa da ita, daukar wayarsa da ta
ajiye bedside drawer yyi yana kallonta, gaba daya ta takure waje daya saman gadon
sleeping peacefully sai dai ta cire duvet din, dauka yyi ya rufa mata ya tafi gun
switch din fan din dakin ya kashe fan din gaba daya ya juya xai fita yaga Ammi
tsaye bakin kofa, still yyi ya kasa cewa komai, lkci daya ya sauke kansa ya fara
kame kame yace "I... I came to take my phone"

26.....

Ammi ta dinga kallonsa kafin a nutse tace "I want to give u this warning Mujaheed,
stay away from Imaan" shi dai bai yarda ya kalleta ba, bai kuma ce komai ba, juyawa
tayi ta bar bakin kofar, Mujaheed ya fita xuwa kofar fita parlon. Washegari da safe
Imaan ba inda bata duba ba a dakin tana neman wayar Mujaheed ganin bata gansa inda
ta ajiye ba, kamar xata yi kuka ta fito parlor sanye da uniform din islamiyya, tana
kallon Ammi a hankali tace "Ammi kin ga wayar nan na jiya?" Ammi ta mata wani kallo
tace "Wanda kika bani ajiya?" Shiru tayi bata ce komai ba, Ganin ko kallonta Ammi
bata sake yi ba ta juya ta wuce dinning don yin breakfast, mamaki ta dinga yi ta ya
xata nemi wayar ta rasa a inda ta ajiye, daga karshe tayi concluding kawai Ammi ce
ta boye, ta tura soyayyen dankalin gabanta ta mike ta dawo cikin parlor, safarta ta
sa ta xura Hijab din makarantarta ta dau jaka tana kallon Ammi dake parlor kamar
xata yi kuka tace "Ammi fa kila xai yi amfani da wayarsa don Allah ki bani in kai
masa plss" Ammi ta daga kai tana kallonta, da sauri Imaan ta fice daga parlon don
ta san sauran, parking space ta tafi ta tsaya tana jiran su Maimoon su fito,
Mujaheed ne ya fito tare da Yusuf, Imaan ta dinga kallon hannunsa da mamaki ganin
wayarsa, bai ko kalli inda take ba ya nufi gun motarsa ya bude ya shiga, Yusuf dake
kallonta yyi murmushi yace "Why are you looking at him that way" kamar xata yi kuka
tace "Ya Yusuf jiya ya dauke min wayata shine nima naje dakinsa na dauke nasa toh
yanxu ga na sa a hannunsa ban san ya aka yi ya dauke ba, ni kuma nawa har yanxu ya
ki bani" Yusuf yace "Toh me yasa ya dauke wayar ta ki?" Tace "Nima ban sani ba kuma
har daki na ya shiga ya dauka, ni dai wllh ya bani waya ta xan je in gaya sa da
inna" Yusuf ya kalli Mujaheed da har ya tada motarsa amma idonsa na kansu, dauke
kai Yusuf yyi yace "Yaushe har ku ka fara shiri da Mujaheed da har ya shiga dakin
ki ya dauke waya?" Ta turo baki tace "Ni ba wani shirin da mu ke, kawai ganinsa
nayi a dakina bayan Ammi da daddy sun fita" Yusuf ya sake kallon Mujaheed da yaki
driving din motarsa, ya dauke kai, Imaan tace "Ya Yusuf ka yi masa magana plss kuma
fa ana kirana a wayar" Yusuf yace "Wa ke kiran ki?" Boye fuskarta tayi ta fara
dariya, Yusuf ya dinga kallonta, ta xame Hijab din da ta rufe fuskarta a hankali,
sai a sannan ya sauke idonsa yace "Baxa ki gaya min ba" ta wara ido tace "Ya Yusuf
wani ne, he is my friend" jin Yusuf bai ce komai ba tace "Ni dai kafin su fito bari
in je in gaya ma inna" daga haka ta wuce ya bi ta da ido kamar yanda Mujaheed ma ya
bi ta da kallo, waje ta ga inna tana ta faman goge window with seriousness, Imaan
tace "Ina kwana inna" Inna ta d'an kalleta kafin ta dauke kai tace "Aa ba wani inna
ina kwana, ke din ce xa ki xo gaisheni takanas da safe, ke dai fadi abinda ya kawo
ki ina ji" Imaan tace "Toh ko ba yaya bane ya dauke min wayata tun jiya ya ki bani"
Kamar xata yi kuka ta kare maganar, Inna ta ajiye tsumman hannunta a bokiti da
mamaki tace "Waye kuma yaya?" Imaan ta rungume hannunta xata yi kuka, inna tace
"Lallai ba lafiya, shi Mujaheed din akwai wani alaka ne tsakanin ku wanda ni ban
sani ba da har xai dauke maki waya? ko sata ya fara yi ba a sani ba a gidan, ni dai
naga abinda ya isheni, gaskiya wannan d'a na Ahmadu yana cutar mu a gidan nan, to
meye kuma xai dauke maki waya kamar shi ya siya? ko yana bin ki bashi ne? Toh a
gaskiya ya kamata Mujaheed yyi aure ya kama gabansa na gaji da maganarsa kuma haka
Allah ya gani nayi kokari, shekara kusan talatin da biyu ana abu daya, wannan ai
fitinanne ne mara son xaman lafiya, mu je gun Ahmadu in ji ko shi ke koya masa ya
dinga walakanta ni a gidan nan" daga haka inna tayi gaba imaan ta bi bayanta, Inna
ta tsaya kamar warce taga mugun abu ta juyo da sauri tana kallon Imaan tace "Toh da
ya dauke wayar ta ina Bulasawan ke kiran ki?" Imaan tace "Toh ba wayar na wajensa
ba, kila ma ana ta kirana ya daga" Inna ta saki salati tace "Ashe yau xa a ga
barbadin fitina a gidan nan, mu je gun Ahmadun" Yusuf na nan tsaye inda yake,
Mujaheed kuma ya wuce kenan inna ta iso kamar xata tashi sama, Yusuf na kallonta
yace "Ina kwana Inna" a fusace ta juya tana kallonsa tace "Da ban kwana ba xaka gan
ni, ko a titi kake gaida uwarka Amina, to hirr dinka... Dama duk gantalallen da
yace jikata xai sa ma ido ya dinga yi ma bakin ciki to yyi ta kansa inyi nawa a
gidan nan, ba ruwana, kada ma ka sake gaisheni bana so, ko kuma in tsine ma
gaisuwar...." Kallonta kawai Yusuf yake bai ce komai ba, Inna ta wuce kamar xata
tashi sama, imaan da ta ki yarda ta kallesa ta bi bayanta, Anty na goge goge parlon
Abba inna ta shiga imaan na biye da ita, Anty tana kallonta tace "Ina kwana Inna?"
Inna tace "Ke ba xancen ina kwana, Amina ashe kema jaraban kika haifa ban sani ba
sai jiya, ashe Isuhu ma ba mutumin kirki bane na banxa ne ni ban sani ba, ashe
halinsa daya da tijararren nan Mujaheed, to Ahmadu ya ga ta kansa kuwa don wannan
ba yaran nunawa bane, banda haka ta ya xa su nuna bakin ciki da hassadansu a fili
kan jikata, daga Allah ya axurtata da mai kudi saurayi sabon jini sai hassada ya
tashi? toh wllh su cire idanuwansu kan imaan, shi Isuhu tsabar shaharan da yayi a
fannin bak'in ciki ce min yyi a bar xancen sabon saurayin ma gaba daya, ke ki ji
min mugunta, kice min lalacewa bai xo duniya ba?? saboda mamakin abinda yace min
sai nake tambayarsa ko idan aka bar batun sabon saurayin su xa su aureta?? Budan
bakin katon sai ce min yyi to na sani ko su xa su auretan? Ke ki ji wani sa6o fa,
kawai ya ja gida ya rushe da ni a ciki" Inna ta fara matsar kwalla tace "Yanxu
Isuhu bai ji kunyar gaya min haka ba, idan ba ta6ewar basira ba dama ina su ina
Imaan daga shi har Mujaheed din, wllh ta fi karfinsu, me garesu da har xa su rike
min ita salon wataran in xo daukar gawarta ina kuka suna bani hakuri, haka kawai su
kai ni su baro, yanxu fisabilillahi Allah ya dubeni ya fiddo mata dai dai ita kuma
sai bakin cikin yan uwa ya tashi, to Allah ya so ni dama ba abinda na hada da su,
ba dangin iya balle na baba, kawai ni dai nasan na haifi Ahmadu shi kuma ya
haifesu, ni sai ince Bukar ya tattara ya bar gidan ma...." Shigowar Abba yasa ta
dakata, Abba na kallonta yace "Lafiya inna?" A fusace tace "Ina fa lafiya Ahmadu
isuhu da Mujaheed sun fi karfina, kawai yaro ya dage ya kwace ma yarinya waya sai
kace Rukayya ce ta siya wayar, to wllh kafata kafar wayar nan yau idan ba haka ba
in bar kowa da Allah, kuma gaskiya a daina bata min rai gidan nan don duk ranan da
xuciya ta debeni idan ban bi Bukar Abuja ba ace bani bace" Abba dai ya kasa cewa
komai, Ajiyar xuciya Anty ta sauke tace "Toh ina Mujaheed din?" Inna tace "Sai ki
tambayeni Mujaheed ba tare ku ka kwana gidan nan ba ke kuma" Abba ya dau wayarsa
yyi dialing number Mujaheed, Mujaheed na driving ya daga wayar, Abba yace "Where
did you drop imaan's phone?" A hankali Mujaheed yace "It's with me" Abba yace
"Bring it back now" daga haka Abba ya katse wayar, inna ta xauna kan kujera tana
kallon Imaan tace "Xauna mu ga ta inda wayar xai fito" Imaan da ta ki yarda ta
kalli Abba ko Aunty ta karasa kusa da inna ta xauna, Inna tace "Ahmadu dai bai yi
sa'an 'ya ya ba gaskiya, don Mujaheed da Isuhu sai su iya kashe mutum" Anty ta ci
gaba da aikin da take yi, Inna sai girgixa kafa take bayan kusan minti goma sai ga
Mujaheed ya shigo parlon, Inna tace "Huuuu an dai ji kunya, fito da wayar da ka
dauke" Mujaheed dai bai ko kalleta ba ya mika ma Abba wayar, Abba ya mike ya ba
inna, inna ta karbe ta mika ma imaan tace "Tashi mu je, daga yau dama duk inda kika
ga Mujaheed ki canza hanya da gudu don ba mutumin kirki bane" Imaan ta mike ta bi
bayan inna, inna ta bude kofa tana cewa "Sai kuma ka sace wayar Rukayya idan ta
ajiye ba dai na imaan"
Karfe biyar saura na yamma Sadeeq yayi parking kofar gidan su Imaan ya kashe
motarsa ya jinginar da kujeran motar, Muhsin dake kallonsa yace "Ya da gyara xama
kuma Doctor" Sadeeq ya shafa kansa a hankali yace "Ni fa I told you ban taba xuwa
gidansu yarinyar da nake nema gun iyayenta ba, I don't even know where to start
from, to idan ma na shiga me xan ce masu? All that aside, ni ban ma san me yasa ake
nemana ba" Muhsin yyi dariya yace "Toh dama kuwa ina xaka je gidan su yarinyar da
kake nema bayan duk turawa ne Sadeeq, kaga kawai idan baxa ka iya shiga ba mu rabu
da su mu koma kada mu je ka kunyata ni gaskiya" Sadeeq ya sauke glass din idonsa
yana kallon Muhsin, can yyi murmushin sa mai kyau cikin cool voice dinsa yace "In
koma fa kace" Bai jira cewar Muhsin ba ya mayar da glass dinsa ya bude motar ya
fita, sanye yake da kananun kaya da suka yi matukar amsan jikinsa, Muhsin ya fito
motar yana kallonsa yace "Ehh lallai Abokina ya xurma da yawa" Sadeeq dai bai tanka
sa ba ya gama danne danne wayarsa ya kai kunne, bayan wani lkci yyi kasa da murya
yace "Abba gani a waje" Abba dake xaune parlonsa tare da Daddy yace "To madallah
bari they will lead you in now" Ba a dau lkci ba Yusuf ya fito kofar gidan, Kallon
Sadeeq ya dinga yi har ya isa inda suke, suka gaisa Muhsin yace "Ashe dai Engnr
kana gari?" Yusuf yyi murmushi yace "Sure ina nan, ya aiki" Muhsin yace "Alhmdllh"
Yusuf ya shiga da su compound din har xuwa parlon Abba, Sadeeq na shiga parlon ya
cire glass yyi kasa da kai har xai xauna saman kujera sai kuma ya fasa ya xauna
kasan rug ganin nan Muhsin ma ya xauna, har sannan bai dago kansa ba ya gaida su
Abba da Daddy, duk suka amsa suna masa sannu da xuwa, Daddy yace "Muhsin abokin ka
ne dama kenan" Muhsin yace "Ehh Abba abokina ne" Daddy ya gyada kai yace "That's
good" Abba ya kalli Yusuf da ya xauna yace "Where is M.A?" Bude kofar parlon aka yi
sai ga Mujaheed ya shigo parlon da sallama can ciki, kansa a kasa ya xauna kusa da
Yusuf sannan ya kalli Sadeeq da idanuwansa ke kan TV, gaisawa yayi da Muhsin, sai a
sannan Sadeeq ya kallesa yace "Barka da yamma" Mujaheed yace "Same to you" Abba na
kallon Sadeeq yace "Can I know you plss son" Sadeeq ya sauke idonsa kasa yace
"Sunana Abubakar Sadeeq Ahmad, ni haifaffen garin Kaduna ne, mahaifina asalinsa
d'an kano ne, na gama karatu na and I am working as a medical practitioner now"
Abba yace "Maa sha Allah, a wani anguwar ku ke?" Yace "GRA muke" Abba yace "Ohk can
i know ur dad?" Sadeeq ya d'an yi Shiru kafin yace "Alhaji Ahmad sunansa, d'an
kasuwa ne Abbana, yana kuma xaune nan Kaduna" Abba ya gyada kai cike da gamsuwa,
bayan few seconds yace "What is ur intention toward my daughter Abubakar?" Sadeeq
ya kasa dago kansa, Daga Mujaheed har Yusuf kallonsa kawai suke, can ya dago kansa
a hankali yace "Abba sonta nake da aure...." Mikewa Yusuf yyi yana kallon Abban
nasa yace "I want to excuse my self plss..." Abba ya gyada masa kai ya juya ya fita
parlon, Abba yace "Toh naji dadin jin hakan daga gare ka Abubakar amma kasan ajin
da Imaan take yanxu?" Ya gyada kai a hankali yace "Na sani Abba" Abba yace "Ohk
good, wani xancen kuka yi da kakarta last time da ka xo?" Murmushi yyi ya sunkuyar
da kansa, Abba yace "Yes go on" Yace "Abba ce min tayi idan tayi magana da ku xata
sanar min in turo magabatana" Abba yace "Ohk, kai d'an wajen Ahmad Bulasawa ne?"
Sadeeq ya gyada kai kawai, Abba yace "To yayi kyau, yanxu dai I want to ask for a
favor from you Sadeeq" Sadeeq ya daga kai a hankali yana kallonsa, Abba yace "But
before then bari in maka wannan alkawarin, Sadeeq in dai Imaan ta amince tana son
aurenka, wato ta yarda da kai, sannan iya binciken da xanyi idan ban ga wani flaws
dinka mara kyau ba ni nayi maka alkawarin xan baka Imaan in sha Allah, yea it's a
promise I am making" mikewa Mujaheed yyi yana kallon Abba yace "Abba I want to pick
a call" bai jira cewar Abba ba ya fita, Sadeeq dake kallon Abba yace "Toh nagode
Abba" Abba yace "Toh favor da nake son ka min ynxu shine.... Kakarta nake son ka
samu amma ba yau ba, but cikin satin nan, sai ka ce mata mahaifin ka bai kasar
yanxu kuma xai dau lkci kafin ya dawo, yana dawowa kuwa xaka sanar masa xancen
auren... Am doing this to allow my daughter finish her secondary schl, wato na da
shekara daya, kasan yanda tsoffin nan suke, there is nothing da xan gaya mata da
xata fahimce ni, amma kai idan kace mata haka to an gama komai, kaga ko da tana
gamawa ne sai ayi magana amma yanxu kam I don't think xan iya bada ta tana ss2,
that aside.... my promise of giving u my daughter's hand in marriage will count
only on one condition ko da ta gama secondary schl, the condition is that xaka
yarda ko bayan kun yi aure ta ci gaba da karatu a dakinta" Sadeeq ya d'an yi
murmushi yace "In sha Allah Abba" Abba yace "Toh Allah ya mana xabi mafi alkhairi"
Sadeeq yace "Ameen Abba na gode sosai, Allah ya kara girma" Abba yace "Allah maka
albarka" daga haka Abba yace masa xai iya tafiya, nan suka yi sallama da Daddy da
Abban sannan suka fita parlon. Muhsin na kallonsa yace "Mu je in gaida Mum dita"
Sadeeq ya xaro ido yace "No kai dai kaje zan jira ka a waje" Muhsin yyi dariya yace
"Common Mum dita fa na ce maka..." Da kyar ya ja Sadeeq suka nufi part din su
imaan, Bell Muhsin ya danna, Ammi na kitchen xata fito Imaan ta bude kofar dakin
ta, Wani kallo Ammi tayi mata tace "Kika san waye bakin kofar xa ki tafi a haka?"
Imaan ta xaro ido ta juya ta koma ta dau Hijab dinta ta sa ta fito ta nufi kofar,
bude kofar tayi, lkci daya tayi still tana kallon Sadeeq, Muhsin yace "Toh ko mu bi
ta kanki" da sauri ta juya ta bar wajen, kafin su shiga parlon har ta koma dakin ta
ta kulle, Dariya Muhsin yyi ya xauna, Sadeeq that was uncomfortable shi ma ya
xauna, Ammi ta fito kitchen ganin Muhsin tace "Ka shigo anguwar kenan" yayi dariya
yace "Ammi takanas nan fa na xo wllh" tace "Keep quiet kai din" yace "Ki tambayi
abokina Ammi" Ammi ta karasa shiga cikin parlon tana murmushi tace "Toh sannun ku
da xuwa" Muhsin ya gaidata, tun da Sadeeq ya kalleta sau daya bai sake yarda ya
kalleta ba shi ma ya gaisheta, ta amsa da fara'a tana masu sannu da xuwa, Muhsin
yace "Kawai ce masa nayi ya rakani in gaida Mum dita" Ammi tace "Toh kun kyauta
kuwa nagode, sai dai abokin naka kamar d'an uwan mu ne Bafillatani" Dariya kawai
Muhsin yake, Sadeeq dai yyi murmushi bai dago ba, Ammi ta tambayi Muhsin yayanta
sannan ta tambayi Sadeeq iyayensa, Sadeeq yace "Duk suna lafiya lau" Ammi na kallon
kofar dakin Imaan tace "Imaan" Muhsin yace "Kawai daga gani na shine ta shige daki
saboda bata da gaskiya bata gaida mutane ko a waya" Dariya Ammi tayi tace "Ae ban
san yanda xanyi da ita ba, ko nace tayi sai tace ta manta" Sai da Ammi ta kara
kiranta ta fito da kyar, wannan karan Hijab har kasa ta sa, Ammi tace "Baxa ki
gaida yayanki ba kika shige daki?" Bata yarda ta daga kanta ba har ta iso cikin
parlon kamar munafuka ta xauna kasa kusa da kujera tace "Ina yini Ya Muhsin?" Yana
murmushi yace "Lafiya lau Imaan, ya gida?" Tace "Lafiya lau" ta saci kallon sadeeq
da yaki kallon inda take tace "Ina yini" yace "Lafiya lau" Ammi tace "Ki dauko masu
ruwa fridge" mikewa tayi ta wuce kitchen, Ammi tace "Jiya mun yi waya da yaya yace
gobe xai dawo" Muhsin yace "In sha Allah, haka yace min" Imaan ta shigo cikin
parlon ta durkusa ta ajiye tray din ruwa da lemon five alive sai glass cups biyu,
Ammi tace "Na gama girki bari in xubo maku" Muhsin yace "A'a ki bar shi kawai Ammi
a koshe mu ke..." Ammi tace "Idan kai baxa ka ci ba sai abokin naka ya ci, ya
sunansa ma dai?" Dariya Muhsin yyi yace "Sunan Daddy garesa" Ammi tayi murmushi
tace "Ikon Allah, mai gida ne ashe" Muhsin ya kasa daina dariya, Imaan na ajiye
drinks din dama ta shige daki ta kulle kofa, Ammi na shiga kitchen Sadeeq yyi kasa
da murya yace "Don Allah ka rufa min asiri mu wuce Muhsin" ko kallonsa Muhsin bai
yi ba ya mike ya bi bayan Ammi kitchen, har ta fara xuba masu abincin a plate yace
"Ammi kinsan waye muke tare da kuwa?" Ammi ta juya tana kallonsa tace "A'a, waye?"
Kasa daina dariya yyi yace "Wllh surkin ki ne, saurayin Imaan" Ammi ta saki serving
spoon din hannunta tana kallon Muhsin baki sake tace "Amma baka da kirki Muhsin
shine ka bar ni ina ta xuba a parlor?" Dariya kawai Muhsin yake, Ammi tace "Ni dai
ba ka kyauta min ba, haba naga yaro ya ki sakin jiki, ita kuma Imaan sai na ci
mutuncin ta..." Da sauri ya dakatar da ita yace "Wllh bata sani ba, baki ga ita ma
duk ta ki sakin jiki ba" Ammi tace "Ni dai ka cuce ni, har kasa naje ina ce masa
mai gida" Shi dai bai fasa mata dariya ba, ta gama xuba abincin tace "Ai sai ka
daukar maku, ni kam na wuce daki" bata kara sauraransa ba ta fita kitchen din ta
wuce bedroom dinta, Muhsin ya ci abincinsa ya koshi, Sadeeq kam ruwa kawai ya sha
ya mike yace "I am waiting for you outside" duk yanda Muhsin ya so tsayar da shi
kin saurarensa yayi har ya fita, nan Muhsin ya kira Ammi a waya yace "Toh ya dai
fita Ammi ki fito mu yi sallama" Ammi ta fito parlon tace "Bai ci abincin ba kenan"
Muhsin yace "Ae baxai ci ba, Ammi Abbansu Mujaheed ne fa ya kirasa yana nemansa
shine muka taho tare" Ammi tayi shiru tana kallonsa da mamaki, can tace "Toh ya aka
yi da ku ka je?" Muhsin yace "Ba wani matsala wllh, Ai nasan daddy xai maki bayanin
komai idan ya shigo, yanxu dai xan wuce kinga yana can waje yana jirana" Ammi tace
"Toh shikenan ka gaida Hajiya da Hajjo" Yace "In sha, kice ma Imaan ta fito mu dai
mun wuce" daga haka ya fita parlon yana murmushi, a can kofar gida ya tadda Sadeeq
xaune cikin mota yana jiransa, Muhsin ya bude motar ya shiga yana kallonsa yace
"Kai dai ka rage munafurci Sadeeq duk rashin jin ka don ka xo gaban surkai sai kayi
ta wani sinne kai" Murmushi kawai Sadeeq yyi ya saka glasses dinsa ya tada motar
yace "I will have ur time later" daga haka ya fara reverse suka bar layin. Kamar
yanda Muhsin ya fada hakan ne ya faru don daddy na shigowa bayan Magrib ya yi ma
Ammi bayanin duk abinda ke faruwa,
Ammi tayi shiru duk jikinta yyi sanyi, A hankali tace "Toh yanxu ya ake ciki
yallabai?" Ya sauke ajiyar xuciya yace "Ina imaan din, taje can barrister na kiran
ta" Ammi tace "Ni dai Yallabai da dai a dakatar da yaron gaba daya, imaan har nawa
take don Allah" Daddy yace "So kike ki ja mana matsala gun inna kenan, did you know
maganar da ya dawo dani weekend kenan, ke kin ga abubuwan da inna ta dinga fadi a
parlor kuwa jiya?" Ammi dai bata ce komai ba, Daddy ya girgixa kai yace "Fatanmu mu
rabu da ita lafiya, gaba daya ta rikice ne yanxu" murmushi kawai Ammi tayi, Daddy
yace "I don't even know me yasa xa ki ba Imaan fuskar kula saurayi at the first
place, ko me xaki ce min baxan ta6a yarda baki san da xancen yaron ba, kuma ki wani
ce min nawa Imaan take?" Ammi tace "A'a ko da baxa ka yrda ba I have to tell you I
know nothing much about the boy, of recent naga tana waya shi ma sai da na mata
fada, kai sai kace baka san yar taka bace da nuku nuku" Daddy yace "Wannan ba hujja
bace, kina tare da ita 24/7 a gida...." Ammi ta dakatar da shi tace "Toh duk ba
wannan ba ita innar da ta kirkiro abun sai a fada mata ta gaya ma yaron
lalurorinta... If he wish to be with her like that shikenan, idan kuma baxai iya ba
gwara tun wuri a san haka, I don't want my daughter's heart to be broken or
anything of such..." Daddy ya dinga mata wani kallo ta mike ta wuce kitchen, yace
"Wato you are even in support of the silly thing the girl did, dama nasan kinsan
komai ai, tunda aure take so fine I will give her the best wedding ever" Imaan ta
marairaice tana kallon Ammi tace "Toh me yasa yake kirana Ammi?" Ammi tayi banxa da
ita, a hankali ta mike ta nufi kofa, Ammi tace "Kuma kiyi maxa ki dawo idan ya
sallameki ki xo ki kai ma Inna abinci" to kawai tace ta fita parlon. A hankali
Imaan ta bude kofar parlorn hade da sallama ta shiga ciki, Umma ce xaune parlor sai
Ummi da Rahma, ta dauke xata wuce parlon Abba Umma ta dakatar da ita ta hanyar daka
mata tsawa, Imaan ta tsaya amma bata juyo ba, Umma ta mike tana mata kallon tsana
karara tace "Uwarki tayi ajiya parlon ne ta aiko ki kixo ki dauka?" Imaan taki cewa
komai sai ma dauke kanta da tayi, Xagi Umma ta kunduma mata tace "Kin matsa bakin
kofar nan ko sai na faffalleki da mari"

27.....

Imaan dai bata tanka ta ba ta nufi stairs, Umma tace "Ragowar ciwo kawai" Sai da
Imaan ta isa stairs ta turo baki ta wuce sama, sai kuma ta fashe da kuka, dai dai
corridor suka hadu da Mujaheed ya fito dakinsa, ya bi ta da ido har ta shiga dakin
Aunty, Karasawa stairs yyi yana lekan downstairs ganin Umma xaune ya dawo da sauri
ya bude kofar dakin Aunty ya shiga ya kulle, Aunty na tsaye kanta sai tambayarta me
ya faru take hankali tashe, Imaan da ta xube mata nan tsakar dakin ta dinga kuka ta
ki cewa komai, Aunty tace "Kinga iskancin nan naki ne bana so, baxa ki bude baki ki
min magana ba, me kika yi ma Ammin?" Still ta ki cewa komai, Mujaheed ya karasa
kusa da su yana kallonta yace "Baxa ki bude baki ba ana maki magana?" Ta hade kai
da gwiwa cikin rawar murya tace "Ko ba Umma bace take xagina ni ban mata komai ba
har da ce min ragowar ciwo" Aunty ta ja tsaki tace "Shine xaki xo ki tada min
hankali a nan? Sai me don ta ce maki ragowar ciwo? Xa kuwa ta ga ragowar ciwo a
xuri'arta wataran, domin ita ta gama haihuwa ai yanxu su kuma 'ya yanta xa su
fara...." Juyawa Mujaheed yyi ya nufi kofa, Aunty ta bi sa da harara har ya fita,
Aunty tace "Banda shashanci shine xaki xo kina ma mutane kuka, yau ta saba gaya
maki haka?" Ita dai Imaan bata ce komai ba sai share idonta take, Anty tace "Aiko
ki Ammi tayi ko me?" Ta dago ta kalleta a hankali tace "Abba ne ke kirana" Aunty
tace "Tashi mu je, yana parlon sa ai" mikewa imaan tayi ta bi bayan Aunty suka
fita, Umma ta dinga bin su da wani kallo, Aunty ta nufi parlon Abba tana cewa "Ae
ba mahalukin da ya isa raba ki da ubanki, sai dai a ganki a kyale bbu ynda aka iya
da ke" Aunty ta bude mata kofar tace "Shiga" Imaan ta shiga parlon Aunty ta rufe
kofar ta koma sama, Abba na xaune yana kallon news Mujaheed ma na parlon, sallama
Imaan tayi ta xauna kasa ta gaida Abba dake kallonta, yace "Lafiya lau Mamana sai
yanxu kika xo?" Kai kawai ta gyada masa, Abba yace "Toh yayi" bai kuma cewa komai
ba, Imaan ta saci kallon Mujaheed taga kallonta yake, suna hada ido ya hade rai,
turo baki tayi tana fidgeting fingers dinta, Bayan few minutes Abba yace "Imaan ai
kin san wannan yaron Sadeeq koh?" Shiru tayi bata ce komai ba ta kuma kasa kallon
Abba, Abba yace "Ina saurarenki" ta gyada masa kai tace "Uhm" Abba yace "Kar fa ki
boye min komai I am ur father, ki gaya min meye tsakaninku" dauke kai tayi ta ki
cewa komai, Abba yyi murmushi yace "Baxa ki gaya min ba kenan" Nan ma dai ta ki
cewa komai, Abba yace "Toh tunda ni kunyata kike ji sai ki gaya ma Mujaheed meye
tsakanin ku" Xaro ido tayi tana kallon Abba, Abba ya mike yace "Xan dawo yanxu, let
me make a call outside, sai ki gaya masa kafin in dawo shi kuma ya gaya min" daga
haka Abba ya fita ya kulle kofar, tun da Abba ya fito Umma ke binsa da kallo har ya
fita main parlor, ta kalli kofar parlon sa.... Imaan dai ta kasa xaune waje daya
bayan fitar Abba, jin shiru ta d'an saci kallon Mujaheed, ganin irin kallon da yake
mata xata mike yace "Koma ki xauna" ta marairaice tana dubansa tace "Ni fa ruwa xan
je in sha in dawo" ya dawo kusa da ita ya xauna yana kallonta da kyau cikin husky
voice dinsa yace "Me nace ki ce ma Abba?" Ta 6ata fuska kamar xata yi kuka a
hankali tace "Yaya ba ka riga ka gaya min jiya ba, ai xan gaya masa...." Sai kuma
tayi shiru, ya hade girar sama da ta kasa yace "I will slap you idan baki gaya min
abinda xaki gaya masa ba" Tace "To ba cewa kayi ince ban san sa ba...." ya dinga
kallonta fuskarsa daure, a hankali ta mike da nufin fita parlon ya fixgota ta fado
jikinsa, xaro ido tayi tace "Yayaa" bude kofar parlorn aka yi yyi saurin janyeta
jikinsa, Kallonsu Aunty ta dinga yi daga inda take tsaye bakin kofa, Mujaheed duk
ya daburce ya mike tsaye, Imaan ta zamo kasan kujeran kamar xata yi kuka, Aunty
tace "Meye hakan" Mujaheed yace "Aunty kawai daga mata magana shine xata fado
kaina" Aunty ta tabe baki har sannan tana kallonsu, juyawa tayi xata fita sai ga
Abba, ta basa hanya ya shigo parlon, Anty ta fita waje, Abba na kallon Mujaheed
bayan ya xauna yace "what did she say about him?" Mujaheed ya xauna saman kujera
yana shafa kansa a hankali yace "Tace ba komai tsakaninsu, bata ma wani sansa ba
kawai shine ke kiranta a waya..." Imaan ta kallesa da sauri, Abba yace "Haka ne
Imaan?" Kamar xata yi kuka tace "Abba ni dai bance masa haka ba, frnd dina ne fa,
kuma yana koya min karatu ta waya wani lkcn, ina ganewa kuma" Mujaheed ya kasa
kallon Abbansa, Abba ya kafe sa da ido, can ya d'an yi murmushi mara sauti yace
"Toh shikenan mamana, tashi ki tafi" mikewa tayi ta nufi kofa, xata fita ta d'an
saci kallon Mujaheed da ya ki dago kansa ta fita. Bata damu da irin kallon da Umma
ke mata ba har ta fita parlon ta wuce part din su. Abincin inna ta dauka ta tafi
kai mata, sallah ta sameta tana yi a parlor ta ajiye abincin xata fita, inna ta
dinga gyaran murya alamar ta tsaya, imaan tayi kamar bata ji ba tayi wucewarta da
sauri, a hanya ta tadda Yusuf rike da ledan fruits xae kai ma inna, ta gaishesa
tana kallonsa, sama sama ya amsa mata ya wuce, ta tsaya ta bu sa da kallo har yyi
nisa, turo baki tayi ta bar wajen, har ta gama shirin kwanciya kiran Sadeeq ya
shigo wayar ta, ta kashe fitilan dakin ta hau saman gado ta rufe har kanta da duvet
sannan ta daga kiran, murya can kasa ta amsa sallamansa yace "Kin fara bacci ne?"
Ta girgixa masa kai tace "A'a" murmushi yyi yace "Toh ya kike?" Tace "Alhmdllh, ya
aiki?" Yace "Lafiya lau..." A hankali tace "Shine daxu baka ce min xa ku xo da ya
Muhsin ba koh?" yyi murmushi yace "Shi yace kar in gaya maki" tace "Toh yanxu da
kun sameni ban sa Hijab ba fa?" Ya wara ido yace "Yea sai in ganki da kyau, ai ba
laifi bane don naga abinda nake so ba hijab" ta xaro ido tace "Uhnnn?" Yace "Yess"
murmushi tayi bata ce komai ba, Yace "Ya Ammi fa?" Tace "Tana lafiya" yace "Maa sha
Allah, kinje gun kaka yau?" Tace "Ehh na je kai mata abinci" yace "Ina son in samu
time in xo mu yi hira sosai da ke da kaka" ta xaro ido tace "Ai ita bata hira, bata
fiye son magana ba ma" Dariya Sadeeq yyi yace "Really?" Kamar xata yi kuka tace
"Ehh" yace "Uhm to shikenan, yaushe xan xo mu yi hiran mu biyu kadai, I want to
tell you lot of things Imaan" Murmushi tayi tace "Ae Daddyna na gari bai koma ba
tukun" Yace "Toh baxa ki gidan gwaggo ba mu hadu can?" Ta d'an yi shiru, murya can
kasa yace "Are you there Imaan?" A hankali tace "Toh gobe xan ce ma Ammina xan je
can dama ai saura kwana uku bikin Anty Halima kilan idan na je sai bayan bikin xan
dawo gida" yace "Toh shikenan idan kin shirya goben sai ki kirani" ta xaro ido tace
"But ai sai Ammi ta amince in je, kasan ba a son ina fita ni kadai" yace "Toh Allah
yasa ta amince" Tace "Ameen" da sauri Imaan ta cire duvet din kanta jin kamar ana
bude window, ganin farin abu tayi ya fadi kasan dakin, ta sauka gadon ta nufi
windon da sauri ta bude labule har sannan waya na kare kunnenta, Mujaheed ne tsaye
kusa da window din, ta xaro ido tana kallonsa, yana mata wani kallo ya juya ya bar
wajen, ta rufe window din ta durkusa ta dau takardan tana kallo, muryar Sadeeq taji
a kunnenta yace "Are you there?" Tace "Yea ina ji" yace "Ko kin fara jin bacci ne"
murmushi tayi tace "Um" don so kawai take ta bude takardar ta ga content dinsa,
yace "Toh shikenan, sleep like a baby dear" murmushi tayi tace "Toh nagode, good
night" daga haka ta katse wayar ta ajiye ta kunna fitilar wayar ta warware takardan
tana haska rubutun kai, xumburo baki tayi ta cukwuikuye takardan ta jefar ta kwanta
kamar xata yi kuka tace "Ni dai ba ruwanka da ni"

Mikewa tsaye Aunty tayi tana kallon Yusuf dake xaune gefen gadonta, shi kam bai
yarda ya kalleta ba, Tace "What are you saying Yusuf?" Still ya ki cewa komai,
aunty ta dinga kallonsa ko kiftawa babu, can ta ja stool ta xauna tace "Ka daga kai
ka min magana malam" Sai a sannan ya daga kai ya kalleta, tace "Are you serious
with what you are saying, or should i say are you on ur right senses?" Cikin sanyin
murya yace "Sure Mum" Tagumi Aunty tayi tana kallonsa with much surprise, can ta
girgixa kai cike da damuwa tace "Kai ma kasan wannan ba abu bane da xai yiwu, ba
abu ne mai sauki, haba Yusuf me yasa ka yarda xuciyarka ta yaudare ka da son abinda
kasan da wuya ka samu, ko da kuwa kana tunanin xaka samu mai yasa baka tsaya kayi
naxarin irin matsalolin dake tattare da samun ba? Wait tukun toh ita Hafsat din
fa?" Ya girgixa kai cikin low voice yace "Ku ke tunanin ina son Hafsat, she is just
a frnd, bani da intention na auranta...." Aunty ta xaro ido tana kallonsa, can tace
"Ikon Allah, i really don't know what to say to you now Yusuf, ban san me xance ba
gaskiya, amma ni da xaka bi shawarata ka bar wannan xancen it's something that
isn't and will neva be possible, forget this pls son" Yana kallonta da mamaki yace
"Why Mum?" Tace "Look Yusuf, Imaan is my daughter, her mother is my very close frnd
as well, infact childhood frnd dita ce Aisha, don ta dalilinta na hadu da mahaifin
ku har muka yi aure, but... ni xan fi son mu ci gaba da xumunci da Hajiya Aisha as
just the frnds we are, and marrying into same family, I mean relationship din
mijinta da mijina, amma bana son xumuncin mu ya koma na in-laws, its somehow, that
aside Yusuf, kusancin inna da Imaan.... don't misunderstanding me plss son, kai ma
inna kakar ka ce, amma gaskiya akwai matsala daga bangaren inna ka bar ni ma in ji
da headache daya...." Yusuf ya girgixa kai yace "Kiyi hakuri Mum, I don't think all
this u are saying is enough da xai sa ki hanani auren Imaan" Aunty ta bude baki
tace "Ni nace xan hana ka aure Imaan Yusuf, idan Allah yyi Ita din matar ka ce ni
na isa in hana? Don't quote me wrong plss, amma kai kasan kana son ta me yasa ko
sau daya baka taba nuna alamar haka ba?" Yace "That's bcos she is still young, har
yanxu Imaan bata san meye rayuwa ba, bata san kanta ba har ynxu, I was thinking
idan ta fara jami'a ta d'an yi hankali sai in fito da intentions dina toward her"
Aunty tace "Toh Allah ya kyauta, I think it's best ka je ka samu abbanku, amma ni
nasan da kyar ne...." Yusuf yyi kasa da kai a hankali yace "Ni dai ki daina cewa
haka plss mum, support me sannan ki min addu'a" a sanyaye tace "Toh na daina cewa
haka, Allah yayi maku xabi mafi alkhairi Yusuf" yace "Nagode mum" daga haka ya mike
ya nufi kofa ta bi sa da kallo har ya fita, Tagumi tayi tana furta innalillahi....
A xuciyarta. Sake baki Abba yyi yana kallon Yusuf with surprise, shi dai Yusuf bai
yarda ya kallesa ba, bayan few seconds Abba yace "Yusuf" Sai a sannan Yusuf ya daga
kai da kyar yana kallon Abban nasa, Abba yace "Kana nufin Imaan kake so?" Yusuf ya
sunkuyar da kai a sanyaye yace "Ehh Abba" Abba yace "Ikon Allah" Shiru ne ya biyo
baya na kusan minti biyu, can Abba ya daga wayarsa yyi dialing number Mujaheed har
ya gama ring ba a daga ba, Abba ya ajiye wayar sanin yana gun aiki, Abba yace "I am
happy hearing this son, but at the same time I am disturbed coz I made a promise to
someone earlier, all the same don't worry, Allah xai shige mana gaba, tashi ka
tafi" Mikewa Yusuf yyi ya nufi kofa Abba ya bi sa da kallo yana murmushi. Ko minti
goma ba ayi da fitar Yusuf ba sai ga Umma ta shigo parlon Abba cikin shirin fita,
har sannan Abba was still pondering at what Yusuf told him, kuma har ransa yake jin
xai fi kowa murna da wannan hadin, Auren d'an sa da tillon 'yar d'an uwansa,
tunanin yanda xai fara billowa al'amarin yake, first ya fara kiran D'an uwan nasa
ya sanar masa sannan su tafi gun Mahaifiyar su ita ma su sanar da ita, yasan Daddy
xai yi farin ciki da hadin shi ma, don fargabarsa a ko da yaushe gidan da only
child din tasa xata fada da sunan aure, yasan Daddy na son imaan fiye da tunanin me
karatu, he can do anything bcos of his only child, Umma Ta karasa cikin parlon tace
"Alhaji kasan Mujaheed ya tura min kudi xan fara hada masa lefe, to yau xan fara
shiga kasuwa" Abba na kallonta da mamaki yace "What? Lefe kuma? But he told me
nothing about that" Umma ta d'an bude ido tace "Toh ba sae an gama hadawa ba xa a
kinkimo maka ka gani, kar ya fada maka kayi tunanin ko so yake ka basa wani abun,
wllh ban son ya daura maka ko wani nauyi ne kaga ba a dade da hidimar seeyama ba,
tunda Allah ya hore masa xai iya komai shi sa kawai nace kada ya gaya maka sai na
gama hada kayan a kawo maka ka gani, ba laifinsa bane shi ma ya so sanar da kai na
hanasa, amma idan hakan ya bata maka rai kayi hakuri don Allah" Abba yace "Toh
Allah ya rufa asiri..." Umma tace "Ameen, tun jiya naga kamar abu na damun ka,
shine nace to mai kuma ya faru, idan ma inna ce don Allah a dinga hakuri, uwa ce...
Sai ayi ta fatan a gama lafiya da ita, ya ci ace duk abubuwan inna ya xame maka
jiki yanxu..." Abba yace "Haka ne" Umma ta xauna ganin maganganunta sunyi tasiri
xuciyar Abba, murya can kasa tace "Toh me kuma take so Alhaji?" Abba yace "A'a
wannan mun shawo shi tare da Sadeeq, Yusuf ne dai ya xo min da wata magana yanxu da
ya kulle min kai... Am still trying to find a way out ne har yanxu" Da mamaki Umma
tace "In ji dai lafiya??" Abba yace "Lafiya lau, yar uwarsa Imaan yake so da aure
wai" Mikewa Umma tayi da mugun mamaki baki bude tana kallon Abba, can tace "Aure
kuma Alhaji??" Abba yace "Kwarai, yanxu ma ya bar parlon nan" Umma tace "Ikon
Allah.... Aure fa???" Juyawa tayi ta nufi kofa tace "Toh Allah yayi mana mai kyau
dai, ya xaba abinda ya fi alkhairi, ae imaan yar uwar sa ce, Imaan ta mu ce..."
daga haka ta fice, direct sama ta wuce ta bude dakin Yusuf ganin baya ciki ta shiga
dakin Aunty, xaune ta samesa tare da Aunty, Umma tace "Amma Yusuf kayi asara wllh,
ka kuma samu tabin kwakwalwa mai wuyar ganowa balle ayi maka magani, yanxu ka rasa
warce xaka je kace ma Ubanka kana so sai Imaan, Yusuf me ya same ka ni Rukayya??
ina ita Hafsar da kake nema take??" Yusuf dake kallonta yace "Umma ni Hafsat ba
aurenta nace xan yi ba" Salati Umma ta saki tace "Amma Allah ya isa tsakaninmu da
kai, mu xaka ka ma bakin ciki Yusuf?? ka bar 'yar attajiri ka dawo kace mai lalura
iri iri kake so? Anya akwai lafiya kuwa, mu xaka kwaso wa mugun iri, irin ciwo a
xuri'ar mu? Yarinya mutu kwakwai rai kwakwai?? Toh wllh tunda an asirce uwarka ta
kasa cewa komai ni kam ba a asirce ni ba sai inda karfina ya kare in sha Allahu,
yanda xan ma Mujaheed haka xan maka don duk daya ku ke a gu na, in sha Allahu sai
naje na gano tushen abun nan... Ba wanda ya isa ya ci nasara a kanka kamar yanda
aka ci a kan kanin Ubanka, uban kuturu yyi kadan wllh balle na makaho" daga haka ta
fice a dakin kamar xa ta tashi sama, Aunty da ta bude baki tana ta kallonta tace
"Ikon Allah ya fi gaban haka...."
Daddy couldn't help it but laugh bayan Abba ya xo har part dinsa ya sanar masa
intention din Yusuf a kan Imaan, Daddy yace "Ikon Allah, nayi farin ciki sosai sai
dai kar ka mance da alkawarin da kayi a baya barrister, ko ya xa mu yi?" Abba yace
"Sure ina sane, shi ma ba wai xa a dakatar da shi bane Sadeeq din, abinda xai faru
yanxu kawai mu fara xuwa gun Inna mu je ta bakin ta kafin a yanke ko wani decision"
Daddy yace "Gaskiya ne wannan" Part din inna suka tafi a tare, Inna ta fito daki
tace "Tun safe in gaya maku nake aiki ban xauna ba, ku leka bandakina ku ga ko tuwo
ya xube kasa xa a iya xaunawa a cinye tass, ba ku ji bayana ba kamar ya balle ni
dai in huta" Murmushi duk suka yi suka xauna, Daddy yace "Gwara dai ki dinga hutawa
haka inna, gashi kince baki son mai aiki balle a samo maki ko yar dattijuwa ce"
Inna tace "Ni ko ina xan so masu aiki mutane duk wari, sannan su cinye ma mutum
abinci, A'a ba ruwana ni ko da rarrafe ne xan yi aikina, 'ya yanku ne sun xama abun
tsoro banda haka Imaan ko Maimoon ko Ummi baxa su dinga xuwa min d'an share share
ba banda karshen duniya da lalacewa ta xo" Abba yace "Inna ke fa kika ce baki so,
ai da suna xuwa..." Inna tace "Ehh ni nace bana so, don ba abinda suka iya gaskiya,
basa min yanda nake so, ni dai nace na yafe su daina xuwa" Duk suka yi shiru basu
ce mata komai ba, ganin ta dauko tsintsiya Abba yace "Inna daxu Yusuf ya sameni kan
wata magana da naga ya dace mu sanar maki kafin mu yanke hukunci...." Ajiye
tsintsiyar tayi ta xauna kan kujera da sauri tace "Me ya faru kuma??" Abba ya d'an
yi murmushi yace "Wai yar uwarsa Imaan yake so da aure...." Inna ta gwalo ido ta
saki baki tana kallonsu, saukowa kasa ta yi a hankali ta xauna kan rug ta fashe da
matsanancin kuka tana tafe hannu tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, LA haula
wala kuwata illa billahil Aliyul Azeem, la ilaha ilallahu Muhammadurrasulillahi
sallallahu alaihi wassalam, hasbunallahu wa ni'imal wakeel.... Na ga abinda ya
isheni ni patuuu" Daga Abba har Daddy kallonta suka dinga yi da mamaki, inna ta
dakatar da kukan da take tace "Toh da kyar idan Imaan bata ta6a shan nonon Amina ba
ma, yo ta ma sha ne kawai... Idan xa kuyi ta kanku kuyi ta kanku"

*The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included


in the payment group.

28.....

Girgixa kai Daddy yayi yace "Hakan bai ta6a faruwa ba Inna, ko kin manta ba gida
daya muke lokacin ba" Inna ta mike a fusace tace "Yau naga jaraba ni Asabe, ka fi
ni sanin abinda nake ne Bukar, so nawa idan matarka xata fita gantalinta na
makaranta take kai ma Amina Imaan, kuma babu wanda bai san irin kukan banxa da
shagwaban da Imaan tayi tana jaririya, bata kuma yarda ta sha komai sai nono, shi
sa ma bana son a kawo min ita ba ruwana, kuma kace min 6ata ta6a shan maman Amina
ba?? karya xan xauna in giggilla maku da tsufa na?" Sai kuma ta fara kuka ta xauna
tayi tagumi tace "Shkkn karshen duniya ta kama....." Abba ya sauke ajiyar xuciya
yace "Toh bari a kira Aminar a tambayeta" Kuka kawai inna take bata tanka su ba,
Abba ya dau waya ya kira Aunty, bayan ta daga yace "Ki taho part din inna yanxu,
it's urgent" tana tambayarsa abinda ya faru bai bata amsa ba ya katse wayar, Aunty
tayi jigum dama ita irin abinda take gudu kenan, haka dai ta sa Hijab ta fita xuwa
part din inna, Daga Abba har Daddy sai kallon inna dake sharban kuka suke, da daddy
yayi kokarin bata hakuri a fusace tace "Rufe min baki, naki hakura, ko dole ne?"
Haka yasa duk suka ja bakinsu suka yi shiru, da sallama Aunty ta shiga parlon inna,
Abba da Daddy kadai suka amsa mata, banda Inna dake hararanta ta gefen ido, Aunty
ta durkusa tace "Ina kwana Inna?" Inna tace "Sai yanxu garinki ya waya da xaki ce
min ina kwana? Ina ce ana idar da sllhn asuba nan ya kamata ku yo ku gaisheni amma
ke da Aisha sai rana tayi gauuu sannan ku yo min nan wai kun xo gaisheni, ni dai ba
ruwana a dinga jin tsoron Allah" Aunty dai ba ta ce mata komai ba sai gaida Daddy
da tayi ya amsa, Abba yace "Amina wai kin ta6a ba Imaan mama?" Da mamaki Aunty ke
kallonsa tace "Imaan kuma?" Abba yace "Ehh" Aunty tace "Ta ya hakan xai faruwa
kuwa? A'a ni ban taba ba..." mikewa inna tayi, tayi mitsi mitsi da ido tace "Toh
bari ku ji... da ki bata mama da kar ki bata duk uwarsu daya ubansu daya a
wajena... in dai da rai na a duniya to wllh Isuhu baxai auri Imaan ba, harammm, ga
dai d'an Bulasawa da ya riga sa sbda ku ba yan gaskiya bane shine ku ke son yi masa
fin karfi, to ni 'yar gaskiya ce, kuma ba a cin amana da ni, na kuma yi ma yaron
alkawari Imaan ta sa ce, don haka duk ku yi ta kanku munafukai kawai, shi isuhun
tun da can bai san yana sonta ba sai da ya ga bulaswa sbda bakin ciki da hassada
kar jikata ta huta, to aniyarsa ta bi sa, to wai ma ina figaggiyar budurwarsa da
har xai ce sai jikata sbda rashin tsoron Allah, to ni ba ruwana ya cire idonsa kan
jikata na riga na mata miji" sai kuma ta fashe da kuka ta rike kai tace
"Innalillahi Wa inna ilaihi raji'un, wayyooo ubangijina, su dai yan gidan nan basa
tsoron Allah na rasa me yasa haka, basa tsoron axaban Allah, xaman gidan nan ya
haramta gun mai tsoron Allah iri na, ni dai idan xuciya ta kwasheni ma sai in tafi
Habuja gun shegen Balan can inyi xamana, don wani lkcn ma gwara 6are da naka"
Mikewa Daddy yyi ya nufi kofa ya fita parlon, Aunty ta tashi ta bi bayansa, A
hankali Abba yace "Toh kiyi hakuri an bar maganar in sha Allah inna" Ta kunce habar
xaninta tana share idonta tace "Ni dai ba ruwana, tunda haka isuhu ya xama dama kar
ya sake tako min nan, gwara min Mujaheed sau sittin a kansa, shi Mujaheed baya
haka, xuciyar sa mai kyau ce, kuma ni duk wanda ya sake tada maganar nan gaskiya
xan ja masa Allah ya isa" Mikewa Abba yayi yace "Sai anjima" ko tanka sa bata yi ba
har ya fita ya kulle mata kofar. Abba ne xaune parlonsa da Daddy sai Aunty, Yusuf
ma na xaune kansa a kasa, a hankali Abba yace "Kayi hakuri Yusuf, Allah ya sa hakan
shi ya fi maka alkhairi" Yusuf ya daga kai ya kallesa yace "Ameen" Daddy kam kasa
cewa komai yayi, Aunty ta mike ta fita parlon.
Misalin karfe goma da rabi na safiyar ranan Imaan ta fito parlor bayan tayi wanka
ta shirya cikin atamfa an mata dinkin riga da skirt da ya amsheta sosai, gaida
Daddy dake parlon a xaune tayi, he was still tensed at what happen safiyar ranan,
bai taba tunanin Inna xata yi masu haka ba, gaba daya bai ji dadi ba, don ko da ace
yau Yusuf bashi da hali bai ci tayi haka ba sbda shima jikanta ne, balle Yusuf is
perfect in every aspect, ko Ammi daddy ya kasa gaya ma, ya kalli Imaan ya amsa
gaisuwar da tayi masa, ta mike ta wuce kitchen gun Ammi, Ammi tace "Ki dau nose
mask ki sa ki tafi ki share balcony din nan ki goge it's too dusty ni kuma xan tafi
unguwar rimi yanxu ina sauke girkin nan" Ta marairaice tace "Ammi toh ai nima can
xanje fa yau, gashi har na shirya" Ammi tace "Me xaki je kiyi biki saura kwana
uku???" Kamar xata yi kuka tace "Don Allah Ammi ki bar ni in je, Anty Halima fa
kawata ce kawai don dai ta girmeni ne, plss Ammi let me go" Ammi tace "A'a ba
ruwana sai daddy ya bar ki, yanxu ki tafi ki share min inda na sa ki" A Hankali ta
juya ta fita kitchen din ta tafi daki ta dauko thick nose mask dinta ta dau sweeper
xata fita daddy yace "Ina za ki?" Tace "Xan share waje ne" Daddy yace "Xa ki share
waje kuma? Ina mamar taki?" Ammi dake jin su a kitchen ta leko tace "Gani!!" Daddy
yace "Ta share k'ura fa kika ce madam" Ammi tace "Ga dai nose mask nace ta sa ae,
toh wai yallabai idan tayi aure ni zan bi ta ina share mata gidan ko kuwa haka za
ta bar gidanta ba tsafta sbda tana da asthma??" Daddy dai bai ce komai ba, Imaan ta
juya ta fita, daddy ya juya yana kallon Ammi yace "Ba lallai tayi aikin gida ba
idan tayi aure, I will get her a housemaid that's capable" murmushi Ammi tayi tace
"Lallai kam, to idan mijin yace bai son Housemaid fa?" Mikewa daddy yyi yace "Sae a
fasa auren, I know what I am saying...." daga haka ya wuce dakinsa, Ammi ta tabe
baki ta juya ta koma kitchen, Imaan na share tiles din dake shimfide a babban
balcony din nasu lkci lkci xata mike ta d'an huta idan ta ji breathing din nata na
sarkewa, kamar ance ta juya taga Mujaheed kai kana ganinsa kasan daga asibiti yake,
mikewa tayi tsaye ta jingina da pillar tana sauke numfashi a hankali, Mujaheed ya
tsaya yana kallonta coz she looks so tired, fuska daure yace "Wa ya sa ki shara?"
Ba tare da ta kallesa ba tace "Ammi" d'an jim yyi sai kuma yyi wucewarsa part din
inna, Xaune ya tadda inna a parlor fuska a tsuke, ya tsaya bakin kofa yace "Me ya
faru kike kirana??" Tace "Baxan kiraka ba Mujaheed, naga xama bai gan ni ba na
tashi naje na sami mai gadi ya nemo min lambarka ya kira min kai, ni dama kai ne
nawa, da kai muke kashe komai mu rufe, tunda ga irin 'ya yan da Allah ya jarabce ni
da samu, ni ba din ba din ba ma sai ince banyi dacen 'ya ya ba, samm Bukar da
Ahmadu ba yaran nunawa bane" Kallonta kawai Mujaheed yake, can ya karasa cikin
parlon ya xauna yace "me ya faru?" Ta fara matsar kwalla tace "Wai kaji fa Isuhu ya
fito masu da cewar yana son Imaan da aure" a hankali Mujaheed ya mike yana kallonta
da manyan idanuwansa, Inna tace "Maimakon su tsigale sa su masa tatass, tunda ga
yaro d'an kirki na nemanta da aure, in gaya maka sai yaran nan suka biye sa, suka
kwaso jiki suka yo min nan suna washe min hakora a can" ta fadi haka tana nuna masa
kujeran da su Abba da daddy suka xauna, A hankali Mujaheed yace "Sai kika ce masu
me?" A fusace tace "Me kuwa xan ce masu Mujaheed?? Balbalesu nayi nace ko bayan
raina bulaswa xa a ba ma imaan, don ni yar gaskiya ce ba a cin amana da ni, kai
kaji bakin ciki irin na d'an uwanka fa?? Shi mai daukan albashin da bai wani taka
kara ya karya ba xai ce xai auri jikata taje ta mutu in shiga uku in lalace? Dududu
albashin nasa ya wuce dubu dari biyu da wani abu?? A'a ba ruwana, ni dai nan na
binne maganar nace bana son a sake tada ta ko inyi Allah ya isa, Imaan ta Bulasawa
ce idan Allah ya yrda, shine abun ya min ciwo na fita na kiraka ina kuka a waya, ko
kai ya ka gani?" Mujaheed ya sauke wani boyayyen ajiyar xuciya ya xauna yace "Haka
ne, tunda ya riga sa" Inna tace "Atohhh... kai dama duk ka fita daban a jikokina,
kai d'an gaskiya ne kamar ni, nasan kuma kai baxa ka ta6a irin wannan kazamin
tunanin ba wai xaka auri Imaan, kai kaji wani sa6o don Allah a ja mana fushin
ubangiji, toh Isuhu dai ya xama abun tsoro, har abada kar ya sake yo min nan don
xan tsallake in gudu gidan bala" Mujaheed dai bai ce komai ba don har sannan
gabansa bai daina faduwa ba ya rasa dalili, Inna tace "Ahmadu da Bukar dai sun xama
shashashai yan cin amana, Allah ya shirye su, kuma su gaggauta tuba ga Allah ni ba
ruwana" Mujaheed ya jinginar da kai da kujera ya lumshe ido a hankali, inna tace
"Baka rufe ido ba wannan abun takaicin Mujaheed, Wllh yanda kake ji haka naji nima
daxu, naji kamar ince wayyoooo Allah, kawai na fashe da kuka bayan fitar su, haka
kawai suje su ja mana girgixan kasa a gidan" Mikewa inna tayi tace "Har naji sanyi
da na gaya maka wllh, ni dai bari in kada shayina in sha, ba ruwana da wahala" Daga
haka ta shige kitchen, Mujaheed ya dafe kansa, lkci daya ya dago yyi murmushi, da
cup biyu ta fito tace "Ko kai ma in kada ma ka shayin ne?" Mujaheed ya kalleta yace
"Toh"
Imaan ta gama goge balcony din ta tafi cikin parlor tana cire mask din bakinta,
Breakfast Ammi ta mika mata a tray ta ajiye ma Daddy a dinning table, karasawa tayi
ta amshi tray din tana ajiyewa dinning sai ga Daddy ya fito, imaan na kallonsa ta
marairaice a hankali tace "Daddy xan je gidan gwaggwo yanxu, sai in dawo bayan
bikin Aunty Halima" Daddy ya ja kujera ya xauna yace "A'a sai dai ku dinga xuwa
kuna dawowa da mamarki" Ammi tace "Sae kace handbag, kawai ka barta ta tsaya can
har bayan bikin mana" yace "kin dai fi ni sanin condition dinta, so I don't need to
talk much" Ammi tace "Imaan fa ba yarinya bace yallabai, she can take very good
care of her self" daddy bai kuma ce mata komai ba. Duk yanda Ammi ta so Imaan ta
jirata su fita tare kin yarda tayi don tuni ta kira Sadeeq bayan daddy ya amince ta
tafi gidan gwaggo ta sanar masa, sai gashi ko 15 mins ba ayi ba ya kirata wai yana
saman layin nasu yana jiranta, Ammi ta dinga kallonta da mamaki ganin ko gama rufe
karamin trolley din bata yi ba amma xata ja haka ta fita, cikin tsawa Ammi tace
"Wai saurin uban me kike haka Imaan??" Waigowa tayi da sauri tace "Ba komai fa
Ammi" Ammi tace "Rashin natsuwa ce kenan, ke kam yaushe xaki yi hankali ne irin na
sauran jama'ah, dubi fa yanda kike jan jaka a bude saboda hankali ya maki kadan"
Daddy dake xaune dinning yace "Komai dai ace sai anyi fada, this isn't fair" Ko
tanka sa Ammi bata yi ba, Imaan ta durkusa a hankali ta karasa rufe jakar, Ammi
tace "toh xaki iya daukar jakar har bakin titi?" Imaan tace "Ai ba nauyi Ammi, kuma
ja xan yi tunda titin layin na da kyau" Ammi tace "Toh Allah ya kiyaye" daga ma
Daddy dake kallonta hannu tayi ta fita, ta rufe kofa kenan sai ga Mujaheed ya taho
daga part din inna, kallonta ya dinga yi tayi saurin dauke kai gabanta na faduwa,
kallon Sashin su yyi sannan ya kalleta yace "Ina xa ki?" Backing dinsa tayi, tayi
kamar tana gyara jakar ne ta turo baki tace "Gidan gwaggwo" Jin bai ce komai ba ta
leka sa daga durkushen da take, kallonta taga yake yi har sannan ta kara turo baki,
jin tafiyarsa ta saci kallon gefenta taga gate ya nufa, sai da ta jira taga fitarsa
gaba daya, bayan few minutes ta ja jakarta ta xuwa gate, tsaye ta gansa jikin
motarsa ya rungume hannu, gabanta yayi mugun faduwa, ji tayi kamar ta rushe da
kuka, tayi saurin dauke kai xata nufi saman layin yace "Xo ki sa jakar a mota" Da
sauri ta kallesa sai kuma ta fashe da kuka ba hawaye tace "Yaya Ammi da Daddy fa
cewa suka yi in tafi da kai na kar wanda ya kai ni wllh" Wani mugun kallo ya mata
yace "Before the count of 3 do what I said now" jingina tayi da gate hankali tashe
tace "Don Allah yaya ka wuce wllh bana son ka kai ni xan je da kai na" hade rai yyi
sosai ya daga finger dinsa daya yyi indicating da one, sannan two, bata jira ya
nuna third finger din ba ta ja jakar hawayen gaske na xubo mata ta bude back seat
ta ajiye ta rufe, cikin rawar murya tace "Xan dauko hand bag dina" bai tanka ta ba
ya xaga ya shiga driver seat ta koma cikin gidan ta fashe da matsanancin kuka,
parking space ta tafi ta tsaya ta yi dialing number Sadeeq, yana fara ring ya katse
ya kira ta, ta kai kunne cikin sanyin murya tace "Don Allah kayi hakuri Yaya xai
fita aiki yanxu shine yace xai yi dropping dina, ni kuma baxan iya cewa A'a ba kar
ya min fada" Sadeeq yace "Ohk no problem imaan, anjima da yamma xanje can gidan in
sha Allah" a hankali tace "Kayi hakuri don Allah" yace "Noo ba komai dear, ai yaya
ne, kar mu yi laifi ko" tace "Toh nagode" daga haka yyi mata sallama ya katse wayar
ta nufi gate fuska daure ta fita, bude motar tayi ta shiga tana cika tana batsewa,
ta gefen ido ya kalleta ya tada motar ya bar layin. Sun yi nisa sosai kamar mai
counting words dinsa yace "I told u what to tell Abba... but you told him a
different thing saboda kin raina ni koh?" A d'an tsawace ya kare maganan, Kin cewa
komai tayi sai ma kauda kai da ta yi tana kallon waje, parking yyi ganin haka ta
juya da sauri tana kallonsa kamar xata yi kuka tace "Don Allah kayi hakuri yaya, ai
ya ma daina kirana, tun shekaranjiya ni bai kira ni ba ma" Fuska daure Mujaheed
yace "In ga wayar ki?" Xaro ido tayi tace "Yaya ai yana gida" tana magana tana
kokarin boye wayar a jikinta, fixgota yyi, ta yi wani kara ta riko hannunsa tace
"Wayyoo yaya me nayi maka..." Ya dage Hijab din jikinta ta xaro ido tace "Yayaaa ka
bari" bai saurareta ba har sai da ya kwace wayar, dubawa yyi yaga ta sa password,
ya mika mata yace "Bude..." Make kafada tayi tana wani murmushi, ya dinga kallonta
kafin ya daura wayar kafarsa ya ci gaba da driving din, har suka iso gidan gwaggwo
bai sake ce mata komai ba, ita ma bata ce masa komai ba, yayi parking kofar gidan,
bude motar tayi ta fita, shi ma ya fito, ta bude back seat ta dau jakarta ta rufe
motar, danna lock yyi ya wuce cikin gidan ta bi sa da kallo kamar xata yi kuka, can
ta bi bayansa, Gwaggwo ce xaune parlor tare da wasu yan uwanta duk maxa, Mujaheed
ya xauna kasa ya gaisheta sannan su ma ya gaishe su, Gwaggwo da fara'a Gwaggwo ta
amsa tana cewa "Ikon Allah, yau Mujaheed ne gidan namu, dama kana garin Mujaheed"
ya d'an yi murmushi yace "ina nan Gwaggwo ya kwana da yawa" tace "Lafiya lau... Ka
guje ni Mujaheed" Har sannan yana murmushi yace "Kiyi hakuri gwaggwo yanayin aiki
ne, xan je anjima da yamma in dawo tun da kina da baki" Imaan ta xaro ido jin
abinda yace, Gwaggwo tace "Ka tabbatar Mujaheed" yace "Xan dawo da gaske" tace "Toh
madallah, sai ka dawo, Allah ya kiyaye hanya, ina nan ina jiran ka" Imaan dai na
makale jikin kofa ta ki shiga gidan, Mujaheed ya fito, kallo daya yyi mata ya dauke
kai ya nufi gate, ta bi sa da sauri tace "Don Allah yaya ka ban wayata" wani kallo
da ya tsoratata ya mata, ta koma baya a hankali, ya nufi gate ya fita gidan.
Tun da yamma yayi hankalin Imaan ya tashi, tasan yanxu kila Sadeeq ya kira ta wayar
Mujaheed kila kuma ya daga, sannan ga Ammi tana gidan, duk abun ya taru ya mata
yawa, ita kadai ce kwance dakin Gwaggwo don anty Halima na tare da kawayenta, ana
idar da la'asar sai ga Halima ta shigo dakin ta mika ma Imaan wayarta tace "Imaan
gashi abokin ya Muhsin xai maki magana" da sauri Imaan ta mike daga kan darduman da
take xaune bayan ta idar da sllh ta amshi wayar Anty Halima ta juya ta fita,
xaunawa tayi gefen gado tayi masa sallama a hankali, ya amsa yace "Is ur fone
down?" Xaro ido tayi da farko ta rasa abun cewa can tace "Um, ka kira a kashe koh?"
Yace "Sure" ta langwabar da kai tace "Ehh a kashe yake" yace "Ohk, ina waje fa" ta
wani xaro ido again, a hankali tace "Toh ina xuwa" yace "Ohk I am waiting dear"
mikewa tayi ta fita, rasa wanda xata gaya ma ana kiranta a waje tayi don tsoron
sanar da Ammi take, gwaggwo ta shiga nema, ta sameta a Wani empty room tare da Ammi
da maman Halima, ta gaida maman Halima da ta amsa mata da fara'a tace "Ya Abban ki
Imaan?" Imaan tace "Yana lafiya mama" daga haka ta nufi gun Gwaggwo ta durkusa
murya can kasa tace "Gwaggwo wai Sadeeq yana waje yana jirana" Ammi dai sai
kallonta take don bata san abinda take gaya ma mahaifiyar tata ba, Gwaggwo tace
"Sadeeq dai da na sani abokin Muhsin?" Imaan ta sunkuyar da kanta, Gwaggwo tace
"Ikon Allah, saurayin ki ne kenan" imaan ta boye fuskarta, gwaggwo tayi dariya tace
"A'a gaskiya naji dadi, Sadeeq ai yaro ne mai hankali da sanin darajan mutane,
tashi ki tafi ina gaishesa, ko kwana uku da suka wuce ya xo gaisheni da Muhsin,
gaskiya nayi farin ciki da wannan al'amarin" Ammi dai sai kallon Imaan take, mikewa
imaan tayi a hankali ba tare da ta yarda sun hada ido da Ammi ba ta fita, tana
fitowa parlor ta ji sallamar Mujaheed, still tayi inda take tsaye, Gwaggwo na jin
muryar sa tace "Ashe dai da gaske yake xai dawo" Mamaki ya sa Ammi ta kasa cewa
komai jin muryar sa ita ma, mikewa Gwaggwo tayi ta fito parlor murmushi dauke
fuskarta tana amsa sallaman tare da few mutanen dake parlon, shigowa yyi suna hada
ido Imaan ta juya masa baya da sauri kamar xata yi kuka, ya nufi kujera ya xauna
Gwaggwo na masa sannu da xuwa, ta kitchen imaan ta bi ta fice daga gidan. Sauke
glass Sadeeq yyi ganin ta, ta sunkuyar da kai har ta isa jikin motar, ya fito ya
jingina gefenta smiling cikin cool voice dinsa yace "Good evening" kasa kallonsa
tayi, a hankali tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau Imaan, ya Ammi fa?" Ta kalli
cikin gidan tace "Tana ciki" yace "Amma ba tare ku ka xo ba ai?" Ta girgixa kai
tace "Na riga ta" har sannan ta ki yarda su hada ido, a hankali yace "Kinyi kyau
sosai, I love the Hijabs you are wearing, you look so cute in them" boye fuskarta
tayi tana murmushi, ya dinga kallonta, kamar warce ta tuna abu ta xame hannunta da
sauri tace "Na manta na daura abu a kitchen kar ya kone" yace "Xa ki wuce ciki
knn?" Cikin sanyin murya tace "Kayi hakuri, ai mun gaisa" ya d'an yi murmushi yace
"Sure, amma ina son mu yi hira sosai, I told you I've got plenty things to let you
know imaan" tace "Toh may be later koh?" Yace "After Magrib or Isha?" Ta gyda masa
kai, yace "Ohk then, Allah ya kai mu lkcn, before then wait...." Yana fadin haka ya
bude motarsa ya fiddo wani abu kamar box mai kyau yace "You put this on for the
wedding" kin amsa tayi, gently yace "Take plss Imaan" ta kallesa a sanyaye, ya
gyada mata kai murya can kasa yace "Take it" risinawa tayi ta amsa tace "Nagode" ya
mata murmushin da ya bayyana dimples dinsa ta mayar masa da light murmushi sannan
tace "Sai anjima" daga haka ta nufi gate ya bi ta da ido har ta shiga gidan, sosai
gabanta ya fadi ganin Mujaheed ya fito parlon gwaggwo, ya dinga kallonta ta fara
tafiya a hankali, kamar warce aka ture ta durkushe nan kasa ta fara yarfe hannu
tana xaro ido, ya karaso inda take yace "Daga ina kike?" Hawaye har ya kawo idonta
tace "Ammi ta aikeni, yaya na gurde kafar fa" bai tanka ta ba ya nufi gate fuskarsa
daure, ta bi sa da kallo gabanta na faduwa ta dinga addu'ar Allah yasa Sadeeq ya
bar layin, kallon box din da ta boye a Hijab ta dinga yi kafin ta bude a hankali
taga babban dankunnen gwal mai kyau sai talli yake a kwance cikin fancy box din....

*The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included


in the payment group.

29....

Mikewa Imaan tayi da sauri ta nufi cikin gidan tana waigan ko Mujaheed ya dawo har
ta shiga ta kulle kofa, dakin gwaggwo ta wuce ta boye box din a cikin trolley
dinta, tsoronta daya yanxu Ammi, bata san me xata ce ba idan ta ga dankunnen, bayan
Magrib suna cin abinci tare da Anty Halima da wata kawarta, wayar Halima ya fara
ring, dauka tayi bayan taga mai kiran ta kalli Imaan tace "Wai ina wayar ki?" A
hankali Imaan tace "Yaya ya kwace min" Halima ta xaro ido tace "Saboda me?" Buda
hannu Imaan tayi alamar bata sani ba, Halima ta mika mata wayar tace "Toh gama
magana tukun" karba Imaan tayi ta kai kunne bayan ta daga hade da yin sallama,
Sadeeq ya amsa mata daga daya barin yace "Har yanxu baki yi charge din wayar ki
bane Imaan?" A hankali tace "Ehh" yace "But naga akwai wuta ai yanxu, ina ma
anguwar" ta langwabar da kai tace "Wayar na gida fa" yace "Ohk after Isha xan kira
ki, it's almost time now" tace "Allah ya kai mu" daga haka ya katse wayar, Imaan ta
ajiye gefen gado, Halima tace "Haka kawai Mujaheed din ya amshe maki waya?" Tace
"Ehh wai saboda abokin Muhsin na kirana" Bude baki Halima tayi tace "Toh shi ina
ruwansa" Imaan ta buda hannu tace "Nima ban sani ba" Rabi'ah kawar Halima tace
"Yayanki ne kuma?" Halima tace "Cousin dinta dai" Rabi'ah ta d'an bude ido tace
"Toh ko son ki yake?" Still Imaan tayi tana kallonta da wani expression, can tace
"Yaya ne fa... Yayana ne shi" Rabi'ah tayi dariya sosai tace "Wai yaya ne, to haka
kawai baxai dinga hana ki waya da samari yana kwace maki wayar idan babu wani abu a
kasa" Imaan ta ajiye cokalin hannunta a hankali tace "Abu kamar me?" Halima tace
"Tukunna dae me yace maki da yaga Sadeeq din na kiran ki?" Imaan ta jingina da gado
tace "Kawai ya hanani waya da shi ne, har blocking dinsa yyi ni kuma nayi
unblocking dinsa, a gida ma da Abba ya kira ni xai tambayeni meye tsakaninmu da
Sadeeq kafin in je ya sameni wai ince ban san sa ba" Dariya sosai Rabi'ah take,
Halima tayi murmushi tace "Tabb, lallai Mujaheed" Imaan dai sai kallonsu take don
bata san me ya basu dariya ba, Rabi'ah ta ajiye spoon din hannunta tana kallon
Imaan da kyau tace "Toh wllh son ki yake...." Imaan ta xaro ido ta koma baya da
sauri tace "Don Allah ki daina cewa haka plss, wllh yaya na ne fa, Anty Halima yaya
fa ne" Halima tayi wani murmushi tace "As far as ba ciki daya ku ka fito da shi ba
ki daina deceiving kanki Imaan Mujaheed son ki yake, so mai tsanani ma kuwa, ni
dama tun lkcn da yake kawo ki nan few years back ina ganin irin kallon da yake maki
nasan ba a banxa ba da abu a kasa, sannan kulawar da yake maki ko kanninsa basa
samun haka, abinda Mujaheed ke maki a da ya wuce shakuwa ko so na 'yan uwantaka, ke
dai ce ban san lkcn da xaki yi wayo har ki fahimci inda ya dosa, wai yaya ne... A'a
ba yaya ba..." lkci daya hankalin Imaan ya tashi ta fashe da kuka sosai tace "Wllh
ku daina cewa haka ba kyau, ni ba wani so na da yake yi, ina ce maku yayana ne fa,
to taya xai so ni, ni kanwarsa ce fa..." Dariya kawai Rabi'ah take don imaan tayi
mugun bata dariya nan kuma ta yarda har sannan Imaan na tare da yarinta ba kadan ba
sannan ga ta only child shi sa abun ya taru ya mata yawa, Imaan ta mike da sauri ta
fice daga dakin ta koma wani daki ta xauna kan gado maganganunsu na mata yawo a
kai, fashewa tayi da matsanancin kuka ta fada kan gadon tace "Ni baxan ma kwana a
gidan nan ba, ta ya xa a ce wai yaya na so na, wai yaya fa?? Allah ya kiyaye wllh"
Imaan bata ta6a jin abu ya tsaya mata a rai irin abinda Halima da kawarta suka gaya
mata ba, wai Mujaheed sonta yake, tabbb, ji tayi ita gaba daya duniyar ma babu
wanda take jin haushi kamar Mujaheed din, duk da tasan baxai ma taba yiwuwa ace
yana sonta ba, amma abinda suka gaya mata yasa ita taji bata ma son sa shi a ido,
bata son ganinsa kwata kwata, lamo tayi kan gado very restless, aka bude kofar
dakin ta juya da sauri, Halima ta shigo tace "Gashi Sadeeq ya kira" Imaan ta mike
xaune a hankali ta amshi wayar ta kai kunne tare da masa sallama, ya amsa yace "I
am outside Imaan" tace "Toh bari in fada ma gwaggo" daga haka ta katse wayar ta
tafi ta nemo gwaggo ta gaya mata, Gwaggwo tace "Toh ya shigo mana ai ba kowa parlon
ma, ce masa yayi shigowarsa kawai" Imaan bata ce komai ba ta sa Hijab dinta ta
fita, tsaye ta gansa ya jingina da motarsa, ta karasa kanta a kasa ta tsaya keeping
a enough distance tsakanin su, kallonta kawai yake, ita ko bata yarda ta kallesa
ba, a hankali yace "What's wrong imaan you look disturbed" da sauri ta daga kai ta
kirkiri murmushi tace "A'a ba komai fa, ya gida" yace "Lafiya lau" tace "Gwaggwo
tace ka shigo ciki ba kowa a parlor" Yace "No ni baxan shiga ba kunyarta nake ji
yanxu" murmushi Imaan tayi tace "Toh akwai kujeru a compound ai, shi ma baxa ka
shiga ba?" Ya shafa kansa smiling sweetly yace "Ohk then mu je" ita ta shiga gaba
ya bi bayanta har suka shiga cikin compound din. Sai da ta fara xama kan farin
plastic chair sannan ya xauna shi ma yana kallonta, dauke kai tayi ganin kallon da
yake mata yace "Amma ba dai kunyata kike ji ba" murmushi tayi tace "Shi nake ji
mana" Yayi dariya yace "Aa kiyi hakuri kar ki ji plss" Ita dai bata ce komai ba,
bayan few seconds yace "Did you know what imaan" ta daga kai ta d'an kallesa, cikin
sanyin murya yace "I am hoping to spend the rest of my life with you" Imaan ta
sauke idonta kasa, yace "I was born and bred in Uk, yawancin rayuwata duk can nayi
sa, daga baya na dawo Nigeria gaba daya, I've neva for once thought xan hadu da
mace yar Nigeria inji ina son rayuwa na har abada da ita sai kan ki Imaan, my ex
was white ita ma it's not as if I have much feelings for her, it's just to while
away time... Here in Nigeria frndship kadai ne tsakanina da yan mata, Ni ban san
meye so ba, I don't even believe in it until I met you few months back, pls don't
break my heart imaan, it's too fragile for something this big...." Imaan tayi
murmushi a sanyaye bata dai ce komai ba, yace "Yea... I have been counting down tun
yanxu xuwa ranan da xaku fara waec, but plss me yasa baxa kiyi waec din a ss2 ba"
xaro ido tayi ta kallesa, yace "Sure, a lot a ss2 suke waec" tace "Aa nafi son inyi
ss3" ya lumshe ido ya bude yace "almost a year to come in sha Allah kenan fa
Imaan?" Imaan ta kallesa tace "Sure" yace "Toh Allah ya kai mu lafiya" Tace "Ameen"
Yace "Promise me something plss...." Imaan tayi shiru tana kallonsa, yace "Ki min
alkawarin baxa ki yi betraying din soyayyata gare ki ba, and I am also promising u
same, I will and will neva leave u for any reason" lkci daya jikin Imaan yyi sanyi
tace "Ae an riga an san ka gidanmu, so there is nothing to worry about" yace "Sure
an san ni, but I am afraid of ur cousins" da mamaki tace "Cousins dina kuma?" Ya
d'an yi murmushi yace "Yea kada su min fin karfi...." Imaan ta kasa daina masa
kallon mamaki tace "Su ai yayyina ne ba so na suke ba" Sadeeq ya girgixa kai yace
"I saw their reactions ranan da Abbansu ya kira ni, more especially the very fair
one" Imaan gabanta ya shiga faduwa, Sadeeq yace "They might not tell you now amma
kada watarana su xo su ce suna sonki ki mance alkawarin mu, kada ki min haka plss
Imaan..." cike da damuwa ya fadi haka, imaan ta ji kamar ta fashe da kuka tace "Ni
ka daina cewa haka, ba wanda ke so na cikinsu duk yayyina ne su wllh, they are only
disturb sbda ban gama secondary schl ba" yace "Toh Allah ya sa haka, amma ba sai
kin min kuka ba gimbiyata, reminder ne" Imaan ta boye fuskarta da Hijab, yyi
murmushi yana kallonta, murya can kasa yace "Kin san inda xan kai ki for our
honeymoon?" Kamr yace ta kara boye fuskarta da Hijab cike da shagwaba tace "Ni dai
bana sooo" yyi dariyarsa mai dadin sauraro yace "Toh na bari baby, when the time
comes xa ki ga, amma fa tare da kaka xa mu" da sauri Imaan ta bude fuskarta ta xaro
ido tace "Aa ba inda xata bi mu" Sadeeq couldn't help it but laugh yace "Are you
serious??" Ita kanta sai daga baya taji kunyar abinda ta fada ta mike da sauri xata
wuce ciki yace "Noo plss wait dear, ki rakani first plss" da kyar ta yarda ta
rakasa gate tana sinne kai, ya juya yana kallonta kafin yace komai, a hankali tace
"Thanks much for the earrings na gode sosai" Ya mata wani kallo yace "Bana son ki
min godiya idan na baki abu, ba don ki gode min bane na baki" murmushi kawai tayi
bata ce komai ba, nan suka yi, sallama ta daga masa hannu ta koma cikin gida.
Washegari gidan gwaggwo ya xamo ba masaka tsinke saboda yan uwa da abokan arxiki
duk da gobe ne daurin auren, imaan dai na daki duk ta takura, ita dama haka Allah
yayi ta bata da sakewa cikin mutane, babu yanda Halima bata yi da ita kan ta bi su
gidan wata makociyarsu ba don can xata xauna har gobe sbda mutane amma taki, Har
daki Ammi ta kawo mata abincin rana ganin ta ki fitowa, ganin yanda take yatsine
yatsine Ammi tace "Ko dai xa ki wuce gida ne bana son matsala" girgixa kai tayi
tace "A'a kawai kaina ke min ciwo amma idan na ci abincin xan sha magani" Ammi ta
tabe baki ta fita dakin, imaan ta gama cin abinda xata ci a abincin ta dau maganin
ta sha, mikewa tayi rike da plate din ta fita don kai wa wajen wanke wanke, tun da
ta fito parlor taji numfashinta na tsarkewa ta dai dinga gyaran murya har ta fita
compound, hayaki ne cike gidan saboda wutan icce da aka hura, ta rike numfashinta
da sauri ta karasa ta ajiye plate din ta juya xata shiga parlor ta saki numfashin,
tari ta fara sosai ta durkushe nan bakin kofa mutane suka taho kanta, Nan Asthma
dinta ya tashi duk Gwaggwo ta rikice tana salati, Ammi ta wuce daki da sauri don
duba inhaler dinta a jaka, Aunty da sauran mutanen wajen suka shigar da ita parlor.
Har Imaan ta samu bacci dakin Gwaggwo bayan an rufe duk windows din an kunna mata
fan Halima ta shigo sanye da Nikab a kan Hijab dinta ta durkusa kusa da ita tace
"Sannu Imaan" bude ido tayi amma ta kasa cewa komai, ba kadan asthman yayi
attacking dinta ba wnn lkcn don har sun yi niyyar tafiya asibiti sannan ya lafa,
Kai kawai ta iya gyada mata, Halima ta dinga kallonta
cike da tausayi, Can tace "Sadeeq ma ya kira har sau biyu, bari in kirasa ince
baki da lafiya" Ita dai Imaan bata ce komai ba, Halima ta kirasa ya katse ya kira
ta, tace "Ka kira daxu ina sllh, na taho gida yanxu na tarar ma Imaan din bata da
lafiya" Yace "Subhanallah what's wrong with her?" Halima ta rasa me xata ce masa da
farko don bata san ko yasan imaan na da Asthma ba, can tace "Gata nan dai a kwance
bari in bata" mikewa Imaan tayi da kyar ta karbi wayar ta kai kunne cikin sanyin
murya tayi masa sallama, cike da damuwa yace "What's wrong with you dear?" a
hankali tace "Naji sauki" yace "But what happened, dama baki da lafiya ne?" D'an
shiru tayi kafin tace "I had an attack..." Da mamaki yace "Are... you asthmatic?"
Ta gyada kai kamar yana ganinta tace "Um" yace "Subhanallah, to Allah ya sauwake...
is ur breathing now ohk?" Tace "Sure" yace "Xa ki iya fitowa yanxu?" Ta yi shiru,
sai kuma a hankali tace "I will try" yace "Alryt gani nan xuwa" katse wayar yyi, ta
koma ta kwanta, Halima na kallonta tace "Allah ya sauwake imaan" imaan ta d'an mata
murmushi, Halima tace "ki rike wayar idan ya kira bari xan je ana jirana na sani"
Imaan tace "Toh nagode" daga haka Halima ta mike ta fita, ba a dau lkci da fitar ta
ba Gwaggwo ta shigo da cup din tea ta xauna gefen gadon tace "Sannu Fatima tashi ki
sha shayi na hada maki" imaan ta mike xaune tace "Gwaggwo ai na ci abinci, a koshe
nake" Gwaggwo xata yi magana sai ga Ammi ta shigo dakin tare da Aunty, aunty na
kallonta tace "Sannu Imaan, ya jikin" imaan ta d'an yi murmushi tace "Na ji sauki
Aunty" Aunty tace "Toh Allah ya kara lafiya" fita Aunty tayi don xuwa su ci gaba da
aikin da su ke yi, Ammi na kallonta tace "Kirjin yyi sauki?" Imaan tace "Kadan
kadan yake min" Ammi tace "Toh sannu, dama sai da daddy ya guji hakan, nima nasan
kawai wahala xa ki xo ki kara min nan" Gwaggwo tace "Wani irin magana ce wannan
Aisha, ita ta daura ma kanta ciwon ashe?" Ammi dai bata ce komai ba, imaan ta kalli
wayar Halima da ya fara ring, Sannan ta daga a hankali ta kai kunne, satan kallon
Ammi tayi, murya can kasa tace ma Sadeeq "Toh..." Daga haka ta katse wayar, Gwaggwo
tace "Wa ye?" Imaan ta sunkuyar da kai tace "Ce min yyi yana waje" Gwaggwo tace
"Sadeeq?" Imaan ta gyada mata kai, Gwaggwo ta kalli Ammi tace "Toh ko ya ajiye ta
gida kawai... Ni xamanta nan bai kwanta min ba, ba a fara komai na girki ba fa
ciwonta ya tashi, ina ga gobe da xa ayi girke girke" Ammi tace "Waye ya kira ki?"
Imaan ta kasa cewa komai, Gwaggwo tace "D'an gidan Bulasawa ne..." Ammi tace
"Bulasawa kuma?" Gwaggwo ta kalli Imaan tace "Ko bata san ki da shi bane??"Imaan
tayi kasa da murya tace "ta san shi" Ammi tace "Na san sa a ina??" Imaan tace
"Abokin ya Muhsin fa" da mamaki ammi tace "D'an Bulasawa ne dama?" Gwaggwo tace
"D'an sa ne na cikinsa, yaro mai hankali da natsuwa yana yawan xuwa tare da Muhsin
gaisheni, ban ma san suna tare da fatimar ba, akwai wani lkcn dai da ya xo ya
sameta a nan, ko tun lkcn suke tare ban sani ba" Ammi ta kasa cewa komai sai kallon
Imaan take, Gwaggwo tace "To tashi ki je, ki ce masa ya shigo ina nemansa" imaan
bata ce komai ba ta mike da kyar ta sa Hijab ta fita, bayan fitarta Ammi ta xauna
gefen gadon tana kallon mahaifiyar ta tace "Anya kuwa Gwaggwo, d'an wajen Bulasawa
fa, ina shi ina Imaan kuma? Kinsan yaudara tayi yawa yanxu a rayuwar fa" Gwaggwo
tace "Fal yaqul khairan auliyasmut... Bana son irin wannan maganan, Sadeeq bai yi
kama da mayaudari ba kuma tun kan ya san imaan yake xuwa min tare da Muhsin, ba a
taba cewa d'an mai kudi ne yaron, faram faram yake da kowa, ni dai har ga Allah ya
min kuma xan yi farin ciki idan Allah yasa shi ne mijin imaan" Ammi dai ta kasa
cewa komai har sannan bata daina mamakin wai Sadeeq yaron Bulasawa bane. Tunda
Imaan ta fito Sadeeq ke kallonta, ta sunkuyar da kai tace "Ina yini" yace "Lafiya
lau, ya jikin?" Tace "Na ji sauki" yace "Tablet kike sha ko inhaler kike amfani
da?" Tace "Inhaler" ya d'an yi shiru kafin yace "Toh Allah ya sauwake" Tace "Ameen,
Gwaggwo tace ka shigo" ya d'an buda ido yace "Da gaske" ta gyada masa kai, yace
"But ba mutane a ciki" d'an murmushi tayi tace "Idan ka shiga xaka gani" Haka nan
dai Sadeeq ya shiga gidan yana sinne kai, bayan sun gaisa da Gwaggwo, Gwaggwo tace
"Ka taimaka ka ajiye fatima a gida Sadeeq bata ji dadi ba" yace "Toh In sha Allah
Gwaggwo" bai jima a parlon ba ya fita bayan yayi sallama da Gwaggwo, imaan ta fito
daga daki rike da trolley dinta tayi ma Ammi da Gwaggwo sallama sannan ta bi
bayansa... the journey was silent, lta dai ta jinginar da kanta tana sauke numfashi
a hankali, lkci lkci Sadeeq ke kallonta sai ya sakar mata lallausan murmushi, ita
dai sai dai ta sauke idonta, dai dai gate din gidansu yyi parking, a hankali ta
kallesa tace "Nagode" yace "How will I reach you ltr, ko xaki yi plugging fone naki
idan kin shiga ciki?" Ta d'an yi shiru kafin tace "Ina wayarka" bata jira cewarsa
ba ta dau tsadadden wayar sa dake ajiye ta yi dialing number din inna yana fara
ring inna ta dauka kamar jira take tana cewa "Ni dai an dameni, tun safe nake aiki
ban xauna ba wllh, waye kuma wannan" murmushi Imaan tayi ta katse wayar, Sadeeq ma
yyi murmushi yace "Number kaka koh?" Ta gyada masa kai ta bude motar ta fita tana
kallonsa, Fitowa yayi ya fiddo mata jakarta yace "Ki huta sosai idan kin shiga ciki
plss" tayi murmushi tace "In sha Allah" yace "Alright dear, Allah ya kara lafiya"
wucewa ciki tayi ta nufi part din Inna, inna ta dinga kallonta daga sama har kasa
tace "Lafiya kika taho min nan da jaka??" Imaan tace "A'a ni daga gidan gwaggwo
nake" Inna tace "To har na ji sanyi" Imaan dai bata tanka ta ba ta ajiye jakar ta
cire Hijab din jikinta ta kwanta kan kujera, inna tace "Toh har an gama bikin ne
kika dawo ko kuma bikin ne dai garau garau kika gudo?" Imaan dai bata ce mata komai
ba, inna tace "Atoh, ni dama shi sa naki xuwa kwata kwata, ba ruwana inje in dawo
da yunwan cikina, biki ba na yan gayu ba, kuma dama Habiba bata ce min tana aurar
da jikarta ba, ni dai na bada dubu biyar a kai mata ban bi ta halinta ba, Allah ne
xai bani lada" Wani bowl dake rufe inna ta bude Imaan dake ta kallonta ta leki bowl
din daga kwancen da take taga nama ne soyayye a cike, inna ta saci kallonta suna
hada ido ta mike ta wuce daki da bowl dinta, ba a wani dau lkci ba ta fito da
bokitai, ta sa makulli a kofar dakin, Imaan tace "Fita xa kiyi kike sa makulli a
dakin?"
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

Inna tace "Baxan sa makulli ba sauro su cika dakin su sa min cuta in bar 'ya yana
da wahala?" Tana fadin haka ta fita waje xata wanke bokitan da ta kwaso, Imaan na
kallon film da ake a TV taji muryar inna tana cewa "Mujaheed kai me cewa inje bikin
su gidan uwar Aisha to ga jikar gidan ma ta gudo daga bikin balle ni karere, ji dai
yanda aka dinga facaka da kaji a bikin kanwarka, toh can ni nasan baxa su yi haka
ba, abinda duk na san su, meye ban sani ba..." Da sauri Imaan ta mike xaune jin
wanda inna ta ambata, Mujaheed dake ta kallon inna yace "Ke dai ki daina haka..."
Inna tace "Ni akwai wanda ya isa hanani fadin gaskiya kuwa duk girman duniyar nan??
to duk ba wannan ba don bai shafeni ba, inji ka siyo min kazar da nace maka nake
marmari" Mujaheed bai tanka ta ba ya nufi kofar shiga parlon, da sauri Imaan ta
saka Hijab dinta ta rufe har kafarta ta kafe TV da ido, Mujaheed ya shigo parlon,
kallo daya yyi mata ya ajiye ledan hannunsa ya xauna yana danna wayar hannunsa,
Imaan ta ki yarda ta kallesa gabanta sai faduwa yake, gaba daya she was
uncomfortable, Inna ta shigo tace "Allah maka albarka, kai kadai dama xance ka siyo
ka siyo" kitchen ta tafi ta dauko plate biyu ta xauna kan tabarma tana gogewa ta
bude ledan kazar ta raba biyu, daya nata daya nashi, can dai ta kallesa tace "Toh
ita kuma warcan matar ya xa mu yi da ita, tunda ba da ita aka siyo ba" shi dai
Mujaheed bai ce komai ba, Inna ta tabe baki ta dauko wani plate din ta dau cinya
daya da tsoka daya ta dangwala a plate ta mika ma imaan tace "Toh gashi dai, ido
guba...." Ba tare da imaan ta kalleta ba ta girgixa kai gently tace "A'a baxan ci
ba" Kallonta Mujaheed ya dinga yi da mamaki, inna ma ta saki baki tana kallonta
tace "Dama baki da lafiya shine kika yo min nan salon ace a nan ciwo ya tashi ni
patuu?? don cuta kadai ke hanaki cin kaza ni dai na sani" Imaan bata ce komai ba
bata kuma kalleta ba, can ta mike ta nufi kofa tace "Ni fa a koshe nake" daga haka
ta fice a parlon.

*The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included


in the payment group

30.......

Documents By AIHAUSANOVELS
Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

Imaan na kwance bedroom dinta dab da Magrib taji an danna bell, tashi xaune tayi
don ita kadai ce gidan Ammi na can Unguwar rimi, daddy kuma bai dawo ba, can ta
mike ta sa Hijab dinta ta nufi kofar a hankali tace "Waye?" Muryar Ummi ta ji tace
"Aunty na kiran ki" Imaan ta bude kofar tana kallonta, a tare suka tafi part din da
Ummi, Imaan ta wuce sama ta bude kofar dakin Aunty, Aunty ta fito bayi bayan tayi
alwala tana kallonta tace "Ya jikin?" Imaan tace "Na ji sauki Aunty" Aunty tace
"Ammi can xata kwana fa, sai ki dawo nan ki kwana ko ki tafi gun inna" Imaan tace
"Xan je gun Inna" Aunty tace "Toh ga abinci ki dauka" ba musu ta durkusa ta dau
warmer din da Aunty ta nuna mata, Aunty tace "Ki tabbatar kin sha magungunanki
bayan kin ci abincin" Imaan tace "Toh sai da safe" daga haka ta bude kofa ta fita,
a stairs suka hadu da Yusuf, suna hada ido ya dauke kai, tace "Lah ya Yusuf kayi
tafiya ne, ban ganka 2 days ba" Yusuf na ci gaba da haurowa stairs din yace "Not at
all" daga haka ya wuceta ta bi sa da kallo, can dai ta sauka ta bar parlon. Part
din inna ta wuce ta sameta tana sllh, ta ajiye abincin hannunta a parlor ta fito
bakin tap ta daura alwala ta koma ciki, tana idarwa ta koma kan kujera ta kwanta,
inna ta gama addu'o'in da take tace "Toh wai me yasa kika baro gidan bikin kika
dawo?" Imaan tace "Dama ba kwana naje yi ba" Inna ta tabe baki tace "Toh ita
Rukayya taje gidan kuwa?" Imaan ta girgixa kai tace "A'a bata je ba" inna tace
"Ikon Allah, Kice Amina ce kawai ta je?" Imaan ta gyada mata kai, inna tayi tagumi
tace "Naga abinda ya isheni, tun da uwata ta haifeni ban taba ganin haka ba wlh,
Rukayya bata da xuciya mai kyau sam, ko da yake abun na da tushe, kinsan lkcn da
Bukar ya auro Uwarki bata da aminiya da ta wuce Amina, lkcn Amina tana nan wata yar
duma duma da ita kamar ki latsa ta jini ya feso, toh a lkcn gida daya Rukayya da
uwarki suka xauna sai dai kowa da sashensa kamar dai Wannan gidan amma ko rabin
gidan nan bai kai ba, lkcn Ahmadu da Bukar na yaku bayi basu da komai sai wahala,
tun ba yau fa suke son junansu in gaya maki, dama a haka kuma suka taso, toh kullum
Rukayya bata da aiki sai neman fitinar uwarki a tsakar gida, kaii Gaskiya Rukayya
ta dade tana hauka, ga uwarki mai hakuri bata biye ta, ga uwa uba kawaici, amma
akwai ranan da xuciya ya debi Aisha ta nakada ma Rukayya shegen duka har sai da ta
targada mata hannu, da kyar aka kwace ta hannun Aisha, ni dai ce ma Bukar da Ahmadu
nayi duk su kora su gidan iyayensu ba ruwana, to sun fa mayar min da gidan 'yaya
wajen dambe, a lkcn kuma kullum Amina sai ta xo gun uwarki, tun fa Rukayya bata san
Amina xata aure mata miji ba ta tsaneta har xage xage sun ta6a yi da jefe jefen
dutse, to ana_nan ana_nan Ahmadu ya kyallara ido ya ga yar duma duma Amina, to
karewa ma gun Aisha ya amshi lambarta idan ba mantawa dai nayi ba, Rukayya na ji
tana gani Ahmadu ya aure kawar makiyiyarta wato Aisha, in gaya maki Aisha ce a kan
gaba na komai da bikin, kuma ni nasan da gayya tayi haka, to da Aisha ma aka raka
Amina dakinta gashi gida daya ya hade su da Rukayya, to kinji musabbabin komai...
Ba irin xugar da Rukayya bata min ba kan in sa ubanki ya kara aure tunda uwarki
bata haihuwa ni dai naki, kinsan da Rukayya yar dakina ce kafin ta xama bala'i, duk
da dai nayi masa magana na yi masa magana har na gaji na kyalesa wato Bukar, to
Aisha ta shanye min shi, daga karshe dai Bukar ya raba fada ya dauke uwarki suka
koma Abuja da xama gaba daya, ai sun fi shekara biyar a Abuja, kuma fa lkcn...
Katse ta Imaan tayi tace "Toh ni dai ban tambayeki ba, wllh har na gaji da jin
labarin nan, a wata sai kin bada labarin nan ya fi sau biyar" Inna tace "Ai ba sai
kin tambayeni ba duk sanda na ga dama dole in bada labari ko da kuwa ni daya ce a
daki, to ina ruwan wani da ni??" Imaan ta tabe baki ta mike ta jona ruwa a heater
don yin wanka, dawowa tayi ta xauna tana jiran ruwan yayi, inna tace "Ke wai
bulasawan na maki waya ma kuwa?" Imaan tace "Ehh" inna ta d'an yi murmushi tace
"Toh madallah, gama wanka ki xo in baki wani labari mai ban al-ajabi" imaan tace
"Ai ruwan bai yi ba ki bani" Inna tace "Ki dai yi wankan tukun" Juye ruwan Imaan
tayi haka ta wuce bayi inna na cewa "Don Allah idan kin gama ki dauraye bayin da
omo, kazanta dai ba kyau" Imaan dai ba ta tanka ta ba ta cire kayanta ta shige
bathroom. Imaan na gama wanka ta fiddo daya daga sleeping wears dinta dake press
din inna ta saka ta feshe jikinta da turarrukan Inna ta fito ta xauna tana kallon
inna da ke xuba gyangyadi a xaune, murmushi imaan tayi ta dau remote xata canxa
tasha aka bude kofar parlor da sauri ta mike xata gudu xuwa daki Mujaheed ya shigo,
tuni ta shige daki ta sa makulli ta wani hade rai, Inna da ta bude ido a gigice
tace "Subhanallahi, lafiya??" Mujaheed dai na tsaye sai kallon kofar dakin yake,
inna tace "Ni dai ba ruwana, ku dinga jin tsoron Allah, ya xa a maida min gida
kamar filin daga, baka ji yanda xuciya ta ta tsinke ba wllh, ni dai ana shiga
hakkina... Wnn 'ya ta Bukar dai ba ta da imani an wani laka6a mata Imaan din karya"
Shi dai Mujaheed bai ce komai ba bai kuma fasa kallon kofar dakin ba, wayar inna ya
fara ring, kamar xata yi kuka tace "Kaga wani bala'in koh, toh meye wnn
fisabilillahi tsakar dare kuma" daukar wayar tayi ta danna inda ake picking ta kai
kunne hade da sallama tace "Waye??" Sadeeq yace "Ina yini kaka?" Tace "Ce maka nayi
waye??" Yace "Sadeeq ne" Inna ta bude ido sosai tace "Bulasawa?" Yayi murmushi yace
"Ehh kaka" Inna tace "Lahh ina yini??" Mujaheed couldn't stop looking at her da
mamaki, Sadeeq yace "Ya gidan kaka?" Tace "A'a lafiya lau wllh Bukar, ya iyayen
ka?" Yace "Suna lafiya lau" inna tace "Toh madallah, shiru shiru ban ganka ba kwana
biyu, Hala imaan ce ta baka lambar wayata?" Yace "Ehh ita ta ban" Inna tace "Toh ai
ta kyauta wllh, shkkn sai in ba Mujaheed da ya tsaya kaina sandandan ya min saving,
yaushe xaka billo?" Sadeeq yace "Gobe in sha Allah" Inna tace "Toh Alhmdllh, da
kaina kuwa xan maka tuwo da miyar taushe in sha Allah" Sadeeq yayi yar dariya yace
"Toh nagode kaka, imaan din na kusa?" da sauri inna ta mike tace "A'ahh toh bari in
bata har ta kwanta ina jin, Kasan bata dade da dawowa daga gidan bikin su kakarta
ta wajen uwa ba" Sadeeq yace "Toh ki barta gobe xan kira in sha Allah, dama ke na
kira mu gaisa" inna tace "Ae ko naji ddi Allah maka albarka, maxa kashe kudin ka na
ta konewa" yyi murmushi ya katse wayar. Inna na kallon Mujaheed ta mika masa wayar
tana washe baki tace "Kai yi min saving, lambar bulasawa ne" Mujaheed ya amshi
wayar yana kallon number, Inna ta xauna tace "Kai amma yaron ya kyauta, wllh na ji
dadi, kaga alamar xai rike min jika da kyau kenan wllh, gashi gobe yace zai shigo,
sai in baka dari biyar dita ka shiga kasuwa ka siyo min kayan miya da nama
lafiyayye in masa miya mai kyau" Mujaheed ya xauna kan kujera har sannan bai daina
kallonta ba, tace "Ka min saving mana Mujaheed kar lambar ya bace" Mujaheed ya gama
danne dannensa ya mika mata wayar ta, ta amsa ta ajiye tace "Dole in tashi da
sassafe kenan gobe, bari ma in dauko maka kudin kar ka manta ka tafi baka amsa ba
in rasa d'an aike" Mujaheed dake kokarin controlling temper dinsa yace "Ki dai ba
Yusuf" inna ta gwalo ido tace "Waye kuma Yusuf?" Mujaheed bai tanka ta ba tace "Toh
bari kaji, Rabonsa da ya tako nan ya gaida ni tun ran da yyi abun kunyar nan, to
dama idan ya xo da wani idon xai kalleni, A'a ba ruwana ni bana bukatansa dama, ga
dai ka" Mujaheed na gyada kai yace "Ita kuma yarinyar nan kice mata wllh idan ta
sake ganina ta kwasa a guje sai na sa ta kuka a gidan nan" inna tace "Oh oh Allah,
yau naga jaraba, baxata gudu ba kana cutar ta Mujaheed? nine fa na koya mata ta
dinga gudu idan ta ganka, toh me xata tsaya ta maka idan ta ganka, ni dai ba
ruwana, ka dinga tsoron Ubangijin ka, ai ta ma kusan aure ta huta da fitinar ka sai
in ga ko gidan mijin xaka bi ta kana cuta kuma, karshenta sai ka kare a kurkuku don
Bulasawa daure ka xai yi a fita da kai kasashen turai ai maka hukunci, ka ga sai ka
bar Ahmadu da Bukar da kashe makudan kudaden da suka fi karfinsu, idan ba haka ba
kuma ka ru6e a kurkuku in shiga uku" mikewa Mujaheed yyi ya nufi kofa fuska daure,
inna tace "Toh kudin cefanen pa, baka amsa ba fa? Ko xaka siyo min da kudin ka"
Washegari da safe Imaan na shan shayin da inna ta hada mata, inna tace "Wai me yasa
kike gudun katon can ne, halan laifi kika masa" Imaan taki cewa komai da farko, can
kuma tace "Ba komai, ni bana son yana kulani a gidan nan nima kuma na daina kulasa,
don Allah ki taya ni gaya masa inna" on a serious note ta fadi hakan, Inna tace
"Toh ai hakan yafi ma, kinga babu ta yanda xai dinga cutarki kuma, wahalan da yayi
a kanki a baya Allah ya saka masa, idan kuma biyansa yake son ayi sai ya fada min
nawa ne bai gagareni in daga daya daga gidajena na gado in siyar in biyasa ba, kuma
ba karamin aikin Bulasawa bane ya siya min wani ma a kasashen turai in xuba yan
haya" Murmushi imaan tayi ta mike ta dauko mata dankunnen da Sadeeq ya bata, inna
na budewa tace "Wannan ai gwal ce, a ina kika samo Imaan?" Imaan tace "Shi ya bani"
Inna ta xaro ido tace "Mujaheed din???" Imaan ta hade rai tace "Sadeeq dai" Inna ta
saki wani kabbara tace "Kinga abinda nake nufi ko, to a xamanin nan wa xai ma naka
haka?? Wllh ki rike yaron nan da kyau kai ko su Maimoon kada ki yarda su san abinda
kike ciki balle wancan mutumin Mujaheed, 'ya yan Ahmadu ba wani tsoron Allah garesu
isasshe ba, duk yan bakin ciki ne, ki bar wannan gu na in ajiye maki, ana nuna ma
su Ahmadu dama cewa xa su yi a mayar tunda ba hankali ya ishe su ba, shi ma mutumin
nan Mujaheed yanxun nan xaki ga ya shigo wai gaisheni bai san ni damuna yake ba,
maxa dauka ki wuce da shi ciki kada...." Bata rufe baki ba aka bude kofa, Abba ya
shigo da sallama Mujaheed na biye da shi, Inna ta boye dankunnen a karkashin
carpet, a hankali Imaan tace "Ina kwana Abba" Abba yace "Lafiya Imaan, naji baki da
lafiya, ya jikin naki?"
Kallonta Mujaheed yyi da sauri, tace "Naji sauki Abba" Abba yace "Toh Allah ya
sauwake" tace "Ameen" kallon inna tayi tace "Inna zan je dauko kayana" inna tace
"Toh yi maxa" tashi tayi ta nufi kofa ta fita, Mujaheed ya fara danna waya ya kai
kunne sai kuma ya mike ya fita yana cewa hello, Imaan na shiga parlon ta nufi
dakinta don har Daddy ya fita ganin bata ga motarsa a parking space ba, tana dauko
kayanta ta ji an bude kofa, ta juya da sauri tana kallon kofar dakinta, can dai ta
nufi kofar ta murda, Mujaheed ta gani tsaye kusa da kofar dakin nata, Xata gudu ya
fixgota waje fuska daure yace "Ni dodonki ne kike gudu na?" Kuka ta fara yi a
rikice taki yarda su hada ido tace "Ban son hka ni ka sake ni yaya" kallonta ya
dinga yi kafin yace "Meyasa kike gudu idan kin gan ni" sosai xuciyarta ke bugawa
tace "Ba komai, ni ka sake ni plss" ya sauke idonsa daga kallonta, can yace "What's
wrong with you?" Da kyar tace "Ni na ji sauki" saketa yyi ya juya ya fita, ta
durkushe wajen har sannan xuciyar ta bai daina bugawa ba. Da yammacin ranan Imaan
na durkushe bakin tap din inna tana alwala kamar ance ta daga kai taga Sadeeq yana
tahowa, da sauri ta rufe gashinta ta xaro ido, murmushi yyi, yana isowa inda take
murya can kasa yace "Good evening dear, sae ynxu xa ki yi la'asar?" Bata iya tace
masa komai ba ya tsaya bakin kofa yyi sallama cikin cool voice dinsa, Inna ta fito
daki tana amsa sallaman, shiga yayi tace "Au, sannu da xuwa Bukar ashe kai ne" ya
xauna yana murmushi yace "Ina yini kaka?" Tace "Lafiya lau Bukari, ya aiki?" Yace
"Alhmdllh mun gode Allah" tace "Toh ya xafi xafi, ko da yake ma akwai Ac ko ina
yanxu" Yayi dariya yace "Haka ne kaka" Tace "Toh madallah, bari in kawo maka ruwa
da lemo" bata jira cewarsa ba ta debo masa su a fridge ta ajiye, tace "Toh nayi
tuwo na ajiye maka ina bacci wannan mutumi Mujaheed ya shigo ya cinye"

*The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included


in the payment group.

31......

Sadeeq yyi murmushi yace "Wani lkcn ai sai ki min kaka..." Inna tace "Toh in sha
Allahu kuwa, yanxu ya maganar da muka yi ranan Bukar?" Sadeeq yace "Kaka Abbana
baya kasar ne, ina jiran sai ya dawo in sha Allah sai ayi magana" inna tace "Toh da
kyau, Allah maido da shi lafiya, ai dama Bulasawa bai fiye xama ba aka ce, baya can
baya nan, to abun ka da babban mutum fitattce..." yar dariya kawai Sadeeq yyi, sun
fi minti talatin da inna dake ta basa labarin da ya kamata da wanda bai kamata ba,
daga karshe ya ajiye mata dubu ashirin yyi mata sallama, xaro ido tayi tace "Kai
dai baka gajiya Bukar, wancan ma da ka ban har yau basu kare ba wllh suna can na
adana su sbda yaran gidan nan, toh ni dai nagode Allah ya maka albarka, ya kara
maka budi" yana murmushi yace "Ameen kaka, nima nagode" inna tace "Toh ka gaida
uwarka ka ji, wataran duk xamu san juna idan Allah ya yarda, to ya sunan uwar
taka?" Yana murmushi yyi kasa da kai yace "Hajiya Khadijah..." Inna tace "Lahh
sunan aminiyata a da kafin ta xama abun gudu, Allah sarki Hadiza ko ana wace
duniyar yanxu kuma" Dariya kawai Sadeeq yyi yana kallonta, Inna tace "Allah ya sa
mu yi kyakkyawan karshe dai, amma Hadiza bata yi abun kirki ba, ga son abun duniya
Allah ya dora mata, wai..." Kofa ya nufa yana nurmushi yace "Sai na sake shigowa
kaka" ta mike da sauri tace "Toh Bukar a gaida gida, Allah maka albarka" ya amsa da
"Ameen" ya fita, Kalle kalle compound din kawai Sadeeq ke yi bayan ya fito amma har
ya kusa gate bai ga alamar Imaan ba gashi wayar ta har sannan a kashe, mota ce ta
shigo gidan driver yyi parking, aka bude motar umma ta sakko tare da Hajiya
Balaraba suka bude bayan mota suka dinga fiddo manyan ledoji, Gaishesu Sadeeq yyi,
Umma ta kallesa ta amsa tana ci gaba da fiddo ledojin, ya wuce su, sai da suka nufi
entrance din shiga gida Hajiya Balaraba tace "waye wancan kuma" Umma tace "Kila
wajen Yusuf ya xo" Hajiya Balaraba yace "Dama Yusuf na gari, ni na xata bai nan,
duk na xo bana ganinsa" Umma ta tabe baki tace "Yana nan, kinsan sa bai fiye faram
faram da mutane ba, ko yana gidan ma to idan bai dakinsa yana bangaren fitinanniyar
kakarsu" Hajiya Balaraba tace "Shi yasa, amma na fi ganin Mujaheed" Umma tace "ko
kwana hudu ba ayi ba aka gama wani case a gidan nan, wai Yusuf ya rasa warce xai
fito yace yana so sai yar wajen Aisha" Hajiya Balaraba ta xaro ido tace "Yar wajen
Aisha kuma, to sai aka yi yaya?" Umma tayi wani murmushi tace "Ai ba xancen ma
yanxu haka, kakarsu dai tace ko bayan ranta bata amince da auren ba, kuma a ranan
na shirya na je wani waje aka ce in kwantar da hankalina ba matarsa bace ba ma,
wannan dai Hafsar ita ce matarsa kuma wai kwanan nan xa ayi bikin, kila a hada tare
da na Mujaheed, tunda gashi har mun kusa gama hada lefen nasa" Hajiya Balaraba tace
"Ke ma dai da daukan ma kai, to meye xaki wani damu a kan lamarin d'an kishiyar
ki??" Umma tace "Ashe ma baki gama sani na ba kenan duk kusancin mu Balaraba, ni
xan so abu mai kyau ya ra6a Aisha da 'yar ta, Yusuf ai abu ne mai matukar kyau,
idan ya auri yar wajen Aisha ai ba karamin dace yarinyar tayi ba, ga arxiki ga shi
da hankali da natsuwa, toh ina xan yarda, kiri kiri fa kun ga bakin cikin da ta
dinga nunawa lkcn bikin Seeyama, babu abinda ta ta6uka da bikin sai dai ta leko ta
koma, da aka tashi kai Seeyama ma ita ce karshen tafiya sannan farkon dawowa duk
sbda hassada, shine xan yarda abun kirki ya sameta ita ma, inaa ai tunda naji ance
min ba matarsa bace hankalina ya kwanta, sai ga kakarsu ma tace samm ba da yawunta
ba" Hajiya Balaraba tace "Toh Alhmdllh" Hajiya Balaraba ta shiga jera tulin inner
wears din da suka siyo kasuwa a daya daga akwatina takwas dake dakin Umma, Umma
tace "Dole ma Mujaheed ya xo ya kara kudi, don wannan da ya rage ba isa xai yi ba
don har gwal ina son mu saka a kayan, ko da dankunne da sarka da xobe ne kawai
banda awarwaro" Hajiya Balaraba tace "Gaskiya kam, xa ma su fi ganin lefen da
mutunci, to shi gogan na duba kayan ma kuwa?" Umma tace "Idan an gama hadawa sai su
duba tare da ubansa, in sha Allahu kafin karshen watan nan xa a gama komai, su tafi
su kai gaisuwa tare da sadaki da ubansa" Imaan na tsaye kitchen tana wanke plates a
sink Ammi ta shigo tace "Kina da card a wayar ki in kira daddy nayi missing calls
dinsa, mine is exhausted" Imaan ta juya ta kalleta da farko rasa abinda xata ce
mata tayi, can a hankali tace "Ammi wayana baya wajena tun 3 days ago fa" Ammi na
kallonta da mamaki tace "Baya wajen ki? To yana ina?" Imaan tace "Yaya ne ya amshe,
ni kuma ban tambayesa ba har yau" Ammi ta wani hade rai tace "Wato ke baxa ki ji
magana ta a gidan nan ba ko Imaan, ban raba ki da Mujaheed ba?" Imaan tace "Wllh
Ammi ni na daina kulasa a gidan nan ki tambayi Inna, idan ma yaje part din inna ni
shigewa daki nake ko in taho gida, wllh na daina xaunawa inda yake ma, kuma da ya
amshi wayar ni ban tambayesa ba har ynxu, ban ma san wayar kuma ko ya bani" Ammi
tace "Toh yayi kyau, xan ji ko shi ya siya maki wayar" Imaan tace "Wai don sbda
Sadeeq na kirana fa shine ya karbe" shiru Ammi tayi tana kallonta, can tace "Toh
ina ruwansa da kiran Sadeeq din?" Imaan ta bude hannu alamar bata sani ba, Ammi ta
juya ta fice daga kitchen din. Da rana Aunty ta shigo parlon su Imaan da sallama,
Imaan dake cin abinci parlor tace "Sannu da xuwa Aunty" Aunty tace "Yauwa Imaan,
Ammi fa?" Imaan tace "Tana daki" direct bedroom din Ammi Aunty ta wuce, Ammi dake
jera kayan guganta a press ta ajiye kayan hannunta tace "Yanxu nake son gamawa inje
in maki ban gajiya Hajiya sai kuma ga ki" Aunty tace "Nima ban gajiya na xo maki
ai" gaisawa suka yi Aunty ta xauna gefen gadon Ammi tace "Halan daddy ya koma" Ammi
tace "Ehh tun jiya ya koma, ya su Maimoon fa, kwana biyu ni ban ga Yusuf ba ko
tafiya yyi babu sallama" Anty ta tayi murmushi don har sannan tasan Ammi bata ji
abinda Inna ta masa ba tace "Yana nan kuwa, amma next week xai tafi Abuja ina jin,
aiki ne fa ya same mu in gaya maki..." Ammi ta xauna tace "Wani aikin kuma?" Aunty
tayi yar dariya tace "D'an ki ne yyi min transfer daxu yana son mu fara hada masa
lefe" Ammi tace "Yusuf?" Aunty tace "Ehh fa" Ammi tace "Ikon Allah, toh Allah ya
bamu iko, Hafsar ce dai?" Aunty tace "Ehh ita" Ammi tayi dariya tace "Allah yayi
kenan, kwanaki fa da nake tambayarsa ita ce min yyi shi fa ba ita xai aura ba, nace
to wacece sai yace tana nan wataran xa mu santa" Aunty ta d'an yi murmushi tace
"Toh dai jiya ce min yyi Hafsah" Ammi tace "Toh Allah yasa albarka, ya kuma sanya
alkhairi" Sun d'an taba hira daga karshe Aunty tayi ma Ammi sallama, Ammi ta rakata
har balcony tana ce mata sai ta leko ita ma. Tun daga wannan rana imaan ta fara
wasar yar buyan gaske da Mujaheed, part din innan ma gaba daya bata son xuwa sai
dole shi ma kai mata abinci, tana ajiye mata kuwa ko xaunawa bata yi xata juya ta
bar wajen, Kwata kwata ita dai ba ta son ma su hadu, da ta tuna maganganun su Aunty
Halima da Rabi'ah sai wani haushin sa ya diran mata, wai yana sonta, kai ta ma san
kawai labarin su Anty Halima ne, ta ya yaya xai so ta, yanxu kam Sadeeq ta wayar
Ammi yake kiranta dama da taji ring din wayar xata tafi da sauri ta duba ko shi ne,
tun Ammi na complain har dai ta gaji ta daina. Yau da daddare Imaan na kwance
parlor suna kallo tare da Ammi dake xaune aka danna bell, mikewa tayi ta sa Hijab
ta nufi kofar ta bude, ido hudu suka yi da Mujaheed dake tsaye bakin kofar, gabanta
ya fadi sosai tayi saurin juyawa ta basa hanya, ya shiga parlon yyi ma Ammi kallo
daya ya sunkuyar da kai ya ajiye ledan hannunsa yace "Ina yini" tace "Lafiya lau,
ya aiki" Yace "Alhmdllh, dama Abba ne yace in kawo wannan" Ammi tace "Toh Allah
amfana" Yace "Ameen, sai da safe" Daga haka ya juya ya nufi kofa ya bude ya fita ya
kulle kofar, Ammi ta bude ledan taga gasasshiyar kaza ce babba, duk son imaan da
kaza kin ci tayi wai ta koshi, har hakan ya ba Ammi mamaki sosai, Ammi ta debi
kadan ta kai sauran fridge ta ajiye. Ana saura few days su yi resuming schl ranan
Friday da yamma sadeeq ya kira ta wayar Ammi, Imaan ta dau wayar da ke dakin ta
yawanci, bayan sun gaisa yace mata yana waje, xaro ido tayi a hankali tace "Toh"
daga haka ya katse wayar, Fitowa tayi daga dakinta gabanta na faduwa ta tafi dakin
Ammi ta makale bakin kofa tana kallonta a hankali tace "Ammi ana kirana a waje"
Ammi tace "Wa ke kiranki??" sunkuyar da kai tayi ta rasa wa xa tace don tun ranan
da ta ambaci sunansa a gaban Ammi Ammi tace mata bata da kunya sunan Mahaifin nata
take kira gatsau, to yanxu kam bata san ya xata kirasa ba, Ammi tace "Toh kar ki
dade a waje" d'an murmushi tayi tace "Toh Ammi" daga haka ta fita dakin, as usual
Hijab dinta har kasa ta saka ta fito, kamar mai tausayin kasa take tafiya har ta
isa gate, Yana ganinta ya bude motar ya fito ya rungume hannayensa yana kallonta
daga glass din idonsa, ta sunkuyar da kai har ta isa kusa da motar, cikin sanyayyan
murya tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau dear, ya gida?" Tace "Alhmdllh" yace "Baki
jin dadi ne, you look pale" tayi murmushi tace "A'a lafiyata lau" yace "To kaka fa,
ko xa ki rakani in je in gaisheta" ta xaro ido tace "A'a ai bacci ma take" dariya
yyi yace "Sure?" Tayi murmushi bata ce komai ba, yace "Ya Ammi" tace "Lafiyarta
lau" yace "I want to take you out for shopping ko tare da cousin sisters din ki ne
xata yarda?" Imaan ta xaro ido tace "A'a baxa a bar ni ba" yace "Ohk then" Shiru
tayi bata ce komai ba shi ma haka, ta d'an daga kai suka hada ido, da sauri ta
dauke kanta, murmushi yyi yace "On Monday xa ku yi resuming third term ss2, I am
still counting fa" yar dariya tayi bata ce komai ba, yace "Yea, ss3 kuma term daya
kawai xa ku yi shkkn, just few months to go in sha Allah" Imaan dai ba ta ce komai
ba ta dinga kallon motar Mujaheed da yyi parking a nan waje maimakon ciki don har
mai gadi xai bude gate sai kuma yaga yyi parking a waje, fitowa Mujaheed yyi daga
motar kana ganinsa kasan daga asibiti yake, Imaan ta sunkuyar da kanta da sauri,
Suna hada ido da
Sadeeq har xai shiga gate sai kuma ya fasa ya nufe sa, Sadeeq yyi murmushi ya mika
masa hannu hade da masa sallama, Mujaheed ya amsa yace "Ya aiki?" Sadeeq yace
"Alhmdllh, wlcm back" d'an murmushi Mujaheed yyi ya juya ya nufi gate, sai bayan da
ya shiga ciki Sadeeq na kallon Imaan da mamaki yace "Why didn't you greet him?"
Tace "Ba ma shiri yanxu" ya buda ido yace "Why??" Tace "Nothing" Sadeeq yace "Uhn
OK, nima daga hospital nake nace let me branch and see you pretty face" Tayi
murmushi ta boye fuskarta, wani leda ya ciro ya mika mata, ganin bata ma san yana
yi ba sbda fuskarta da ta rufe a hankali yace "Take dear" xame hannunta tayi ganin
leda yake mika mata ta xaro ido tace "What?" Yana kallonta affectionately yace
"Take plss" bata fuska tayi tace "Aa thank you bana so" yace "Karba plss" tace "Aa
Ammina xata min fada" Shiru yyi yana kallonta, ta girgixa kai tace "Wllh Ammina
xata min fada" Yace "Toh shikenan" cikin sanyin murya tace "Kayi hakuri" yyi
murmushi yace "Na yi, kar Ammi tace kin dade, ki shiga ciki" tace "Toh nagode" Yace
"No thanks dear, bari in shiga in gaida kaka" imaan ta xaro ido tace "Ae bata tashi
ba" yace "Ehh xan tasheta" daga haka ya nufi cikin gidan ta bi sa da kallo, Inna na
bakin tap ya sameta, ta mike tana washe baki tace "Allah sarki Bukari ka xo min
gaisuwar juma'ah ne" yana murmushi yace "Ehh kaka" tace "Toh shiga ciki ka xauna,
bari in dauraye wajen nan in shigo" yace "Toh kaka" shiga parlon yyi ya xauna, Inna
ta gama dauraye daurayenta ta shigo tace "Toh ya mutan gidan Bukar?" Yace "Alhmdllh
kaka, dama sauri nake, nace bari in shigo mu gaisa, ga wannan a ajiye ma imaan"
ajiye ledan hannunsa yyi, Inna tace "Atoh bari in shiga da shi ciki, Allah yayi
albarka" daga haka ta wuce ciki da ledan, sai ga ta ta dawo da bowl dauke da dambun
nama, ta shiga kitchen ta dauko leda ta fito ta juye a ciki tace "Gashi nan jiya
nayi ni kadai rai na wllh, ko yaran gidan ban tsamma ba ma" Yana murmushi yace "Toh
nagode kaka"
Imaan ta ajiye abincin hannunta tana kallon inna tace "Ina yini" mikewa inna tayi
tace "Jira ni in dauko maki sakon ki, ni dai idan Bukar ya dawo xan ji ko Aisha ce
ta hanaki xuwa bangarena yanxu, banda haka taya kina ajiye min abinci sai ki gudu
kamar ana koranki, Aisha dai bata isa ta raba ni da ke ba tunda ba ita ta haifa min
ubanki ba, idan ma ita ke hure maki kunne duk xan ji idan Bukar ya dawo, ni ba
ruwana" imaan ta bi ta da kallo tana tabe baki, bata dau lkci a daki ba ta fito
rike da ledan da Sadeeq ya bata tace "Wannan yaron kirkin ne ya xo daxu yace in
baki, ko meye a ciki oho, kila wani zinarin ne ma, ni dai ban bude ba don ban gaji
cin amana ba" Imaan ta xaro ido tana kallon ledan, can tace "Me yasa kika karba
inna?" Inna ta hade rai tace "Toh baxan karba ba? A garin fulanawa kika ga ake
maida hannun kyauta baya? Idan baki so sai ki bar min babu abinda ya sha min kai,
ni ina so" wani kallo imaan ta mata ta bude ledan, still tayi tana kallon kwalin
tsadadden waya da ake yayi, Inna ta saki wani kabbara tace "Toh idan ba Sadeeq din
ba dama waye? Wa gare ki banda Allah sai shi din? Ko Bukar baxai siya maki
dankareren waya haka ba balle Ahmadu" Imaan dai ta kasa cewa komai gabanta sai
faduwa yake, Bude kofar parlon aka yi, Mujaheed ya shigo da sallama hannunsa rike
da ledan fruit inna na washe baki tace "Mujaheed kalli wayar da yaron nan Sadeeq ya
siya ma Imaan, ni nasan yayi dubu dari biyar" Mujaheed ya ajiye ledan hannunsa yana
kallon kwalin wayar, Imaan ta mayar da wayar leda taki yarda ta kallesa ta mika ma
Inna tace "Ki ajiye min" inna ta karbi ledan da sauri tace "Toh, nima dai na fiye
surutu wllh" daga haka ta mike ta shige daki, Imaan ta mike ta fice daga parlon da
sauri. Washegari asabar inna na daki ta ji an bude kofar parlornta ta fito tana
tambayar waye, akwatuna taga ana shigowa da, ta saki baki tana kallon akwatunan
tace "Meye wannan kuma?"

*The book Imaan is not free, you read for free ur cup of coffee*

It's 300 via Fcmb 3276052019


Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp digit 07087865788 to be included


in the payment group.

32....

Umma ce ta shigo parlon da sallama, su Ummi da Rahma da Maimoon suka xauna kan
kujera Inna ta kalli Umma sannan ta kalli akwatunan tace "Lafiya Rukayya?" Umma ta
xauna kan lallausan rug din parlon tace "Ina yini inna?" Inna tace "Cewa nayi meye
wannan, daga ina??" Hajiya Balaraba da Hajiya Saude dake tsaye su ma sun shigo
parlon suka gaisheta, Inna ta xauna kan kujera a fusace tace "Oh oh Allah, ni da
ban yini ba xa ku gan ni, akwatunan meye wannan ake shigo min parlor dasu?" Hajiya
Balaraba tace "Na lefe da xa a kai ne" Inna ta xaro ido tace "Lefen wa?" Hajiya
Saude dake d'an tabe baki tace "Wacce Mujaheed xai aura..." Inna tace "Wani
Mujaheed din?" Shiru duk suka yi basu bata amsa ba, Inna ta dinga sakin salati a
jere, can tace "Yanxu Mujaheed aure xai yi ban sani ba sai dai inga akwatuna ana
kokuwan shigo min da su ace min xa a kai lefe? Yanxu Rukayya mancewa kika yi ni na
haifi Uban Mujaheed? Ehh lallai Ikon Allah ya fi gaban haka" daukar waya tayi ta
mika ma Umma tace "Kira min d'an nawa.." Umma da ta daure fuska ta karbi wayar tayi
dialing number Abba ta mika mata, Inna ta karba ta kai kunne, Abba na daga wa Inna
tace "Yanxu Ahmadu ko ba raina kai ba mai ambatan sunana bane kace.... Allah sarki
Inna, gashi Allah yayi lkcn auran Mujaheed baki a doron kasa balle ki sa albarka ke
ma, Amma duk da haka muna maki fatan rahaman Allah... balle da raina da lafiyata
Ahmadu?? wai sai dai inga katuwar matar ka na shigo min da jakunkuna tace min xa su
kai lefe, yanxu ko shi Mujaheed din da nayi bauta da shi yana tsumma na cancanci
yaki fadi min xa a kai lefensa sai dai inji a duniya? Wayyoo duniya Ina xa ki
damu...." Bata jira cewar Abba ba ta katse wayar ta jefar kan kujera ta fashe da
kuka tace "Oh oh Allah, duniya dai ba gaskiya, mutane basa jin tsoron Allah..."
Hajiya Saude tace "Hajiya ba fa kai kayan xa ayi ba yanxu, kawai dai an gama hada
kayan ne aka ce bari a xo a nuna maki, Amma ko gaisuwa ma ba a kai ga kai ma iyayen
yarinyar ba tukun" Inna ta daga kai ta kalleta tace "Ai Rukayyar nan da kike gani
ba mutum bace, idan uwarta ce Hadiza xata mata haka, Ina ce ranan da xa a fara hada
kayan lefen ya kamata ta tako ta xo ta sameni tace to Inna gashi gashi, amma da
yake xuciyarta ba tsoron Allah ban ganta ba, ni dai ba ruwana, kowa yyi da kyau..
kansa, bari kuma Ahmadun ya shigo in ji ko shi yace a boye min har sai an gama hada
lefen" tana fadin haka ta Mike tana kakkabe kujerunta, mikewa Umma tayi tana kallon
kawayenta da su Ummi tace "Ku kwasa mu je" Inna ta juyo da sauri tace "A kwashi
me?? Ai ba ke kika min wahala da Mujaheed din ba, kuma da kyar idan ba da ni xa a
kai lefen ba ma, don haka kada warce ta taba jakunkunan nan duk kuyi ta kanku ku
fita ku bar min parlona in goge, nakudar Mujaheed kawai kika yi da haihuwarsa amma
ni na masa abinda ya fi wannan, irin wahalar da nayi da shi ba sai dai Allah ya
saka min ya biya ni ba, kuma shima Mujaheed din xai shigo ya sameni, idan bai ma yi
hankali ba ma sai ince na bar sa da Allah..." tsayawa Umma tayi tana kallonta bacin
rai karara fuskarta, tuni su Hajiya Saude suka fice a parlon, Ummi da su Maimoon
suka bi bayanta, Inna ta juya tana kallon Umma tace "Ki fita don Allah xan goge
daudar da ku ka shigo min da shi Rukayya" juyawa Umma tayi ta fice, Tsaye ta tadda
kawayenta suna jiranta, Hajiya Saude tace "Amma gaskiya Hajiya Rukayya kina fama,
yanxu haka kike xaune da wannan bala'eyyiyar tsohuwar nan har yau? Har yanxu kin
rasa yanda xa ayi da ita ne?" Umma ta sauke wani ajiyar xuciya tace "Ku bari kawai,
yanxu ina tanka ta abinda xata tsara ma d'an ta daban, shi kuma duk hakurinsa kika
kuskura kika taba masa mahaifiya to babu xaman lafiya ranan, shi sa nake mata
shiru" Hajiya Balaraba tace "Ke ma dai wllh, toh kin kasa yin komai a kanta ne?"
Umma tace "So nawa kuma, sai dai Allah ya kyauta kawai, Amma wannan matar da ku ka
gani ku kyaleta haka kawai" Hajiya Saude tace "A'a baki dai yi abinda ya dace bane,
nima fa haka uwar mijina take a da amma ba yanxu ba kuma wllh, duk da nata bai kai
na tsohuwar nan ba ma, Amma wllh ynxu sai labari, gaba daya gidan sai yanda nace
ake yi, ina xan iya wahala??" Umma tace "Toh mu je ciki sai inji ya xa muyi, wllh
na gaji, ita ce babban matsalata a gidan nan" Hajiya Balaraba tace "Toh kayan da ta
hana fitowa da su fa?" Umma tace "Kayan xa su dawo hannuna in sha Allah, Mujaheed
ne kadai ya isa ya fiddo da kayan daga parlon nan ko ubansa bai isa ba, kuma shi
xan sa bari dai ya dawo" Hajiya Saude tace "Toh yaushe xa a tafi kai gaisuwar ne?"
Umma tace "Uban cewa yyi sai kaninsa ya dawo Abuja, ae tuni na rufe bakinsa shi ma,
komai nace cewa yake tohh" Duk suka kwashe da dariya suka shiga cikin gidan. Da
magrib Imaan taje kai ma Inna abinci ta dinga kallon akwatunan da Inna ta jera a
parlonta gwanin ban sha'awa, Inna ta shafe addu'an da take tace "In fiddo maki
sabuwar wayar taki ne yanxu" Imaan tace "Inna wannan akwatunan fa?" Inna ta tabe
baki tace "Daxu wannan mata Rukayya suka shigo da su wai ashe har xa a kai ma
Mujaheed lefe bani da labari, Ina nan xaune kamar fanko" Imaan ta xaro ido tace
"Aure xai yi Inna?" Inna tace "Ai shine nake jira Ahmadu ya dawo mu ji idan bola
aka maida ni a gidan nan ban sani ba" Imaan da har sannan ke kallon akwatunan da
surprise tace "Waow wllh sun yi kyau sosai, yanxu gidansu Aunty farida xa a kai
kenan" Inna tace "Toh wacece dama banda ita, duk da dai iyayenta yaku bayi ne
yarinyar na da hankali kuma ban jin xata gaji da ni idan na koma gidan Mujaheed da
xama, lafiya xa mu xauna da yarinyar, ke kuma duk sati sai ki dinga xuwa kafin lkcn
naki da bulasawa yayi" Imaan ta fara dariya ta xauna Inna tace "Toh bude mu ga
tsiyar da suka xuba mata" Imaan na murmushi ta dinga sauko da akwatunan, sannan ta
bude daya daga manyan ciki, xannuwa ne tsadaddu kwance a ciki, Imaan ta dinga fiddo
su tana ajiyewa Inna na dauka tana duba kasan xannuwan don ganin ko babba ne ko
karami, can ta tabe baki tace "Kin san Rukayya akwai shegen karya, ko sata xata iya
sa Mujaheed yyi don tayi fafa, Toh xannuwa dai gasu duk masu tsada sai a xo a fidda
min nawa da na takwarata a ciki" Imaan dai bata ce komai ba sai murmushi kawai
take, ta bude wani akwatun, ta shiga fiddo laces masu suna lace, Inna ta rike ha6a
tace "Ehh lallai Rukayya makaryaciya ce, wnn ai sai ta talauta min jika, Toh wannan
ma sai a fidda min daya inyi doguwar riga, idan kyalle ya rage in baki a maki joni"
Imaan dai bata ce komai ba ta bude akwatuna mai dauke da jallabiyoyi tsadaddu, Inna
tace "Ki xabi wanda ya maki a ciki...." Imaan ta xaro ido tace "Innaa?" Inna ta
hade rai tace "Toh sai su fidda min in baki" Akwatin dake dauke da takalma da jaka
Inna ta bude, ta fiddo wani takalmi mai kyau sosai tana kallon imaan tace "Gwada
wannan mu ga" imaan ta wani xaro ido a fusace Inna tace "Don Allah ki gwada" mikewa
Imaan tayi xata sa takalmin aka bude kofar parlon Mujaheed ya shigo da sallama.

Afuwan it's short, gobe da safe xan yi update in sha Allah, I was kinda busy gaba
daya yau ne. Tnxx.

Imaan isn't free, it's 300 via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah.

33.....

Kallonsu Mujaheed ya dinga yi, Imaan ta sunkuyar da kanta ta ki sa takalmin xata


xauna, a fusace Inna tace "Ji walakanci don Allah, ba cewa nayi ki gwada ba?" Imaan
ta hade rai tace "Toh nawa ne da xan gwada?" Inna tace "Oh oh Allah, yau naga
fitina, to Ina ruwana da ko na waye, ni dai ba kawai in cire ma takwarata ba tunda
ni baxan iya sa wa ba?? Ki gwada don Allah" Imaan dai bata ce mata komai ba ta
xauna, Inna ta ajiye takalmin gefenta tana kallon Mujaheed dake tsaye tace "Toh da
kaki gaya min xaka yi aure Mujaheed sai aka yi yaya? Sai aka dinga yagan naman
jikina? Toh baxa dai a taba canxa ma tuwo suna ba, bauta dai na riga na gama maka
sai dai Allah ya saka min da alkhairi, Amma kar dai ka manta akwai ranan sakamako"
Mujaheed bai ce mata komai ba ya xauna kan kujera ya jinginar da kansa da kujerar a
hankali yace "Akwai ruwan xafi?" Inna tace "Wanda Rukayya ta hado tare da akwatuna
ta kawo min ba?" Mikewa Imaan tayi tace "Sai da safe Inna" Inna ta kalleta da sauri
tace "Sai da safe bamu gama kallon kayan ba?" Imaan bata ce mata komai ba ta nufi
kofa, Mujaheed ya bi ta da kallon gefen ido har ta fita sannan ya mike ya bi
bayanta, Inna tayi tagumi tace "Naga abinda ya isheni ni patuu, wannan d'a na
Ahmadu dai fitinanne ne, Ina lura da yarinyar nan gaba daya ta fita harkan ka a
gidan nan, da ta ganka xata yi ta kanta ta bar wajen, gaba daya ta ma mayar da kai
dodo, Ina kuma lura hakan na damunka ainun sbda baka samu damar dinga cutarta ba,
to meye kuma xaka wani bi bayanta bayan bata kula ka ba, Ni dai gwara ma ayi auren
nan ka kama gabanka jikata ta huta nima in huta da maganar ka haka, wllh ka cika
fitina ko don maman Rukayya ka sha oho, tunda ita ma dai fitinanniyar ce" Juyawa
Imaan tayi jin tafiya a bayanta, sosai gabanta ya fadi ganin shi ke bin ta, sai dai
bata gudu ba sai kara saurin ta da tayi, ji tayi ya juyo ta har sai da ta kusa
fadawa kansa ta fixge kanta gabanta na faduwa, a fusace tace "Meye haka yaya?"
Kallonta ya tsaya yyi da wani expression, kamar xata yi kuka tace "Ni ka sakeni"
Calmly yace "Me yasa kike gudu idan kin gan ni?" Kin cewa komai tayi, taji gaba
daya she is very uncomfortable unlike before da bata ki ma ta fada jikinsa ba ta
fara masa shagwaba, Yana kallonta yace "Imaan!" Kasa kallonsa tayi, ya dago kanta
yana kallon manyan idanuwanta, turo baki tayi, and he couldn't stop looking at her,
haka kawai yaji ya samu relieve din abubuwan da dama da ke damunsa, Yace "Answer my
question now, me yasa kike gudu idan kin gani" sauke idonta tayi kasa calmly tace
"Nothing..." jin shiru bai ce komai ba bayan few seconds ta daga kai ta kallesa
taga kallonta yake, sauke idonsa yyi cikin cool voice dinsa yace "Saboda na amshi
wayar ki?" Ta kallesa kafin tace komai ya ciro wayar a aljihu yana mika mata yace
"Take..." bata san lkcn da tayi murmushi ba ta langwabar da kai tace "Ae daddy ya
ce xai siya min wani soon" ya daure fuska yace "Take it now..." ta make kafada tace
"Ni bana so kuma" yace "Take before I knock you" kamar xata yi kuka ta amsa yana
kallonta yace "Shi kenan?" Tace "Ehh" wani boyayyen ajiyar xuciya ya sauke, ta d'an
yi jim, sai kuma tace "Aunty Farida xa a kai ma kaya?" Kasa cewa komai yyi ya
saketa ya juya ya koma part din Inna, ta bi sa da kallo kafin ta juya ta wuce part
dinsu tana kallon wayarta. Mujaheed na komawa part din Inna ya tarar tana ta fiddo
kayan akwatuna, ya xauna yana kallonta yace "Nima fa ban san an fara hada kayan
lefen ba shi yasa ban gaya maki ba, sai daxu Umma ke nuna min" Inna tace "Ni dai ba
ruwana, ku dinga jin tsoron Allah, don an gaya min ai ba gafara aka min ba...."
Wani jallabiya mai kyau da tsada ta daga tana nuna masa tace "Wannan ai xai ma
takwarata koh?" Kallonta ya dinga yi, jin yyi shiru ta ajiye gefe ta maida sauran
ta rufe jakar, ta nuna masa takalmin da ta ba Imaan ta gwada tace "Wannan ma ai dai
dai ita ne koh?" Nan ma dai bai ce komai ba ta ajiye gefenta, body spray biyu ta
dauka ta ajiye gefenta tace "Sai ta dau daya ta bar min daya" murmushi Mujaheed yyi
bai dai ce komai ba, Inna ta bude akwatin jewelries, ta dinga kallon dankunnaye da
sarakuna masu kyau, kala biyu ta cire tana kallonsa tace "Wanne ya fi kyau cikin wa
enannan?" Shi dai bai ce mata komai ba, ta ajiye biyun a gefenta tace "Sae ta xabi
daya a mayar masu daya" bude pack din jan baki tayi ta cire uku tace "Duk da dai ba
shafawa take ba sai ta ba Maimoon daya ta rike biyu" Kaf kayan sai da Inna ta bi ta
cire daddaya ta ajiye ma Imaan sannan ta rufe jakunkunan ta jera su yanda suke, ta
kwaso kayan ta xube su gaban Mujaheed tana kallonsa tace "Ko ban kyauta ba
Mujaheed?" shi dai bai ce komai ba ta kwashi kayan ta kai daki ta fito tace "Toh ai
faridan ma ya kamata ta xo ta gaisheni kafin a kai kayan, kwana biyu shiru bata xo
ba" a hankali Mujaheed yace "Ba Farida xa a kai ma kayan ba..." Inna ta gwalo ido
tace "Wa xa a kai ma?" Yace "Wata ce daban" Inna ta xauna kan kujera ta saki salati
tana tafe hannu tace "Wayyoo.. Amma dai kai shahararren mayaudari ne Mujaheed,
yanxu dama yaudarar yar mutane ka dinga yi ba aurenta xaka yi ba? Kasa yarinya ta
kashe d'an kudinta ta siyo min turare duk da ba mai tsada bane, Mujaheed anya kana
son wanyewa da duniya lafiya kuwa? Ina laifin yarinyar, kyakkyawa ce fa doguwa"
Mujaheed dai kallon kasa kawai yake bai ce mata komai ba, ganin ynda ta dage tana
kiransa da mayaudari ya dago ya kalleta yace "Umma ce bata son aurena da ita, shine
ta hada ni da yar kawarta..." Inna ta xaro tace "Auzubillahi, yanxu Rukayya ce ta
hanaka aurenta? Toh kuwa akwatunan nn babu inda xa su daga parlon nan sai gidansu
Farida, yarinya mai hankali da natsuwa, tun da naga ynda take ji da Imaan take
sonta naji nima ina sonta" Da sauri Mujaheed yace "A'a ita ma fa iyayenta sun riga
da sun mata miji har an sa rana" Inna ta saki baki tana kallonsa, can tace "Toh
wacece wannan kuma xa ka kwaso mana?" Ya d'an yi murmushin karfin hali yace "Idan
anyi auren xaki ganta" Inna tace "Sai ka kawota ai ta gaisheni ba ruwana, Amma dai
kun yaudara juna da farida tunda gashi ita ma har an mata miji kace, ohh mutane dai
tsoron Allah yayi karanci a xukatansu, yanda ka taso gabana Mujaheed bai ci ace
baka da tsoron Allah a xuciyarka ba, Toh ko da yake ai Rukayya ce ta haifeka,
Ahmadu da na haifa ai gashi yana tsoron Allah, haka ma Bukar, duk basa yin abinda
Allah ke fushi da, banda haka kayi ta xuwa gun yarinya kuna tadi ashe ba aurenta
xaka yi ba??" Shi dai Mujaheed kallonta kawai yake, bude kofa aka yi Abba ya shigo,
Inna ta tsuke fuska, Mujaheed kadai ya amsa sallamansa, Abba ya xauna yana kallonta
yace "Ina yini" tace "Toh ni da aka ki gaya min xa a kai ma Mujaheed lefe sai aka
yi yaya??" Abba ya girgixa kai yace "Kiyi hakuri, ni ma ba a gaya min da wuri ba
Inna" Inna tace "Kai dai ka ajiye bala'i a gida kawai kuna xaune, banda haka ya xa
ayi d'an ka a boye maka xa a hada masa lefe?" Mikewa Mujaheed yyi yana kallonta
yace "Sai da safe" tace "Tou yaushe xa a kawo min yarinyar?" Yace "Ehh xa a kawota
in sha Allah" daga haka yayi ma Abba sallama ya fita. Washegari Thursday Imaan na
dawowa schl bayan ta yi wanka ta ci abinci ta shirya ta tafi part din Inna, Inna
dake bakin pampo ta biyota ciki tace "Duk na cire maki kayan na boye maki a sif"
Imaan ta xaro ido tace "Ni dai ba ruwana Inna" wani kallo Inna ta mata ta xauna kan
kujera tace "Toh ni da ruwana, sai in ga wanda xai ce min don me" Imaan ta tabe
baki ta xauna, inna tace "Daxu Bulasawa ya kirani muka gaisa, ni dai tunda uwata ta
haifeni ban taba ganin yaro mai hankali da kirki irin yaron nan ba..." Imaan ta dai
yi murmushi bata ce komai ba, Inna tace "Bayan mun gama waya ni dai nace masa iron
dina ya lalace" Imaan ta xaro ido tace "Kika ce masa haka Inna?" Inna tace "Toh
baxan ce ba, tun yaushe nake bin Bukar da Ahmadu su siya min sai su ce sun mance,
dama wannan yaron isuhu kadai ne xan ce ma abu ya min nan take, shi Mujaheed ban ma
sa shi a layi, ko ya siyo sai ya kai ma wancan katuwar matar, to wai ni isuhu na
gidan nan ma kuwa?" Imaan ta bude hannu alamar bata sani ba, Inna tace "Ikon Allah
ni toh bai xo ya ce min xai yi tafiya ba... Kai bari dai inje bangaren nasu inji
lafiya, bai taba min irin haka ba da ma dai Mujaheed ne ni baxan damu ba" Inna ta
saka Hijabi da ta dauko tace "Tashi ki rakani, ba lafiya yau kusan kwana goma ban
ga isuhu ba, to ko bai da lafiya ne" Imaan ta mike suka fita parlon, Inna ta rufe
kofar ta da makulli Imaan tace "Inna to meye na sa makulli" Inna tace "Baxan sa
makulli ba? Ko datti ya shiga parlon ba a cuce ni, ko Kandangare ya ji shiru yana
iya shiga in shiga uku" Imaan tayi gaba Inna ta bi bayanta tana cewa "Don Allah ki
dinga cin abinci mai yawa Imaan, kinsan fa Bulasawa mai mutane ne, haka xa a ga
amarya kamar tsinken tsire a sa mu a bakin duniya, ni dai ki rufa mana asiri" imaan
dai bata tanka ta ba har suka iso part dinsu Maimoon, Inna ta shiga parlor tana
kallon Ummi tace "Ke Isuhu na nan?" Bata jira cewarta ba ta wuce sama tana kallon
stairs din palon tace "Matan Ahmadu dai kazamai ne, dubi fa yau basu goge nan ba
ina ga" dakin Anty ta bude Aunty ta mike ganinta tace "Sannu da xuwa Inna" inna
tace "Kwana biyu ban ga isuhu ba ko ke kika hanasa xuwa inda nake" Aunty tace "Ni
na isa Inna, ban ma san bai je ba ai, yanxu dai baya nan" Inna tace "Toh yana
dawowa kice ya xo ina nemansa" Aunty tace "Toh" Imaan ta gaida Aunty, Aunty ta amsa
da fara'a, Umma ta leko ganin Inna ta koma ciki da sauri ta rufe kofarta, inna ta
juyo tace "Toh ita kuma mai hada lefe ana ciki kenan, Toh dai baxan shiga ba" daga
haka ta fara sauka stairs din Imaan ta bi bayanta. Bayan magrib Imaan na part din
Inna Mujaheed ya shigo, xaunawa yyi ya gaida Inna da ke cin abinci tace "Mujaheed
ni fa ban ga isuhu ba har yanxu, ban san me ya faru ba" Mujaheed na kallon boxes da
ta jera yace "Inna xa a mayar da akwatunan can gida" Inna ta ajiye cokalin hannunta
tace "A kan wani dalili?" Yace "Ai ba a gama xuba kaya ba" Inna tace "Toh sai a
dinga xuwa nan ana xuba su, in dai kaga an fitar da akwatunan nan daga parlona to
gidan amaryar xa mu tafi kai wa, ai ba wani ya min wahala da kai ba, ko Ahmadu da
na haifa ban masa wahala yanda na maka ba, Rukayya dai ta shiga hankalinta a gidan
nan ta daina shiga hurumin da ba nata ba" Bai kuma cewa komai ba, ya kalli Imaan
dake xaune tana kallo, ta gefen ido ta ga yana kallonta ta mike tace "Sai da safe
Inna" daga haka ta fita parlon, Bai dade xaune parlon Inna ba ya mike ya fita, yana
isa part dinsu Imaan ya shiga balcony ya danna bell sannan ya bude kofar, Ammi dake
xaune parlor ta dinga kallonsa har ya shigo, kasa kallonta yayi ya dukar da kansa
ya xauna saman kujera yace "Ina yini Ammi" Ammi tace "Lafiya lau ya aiki" yace
"Alhmdllh" tace "To maa sha Allah" kasa cewa komai yyi, can yana shafa kansa yace
"Ammi dama..." Sai kuma bai ce komai ba, Ammi tace "Dama me?" Yace "Ina son Imaan
xata rakani ne" Da mamaki Ammi tace "Ta raka ka ina?"

Yanxu xan dinga update twice sbda xan rage tsayin rubutun, sai kuma da daddare in
sha Allah.

*The book Imaan isn't free, you read for free ur cup of coffee...*

It's 300 via


Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah, then you show ur evidence of payment through my
WhatsApp digit 07087865788 to be included in d payment group.
34......

Mujaheed ya kalleta yace "Ina son xan je gidansu Farida ne" Ammi tace "Wace
faridar? Wace ku ka yaudara ko wata daban?" Shiru yyi bai ce komai ba, Ammi ta tabe
baki ta maida dubanta kan TV, yace "Ni ban yaudare ta ba Ammi, kila hakan Allah ya
tsara we are not destined to be together" Ammi tace "Toh yayi kyau, haka Allah ya
tsara" Bai ce komai ba, can ta kallesa tace "Toh me xaka je ka mata?" Yace "Ina son
xuwa in bata hakuri ne, idan ta gan ni da Imaan she might listen to me, bana son
tayi tunanin yaudararta nayi" Ammi tace "Toh Allah ya kyauta, amma yanxu dare yyi
sai ka bari gobe" yace "Gobe da safe xata wuce kano" Ammi ta girgixa kai, tace "Toh
ba sai ku tafi har da Maimoon ba" yace "Eh xa mu je tare" Ammi tace "To ka turo
Maimoon din xa su fito tare" yace "Toh nagode" daga haka ya mike ya mata sallama ya
fita parlon, Ammi ta mike ta shiga dakin Imaan xaune ta sameta tana karatu, Ammi
tace "Ki shirya ke da Maimoon xa ku raka Mujaheed wajen Farida" Imaan ta xaro ido
tace "Yaya kuma? A'a ni Ammi baxan je ba" Ammi ta dinga kallonta sannan tace "Me
yasa?" Girgixa kai tayi tace "A'a ni bacci nake ji" Ammi tace "Me ya hada ku da
Mujaheed din?" Da sauri ta kalli Ammi sai kuma ta dauke Kai tace "Ba komai fa Ammi"
Ammi tace "Toh tashi ki rakasu ku dawo" daga haka Ammi ta fita dakin, da kyar Imaan
ta mike har ranta bata son bin Mujaheed, can dai ta sa Hijab dinta har kasa ta
fito, dai dai nan Maimoon ma ta shigo parlon, Ammi na kallon Imaan tace "You pray
before leaving, and ku kula" A hankali Imaan tace "Toh" daga haka suka fita tare da
Maimoon bayan ta gaida Ammi, a waje suka samesa yana jiransu cikin mota, Maimoon ta
shiga back seat, Imaan ta hade rai ta shiga ita ma, Maimoon tace "Ki tafi gaba
mana" Imaan tayi mata banxa ta rufe motar, Mujaheed yace "Wata ta dawo gaba, I am
a driver to none of you" Maimoon ta turo baki ta bude motarta ta fita ta koma gaba,
tada motar yyi suka dau hanyar titi, lkci lkci yake kallon Imaan dake kallon waje,
gidan yayar Farida dake unguwar sanusi suka tafi, Mujaheed yyi parking kofar gidan
ya kashe motar, yace "You two should go in, ku ce mata I am outside, she isn't
picking her cals" Imaan ta bude motar ta fita, Maimoon ma ta fita suka shiga gidan
a tare, A parlor suka tadda yayarta da yaranta uku, tana kallonsu ta amsa
sallamarsu, Imaan ta xauna ta gaisheta Maimoon ma ta gaisheta duk ta amsa amma da
alamar bata gane su ba ma, Maimoon tace "Aunty Farida fa?" Yayar tace "Tana daki"
karamin yaronta ta aika ya kirata a daki, sai ga ta ta fito, tsaye tayi tana
kallonsu, can tayi murmushi tace "Sannu ku da xuwa" Imaan tace "Ina yini Aunty
farida" Farida ta xauna tace "Lafiya lau Imaan ya Ammi fa" Maimoon ma ta gaisheta
ta amsa tace "Daga Ina ku ke haka da daren nan?" Imaan tace "Daga gida mana"
Murmushin fuskarta yayi fading tace "Toh a xubo maku abinci" Imaan tace "A'a mun ci
abinci, Aunty farida Ammi ce ta aiko ni" Farida tace "Ayya, toh ina jin ki" Imaan
tayi murmushi tace "Ko xa mu je waje?" Farida ta mayar mata da murmushin sannan ta
kalli yayarta tace "Anty kanin Mujaheed ne" lkci daya yayar ta hade rai ta ci gaba
da kallonta, Imaan ta mike tayi ma yayar sallama Maimoon ma haka sannan suka fita,
Farida ta mike ta bi bayansu, mamaki ya kamata ganin sun fita wajen gate don ta
xaton cikin compound din Imaan xata bata sakon Ammi, ta dai bi bayansu har waje,
sosai gabanta ya fadi ta tsaya tana kallon Mujaheed dake tsaye jikin mota ya
rungume hannunsa, ta sunkuyar da kai ya karasa har inda take, Juyawa tayi xata koma
ciki ya kamo hannunta a sanyaye yace "Pls listen to me Farida" kasa kallonsa tayi
hawaye ya kawo idonta, sosai jikin Imaan yyi sanyi, Maimoon ta bude mota ta shiga
don ita ma ta bata tausayi, cike da karfin hali Mujaheed yace "I neva meant to
break ur heart Farida, even for once, but you know Allah plans best, may be we were
neva destined to be together, ki yafe min pls, Umma ta bata son aurenmu and I can't
disobey her" Hawaye na xuba idonta tace "Allah yasa hakan yafi alkhairi, and I am
wishing a happy married life in advance" a sanyaye yace "Forgive me plss Farida" ta
gyada masa kai da kyar tace "I have done that in sha Allah" Yace "Tun daga farkon
relationship dinmu 4 years ago har xuwa yanxu idan na 6ata maki kiyi hakuri ki yafe
min" tace "Baka min komai ba kuma na yafe maka ni ma ka yafe min, Allah kuma ya
saka maka da alkhairi abubuwan da ka min from the beginning har xuwa yanxu, thank
much Muhd, Allah kuma ya baka Ikon ci gaba da yi ma mahaifiyar ka biyayya, ku rabu
lafiya" Ya sauke idonsa kasa yace "in sha Allah xa mu dinga xumunci..." xame
hannunta tayi ta juya ta nufi gate dinsu, a hankali yace "Idan Allah ya kaddara you
will still be my wife some days, I will be very glad in hada ki da kanwarki...."
Farida bata juya ba har ta shiga ta rufe gate din, Juyawa Mujaheed yyi kamar mai
tausayin kasa ya xaga ya bude driver seat ya shiga,Tada motar yyi yana kallon Imaan
da ta turo baki bayan ta goge hawayen idonta, Bai ce komai ba ya bar layin da
motar, har suka isa gida babu wanda yace komai cikin motar, the journey was very
silent, yyi parking a kofar gida Maimoon ta bude motar ta fita, Imaan ma ta fita ta
shiga gate da sauri, Parlor ta tadda Ammi, ganin mood dinta Ammi tace "Ya aka yi"
xaunawa tayi hawaye ya kawo idonta tace "Ammi ta ban tausayi, me yasa Yaya xai mata
haka, he betrayed her" Ammi ta tabe baki bata ce komai ba, tace "Har kuka fa sai da
tayi" Ammi tace "Toh Allah ya bata wanda ya fi sa, wani hanin ga Allah bai wa ne,
bata san ma wani gata Allah ya mata da ya rabasu ba, don Ina tausaya mata idan
Mujaheed ya aureta barin yanda uwarsa bata sonta" Imaan tace "Toh Saboda me?" Wani
murmushi Ammi tayi tace "Ko makiyina baxan ba shawara ya ba ma Mujaheed 'yar sa ba,
Kinga Hajiya Rukayya ta wuce tunanin kowa, ni ba miji daya muke aure ba amma irin
xaman da muka yi ba shi da banbanci da muna auren miji daya, na sha wahalar ta ne,
sam bata san da annabi ya kafu ba" Imaan dai tayi shiru, Ammi tace "Don haka gwara
dai ta aura ma d'an nata yar kawarta, sun fi kusa kuma sun san kansu" Washegari
Juma'ah Imaan na dawowa schl ko uniform bata cire ba sai ga inna ta sha atamfarta
mai tsada an yafa mayafi, Ammi tace "Sannu da xuwa Inna" Inna tace "Yauwa takwara
ta dawo makaranta kuwa?" Ammi tace "Ehh yanxu ta shigo" inna tace "Toh da kyau,
dama so nake ta rakani gidan ta rasulu kwana biyu shiru ban ganta ba" Ammi ta kwalo
ma Imaan kira, Imaan ta fito, Ammi tace "Xa ki raka Inna anguwa" Imaan ta hade rai
tace "Ban ma yi wanka ba kuma ban ci abinci ba, gashi kai na ma ciwo yake min" Inna
tace "Kanki na ciwo kuma? Toh yi xaman ki bari in je in samu Maimoon ko Ummi su
rakani, ya xan yi dake idan kin fadi a titi, wa gareni titin?" Daga haka ta juya ta
fita, Imaan ta koma dakinta. Imaan na wanke wanke kitchen da yamma Ammi ta kwalo
mata kira fito da sauri, Ammi tace "Kiran ki ake a waya" daukar wayar tayi ganin
Sadeeq ne ta daga ta bar parlon, gaisawa suka yi yace "Pls dear ki d'an fito ki
amshi sakon Inna am outside" Imaan tace "Sako kuma?" Yace "Ehh ko kina wani abu
ne?" Tace "A'a ka dai shigo ka kai mata ai ni bn san da sakon ba" yayi murmushi
yace "Ai anjima da daddare xan xo sai muje part din nata tare, yanxu sauri nake Mum
dita ta aikeni xan kai mata sako" Imaan tace "Toh sakon meye?" Yace "Ke dai fito ki
gani" a hankali tace "Toh" Daga haka ya katse wayar, Ammi dake jin wayar da take
tace "Sakon meye?" Imaan tace "Ko ba Inna bace tace ya siya mata iron" tagumi Ammi
tayi tana salati, can tace "Yanxu Inna mutunci take nema mana gun yaron nan ko
tsiya, sam ban ji dadin sanin yaron nan da tayi ba, me kuma xata yi da iron idan ba
fitina ba anjima ta hada kayan ta bada a goge mata gun masu laundry, wannan wani
irin kaskanci ne fisabilillah, to ita Ina nata iron din?" Imaan tace "Daga ranan
Ummi ta ce ya mata shocking shikenan Inna ta saka a bola" Ammi tayi salati tace
"Wannan tsohuwa dai Allah ya raba mu da ita lafiya, ynxu abinda nake so da ke idan
ta dawo anjima ki dau wayarta kiyi blocking number sa sannan kiyi deleting don ba
mutunci take siya maki a gun sa ba, snn ki nuna masa baki son ma yana xuwa
bangarenta kwata kwata" a hankali Imaan tace "Toh" Hijab kawai ta sa ta fita kofar
gida, waya na kare kunnensa ya kafeta da ido har ta iso inda yake, katse wayar yyi
yace "How are you doing dear" tace "Alhmdllh ya aiki?" Yace "Fine Alhmdllh" Bude
motar yyi ya fiddo wani leda ya mika mata yace "Gashi ki ba Grandma" Shiru tayi
bata ce komai ba, can ta amsa tace "Toh angode" wani ledan ya fiddo ya mika mata
yace "This is for you" Ta girgixa kai tace "A'a nagode" a hankali yace "Bana son
Ina baki abu kina ce min A'a dear" tace "Ni dai nagode" kallonta ya tsaya yi, dai
dai nan mota yayi parking bayan nasa, Bude motar aka yi Umma ta fito, kallonsa ta
dinga yi sannan ta kalli Imaan ta kara kallonsa ta kalli Imaan, Sadeeq ya gaisheta
with respect, Sai da ya kara gaisheta ta amsa da sauri tace "Lafiya lau" Tana isa
gate ta sake Juyawa ta kallesa saura kiris ta fada bakin gate din tayi maxa ta
shige ciki, Sadeeq da ya bi ta da ido ya kalli Imaan dake wasa da fingers dinta
yace "Who is she?" Imaan ta kallesa ta d'an yi murmushi tace "Mum din Yaya" Sadeeq
yace "Ohk, but why didn't you greet her" Shiru tayi kamar baxata ce komai ba, can a
hankali tace "Xan gaisheta ai idan na shiga" yace "Noo, that's not a point..." Ta
d'an yi murmushi kawai, yace "Though I don't know why is that, and I am not suppose
to intrude into family issue but promise me xaki dinga gaisheta daga yau, ita din
ai babbace" Imaan ta kallesa, yace "Yea promise me" sunkuyar da kanta tayi a
hankali tace "Toh in sha Allah" yayi cute smile dinsa yace "Maa sha Allah" kan wani
farin kujerar roba ya ajiye ledan da ya bata ta ki ta amsa yace "Shikenan sai mu yi
sadaka da shi tunda baki so, I am leaving now, mum dita na jirana" Bai jira cewarta
ba ya shiga motarsa ya tada, d'an murmushi tayi cikin sanyayen murya tace "Toh
nagode" ya kashe
mata ido daya ya ja motar ya bar layin, a hankali ta kai hannu ta dau ledan ta
wuce ciki. Sai kusan Isha ta tafi kai ma Inna abincinta bayan Ammi ta kara maimaita
mata tayi blocking number Sadeeq a wayar Innan sannan tayi deleting, tana isa
parlon ta ajiye abincin da ledan iron din ta gaida Inna dake goge gogen kayan
kallo, Inna tace "Allah dai ya bar ni da ta rasulu kawai, Ni fa ta fiye min wasu
daga yan uwa da basu da kirki ynxu, har maganar ki da yaron nan Sadeeq sae da na
mata yanxu kawai kudi xan bada a kauda idon makiya a lamarin, gobe ma xan ba
Mujaheed kudin ya kai mata, wa xai xauna yanxu?? Kowa ya tashi tsaye ya nemi kariya
kawai" Imaan bata dai ce mata komai ba ta xauna ta dau wayarta dake kan kujera tace
"Inna ga iron dinki an kawo daxu" Inna tace "Haba, Kai Allah masa albarka, to da
Ahmadu ne sai dai yace min ya manta, kinga alamar wnn yasan darajan babba ko to ni
dai ba ruwana, idan xaki rikesa hannu bibbiyu ki rikesa mijin aurena wllh, Allah
dai ya saka masa da alkhairi, ke kuma na gaji da ajiyar wayar da ya kawo maki idan
baxa kiyi amfani da shi ba a tafi kasuwa ki siyar kudin xai yi maki amfani" bata
jira cewar Imaan ba ta shiga ciki, har Imaan ta gama blocking da deleting lambar
Inna bata fito ba, tana kokarin tashi tace mata xata tafi, Inna ta fito duk ta hada
xufa a gigice tace "La ila ha illallahu Muhammadur rasulillahi sallallahu alaihi
wassalam, Innalillahi wa Inna ilaihi raji'una, laaa haula wala kuwata illa billahil
Aliyul azeem... To barawo ya sace wayar" Imaan ta mike tana kallonta da mamaki,
Inna ta fashe da matsanancin kuka tace "Wlh a karkashin kwalla na adana ledan wayar
yanxu ko sama ko kasa wani ya shigo ya sace ban san waye ba, na shiga uku na lalace
dukiyar mutane, Allah ka rufamin asiri" Mayafinta ta fixga ta fice daga parlon tana
rusa kuka, Imaan dai tayi still tana kallon kofar dakinta can ta bi bayanta, tuni
har Inna ta isa part din Abba, Imaan ta shiga nasu part din, Inna na shiga su
Maimoon na gaisheta cikin kuka tace "Ina Ahmaduna yake?" Mujaheed dake sakkowa
downstairs ya dinga kallonta da mamaki Aunty dake xaune parlor kuwa sai tambayarta
me ya faru take, Inna ta rushe da sabon kuka ta xaune kasa tace "Nashiga uku,
Ahmadun bai dawo bane?" Umma ta leko parlon daga kitchen bata dai fito gaba daya
ba, Mujaheed ya karaso yace "Wai me ya faru ne??" Cikin kuka tace "An sace wayar da
Bulasawa ya kawo ma Imaan a dakina cikin kwallaa...." Ta kunce ha6ar xaninta ta
rufe fuska ta dinga kuka tace "Yanxu wani kallo yarinyar nan imaan xata min, wayar
fa ance ya kai dubu dari biyar... Wayyo ni dai na shiga uku an goga min bakin
fenti" Umma sai xaro ido take daga kofar kitchen tana kallon Inna jin ta ambaci
Bulasawa, Aunty tayi tagumi tana kallon Inna, su Maimoon da Rahama kuwa banda
dariya babu abinda suke kasa kasa.

*imaan isn't free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah. Subscribe and read happily.

35....

Aunty tace "Daxu da kika fita baki kulle kofar bne Inna?" Inna na sharban kuka tace
"Wllh na kulle Amina sai dai idan sabon makulli aka yi aka bude kofar..." Da mamaki
Aunty tace "Ikon Allah, amma mu je dai a kara duba dakin Inna kila dai baki duba a
nutse bane" a fusace Inna tace "oh oh Allah, Wani dakin xa aje kuma bayan nace maki
duk na xaxxage kayan kwallan, wllh sacewa aka yi, kuma wannan barawon da ya san ni
ne, yasan me nake ciki a rayuwa" Aunty na kokarin danne dariyarta tace "Gaskiya
wannan abu da mamaki, anya ba Imaan din bace ta dauke kayanta kuwa??" Inna ta tsuke
fuska tace "Don Allah Amina ki rabu da ni kiyi ta kanki, idan baxa ki fadi alkhairi
ba kiyi hakuri ba don ni ba don Allah kiyi shiru, ta ina Imaan xata dauke waya bata
gaya min ba" Tuni Mujaheed ya koma dinning ya xauna ya bude warmer yana diban
abinci, Sallaman Abba yasa Inna ta mike tana matsar hawaye tace "Ahmadu yau an
shafa min bakin fenti a gidan nan, ban san wanda ya shiga ya sace wayar da Bulasawa
ya bani in ba Imaan ba, wayar tayi na miliyan Ahmadu, ka rufa min asiri mu tafi aje
a sake dubawa, da wani idon xan kalli Bulasawa idan yaji labarin waya ya bata a
wajena" Abba dake tsaye ya ma rasa abinda xai ce sai kallonta yake da mamaki, can
dai ya girgixa kai yace "Wayar ta miye yaron ya kawo da ba mu da labari??" Inna ta
wani hade rai tace "Ta imaan ce wayar ya kawo mata kyauta, kuma ta hannuna wayar ya
biyo, ko an daina ihisani ne a duniyar?" Abba yace "Amma da ya bada ai sai ta kawo
nan ta nuna min tunda shi Sadeeq bai nan, wannan bai kamata ba sam inna, a kan wani
dalili ma xai bata waya??" Inna tace "Kaga Ahmadu kayi hakuri kar a shashantar da
xancen bacewar waya mu tafi mu nemi waya duk inda ya shiga" Abba ya dinga kallonta,
a fusace tace "Ahmadu kana kallona, don Allah ka shiga gaba mu je, idan ma ya kama
a fiddo duk kayan cikin dakin sai a fiddo, yau dai xan ga batar nono a kirjin
Budurwa" Kofa Abba ya nufa ta bi bayansa fuska a tsuke, Aunty ta fita ita ma, su
Maimoon ma suka bi bayanta, Mujaheed dai cin abincin sa kawai yake a nutse, Umma da
ta makale a kitchen, tana jin sun fita ta fito da sauri, duk ta hada xufa tace
"Mujaheed, wani Bulasawan Inna ke nufi?" Mujaheed ya kalleta yana cin abincinsa a
hankali yace "Ni ma ban gane xancen da take ba gaskiya" Umma ta tafi sama sai gata
ta sauko da hijab xata tafi bangaren Inna, shi dai Mujaheed bin ta kawai yake da
kallo har ta fita, Tana isa part din ta shiga parlon ta ga su Maimoon na ta fito da
kaya daga cikin daki, Inna na tsaye daga gefe sai wurwurga ido take, Abba dai na
tsaye daga bakin kofa ya rungume hannu, Aunty kuma na can uwar dakan Inna, Inna ta
saki salati ta rushe da kuka tace "Kin ga ta kanki yau patuu, tunda uwata ta
haifeni ba a ta6a ban ajiya ya bace ba..." Umma ta shigo parlon cike da damuwa tace
"Wai har yanxu ba a ga wayar ba Inna?" Inna na goge hawaye tace "Wllh ba a gani ba
Rukayya, ranan Ina bakin pampo ina gurje daudar wajen sai ga yaron ya shigo...."
Umma tace "Wani yaro?" Inna tace "Bulasawa mana, waye bai san imaan da Bulasawa ba
kuma a gidan nan, ba dai Bulasawan da kansa ba, d'an cikinsa ne dai, wllh yana bani
wayar bayan ya fita kinga inda na ajiye wayar can" Umma ta kalli inda Inna ke nuna
mata, Inna ta fashe da wani sabon kuka tace "Ni dai yau xan ga batar nono a kirjin
budurwa ni Asabe" Umma dai ta kasa tsaye waje daya, Kai kana ganinta xaka ga tashin
hankalin da ya ki boyuwa karara a fuskarta, Dakin Inna ta shiga ta gama xagaye
xagayenta sannan ta fito tace "Kuma Inna babu kowa parlon San da aka baki wayar?"
Inna ta d'an yi shiru sannan da sauri tace "D'an ki ne Mujaheed kadai a parlon a
lkcn, Toh ga dankareren dankunnen zinari ma da ya bata ta bani ajiya bai bata ba,
duk da ranan ba kowa a parlon ta bani, waya dai Mujaheed na wajen lkcn" Inna ta
xaro ido ta dafe kirji tace "To ko dai sata Mujaheed ya fara a gidan nan ba a sani
ba??" Umma dai sai hada xufa take tana kallon inna, Inna ta kalli Abba tace "Anya
Ahmadu baxa a caji Mujaheed ba, wllh shine a parlon ranan, Ni dai na shiga uku na
lalace" Abba dai bai ce mata komai ba, Umma ta dake tace "Inna bari in kashe gas na
daura ruwan shayi, xan dawo yanxun nan, ae wannan babban magana ce" Inna tace "Yi
maxa kar ki ja wata fitinar ba a gama kashe wata ba" da sauri Umma ta fita, tana
komawa bangarensu bata ko kalli Mujaheed ba ta wuce sama jikinta na rawa. Washegari
har Ammi ta gama soye soye a kitchen shiru imaan bata fito ba, dakinta Ammi ta
shiga don ya ci ta fito ynxu ta gama shirin islamiyya, kwance Ammi ta ganta cikin
duvet, ta cire duvet din tana kallonta ta kai hannu jikinta, janye hannun tayi tana
kallonta tace "Imaan?" A hankali imaan ta bude idonta da ya rine tana kallon Ammi,
Ammi ta xauna gefen gadon da damuwa tace "What's wrong imaan?" Da kyar ta nuna ma
Ammi kanta murya can kasa tace "It's aching me" ta nuna ma Ammi kafafuwanta ma,
Ammi ta dinga kallonta cike da tausayi tace "Kin daina shan maganin ki ko
daughter!" Imaan ta girgixa mata kai kawai ta kasa cewa komai, mikewa Ammi tayi ta
wuce bathroom dinta ta hada mata ruwan wanka ta fito ta daga ta, ita ta taimaka
mata har xuwa bathroom din sannan ta fito, ta ciro mata kayan da xata saka sannan
ta fita, Imaan na fitowa wanka ta kwanta kan gado daure da towel ta rufe jikinta da
duvet, Ammi ta dawo dakin rike da cup din shayi da ledan bread ta ajiye kasa tana
kallonta tace "Toh tashi ki shirya sai kiyi breakfast ki sha magani" Ganin she is
shivering Ammi ta dauko cream dinta ta taimaka mata ta shafa sannan Imaan ta saka
kayan da Ammi ta fiddo mata, shayi kawai ta sha da drugs dinta sannan ta kwanta
Ammi ta fita da cup din. Aunty ce xaune parlon Abba bayan ta kawo masa breakfast,
ganin mood dinsa tace "Don Allah ka daina damuwa da abubuwan inna, kun fa fi kowa
sanin halinta, Bai kamata kuna sa abun a rai ba, kuma uwa ce fa" Abba ya girgixa
kai yace "Ni kadai baxan iya dinga nuna ma Inna abinda ya dace da wanda bai dace
ba, ya kamata ku ma ku dinga contributing...." Aunty ta sake baki tace "Mu a suwa
Alhaji, ku ma ya ku ka kare balle mu, ai sai ta kora mu gidajen iyayenmu..." Abba
yace "Wannan ba point bane, idan a nuna mata ta gyara ai da matsala babba, Dama ta
fi sauraran Sadeeq to shi baya nan, ni kuma inyi magana ta fara min kuka, wllh duk
abubuwa sun taru sun min yawa a kai" Aunty tace "Ai tana jin maganan Mujaheed ma"
Abba ya kalleta yace "Toh cewa tayi a tafi Police station Mujaheed ne ya dauke
waya, har da kukanta fa, Yanxu fisabilillahi maganan nan ya maki dadi?" Aunty ta
kasa danne dariyarta tace "Tsufan kenan ai Alhaji, a dinga yi mata uxuri don Allah,
Toh shi me Mujaheed din yace?" Abba ya girgixa kai yace "Ni ban ma gansa ba tun
jiyan, sai daxu da muka hadu masallaci, gaskiya Inna na daga min hankali da yawa
ban san yanda xan yi ba" Aunty tace "Toh Allah dai ya kyauta" Yusuf ne yyi sallama
bakin kofa Aunty ta amsa ya shigo parlon ya mika mata wayarta yace "You missed a
call" Abba na kallonsa yace "M.A fa?" Yusuf yace "Yana bedroom dinsa" Abba yace
"Kira min shi ku taho tare" Yusuf ya amsa da to sannan ya nufi kofa, hanya ya ba
Umma ta shigo parlon sannan ya fita, Daga Aunty har Abba suka dinga kallonta, duk
gaba daya a sanyaye take tace "Alhaji xan je gidan Mariya wai suma ta dinga yi jiya
basu yi bacci ba, yanxu haka suna asibiti tun asuba wai" Aunty tace "Subhanallahi,
Toh Allah ya bata lafiya ya yaye ma duk musulmi ciwo, in sha Allah xan shigo anjima
nima" da sauri Umma tace "A'a Hajiyar mu tace mu taho da ita zaria kawai, yanxu Ina
xuwa Zaria xa mu wuce da ita" Abba yace "Toh Allah ya bata lafiya, ya sa kaffara
ne" tana goge hawayen da ya cika idonta tace "Ameen" Abba yace "Da driver xa ku
tafi kenan?" Umma tace "A'a adaidaita xan hau xuwa asibitin daga can sai mu tafi a
motar mijinta" Abba yace "Toh Allah ya kiyaye hanya, do you need anything?" Tace
"Ehh a min transfer din abinda ya sauwaka" Abba yace "Alright" sallama tayi masu ta
fita parlon Aunty na mata Allah kiyaye hanya, bayan ta rufe kofa Aunty ta duba call
din da tayi miss taga Ammi ce ta kirata, dialing number din tayi yana fara ring
Ammi ta daga suka gaisa, Ammi tace "Dama tambaya xanyi ko driver na nan Hajiya..."
Aunty tace "Ehh toh bai dawo daga kai su Maimoon islamiyya ba..." Ammi tace "Toh
dama Imaan ce bata ji dadi ba xa mu je asibiti" Aunty tace "Subhanallahi tun
yaushe?" Ammi tace "Yau dai da ciwon nata ta tashi" Aunty tace "Toh bari in ma
Yusuf magana ko shi sai ya kai ku asibitin" daga haka ta katse wayar, Abba yace
"Mamana ce ba lafiya?" Aunty tace "Wllh kuwa, Wai ciwonta ne ya tashi" Abba ya d'an
yi shiru sannan yace "Bari Mujaheed ya shigo mu ji ko xa a kaita asibiti ne ko a
bata medication a gida" dai dai nan Mujaheed ya shigo tare da Yusuf, Abba ya mike
yace "Mu je ka duba Mamana wai bata ji dadi ba" Mujaheed ya d'an yi jim, sannan ya
bi bayan Abba suka fita parlon, Aunty na kallon Yusuf tace "Kai baxa ka je dubata
ba" Yace "Xan je anjima mum" Har bedroom din Imaan Abba da Mujaheed suka shiga Ammi
dai ta tsaya daga bakin kofar, bacci take suka sameta, Mujaheed ya duka kusa da ita
a hankali yana kallonta ya kai hannu forehead dinta, bude ido tayi ganinsa ta ja
duvet ta rufe kafarta da sauri. Abba ya karasa kusa da gadon yace "Sannu mamana, ya
jikin?" Da kyar tace "Da sauki Abba" Mujaheed na kallonta yace "Where are you
feeling pains?" Ba tare da ta kallesa ba ta nuna masa kafafuwanta da baya, yace
"Kin sha magani ne?" Kai ta gyada masa, Yace "Ina drugs din" ledan maganin dake
ajiye ta nuna masa ya dauka ya duba su sannan ya ajiye yana kallon Abba yace "Let
me get some injections da drugs" Abba yace "Ohk" daga haka ya nufi kofa Ammi ta
basa hanya ya fita. Abba na kallon imaan yace "Allah ya sauwake imaan" ta d'an yi
murmushi a hankali tace "Ameen" Abba ya juya ya nufi kofa yana kallon Ammi yace
"Allah ya bata lafiya" Ammi tace "Ameen thumma Ameen" yace "Amma kada a gaya ma
Inna" Ammi tace "In sha Allah" kofa ya nufa yace "Xan fita office, I will call
later" Ammi tace "Allah ya kai mu, Allah kuma ya tsare" yace "Ameen" sannan ya
fita parlon. Ammi ta karasa cikin dakin tana kallon imaan tace "In kara hada maki
shayin ne?" Da sauri ta girgixa kai, Ammi ta dinga kallonta sannan ta juya xata
fita, murya can kasa tace "Ammi don Allah ki shafa min maganin a kafa kafin Yaya ya
dawo ni bana son ya shafa min"

*Imaan isn't free....* it's 300 Via Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah
Then you show ur evidence of payment via 07087865788 to be included in the payment
group....

36......

Mujaheed na dawowa ya tadda Ammi xaune parlor, Ammi ta amsa sallamansa yace "Ta ci
abinci ai" Ammi tace "Ta sha shayi daxu" yace "Tana ciki har ynxu?" mikewa Ammi
tayi tace "Ehh tana ciki" bedroom din Imaan ta nufa, ya bi ta da kallo sannan ya bi
bayanta, Ammi ta cire duvet din jikinta xuwa kafanta tace "Imaan" tashi xaune imaan
tayi ganin Mujaheed ta daure fuska ta ja duvet din xuwa waist dinta, a hankali tace
"Ammi na ma fara jin sauki" Ammi ta kallesa tace "Magunguna ka siyo mata?" Mujaheed
ya girgixa kai yace "A'a injections ne, sai na shafa..." Ammi tace "Ta sha drugs a
bar injections din anjima" kallonta yake sannan yace "Amma na yanxu ne alluran..."
Imaan tace "Toh na ji sauki ai yaya" Bai kuma cewa komai ba sai kallonta da yyi ta
gefen ido babu yabo bbu fallasa, Ammi tace "Ina lotion din tube din?" Mika mata
ledan yayi ta amsa ta cire man xafi dake ciki, Mujaheed ya kara kallon Imaan da ta
ki kallonsa, Juyawa yayi ya nufi kofa kamar baxai ce komai ba bayan ya bude kofar
yace "Sai anjima" ba tare da Ammi ta juya ba tace "Allah ya kai mu" da kanta ta
shiga shafa mata man xafin a kafafuwanta da bayanta, Tana yarfe hannu tace "Toh
Ammi alluran fa, ni dai bana son Yaya ya min, Kuma har yanxu Ina jin joint pain
din" Ammi tace "Anjima Dr Habib xai xo..." Ammi na gama shafa mata ta fita dakin
imaan ta koma ta kwanta ta lumshe ido. Da yamma Imaan na xaune parlor pepper soup
din naman ragon da Aunty ta kawo mata na gabanta ta kasa ci don gaba daya bata da
appetite, har wani rama tayi kamar warce tayi sati ba lafiya, xuwa lkcn dai ta ji
sauki sai rashin kwarin jiki don Dr Habib ya xo ya mata injections din da Mujaheed
ya siyo daxu, Ammi ce ta fito parlon ta iso kusa da ita tace "Idan baxa ki ci ba ki
kai kitchen ki rufe Imaan, ai ba dole bane" Imaan bata ce komai ba ta amshi wayar
da Ammi ke mika mata, Sadeeq ne ke kira a wayar, ta kalli Ammi da ta juya xata koma
daki sannan ta daga wayar ta kai kunne hade da masa sallama murya can kasa, daga
daya bangaren ya amsa yace "Are you okay?" Ta gyada masa kai tace "Sure Ina yini?"
Yace "No, you sound sick ki gaya min baki da lafiya ne?" Cikin sanyin murya tace
"Ae na ji sauki" Yace "Subhanallah, me ya sameki?" Ta girgixa kai tace "Kawai
xaxxabi amma naji sauki sosai" ya d'an yi shiru sannan yace "Toh Allah ya kara
lafiya, anjima xan xo in sha Allah" tace "Toh Allah ya kai mu" yace "Ameen, I will
call you idan na iso" tace "Toh" katse wayar tayi ta ajiye tana shan pepper soup
din naman a hankali, Bude kofar parlorn aka yi Inna ta shigo ta tsaya tana kallonta
tace "Ikon Allah, yanxu don kaddara ta fada ma wayar ki sai ki kwanta ciwo imaan??
anya kuwa xa ki yi tawakalli irin nawa? Kinsan irin asaran da nayi a rayuwar nan
kuwa tun tasowata har ixuwa yanxu? To 6arin ciki hudu nayi a gidan mijina, na haifi
'yan biyu suka mutu rana daya, dakina ya ta6a konewa kurmus bbu abinda aka fitar da
sai mafici, kishiyata ta ta6a turo min yan fashi suka kwace min jakata a titi Allah
ya so bbu komai ciki sai naira daya, 'ya yana uku kacal a duniya, da ubanki, sai na
Mujaheed sai kanwarsu Hadiza dake kasashen turai, to ban gode ma Allah ba? Me ya
sameni, ke don kawai an dauke wayar da bai fi dubu hamsin ba idan ma ya kai sai ki
sa ma kanki damuwa kiyi ta ciwo kamar wayar jaraba, in dai waya ce ni baxan bari ki
sani a bakin duniya ba xan ba Ahmadu dubu goma ya cika ya siyo maki wata ba ruwana"
Imaan dai bata ko kalleta ba balle ta tanka ta, Ammi ta fito ta gaida Inna, Inna ta
amsa tace "Aisha yanxu baki nuna ma yarinyar nan karatun tawakali??" Ammi tace
"Ciwonta ne fa ya tashi Inna" Inna tayi shiru tana kallonta, can tace "Dama imaan
na da wani ciwo ne da ban sani ba?" Ammi tace "Ciwon nata kuma Inna kika manta?"
Inna ta rike ha6a baki Bude tana kallon Ammi, can tace "Ni dai ba ruwana, ku je
kuna fadan haka wani ya ji, dama banda rashin lafiya da kowa ke yi Imaan na da wani
ciwo na daban ne ban sani ba?" Ammi tace "Toh ko jiya ma Abbanta yace wannan yaron
da ke nemanta ya kamata a sanar masa laluranta tun yanxu" Gwalo ido Inna tayi ta
saki salati tana tafe hannu ta xauna ta rike kai tace "Naga abinda ya isheni ni
patuuu, wayyoo Allah duniya ta lalace" dagowa tayi tana kallon Ammi tace "Aisha da
hankalin ku ke da Bukar kuwa? Dama Imaan na da wani ciwo ne ni da ban sani ba, ku
dai ku dinga fadin gaskiya ku ji tsoron Allah, yaushe rabon da in ji Imaan bata da
lafiya a gidan nan, Ni dai kada wanda ya laka ma jikata ciwo lafiyarta lau, waye
baya xaxxabin maleria da thypho, to kada ma ku kuskura wani yaji wannan mugun
xancen, ku dai ba kwa fadan alkhairi a gidan nan, Ni dai ba ruwana, yaushe rabon da
tayi ciwo?? Ai yafi shekara biyar ba ma banda sharri irin naku...." Mikewa Inna
tayi ta nufi kofa rai bace tana cewa "Mutane dai ba tsoron Allah, meye kuma wai a
gaya ma yaron da ke nemanta laluranta kamar mai cutar AIDS... Ni dai ba ruwana" a
bude tabar masu kofar bayan ta fita ta kara gaba, Ammi na kallon Imaan tace "You
make sure you tell him everything about ur health condition, kar ki boye masa
komai" Imaan ta sauke idonta kasa a hankali tace "Toh Ammi" Ammi ta xauna kan
kujera a ranta tana jinjina halin inna, imaan ta kalleta tace "Ya ce xai xo anjima"
Ammi tace "Toh sai ki gaya masa" biyar da few minutes Sadeeq ya kira Imaan ta wayar
Ammi ya sanar mata yana waje, bayan ta gaya ma Ammi, Ammi tace "Toh kar ki dade dai
a waje" "Toh" kawai imaan tace ta sa hijab dinta ta fita, tana isowa gun motar ya
bude mata back seat yana kallonta yace "Shiga ki xauna" girgixa kai tayi tace
"A'a..." Yace "No pls ki shiga kinga you are sick, you look so weak, bana son musu
get in plss" shiru tayi bata ce komai ba, komawa gefe yyi ta shiga motar a hankali,
yana kallonta yace "Kun je clinic kuwa?" Tace "A'a Dr dina ya xo ya min allura" ido
ya kafeta da shi, hakan yasa ta sunkuyar da kanta yace "What's wrong with you?" Ba
tare da ta dago ba tace "I woke up with headache, backache and joint pain... pains
everywhere...." Ya d'an bude ido da mamaki ya cire glasses din idonsa yace "Yana
maki haka ne dama?" Ta kallesa ta gyada masa kai gently, kasa daina kallonta yayi,
murya can kasa yace "Are you... A sickler?" Girgixa masa kai tayi tana murmushin
karfin hali tace "I am a carrier, I am carrying the trait" jin yyi shiru ta daga
kai ta kallesa, tausayi taga karara a kwayar idanuwansa yana kallonta, underneath
his breath yace "Ya Salam, a very rare case, Subhanallah" murmushi kawai tayi bata
ce komai ba, jingina yyi da motar ya rungume hannunsa yana kallon gate din shiga
gidan looking so disturbed.

Umma ta share xufar da ke keto mata bayan ta gama sauraran bayanin mutumin gabanta,
Hajiya Saude sai jinjina kai take, da kyar Umma na gyara xama tace "Toh malam yanxu
meye abun yi.... A taimaka don Allah, wllh ji nake kamar xuciyata xata fashe, ko
kuma in hadiye xuciyar, duk duniya bani da makiya da ya wuce yarinyar nan da
uwarta, uwarta ta xalunce ni a rayuwa ta cuce ni, a dalilin uwarta na shiga gararin
rayuwa malam ka taimakeni ko nawa ne ni xan biyaka wllh, Malam ka dubeni..."
Mutumin dake xaune gabanta ya girgixa kai yace "Auren nan fa na gaya maki idan ba
wani Ikon Allah ba sai an yi sa, mijinta ne d'an gidan attajirin babu tantama, sai
dai kuma wani Ikon Allah, gashi nan na gani, gashi nagani har ranan bikin..."
Hawaye ya kawo idon Umma tace "A dai duba malam a taimaka" Malam yace "Toh ga
takarda sai ki rubuta abinda kike son ayi a ciki, amma fa banda kisa... don
yarinyar na da tsawon rai haka ma Yaron sai dai kuma wani Ikon Allah, sannan kuma
baxa a iya raba su ba.... yar ki kuma da kike son yaron ya fara nema kuma ba
mijinta bane baxai taba yiwuwa ba, ba mijin yar ki bane yaron attajirin.... Sannan
ina maki tuni surkarki a tsaye take kan yarinyar.... Tasirin aikinmu a kanta kamar
ko da yaushe dai kalilan ne kema kin sani, Ki rubuta komai amma banda abubuwan da
na lissafo maki a baya" Umma ta gyara xama tana share hawayen idonta ta amshi
takardan da biro ta ajiye kasa ta fara rubutu.....

*imaan isn't free* it's 300 via


Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

37.....

Da addare Imaan na kwance parlon Inna dake xuba wani garin magani a kindirmon dake
cikin cup din gabanta, Maimoon ta shigo da sallama ta ajiye abincin hannunta ta
gaida ta, Inna ta mika mata cup din tace "Mika ma waccan matar" Imaan ta juya masu
baya da sauri tana turo baki, Inna ta kalli Maimoon tace "Kinga walakanci ko,
wannan wace irin yarinya ce don Allah, ta san daga inda maganin nan ya fito?" Imaan
tace "Ni nace maki na sha magani fa a gida, ya xa ayi in hada magani iri biyu" Inna
ta ajiye spoon dina hannunta tayi tagumi tace "Oh waannan 'ya ta Bukar dai
jarababbiya ce wllh, Toh meye da maganin da baxata sha ba? Ba daci, ba 6auri, ba
hamami, ba galmi sai ma gyara mata bakin ta da xai yi, ta ji dadi kuma a jikinta,
to ni dai ba ruwana gashi can uwar ki da ubanki sun fara laka maki ciwon da ba a
san ki da shi ba ba a san kansa ba, wai dama idan lkcn gabatar da yaro ya kusa ba
duk iccen da aka jika ma yaron aka basa sai ya amsa ya sha ba sbda a kauda ikon
makiya, Ni dai ba ruwana Ina taimakon ki kina min wlknci, idan ta uwarki ce sai dai
fa ki mutu ba abinda xata maki, shi kuma Bukar na can na neman na abinci a Habuja,
to wa gare ki banda Allah sai ni din, to ni ba ruwana, ki tashi ki amshi maganin
nan ki sha ni ba asararriya bace, uwata bata ce min jeki kya gani ba da xan dinga
maki bauta baki gani, ko ubanki bai samu haka a guna ba" Maimoon ta ajiye cup din
hannunta ganin imaan ta ki amsa tace "Inna ni dai xan je inci abinci" Inna tace
"Toh idan kin gama ki dawo kema ga naku da su fitsararrun can Ummi, ba dai don
halinsu ba, ya xanyi tunda ni na haifi Ahmadun" Maimoon dai bata ce komai ba xata
fita sai ga Mujaheed ya shigo parlon, gaishesa Maimoon tayi ta fita, Inna tace
"Mujaheed waya dai ko sama ko kasa, an dai rasa wanda ya sace, ni na ma fi xaton
hauro kantangar aka yi, ai daga yanxu ni kaca ma xan dinga sawa in rufe kofar da
kwado idan xan fita, Ina dalili? Ai ko ya daukan ma kansa fitinar duniya" Mujaheed
ya gaisheta sannan yace "Za a xo daukan akwatunan nan" Inna ta kallesa sannan tace
"Ita da ta turo ka ba sai ta xo ta kwasa ba in ga, Rukayya dai tayi hankali da ni
ba ruwana.... Wannan yarinya kuma kayi mata magana ta rufa min asiri ta dau nonon
nan ta sha ba sato kudin nake yi ba, dubu goma kenan cikin kofin a kwance ta rasulu
ta sa aka amso min" Mujaheed bai ko kalli imaan ba yace "Kaya xa a karasa xubawa
cikin akwatunan shi sa xa a dauka" Inna tace "Sai kuma ka yi ai, ko Ahmadu bai isa
yace xa a dau akwatunan nan ba balle kai" Kallonta ya dinga yi fuska daure, can ya
juya ya fita. Washegari da safe Mujaheed ya shigo parlon Abba da sallama ta dalilin
kiransa da yayi a waya, Abba na kallonsa yace "Jikin Imaan ya matsanta mata, yanxu
Hajiya Aisha ta kirani..." Mujaheed yace "Toh a tafi asibiti kawai" Abba yace "Toh
xa ka kai ta ne?" Girgixa kai yyi yace "Zaria xan tafi Abba, kuma likitan ta na
gari ai" kallonsa kawai Abba yayi bai ce komai ba, Mujaheed yace "Xan je in shirya
yanxu" Abba yace "Ohk then" Juyawa yayi ya fita parlon. Sai kusan la'asar Ammi da
Aunty suka dawo asibiti da Imaan, nan parlor Imaan ta kwanta Ammi ta shiga kitchen
don girka mata light food ta ci, Imaan ta jawo wayar Ammi dake vibrate kusa da ita
ta kalli screen din, Sadeeq ta ga ke kira, sai da ya kusa katsewa ta daga da kyar
ta kai kunne tayi masa sallama, ya amsa yace "Kun dawo gida ne?" Tace "Um..." yace
"Ohk before magrib xan kawo maki drug din, but I have to see wanda aka baki a
asibiti" tace "Toh" yace "Allah ya kara lafiya" a hankali tace "Ameen" yace "Do you
need anything" tace "A'a" yace "Sure?" Ta gyada kai kamar yana ganinta, yace "Ohk
sai na xo" daga haka ya katse wayar. Karfe shidda saura Yusuf ya shigo parlon da
sallama, Imaan na xaune bayan tayi wanka ta shirya tana cin farfesun kayan ciki da
Ammi ta mata, xaunawa yyi ya sakar mata murmushi yace "Sannu, ya jikin?" Ta mayar
masa murmushin tace "Da sauki ya Yusuf" yace "Toh Allah ya kara lafiya, Ammi fa?"
Imaan tace "Ta shiga daki" Yace "Ohk, me xa a kawo maki na marasa lafiya" ta
kallesa ta marairaice tace "Kawai awara nake son ci" ya d'an buda ido yace "Awara?"
Ta gyada masa kai a hankali, yyi murmushi yace "Toh bari a nemo maki" mikewa yayi
yace "Anjima xan taho maki da shi, ki gaida Ammi idan ta fito" tace "Toh" daga haka
ya nufi kofa ya fita, ko minti biyar ba ayi da fitansa ba sai ga kiran Sadeeq,
sanar mata yyi yana waje tace "Toh ka shigo" Sadeeq ya d'an buda ido yace "Ni fa
Ina jin kunyar Ammi" Murmushi tayi tace "Ae tana daki" Yace "Uhn toh gani nan
shigowa" ajiye wayar tayi bayan ta katse, ta mike ta wuce dakin Ammi ta sanar mata
Sadeeq xai shigo, Ammi tace "Toh haka xaki tsaya babu hijab" ta girgixa kai tace
"A'a xan dauko a daki yanxu" Ammi tace "Ohk" daga haka Imaan ta fita ta shiga
dakinta ta dauko hijab ta sa ta dawo ta xauna xata rufe farfesun gabanta yayi
sallama bakin kofa, ta kalli kofar ta amsa sallaman sa, ya shigo parlon, sunkuyar
da kanta tayi ya xauna saman kujera ya ajiye ledan hannunsa a kasa yana kallonta
yace "Sannu Imaan, ya jikin?" d'an murmushi tayi tace "Ina yini" yace "Lafiya lau,
Ina drugs din da suka baki a asibiti" mikewa tayi ta nufi daki ya bi ta da ido, ta
dawo rike da ledan drugs din, ajiye masa tayi a kusa da shi, sannan ta koma ta
xauna, yayi murmushi ya dau ledan ya fiddo Magungunan yana dubawa, can ya mayar da
su, ya dau karamin ledan da ya shigo da ya ciro drugs biyu yace "You can take this
also ba komai, na rubuta prescription din a jiki" ta gyada masa kai ya ajiye
maganin, ya ciro wani na tube yace "Wannan ma ki dinga shafawa a duk inda kike jin
pain" Imaan tace "Toh..." Ya d'an bude ido murya can kasa yace "Ko in shafa maki
dear?" Xaro ido tayi ta kallesa sai kuma ta boye fuskarta a kujera, murmushi kawai
yake yana kallonta, ganin ta ki dagowa yace "Toh baki cinye pepper soup dinki ba" a
hankali ta dago tace "Ko xaka ci ne?" Yayi murmushi yana shafa beard dinsa yace "Ai
baki bani ba" daukan bowl din tayi ta kai gabansa ta ajiye, ya xaro ido yace "I am
only joking" tace "Ae sai ka ci" yace "Plss ki dauke, wllh wasa nake maki I am
okay" ta make kafada tace "Ai kace ban baka ba to gashi ynxu na baka" ya wani xaro
ido yace "Kar Ammi ta fito ki dauka plss" cike da shagwaba tace "Sai ka ci" yace
"Ohk ohk idan na ci xaki dauke" tana murmushi tace "Ehh" yace "Toh dago min" daukan
bowl din tayi ta rike da hannu biyu ta durkusa gabansa tana kallonsa har sannan
tana murmushi, ya lumshe ido ya bude ya dau spoon din ya dau nama guda daya yayi
kamar xai bata a baki ta koma baya da sauri, bakinsa ya kai spoon din ya ci, ta
wara ido tana kallonsa, ya lumshe ido yace "It's sweet" dariya ta fara yi kasa kasa
tace "Ashe kai ma ka iya kwadayi" da sauri ya bude ido, ta koma ta xauna still tana
dariya, murmushi yyi yace "Ai xan rama" ta buda masa hannuwanta tace "Ko dai ka
rame" kallonta kawai yake affectionately, ta turo baki tace "Ni dai ka daina
kallona haka" dauke idonsa yyi yana murmushi yace "Watarana xaki yi bayanin me yasa
xan daina kallonki" bude kofar parlon aka yi duk suka juya, daddy ne ya shigo
parlon da jakar laptop dinsa Mujaheed na bayansa rike da traveling bag dinsa, imaan
ta wara ido ta mike da sauri tace "Daddy" murmushi ya sakar mata, tana son xuwa ta
rungumesa amma ta kasa saboda Sadeeq, ta isa gabansa cike da farin ciki, a hankali
tace "Sannu da dawowa Daddy, baka ce min yau xaka dawo ba" Daddy ya shafa kanta
yace "I just decided to come back and check on you daughter, how are you feeling
now" tace "Da sauki sosai Daddy, har na ci abinci ma" amsan ledan hannunsa tayi, ya
karasa parlon yana kallon Sadeeq kamar yanda Mujaheed ma ke kallonsa, Daddy na
murmushi yace "Sadeeq" Sadeeq yyi kasa da kai yace "Sannu da dawowa Abba" Daddy
yace "Thanks son, ya aiki" Sadeeq yace "Alhmdllh" Daddy yace "Ya Mai jikin?" Sadeeq
yace "Alhmdllh she's getting better" Daddy yace "Maa sha Allah" Kallon Mujaheed
Sadeeq yayi yace "Barka da yamma...." Mujaheed yace "Thank you" Ajiye jakar
hannunsa yayi yana kallon daddy yace "Allah huta gajiya Abba" Daddy yace "Ameen
son" imaan dai ko kallonsa bata yi ba kamar yanda shi ma bai ko kalleta ba ya juya
ya nufi kofa, Daddy ya wuce bedroom dinsa, mikewa Sadeeq yayi yana kallonta yace
"Kin ga kunyar da naji" dariya imaan tayi tace "Kunyar me? Sadeeq na shafa kai a
hankali yace "Kunyar Abba mana" Imaan tayi murmushi bata ce komai ba, yace "Ki
gaida min da Ammi, let me get going now" a hankali imaan tace "Toh nagode, Allah ya
tsare" yace "Ameen dear, Allah ya kara lafiya, and plss kar kiyi wasa da drugs din
ki" Ta d'an yi murmushi tace "In sha Allah" yace "Toh baxa ki rakani ba" tace "Toh
xan raka ka bakin kofa" yace "Noo bakin mota dai plss my dear" tace "Toh idan na
fadi a hanya fa" yace "Sai in daga ki sweet" boye fuskarta tayi ya nufi kofa yana
murmushi ta xaro ido tace "Ka manta ledan ka" ba tare da ya juyo ba yace "Na ki
dai" shiru tayi tabi sa da ido sannan ta bi bayansa, kamar mai tausayin kasa ta isa
kusa da shi don tsaye yyi yana jiranta, a jere suka dinga tafiyar yana kallonta ita
ko ta ki yarda ta kallesa, Ni kam nace waow perfect couples they will make... Lol,
A dai dai bangarensu Maimoon Umma ta fito ta nufi parking space kana ganinta kasan
fita xata yi, Sadeeq ya kalleta yace "Ina yini" tace "Lafiya lau" Imaan tayi kasa
da kai a hankali tace "Ina yini?" Banxa Umma tayi mata ta bude back seat xata
shiga, Imaan dai bata kalleta ba suka fita tare da Sadeeq, ido hudu tayi da
Mujaheed dake xaune gun Mai kiosk dake kusa da gate din su, Dauke kai tayi da
sauri, Sadeeq bai ma lura da shi ba, ya isa gun motarsa tana biye da shi, Yana
kallonta yace "Keep on greeting her xata amsa wataran, you will loose nothing don
kina gaisheta...." murmushi kawai Imaan tayi, ya kafeta da manyan idanuwansa, murya
can kasa yace "Plss ki dinga cin abinci da yawa sweet, kin rame fa" ta wara ido
tace "A'a ni dai haka nake" kallonta kawai yake bai ce komai ba, ta sunkuyar da kai
tana wasa da fingers dinta, underneath
his breathe yace "I have always loved you from day 1 imaan..." kasa kallonsa tayi
gabanta ya dinga faduwa, kamo hannunta yyi a hankali ya lumshe ido xai kai lips
dinsa ta kwace hannun da sauri tana satan kallon inda Mujaheed yake, kallonsu taga
yana yi, Sadeeq ya kalli inda ta kalla suka yi ido hudu da Mujaheed, dauke kai yyi
a hankali yace "We will talk later dear" daga haka ya shiga motar ta juya ta nufi
gate gabanta na faduwa tana satan kallon Mujaheed da ya bi ta da ido fuskarsa dauke
da wani expression, rufe gate din tayi tana kara kallonsa sannan ta wuce part din
su da sauri. Mujaheed na gama parking ya juya yana kallon ummansa dake Bayan motar
sai danna waya take, ta daga kai da sauri tace "Au, har an kawo ashe" bude motar
tayi bayan ta ajiye wayar tace "Ka jira ni ba dadewa xan yi ba" yace "Umma aiki
nake son wucewa don Allah kar ki dade" tace "Na sani baxan dade ba Mujaheed" daga
haka ta fito motar ta shiga gidan Hajiya Balaraba, ita kadai ce babban gidan duk
kishiyoyinta dama ta rabasu da gida, Hajiya Balaraba dake parlor xaune tace "Daga
Ina haka Hajiya Rukayya" Umma tace "Daga gida Ina son kai ma Hajiya Saude kudin da
ta ranta min na ba mutumi, sannan ku dai xauna da shiri sati mai xuwa xa a kai lefe
gidansu Safeenah" Hajiya Balaraba tace "Toh Allah dai ya kai mu lafiya, amma ya ku
ka kare jiya ina ta son in kira ki ko inje gida in sameki" Umma ta tabe baki tace
"ya dai sa in rubuta masa abinda nake so ya faru, na kuma rubuta yace min in sha
Allahu an gama, abu ne mai matukar sauki.... Kar ki so ki ga irin farin cikin da
nake wllh Hajiya, idan hakan ya faru ae har Aisha ta mutu baxata rabu da ciwon
xuciya ba" Hajiya Balaraba ta xaro ido tace "Toh me kika rubuta halan?" Umma ta
rike ha6a tace "Cewa yyi kar in gaya ma kowa, ki sha kurumin ki aminiya, komai xai
fito fili xa ki gani" Hajiya Balaraba tace "Amma xa su yi auren kuwa" Umma tayi
dariya tace "Ehh to yace yaga da auren, amma ban jin abinda xai faru xai sa ayi
auren nan... Kinga bari inje na bar Mujaheed yana jirana a waje" sallama tayi mata
ta fita tana murmushi.

*imaan isn't free* the subscription is 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

38....

Imaan na kitchen tana yanka ma Ammi pumpkin leaves ta ji an danna bell, barin
ganyen tayi a chopping board ta dauraye hannunta ta fito, bedroom dinta ta shiga ta
dauko hijab ta sa sannan ta nufi kofar ta bude, Mariya ta gani tsaye bakin kofar ta
xaro ido tace "Mariya Ahmad" Mariya na murmushi tace "Am I not welcm?" Sai a sannan
Imaan ta kara ganin mugun kamar da suke da Sadeeq har dimples din, ta kamo hannunta
cike da murnar ganinta tace "Sosai ma besty, daga Ina kike haka? Come in plss"
Mariya ta shiga parlon tace "Mumy ce ta aiko ni wancan layin dake gaba da naku
shine nace let me branch and say hi, ni da yayanmu ne ma" Imaan ta wara ido tace
"Wanne?" Mariya tace "Wannan da ya taba maido ki gida da kika xo gidanmu" Dariya
kawai Imaan tayi bata ce komai, har yau kuma tana mamakin me yasa Mariya bata ta6a
nuna mata ta san suna tare da Sadeeq ba, ko bata sani bane?? She still can't tell,
Imaan tace "Toh xauna plss in kawo maki ruwa mana" Mariya ta xaro manyan idanuwanta
tace "Ya Sadeeq xai wuce kenan ya bar ni, dama kawai shigowa nayi mu gaisa ai daga
gida muke, am okay dear" Imaan tace "Toh shkkn nagode kuma naji dadi" Mariya tace
"Mum fa?" Imaan tace "Taje kasuwa tare da mamansu Maimoon" Mariya tace "Toh ki
gaishe min ita idan ta dawo, mu je ki rakani, baya son jira wllh" imaan na murmushi
tace "Toh shikenan mu tafi in raka ki" a tare suka nufi gate bayan sun fito parlon,
Mariya tace "Ya shirin Sauka fa?" Imaan tace "Ina ta yi" Mariya tace "Ae kam gashi
lkci sai matsowa yake..." Imaan tayi murmushi bata ce komai ba har suka fita gate,
ta dinga kallon lafiyayyen ride dinsa dake parke a waje ba wanda ya saba xuwa da
shi wajenta ba, tun da suka fito Sadeeq ke kallonta ta cikin glasses din idonsa ko
kiftawa babu, har suka iso kusa da motar ya sauke glass din motar yana kallonta
murmushi dauke fuskarsa, imaan ta sunkuyar da kanta tana fidgeting fingers dinta
tace "Ina yini?" Cikin cool voice dinsa yace "Lafiya lau" Mariyata kallesa tace
"Yaya ka tuna ta? Frnd dita din nan..." Sadeeq yyi murmushi ya girgixa kai yace "Ni
kuma sbda mantuwa na yyi yawa kullum sai anyi min introducing dinta koh?" Dariya
Mariya tayi tace "Eh mana Yaya frnds dina kullum ba ganesu kake ba sai kace ka
manta, to ita ma nasan ka manta ta" Ya shafa kansa yana kallon Imaan har sannan
yana murmushin sa mai kyau yace "Ita ai baxan manta ta ba" Imaan dai bata yrda ta
kallesa ba, Mariya ta juya ido tace "Toh ya sunanta?" Yar dariyarsa yyi mai kyau
yace "Kin fini sanin sunanta ai" Mariya tace "Na kamaka a nan, you are just
pretending amma ka mance ta yaya" Sadeeq ya daga kafada yace "Ohk then, let leave
it that way, na manta" Mariya tace "Tohm gwara dai" kallon Imaan tayi tace "Bye
frnd ki gaida mum idan ta dawo plss" Imaan tace "In sha Allah, nagode da ziyara"
Sadeeq ya d'an kalleta yace "Toh kawar Mariya sai anjima" Imaan ta hararesa ta
gefen ido ta wuce ciki da sauri, ya bi ta da kallo yana murmushi, Mariya ta rungume
hannayenta tace "Hmmm Yaya wannan kallon fa?" Da sauri ya kalli step sis din tasa,
sai kuma yyi murmushi yace "Kallon gate din gidan?" Dariya tayi sosai ta xaga ta
shiga gaban motar ya tada motar ya bar layin. Mamaki Imaan ta dinga yi na me yasa
Sadeeq ke boye ma yan gidansu gashi dai ajinsu daya da Mariya both islamiyya da
Schl amma bai gaya mata ba, tabe baki tayi ta cire hijab dinta ta shiga kitchen ta
ci gaba da aikin da take. Bayan ta gama duk abinda xata yi bayan la'asar ta wuce
part din Inna don su Ammi basu dawo ba har sannan, Mujaheed ta tarar bakin tap yana
alwala, tun da ya kalleta sau daya bai sake kallonta ba ya ci gaba da performing
ablution dinsa, ta wucesa ta shiga parlon Inna, Inna ta mika mata abun kwashe
sharan hannunta wanda ba komai ciki sai few dirt tace "Xubar min wannan a bola,
dubi fa parlon kamar ba komai amma ji yanda datti suka cuceni suka makale, kamar na
sani nace bari dai in share in gani, ilai kuwa ga shi har da guntun kasa, kila ma
wannan mutumin ne ya shigo min da su, sam datti bai da masugunni a parlona gaskiya"
amsa imaan tayi ta fita ta kakkabe abun kwashe sharan ta dawo, ta bi Mujaheed da
kallo ganin wucewarsa yyi ta shiga parlon, Inna ta shimfida tabarma ta xauna tace
"Ke ki ji ya xo min nan ya kwanta salon ya fara wannan xaxxabin nasa a ce a parlon
Inna haka ya faru" Imaan ta xauna saman kujera tace "Ba shi da lafiya ne?" Inna
tace "Wai daga anje an kai kudin gaisuwa shine har ya fara tunanin rabuwa da ni bai
san tare xa mu tare a can gidan nasa ba" Imaan ta xaro ido tace "Shi yace maki
haka?" Inna tace "To sai ya fada?? ko bai fada ba nasan hakan ne ma, ke kinsan
shakuwar da Mujaheed yyi da ni kuwa? Nima har na fara jin xaxxabin xai rufe ni"
Imaan tayi dariya tace "Yaushe aka kai gaisuwan?" Inna tace "Daxu da safe su Ahmadu
da Bukar da Bala da abokan Ahmadun suka kai... jibi kuma xa mu je kai lefe ki
shirya tare xa mu dake" Imaan ta xaro ido tace "Har da ke?" Inna ta saki baki tana
kallonta tace "Oh oh Allah, ban gane har da ni ba, to dama su waye masu kai lefen
idan ban da ni... Ni ana bani mamaki wllh haka Ahmadu da Bukar wai bai dace ba inyi
xamana a gida, to a kan me? Ni fa nayi wahala da shi Mujaheed din, sannan ba shi da
wata kaka da ta wuce ni a duniya, in har baxan je ba dama sai dai iyayen yarinyar
so su dau lefen da kansu ba ruwana" Imaan dai bata ce komai ba, Inna ta mike ta
shiga daki sai ga ta ta fito rike da wani takarda, tana kallon imaan tace "Duk
cikin jikokina kece kadai xan ce tayi abu tayi, da kyar kiyi min musu, sauran kuwa
dama baxa su yi ba, to wannan ba wani damu na yayi ba don kansu suke ma, ga wannan
wanka xa ki yi da shi ni dama baxan ba su Ummi su xubar min dukiya ba ba ruwana ba
sato kudin nake ba, ke kadai ma amsowa" Imaan ta turo baki tace "Meye shi din?"
Inna tayi kasa da murya tace "Wllh garin magani ne, sai kamshi ma yake, ko uwarki
kada ki gaya ma ba hankali gareta isasshe ba sai ta hanaki amfani da shi, ki xuba a
cikin bokitinki ki tara ruwa bakin ki a leko ki yi ki fito kin ji takwarata" Imaan
tace "Ni wllh kaikayi xai dinga min a jiki fa" cike da fada Inna tace "Yau naga
jaraba sai kace warce xan ba karara? Meye kuma wani kaikaiyi ni patuu? Garin magani
ne fa ba wani abu ba" Imaan ta hade rai tace "Toh bana so baxan yi ba" Inna tayi
kasa da murya tace "Toh yi hakuri takwara, abinda ma idan kika yi yau kika yi gobe
shkkn, wllh dubu goma kenan kar ki ja min asara ba ramin kudi gareni a dakina ba,
ba komai sai tarkacen kwallaye da tsoffin akwatuna" imaan ta turo baki ta amsa tace
"Toh wai na meye?" Inna tace "Kaikayi koma kan mashekiya" Imaan ta xaro ido tace
"Meye hakan?" Inna tace "Duk wanda xai sa maki ido a duniyar nan idonsa xai tsiyaye
tass barsa da jakar idon, idan kuma mugun abu xai maki to fa sai dai ya koma kansa
ne ni ruwana, babu wanda ya san ta yanda Bukar ya sameki" Murmushi kawai Imaan
tayi, Inna tace "Su Maimoon ma ga nasu can na ajiye masu ba don halinsu ba" Imaan
tace "Toh" Inna tace "Ni kwana biyu banji Bulasawa ya kirani ba, ko dai lambar ta
bace a wayana ne shi sa baya iya kirana" daukar wayar tayi ta mika ma imaan dake
dariya tace "Ke duba min, ba halinsa bane rashin kiran duk kwana biyu kya ga ya
kirani mun gaisa har in fada masa damuwata" imaan ta gama danne dannenta ta mayar
mata wayar tace "Network ne ya dauke sai bayan sati daya xai dawo" Inna ta saki
baki tace "Saboda me toh?" Imaan ta mike tace "Ae haka yake yi" daga haka ta fice
parlon tace "Na tafi" Inna ta ajiye wayar tace "Toh Allah ya mana tsari da su masu
wayan" Ranan Friday da yamma babu yanda Abba da Daddy basu yi da Inna kan cewar
tayi hakuri ta bar yan uwan umma, Matan kawu Bala, Ammi da Aunty sai kanwar umma da
kawayenta biyu su kai lefe gidansu Safeenah ba inna tace samm bata san xance ba da
ita xa a kai kayan, Daddy dake ta kallonta yace "Yawanci ynxu fa iyaye maxa ne ma
ke kai kayan ba mata ba Inna, ke me xaki je kiyi cikin yara don Allah" Inna ta masa
wani kallo tace "Toh ko a baka kayan ka kai ne Bukar?" Daddy bai ce komai ba, Inna
tace "Yau naga jaraba, to wai ina ruwan Bukar a maganan nan fisabilillahi, Wai
xanje cikin yara, A'a gyambo ce ni karewar girma, kawai ayi ta laka ma mutum tsufa,
ni din nawa nake gaba daya tukunna ma dai, kamar warce dai ta haifi duniya??" kawu
Bala yyi kasa da murya yace "Hajiya Inna da dai kiyi hakuri ki bari su kai kawai,
ke fa babba ce...." Inna ta dakatar da shi a fusace tace "Kai rabu da ni Balalau,
Ina ruwanka?? Ka san da xamana a kaduna ko ka taba xuwa takanas ka gaisheni? Ko
gantalallun matan ka ma ba turo su kake ba balle yaranka, yau da Hurera na da rai
xaka mata haka, Allah dai ya mata Rahama ya gafarta mata bata min komai ba, lafiya
muka xauna da ita...." Mikewa daddy yyi ya fice a parlon, Inna ta bi sa da kallo
tace "Wannan Bukar din dai ba shi da kirki wato ga mahaukaciya na magana shine ya
fita, Wai... Ai da Bukar ne ke xaune a kaduna wllh baxan sha ruwa a gidan nan ba,
mulkata kawai xai dinga yi da bafillatanar nan da figaggiyar Yar su, Toh sae Allah
ya rufa min asiri Ahmadu ne, kwata kwata Ahmadu dama bai son abinda xai ta6a ni a
duniyar nan shi da yaransa, kaga inda ya fi Bukar kenan, to meye kuma daga magana
dai ta fahimta xai kwashi jiki ya fita" murmushi kawai Abba ke yi da kawu Bala da
yyi hamdala a xuciyarsa da ta katse tsigesan da tafara yi ta koma kan daddy, Abba
yace "Toh shikenan dai Inna, Allah ya kiyaye hanya sai kun dawo" Inna tace "Toh
dama mota daya xa a ware mana da imaan da kawata ta rasulu, tace min tana hanya"
Abba ya buda ido da mamaki yana kallonta, kawu bala yace "Toh madallah Allah kawota
lafiya" daga haka ya fita Abba ya bi bayansa, Kawu Bala na ta murmushi yace "Ayi ta
hakuri Barrister tsufa ne" murmushi kawai Abba yyi yace "Ana ta yi, sai dai Allah
ya kara mana hakurin" Kuka umma ta xauna kan gado ta dinga rusawa jin da Inna xa a
je kai lefe tana kallon kawayenta tace "Babu abun kirki idan aka tafi da matar nan
wllh, xuwa xata yi ta mana tonon asiri, tayi ta sakin xance a gidan"

*The book Imaan isn't free* it's 300


Via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence of payment via my WhatsApp digit


07087865788 subscribe and read without been judge by ur conscience.

39.....

Mujaheed dai na tsaye kitchen sae kallon Umma yake har ta kai aya, jin yyi shiru a
fusace tace "Wae ba da Mujaheed nake magana bane??" Ya d'an shafa kai yace "Ina ji
Umma, Toh ni ya xan mata, kinsan tunda tace sai taje, ba wanda ya isa hanata xuwa
ne" Umma ta hade rai tace "Yanxu baxa ka samo dubara da xaka hana xuwan nata ba,
wllh idan taje gidan nan tsaf xata iya sa su fasa baka mata, tun da uwata ta
haifeni ban taba ganin mutum sakakka irin tsohuwar nan ba, ni dai duk yanda xa ka
yi ka rufa min asiri kayi ka hanata xuwa Marafan nan don Allah, ga ta can bakin
motoci tsaye sai nuna hali take" Mujaheed yyi murmushin karfin hali yace "Toh..."
Juyawa Umma tayi ta fice daga kitchen din rai bace, Inna dai na tsaye an sha super
da mayafi da yar jakarta sae xuba kamshi take, duk mutan wajen dama sun bar jikin
motar an bar ta ita kadai barin kawayen Umma, ta aika Maimoon ya fi sau uku ta kira
mata Imaan amma shiru, ganin Maimoon ta dawo for the 4th time Inna tace "Yau naga
abinda ya isheni ni patuu, Ina Imaan din ta shiga ne wai??" Maimoon tace "Inna ni
fa ban ganta ba" Part dinsu Imaan Inna ta nufa fuska daure tana cewa "Ni ai xan
ganta idan naje" Daddy ne xaune parlorn yana operating laptop dinsa, ta shigo
parlon ko sallama babu tana kallonsa tace "Bukar Ina Imaan ta shiga ne wai, ko bata
san duk jama'ah sun taru ita ake jira bane?" Daddy ya kalleta yaci gaba da abinda
yake yace "Tana daki...." Inna tace "Kaga walakanci ko, wllh tarbiyar 'yar ka
kalilan ne Bukar, ce mata nayi fa ta shirya ta fito mu tafi amma don wlknci ta
shanya ni a rana ina ta jiran fitowarta, gafara xata min ne ko menene haka??" Daddy
ya kalleta yace "Ku je Ina wai?" A fusace Inna tace "Kai lefen mana, ko gwari nake
maka" girgixa kai yayi yace "Don Allah ki bari Inna, me xata je yi gidan... cikin
manya kuma, kai lefe dai tun daxu ana ta abu daya ya ki ci yaki cinyewa, Ni nace
mata baxa ta je ba don babu sa'anta a masu kai kayan, kema kawai don kince sai kin
je ne babu yanda muka iya..." Inna ta saki baki tana kallonsa, can tayi kasa da
murya tace "Meye laifina don nace xanje kai kayan jikana da nayi wahala da tun yana
tsumma, me yasa baka da fahimta d'an uwanka ya fi ka fahimta Bukar...." Sai kuma ta
fara matsar kwalla tace "Toh ai shikenan sai in fasa xuwa a kira ta Rasulu ace tayi
xamanta, ai ba aikin Allah bane kai lefen na hakura" Daddy yace "A'a ni bance kar
ki je ba tun da kinyi niyya kiyi tafiyar ki amma Imaan baxata je ba gaskiya" Inna
tace "A'a su tafi, haka kawai in bata maku rai kan tsinannen lefe, dama ai babu
sa'a na a masu kai kayan sai ta Rasulu ita ma xan sa a kirata ince tayi xamanta
kawai, ae gaskiya ku ka fada, duk wanda kuma ya rasa mai gaya masa gaskiya a duniya
yyi asara, ni dai na hakura da in bata maku rai sbda kayan mutane" Daddy dai bai ce
mata komai ba har ta fita, Ammi da har ta gama shiryawa ta fito daga daki tana
kallon Daddy tace "Kai me ya kai ka yin haka yallabai, maimakon ka barta tayi
tafiyarta tunda ta sa rai" Daddy yace "Gwara ana yi ai ana mata gyara, ba gashi
yanxu tace ta fasa ba, Amma komai tace be it right or wrong sae barrister ya biye
mata" Ammi dai bata sake cewa komai ba. Inna na xaune parlonta bayan Yan kai lefe
sun tafi kai lefen, Umma kam kamar ta xuba ruwa kasa ta sha duk tunaninta Mujaheed
ne yyi mata magana ta fasa xuwa farin ciki gunta ba a cewa komai sai murmushi take
bayan an tafi kai kayan. Mujaheed ne ya shigo parlon Inna da sallama ta dalilin
sawa da Innar tayi a kirasa a waya, ita kadai ce parlon xaune kan kujera fuskarta
shabe shabe da hawaye har da majina, Kallonta Mujaheed ya dinga yi da mamaki yace
"Mai ya faru kuma?" Ta rushe da sabon kuka tace "Babu abinda Bukar ya mance bai
gaya min ba Mujaheed wai daga nace xan je kai kayanka don Allah ya albarkaci kayan,
shine ya tsitstsige ni ya gaggaya min ba dadi, yayi ta min bala'i kamar xai ari
baki wai xan je cikin yara tsofe tsofe da ni, inda Bukar yake shiga ba nan yake
fita ba, yayi min tatasss...." Wani kukan ta kara fashewa da, Mujaheed ya xauna
yana murmushi yace "Shine kike kuka?" Cikin rawar murya tace "Baxan yi kuka ba
Mujaheed, Bukar ya lalace, yau har nuna min yayi bani da iko da figaggiyar 'yar nan
tasa mai ciwace ciwace iri iri kamar warce ta kashe d'an mutum, Ni dai ba Ruwana ba
haka Bukar dina yake ba da, duk Aisha ta lalata sa da halinsu na fulani, ta sa ya
xama jarababbe ya xama fitinanne, ga bakar xuciya.... Ni dai ban tanka sa ba nayi
shiru Ina ta kallonsa don gani nayi abun ba na lafiya bane, Ni Ahmadu baya min haka
komai nace sai dai yace min to, kwata kwata bai son bacin raina, Bukar dai ya
lalace kuma ni ba ruwana da shi da 'yar sa.... su je can su karata idan Bala ma xai
tafi ni bin sa xan yi kawai, duk kwana biyu sai in dinga kiran Ahmadu muna gaisawa"
Murmushi kawai Mujaheed yake yace "Kece fa baki fahimci daddy ba ba fada yake maki
ba kawai dai gyara ne" Inna ta daga hannu sama tace "A'a wllh fada ya dinga min
kamar xai ari baki, ni ba ruwana kar ka xo nan ka karesa.... lalacewa ne dai ta
riga ta samesa, har ni xai bude baki yace ma babu inda yar sa xata bi ni" Sai kuma
ta fara kuka tace "A karkashin akwati fa na fiddo kayan nan ko sa su ban taba yi ba
gashi yanxu babu inda naje sai na wanke su kar su yi warin jiki, kasan mutum ba
komai bane facce datti" Mujaheed ya tabe baki yace "Kiran kenan?" Tace "Eh wllh, na
rasa wanda xan gaya ma ne na kira ka, gashi har naji sanyi, to wa gareni dama banda
Allah sai kai din, sai kuma Ahmadu" mikewa yayi yace "Toh ki shirya sai in kai ki
gidan nawa ki gani...." Tace "Gidan da xa mu xauna?" Ta gefen ido ya kalleta bai
tanka ta ba ya fita tace "Toh ai kawai bari in fito tunda ban tu6e kayan ba...."
Mujaheed na isa part din su Imaan ya shiga da sallama, har sannan Daddy na parlorn
a xaune, ya xauna saman kujera ya gaishesa with respect, daddy ya amsa da murmushi
yace "Ya gajiya" murmushi kawai Mujaheed yyi yace "Abba dama wai Inna ce..." Sai
kuma yyi shiru yayi yar dariya yana kallon daddy, daddy yace "Kiran ka tayi kenan"
Kai ya gyada masa, Daddy ya girgixa kai bai ce komai ba, nan Mujaheed ya fada masa
duk yanda suka yi da ita, daddy murmushi kawai yake yace "Dama xan je yanxu in
sameta" Mujaheed yace "Amma kuma xan fita da ita xuwa can gidan ta gani, xaka
sameta yanxu ko sai mun dawo?" Daddy yace "Toh shikenan ku tafi kawai, anjima xan
je idan kun dawo, Ku tafi tare da imaan din..." Mujaheed yace "Toh" Daddy ya kira
Imaan dake dakinta, fitowa tayi parlor, ganin Mujaheed ta xaro ido ta koma da sauri
ta dauko Hijab dinta tasa, shi dai Mujaheed dauke kansa kawai yyi, Bayan ta sake
fitowa daddy yace "Ki shirya xa ku fita tare da Inna yanxu" a hankali tace "Toh"
daga haka ta juya ta koma daki, Mujaheed ya mike yace "Toh sai mun dawo Abba" Daddy
yace "Toh Allah ya tsare, thank you son" murmushi kawai yyi ya fita parlon. Back
seat ya bude ma Inna ta shiga tana cewa "Allah dai ya shiryi Bukar, Ni dai inaga
bakin cikin 'yar kazar da xa a ban in ci a can yake min, to ni kuwa wani irin nama
ne ban ci ba a rayuwar nan, ni wllh ya ma fara bani tsoro, sam ba haka yake ba da,
yasan wahalan da nayi da shi yana karami kuwa, kamar fa baxai yi rai ba mayu suka
kama min shi, kasan lkcn yana da kyau tsantsaa ga shiga rai yanda dai kaga wannan
figaggiyar yar tasa da ya haifa, haka nayi ta wahala in gaya maka Mujaheed, Ni ce
can nice nan cikin kishiyoyi gantalallu lkcn Ahmadu na da shekara hudu shi kuma ba
shi da aiki sai shegen kiriniya yyi ta kwaso min kayan bola...." Rufe motar
Mujaheed yyi bayan ta shiga ya juya suka yi ido hudu da imaan dake tahowa sanye da
hijab dinta har kasa hannunta rike da wayarta.... Ya dauke kai ya xaga ya bude
driver seat ya shiga, Imaan ta bude back seat xata shiga ya juya ya jefa mata wani
mugun kallo yace "Do I look like ur driver?" Turo baki tayi bata shiga ba kuma bata
ce komai ba, Inna tace "Oh oh Allah, kaga jaraba ko Mujaheed, yanxu wa ya gayyatota
nan, ba Uban cewa yayi kar ta bi ni ba, meye kuma ta wani xo mana nan salalo
salalo" Imaan ta hade rai tana kallonta, Inna tace "Ni dai ba ruwana, ki shiga gaba
ki xauna tunda ubanki ba son tarayyar mu yake ba, ni ki daina ma xuwa min sashina
nunawa yake a fakaice wai ina koya maki bakin hali" Imaan taji kamar ta juya ta
koma bangarensu amma sanin Daddy na parlor kuma kafin ta fito ta ce masa ita baxata
bi su ba yayi insisting sai taje, tasan tana komawa yanxu fada xai mata yace ta
koma, haka nan babu yanda ta iya ta shiga front seat din fuskarta a daure. Tafiyar
kusan minti ashirin suka yi xuwa gidan Mujaheed dake Unguwan sarki, throughout
journey din Inna bata yi shiru ba, Daga Mujaheed har Imaan babu mai ce mata komai,
wayarta dake hannunta ya fara vibrate ta kalla taga Sadeeq ke kiranta, silencing
wayar tayi gaba daya ta saci kallon Mujaheed suka hada ido don shi ma kallon nata
yake a sace, da sauri ta dauke kai bata sake kallon gefenta ba, Mai gadin gidan ne
ya bude gate ya shiga ciki da motar yyi parking a space din mota uku dake cikin
babban compound din da ya kawatu da shuke shuke masu kyau da daukar hankali, Kashe
motar yyi ya fito, Inna ma ta bude motar ta fito tana kallon babban duplex din tace
"Lahhh, toh ai wannan ya ma fi na ubanka kyau da haduwa, kasan lkcn da ka kawoni ba
a gama ginin gidan ba duk sai na raina gidan...." Imaan ta bude motar ta fito fuska
daure, Inna na kallonta tana washe baki tace "Kema dai Allah yasa wanda Bulasawa
xai saka ki ya fi wannan komai da komai...." Tana fadin haka ta bi bayan Mujaheed
da ya nufi main entrance din gidan, imaan ta bi bayansu tana tabe baki, da makulli
ya bude kofar shiga gidan inna ta riga sa shiga tana rafka uban sallama, the parlor
was well furnished, babu abinda babu a ciki na xamani, Inna ta rike ha6a tana
kallon Mujaheed tace "Mujaheed duk kai ka xuba wa enannan kayan a parlon nan, kar
fa kaje bashi ya hau kanka mu shiga uku..." Bai tanka ta ba ya wuce sama ta bi
bayansa da sauri, imaan ta kyabe baki ta dinga bin hadadden parlon da kallo, wani
kofa da
ta gani a parlon ta bude ta ga daki ne babba da bathroom a ciki, ta kara bude wani
taga makeken well furnished kitchen sai dai babu kaya a ciki, ta karasa cikin
kitchen din ta bude wani kofa dake ciki taga store ne na ajiye kayan abinci, sai
kuma wani kofa da xai yi leading dinka xuwa bayan gidan, rufe store din tayi ta
fito ta rufe kitchen din ma sannan ta wuce sama, dakuna hudu ne a jere amma da
distance mai d'an dama tsakaninsu, sannan corridor din na da fadi da tsayi sosai,
wani kofa ta bude taga daki ne da bathroom a ciki, babu komai dakin sai Ac da
curtains sai fitilu, ta rufe ta bude wani taga irin wancan ne, kin bude Wanda taga
alamar suna ciki tayi don muryar Inna kamar speaker a dakin, ta bude last door din
dake corridor din, well furnished parlor madaidaici ta gani ta shiga tana kare ma
hadadden parlon kallo, can ta bude wani kofa da ta gani a parlon taga bedroom ne,
shiga ciki tayi ta rufe kofar tana kalle kalle ta karasa ta bude wani kofar taga
bathroom babba, ta d'an tabe baki ta juya ta nufi kofa ta bude suka ci karo da
Mujaheed, juya masa baya tayi da sauri tana xaro ido, taji kamar ta nutse a wajen,
jin yana sa makulli a kofar ta juyo da sauri tana kallonsa....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

40....

Ja baya Imaan ta dinga yi ganin kallon da yake mata fuskarsa a daure, ta 6ata fuska
kamar xata yi kuka, a hankali tace "Yaya fita fa xan yi...." Bai tanka ta ba kuma
bai fasa bin ta ba tana komawa baya, ganin kiris ya rage ya risketa ta koma can
kusa da window din dakin ta tsaya xuciyarta na bugawa tace "Wayyo ni dai ka kyaleni
in fita, me na maka" dab da ita ya tsaya, xata durkusa ya dago ta yace "Training da
Ammi ta maki kenan na ba ma namiji hannun ki yayi kissing a bakin mota kina washe
baki koh?" Ta wani xaro ido tana kallonsa, tsawa ya mata yace "Baxa ki bani amsa ba
sai na baki dirty slap?" Tsorata tayi ganin babu wasa fuskarsa, kamar xata fashe
masa da kuka tace "Ni fa Yaya...." Fixgota yayi lkci daya idanuwansa suka canxa
yace "Ke fa me?" Kasa cewa komai tayi, ta hadiye abu da kyar tace "Don Allah kayi
hakuri, ni bani na basa hannun...." Bai jira ta karasa ba ya buge mata baki da
karfi, Ta kai hannunta da sauri bakinta, lkci daya hawaye ya kawo idanuwanta, cikin
husky voice yace "I am making you this promise... babu abinda xai hanani gaya ma
Abban ki sooner or later...." ta wani gwalo ido a rikice tace "Don Allah Yaya kayi
hakuri wllh ba da gangan yayi ba shi ma bai sani ba" Bai san lkcn da ya kara buge
bakinta ba, tayi tsit hawaye na sauka idonta, yace "Wato ke yanxu kina ganin kin
girma kin isa tadi da maxa, har wani rawan jiki kike ki fita idan ya xo, har da jan
sa xuwa parlon ku ki ajiye masa nama a gaba Saboda kinga Inna na goya maki baya, to
bari ki ji abinda baki sani ba, as far as I Muhammad is concerned babu aure
tsakanin ki da mutumin nan, you had better stop wasting ur time and face ur study,
kamar yanda na xa6a ma Seeyama miji ke ma haka da kai na xan xaba maki mijin da ya
dace da ke, duk ki gama rawan kanki xaki sha mamaki na, wannan mutumin da kike gani
is just here to spoil and use you, ba so na tsakani da Allah yake maki ba, ki bar
ganin yana kashe maki kudi ki xata wai son Allah yake maki, lalata maki rayuwa xai
yi which I will neva allow, and let me give you this warning....." Ita dai hawaye
kawai take xuciyarta na bugawa tana kallonsa, "Daga yau kika sake tsayawa kusa da
motarsa sai na kusa sumar da ke wllh, duk karyar da xai maki ya maki a waya ba sai
ya sake xuwa kofar gida ba, idan kuwa ba haka ba a gaban daddyn ki xan xane ki sai
dai duk abinda Inna xata yi tayi..." Kuka kawai imaan take bata ce masa komai ba,
strictly yace "Am I clear?" Ta gyada masa kai da sauri, muryar Inna suka ji tana
cewa "Naga abinda ya isheni ni patuu na 6ata a gidan Mujaheed" sai kuma ta kwalo
masa kira, bude kofar Mujaheed yyi ya fita ya jawo kofar, Imaan ta durkushe a dakin
tana kuka a hankali, Inna na ganin Mujaheed tace "Alhmdllh, ni na xata 6ata nayi,
Toh ita kuma matar ina ta shiga, har kasa fa na sauka ban ganta ba, kada ta shiga
wani waje in shiga uku dama ga Bukar ya xama abun tsoro, ba da xuciya daya ya yarda
ta biyo mu ba" Mujaheed yace "Tana waje, muje ki ga dakin dake kasa" Inna tace "Na
waye dakin?" Yace "Baki" inna tace "Irin su Hansai da 'ya yanta knn idan sun xo"
murmushi yyi ya bude kofar parlon yace "Har ke ai" Bai jira cewarta ba ya fice. Har
garden sai da Mujaheed ya kai Inna ya xaga duk gidan da ita, tana kallonsa tace
"Toh ai tun yanxu ya kamata mu shiga gun makota a san juna kafin mu tare, ko ya
kaga?" Kallonta yyi ya dauke kai, tace "A'a ba xancen dauke kai ba yana da kyau in
san su su san ni, ko haka mutum xai ta xama ba jama'ah a gida, ai mutane Rahama ne"
Mujaheed yace "Sai ki jira idan kin ga dawowarki gidan" Inna tace "Wannan gaskiya
ne, to ni na shiga uku ban fa yi la'asar ba Mujaheed" yace "Toh mu je ciki kiyi"
parlon suka koma ya nuna mata dakin dake downstairs yace "Sai kiyi alwala a bayin
ciki kiyi sllhn" tace "Toh dakin su Hansai kenan" shi dai bai ce mata komai ba ta
wuce ciki, kallon agogo yyi sannan ya wuce sama, parlonsa ya shiga ya bude kofar
dakin, durkushe ya ganta inda ya bar ta har sannan tana kuka, tana ganinsa ta mike
tsaye, karasawa cikin dakin yyi, ta hadiye kukan da take ta sunkuyar da kanta,
takawa yayi har gabanta ya tsaya ta ki yarda ta daga kai balle ta kallesa, ya dago
kanta a hankali, ta kallesa sai kuma ta fashe da kuka ta juya masa baya, xagawa
yayi gabanta ta rufe fuskarta tana shessheka, d'an murmushi yyi, kamar baxai ce
komai ba sai kuma yace "ki dinga jin magana ta idan baki son na dinga sa ki kuka"
ta kara juya masa baya cikin kuka tace "Ni bana soo" xagawa ya kara yi gabanta ya
jawo ta kusa da shi, ta kuma fashewa da kuka, ya d'an hade rai yace "Toh baxa ki yi
shiru ba" kin cewa komai tayi, ya ja ta xuwa bathroom, ruwa ya bude yana kallonta
ta madubi a hankali yace "Wash ur face now" ta turo baki ta ki cewa komai, tara
hannunsa yayi ya debi ruwan ya dukar da ita ya shiga wanke mata fuskar, yana gamawa
ya ciro handkerchief dake aljihunsa ya fara goge mata ruwan fuskar, yana kallonta
ta madubi yace "Promise me xaki fara jin magana ta daga yanxu...." Kin cewa komai
tayi ya hade rai yace "I am talking to you" da kyar tace "Na ji" yace "Kin ji me?"
A hankali tace "Abinda ka ce" mayar da handkerchief din yyi aljihunsa ya juya ya
fita bathroom din, murguda baki tayi ta juya tana kallon kofar bayin. Parlor
Mujaheed ya xauna yana danna wayarsa har Inna ta fito dakin da ta shiga yin sllh,
tace "Wai Mujaheed ni fa ban ji motsin Imaan ba.... A rufa min asiri mu dubota"
Mujaheed yace "Tana sama ai" Inna tace "Toh ni dai mu je in ganta" bata jira
cewarsa ba ta nufi stairs ya mike ya bi bayanta, dakinsa ya shiga da ita suka ganta
tsaye jikin window waya kare a kunnenta, tana jin an bude kofa tayi saurin dauke
wayar daga kunnenta tayi tsuru tsuru, kallonta Mujaheed ya dinga yi, Inna tace "Toh
ke daga ganin gida sai ki shige dakin matar mutane ki xauna, jira xa ki yi Allah ya
kawo lkcn naki da Bulasawa ae" Juyawa Mujaheed yyi ya bar bakin kofar, Inna tace
"Toh fito masu a daki yi hakuri haka" imaan bata tanka ta ba ta nufi kofa gabanta
na faduwa ta fita, Inna ta bi bayanta, balcony suka tadda Mujaheed suna fitowa ya
kulle gidan da makulli ya tafi gun motarsa, imaan bata yrda ta kallesa ba ta bude
front seat ta shiga kamar munafuka Bayan Inna ta shiga baya, ya ja motar ya fita
compound din yyi ma Mai gadi sallama. Suna hawa saman titi Inna tace "Ni dai
Mujaheed da dai in samu kaza in siya, naji raina na so sosai" Mujaheed yayi parking
dai dai gun masu gashin kazan da ta gani ya sa tayi magana, tana washe baki tace
"Allah dai ya maka albarka" Bai ce komai ba sai ma jinginar da kai da yayi da
kujeran motar ya lumshe ido, Inna tace "Toh ko ta fita ta amso?" Ba tare da ya bude
idon ba yace "Ehh" inna tace "Toh guda nawa?" Jin bai ce komai ba Inna ta gyara
xama tace "Ko guda uku ai yyi, Ni daya ita daya, yan sa ido kuma sai in kacalcala
masu daya" Mujaheed yace "Ohkk" Inna tace "Yi maxa ki sauka imaan, kice masu su
xabo manya don Allah na tsohuwa ce kuma ba miji gareni ba" Imaan ta bata fuska ta
juya tana kallon Inna, inna tace "Naga Ikon Allah, ko in sauka da kaina ne? Me
mutanen xa su maki ko ina ruwanki da su" bude motar Imaan tayi ta fita ta tafi gun
masu gashin, Mujaheed ya bude ido ya bi ta da kallo daga cikin motar, ba laifi
akwai maxa a gun, imaan na sunkuyar da kai ta amsa tambayar da masu wajen ke mata
tace "Guda uku" tana ta tsaye har aka gama packaging kajin a leda daban daban ta
amsa ta nufi gun mota ta bude back seat tana kallon Inna tace "Wai dubu hudu da
dari biyar" Inna tace "Toh ni xa ki gaya ma? sai ki gaya ma me siyan ai" Ta madubi
Mujaheed ya kalleta yace "Waye me siyan ban da ke?" Inna ta gwalo ido tace "Ban
gane ba" ya buda ido sosai yace "Ko sisi bani da shi, ban fito da kudi ba" Inna ta
saki salati mai tsayi tana xaro ido tace "Nima ko sile ban fito da ba Mujaheed"
Mujaheed ya daga kafada yace "Sai ki san abinda xaki ce masu" Inna ta kara sakin
salati tace "Yau babu lafiya ni patuu an kacalcala kaji uku ba kudi" shi dai
Mujaheed bai sake ce mata komai ba, ta kalli Imaan da xaro ido tana kallonsu, Inna
tace "Maxa maida masu tsiyar su kice basu da girma an fasa siya, maxa koma" Imaan
ta wani xaro ido tace "Iyyee, bayan an yanyanka wllh ni ba inda xan je" a fusace
Inna tace "Da aka yanka ci muka yi? Ni naga abinda ya isheni, ki juya ki mayar masu
kayansu ba mu da halin biya" Imaan duk ta rikice barin yanda taga duk mutan wajen
na kallonsu tace "Na shiga uku, wllh Inna baxan iya komawa dubi fa maxa a wajen da
yawa" jaraba Inna ta dinga yi inda take shiga ba nan take fita ba tace "Mazan banxa
maxan hofi ina ruwanmu da su bamu da kudin biyan kaji..." wani gentleman dake xaune
wajen ne ya taso ya iso gun motar yana kallon Imaan yace "Lafiya kuwa?" Inna tace
"Ina fa lafiya yaro an kacalcala kaji uku ba kudin da xa mu biya, nace ta mayar
masu tsiyar su shine take kokarin tara min jama'ah wllh ko amsar ledan ma ni ban yi
ba balle inji kamshin naman ciki, Toh a kan meye baxa su amsa ba? Dama haka ake
yi?" Murmushi kawai mutumin yake yana kallon Imaan yace "Kazan guda nawa ne?" Da
sauri Inna tace "Gudu uku ne wllh, daya nata daya nawa, daya na yan sa ido a
gida..."
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

Hannu ya sa a aljihu yana kallon Imaan, Mujaheed ya bude motar ya fita gun masu
gashin kajin ya fiddo dubu biyar ya mika masu, daga Inna har mutumin da imaan bin
sa da kallo suka yi, Inna tace "Kaga katon banxa ko? Ce mana yyi ba shi da kudi fa
har sai da ya bari duniya ta gama sanin abinda muke ciki sannan ya fita wani zokai
zokai da shi xai bada kudi, Toh Allah ya saka min kunyata ni da ya so yi gaban masu
kaji da tona min asiri da yyi a gabanka" Dariya mutumin ya dinga yi yana kallon
Inna da ta tsuke fuska tana kallon Mujaheed, imaan ta kalli mutumin gabanta ta
mayar masa da kudin da ya mika mata tace "Mun gode" Yana murmushi yace "Don't
worry...." Dawowa Mujaheed dake kallonsu yyi ya amshi kudin hannun imaan ya kamo
hannun mutumin ya saka masa a ciki yace "Thanks for ur concern" daga haka ya bude
mata front seat yana kallonta, ta sunkuyar da kanta ta shiga ya rufe motar, ya xaga
ya shiga motar ya tada ya bar wajen. Inna tace "Ni dai duk wanda niyyarsa ya
kunyata ni a duniya Allah ya min kantangar karfe da shi, kuma ya saka min" Shi dai
Mujaheed bai tanka ta ba har suka isa gida. Shirye shiryen biki aka shiga yi a
gidan ba kama kafar yaro barin bangaren Umma da kawayenta, ji take kamar an mata
albishir da aljanna xata aurar da first and only son dinta xuwa ga 'yar masu kudi
ba na wasa ba, shi ko gogan kamar ba shi xai yi aure ba babu Shirin da yake, idan
ya fita aiki tun safe dama sai dare xai dawo don kawai bai son participating a
shirin da ake a gidan, shi gaba daya bai fi sau uku suka hadu da Safeenar ba ma,
kuma duk Umma ke tilasta sa sai yaje, ko da wasa bai taba dialing lambar Safeenah
don kansa ba sai idan yayi missing call dinta, a rana kuwa tana kiransa fiye da sau
goma, shi kansa mamakin irin son da take masa yake duk da yasan dole ta fahimci fa
baya yinta amma duk class dinta bata nuna ta damu ba sai kara shige masa take. Tun
ranan da Mujaheed yyi ma Imaan warning ko da wasa bata son Sadeeq ya xo kofar
gidansu sai dai waya amma abinda ke bata mamaki yanda taga shi ma bai damu ya xo ba
kamar da, da kusan kullum sai ya xo, sai dai suna kusan raba dare suna waya da shi
cikin duvet yanda Ammi baxata ji ba, Duk Friday day kuma sai ya aiko wani worker
din gidansu gun Inna ya kawo mata sako, Imaan dai ta tasan soon Mujaheed xai yi
aurensa ya kara gaba sai taga ta yanda xai hanata tsayawa da Sadeeq kuma. Yau
Friday da ya kama saura sati daya bikin Mujaheed da Safeenah Imaan ta fito daga
dakinta ta shiga na Ammi, durkusawa tayi kusa da gado tana kallon Ammi tace "Ammi
xan wuce yanxu" Ammi tace "Toh na dai gaya maki kar ki dade imaan" tace "Wallahi
baxan dade ba Ammi" Ammi tace "Toh ki gaisheta Ina mata ya jiki" Imaan tace "Toh
xata ji" mikewa tayi ta fita daga dakin ta shiga kitchen ta dauko wani leda mai
dauke da can malt ta fito parlor ta dau jakarta sannan ta fita gidan, kamar mai
tausayin kasa ta isa bakin titi bayan few minutes ta samu adaidaitan da xai kai ta
GRA, tafiyar kusan minti ashirin suka yi, suka shigo gate din layin as usual ko ina
tsit sai haushin karnuka, dai dai gate din kantamemen gidan Imaan ta sa mai adai
daitan ya tsaya ta sauka ta basa kudin tana kallon masu gadi dake xaune bakin gate
din gidan, gaishesu tayi daya daga cikinsu yace "Wa kike nema?" Tace "Mariya" Mai
gadin yace "Toh ki kirata" shiru tayi tana kallonsa don kwanaki da dadewa da ta xo
ae basu mata tambayar komai ba, ba musu ta fiddo wayarta a jaka ta shiga Kiran
Mariya, Ba a dau lkci ba sai ga Mariya ta fito gidan, Rungume imaan tayi tace
"Welcome frnd" tana kallon masu gadin tace "Kawata ce duk ranan da ta xo ku bar ta
shigo babu interrogation" bata jira cewarsu ba ta ja hannun Imaan cike da farin
cikin ganinta suka wuce ciki, Imaan tace "Dama kin ma ji sauki koh?" Mariya ta
marairaice tace "Yau fa nayi getting self dina" Imaan na murmushi tace "Toh Allah
ya kara lafiya" sai da ta fara kai Imaan dakin Mahaifiyar ta ta gaisheta sannan ta
ja ta xuwa makeken bedroom dinta, imaan ta xauna tace "Siblings din ki fa?" Tana
fiddo ruwa da lemo a fridge dinta tace "Sun fita da Yaya Annur shan ice-cream
kinsan yau Friday" murmushi kawai Imaan tayi, Mariya ta ajiye mata drinks din tace
"Me xa ki ci, akwai yam with sauce, cous cous with sauce, or kin fi son snacks?"
Imaan ta girgixa kai tace "A'a na ci abinci a gida" Mariya ta harareta tace "A'a ni
dai sai kin ci wllh" Imaan tayi dariya tace "Bayan nace maki na koshi, Ni la'asar
kawai xan yi" Mariya ta nuna mata bathroom dinta tace "Kiyi alwala ga bathroom
kafin ki fito xan kawo maki abincin" bata jira cewar Imaan ba ta fita da sauri,
Murmushi imaan tayi ta mike ta cire Hijab din jikinta ta ajiye ta shiga bathroom
din, tana gama alwala ta fito dai dai nan aka bude kofar dakin, still tayi tana
kallonsa, kamar yanda shi ma ya tsaya yana kallonta, juya masa baya tayi da sauri
tana xaro ido....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

41.....

Sadeeq yayi murmushi a hankali yace "But you didn't tell me you where coming here
da muka yi waya daxu" Ta dau hijab dinta ta saka still bata juyo ba tace "Ae ba
wajen ka na xo ba" murmushi kawai yake yana kallonta, Mariya ta iso bakin kofar
rike da tray din abinci tace "Ya Sadeeq Aunty na neman ka fa" ya kalleta yace "Har
kin ji sauki kenan" dariya tayi tace "Ehh mana bayan alluran da ka sa aka min, Kuma
ga kawata ta xo, Hope yau dai ka tuna ta" Ya langwabar da kai yace "Bayan ta ki
juyowa ma in ga fuskarta balle in san wacece" Mariya ta wara ido ta kalli Imaan da
ta ki juyowa da gaske, ta yi dariya ta karasa cikin dakin ta ajiye abincin hannunta
ta isa kusa da Imaan ta juyota suna facing Sadeeq tace "Toh ka gane ta yanxu?"
Shafa kai yayi yana cute smile dinsa yace "Anya.. wani anguwar take? Na taba
ganinta ma kuwa?" Imaan bata san lkcn da tayi murmushi ba ta sunkuyar da kanta,
Mariya ta bata fuska tana kallonsa don da gaske bata ji dadi ba, Sadeeq ya wara
manyan idonsa yace "Toh Sannu da xuwa kawar Mariya, duk da dai ni ban gane ki ba"
daga haka ya juya ya rufe masu kofar, duk yanda Mariya tayi forcing din Imaan ta ci
abincin da ta kawo mata kin ci tayi wai ta koshi, ruwa kawai ta sha shi ma sip
daya, Mariya da gaba daya bata ji dadin kin cin abincin da Imaan tayi ba tace "Dama
ki dau drinks dinki ki koma da su bana so da gaske" dariya kawai Imaan tayi ta mike
tace "Sai ki ba su Hafsat idan sun dawo, ni dai tashi ki rakani" Mariya tace "Bayan
kin walakanta ni xa ki ce in raka ki" Imaan na murmushi ta nufi kofa tace "Toh ni
fa na ci abinci a gida nace maki Mariya" Mariya ta mike ta bi bayanta suka fita
dakin tace "Toh mu je ki yi ma Aunty sallama ya na iya da ke, nima dai ko ruwa kika
ban idan naje gidan ku baxan sha ba" Imaan ta kalleta ta gefen ido tana murmushi
suka shiga parlon mum dinta, Sadeeq na parlon tare da mum din nata a xaune, Imaan
ta durkusa kusa da kujera tace "Aunty xan tafi" Mum din Mariya tace "Da wuri haka
Imaan, toh Ina xuwa" tashi tayi ta tafi dakinta, Imaan ta sata kallon inda Sadeeq
yake taga kallonta yake, ta dauke kai da sauri, Mariya tace "Ya Sadeeq yanxu fa su
ya Annur xa su iya dawowa basu kawo min komai ba ko?" Yace "Toh ki kirasu mana"
Tace "Toh don Allah kira min su ta wayarka, I can't imagine me not eating shawarma
today" yace "Wayana na can gida" tashi tayi ta bi mum dinta daki don daukan wayarta
ta kira step brother din nata, Sadeeq na kallon Imaan yace "Me yasa baku xo tare da
kaka ba?" Ta dai yi murmushi bata ce komai ba, Aunty ta fito rike da leda ta ajiye
kusa da Imaan tace "Ki gaida min mum din ki kinji Imaan" a hankali Sadeeq yace
"Aunty ita ce fa warce nake yawan baki labari a kai...." Aunty ta kalli Imaan
sannan ta kallesa da mamaki tace "Imaan din kuma?" Yana murmushi yace "Sure..."
Sake baki tayi tana kallonsa, ya shafa kansa yace "Dama nace maki ba ma sai na kawo
maki ita ba da kanta xata xo wataran ki ganta" Imaan taji kamar kasa ya bude ta
shige don kunya, ta kasa dago kanta ta kalli Aunty, Aunty tace "Ikon Allah, wai da
gaske kake don Allah Sadeeq" Yace "Gata ki tambayeta, but aunt this is our secret
ko Mariya kar ki gaya ma plss Aunty, you know Mariya talks a lot...." Dariya kawai
Aunty tayi ta xauna tace "Ikon Allah, Toh Allah ubangiji ya sanya alkhairi, yayi
xabi na gari..." Yace "Ameen" Mikewa yayi yana kallon Imaan yace "Let me drop you"
da sauri ta girgixa kai sai dai bata ce komai ba, Aunty tayi dariya tace "Aa ki je
dai ya ajiye ki gida Imaan, ki gaida mutanen gidan kin ji, Allah maki albarka..."
Sadeeq na murmushi ya nufi kofa ya fita, Aunty na kallon Imaan tace "Imaan idan ma
kina da doubt a kan Abubakar a da, tohh stop that now kinji daughter, Sadeeq na son
ki fiye da yanda kike tunani, I was so surprise da naji yace min ya sami yarinyar
da yake so da aure yar Nigeria, coz ni nasan waye Sadeeq, I know him fiye da uwar
da ta haifesa ma, kuma wllh duk jinsa nake ba wai na yarda ba, har gajiya nake da
jin labarin ki a bakinsa, But plss kiyi kokarin kame kanki ki kare martabar ki na
'ya mace, am not saying this bcos Sadeeq is bad or anything of such, A'a Ina gaya
maki haka ne a matsayina na uwa, ko Mariya iyakar shawarar da xan bata kenan...."
Imaan dai ta kasa dago kanta, fitowar Mariya yasa Aunty tayi shiru, Aunty na
kallonta tace "Ki rakata compound Sadeeq xai ajiyeta gida yanxu, he is waiting for
her" Imaan ta mike tayi ma Aunty godiya cikin sanyin murya ta fita, Mariya ta dau
ledan da Aunty ta ajiye mata tace "Mun gode Aunty" daga haka ta bi bayan Imaan da
sauri, Mariya ta bata fuska ganin bata ga Sadeeq a bangarensu ba, tace "Kai ya
Sadeeq maimakon ya dau motar dake nan yanxu sai mun bi sa har can" ita dai Imaan
bata ce komai ba, haka suka dinga tafiya a lafcecen compound din xuwa bangarensu
Sadeeq, Building din ya kusa biyun nasu Mariya, Kai kana gani kasan an rasa yanda
xa ayi da Naira kuma, Motocin dake parking spaces din wajen sun yi goma ko wanne
kuma ya wuce a kirasa mota sai dai Ride, ni kam nace don ma Inna bata xo taga gidan
ba... Ai da gobe gobe xata sa Bukar da Ahmadu gaba ta tada bala'i a daura auren
Imaan da Bulasawa... Lol, Sadeeq na xaune cikin daya daga motocin parking space din
idonsa a kan Imaan dake tahowa tare da Mariya, irin kallon da yake mata yasa Mariya
ta kalli Imaan sai dai bata ce komai ba, ana haka aka bude gate din gidan wani ride
ya shigo compound din, Mariya tayi ma motar kallo daya ta dauke kai, Drivern yyi
parking aka bude back seat, wata da baxata wuce shekaru hamsin ba ta sakko motar
cikin shiga ta alfarma, tun daga kunnenta, wuyarta, finger, da wrist duk gold ne,
tun da Imaan ta kalleta sau daya ta gane Mahaifiyar Sadeeq ce, Mariya tace "Sannu
da dawowa Mami..." Sama sama matar ta amsa, Imaan ma ta gaisheta, ba tare da ta
kalli Imaan ba ta amsa, tana kallon Sadeeq tace "Fita xaka yi yanxu Abba..." Ya
fito daga motar yace "Welcome back Mami" tace "Yauwa..." Yana shafa kansa yace
"Aunty tace in ajiye bakuwarta a gida..." Daga sama har kasa ta kallesa bata dai ce
komai ba ta nufi entrance din babban gidan, ya bi ta da kallo, can yace "Mami xa a
maki wani abun ne?" ba tare da ta juyo ba tace "Noo ka tafi inda aka aike ka, ka
sameni parlona dai idan ka dawo, is Annur back?" yace "I don't think so" Front seat
ya xaga ya bude ma Imaan yana kallonta, Mariya ta ajiye ledan hannunta a bayan
motar ta xaga gun imaan tace "Plss kice ma Ammi ina gaisheta kin ji" Imaan ta shiga
motar tana murmushi tace "Toh xan gaya mata" Sadeeq ya tada motar suka fita
compound din Mariya na daga masu hannu, Sai da suka hau saman titi murya can kasa
yace "Nayi missing din beautiful face din ki two days Imaan" Murmushi kawai tayi,
yace "ke ko naga ma baki damu da rashin xuwa na ba koh? You won't even understand
what I am going through now" Ta kallesa a hankali tace "I thought you are busy this
days ne shi yasa" girgixa kai kawai yayi, bayan kusan minti biyar yace "My birthday
is coming soon...." Ta kallesa tace "When" yace "7 days from today in sha Allah"
shiru tayi don ranan daurin auren Mujaheed kenan, can tace "Toh Allah ya kai mu
lafiya" yace "Anything for me?" Murmushi tayi tace "Me kake so?" Murya can kasa
yace "Ke nake so Imaan" ta wara ido tace "Ni kuma" ya gyada kai yace "I don't
know... i just have this urge of wanting to be with you, sai yanxu nake ganin nisan
kwanakin da suka rage... I want you by my side as my wife" kasa kallonsa tayi ta
kuma kasa cewa komai, ya kamo hannunta yace "Kin yi shiru" kwace hannunta tayi a
hankali still ta ki cewa komai, parking taga yayi ta juya tana kallonsa, yayi kasa
da murya yace "I am thinking of meeting grandmum, ko xata kara yi ma su Abba
magana" Imaan ta kallesa da sauri tace "Maganan me?" Yana kallonta yace "Su yi
hakuri su bani ke any time from now, wllh har professor xan iya barinki ki xama a
gidana" Imaan ta girgixa kai kamar xata yi kuka tace "A'a ni dai, bayan ga abinda
daddy na yace" Shiru yyi yana kallonta, cikin sanyin murya yace "Toh shikenan i
will continue waiting and having patient in sha Allah" Driving ya ci gaba da yi,
sai da suka kusa layinsu yace "My frnds are throwing a birthday party for me, kuma
ke ce babban guess a wajen ranan" ta wani xaro ido tana kallonsa yace "Yea, don't
turn down my offer baxan ji dadi ba....." Kasa cewa komai tayi yana shigowa layinsu
gabanta yyi mugun faduwa, what if Mujaheed na waje yanxu haka, kafin ya isa kusa da
gate dinsu da sauri tace "Kawai ma ka ajiye ni a nan ba sai ka karasa can ba" ya
kalleta yace "Why?" Ta hadiye abu da kyar tace "Nothing" Bai ce komai ba ya kai ta
har bakin gate din ta fara kalle kalle kamar munafuka ta bude motar ta fita yace
"Wait Imaan" tsayawa tayi ya juya ya dauko ledan da Mariya ta ajiye mata, Mika mata
yayi ta amsa tace "Nagode sai anjima" daga haka ta shige cikin gidan da sauri har
hakan ya basa mamaki ya bi ta da kallo, tana shiga kuwa ta kulle gate din, sai da
xuciyarta ya kusa shigewa cikinta ganin Mujaheed da Yusuf a compound din, Yusuf na
xaune kan farin kujera Mujaheed kuma da alama gate xai fita amma sai kallonta yake,
bata tsaya wani tunani ba ta fasa wani ihu ta sake ledan hannunta ta durkushe wajen
tana yarfe hannu tana kiran Ammi, Mujaheed ya karasa inda take da sauri yana kallon
kafarta yace "Me ya faru??" Ta kamo hannunsa tace "Wayyo Yaya kafana ban me ya same
shi ba..." durkusawa yyi ya daga dogon hijab din jikinta yana kallon kafar, ta
gefen ido ta dinga satan kallon kasan gate taga ko Sadeeq ya gama reverse.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah


Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788

42....

Imaan ta kwace kafarta a hannunsa bayan ta ga Sadeeq ya wuce tana turo baki a
hankali tace "Ni ya ma daina, dama gurdewa kawai nayi" bata jira cewarsa ba ta mike
da kyar, Yusuf dake tsaye shi ma ya iso wajen yyi murmushi yace "Dama ba wani ciwo,
ke dai kika san abinda kike boyewa a waje" Mujaheed ya kalleta ya kalli gate da
sauri, ledan da ta jefar ya dauka ya bude yana kallon abinda ke ciki, sai kuma ya
nufi gate din.... Tana ganin haka ta dau ledarta da takalmanta ta wuce apartment
dinsu da sauri tana waigan Mujaheed, Yusuf yyi murmushi ya koma ya xauna, Parlor ta
tadda Ammi xaune, Ammi ta amsa sallamarta tace "Meye kuma kike sa min makulli a
kofa" ta xaro ido tace "Ohh na manta, nayi xaton dare yyi..." Still dai bata bude
kofar ba tana murmushi ta karasa cikin parlon ta xauna tace "Ammi Sannu da gida"
Ammi tace "Yauwa, ya mai jikin?" Imaan tace "Da sauki, Mum dinta tace in gaishe ki,
ta ma bani wannan" tana fadin haka ta ajiye ledan a kusa da Ammi, Ammi tace "Toh
Allah ya amfana" mikewa Imaan tayi ta wuce daki har sannan xuciyarta bai daina
bugawa ba, yanxu da Mujaheed ya ga Sadeeq ya xata yi yau. Tun bayan da ta idar da
sllhn magrib Ammi ta ce ta dau abincin Inna ta kai mata gabanta ke faduwa, har
claiming ciwon kafa tayi duk don Ammi ta kira Maimoon ta kai ma Inna abincin amma
Ammi tace ita dai xata daure ta kai a hakan, tana goge guntun hawayenta ta dau
abincin ta fita a sanyaye, ita kanta bata gane wani sabon tsoron Mujaheed da ya
diran mata yanxu ba, a hankali ta bude kofar parlon Inna ganin takalmin da bata dai
san ko na waye ba bakin kofar, ta ajiye abincin a nan bakin kofa Inna na tambayar
wani munafukin ne amma tuni ta juya da sauri har tana tuntube ta koma part din su.
Washegari Saturday karfe takwas saura Imaan ta fito bangarensu cikin shirin
islamiyya, duk gaba daya a tsorace take har Ammi ta lura da hakan amma da ta
tambayeta damuwarta sai cewa tayi ita bayanta ke mata ciwo, Ammi ta sa ta sha
magani sannan ta fita, parking space ta dinga lekawa ko xata hango motar Mujaheed,
ganin motar tasa yasa ta ki jiran su Maimoon ta nufi gate da sauri, ta gwammace ta
tafi bakin titi ta samu adai daitan da xai kai ta islamiyyar. Suna jiran drivernsu
bayan an tashi islamiyya Maimoon tace "Imaan wai me yasa kika ki jiran mu daxu?"
Imaan ta tabe baki tace "Salon kawai ku 6ata ma mutum lkci mu yi ta yin latti ana
xane mu, naga baku fito ba ni kuma bana son inyi latti shi sa nayi wucewata" Rahma
tace "Har akwai wanda ya kai ki saka mutum yin latti? Kullum sai mun yi ta jiran ki
bakin mota kafin ki fito, daga ace bayan ki ya rike sai ace kafar ki ya rike, to
daga yau ma kar ki sake jiranmu kiyi wucewar ki" Imaan ta kalli Maimoon tace "Kin
ga dai ba da wannan matar nake magana ba ko, ki gaya mata ba ruwanta da harkata
tayi ta kanta ta kyaleni..." Rahma tayi dariya tace "Ehh gwara in kyaleki kiji da
ciwace ciwacen ki kam....." Maimoon ta kalli Rahma tace "Haba meye haka Rahma?"
Rahma ta watsa mata wani kallo tace "Sai dai ki tambayeta meye haka, ko ni sa'arta
ce aka gaya mata??" Tsaki tayi ta wuce gun motar gidan su da yyi parking dai dai
lkcn, Ummi ta ja tsaki tace "Mutum sai neman fitina kawai, ana taba ta kuma lalura
ya tashi a shiga uku, to dama wa xai taba sauran ciwo idan ba tsautsayi ba ma" tana
fadin haka ta wuce ta shiga mota ita ma, Maimoon ta kalli Imaan dake kallonsu tace
"Ki rabu da su kiyi hakuri" Imaan bata ce komai ba ta bude front seat ta shiga
Maimoon ma ta shiga back seat... Suna isa gida driver yyi parking Imaan ta bude
motar ta fita bata xame ko Ina ba sai part din Inna, Inna na xaune parlon tana hada
kwadon rama Imaan ta shigo ta xube nan kan kujera ta fashe da matsanancin kuka,
Inna ta tura roban gabanta tace "Auzubillahi, me ya sami Aishar?" Cikin kuka Imaan
tace "Ko ba su Rahma da Ummi bane daga Ina magana da Maimoon suka fara xagina har
da ce min sauran ciwo...." Mikewa Inna tayi ta rufe roban kwadonta ta dau gyalenta
ta nufi kofa ta fice, Imaan ta dinga kuka har da shessheka, can dai tayi shiru ta
goge idonta ta shiga kitchen ta dauko wani plate ta debi kwadon da Inna ke hadawa
ta fice a parlon. Babu abinda Inna ta mance bata xaxxaga ma Umma dake dakinta a
xaune tare da su Ummi dake mata tsarin abinda ya faru tsakaninsu da Imaan, Inna na
huci tace "Kuma in sha Allahu sai kinga sauran ciwo a jikokin da xa a haifa
maki..." Da sauri kuma tace "Astagafirullah, jikokin ki ai na Ahmadu ne, to in sha
Allahu sai kinga sauran ciwo a dangin ku.... Kuma a kawo maki riko kiyi ta fama,
duk wanda ya sake sa min jikata a bakin duniya Allah ya isa ni dai, Allah ya isa,
kuma bari Ahmadun ya dawo...." Tana fadin haka ta fice. Imaan na shiga apartment
din su ta tadda Ammi na ta girke girke, gaisheta kawai tayi ta wuce daki, tayi
wanka tayi sllh sannan ta shirya ta fito parlor, kitchen ta shiga gun Ammi dake
hada drink din Zobo tace "Ammi jirgi daddy xai biyo ko train?" Ammi tace "Ce maki
yyi xai dawo yau?" Imaan ta xaro ido tace "Naga kina girki ne ai" Ammi tace "A'a
mamar ku ce dai ke hanya...." Imaan tace "Mama Hadiza?" Ammi tace "Ehh sun ma kusa
landing Ina ga" Imaan ta wara ido tace "Shine Inna bata gaya min ba?" Ammi tace
"Ita ma bata sani ba shi yasa ban gaya maki tun jiya ba kar ki je ki gaya mata don
ba control gare ki ba" Murna Imaan ta dinga yi tace "Da su Maryam xa ta xo in gansu
plss?" Ammi tace "Da Maryam kadai suka taho" Imaan tace "Toh wa xai je daukota a
airport nima xanje plsss" Ammi tace "Mujaheed Daddy yace yaje ya daukota" shiru
Imaan tayi bata ce komai ba, can ta dau plate ta bude abinci xata diba. Hudu na yi
Mujaheed ya tafi airport dauko small mum din tasa da autar ta, tun da suka kamo
hanyar gida Maryam ke tambayar sa Imaan da turancinta dake kala da na turawa, yyi
murmushi yace "Tana nan, tsayin ku daya sai dai ita bata jin magana..." Maryam ta
kyalkyale da dariya tace "Ni duk na kagu in ganta wllh, muna fa vid call da ita
once in a while" Mujaheed yace "Ae xa mu je ki ganta" Mama Hadiza tace "Amma dai
yanxu ta ji sauki sosai koh?" Yace "Ehh mama da sauki sosai" Hadiza tace "Toh
Alhmdllh haka Yaya Sadeeq din yace min, Toh in ji dai xa a kawo min amaryar mu
gaisa kafin biki..." murmushi kawai yyi bai ce komai ba, tace "Au baxa ka kawota ba
kenan" yar dariya yyi yace "Toh xa a kawota in sha Allah mama" Mama Hadiza tace
"Toh da dai ya fi, kuna ta dai hakuri da tsufan Inna koh?" Mujaheed yace "Mu wllh
da ma ki tarkatata ku koma tare mama" dariya Mama Hadiza tayi tace "Baka da kirki
Mujaheed, ita uwar tawa kake cewa in tarkata?" Yace "Wllh mama duk ta addabi kowa a
gidan..." Mama Hadiza tayi murmushi tace "In sha Allahu nan da wata hudu ma xa mu
dawo Nigeria gaba daya sai in dauke uwata ta dawo wajena sai in ga ta inda xa ku
dinga gajiya da ita" Mujaheed yyi dariya yace "Wllh baxata yarda ba, xata gwammace
tayi ta xama tana dagawa Ahmadu da Bukar hankali" Mama Hadiza tayi dariya tace
"Baka da mutunci wllh Mujaheed" parking Mujaheed yyi a parking space din su bayan
sun isa gidan, Mama Hadiza tace "Allah sarki, rabona da gidan nan shekara uku
kenan, anjima idan na huta da Magrib sai ka kai ni gidan Seeyama" yace "Toh Mama
Allah ya kai mu" part din Abba Mama Hadiza ta fara shiga tare da Maryam don gaisawa
da Aunty da Umma... Bata wani dau lkci a part din ba ta fito tare da Aunty, Umma
dama tun bayan da suka gaisa ta shige daki ta kulle, Mama Hadiza na kallon Aunty
tace "Rukayya dai na nan da rashin kirkinta har yanxu koh?" Dariya kawai Aunty
tayi, Mama Hadiza tace "Toh yayi kyau ta ci gaba, har ni xata walakanta ta shige
daki sbda bata da mutunci" ita dai Aunty bata ce komai, suka shiga part din su
Imaan, Imaan ta fito daki jin muryar Maryam ta rungume ta cike da murnan ganinta,
Ammi na kallon mama Hadiza bayan sun gaisa tace "Toh Ina jakar? Ko ba nan dama xa
ku sauka ba" Mama Hadiza tace "Yana cikin mota Mujaheed bai fiddo ba" Ammi ta kai
ta har bedroom dinta don ta kintsa, Aunty dai tayi masu sallama ta koma.
Maryam na idar da sllh bayan ta ci abinci tayi wanka dakin Imaan, suka dinga
hira... Ganin Magrib ya kusa Imaan tace "Plss mu je ki ba Inna surprise kawai ta
gan ki" Maryam tace "Hope ta daina xagin mutane dai yanxu" Imaan tayi dariya sosai
tace "Sai dai bata ga abinda xata xaga ba, ke dai mu je" A tare suka fito dakin
suka wuce part din Inna ba tare da sun sanar da su Ammi dake bedroom ba, Inna na
bakin tap suka iso bangaren nata, ta daga kai tana kallonsu, Imaan dai sai murmushi
take, Inna tace "Waya wannan kuma kamar Zabiya?" Imaan ta fara dariya tace "Baki
ganeta ba Inna?" Inna ta ci gaba da wanke wajen tace "Ka dai ji wata magana wai ban
ganeta ba, yanxu ko uwata ce ta fito daga kabari idan ban ganeta baxan ce mata ban
gane ta ba, tun daxu nake durkushe a nan nake aiki babu mai taimakona, baki ji
bayana ba kamar ya balle in huta...." Maryam ta hade rai ta shige parlonta, Imaan
tace "Maryam ce fa Inna" Inna tace "Waye kuma Maryam" Dariya kawai Imaan take tana
kallon Inna, Inna tace "ita ce ta xama kamar zal6e?" Imaan ta xauna a balcony din
tana dariya, Inna ta tabe baki tace "Ku dai baku son gaskiya a gidan nan, yanxu da
ba don wannan yar albarkan Maimoon ta gaya min a boye ba daxu da baxan ma san
Hadiza xata xo gidan nan ba, Toh kuma kya taho min da yarinya tsigi tsigi kice
Maryam, Yar da aka haifa hannuna ce aka ce maki baxan gane ba, ni fa na mata wankan
farko kuma a gabana aka yayeta..." Inna ta tabe baki tace "Ni dai ba ruwana" Fitowa
Maryam tayi daga parlon ta yi wucewarta, Inna ta bi ta da kallo ta kyabe baki tace
"Ubansu dai ya cuce su ya hallaka su, ya kwashe su ya tafi kasar tsinannu yayi kaka
gida, toh tana ma jin hausar kuwa" Imaan dai ta kasa cewa komai sai dariya take,
Inna ta gama dauraye bakin tap din ta mike ta shige cikin parlonta tana cewa "Bukar
dai ya haifi jaraba, ba don naka naka bane ai ni bana bari a cuci Bulasawa a lika
masa ke ba, to banda haka ni sa'ar uwarki ce xaki xauna bakin kofa kina babbaka min
dariya kamar mahaukaciya?? ita ma Hadizar dama kada ta kuskura ta xo min nan xan
koreta tunda bata maida ni bakin komai ba, banda haka ta kamo hanya rai kwakwai
mutu kwakwai baxata gaya min ba in mata addu'a, wannan ba shawarar kowa bace illa
wannan mutumi Bukar don shi ne me irin wannan tunanin na marasu nutsuwa, Amadu baya
haka" mikewa Imaan tayi ta bar wajen ta koma part din su... Bayan magrib tare Abba
suka tafi gun Inna da Maryam, Inna na xaune parlon tare da Mama Hadiza da Mujaheed,
Inna na ganin Maryam ta washe baki tace "Yanxu nake rokon Mujaheed ya tashi ya nemo
min ke don tun saukan ku bamu hadu ba kin xo daxu ina gurje bakin pampo ke kuma
baki jira in gama ba kika yi wucewar ki" Maryam ta xauna ta gaisheta babu walwala,
Inna ta amsa da fara'a tace "Kun sha hanya, sai kawai naga kin kusa kamo imaan a
tsayi..." Maryam dai bata tanka ta ba, Mama Hadiza sai murmushi take, Abba ya gaida
Inna ta amsa tace "Ae gwara da ba a gaya min suna hanya ba Ahmadu da baccin kirki
ma ni baxan yi ba, amma da na gansu kamar daga sama ai yafi ko" Abba na murmushi
yace "Gaskiya ne" Mikewa Mujaheed yyi ya fita parlon Maryam ta bi bayansa, a jere
suke tafiya tace "Ya M.A kaga abinda Inna ta min daxu kamar bata taba ganina ba"
Dariya Mujaheed yyi yace "Xata maki fiye da haka ma, so take it off ur mind plss
haka nan take, ya karatu?" tace "Alhmdllh...." Ya kalleta yace "Hope baki kula
samari sai kin gama karatun" tayi dariya tace "Kai ya M.A, bayan ga Imaan ma tana
da saurayi, ta ma ce min xai yi birthday soon and his frnds will be celebrating it
for him, wai in bata shawarar abinda xata basa" Tsayawa Mujaheed yyi yana kallonta,
can yace "When tace maki birthday din?" Ta wara ido tace "I didn't ask her, mun ma
gaisa da shi a waya yace xai xo gobe ya gaisheni, his voice is cute..." Tana
murmushi ta kare maganar, Shiru yyi bai ce komai ba ya ci gaba da tafiya a hankali
tana biye da shi, Xaro ido tayi tace "Wait... Am I even suppose to tell you this??"
Yar dariya yyi yace "Me yasa kika ce haka?" Tace "Naga irin kamar you are
surprise.... Kila ma baka san tana da saurayin ba ni ce na maka revealing koh?"
yace "Yes.. boye mana take, Amma kar fa ki ce mata kin gaya min she won't be happy"
Maryam ta marairaice tace "Toh nima kar ka mata magana about it she won't be happy
with me...." Yace "Sure I won't" suna isa part din su Imaan tace "Am spending the
night here, ka ce ma su Maimoon, Ummi da Rahma su xo muyi hira plss" yace "Ohk xan
gaya masu" daga haka ya wuce, tafiya yake amma gaba daya abinda Maryam ta gaya masa
ne ke yawo a ransa... Wani murmushi yyi ya shiga sashin su.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

43....

Washegari da safe Imaan na kumbure kumbure ta gama shirin islamiyya bayan Ammi tace
baxata xauna mata a gida ba, Maryam ta sami Ammi a kitchen a hankali tace "Ammi don
Allah ki barta kar ta je yau, I don't have anybody to gist with idan ta tafi fa"
Ammi tace "Ga kakarki can ki je ku yi hiran mana" da sauri Maryam tace "A'a ni bana
son hirarta kawai tayi ta xagin mutane, nima ta fara xagina" Ammi tayi murmushi
tace "She is ur grandma dai" Maryam tace "Sure, pls Ammi kin yarda kar taje?" Ammi
tace "Karfe sha biyu xa su tashi ai, kuma sauka xa su yi soon Maryam, imaan ko
shakkar fashi bata yi shi sa nayi forcing dinta ta wuce" Maryam tace "Ohk then,
Allah ya kai mu 12 din" daga haka ta fita kitchen din, Imaan ta fito daki bayan ta
dauko jakarta ta nufi kitchen ta tsaya bakin kofa kamar xata yi kuka tace "Ammi na
tafi" Ammi tace "Breakfast din fa?" Ta girgixa kai tace "Ni sai na dawo" Ammi tace
"Oho cikin ki" Juyawa imaan tayi ta fita, Maryam ta rakata xuwa parking space, dai
dai fitowar Mujaheed da makullin mota a hannunsa, Maryam tayi masa murmushi tace
"Good morning ya M.A" ba tare da ya kalleta ba yace "Morning Maryam kin tashi
lafiya?" Tace "Sure.. Alhmdllh" Imaan dai tuni ta dauke kai, Maryam tace "Aiki xaka
fita ya M.A" yace "Noo, sai da yamma nake fita aiki during weekends" Tace "That's
nyc... Do you need my company?" Ya kalleta kamar baxai ce komai ba sai kuma yace
"Sure... if that will suit you" ta kalli Imaan tace "Alryt sweetheart xan raka Ya
M.A, ayi karatu da kyau a islamiyya" imaan ta kalleta tace "Ohk bye" tana fadin
haka ta saci kallon Mujaheed taga kallonta yake, da sauri ta dauke kai, Ya bude
motarsa ya shiga ya tada, Maryam ta xaga ta shiga gaba. Ko da Imaan ta dawo daga
Islamiyya karfe sha biyu Maryam bata dawo ba, Imaan na kallon Ammi tace "Ammi wai
tun da safe har yanxu Maryam bata dawo ba?" Ammi tace "Ehh wai sun fita tare da
Mujaheed koh?" Imaan ta tabe baki ta mike ta wuce dakinta. Bayan azahar tana gama
cin lunch ta tafi bangaren Inna, Inna na xaune parlor tare da Mama Hadiza, Imaan ta
gaida small mum din nata sannan ta gaida Inna da ta tsuke fuska, Inna ta amsa tace
"Ke kiji Hadiza da wani mummunan xance Imaan, wai duk abinda xa ayi na bikin
Mujaheed mai kyau ko mara kyau in saka ido kar in yi magana, Saboda ita bata da
tsoron Allah, bata son gaskiya xuciyarta ta kekashe, to me mutum xai min wanda
Allah bai min ba" Mama Hadiza tace "Ni dai ki fahimce ni Inna, idan ba mu fada maki
gaskiya ba kina da mai gaya maki ne, ba girman ki bane komai kika gani ki tanka a
tafi da ke a baki, Haba inna" Inna tayi mitsi mitsi da ido tace "An dade ba a tafi
da ni bakin ba, ni da bikin jikana ki dinga gaya min maganan banxa, ke kinsan
wahalan da nayi da Mujaheed kuwa, wllh wllh ko Rukayya bata da iko da shi a yanxu,
mutumin da yasa na dinga fada da jama'ah a anguwa yau ya kwale d'an wancan gobe ya
danne d'an wancan, da ma Allah ya rufa min asiri bai sa an min duka a anguwar ba
har Allah ya raba ni da anguwar? ke kinsan sau nawa na shirya na tafi makarantar su
Mujaheed fada da malamai kuwa... Kishiyoyina kuwa duk min dambatu da su a kan
Mujaheed, Sannan ace wai in xama kurma a bikinsa kamar uwata tace min je ki kya
gani? To wllh karya ake...." Mama Hadiza tace "Ba ace ki xama kurma ba amma ba
komai xa ki tanka ba, ba komai xaki shishshige ma ba, Allah na tuba Rukayyar da ma
in don ta nata ne bata son a shiga lamarin bikin, ji fa tasan don bikin takanas na
xo kasar nan amma tun sannu da xuwan da ta min jiya a bangarensu ban sake ganinta
ba, ace kuma tayi farin ciki da xuwana...." Inna ta kunduma ma Umma xagi tace "Ai
ba ita ke aurar da d'a ba nice nan mai aurar da Mujaheed kar ki ji komai, mu xuba
kuma a gani, Allah dai ya kai mu ranan da rai da lafiya, sai dai mu kwashi yan
kallo da ita a bikin nan idan kuma bata yi hankali ba dama baxata kwana gidan nan
ba ranan bikin" Mama Hadiza ta tabe baki bata dai ce komai ba, Inna tace "Haka
kawai, inyi wahala da shi a dinga gaya min maganan banxa" Imaan dai murmushi kawai
take tana danna wayar hannunta, sallama aka yi bakin kofar parlon, Imaan ta juya da
sauri jin muryan Sadeeq, Inna ta mike daga xaunen da take da sauri tana washe baki
tace "A'ahhh sannu da xuwa Bukar, kai ne da ranan nan... Bisimillah shigo abun
ka... Ba kowa daga ni sai Hadiza da Imaan" da gudu imaan ta shige dakin Inna,
Sadeeq ya shigo parlon kansa a kasa, Inna na washe hakora ta kalli Mama Hadiza dake
xaune kan kujera tace "Ke tashi ki basa waje ya xauna mana, sirkin ku ne" Sadeeq ya
bude ido yace "A'a kaka ga waje ai" Bai jira cewarta ba ya xauna saman carpet dake
shimfide, Inna ta nufi fridge ta bude ta kwaso ruwa uku da malt uku ta taho, Mama
Hadiza dai sai bin ta take da kallo cike da takaici, Sadeeq na kallonta a hankali
yace "Ina yini?" Mama Hadiza tace "Lafiya lau, Sannu da xuwa" Inna tace "Saurayin
Imaan ne, jira kawai yake ta kare sakandari ayi magana, d'an gidan Ahmad Bulasawa
ne mai gidajen man fetur a arewa, sunan yayanki garesa.... Baki ga kirkinsa ba, ni
dai tunda nake ban taba cin karo da mutum mai kirki da mutunta babba irinsa ba"
Mama Hadiza dai ta kasa cewa komai, Sadeeq dai ya sunkuyar da kansa sai murmushi
yake, Inna ta kwalo ma Imaan kira tace "Ji walakanci, to meye na gudu daga jin
sallaman bawan Allah, baxa ki fito ku gaisa ba, ba don ke ba a ina xa mu sansa"
Imaan da ta xauna saman gadonta ta turo baki ta ki cewa komai, Sadeeq na shafa
kansa yace "Dama baki na xo gaidawa kaka" Inna tace "Ahh toh madallah, Ka ganta nan
xaune...." Ta fadi haka tana nuna masa Mama Hadiza tace "Uban Imaan ne ya sha nono
ya bar mata, ita ce autata, yaranta hudu a duniya Allah yayi ma daya rasuwa, dayar
tayi aure tana can gidan mijinta a kasashen turawa, sai kaninta da ke karatu sannan
wannan yarinya Maryam da suka xo tare, sa'ar Imaan ce yarinyar kawai dai Imaan ta
fita tsayi, ita kuma Maryam din ta fi Imaan xama mace" Tagumi Mama Hadiza tayi tana
kallon uwartata, Sadeeq kam murmushi kawai yake kansa a kasa, Inna tace "Toh duk ba
wannan ba, kana da labarin bikin Mujaheed wannan Juma'ah me xuwa ne kuwa Bukar?"
Sadeeq ya kalleta yace "Ai kam bata gaya min ba kaka..." Inna ta saki salati ta
rike ha6a tace "Kaga fitina koh? Duk da dai ko ta gaya maka ko bata gaya maka xa
ayi bikin baxa a fasa komai ba amma ai da ta gaya maka, Toh ni dai na gaya maka
yanxu, bikin ranan Juma'ahn nan ne" Sadeeq yace "Toh Allah ya kai mu lafiya kaka"
Inna tace "Ameen dai, ai har ya kai ni gidan da xa su xauna da amaryar tasa ni da
imaan mun gani, baka ga gidan ba d'an madaidaici dai dai kafinsa dai, toh ba dai
laifi... ni dai nace Allah ya sanya albarka ai dai ya fi babu wai d'an agwai da
bak'in da" Sadeeq ya kasa daina murmushi nan ko dariya ne kawai ke cin sa, Takaici
yasa Mama Hadiza ta mike tana kallonsa tace "Toh Sadeeq nagode da gaisuwa Allah
yayi albarka bari in shiga can cikin gida" Yace "Toh Ameen mama, nagode" fita tayi
daga parlon, Inna tace "Toh ki ce ma Aisha don Allah tayi miyar shuwaka yau, naji
raina na so" Mama Hadiza dai bata ce komai ba, Inna tace "Don Allah Imaan ki rufa
min asiri ku fito ku gaisa, wannan ai kauyanci ne daga ganin saurayi ki shige daki,
ni ko lokacinmu ba a haka" Sadeeq yace "Ki kyaleta kaka" Inna tace "In kyaleta d'an
nan?" bata jira cewarsa ba ta mike xata shiga dakin, Imaan na ganin haka ta maxa ta
sa hijab dinta ta fito, Inna tace "Ki daina haka don Allah sai ayi tunanin goyon
kauye ce ke, nan ko a Habuja aka haife ki" Dariya Sadeeq ya fara yi imaan ta daure
fuska ta xauna saman kujera a hankali tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau, ya gida?"
Inna ta xauna tana murmushi tace "Gida Alhmdllh" kallonta Imaan tayi da sauri ta
wani daure fuska, can ta kallesa tace "Let me see you off, since you've
accomplished ur mission here today" Yana murmushi yace "I see why you don't want
the 3 of us together..." Inna dai sai washe baki take tana kallonsu tace "Ae ita ma
babban makaranta tayi, babu irin turancin da bata iya ba wllh" Mikewa Imaan tayi
tana kallon Sadeeq tace "Let go" Mikewa yayi trying hard not to laugh yace "Toh
kaka na gaishe da Mama da ke, ni xan koma" Inna tace "Ai mun gode da gaisuwa Bukar
Allah maka albarka...." Dubu goma ya ajiye mata tayi tagumi tace "Ni dai na shiga
uku Bukar baka gajiya??" kofa ya nufa yace "Ai ba yawa kaka, ayi hakuri" daga haka
ya fita don tuni Imaan ta fice daga parlon, sai da suka bar part din Inna Sadeeq ya
tsaya ya dinga dariyar da bai samu damar yi a parlor ba non stop, Imaan ta dinga
kallonsa kamar xata yi kuka, ganin yanda yake dariya seriously ta jingina da flower
tana ci gaba da kallonsa don bata taba ganin dariyarsa haka ba sai this very
moment, he looks more cute laughing, bata san lkcn da tayi murmushi ba her eyes
still on him, don kansa ya gaji ya dakatar da dariyar haka, a hankali tace "You
look cute while laughing" da sauri ta rufe fuskarta bayan ta fadi haka, ya kafeta
da manyan idanuwansa, kamar ta sani kuwa ta juya masa baya tana xaro ido, and he
felt like hugging her tightly to himself, ya dai yi murmushi ya sauke kansa kasa
praying in his mind Allah yasa xuwa wajensu Abba da xai yi tare da uncles dinsa in
few days time won't be a futile effort... Takun da suka ji a bayansu yasa duk suka
juya a tare, Mujaheed ne ke tahowa tare da Maryam, Sosai gaban Imaan ya fadi tayi
still inda take, tunda ya kallesu sau daya ya dauke kai, Murya can kasa Sadeeq yace
"Is she the Maryam?" Imaan ta gyada kai a hankali tace "Sure" Suna isowa inda suke
Sadeeq ya mika ma Mujaheed hannu, Mujaheed na kallonsa ya mika masa nasa, Sadeeq
yace "Ya aiki?" Mujaheed yace "Alhmdllh" daga haka ya wuce, Maryam ta gaida Sadeeq,
Yana murmushi yace "It's nice meeting you Maryam, hope babu gajiyan hanya yanxu"
Tace "Ba gajiya kam, kun fa dace da sis dita, Allah ya bar ku tare" ya wara ido
yace "Ameen, I love those last words of urs... Kuma dole sai na biya words din, you
say what ever you want ko menene idan kuma kin bar min xabi shikenan" ita dai
Maryam dariya kawai take
tace "Toh nagode Sadeeq" daga haka ta bi bayan Mujaheed da sauri, tana iskesa
murya can kasa tace "Wllh he is just too cute Ya M.A, Imaan is very lucky..."
Mujaheed bai tanka ta ba ya bude kofar parlon Inna ya shiga ta bi bayansa, tana
cewa "Nama san me xan ce Imaan ta basa for his birthday...." Kallonta yayi yace "Me
xaki ce mata.." ta kashe masa ido tace "That's our secret big Bro" Xaunawa yyi
saman kujera yana kallon Inna, Inna tace "Yanxu wannan yaron dake neman Imaan ya
fita, baka ga yanda ya dinga fada imaan bata gaya masa bikin ka ranan Juma'ah bane,
gaba daya bai ji dadi ba, Allah kadai yasan me Bulasawan da kansa xai baka, mutum
miloniya meye kuma baxai bada ba" a fusace Mujaheed yace "Sai dai ya baki ke da
kike bukata, amma ni bana bukata, kuma don Allah kiyi hakuri ki daina maganata a
gaban mutane bana so, ni abinda nake da shi ya isheni xaman duniya ba sai na hangi
na wani ba" Yana fadin haka ya fice daga parlon, Inna ta tabe baki tace "Uwarka
Rukayya ka gaggatsa ma magana ka fita ba ni ba wllh, ba abinda ya hada ni da kai
dama, kawai Ahmadu ne ya haifeka ni kuma na haifesa, Ni ban yi mamaki ba tunda
goyon Rukayya ce kai din ai, xaka yi fiye da haka" Maryam na dariya ta mike ta fita
a parlon ita ma, da daddare Imaan na fitowa daga wanka daure da towel tace "Wai ina
kuka je daxu da yaya tun safe" Maryam dake operating laptop tace "Wato kina wanka
hankalin ki na wajen ki fito kiyi tambaya" Dariya Imaan tayi tace "Eh mana" Maryam
ta ajiye laptop din a gefe tace "Ae babu inda ba mu je ba..." Imaan tace "Kamar Ina
da Ina?" Maryam tace "Ya fa ce kada in gaya ma kowa har ke" Imaan ta xauna kusa da
ita tace "Don Allah ki gaya min, ai ba gaya masa xan yi ba" Maryam tayi dariya tace
"Anya xan iya gaya maki kuwa, ce min fa yayi amana, kuma sbda ke muka je wajen...."
Imaan kamar xata yi kuka tace "Don Allah ki gaya min, wllh baxai sani ba, abinda ma
ba shiri muke da shi ba yanxu"

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

44....

Maryam tayi dariya tace "Kai Imaan haka kike da son jin abinda bai shafe ki ba?"
Imaan ta marairaice mata tace "Ni dai ki gaya min" Maryam na murmushi tace "Ke ba
ko ina mu ka je ba, kawai dai ya kai amaryar tasa plazan da xa ayi mata dinkunan
bikin ne ya bada kudi, sai kuma gold na rings guda uku da ya siya mata for the
wedding, sannan muka koma gida muka ajiye ta, after that muka je kasuwa siyo drinks
da Ummansa tace ya siyo, sai flasks da bedsheets da xata yi souvenir ma
kawayenta....." Imaan ta ja tsaki tace "Toh meye na cewa kar ki gaya min, ko ni ina
ruwana?" Maryam tace "Ke wasa nake kawai Inna yace kar in gaya ma amma ba ke ba"
Imaan ta mike tana goge jikinta tace "Toh shine xa ki ce saboda ni ku ka je inda ku
ka je?" Maryam tace "I am just pulling ur legs, kin taba ganin amaryar tasa kuwa?"
Imaan tace "Ehh na taba ganinta a gidansu" Maryam tace "She is beautiful but her
fairness isn't natural" Imaan tayi dariya tace "Artificial ne kenan" Maryam tace
"Probably... And she isn't friendly, she didn't even acknowledge my present sosai,
kamar bata son mutane, sai kin ga ma yanda ta amsa min gaisuwan da na mata, she
just shunned me..." Imaan tace "Tohh ba sai ki fasa bin su ki dawo gida ba, Toh me
yayan yace?" Maryam tace "He couldn't say anything to her, amma shi ma naga bai ji
dadi ba, coz he even introduced me to her again, amma ta ki cewa komai" Rai bace
imaan tace "Toh wai me yasa baki dawo gida ba??" Maryam tace "Ae ban san hanya ba,
beside I am not with money, ga shi in gaya maki sai wani shagwaba take masa a mota,
shi ko a cikin magana goma bai fi ya amsa mata uku ba" Imaan tayi dariya tace
"That's their problem" Maryam tace "Yea least I forget, na yi maki deciding abinda
xa ki siya ma Bf din ki for his birthday" Imaan na shafa lotion dinta tana kallonta
ta madubi tace "And what's that?" Maryam tayi murmushi tace "But wait... did he
invite u for the birthday party?" Imaan ta gyada mata kai, Maryam tace "Kuma xa ki
je?" Langwabar da kai Imaan tayi a hankali tace "Toh I haven't decided yet, ban
sani ba tukun" Maryam tace "Toh after ur decision xa a bar ki kije a gida kuwa?"
Imaan ta xaro ido tace "Dama wa xan gaya ma?? Tab... Am telling nobody" Da sauri ta
dawo kusa da Maryam ta xauna tace "Plss Maryam wannan ya xama sirri tsakanina da
ke, Kinga even Maimoon da ta ke kawata ma ban gaya ma ba, don Allah kar by mistake
ki ce ma Ya Mujaheed anything about the birthday" Shiru Maryam tayi tana kallonta,
hankali tashe Imaan tace "Ko dai har kin gaya masa?" Maryam tayi yake tace "Haba
dai why will I, of course ban gaya masa komai ba" Imaan ta sauke wani ajiyar xuciya
tace "Better" Maryam tace "May be... A day to the birthday sai mu fita babban
shopping mall in nuna maka abinda ya kamata ki siya masa" Imaan tayi shiru tana
tunani, can tace "Toh Allah ya kai mu" kayan baccinta ta saka ta hau saman gadon ta
dawo kusa da Maryam tana kallon abinda take yi a laptop dinta.
Slowly ranakun suka dinga tafiya har ya rage saura kwana biyu bikin Mujaheed da
Safeenah, gida ya cika da Yan uwa da abokan arxiki, matan kawu Bala, Hansai da
yaranta kai duk yan uwa dai an cika gidan barin part din su Umma, duk inda kaga
Imaan toh xaka ga Maryam a gidan kamar da can sun saba da juna sosai, seriously
Mujaheed ya sa ma Imaan ido a gidan, ita kuwa ko sanin yana yi bata yi ba. Da yamma
Imaan na parlon Inna tare da Maryam sun kawo mata abinci, sai bin Inna dake ta
neman makullin bandakinta suke da kallo, duk ta hada xufa ta wani tsuke fuska,
komai sai da ta daga a parlon amma babu makulli babu labarin sa, Mama Hadiza ta
fito daga daki da alamar ita ma neman makullin take tace "Toh wai ina kika ajiye
makullin Inna?" Inna tace "Ke ki rabu da ni don Allah, nasan inda na ajiye xan ta
neme neme, da ba don rubabbun dake shigo min nan ba har xan wani kulle bandaki
kamar warce ta ajiye gwalagwalai a ciki har shegen makullin ya bata?? Ni dai ba
ruwana a ma daina xuwa min nan gaba daya, tunda ba ni ke aurar da mutumi ba" Dariya
Maryam ta dinga yi Inna ta daga kai daga duken da take tana kallonta, Sallama aka
yi bakin kofa Inna ta mike tsaye ta amsa sallaman, Ta rasulu ta shigo tana kyabe
fuska, Rahma ta ajiye mata karamin jakarta ta juya ta fita, Inna na washe baki tace
"Sannu da xuwa Ta Rasulu kinga na rasa inda na jefa makullin bandaki, gudun kar a
shigar min bandaki na kulle na saka makullin a bakin zani to yanxu gashi ko sama ko
kasa" Ta rasulu tace "Toh ai gwara da aka nema aka rasa gaba daya, kinga bayan
bikin sai a balle kofar kawai, don wani na iya xuwa ya maki dadin baki ki kunce
makullin ki basa, mutane dai basu gaji mutunci ba, kinga yanda aka 6ata tsakar
gidan da shinkafa ga yara jage jage kamar daga kauye, ni dai ba kowa ma ya kamata a
dinga bari yana shigowa ba ma wllh, sai kace ba bikin yan gayu ba" Inna tayi tagumi
tace "Naga abinda ya isheni, kin ji wata fitina koh, Kai mutane dai jarababbu ne,
kice tsakar gida na nan duk wari?" Ta rasulu ta tabe baki ta wuce cikin dakin tace
"Ae kuma sai ki yi, abinda tsoron Allah yayi karanci a xukatan mutane yanxu" Inna
tace "Toh ni kuwa xan je in basu hakuri su rufa mana asiri kada gidan 'ya yana ya
lalace mu shiga uku, sannan biki dai ba ace a xo da yara ba" Mama Hadiza ta leka
dakin ta gaida ta rasulu sama sama ta fita parlon gaba daya, Imaan ta tabe baki
xata tashi Inna tace "Toh ke kin gaida ta rasulun ma kuwa" daga cikin daki ta
rasulu tace "Ina fa ta gaida ni tana kallona ina kallonta, yaran yanxu kam sai ka
kyalesu, mu dai muna masu fatan alkhairi Allah kuma ya basu miji na gari, har
wannan figaggiyar ta kusa da ita ma ni bata gaisheni ba ai" Imaan ta gaida ta daga
inda take tana turo baki ta mike ta fice a parlon, Maryam ta mike ita ma ta gaidata
ta fice Inna na cewa "Iyayenku ku ka ma haka ba mu ba wllh" Daren ranan Daddy ya
iso daga Abuja, bayan ya huta suka d'an taba hira da Mama Hadiza da yake a part din
ta sauka, sannan ya fita don xuwa ya gaida Inna, Imaan ta bi bayansa da sauri,
bayan sun sauka balcony yana kallonta yyi murmushi saboda yasan akwai abinda take
son gaya masa kenan tunda ta biyosa, yace "Do you need anything Imaan..." A hankali
tace "Daddy kaga mutane sun yi yawa a gidan nan plss ni dai ina son xuwa gidan
gwaggwo in xauna har a gama biki in dawo Saturday" Da mamaki yace "Bikin yayan naki
kuma Imaan?" Tace "Daddy I will be very uncomfortable, ai da rana xan wuce gidan
gwaggwo din ba da safe ba" Yace "Toh ita kuma Maryam fa, won't she be lonely" Imaan
tayi dariya tace "Ae tare xa mu je daddy, ita ma tace min she's already
uncomfortable tun daga jiya da mutane ke ta xuwa" Murmushi Daddy yyi yace "Ohk then
sai ki gaya ma Ammin ki" Imaan ta wara ido cike da jin dadi tace "Toh Daddy nagode
sosai, ai dama Ammi...." Shiru tayi hango Mujaheed da ta yi yana tahowa daga part
dinsu, Daddy ya kalli inda take kallo, ganinsa ya tsaya har ya iso inda suke, da
ladabi Mujaheed ya gaida Daddy, daddy ya amsa yace "Ya shirye shirye M.A" Murmushi
kawai Mujaheed yayi, Imaan tayi wucewarta gaba ta bar su tana cinno baki, da
sallama ta shiga parlon inna, Ta Rasulu na xaune kan darduma ta daura kafa daya kan
daya ta rungume hannu tana sakace hakori, Inna kuma na xaune kan tabarma ita ma ta
daura kafa daya kan daya, Umma na parlon xaune ga bucket cike da cin cin da alkaki
da ta shigo da sai kallon ta Rasulu take kasa kasa, Ta Rasulu ta kyabe baki tace
"Yo ai duk matsiyata ne Asabe, ni shi sa ba ruwana da kowa wllh, ba ruwana" Inna
tace "A'a dama fa nasan a wajensu tsiya ya kare, ni ina ruwana da su Ina ta kai na,
oh oh wlh" Ta Rasulu ta kalli Imaan sannan ta kalli Inna tace "Matar nan na amfani
da iccen da kika bata kuwa?" Inna xata yi magana Daddy ya shigo da sallama Mujaheed
na biye da shi a baya, Inna tace "Allah dai ya baku lada wannan hidima da kuke ta
yi da Mujaheed, ko kudin jirgin da ka kashe yau ma ai xaune yake da kansa, Allah
dai yasa ya ji k'an ku nan gaba, yayi ma imaan abun kirki ranan bikinta" Daddy ya
xauna yana murmushi ya gaisheta sannan ya gaida Ta Rasulu, Umma ta gaishe sa sama
sama, ya amsa yana tambayarta taro, ta Rasulu ta rike ha6a tana kallon Daddy tace
"Ohh Bukari kana nan dama, rabona da kai fa tun da ka xo daurin auren ishaq" Daddy
yace "Ina nan Baaba, sai dai yanxu a Abuja nake" Ta Rasulu tace "Toh Allah yayi
maku albarka, ya kare ku sharrin masu sharri, ya sa ku gama lafiya da mu, ya ba
matanku ikon yi mana biyayya yanda ya kamata" Yana murmushi yace "Ameen Baaba"
Mujaheed ya gaida ta Rasulu, ta Rasulu tace "Sannu ango, amma kuma duk naga ka rame
baka cin abinci ne?" Inna tace "Ke ma dai da wata magana ta Rasulu, ina xai ci
abinci yana tunanina, kin xata rabuwa da ni abu ne mai sauki?" Dariya Daddy yayi
yana kallon Mujaheed, Mujaheed ya kalli Inna ta gefen ido bai dai ce komai ba, Umma
ta wani daure fuska tana hararan Inna ta gefen ido, Ta Rasulu tace "Toh kayi hakuri
Mujaheed, abinda bayan bikin da sati daya kawai sai ka xo ka dauketa ka mayar da
ita gidan naka gaba daya, ohh sa6o turken Wawa" Inna tace "Ae shine na ga, nayi
kokarin fahimtar da shi hakan amma ya kasa kwantar da hankalinsa, sai in koma can
gaba daya Imaan kuma ta dinga xuwa duk Juma'ah ta koma lahadi" Daddy dai sai
murmushi yake, Imaan ta saci kallon Mujaheed taga kallonta yake, dauke kai tayi da
sauri, Inna tace "Toh ni dai ta Rasulu ga ki ga Bukar yau, sai ki masa bayanin
mutumin nan na bayan tsauni a tsanake, tunda ni na kasa fahimtar da shi da Ahmadu
suna ganin kamar ko boka ne, Ni ko me xai kai mu gun boka mu masu tsoron Allah" ta
Rasulu tace "Wllh Bukar ku maida hankalin ku don sai anyi da gaske da 'yar nan taka
Imaan, tana da makiya ne ba na wasa ba, sannan wannan ciwace ciwacen nata ma ance
ba banxa ba da sa hannu, sai an tashi tsaye kyam kada a kai mu a baro, bangaren
aure kuma ance xata auri wanda ke bala'in sonta, wasu xa su yi murna da auren wasu
kuma bakin ciki da hassada baxai bari su yi ba, wasu kuma takaici baxai yarda su yi
murna ba, sannan da matsalaloli iri iri a xaman auren, matsaloli masu girma ba
dadin ji kuwa, ni dai ba fata nake ba amma gaskiya abun ba dadin ji, kuma ance sai
ta cika maka parlor da jikoki, toh ni abinda ban gane a nan ba shine... Kyashin
fidda kudi kake a nema ma tillon yar ka lafiya ko kuwa kudin ne baka da shi Bukar?"
inna tace "A'a sai dai kyashi, amma yana da shi wllh, Toh wllh sai ma kin tafi
bayan biki xa su xo su sameni shi da d'an uwan suce in rabu da ke ba hanyar kirki
kike nuna min ba, Toh wai dama Allah ba yace mu tashi ya taimake mu ba??" Daddy ya
kasa daga kai, ta rasulu
ta saki salati tana tafe hannu tace "Sai su ce ki rabu da ni kuma?" Inna tace "Wllh
kuwa tatas xa su min suce in raba kaina da ke, ai ga shi nan xaune da ransa ba
sharri na masa ba kullum na kawo masu xancen sai su gwaleni suce karya ce inyi ta
kaina, to ni ya xan yi da su??" Mujaheed ya sunkuyar da kai sai murmushi yake,
imaan ta boye fuska bayan kujera tana dariya kasa kasa, Daddy dai ya kasa dago kai,
Ta rasulu tace "Dago kanka ka kalle ni Bukar, wllh wannan 'yar taka idan ba a tashi
tsaye kanta ba duk sai mun shiga uku a duniyan nan, idan ma xaka fiddo kudi ka
fiddo kudi a nema mata magani ta xama mutum, tunda har kuka iya karyata ni kai da
Ahmadu to xa ku iya karyata Asabe ma" Inna tace "Yo na nawa kuma? Ai sun ma karya
ta ni, sai dai Allah ya shirye su, ni dai na yafe masu" Daddy dai kansa na kasa, Ta
Rasulu tace "Yanxu bayan biki sai ka ba Asabe dubu dari, idan ma ya kama muje tare
da ita da Imaan din ne sai duk mu tafi...." Inna tace "Haba sai kace xa ki cuce ni,
ai kawai ki je ke daya ba komai wllh" Daddy yace "Toh Allah ya kai mu xa a bada"
Mikewa yayi yace "Na gaisheku xan je in huta" a tare suka hada baki wajen cewa "Toh
Allah maka albarka" yace "Ameen" sannan ya fita parlon yana girgixa kansa. Umma da
duk ta hada xufa gaba daya jikinta tana murmushin karfin hali tace "Toh Inna ayi
hakuri da wannan din don Allah, ni xan koma in ji da baki" Inna tace "Toh ai ya fi
babu, Allah dai yayi albarka" tana murmushi tace "Ameen" ta fice parlon da sauri
tana share xufar goshinta a ranta kuwa hamdala take da Allah ya bayyana mata Ta
Rasulu.
Washegari Thursday duk yan matan gidan na ta shirye shiryen fita saloon da yin
lalle, ita dai Imaan sai kumbure kumbure take...

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

45.....

Mujaheed na dinning a xaune Maryam ta sakko downstairs tare da Maimoon, yana


kallonta yace "Maryam" ta kalli direction din sannan ta tafi tace "Sai yanxu kake
breakfast?" Yace "Ehh... xauna" ba musu ta ja kujera ta xauna, ya ajiye cup din
coffee dake hannunsa yace "When did she tell you is the birthday?" Maryam ta
langwabar da kai tace "She told me nothing about it again, tun ranan bata gaya min
komai ba" Yana kallonta da kyau yace "Karya kike Maryam" ta xaro ido tace "Karya
kuma ya M.A, bana ma tunanin Birthday din na nan don bata ce min komai ba, kuma
kaga gashi ana ta hidiman biki, kila ma ta manta idan ma Birthday din na nan" yace
"Make me a promise Maryam" tace "What promise" yace "You will watch her movement
keenly" dariya tayi tace "Ohk then, amma kuma abun mamaki ina ma xata je ana biki"
Yace "Just do what I say" tace "Toh na ji" yace "Good tashi ki tafi" Mikewa tayi ta
bar dinning din, ya dau coffee dinsa ya ci gaba da sha a hankali. A bedroom Maryam
ta tadda Imaan dake ta shiryawa slowly wai don a tafi a mance da ita, Maryam tace
"Naga alamar baki son xuwa saloon din nan imaan" kamar xata yi kuka tace "That's
just it, ni scalp dina ma ciwo yake min, aje ayi ta ja min gashi kaina ya fara min
ciwo, ni dai kawai ku tafi kice masu baki gan ni ba" Maryam tayi dariya tace "Kai
Imaan, da ni ke da irin gashin ki ai duk sati sai naje saloon" ita dai Imaan bata
ce komai ba, Sadeeq ne ya fado mata ta tuna wata rana da daddare suna waya yake ce
mata shi dai yana son dogon gashi, haka kawai taji tana ma son xuwa saloon din,
Maryam ta gama yafa karamin veil din abayar jikinta tace "Ohk then xan ce masu ni
ban gan ki ba" Imaan tace "Ko kuma ma dai kawai bari mu je, idan ya so ana gama
mana sai mu tafi mu siya abinda xa mu siya a shopping mall, koh?" Maryam ta wara
ido kamar baxata ce komai ba sai kuma tace "Ehh haka ne kuma" Imaan tace "Kinsan fa
gobe ne birthday din kuma I have to give him the gift this night" Maryam tace "Au
haba, same day da bikin Ya Mujaheed kenan?" Imaan tace "Sure" Maryam tace "Tabdi,
Toh yanxu ya xa ki yi? Ga biki ga birthday" Imaan tayi yar dariya tace "Ni ina
ruwana da biki, Ai na riga na ce ma Daddy xan je gidan Gwaggwon Ammina gobe da
safe" Maryam ta marairaice tace "Tafiya xa kiyi ki bar ni yanxu?" Imaan tace "Of
course no, tare xa mu ai" Maryam ta langwabar da kai tace "Yanxu haka xa mu yi
missing bikin ya MA, gashi ma anjima da daddare xa ayi dinner fa" Imaan tace "Aa
idan kinga xaki tsaya ki tsaya ni dai ba ruwana" Maryam tayi murmushi tace "Aa mu
je gidan grandma din dai..." Imaan tace "Better" a tare suka fita dakin, Ammi dake
parlor ta nuna ma Imaan kan kujera tace "Ga kayan ku nan ki shiga da shi ciki yanxu
aka kawo" Imaan ta dauko ta kai daki sannan ta fito, sosai gaban Imaan ya fadi
ganin Mujaheed parking space a tsaye, tun da ya kalleta sau daya ya ci gaba da
danna wayarsa, ta dauke kai ta isa gun motar da ake kai su makaranta tana kallon
Maimoon, Maryam kuma ta tafi gun Mujaheed tana murmushi tace "Our handsome
groom..." Imaan ta tabe baki tana kallon Maimoon tace "Ina Drivern da xai kai mu
Saloon din?" Maimoon tace "Ya Mujaheed yace xai ajiye mu shima fita xai yi yanxu"
Xaro ido imaan tayi tana kallonta, ta hade rai bata dai ce komai ba, Ummi ta fito
bangarensu tana kallon Mujaheed tace "Rahma xata taho daga baya, wai xa su fita
tare da Umma yanxu" bude driver seat Mujaheed yyi ya shiga yana kallon Maryam yace
"Har da ke xa aje gyaran gashin?" Ta xaro ido tace "Eh mana" murmushi yayi yace
"Toh shiga..." imaan ta bi bayan Maimoon tana cika tana batsewa ta shiga back seat,
Ummi ma ta shiga. Suna isa saloon din yyi parking yana kallon Maimoon ta madubi
yace "Since babu mutane sosai a saloon din xan jira ku gama" Maimoon ta washe baki
tace "Tohh mun gode Ya Mujaheed" a fusace imaan ta fice a motar ta bar door din a
bude cikin tsawa yace "Keee" juyowa tayi da sauri, fuska daure yace "Xo ki rufe min
mota kada in sauka in xane ki yanxu" Ganin babu wasa tattare da shi ta dawo kamar
xata yi kuka ta rufe motar ta juya ta shiga saloon din, Maryam tayi murmushi tace
"Ya M.A kai dai kawai kayi tafiyarka ko motorcycle din nan mai kafa uku sai mu hau
ya dawo da mu gida" Mujaheed yace "Sauka kije kiyi abinda ya kawo ki nan" Yar
dariyar yake tayi ta bude motar ta fita, ita kanta bata ji dadin jiransu da yace
xai yi ba, shikenan ya ruguje masu plan. gyara ma Imaan gashi ake amma gaba daya
hankalinta na gun lekan waje don ganin ko Mujaheed ya canxa mind dinsa ya tafi,
amma duk ta leka sai taga yana nan, ta ji kamar ta kurma ihu, a haka har aka gama
masu gyaran gashin aka fara masu lalle a hannu, Maimoon ce ta fara fita bayan an
gama masu, Ummi ma ta fita, Maryam na kallon Imaan a hankali tace "Kinga yayi
spoiling plan dinmu ko, yanxu how are we going to get the gift?" Imaan ta rasa
abinda xata ce mata, can Maryam tace "You know what, kawai mu koma gida, dama akwai
few abubuwan da nace ma mum xan siya a Nigeria, muna isa gida yanxu xan amshi card
dinta mu fita daga can ma sai in siya abubuwan da nace" Sosai hankalin imaan ya
kwanta, ta d'an yi murmushi tace "Toh shikenan, har naji dadi" tashi Imaan tayi
suka fita saloon din din Maimoon ta bada kudin kafin su fita, tun da suka fito
Mujaheed ke kallonsu ta madubi har suka iso gun motar, ganin Ummi xaune a gaba
Maryam ta shiga back seat tare da Imaan, tada motar yayi ya dau hanyar gida. Suna
isa gida Mujaheed yayi parking ya kashe motar, Imaan ta fita ta dau hanyar
apartment dinsu, ya gyada kai yana bin ta da ido ta madubi... Maryam tace "Mun gode
ya M.A" bai amsa ta ba tayi wucewarta tana murmushi. Maryam na gaya ma mama Hadiza
xata fita shopping ta hanata wai bayan biki sai su je, ba ynda Maryam ta iya ta
koma dakin Imaan a sanyaye ta sanar mata abinda mamarta tace, imaan ta rasa yanda
xata yi, Maryam tace "Toh ko mu bari kawai gobe da safe idan mun fita xa mu gidan
grandma dinki sai mu shiga mu siya" a hankali Imaan tace "Noo yau ya kamata in
basa, yau nake son in basa" Shiru Maryam tayi, can tace "Ba xa mu je dinner ba
anjima, kawai mu jira sai mutane sun cika wajen sai in sulale da makullin motar
Yaya Yusuf mu je mu dawo" Imaan ta xaro ido Tace "Ni fa ban yi niyyar xuwa dinner
din ba wllh" Maryam tace "Ae ko gwara ki daura niyyar xuwa yanxu, don that's the
only way out" Imaan tace "Toh shikenan" Ana idar da Magrib duk aka gama shirin
tafiya wajen dinner, duk wannan abun Mujaheed na lura da su keenly, kuma yaki
tafiya duk da yanda abokansa suka dinga takurasa su wuce saboda amarya har ta iso
wajen, Maryam dai ta dinga bin Yusuf wai ya bata makullinsa tayi driving din, daga
karshe dai babu yanda ya iya ya bata, da kyar imaan ta saka gyale a kan ankon su na
Dinner da Daddy yayi masu gaba daya gidan, tayi kyau har ta gaji amma sai wani
nonnokewa take abunka da ba sabon ba, Maryam ce tayi driving din nasu xuwa hall din
da xa ayi dinner din.... Waje ya cika makil da masu kudi sai ruwan naira ake tun
kan a fara komai, Fara'a gun umma ba a cewa komai, Inna na xaune tare da ta rasulu
a table guda duk sun sha atamfar England an yafa gyale sun tsuke fuska suna kallon
ikon Allah, Imaan na shigowa hall din tare da su Maryam ganin Inna da ta rasulu ta
rufe fuskarta gyalen jikinta ta dinga ba66aka dariya, suka nemi waje suka xauna,
kallon inda amarya da ango ke xaune tayi, taga Safeenah da tayi wani kyau irin na
aljanu sai sheki gwalgwalan jikinta suke, kayan jikinta kam dama ba acewa komai, ta
kalli Mujaheed da ya sa lafiyayyen farin gezna sai walkiya yake, hada ido suka yi
da shi tayi saurin kauda kai, Imaan ta kalli Maryam tace "Ni dai xan koma gun su
Inna kafin mu fita" bata jira cewar Maryam ba ta mike ta tafi gun su Inna Mujaheed
ya bi ta da ido.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

46....

Inna na kallon Imaan da ta xauna kusa da ita cike da damuwa tace "Toh ba gashi kin
fito sak mutum ba yau kin sa gyale, amma da kullum da hijabi xulum xulum kamar
matar ladani..." Ta rasulu dake ta bin jama'ah da kallo tace "Toh wai ni abinda na
kasa ganewa a nan shine... uwar amaryar da danginta basu san kin xo nan bane ban ga
an xo gaishe ki ba har yanxu, dubi fa yanda muke xaune kamar gantalallu marasu
makabuli babu wanda ya bi ta kan mu, an san ke kika raini Mujaheed tun yana tsumma
kuwa, Kai duniya dai ta lalace ni ta rasulu" Inna ta tabe baki tace "Shine nake ta
kallon ikon Allah, sai yawo suke mana da gwalagwalai kamar barayi babu wanda ya xo
ya durkusa nan yace Sannu Inna... ya taro? To Allah ya sanya alkhairi ya nuna mana
na 'yan baya, shi kuma Mujaheed din dubi yanda ya wani yi tsamo tsamo da shi kusa
da amaryar babu walwala kamar dai wanda aka tilasta ya xo casun..." Imaan tayi
murmushi ta kalli Mujaheed sannan ta kalli Inna tace "Toh ke ina ruwanki..." Inna
tace "A'a da ruwana mana, ni ba karamin aikina bane in tashi inje samesa yanxu in
ji ko lafiya..." Ta rasulu tace "Maxa je ki, nima naga rashin walwalan yayi yawa
sai yake kawai yake, kamar wanda aka ma dole, anya ma auren soyayya xai yi kuwa"
Inna ta tabe baki ta mike tace "Toh wani ya rainan min shi da baxan sani ba idan
yana cikin damuwa ko akasin haka, sarai nasan sa ciki da bai, da abinda ke damunsa
a xuciyarsa xaman da yayi a nan" Kutsawa ta dinga yi cikin mutane wanda yaki
matsawa dama hankadesa take tana cewa "Yau naga bala'i mutane an xo cin shinkafa da
yar kaza kamar mayu, an ki bani hanya..." Kallonta aka dinga yi ana bata hanya tace
"Banda jaraba ko wacce ta fiddo kayanta na karkashin akwati ta saka ta xo mana nan
tana jiran shinkafa da salaq da kaza, ohh yunwa ta yi yawa a duniya" A haka har ta
isa inda amarya da ango ke xaune, wata kawar amarya ce tsaye tana bada history din
amarya sai wani yauki take tana jujjuya idanuwanta, cool music sai tashi yake
mutane na mata tafi... sake baki Inna tayi tana kallon yarinyar, can dai ta karasa
inda take tsaye ta d'an ta6o ta a kafada, gaba daya wa enda suka san Inna suka xaro
ido suna kallon ikon Allah, juyowa budurwar tayi tana kallon inna murmushi dauke
fuskarta, Inna ta matsa kusa da ita sosai murya can kasa tace "Wani tsinannan telan
kika ba kayan ki ya lalata maki haka saboda rashin tsoron Allah, duk duwaiwuka a
waje?" Ba karamin tsorata da girgixa Inna tayi ba tana xare ido jin muryarta ya
kauraye makeken hall din gaba daya ta cikin speakers, Hall ya rikice da dariya,
Mujaheed ya sunkuyar da kansa, Umma ta kasa motsi inda take tsaye sai hadiye abu
take da kyar, Imaan ta hade kai da table tana dariya kasa kasa, su Maimoon ma suna
ta dariya daga inda suke xaune, Aunty da Ammi da Mama Hadiza dama tagumi suka yi
suna kallon Inna da tayi tsamo tsamo a gaban hall sai kallon jama'ah dake dariya
take, gaba daya yan uwan amarya wani kallo suka dinga yi ma inna, ita kuwa mai bada
history ta ji kamar ta nutse gashi an ki daina dariya a hall, Safeenah ta wani hade
rai tana kallon Mujaheed tace "Haba Mujaheed dama gate pass din wa enda suka kamata
da wanda basu kamata ba ku ka dinga raba ma suka shigo mana nan, dubi wannan
tsohuwar me ya kawota nan ta ina ta samu pass din shigowa har xata kunyata
aminiyata cikin mutane, kasan Yar gidan wacece ita kuwa??" Gently Mujaheed yace
"Watch ur words..." A fusace tace "Don't tell me that Mujaheed, how dare the old
woman insult my friend that way, yar gidan governor ce fa tsaye a wajen..." Calmly
yace "Ko yar gidan uban wacece, ke kawarki ce, to ni kuma grandmum dita ce a kusa
da ita, so you dare not look into my face and say nonsense about her" Wani kallo
Safeenah ta dinga ma Inna da ta tabe baki cikin sanyin murya tace "Ba lafiya, dama
ba a sirri a nan, daga magana kuma sai sipikoki su dauka su min terere...." Juyawa
tayi ta kalli yarinyar da ta kasa cewa komai har sannan tace "Ki dai maida masa ya
gyara maki ai kudi kika biya ya cuce ki ya maki wannan dinkin" daga haka ta bar
wajen ta tafi gun Mujaheed, har sannan Safeenah bata daina bin ta da wani irin
kallo ba har ta iso inda suke tana kallon Mujaheed tana washe baki tace "Wannan ce
amaryar Mujaheed" Safeenah ta dauke kai fuska daure, Inna ta rike ha6a tace "Ikon
Allah, Toh Allah ya bada xaman lafiya, ta dai sha gwalagwalai maa sha Allah"
Hajiyan Marafa ce tsaye kan Umma tana bala'i a mugun fusace tana cewa "Haba Rukayya
ke baki ga irin manyan mutanen da muke ba gate pass bane xa ku ba wannan tsohuwa
mai wanke wanke ta shigo mana hall tana shirme tana kunyata mutane, kin san yar
gidan wacece tsaye a wajen take magana kuwa?? reputation dina da na 'ya ta kuke son
6atawa ko meye hakan?" Umma dai sai hakuri take bata a rikice tana cewa "Wllh ban
san wanda ya bata pass din ba, don Allah kiyi hakuri Hajiya, wllh ban san daga inda
ta taho ba...." A mugun fusace Hajiyan Marafa tace "Toh maxa ki sa a fitar da ita
daga hall din nan tun wuri kada ayi mummunan abu a nan, maxa a fita da ita kada in
sa masu gadi su fitar min da ita ta tsiya" Umma sai cewa take kiyi hakuri Hajiya xa
ta tafi yanxun nan kuwa, ae ba ku kadai ta kunyata ba har mu wllh, ban san wanda ya
bata pass ta shigo ba ni ban ma santa ba, haka irin tsoffin nan suke idan suka ga
ana taro su shigo cikin jama'ah" Hajiyan Marafa ta juya fuu ta wuce tana cewa "Maxa
ta bar nan kada in sa masu gadi su ja ta su fitar..." Inna na kallon Mujaheed tace
"Toh naga duk baka da walwala lafiya kuwa, ko baka ci abinci bne?" Ya girgixa kai
yace "Ba komai, ki koma kiyi xaman ki" Inna tace "Toh madallah sai dai har yanxu mu
dai babu abinci babu labarinsa, ga ta rasulu can ma sai hamma take" Tana magana ta
dau tsadadden drink dake gabansu tace "Ko in dau wannan" yace "Dauka" dauka tayi
tace "Toh shikenan, Allah dai yasa ba mai halin uwarka xaka auro mana ba dai" daga
haka tayi wucewarta, Safeenah ta bi ta da wani harara tana kyabe baki, Umma ta rasa
yanda xata yi ta fitar da Inna a hall din cikin lumana, duk ta rikice taje can taje
nan, Inna na dawowa xuwa seat dinta ta dinga cewa mutane "To dai duk wanda ya ci
abu yyi hakuri ya saka gwangwani ko kwalin a jakarsa kada mu bata masu waje da
kazanta mu cuce su...." A haka har ta koma gunta, ta ajiye ma ta rasulu drink din
daya ta ajiye daya gabanta tace "Ma rage xafi..." Ta dau drink din ta fara budewa,
Inna ta xauna tace "Naje na samesa amma kinsan ko gaisheni amaryar bata yi ba, ni
dai ban kulata ba, ba ruwana kada in kunyata kai na cikin jama'ah ga ni babba, taro
yayi taro in je inyi magana in kunyata Mujaheed din ma gaba daya, bakina a leko na
juyo na dawo ai ana tare...." Ta rasulu tace "Gwara da baki kulata ba kam, ki bari
sai an kaita dakin nata ki shirya kije ki mata tatas ki gaya mata yanda kike da
Mujaheed" Inna tace "Ehh dama ai dole in sanar mata wahalan da nayi da shi don ta
gane matsayina a wajensa, ana kai ta da washegari dama Imaan xan ce ta rakani inje
in karanta mata yanda muke da shi" Umma ce ta taho gun Inna da sauri tana haki tace
"Inna yanxu aka kirani wai ruwa ya cika parlon ki sai kwararowa waje yake ga kofar
a rufe, ko dai kin bar pampon bayan gidan ki a bude baki sani ba?" Inna ta mike ta
rafka uban salati a rude tace "Hadiza ta cuce ni ita ta shiga bandakin karshe tayi
fitsari, shikenan ruwa ya shanye min gida na shiga uku na lalace ni patuu, ga
dukiyoyi irinsu kujeru, tv, gado carpet, fridge duk a ciki" ta rasulu dake xabga
salatin ita ma ta mike tace "Na shiga uku ni ta rasulu, jakata na dakin nima har da
kudi dubu biyu, yanxu me xan ce ma 'ya yana daga xuwa biki ambaliya ya rutsa da
ni??" Umma tace "Toh bari in sa driver ya maxa ya maida ku gidan gaskiya, don ruwa
aka ce duk ya cika tsakar gida" Ko sauraranta Inna bata yi ba ta fice da gudu tana
cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'una ambaliyan ruwa a gidana a kira min yan
kwana kwana, ga gudunmawar dubu hamsin da Bulasawa ya bani a dakin...." ta rasulu
na biye da ita a baya ita ma da gudu tana salati, Mama Hadiza da su Aunty na ganin
Inna ta fita da gudu suka taho gun Umma dake tsaye suna tambayarta me ya faru, Umma
tayi wani dariya tace "Wai fa kudin da xata yi liki ta mance a gida shine wannan
saurin wai driver xai maida ta gida" Kasa cewa komai Mama Hadiza da su Aunty suka
yi, Umma tace "Allah dai ya kyauta, lamarin Inna ae sai ita" daga haka ta wuce ta
bar su wajen a tsaye, Imaan dai na xaune an barta da jakunkuna irin na tsofaffi,
Maryam ce ta taho gun Imaan da sauri tace "Ke maimakon mu bi su Inna mu je mu yi
abinda xa mu yi kika bari suka wuce" Imaan ta xaro ido tace "Ae kuwa, toh kawai mu
yi kamar xa mu bi su da jakar su sai mu wuce" Maryam tace "Toh dauko mu tafi" Imaan
ta dau jakar Inna ta mika ma Maryam na ta rasulu, kallon Mujaheed tayi taga idonsa
na kansu, ta dauke kai tana xaro ido tace "Maryam kin san Yaya kallonmu yake"
Maryam ta kallesa taga still kallonsu yake duk da liki da mutane suka taru wajen
suke masa da Safeenah, Maryam ta koma ta xauna tace "He is suspecting us Seriously,
kin san me xai faru?" Imaan ta girgixa kai, Safeenah ta bude jakarta ta ciro new
note din naira dari dari tace "Gashi ki tafi kiyi masu spraying, kafin ki dawo na
fita gun mota sai ki sameni da sauri, but before then Bari in canxa seat" Imaan ta
nufi can gaban hall din hannunta rike da tulin kudin, su Maimoon, Ummi, Rahma da
wasu kawayen Safeenah da yan uwanta da suka sha gold sai cashewa wa suke da wakar
jarumar mata da ya cike hall din Lol.... Safeenah ma na tsaye tana rawa gently tana
kallon Mujaheed with love, shi ko yana tsaye kamar statue yana jujjuya wayar
hannunsa, dance floor din kuwa banda dubu dubu babu abinda xaka gani a kasa sae few
five hundred notes, Imaan ta isa kusa da su ta ki yarda ta kallesa tana kallon
Safeenah dake rawa ta fara mata likin a hankali, kallon cikin ido Safeenah ke mata
haka kawai Imaan taji gabanta na faduwa bata sake yarda sun hada ido ba tana ci
gaba da yi mata likin kudin, Bandir din dubu daddaya Mujaheed ya ciro
ya nufi gun kanninsa da suka dage sai cashewa suke barin Maimoon, Ya fara manna
masu da daddaya da daddaya, Safeenah ta bi sa da wani harara ganin kanninsa kawai
yake lika ma, Imaan na lura da abinda tayi haka yasa taki lika mata kudin hannunta
gaba daya ta koma gun su Maimoon ta fara masu likin, Mama Hadiza ta xo ita ma tana
ma su Maimoon da Imaan likin kamar su kadai ne a wajen tana murmushi, facing din
Imaan Mujaheed yyi yana kallonta ya fara xuba mata one thousand naira note din a
hankali, kasa kallonsa ta yi kanta a kasa, can kuma a hankali ta fara lika masa na
hannunta, Mama Hadiza ta juyo ta dinga xuba masu na hannunta ita ma, Aunty ma haka,
da abokansa gaba daya da suka cika wajen lkci daya, Safeenah ta ji kmr ta nutse don
ba kowa wajenta sae flowing gown din jikinta, duk aka koma ana ma Mujaheed da Imaan
liki, Umma sai xare ido take tana kallon ikon Allah, kowa ya xo sai ya fara ma
Imaan da Mujaheed liki kamar ita ce amaryar, don wasu ko noticing Safeenar ma basu
yi ba balle su san ba ita suke ma likin ba, Imaan dai ta dawo amarya a wajen duk
kunya ya isheta.... Sai da Mujaheed ya manna ma Imaan gaba daya note din hannunsa
yana kallonta, ita dai sai kokarin barin wajen take amma saboda yanda aka kewayesu
ta rasa hanyar fita, da kyar dai ta samu ta lallaba ta fita taron xuciyarta na
bugawa, tana kallon inda Maryam ke xaune taga har ta fita, da sauri ta nufi door
din fita hall din ta fice fittt, Maryam na ganinta ta dallo mata fitilar motar ya
Yusuf, xata tafi gun motar taji an fixgota, ihu tayi a tsorace ta juya xuciyarta na
bugawa.....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

Afuwan for the late and short update, am not feeling too well... Thanks in
anticipation for understanding.
47....

47. Imaan

Imaan kamar xata yi kuka tace "Ya Yusuf dubi fa yanda ka ban tsoro...." Yusuf yace
"Ehh gwara ki ji tsoron, ina xa ku je?" Turo baki tayi tace "Gida mana, mun gaji"
yana kallonta da kyau yace "Karya kike yi, ban kuma san lkcn da kika fara karya ba,
and I need not to remind you the consequence of lying Imaan" shiru Imaan tayi tana
kallonsa, ya d'an hade rai yace "birthday din makaryacin saurayin ki xa ku tafi
koh, ke kin san waye Sadeeq kuwa? Kin san irin mutanen da yake abota da? Kinsan
abubuwan da xa su faru gun birthday din nan da kika kwallafa rai sai kin je, why
all of a sudden kika canxa from the decent Imaan da muka sani kika dawo mara ji?"
Fuska daure yayi mata tambayar, kamar xata yi kuka tace "Ni fa ba birthday nace xan
je ba, ai ba yau bane birthday din, kuma I only want to get him a gift now coz I
know I might not get it tomorrow, ban ce lallai sai na je birthday ba" Kallonta ya
dinga yi ta sunkuyar da kai a sanyaye, wayarsa da yyi vibrate ya kalla yyi replying
text din da ya shigo sannan ya tafi gun motarsa ta bi sa da kallo, Maryam ta
langwabar da kai tana kallonsa, yace "Ke ce ke xugata koh Maryam?" Xaro ido tayi
tace "I don't get you" yace "Idan ke baxa ki gaya mata gaskiya ba why encourage
her??" Maryam tace "Is there anything wrong with her getting her bf a birthday
gift, we are in a civilized world Yaya Yousuf...." Yana mata wani kallo yace "Bani
makulli na" Mika masa makullin sa tayi ta fito daga motar, Imaan dai sai kallonsu
take ta gefen ido, ya juya ya koma inda take yace "Koma ciki..." A hankali tace
"Toh ni gida xan tafi..." Ya daure fuska yace "Koma ciki nace" turo baki tayi ta
juya ta koma cikin hall din, Maryam ta wucesa rai bace ta koma cikin hall din ita
ma, Imaan na shiga ta tafi inda suke xaune tana kallon Mujaheed dake kallonta ta
xauna, Maryam ma ta xauna a fusace tace "Gaskiya guys din nan sun fiye takura
mutane, haka suke da sa ido dama, I won't tolerate this shit assuming we are
staying together with them" Imaan ta tabe baki tace "I don't even know what's their
business with me, sun dameni wllh" Maryam tace "Kece kike nuna kina tsoronsu ai"
Imaan kamar xata yi kuka tace "Toh ni yanxu ya xanyi plss?" Shiru Maryam tayi tana
kokarin nema masu wani option din, Yusuf dai na xaune d'an nesa da su yana kallonsu
lkci lkci, ana fara cin abinci Maryam ta mike ta tafi ta debo masu yar fried rice
ta cika nama ta dawo tana kallon Imaan tace "Let eat" Imaan ta girgixa kai tace "Am
not eating" Har aka tashi dinner din Imaan bata da walwala, gashi da ta kalli
Mujaheed sai ta ga kallonta yake, Tasowa Yusuf yyi ya taho inda suke ya ajiye ma
Maryam makulli yace "You two should wait for me..." Daga haka ya wuce, Maryam tayi
tagumi murya can kasa tace "Amma gaskiya wa ennan mutanen mayu ne, may be they know
what we are up to" Ita dai Imaan bata ce komai ba idonta na kan Safeenah dake
tahowa tare da Mujaheed kawayenta na biye da su a baya, hada ido suka yi da ita
Safeenah ta wani daure fuska, Imaan ta dauke kai hade da tabe baki, sai da taga sun
fita hall din sannan ta mike Maryam ma ta mike tace "Kinga hararan da yarinyar ke
maki kuwa, did you know her b4?" Imaan tace "I don't know her fa" fita waje suka yi
xuwa gun motar ya Yusuf, Aunty na kallon Yusuf a haraba hall din tace "Ka ajiye
Mama Hadiza da su Hajiya Lailah a gida Yusuf..." Yusuf ya d'an bude ido amma bai ce
komai ba, da sauri Imaan ta dauke kai tana wani murmushi, xagawa yyi ya budu front
seat yana kallonta yace "Xo ki shiga nan" ta d'an xaro ido tace "Ya Yusuf Maryam
fa?" Yace "Xata shiga wani motar, bana son musu ki xo ki shiga" Maryam ta hararesa
ta dauke kai, A hankali Imaan ta taka ta isa front seat din ta shiga, Mama Hadiza
da kawayen Aunty biyu suka shiga back seat, ya shiga motar ya bar haraban hall din.
Yana parking a compound Imaan bata ko kallesa ba ta bude motar ta fice xata wuce
apartment dinsu ta ji muryar Inna bakin gate tana cewa "Iliya Ahmadun bai dawo ba
har yanxu??" Mai gadi da ya bar gate bude ganin motoci har uku dake bin bayan motar
Yusuf yace "Ehh bai dawo ba Baaba" Inna na hango Yusuf da ya fito daga mota da Mama
Hadiza da kawayen Aunty ta fashe da matsanancin kuka, da sauri Mama Hadiza ta
nufeta tace "Me ya faru Inna" cikin kuka tace "Me na ma Rukayya a duniyar nan xata
saka min da haka, ni fa na yarje ma Ahmadu aurenta tun tana yar jagaliya, yar
yagalgal tana yawo da kodadden zani da yagaggen Hijabi" Mama Hadiza tace "me ya
faru" Inna ta sharen hawayenta bata tanka ta ba tana kallon ta rasulu tace "Mu je
kawai" ta rasulu tace "Idan ma kika yarda Rukayya ta kwana gidan nan yau Allah ma
sai yayi fushi da mu da bamu dau mataki ba, irin wannan cin mutunci da raini haka?
Oh oh tun da uwata Mai salati ta haifeni ban taba gani ko jin labarin irinsa ba,
waiii.... Ai wannan babban magana ce wllh, ko kotu aka kai kara ba karamin
muhimmanci xa su ba maganar nan ba, kuma da kyar idan ba sai an yanke mata hukuncin
kare rayuwarta a gidan yari ba" Inna tace "Toh kun ji dai, ke dai mu je kawai wanda
ya ajiyeta a gidan xai dawo duk gidan uban da yaje ya same mu, casun kuma da bamu
samu ganin yanda xa a kare ba Allah ya isa xa mu hadu gaban ubangiji...." Ta rasulu
na biye da ita tace "Ke ma dai wllh, sai ma kin fada?? Ae wannan a rubuce yake
Asabe, abinda ba yafewa xa mu yi ba" Mama Hadiza da su Hajiya Lailah dai suka bi su
da kallo. Imaan na kokarin saka kayan baccinta bayan ta fito wanka aka bude kofar
dakinta, Maryam ce ta shigo ta tsaya tana kallonta tana murmushi, da mamaki Imaan
tace "Ina kika je tun daxu kowa ya dawo banda ke??" Maryam tace "Close ur eyes
please" Imaan tayi shiru tana kallonta, Maryam ta hade rai tace "Toh ko inyi
wucewata" Murmushi Imaan tayi don sai sannan ta lura da hannunta dake boye a
bayanta, a hankali Imaan ta lumshe idonta tace "Toh na rufe" Maryam ta isa kusa da
ita ta tsaya tace "Bude ki ga gift da xa ki ba Sadeeq din ki" da sauri Imaan ta
bude idon taga wani flower mai kyan bala'i da cards Maryam na mika mata tana
jujjuya eye balls dinta, Imaan ta saki baki tace "What's this?" Maryam tace "Gift
din da xa ki ba sa mana" Dariya Imaan tayi tace "You are very funny wllh, me xai yi
da wannan din" Maryam ta xaro ido tace "Me xai yi da shi fa kika ce?matsalar ku
kenan yan Nigeria wllh, ke kinsan Value din abun nan dake hannuna kuwa, kin san mu
a turai wannan ya fiye mana kudi da wasu abubuwan rayuwa idan aka xo fannin
kyautatawa, wllh I am telling you this sai ya fi son wannan akan kudin da xaki basa
ko abinda xa ki siya masa, idan kin basa kudi me xai yi da shi bayan yana da fiye
da wanda xaki basa, sai dai ma ya bada kudin kyauta tun bai shiga gida ba, idan
kika ce xaki siya masa abu me xai yi da shi bayan bai fi karfinsa ba?? Wannan kam
kina basa am telling you xa ki ga reaction dinsa..." Tana murmushi ta kare maganar,
Imaan dai sai kallonta take nan kuwa a xuciyarta tunani take kuma fa gaskiyan
Maryam tunda shi ma a turan ya taso xai so gift din sosai, Maryam ta kai mata
flower din hancinta tace "Smell it" lumshe ido Imaan tayi jin wani cool scent da
flower din yake, ta amsa tana murmushi tace "It smells nice, I love you Maryam"
ajiye flowers din da card tayi gefen gado ta rungume ta. Umma na dawowa daga hall
din dinner tare da kawayenta bayan sun sallami mutane gaba daya dama bata yarda ta
shiga gidan ba, kawayenta su Hajiya Saude ne kadai suka shiga cikin gidan tunda
haka dama suka shirya tun a hanya, Umma ta dau wayarta ta nemo lambar daddy tayi
dialing, ba a dau lkci ba ya daga, tayi kasa da murya ta gaishesa ya amsa yace
"Lafiya dai koh Hajiya Rukayya" Tana yake tace "Lafiya Baban Imaan, nace kana gida
kuwa?" Daddy yace "Ehh na kusa gidan yanxu, driving nake" Umma tace "Toh Ina ma
kofar gida, xan jira ka iso" yace "Ohk" daga haka ya katse wayar, Daddy na shigowa
layin ya hangota tsaye d'an nesa da gate din gidan, parking yayi kusa da gidan ya
fito yana kallonta yace "Lafiya kuwa?" Tace "Toh lafiyar kenan dai..." Yace "Mu
shiga ciki toh" da sauri tace "A'a bari dai in maka bayanin a nan" Ya rungume
hannunsa yana kallonta yace "Toh ina ji" Tace "Wllh Baban Imaan daxu ne Inna taje
wajen da ake dinner...." Da mamaki Daddy yace "Yanxu sai da taje dinner din nan duk
abinda muka gaya mata??" Umma ta bude hannu alamar ai shine, tace "Kuma da aminyar
nan tata Baaba ta rasulu, wllh Abban Imaan sai kaga abinda taje ta dinga yi" Daddy
ya girgixa kai yana kallonta, Umma tace "Wata kawar amarya na tsaye gaban jama'ah
tana bada tarihin amarya in gaya maka sai Inna ta tafi ta sami yarinyar ya amshe
microphone ta fara xaginta wai wani tsinannen tela ta ba kudi ya mata dinki, Kai
maganganu dai babu dadin ji Abban imaan, ai su Mama Hadiza da Hajiya Aisha na wajen
ni ba sharri na mata ba, wllh kunya kamar in nutse, dama imu imu ne abun xai xo da
sauki amma fa ga dangin amarya sun cika wajen kuma Yan babban gida, bayan ta gama
da yarinya mai bada tarihi ta tafi ta kwashe duk abinda aka ajiye ma amarya da ango
a gabansu ta wuce ta bar wajen sirara, haka ta dinga ma mutane fada wai kada a
xubda datti sun xo cin shinkafa da miya da kaza mayunwata kawai, maganganu dai ga
su nan xar kayan kunya xar takaici Abban Imaan, yanxu fisabilillahi hakan ya dace?"
Girgixa kai kawai daddy ya dinga yi yana salati, Umma tace "Toh ganin abun sai gaba
yake sai naje na sameta nace toh fa ga ruwa can ya cike parlonta ta bar pampon
bandaki a bude, shine Inna ta bar wajen ba shiri da kawarta Baaba ta rasulu, yanxu
nayi laifi a nan Abban Imaan?" Daddy yace "Aa dai dai kenan" Umma tace "Toh nasan
yanxu suna can kila ma ta tara jama'ah ana jirana, kuma ko me xata gaya ma Abbansu
Mujaheed wllh yarda xai yi ya xauna a kai, shi sa ma nace bari in maka bayani
tukun" daddy ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh Allah ya kyauta, kuma hakan da kika
yi shine dai dai, don da ba don haka ba baxa su bar wajen ba, kada ki damu nasan
abinda xan yi, kiyi wucewar ki ciki" Umma ta d'an yi murmushi tace "Toh ngd Abban
Imaan da ka fahimce ni" cikin gidan ya nufa
ta bi bayansa bayan ta sauke boyayyen ajiyar xuciya. Inna ce xaune parlonta kan
tabarma ta daura kafa daya kan daya fuskarta shabe shabe da hawaye tana fyace
majina da hankicin hannunta, ta rasulu dake xaune kan darduma ta girgixa kai kamar
xata saki kuka tace "Ni Ahmadu babu abinda ya fi min ciwo irin yanda muka dinga
yawo muna xaga garin kaduna a adaidaita sahu muna neman wajen casu bayan mun dawo
mun ga karya Rukayya take, daga karshe sai dawowa gida muka yi bamu gane wajen ba,
mai adaidaita na bala'i mu ma muna bala'i, haka muka yi asaran dari biyun mu don da
kyar mai adaidaitan ya amshi dari biyun wai sai dari shidda xa mu basa, wllh mune
har sabon kawo neman wajen casu, babu wajen casu babu labarinsa" Mujaheed dai na
xaune parlon sai kallonsu yake, Yusuf ma haka, Aunty da Ammi da Mama Hadiza ma duk
suna xaune, Abba dai kansa na sunkuye yana sauraronsu, Cikin kuka Inna tace "Duk a
kanmu sanyin daren yau ya kare muna yawo a daidaita neman wajen casu kaman yan
iska, kuma ace inyi hakuri saboda ba a san ciwo na ba, ni wllh yau duk sai mu
tattara mu tafi Police station, wacece kuma Rukayya da xata min wannan toxarcin, me
aka yi aka yi ta, Rukayyar banxa Rukayyar hofi, ni dai wllh Ahmadu na xuba ido
yanxun nan in ga matakin da xaka dauka kan katuwar nan, bikin ma ni sai in iya cewa
a dage sai an bi min hakkina da na Aminiyata ta rasulu tukun, shkkn haka aka kare
casun yau banda mu, ba mu ci Yar shinkafa da kazar da aka raba ba" sai kuma ta
fashe da matsanancin kuka, Yusuf ya sunkuyar da kai yana murmushi, Ta rasulu na
matsar kwallan da ya cika idonta tace "Ni wllh Asiya bata isa ta min haka ba, don
sai dai in sa Muhammadu ya xabi ko ni ko ita...." Sallama aka yi bakin kofa, Inna
ta amsa cikin rawar murya tace "Bukar yau dai bamu samu casun bikin Mujaheed ba,
Rukayya dai yar iska ce wllh"

*Thanks for the prayers via phone calls and WhatsApp messages fans, Allah bar
xumunci, nagode sosai, am feeling a little better in sha Allah*

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

48.....
Shigowa Daddy yayi parlon yana bin dukansu da kallo, Mujaheed ya mike ya koma kusa
da Yusuf, Daddy ya xauna yana kallon Inna yace "Lafiya? Me ke faruwa?" Inna ta
fyace majina a hankali tace "Kana ji Bukar? Bayan fitar ku daxu da yamma shine
kawai na yanke shawarar tafiya wajen da ake casun ko minti sha biyar ne in yi in
juyo duk da dai kun hanani, Toh ya xa ace bikin Mujaheed guda baxan je wajen casu
ba, wllh Bukar mun shiga wajen da ake abun kenan mun xauna ko kayan kwalaman ba a
fara rabawa ba sai ga Matar nan Rukayya tana haki wai in maxa in koma gida ance
ruwa ya cika min daki da parlor, shine fa muka taho kamar mahaukata tare da Ta
rasulu, muna shigowa gida in gaya maka sai muka ga bandaki a bushe tass babu ko
digon ruwa balle ambaliyar ruwa, shine dai muka ta fada rai bace tare da Ta Rasulu
nace mu koma wajen mu ji dalilin da ya sa xata gilla mana irin wannan karyar me
tsada ko mu sa'annin uwarta ne, to fa muka dau adaidaita xa mu koma amma neman
duniya mun wa wajen casun nan bamu gane ba haka muka ta walagigi a adaidaita sahu
sanyin daren nan duk ya kare mana daga karshe muka dawo gida, yanxu fisabilillahi
me na ma Rukayya xata min haka?" Daddy ya girgixa kai yace "Amma ba nace maki kada
ki tafi wajen ba daxu da yamma Inna?" Inna tace "Bukar cewa fa nayi minti goma sha
biyar kawai xan yi, ai da ban leka wajen ba wllh kullatata Mujaheed xai yi shi sa
nace bari kawai in je a tsatstsaye in dawo, kuma meye laifina" Daddy yace "Haba
Inna, yanxu fisabilillahi ki shirya ki shiga cikin yara ki xauna kice kin tafi
wajen casu, me yasa kike mana haka don Allah?" Inna tace "Haba Bukar don dai minti
sha biyar in juyo, wa ma xai san naje wajen banda mai sa ido? a baya fa muka xauna
don ma kada a lura da mu" Daddy yace "Kwata kwata bai kamata, ban ga amfanin shiga
cikin jikokin ki wai kinje casu ba, mu dai idan mun gaya maki magana baki ji baki
amfani da shi, bamu san ko kina da wasu masu gaya maki bane bayan mu, ni bana jin
dadin hakan da kike yi, kullum ayi ta magana amma baki gyarawa Inna, abinda baki
sani ba a nan shine har mu kina xubar mana da mutunci a idon duniya...." Shiru Inna
tayi sai 'yan idanuwa, a hankali ta Rasulu tace "Wllh Bukar sai da nace mata mu
hakura kar mu je amma Asabe taki saurarata....." Juyawa Inna tayi tana kallonta
baki sake, can ta kalli Daddy tace "Kaga xata gilla min sharri da rai na ko Bukar,
to wllh ta ma riga ni shiryawa har tana cewa xata tafi ta bar ni ina bata mata
lokaci, ni dai a dinga jin tsoron Allah ba ruwana" Ta rasulu tace "Yo idan ban ji
tsoron Allah ba tsoron ki xan ji Asabe? Ke dai ki dinga bin 'ya yan ki sau da kafa
baki da kamarsu, da Muhammadu ne yace min kada in tsallake ko nan da kofa wllh
baxan tsallake ba, kawai ki sa mu shiga cikin jikokinmu mu xauna kamar wasu
gantalallu har ana gilla mana karya don a kora mu...." Inna tace "Ni dai nace a
dinga jin tsoron Allah ba ruwana, biki kuma gashi nan dai an gama sai kowa ya san
na yi..." Ta Rasulu tace "Ina nan sai na raka Mujaheed gidansa na sa albarka...."
Inna ta tabe baki tace "Toh naji na tafi casu ba da izinin ku ba Bukar, walakanta
ni da Rukayya tayi fa??" Daddy yace "Ae ni na kirata nace ta fada maki haka saboda
hakan kadai ke iya sawa ki dawo gida, don xuwan ki wajen bashi da fa'ida" Salati
Inna ta saki tana kallonsa a hankali tace "Allah ya fi annabi sani...." Ta Rasulu
tace "Toh ai da sauki tunda kai ne ka sa ta, kuma gaskiya da ba haka aka yi ma
Asabe ba bata da ranan baro gun" Inna ta kalleta ta gefen ido ta rike ha6a tace
"Ohh.. Naga abinda ya isheni, mutane dai basa tsoron Allah, da ranka ma sai an
dinga bin ka da sharri" Mikewa Daddy yayi yace "Mu dai muna neman alfarmar ki dinga
daukar maganar mu kina aiki da shi ba don mu ba don Allah..." Inna tayi kasa da
murya tace "Toh ni dai kayi hakuri kuskure ne na riga nayi, sai dai Allah ya kyauta
na gaba" Bai tanka ta ba ya fita parlon, Inna ta bi sa da kallo, Mikewa Abba yayi
yace "Toh a dai yi hakuri inna" daga haka ya fita parlon shi ma ta bi sa da kallo,
Mujaheed ya mike yace "Tsofe tsofe kice sai kin je casu..." Bai jira cewarta ba ya
fice parlon yana murmushi ta bi sa da kallo, Yusuf ya mike ya fita parlon shi ma ta
bi sa da kallo, Aunty dake kokarin danne dariyarta ta mike tace "Toh don Allah kuyi
hakuri Inna" Inna ta tabe baki bata dai ce komai ba, Aunty tace "Bari in je Inna,
muna aiki ne" daga haka ta fita, Ammi ma tayi mata sai da safe ta fita, tagumi inna
tayi bayan duk sun fita tace "Lallai Bukar ya xama abun tsoro Ta Rasulu, ni da ba
don a kan idona na haifosa ba ma sai ince canjin sa aka min a tsinannen asibitin
turawan da na haifesa, ke kiji ashe shi yasa katuwar mata ta kirani ta gilla min
karya, duniya ta lalace ni patuu" Ta Rasulu tace "Ai yanxu darajar sa Rukayya xata
ci baxa mu daukaka kara ba, amma wllh bata ci bulus ba, ki kyale Yar iska Allah ya
kai mu wayewan garin gobe lafiya" Inna tace "Shi kuma Bukar dama kada ya sake tako
min nan tunda haka ya xama, ba ruwana ya je yyi ta kansa" Ta Rasulu tace "Atoh, ni
da ace Salihu ne da na masa barbadin bala'i ynxu...." Mama Hadiza dai sai kallonsu
take daga inda take xaune, Inna tace "A'a ni dai gwara da na bar figaggen da
halinsa ba ruwana ace naje ina cecekuce da shi, gwara kawai da na masa shiru ya
gama bambaminsa ya fita, ae shi Ahmadu baya haka, dama ni ban so ya shigo ba sai
Ahmadu ya gama yanke hukunci, Toh sai gashi Allah ya jefo mana shi, haka kawai inje
inyi magana bafillatanar matar sa ta ji haushi na ta kullace ni, A'a ba ruwana" Ta
Rasulu tace "Dama shirun ya fi ina xaki tsaya cecekuce da d'an cikin ki?" Inna ta
tabe baki tace "Ni dai ba ruwana, Allah ya shirye sa, amma Bukar gaskiya ba shi da
hali duk cikin 'ya yana"
Washegari tun da imaan ta tashi take jin xaxxabi da ciwon kafa, har karfe tara bata
fito ba don ko Ina a gidan cike yake da jama'ah, Maryam dai tun da ta kawo mata
breakfast dakin bata sake ganinta ba, Ammi ce ta shigo dakin karfe goma saura
ganinta kwance ta karasa kusa da gadon tana kallonta tace "Lafiya?" Mikewa xaune
tayi da kyar tace "Ammi kamar xanyi xaxxabi kuma kafana ciwo suke min" Ammi ta kai
hannu jikinta ta ji da xafi, Juyawa tayi ta fita ta wuce kitchen ta hado mata wani
shayin ta dawo tace "Kin ma yi wanka?" Kai ta gyada ma Ammi, Ammi ta mika mata
shayin tace "Ki sha shayin sai ki sha drugs din ki" karba Imaan tayi ta fara Shan
shayin Ammi ta dauko drugs dinta inda suke ta ballar mata bayan ta sha kusan rabin
shayin Ammi ta mika mata maganin, Karba tayi ta sha Ammi tace "Ki tafi can bangaren
Inna ki kwanta baki xa su sauka nan xuwa anjima kadan" Imaan ta xaro ido tace "Ammi
bandakina fa?" Ammi tace "Ku dai ba ku da hali mai kyau abu dai na kwana daya, to
sai ki kinkimi bandakin ki tafi da shi bangaren Inna ki ajiye" Imaan kamar xata yi
kuka tace "Wllh bata ma mutum fa xa su yi, ni dai gwara in kulle in boye makullin"
Ammi tace "Toh ki kulle tunda baki da hankali" Imaan bata ce komai ba Ammi ta juya
ta fita, Mikewa tayi da kyar ta kwashe gaba daya kayan cosmetics dinta dake gaban
madubi ta xuba su drawer, ta cire farin bedsheet dinta ta dau mai duhu ta shimfida
tana turo baki, ta shiga bandaki ta dauke sabulu da sponge dinta sai brush da
toothpaste ta dawo daki ta adana, hijab ta saka bayan ta dau sabbin kayanta na biki
da xata saka a cikin leda ta fita dakin tana dingishi, babu yanda ta iya haka tayi
ta gaida mutane har ta isa part din Inna, Ta Rasulu ce tsaye bakin kofa tana kallon
tsofaffin da ke xaune cikin parlon tace "Don Allah ba don mu ba idan kun cire
takalma a dinga ajiyewa a gefe guda kar su bata bakin kofar, bikin fa na yan gayu
ne, haba takalma sai kace na masu talla" Imaan ta raba ta gefenta ta shiga parlon,
daga kitchen Inna ya fito rike da cooler da plate ta duka tace "Toh ni dai basu
gama girkin ba ina ji, wannan dai 'yar wainar da aka xubo min ne da safe sai in
manna ma kowa guda biyu, ga miyar taushen mai kyau da nama...." Kallon Imaan dake
gaida mutanen parlon xata wuce daki Inna tayi da sauri tace "Waye wannan kuma?"
Juyowa Imaan tayi ta hade rai tana kallonta, Inna ta mike tace "Me xaki je ki min a
daki??" Imaan ta marairaice tace "Inna baki suna dakina ne kuma bacci nake son yi"
Inna tace "Naga abinda ya isheni, to Ina ruwanki da bakin Imaan? Gaskiya ni dai
kiyi hakuri ki xo ki wuce na saka ma dakina turaren wuta kuma ma wannan
mutumin...." Ko sauraranta Imaan bata yi ba ta shige dakin da sauri tana turo baki
ta kulle, juyawa tayi, tayi still ganin Mujaheed kwance saman gado... Ta xaro ido
tana kallonsa, A hankali Imaan ta bude kofar xata fita sai kuma ta juya tana
kallonsa, Bude ido yyi yana kallonta shi ma, ta turo baki ta fita da sauri ta kulle
kofar. Inna dake ta xuba waina a plate tana diga miya kamar xa a ba jarirai ta
kalleta tace "Har kin fito knn, toh sai ki koma ki tambayar min shi ko in xuba masa
wainar, tun safe yake nan ni dai ban ga ya ci komai ba, to rabuwa da ni haukane da
xai daga hankali haka? Ni dai ba ruwana" Imaan xata fita Inna tace "Ji walakanci
ina mata magana tana wucewa, baxa ki shiga ki tambayar min shi bane in je da kai
na?" Dawowa tayi tana turo baki ta shiga dakin, Inna tayi tsaki tace "Babu abinda
ta mance a halin ubanta mara kirki, nan ya wanke ni tass jiya da daddare, ni dai na
yafe masa ba ruwana, ba don naka naka bane ai yanxu da sai dai in kora figaggiyar
'yar nan tasa ince ta fita, Toh kada laifin ubanta ya shafeta" Imaan na komawa
dakin ta samesa idonsa rufe kamar daxu, ta d'an yi jim, can ta karasa kusa da gadon
tace "Inna tace ta xubo maka wainar shinkafa?" shiru yyi har sannan bai bude idon
ba, tace "Ka ji" nan ma bai ce komai ba, ta d'an ta6a kafarsa tace "Yaya ka ji?"
Nan ma shiru kake ji, tabe baki tayi ta juya xata wuce ya fixgota ya bude manyan
idanuwansa da suka sauya kala yace "Sai kin min ihu a kai saboda baki da hankali?"
Shiru tayi tana kallonsa, can ta ta6a hannunsa ta durkusa kusa da shi a hankali
tace "Baka da lafiya ne Yaya?" Mikewa xaune yyi ta dinga kallonsa, murya can kasa
yace "Make me a cup of tea" Mikewa tayi ta nufi kofa ya bi ta da ido, Inna dake
duke har sannan tana jiran ta fito tace "Xai ci ko in rabar ma tsofaffin nan?"
Imaan tace "Shayi yace in kawo masa" bata jira me Inna xata ce ba ta shiga kitchen
ta dau cup ta bude flask ta xuba ruwan xafi a cikin cup din sannan ta dawo tana
kallon Inna tace "Ina Kayan shayin?" Inna tace "Wanda ke da shi ku ka siyo ku ka
ajiye min kenan, toh kar ma ki bata lkcn ki ki koma bangarenku ki xuba masa kayan
shayin a ruwan xafin nawa ya kusa karewa bbu wanda xan ba ma wllh" Wata tsohuwa
dake xaune parlon tace "Haba Hajiya Asabe sai kace ba iyayensu ke siya maki ba?"
Inna ta mike tana kallonta, can tace
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

"Ehh lallai duniya ta lalace, toh wllh har na mance rabon da iyayensu su siya min
kayan tea, sai dai yaron nan Bulasawa, kuma baya jiran wani ya kare yake kawo min
wani, kawai mata tsohuwa baki san kan komai ba ki tsomo mana baki muna magana, ni
dai ba ruwana a dinga jin tsoron Allah" Tuni imaan ta fice ta wuce part din su tana
turo baki, Bedroom dinta ta fara shiga ta dau wayarta tayi dialing number Sadeeq,
katsewa yyi ya kirata, a hankali tace "Good morning...." Yace "Morning my dear,
hope kin tashi lafiya?" Imaan ta langwabar da kai tace "Sure, happy birthday once
again..." Yana murmushi yace "Thanks much baby, I was so happy with ur text earlier
this morning, naji dadi sosai baby" murmushi tayi tace "When xaka xo ka amshi gift
din ka?" Yace "Ohh wai baxa ko xo party din ba?" A hankali tace "I might, I might
not, kasan fa yau muna biki a gida.... But all the same ka dai xo ka fara amsar
gift din ka" yace "Ni dai sai kin xo party din dear" murmushi tayi tace "Na ji"
yace "Toh yaushe xan taho amsar gift din?" Tana juya ido tace "After Juma'at
prayer" Yana murmushin sa mai kyau yace "Toh sai na xo baby" tace "Amma fa kar ka
shigo layinmu, ka tsaya bakin titi xan fito" yace "Alryt dear xan kira ki idan na
iso" tace "Tohm bye" daga haka ya katse wayar. Kitchen ta wuce don hada ma Mujaheed
shayi, Ammi dake bayan kitchen din da Mama Hadiza suna magana tana kallon Imaan ta
window tace "Me kike nema?" Imaan tace "Inna xan xuba ma kayan shayi nata ya kare"
Ammi bata ce komai ba suka ci gaba da maganan su da Mama Hadiza, imaan ta hada
shayi mai kauri ta rufe cup din ta fita, Ko kallon Inna bata yi ba ta shige cikin
daki Inna na cewa "Ni dai dakina ya xama kamar kasuwa yau duk a tafi a bar ni da
wari..." Ajiye shayin Imaan tayi tana kallonsa tace "Gashi yaya" ya bude ido ya
mike xaune ta dau shayin ta mika masa tana kallonsa ya karba, makulli ya mika mata
yace "Go to my bedroom and get me my phone" ta xaro ido tace "Ni kuma? A'a sai da
in gaya ma Maimoon ta dauko sai ta bani, ni ba ruwana" Bai ce komai ba ya dinga
sipping shayin a hankali, Mikewa Imaan tayi ta fita, tana fitowa parlon Inna ta
kusa cin karo da Mama Hansai "Inna na ciki kuwa? Ga Ta Rasulu can tana fada da
Hajiya Rukayya" Cewar Hansai kenan tana haki ta shige parlon Inna, Imaan dai tayi
wucewarta, tsakar gida ta tadda ta Rasulu tsaye tana fadi Umma na fadi, Ta Rasulu
na tafe hannu tana jujjuya ido tace "Nan nan aka auro ki kina raka yayarki Shafa
tallan shinkafa da wake a kasuwar tasha, Hijabi duk a yakune, Zani duk duwaiwai a
waje tsabar kodewa shine kin xo kin samu gida kin xama kamar buhun masara xaki kawo
ma mutane raini toh wllh idan ban sa yarana mata sun nakada maki shegen dukar da
xai fidda maki hakora uku ba kice ba Yar gidan mai salati bace ni, Ni nafi karfin
ki wllh ni ba Asabe bace...." Muryar Inna suka ji tana sakin salati da karfi tace
"Rukayya ita aminyar tawa ta Rasulu kike ma xagi ta uwa ta uba?? Ita ta rasulun
kike kokarin dambe da?? La ila ha illallahu Muhammadur rasulillahi sallallahu
alaihi wassalam, karshen duniya ta kama, ayi maxa a kira min Ahmadu amma banda
Bukar...." Imaan ta girgixa kai tayi wucewarta ciki ta wuce sama, bude kofar dakin
Mujaheed tayi ta shiga ta lumshe ido ta nufi saman gadonsa ta dau wayarsa, calls
kusan ashirin yyi missing, yawanci kuma duk na Safeenah ne sai abokansa dake ta
nemansa tun safe, ta tabe baki ta juya xata fita sai ga kira ya kara shigowa wayar,
kallon screen din tayi ganin Safeenah ne tayi tsaki har ta isa kofa sai kuma ta
daga ta kai kunne tayi shiru, daga daya bangaren Safeenah tace "Haba Mijina, tun
asuba Ina ta kira no response are you okay?" imaan ta tabe baki tace "Toh ba shi
bane" Da mamaki Safeenah tace "Wacece wannan?" Imaan tace "Kanwarsa ce, sai ki jira
idan na kai masa wayar" bata jira cewarta ba ta katse kiran ta fito dakin ta kulle
kofar. Ba karamin taro aka hada a tsakar gida ba Inna na ta ma Umma tijara Ta
Rasulu na taya ta, ba abinda suka mance basu gaya mata ba, mutane sai bada hakuri
suke, Ammi dama ko a gyalenta sai aikinta take, haka ma Mama Hadiza da ta ki
fitowa, Aunty ce dai ta taho tana bada hakuri Inna ta tsigaleta ita ma ba shiri ta
bar wajen, inna na ganin Imaan ta fixgota tana nuna ma jama'ah ita tace "Tana kamar
haka fa Ahmadu ya aurota, amma yanxu ku dubi yanda ta koma kamar alade, Toh komai
ta samu raruma take ta boye... ya ki halal ya ki Haram, duk ta tsiyace min d'a
na... Shine kuma saboda abinci xata yi ma aminiyata rashin mutunci... Allah ya
tsine ma abincin da xa aje a xaxxage a shata, tunda a kansa xaki xagar min Ta
Rasulu, to wllh yau sai Ahmadu ya xaba ko ni ko ke a gidan nan ba ruwana, dama har
yanxu ban huce casun da kika hanani ganin karshensa ba..." Umma dake ta kai koma ta
kinkimo babban cooler din shinkafa da nama, da wani cooler din tuwo da na miya, da
na fried rice da soyayyen kaji, da na masa duk ta dire masu a gabansu tace "Ni dai
na xama kadangaren bakin tulu, ba kuma wani ya haifa min Mujaheed ba balle a nuna
min iko da shi, Ikon ku ya tsaya iya Bukar da Ahmadu amma banda Mujaheed, abinci
kuma ga shi aje ayi ta ci ayi kashi...." Ammi dake tsaye gefe ta taho har inda Umma
take tace "ke dai a kwakwalwarki hauka ya kare, ita Innar kike fada ma magana haka
saboda shinkafa" dakatar da ita umma tayi ta hanyar daga mata hannu tana mata
matsiyacin kallo tace "Ni ban yi da juya ba, kije can ki ji da sauran ciwon da kika
haifo duniya..." Aunty ta riko Ammi ganin finciko Umma xata yi, babban Jambox
Hajiya Saude ta dauka ta kunna waka ya kauraye tsakar gidan kawayen Umma suka fito
aka fara taka rawa irin na manya ana jujjuyawa, Umma na ganin haka ita ma ta shige
cikin masu rawa ta fara takawa tana tafe hannu, Inna ta gwalo ido sai kuma ta fashe
da matsanancin kuka tace "Ni kika xaga Rukayya?? Ni din??" Ta Rasulu ta dinga bude
kulolin abincin tana ball da su duk abincin ya tarwatse a kasa, tana huci tace "Don
kaza kazan ki dake da abincin kun ci kaza kazan ku...." Mama Hadiza ta fito daga
part din su Imaan da sauri ta tafi ta dauke jambox din da waka ke tashi ta kashe
sannan ta tarwatse sa a kasa tana kunduma ma Umma xagi tace "Idan kina tunanin
uwata xa ki gaya ma magana yau ki xauna lafiya kin yi karya wllh, dama can ba son
auren nan Mujaheed yake ba, ke ce ke son auren saboda abun duniya, xabin ki ce
yarinyar ba tasa ba, kuma wllh wllh kin ji rantsuwar musulmi koh?? To baxa a daura
auren nan ba, bari Ahmad din ya shigo.... in sha Allahu sai kin ji kunya yau, sai
mun kunyata ki yau...."

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

49.....

Shewa Umma tayi tana dariya tana ma Mama Hadiza wani kallo tace "Toh Sannu Uban
Mujaheed.... Ahmadu, bari ki ji ko ita Mahaifiyar taku bata kai ta hana auren nan
ba balle ke...." Mama Hadiza tace "Toh mu xuba da ke yau, wllh sai kin san kin yi
da Inna, sai kin san kin taba uwar mu, xaman ki a gidan nan ya kare in sha Allah"
Umma na ta rawa tace "Toh Ahmadu" Kujerun da aka jera a tsakar gida Inna ta dinga
watsi dasu tana ball da su tana cewa "Kowa ya tafi gidan ubansa an fasa bikin, in
dai da raina ni patuu baxa ayi auren nan ba, a kira min Ahmaduuuu..." Cikin daga
murya ta Rasulu ma ke cewa "An fasa biki kowacce ta tattara ta koma inda ta
fitoooo, Aisha ki kukkula masu shinkafar a leda su wuce, an fasa bikin...." Mama
Hadiza da xuciyarta ke tafarfasa ta shiga kiran Abba da wayarta, yana dagawa tace
"Ya Ahmad kana Ina? Ka dawo gida yanxun nan don Allah...." Abba yace "Lafiya?" Mama
Hadiza tace "Ba lafiya ba, ka taho yanxu don Allah" bata jira cewarsa ba ta katse
wayar, Yusuf da shigowarsa gidan kenan ya nufi Inna da mamaki ganin yanda take ta
watsi da kujeru yace "Lafiya Inna?? me ke faruwa??" Inna ta fashe da matsanancin
kuka tace "Isuhu xagi ta uwa ta uba Rukayya ta mana ni da ta Rasulu daga nace ta
Rasulu taje ta amso mana abincin da xa mu raba ma bakin da ke parlona kada su tafi
su ce an bar su da yunwa a bikin jikana, shkkn Rukayya ta dinga xagin ta Rasulu har
ana rirriketa, da gudu Hansai ta xo ta sanar min shine na taho da sauri jin ba'asi,
Toh wllh ni har xagin da ban san da shi ba a rayuwar nan sai da Rukayya ta min, har
da ce min Ahmadu da Bukar kadai nake da iko da a duniyar nan, tana xagina tana
xagin ta Rasulu, Aisha ta xo ta mata magana ta hada da ita, Hadiza ma ta xo yi mata
magana ta hada da ita, Uwarka kadai ce munafuka wai ta xo tana ban hakuri maimakon
ta taya ni kamar yanda Aisha tayi, Toh ni dai nace wllh an fasa daurin auren nan...
yau dama naji labarin ita tayi masa xabin shegiyar yarinyar, to jiya a wajen casu
ko gaisheni fa yarinyar bata yi ba sai kallon banxa ta min da lebbenta kamar gandan
saniya" Yusuf ya kamo hannunta a hanki yace "Haba Inna, wannan ba girman ki bane,
kiyi hakuri don Allah, gidan fa da baki don Allah kiyi hakuri ki bari....." buge
masa hannu Inna tayi a fusace tace "Kaji min mutumin banxa ina ruwana da baki, ba
suna kallo ake ci min mutunci ba sun taho sun tare min? Bakin banxa bakin hofi...
To wllh kowa ya kama hanyar gidansu dama ba ruwana...." Gaba daya su Maimoon da
Maryam dai na tsaye gefe sai kallon ikon Allah suke gida duk ya hautsine, kawayen
umma da umma kuma basu fasa kunna Jambox suna ci gaba da taka rawa ba suna tafi, Ta
rasulu ta tafi iya karfinta ta wangale gate cikin daga murya tana cewa "Ku fito ku
tafi gidajen ku babu xancen biki jama'ahhh" Aunty ce ta dinga tambayar su Maimoon
inda Mujaheed yake don tasan shi daya ke iya jan Inna ta bar tsakar gidan, Imaan
dake tsaye sai hararan umma take, nan ko jira take ta kara gaya ma Inna magana ta
rama mata, tana kallon Aunty tace "Yana can dakin Inna" Aunty tace "Yi maxa ki tafi
ki kirasa kiyi sauri" Juyawa tayi ta wuce part din Inna tana rike da wayarsa har
sannan, babu kowa parlon Inna duk mutanen ciki sun taho tsakar gida kallo, Ta bude
kofar dakin ta shiga, Xaune ta samesa har sannan bai gama shan tea din hannunsa ba,
ta hade rai tace "Yaya Aunty tace in kira ka...." Ya mata wani kallo yace "Did I
ask you to announce I am here?" Turo baki tayi tace "Toh Inna ce da Baaba ta Rasulu
ke fada a tsakar gida" Ya buda manyan idanuwansa yace "Fada kuma??" Ta gyada masa
kai, yace "Da wa?" tace "Umma" shiru Mujaheed yyi, can ya girgixa kai ya ajiye cup
din hannunsa ya mike ya fita, bin bayansa imaan tayi, Tun daga nisa Mujaheed ya
tsaya ya dinga kallon crowd da aka tara a tsakar gida, ga sautin waka, ga muryar
Inna, ga muryar ta Rasulu, abinda bbu dadin ji, imaan ta iso inda yake tsaye tace
"Yaya kaje ka ma Inna magana" shi dai bai ce komai ba, can ya karasa wajen a
hankali yana kallon Inna kafin yace komai ta rushe da kuka tace "Mujaheed wai ni
yau Rukayya ta xage tass, Mujaheed ba abinda ta mance bata gaya min ba...." Yace
"Toh mu je ciki a kira maki Abba yanxu, wayar na can bangaren ki" Bayani ta dinga
masa tana kuka, yace "Nace mu je a kira Abba..." da haka Inna ta bisa tana kuka
wiwi tana jera Allah ya isa ma umma, Ta Rasulu dai na can bakin gate tsaye ta
wangale gate din tana ihun a xo a tafi gida an fasa biki, su Aunty suka dinga hada
kujerun da aka tarwatsa tsakar gidan kowa dai rai ba dadi. Mujaheed ya dinga kallon
Inna Bayan sun shiga parlonta, tayi kukanta mai isarta, Imaan dai na durkushe
parlon ita ma tana kallonta, Inna ta hadiye kukan da take tana kallon bakin kofa
ganin Tsofaffin da suka xo biki ne suka dawo mata tace "Yau naga abinda ya
isheni.... ba an fasa bikin ba ku yi ta kanku ku koma gidajen 'ya yan ku mana bayin
Allah...." Wata Yar tsohuwa tace "Ae bai kai ga haka ba Hajiya Asabe hakuri xa ki
yi, tun da an fara abun nan a gama...." A fusace Inna tace "Toh duk ku koma tsakar
gidan ku xauna a can, ni dai ba ni ke aurar da d'a ba ba ruwana, a rufe min kofa"
sallama suka mata suka wuce ta mike ta kulle kofarta ta dawo tana kallon Mujaheed
tace "Ka kira min Ahmadun?" Shi dai bai ce mata komai ba, a fusace tace "Wai baka
ji na ne Mujaheed??" Yace "Ae sai ki saurara ki gani" tana fyace majina tace "Dama
kada in kuskura in ga Bukar a parlon nan yau ba ruwana, kada ya xo min Ahmadu kawai
nake bukata" Bata rufe baki ba sai ga Abba ya shigo da sallama tare da Daddy ko
wannensu da wani expression yake kallonta, Inna ta tsuke fuska tace "Ni dai Ahmadu
kadai na kira...." Abba ya xauna har sannan bai daina kallonta ba, Daddy dai bai ce
komai ba ya xauna, sai ga Mama Hadiza ta shigo, Inna tace "A kira min Aisha da
Amina ma su xo a akan idonsu aka yi komai ai" Mama Hadiza ta nemi waje ta xauna
babu walwala tace "Suna xuwa" Aunty ce ta fara shigowa sannan Ammi duk suka xauna
saman tabarma, Ta Rasulu ce ta shigo parlon tana kuka wiwi kamar yarinya ta wuce
daki sai ga ta ta fito da 'yar jakarta tace "Asabe gidan nan ba gidan xama bane, ni
tunda uwata Mai salati ta haifeni ba a ta6a min cin mutuncin da Rukayya ta min yau
ba, Ina dalili ina Dan mafari ni sai yanxu wasu maganganun ke dawo min suna min
ciwooo..." Mikewa Inna tayi ta rushe da kuka ta rike jakarta gamm tace "Ai babu
inda xaki Ta Rasulu muna nan sai an bi mana hakkinmu....." Rungumeta ta Rasulu tayi
nan suka dinga rusa kuka a tsaye, imaan ta boye fuskarta ta dinga dariya kasa kasa,
Mujaheed kam sunkuyar da kansa yyi, Abba ma dai kansa na kasa, Daddy kuwa sai
kallonsu yake, kuka mai isansu suka yi sannan suka saki juna, Inna ta maida jakar
daki ta fito, Ta Rasulu ta xauna ta daura kafa daya kan daya ta tsuke fuska, Inna
ta xauna tana kallon Abba tace "Toh Ahmadu yau dai sai ka xaba ko ni ko matarka
Rukayya...." Sai a sannan Abba ya dago kai yana kallonta, Inna tayi mitsi mitsi da
ido tace "Kuma aure na samu labarin xabinta ce yarinyar ba xabin Mujaheed ba don
haka daurin aure ya fasu in dai ni na haife ku" Abba ya girgixa kai ya ma rasa
abinda xai ce, daddy ya d'an sauke ajiyar xuciya gently yace "Amma me ya faru Inna?
Meye musabbabin matsalar?" Wani kallo Inna ta jefa masa ta kankance ido tace "Dama
wannan ya xama maganan ka ta farko kuma ta karshe a parlon nan, don ni ban san ma
wa ya gayyato min kai ba, abinda ya faru kuwa shine yau har uwata dake kabari sai
da Rukayya ta xaga a kan shegiyar shinkafa, har tana neman dunguri na, ga rawa da
ta dinga yi a gabana tana min murgude murgude da kawayenta wai su fitsararrun yan
tasha, daga fa mun je amso ma bakin mu da ta Rasulu shinkafa, xagi ta uwa ta uba
dai yau mun sha sai godiyar Allah..." Girgixa kai kawai daddy yake yace "Ikon
Allah" cikin rawar murya Inna tace "Toh ni yanxu na xuba ido in ga matsayina a
wajen ku in ga matakin da xa ku dauko, ko kaffara baxan yi ba tun da Ahmadu yake ko
kallon banxa bai taba ma Hadiza Uwar Rukayya ba, toh ni me na mata daga xuwa amsan
shinkafan biki xata tsigaleni..." Sai kuma ta fashe da kuka mai ban tausayi tace
"Me na ma Rukayya yau ta min cin mutunci wanda da wuya tabon ya goge a jikina" Ta
Rasulu ta saki kukan ita ma tace "Me kuwa xa ki mata Asabe, ni ba don albarkacin ki
ba nasan da yau sai 'ya yana sun turo motar sojoji an fitar da Rukayya gidan
nan...." Inna ta dakatar da kukan da take da sauri tace "A'a yanxu ma bai baci ba
Ta Rasulu, kira su su turo motar babu abinda ya sha min kai wacece kuma Rukayya ina
ruwana da ita xata ci albarkaci na? Su kwasheta ba ruwana" Abba dai bai ce komai ba
har sannan, can dai ya dau wayarsa ya shiga kiran layin umma, har ya gama ring ba a
dauka ba, ya kalli Mujaheed da ke ta kallon inna yace "Tafi ka kira min uwar ka
yanxu..." Mujaheed ya sunkuyar da kansa bai dai ce komai ba ya mike ya nufi kofa a
sanyaye ya bude, karo ya kusa ci da umma dake labe tana sauraron komai, shi dai bai
ce mata komai ba, har xai tsaya kawai yayi wucewarsa don bai ma son ransa ya kara
baci, Sallama Umma tayi ta shiga parlon da lullubi kanta a kasa, Inna na ganinta ta
saki salati tana tafe hannu tace "Almunafunfun kenan ku ke ga, to ai ba da gyale
kika min cin mutunci a tsakar gida ba don haka sai ki cire ki ajiye a gefe a gama
magana, kuma ni dai Allah ya isa rawan da kika dinga yi a gabana kina mokade
mokaden maxaunai" Umma ta xauna nan kusa da kofa bata dai tanka ta ba, tana
kallonsu Abba tace "Ga ni nan" Sai hararanta Mama Hadiza take, Abba na kallonta da
kyau yace "Ita Innar kika xaga yau ko?" Ta Rasulu tace "Ta uwa ta uba kuwa, har ana
rirriketa xata doketa, ni dai guduwa nayi na koma bakin gate, kawai 'ya yana su ji
daga xuwa biki duka ya ritsa da ni" Abba na kallon Umma yace "Toh yayi kyau, ki
tafi gidan ku yau, ko minti goma ban son ki kara a gidan nan...." Da sauri Inna
tace "Aa baxa fa ta tafi da igiyar ka mai daraja ba tana galantoyi a titi, yanxun
nan xaka datse shi ta tafi gidan nasu tsirara, sai kuma taje can ta dinga xagin
uwarta mai ciwon
kafa a kano..." Ta Rasulu tace "Ko ta koma wajen shafa mai shinkafa da wake a
kasuwar tasha" Umma tace "Toh Alhmdllh xan tafi amma sai a barni in sallami bakina
da suka xo biki ko xuwa da yamma" Inna ta mike tace "Wani biki? Bikin da aka fasa
ko kuma wani daban kike nufi?" Kallonta umma tayi da sauri, Inna ta tabe baki tace
"Ae babu xancen wannan auren, don baxa a ma jikana dole ba, maxa maxa a kira dangin
shegun amaryar a sanar masu suyi hakuri Mujaheed yace ya fasa, in dai da raina wllh
an fasa auren nan, ni ba ruwana" Abba yace "Bai kai ga haka ba Inna..." Katse da
tayi tace "Ya kai har ya xarce Ahmadu" Daddy yace "Haba Inna, kananun mutane kike
son ki maida mu, daurin aure nan da 'yan awanni kice a fasa???" Inna tace "Ba
ruwana idan ma jarirai xan maida ku, daurin aure dai ni patuu nace bbu shi, idan
kuma akwai wanda ya isa ya ja da ni to Bismillah...." Mama Hadiza sai gyada kai
take don hka ya mata mugun dadi, a hankali Abba yace "Inna to bakin da suka xo daga
garurruwa da dama don bikin fa? Ya xa mu yi da su?" Inna tace "Oho sai a nemi wata
a daura auren da ita amma ba xabin Rukayya ba, babu kuma shegen da ya isa ya sa in
canxa ra'ayi na gaskiya..." Ta Rasulu tana tabe baki tace "In har kuna son gamawa
da Asabe lafiya ku bi abinda tace sau da kafa, jama'ah kuma da aka tara tunda abun
kunya ku ke gudu sai a samo yarinya ko cikin 'yan uwana ne a daura auren kowa ya
hutu" Inna tace "Shi kansa Mujaheed din ba son auren yake ba wllh wllh, idan kuma
karya ne a kirasa a tambayesa a ji ta bakinsa, haka kawai xa a cutar min jika a
masa auren dole abinda aka daina yayi tun lokacin kakata Furera...." Daddy yace
"Toh gwara a kira Mujaheed din a fara jin ta bakinsa Inna...." Dakatar da shi Inna
tayi tace "Ka karyata ubanka isuhu Bukar.... Kuma a kira Mujaheed din" babu Wanda
yace mata komai a parlon, Umma dai tuni yan hanjinta suka kada ta fara matsar
kwalla, idan aka ce an fasa auren nan da gaske ai an kasheta kenan balle ta san in
sha Allahu sai anyi, cikin tsawa Inna tace "A kira Mujaheed din mana tun da karya
nake" Mama Hadiza ce ta kira layin Mujaheed, yana dagawa tace "Ka taho parlon Inna
yanxu" daga haka ta katse wayar, Inna dai sai girgixa kafa take, ba a dau lkci ba
Mujaheed ya shigo parlon da sallama kansa a kasa, nan kusa da imaan dake xaune
jikin kujera ya duka don babu waje parlon bai kuma son xama kan kujera, Inna na
kallonsa tace "Tsakanin ka da Allah Mujaheed kana son auren yarinyar nan da Rukayya
ke son hada ka da?" Shiru Mujaheed yyi yana kallonta, can ya saci kallon Umma dake
kallonsa tana matsar kwalla, sunkuyar da kansa yayi, Inna tace "Kun ga munafuki
koh??" Abba ya hade rai yace "Don't waste our time Mr Man" d'an murmushi yyi yana
kallon Inna yace "Toh Inna da bana sonta ai baxan yarda da auren ba" Sake baki Mama
Hadiza tayi tana kallonsa, Umma ta sauke boyayyen ajiyar xuciya, Inna ta saki
salati tace "Jini ba wasa ba ni Asabe, Allah sarki Ahmadu kana cikin jarabawar
ubangiji 'ya ya duk sun kwaso halin uwa...." Wani kallo Mujaheed ya dinga mata,
Inna tace "Toh oho dai, da ka so yarinya da kar ka so ta duk uwasu daya ubansu
daya, aure dai tunda aka xageni aka ci ma ni da aminiyata mutunci babu xancensa an
fasa, sai dai duk abinda xai faru ya faru Babu kuma wanda ya isa ya canxa min
ra'ayi ko waye shi kuwa, idan baku son a maku kallon kananun mutane kamar yanda ku
ka ce sai a samu wata yarinyar a aura masa amma ba xabin Rukayya ba, xan nuna ma
kowa ni jarababbiya ce yau" daga haka ta mike ta shige daki tana goge guntun
hawayenta, Abba ya jinginar da kansa da kujera yana salati a ransa, Daddy kam sai
girgixa kai yake ya rungume hannayensa, a hankali Imaan ta mike ta fita parlon
Mujaheed ya bi ta da ido haka ma Abba da Daddy.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788
50. Imaan

Daddy na kallon ta Rasulu a hankali yace "Yanxu Baaba don Allah baxa ki bata hakuri
a daura auren nan ba saboda mutanen da aka tara??" Ta Rasulu ta xaro ido ta mike
tace "Toh Asabe ga Bukar nan wai in baki hakuri a daura auren... da yake dama cikin
'ya ya ma akwai mai gudun bacin ranka akwai kuma wanda bai san ciwon ka ba kwata
kwata, toh Bukar dai bai san ciwon ki ba, don da ya sani sai in da karfinsa ya kare
a shakiyancin da Rukayya ta mana yau" Daga haka ta shige daki murya can kasa tana
cewa "Ba ruwana.... Haka kawai ince Asabe ta hakura ta ji haushi na..." Mama Hadiza
na kallon su Abba on a serious note tace "Wllh Yaya tun da Inna tace baxa ayi auren
nan ba fa baxa ayi ba, nima kuma dama nace baxa ayi din ba, ba kuma abinda xai sa
ayi, sai an nuna ma Rukayya duk fitinar uwar mu a haka muke sonta kuma babu shegen
da ya isa ya taka mana ita ya xauna lafiya, babu shi a duniya wllh, tun wuri ku
kira dangin amaryar ku sanar masu an fasa don su san nayi, tunda uwata tace baxa
ayi ba baxa ayi ba, ni nayi Imani da Allah da kun ji irin cin mutuncin da tayi ma
Inna yau baxa ma ku tsaya kuna bin maganar a sanyi sanyi ba, kuna shakku a ran ku,
me aka yi aka yi Rukayya xata raina mana uwa mu kasa daukan mataki?? to wllh yau
sai ta ga iyakarta sai dai idan ban haifu ba...." Tana kai wa nan ta mike a fusace
ta fice a parlon, Umma ta tabe baki ta dauke kai, Mikewa Daddy yayi ya fice daga
parlon shi ma, a hankali Mujaheed ya mike ya bi bayansa, Abba ya kalli umma da kyau
yace "Ki bar gidan nan as soon as possible Rukayya bana son ganin ki..." tace "Toh
xan tafi ai dama ba sai ka maimaita ba yallabai, amma dai kar ka manta yar gidan
wacece Mujaheed xai aura, tsaf xa ku xubar da mutuncin ku da kimar ku a idonsu, da
ma duniya gaba daya, barin kai da kake sanannen Barrister" tana magana tana matsar
kwalla, har xata fita sai kuma ta tafi kofar dakin Inna, Bude kofar tayi ta durkusa
tana goge kwallan idonta tace "Ina neman gafaran ku inna, ku yafe ni ku yi hakuri
sharrin shaidan ne..." Inna ta mike a rikice tace "Auzubillahi, garin yaya aka bar
ta taxo min nan ni Asabe, don Allah ki rufa min asiri ki fita ba don hali na ba, ki
tafi don Allah Rukayya" Mikewa Umma tayi ta fita parlon....
Abba da Daddy ne xaune parlon Abba duk sun rasa abun yi gashi har sha biyun rana
ya kusa, fasa aure gaskiya is out of the point yanxu, bai kamata bane kwata kwata
amma basu san ta inda xa su billo ma al'amarin ba, Mama Hadiza ce ta shigo parlon
da sallama ta dalilin kiranta da Abba yyi, Ta nemi kujera ta xauna tana kallon
yayyin nata, Murya can kasa Daddy yace "Yanxu Khadija baxa ki taimaka ki ma Inna
magana ta janye wannan batu na fasa aure ba, da dai ace daga wajen mu aka fasa
daurin auren nan gwara hakan ya faru daga bangaren iyayen amaryar.... Ki dubi irin
mutunta gidan nan da ake amma aga irin haka ya billo daga gidan, ga mahaifin
yarinyar dattijon kirki ga kuma irin manyan mutanen da xai gayyato daurin auren
nan, kaninsa kuwa wajen aikinsu daya da Sadeeq kuma suna mutunci....." Mama Hadiza
ta katse sa tace "Toh ko in ja Innar mu tafi gidansu amaryar tayi abinda xai sa
daga wajen su suce sun fasa daurin auren tunda dama kowa kallo masifaffiya mara
hakuri yake mata?" A fusace Abba yace "Ji wata maganar banxa, kina ma da hankali
kuwa Hadiza?" Mama Hadiza ta mike tsam tace "Ehh kwarai Ina da hankali Yaya, dama
naga take taken ku, wato ku baku ma wani ji haushin abinda aka ma mahaifiyar ku ba
saboda fitinarta ko, infact ba ku ma yarda cewar ita ke da gaskiya ba, to wllh bari
ku ji in har baxa ku bi abinda tace ba toh ku xa ku yi ta ganin ba dai dai ba, ba
ruwana, sannan duk fitinarta xan dauketa daga gidan mu tafi sai ku xauna da matanku
ku ci karanku ba babbaka, ita ma Rukayyar sai ka ce ta dawo masifaffiya ta tafi"
daga haka Mama Hadiza ta fice daga parlon a fusace, Daddy ya girgiza kai yace "Bata
da hankali kwata kwata" Abba ya sauke ajiyar xuciya yace "Ni fa nasan duk abinda
Inna ta fada Rukayya xata iya aikatawa, kuma ko wani hukunci tace in yanke mata
yayi dai dai, amma not to the extent da xata ce a fasa daurin aure ranan daurin
aure, meye laifin iyayen amaryar? Ina ce Rukayya ce ta mata laifi ba su, gaskiya
Inna tana son ta samu cikin wani yanayi ne, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un..."
Daddy da yyi shiru yana sauraren yayan nasa yace "Ko xaka kira Bala da su Jibril su
mata magana?" Abba yace "Sai kace baka santa ba ai ni har yanxu ban ga wanda ya isa
ya sa Inna ta canxa ra'ayin nan ba sai dai wani Ikon Allah" Abba ya jinginar da
kansa jikin kujera yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, where are we to start
from coz gaskiya babu xancen fasa aure, duk hukuncin da tace ayi ma Rukayya xa ayi
amma banda fasa aure don iyayen yarinya basu san hawa ba basu san sauka ba xa mu
kunya ta su a idon duniya" Daddy ya tallabi chin dinsa thinking of a way out also.
Karfe sha biyu Abba da Daddy da su kawu Bala da Jibril da wani kanin Inna da suke
uba daya suka kara komawa bangaren Inna don su bata hakuri ta janye batun fasa
auren Mujaheed da Safeenah, kora irin ta kare Inna ta masu da maficin hannunta,
har kawu Bala na neman faduwa saboda saurin ya fita a parlonta, Inna ta rakosu har
bakin pamponta tana huci tace "Munafukai kawai" Su dai basu juyo ba, amma daddy
gaba daya ransa ya gama baci, Abba dai ne ke murmushin karfin hali, su Bala da
Jibril ba bakin magana sai yan idanuwa, kanin Inna Alhaji Audu ne ya dinga cewa
"Tun da muka fito lafiya Alhmdllh, Asabe ba kyau" Daddy na isa part dinsa ya shiga
ko sallama bai masu ba, Imaan da Maryam na dinning xaune Imaan na bata labarin
abinda ya faru parlon Inna kasa kasa, Mama Hadiza na daki tare da Ammi, Ammi ta
fito jin an bude kofa ganin daddy ne tana kallonsa ta xauna saman kujera bata dai
ce komai ba don Mama Hadiza fa na kan bakanta na cewa babu xancen daurin aure ranan
har ta gama hada kayanta, Daddy ya jinginar da kansa da kujera yace "Inna na son
bata sunan gidan nan ta kunyata mu a idon duniya ne kawai, ta mance cewa bayan
Mujaheed akwai yan baya da xa su yi aure, ta mance gaba daya akwai Yan baya....
wani interpretation take son mutane suyi ma gidan nan, auren namiji ma ga abinda ya
faru balle mace?? This is very serious...." Ammi dai ta kasa cewa komai sbda Mama
Hadiza, Imaan ta taso ta dawo parlor don a rayuwarta na duniya bata son abinda xai
6ata ma Daddynta rai, Durkusawa tayi gefensa a hankali tace "Daddy ku yi hakuri"
Daddy bai iya yace Komai ba.... Can Ya kalli agogon wrist dinsa yace "Ya Allah,
just an hour remaining, Me xa mu ce ma mutanen nan fisabilillahi??" Ammi dai ba
bakin magana, Mikewa Daddy yyi ya fita parlon, duk suka bi sa da kallo, Ammi ta
sauke ajiyar xuciya, imaan ta mike a sanyaye ta wuce daki. Hijab dinta ta saka ta
tafi part din Inna, suna xaune tare da ta Rasulu sun cika faranti da shinkafa
jollof ga kaji kusan goma ana ta ci, turo baki tayi ta xauna tana kallon Inna a
hankali tace "Inna don Allah ku yi hakuri ku bari ayi auren nan, kuna son a dinga
ma su Abba kallon kananun mutane ne a garin nan?" Inna ta ajiye cinyar kazar dake
hannunta tana kallonta baki bude tace "Shi Uban naki ne ya aiko ki in tafi in
samesa yanxu?" Imaan tace "Ni ba wanda ya aiko ni" Inna na nuna mata kofa tace "Toh
maxa kiyi ta kanki, tunda ba uwar ki aka xaga ba dama me xai dameki, gantalalliya
ki ma je ki ji da lalurorin ki xa ki dinga tsoma baki a xancen manya kina yar
yarinyar ki da ke...." A fusace Imaan ta mike ta fice a parlon, part dinsu ta koma
ta shiga dakinta ta tadda Maryam a dakin, Maryam tace "Ina kika je?" Imaan ta xauna
gefen gado tace "Wajen Inna mana, naje na mata magana ta xageni" Maryam tace "ke me
ya kai ki, ni fa am happy gwara a fasa auren gaba daya... yarinyar da ta walakanta
ni ranan farkon da muka hadu, I sooo hate her with passion" Imaan tace "Toh
reputation din su Abba da Daddyna fa? Ae shine abun dubawan ba fasa auren ba"
Maryam tace "It's just for sometimes dear, ke kina ga akwai wanda ya isa ya sa Inna
ta canxa ra'ayin ta?" Shiru Imaan tayi, can a hankali tace "Na san me xan yi, I
pray it works" Inna na bakin tap tana wanke kwanukan da suka ci abinci da ta Rasulu
tana yan wakeken su shata na tale tale ta daga kai jin tafiya, Mikewa tsaye tayi
tana washe baki tace "A'ahhhh sannu da xuwa Bukar, Sannu da xuwa...." Sadeeq dake
sanye da tsadadden Gezna fari kal sai walkiya yake ya iso inda take yana murmushi
yace "Sannu kaka, ke kam baki gajiya da aiki...." Inna ta xaro ido ta rike ha6a
tace "Huuuu in gaji da aiki in mutu cikin wari Bukar, Allah ya tsareni... maxa
shiga ciki gani nan tahowa na ma gama ae" Sadeeq ya cire takalmansa ya shiga parlon
dake ta kamshin turaren wuta ya xauna saman lallausan rug din, Inna ta shigo tace
"Bari in kawo maka abincin bikin da aka fasa, ai ko yayi dadi har da na fitina,
yana nan ta Rasulu ta jido mana har da nama ba iyaka, ni dai hakorana har ciwo suka
fara yi saboda cin kaji, yanxu ma ta Rasulun ta shiga wanka ne..." Yana murmushin
sa mai kyau yace "Kaka ni a koshe nake wllh kuma lkcn Juma'ah ya kusa sauran yan
mintuna..." Inna tace "Toh yi maxa ka tafi idan an sakko sai ka dawo" Yana shafa
kansa yace "Ehh xan tafi yanxu kaka...." Tace "Toh ko in dauko maka darduma, jiya
na wanke sa tasss nasa Maimoon ta goge min na feshe sa da turare" yar dariya yyi
yace "A'a kaka Ina da darduma a mota, xauna mu yi magana" Inna ta dawo da sauri ta
xauna tace "Toh gani Bukar, in ji lafiya dai???" Yayi sunkuyar da kai yace "Na ji
abinda ya faru ne daxu...." Bai kai aya ba Inna ta fashe da kuka tana kunce ha6ar
xaninta cikin rawar murya tace "Wllh abinda ya faru kenan Bukar shine yasa nace
baxa a daura auren ba, ba ruwana, yanxu haka an fasa duk nasa a sallami bakin da
suka xo" Sadeeq yyi kasa da murya a hankali yace "Don Allah kaka kiyi hakuri, kinga
su Abba da Daddy baxa su ji dadin kallon da jama'ah xa su masu ba, gashi ana ganin
mutuncin gidan nan, babba dama shi da hakuri aka san sa, kuma wanda aka cuta shi
ake ba hakuri dama..." da sauri Inna tace "Inaaa Bukar ai tuni an fasa daurin
auren...." Yace "A'a na fa ce kiyi hakuri kaka, kuma ni dai na san ki da hakuri...
Ke babba ce fa Kaka" shiru Inna tayi tana matsar kwalla, can tace "Wllh ni dai
kunyar ka nake ji Bukar" Yana murmushi yace "Toh don Allah ki janye batun fasa
auren" Inna ta d'an yi shiru, can tace "Toh ai shikenan, sun ma kansu ni dai ba
ruwana, kuma na hakura aje a daura auren" Murmushi sosai Sadeeq yayi yace "Yauwa
Kaka Allah ya kara girma, na ji dadi sosai da kika dau shawarata, Allah ya kara
girma" Inna tace "Toh ai dama meye amfanin babban da bai daukan shawara, hakuri
kuma ai Allahn da ya halicce mu ma hakuri yake da mu balle ni, na hakura wllh, ga
waya sai ka kira min Bukar uban Imaan dama ya fi saka abun a kai uwa kanwar uwarsa
ce amaryar, oho dai kirasa ince masa su je su daura auren hankalin su ya kwanta"
Yana murmushi ya amshi wayar yayi searching sunan da tace anyi mata Saving lambar
daddy da shi ya kira sannan ya mika mata, Daddy na dauka tace "Toh ni dai ba ruwana
Allah ma hakuri yake damu, ku je ku daura auren ni na hakura Allah ya saka min da
alkhairi" bata jira cewar daddy ba ta katse wayar, Inna ta kalli Sadeeq tace "Ni
Rukayyar ma bata taba min irin haka ba gaskiya, ban dai san shaidanin da ya makale
a xuciyarta ba yau, amma dai gaskiya tatattce ne d'an iska, ya cuceta ba kadan ba
yau, nace to ko radion da suka kunna ya cika gida ne yasa shaidanin ya samu nasarar
rudar ta, amma gaskiya ni bata tanka ni kwata kwata a gidan nan, kuma har xaunawa
take idan xata gaisheni, shi kuma Ahmadu sarkin xuciya har ya yanke hukuncin ta
tafi gida, ni sai ta ban tausayi ma wllh...." Sadeeq dai sai kallonta yake yana
murmushi yace "A dai yi hakuri kaka" tace "Atohh, biyayya iya biyayya dai suna min
ni baxan masu sharri ba...." Daddy ne ya shigo parlon tare da Abba da kawu Bala,
Inna na washe baki tace "Sannun ku da xuwa" Sadeeq ya gaishe su gaba daya da
ladabi, Inna tace "Toh gaskiya duk babban da yace baxai dinga daukan shawaran yaro
ba yayi asara, me yyi min xafi da xan bari inyi asara, wannan yaro Sadeeq dai ya
shigo ya ban baki kuma wllh na hakura aje a daura auren Allah ya sa albarka, kamar
daga sama ya fado min yanxun nan, wato har labarin ya
baxu duniya Kai jama'ah.... Kuma da kun san ta yanda xa ku bi da ni da xancen bai
yi tsayi ba haka ba duk baku da wayo, ni dai na yafe, aje a daura auren" Abba ya
d'an yi murmushi yace "Toh madallah mun gode Inna, Allah ya kara girma, xa mu je
masallaci ynxu lkci ya kusa" Inna tace "Toh ku tafi Allah maku albarka, Bukari kai
ka dawo in xuba maka abinci don Allah har da kaji xuka xuka" Sadeeq na murmushi ya
mike yace "Toh in sha Allah xan dawo" Bin bayan su Daddy yyi ya fita, Abba na
kallon Sadeeq yace "Maa Sha Allah, I am very happy at ur contribution Allah ya
saka" Sadeeq yyi murmushi bai ce komai ba, a haka suka fita gidan Abba na kiran
wayar Mujaheed, Mujaheed was so shock da ya ji wai ai Inna ta hakura, kuma wai
Sadeeq Bulasawa ne ya bata hakuri, har reaction dinsa ya ba Abbansa da Daddy
mamaki, haka dai suka wuce mosque ana sakkowa masallaci kuma aka daura auren
Mujaheed Ahmad da Safeenah Usman, ko jira Mujaheed bai yi su gaisa da abokansa da
suka taho daga nisa ba ya koma gida, direct part din Inna ya nufa, Imaan na tahowa
daga part din innar rike da warmer xata sha corner suka kusa cin karo da shi,
fixgota yyi wanda hakan yasa ta saki abincin hannunta a tsorace, yana mata wani
mugun kallo da idanuwansa da suka rine cikin tsawan da ya raxana ta yace "Uban wa
ya aikeki ki sa saurayin ki yaje ya ma Inna magana? Uban wa ya sa ki????"
*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

51....

Kasa cewa komai Imaan tayi tana kallonsa don ba karamin tsorata tayi ba, cikin
tsawa yace "Ba tambayar ki nake ba sai na baki dirty slap?? Who sent you, waye ya
aike ki??" Hawaye ya cika idonta ta sunkuyar da kanta bata dai ce komai ba, saketa
yyi ya jingina da bango xuciyarsa na bugawa, ta tsallake abincin da ya xube ta wuce
da sauri tana goge idonta ya bi ta da kallo har sannan kirjinsa bai daina bugawa
ba, hade kai yyi da bango yana Kiran Allah a ransa, ya fi minti biyu a haka sannan
ya juya da kyar ya nufi bangarensu yana jin idanuwansa na juya masa. Imaan na
kwance daki da yamma idonta a lumshe duk da ba bacci take ba, wayarta dake kusa da
ita ya fara vibrate, bude ido tayi tana kallon wayar, tun abinda Mujaheed yyi mata
daxu take daki taki fitowa duk nacin da Maryam tayi da ita ta fito, gaba daya she
is moody, a hankali ta dau wayar tayi picking ganin Sadeeq ne ke kiranta, sallama
yayi mata daga daya barin, murya can kasa ta amsa, yace "Are you okay dear?" Shiru
ta d'an yi sai kuma tace "Bana jin dadi" yace "Subhanallah baki jin dadi kuma, kin
yi stressing kan ki da yawa kenan, what's wrong? I mean me kike ji ke damun ki?"
Cikin sanyin bemurya tace "Ache all over" yace "Subhanallah, kin sha drugs din
ki?" Ta gyada kai kamar yana ganinta yace "Ohk toh xan kawo maki wani yanxu sai ki
sha shi da daddare, you will feel much better" tace "Toh" yace "Xan kira ki idan na
iso" daga haka yyi mata sallama ta katse wayar ta ajiye ta rufe idonta. Biyar saura
ya sake kiranta yana waje, Hijab ta saka har kasa, xata fito ta tuna birthday gift
dinsa ta koma ta dauko flower din da cards ta saka cikin hijab ta fito, Few
visitors ne a parlon nasu, ta tafi dakin Ammi ganin bata ciki ta fito, a balcony ta
tadda Ammi da Mama Hansai, Ammi na kallonta tace "Ina xa ki?" Ta sunkuyar da kai
tace "Ammi ba dadewa xan yi ba ana kirana a waje ne" Ammi na kallon hannunta dake
cikin Hijab tace "Meye wannan kike boyewa a hijab?" Murmushi tayi kanta a kasa tace
"Ammi ba komai bane, sako ne fa" Mama Hansai na dariya tace "Yi wucewar ki kinji"
wucewa imaan tayi tana murmushi, Yana tsaye jikin motarsa idonsa sanye da glass ya
sa kananun kaya, sunkuyar da kai tayi ta isa kusa da shi, da damuwa yace "Ya jikin"
tana d'an murmushi tace "Da sauki" ya dauko wani leda a gaban motar ya mika mata
yace "ki sha tablets daya each each kafin ki kwanta" Bata amsa ba ta fiddo hannunta
dake cikin hijab ta mika masa flower din hannunta cikin sanyin murya tace "Happy
birthday dear" still yyi yana kallon flower din ko kiftawa babu" lkci daya ya karba
yana wara ido so happy yace "Waowww Thanks soo much baby I love it...." Ita dai
murmushi kawai tayi, a hankali tace "i am happy u love it...." Ko bai fada ba she
can see how happy he is, yana wara manyan idanuwansa yace "But baby how did you
know I love flowers plss?" Ta langwabar da kai tace "I only guess" lumshe ido yyi
murya can kasa yace "I feel like hugging you sweetheart" d'an murmushi kawai tayi
ta dauke kai tace "Ni xan koma ciki, and I am sorry I won't be able to attend ur
party saboda bana jin dadi" a sanyaye ta kare maganar, cike da damuwa yace "Ai na
maki uxuri dear, Allah baki lafiya thanks a lot, I will give you a call later" a
hankali tace "Ameen ngd" daga haka ta juya ta koma cikin gida ya bi ta da kallo
still smiling. Mama Hadiza ce xaune parlon Inna tare da Ta Rasulu, cikin rashin jin
dadi Mama Hadiza tace "Yanxu fisabilillahi kin kyauta min Inna, duk yanda na
takarkare a kan an ci maki mutunci sai ki watsa min kasa a ido??" Inna tayi kasa da
murya tace "Toh Hadiza shikenan ana ta bani hakuri ana hada ni da Allah sai in
botsare kamar shaidaniya? Babba fa dama da hakuri aka san sa, baki ga yanda aka
cika min parlon nan ba daxu ana bani hakuri har da su Audu d'an tsut, daga karshe
sai kuma ga Bulasawa da kansa shi ma ya tako har parlon nan ya ce inyi hakuri, to
idan dai ni ba tsohuwar banxa bace mai kunnen kashi mara jin magana Hadiza ai ya ci
ace na yayyafa ma raina ruwan sanyi in hakura, kuma ni dai gaskiya Rukayya bata
ta6a min irin haka ba, hau ne ya fada mata...." Ta Rasulu na nuna Inna ta kankance
ido tace "Ke dai Asabe ki dinga jin tsoron Allah, nan kika maida mu mahaukata muna
bambami daga karshe kika watsa mana kasa a ido wai kin hakura, Toh ai ina gida xa
ki sa a kirani ki kawo min karar Rukayya, ba kuma ruwana wllh don baxan saurare ki
ba, ke kuma Hadiza me xai dame ki?? Ai kadan da aikin Asabe kenan baki biyu, ni ban
yi mamaki ba, ni ba dai ruwana ban ce komai ba in yi magana ta kullace ni, amma
banda haka me aka yi aka yi wani shegen Bulasawa da har xai bata hakuri ta hakura?
Bayan abinda tsinanniyar matar nan Rukayya ta mana, Kai Asabe Allah ya baki lafiya,
ya kuma shirye ki, ni dai kin ga tafiyata nan...." Inna ta tsuke fuska tace "Toh ai
ni ba gantalalliya bace da xa ayi ta ba ma hakuri in ki hakura kamar kafurar Bayan
tsauni, ehe... Bulasawa kuma ni ya fi min kowaaa, yaro mai hankali da natsuwa mai
magana irin ta manya, duk sai da ya fada min maganganu masu dadi da kwantar da
xuciya wanda su Amadu suka kasa, toh ni ko me xance ma yaron Banda Allah ya masa
albarka, ai in dai bai auri Imaan ba to sai dai in ni Asabe bana numfashi, Imaan ta
sa ce in sha Allah, Bai fi min wasu 'yan uwan nawa ba ma ni Allah na tuba, Rukayya
kuma ai tuni tana akurkin gidan da ta gina ma iyayenta sai kace ba ni ta ma rashin
mutunci ba da xa a bar ta ta kwana gidan nan...." Ta Rasulu ta mike tace "Ni dai
tunda kika kunya ta ni, kika kunyata Hadiza Allah sai ya saka mana ya bi mana
hakkin mu, Rukayya kuma mu dai je xuwa muna nan dake xata dawo gidan nan...." Inna
tace "Ke ni fa ban hakura da abinda Rukayya ta min balle ta dawo, ai Rukayya yar
iska ce, aure ne dai nace aje a daura kada 'ya yana su ji kunya" Ta Rasulu tace
"Oho dai ni kin ga tafiyata sai ki saka Bukar gaba ya bada kudin nan na laluran
Imaan a san abun yi...." Daga haka ta fice daga parlon, Inna tace "Toh Allah bar
xumunci ta Rasulu, Allah ji kan mai salati da jikan shehu, Allah ya saka da
alkhairi ai ni kin gama min komai a duniya wllh kin fi min kowa ma, Allah ya bar mu
tare sai kuma kin dawo bikin Imaan da Maimoon in sha Allah, Kai ae xan taho har
gida maki ban gajiya, Bari dai 'yan kauyen nan su koma kauyukansu xa ki gan ni"
Mikewa Mama Hadiza tayi ta fice daga parlon rai ba dadi, Inna ta bi ta da kallon
gefen ido tace "Toh meye kuma axumi uku da xa ki yi, sai kace warce bata axumin
Ramadan, Ni dai ba ruwana dama ban aike ki kiyi ta rantse rantse ba...." A ranan
Mama Hadiza bata kwana gidan ba ta tafi gidan wata yayar Mai gidanta dake nan garin
kadunan. Imaan na parlon Inna bayan isha tare da Maryam suna cin abinci aka bude
kofa, kallon kofar suka yi Mujaheed ya shigo da sallama murya can kasa, wani
daddadan kamshi ya gauraye parlon, yayi wani kyau na daban cikin milk shaddar
jikinsa dake ta talli, Maryam na murmushi tace "Groom dama har yanxu baka tafi ba?"
shi dai bai ce mata komai ba ya xauna, Imaan dai bata kalli inda yake ba tun bayan
da suka hada ido shigowarsa, ta dinga cin abincinta a hankali, daga cikin dakin
Inna tace "Mujaheed ne?" Maryam tace "Ehh" da sauri Inna ta fito ta marairaice tace
"Tun daxu nake cigiyar ka Mujaheed, nace to ko har ka tafi wajen amaryar ne ba
sallama ni patuu...." Kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Yanxu xan tafi"
Xaunawa Inna tayi ta fashe da kuka a hankali tace "Shikenan yanxu Mujaheed sai dai
ka xo ka gaishe mu ka tafi?? Shikenan ba kai ba kwana cikin gidan nan yanxu balle
ka xo da sassafe ka gaisheni, wa xai dinga shigo min nan muna hira? Shikenan tafiya
xaka yi ka bar ni yanxu, dama ba kowa gare ni ba sai Allah sai kai, kaine me debe
min kewo gashi yanxu kayi aure xaka tafi gidanka ka barni ni kadai raina..."
Mujaheed bai san lkcn da yyi murmushi ba sai dai bai ce komai ba yana danna
wayarsa, Inna na share hawayenta cikin rawar murya tace "Rayuwa kenan, lallai sabo
turken wawa, Allah ubangiji ya ba ku xaman lafiya da matar, in sha Allah xuwa nan
da kwana biyu imaan xata rakoni don baxan gane gidan ba in xo ganin daki in sa
albarka kuma in maku nasiha da amaryar, Allah ya sanya alkhairi... Ni dai baka taba
min komai ba Allah maka albarka" Mujaheed na murmushi a hankali yace "Ameen" Mikewa
yayi yace "Toh sai da safe" Inna ta kara rushewa da kuka har da rike kai, Maryam ta
kasa ci gaba da danne dariyar da ke cinta, Imaan kam kin dago kanta tayi tana juya
shinkafar gabanta, Cikin kuka sosai Inna tace "Shikenan kuma, wayyo rayuwa
kenan...." Maryam na murmushi tace "Allah ya bada xaman lafiya Ya M.A, sai mun xo
ganin dakin Aunty amarya" Mujaheed ya d'an yi murmushin karfin hali ya gyada mata
kai ya juya ya nufi kofa, Inna na kallon Imaan da ta sunkuyar da kai tace "Toh ke
baxa ki ma yayan naki fatan xaman lafiya da matarsa ba Imaan" Shi dai Mujaheed bai
tsaya ba har ya fita, bin sa da kallo imaan tayi sai kuma ta mike ta bi bayansa da
sauri, Maryam ta xaro ido tana kallon Inna tace "Wai kuka fa take yi..." Inna ta
kara rushewa da kuka tace "Ka ji ki da wata magana, baxa ta yi kuka ba?? ke kinsan
wahalan da Mujaheed yyi da ita tun tana tsumma, ke kinsan irin fadi tashin da yayi
a kanta tana karama, to ko ubanta bai yi wahalar da Mujaheed yyi a kanta ba, kullum
a makale da shi xa ki ganta duk ta takura bawan Allahn duk inda xa shi tana
hannunsa, tayi ta basa wahala, har goyata ya sha yi, ta xo ta fara ciwace ciwacen
da ba a san kansa ba nan ma babu irin wahalan da bai yi da ita na ganin ya nema
mata lafiya ba, ai shakuwar dake tsakaninsu ko d'a da uwa sai haka, kuma kice
baxata yi kuka ba yau xa su rabu na har abada" tana kai wa nan ta fashe da
matsanancin kuka ta xamo daga kan kujera tayi xaman dirshan a kasa, Maryam dai sai
dariya take kasa kasa. Imaan na fita parlon Inna taga har yayi nisa, ta bi bayansa
da sauri tace "Yaya" tsayawa yayi ya juya yana kallonta, Bata san lokacin da ta
fashe da kuka ba ta nufesa da gudu ta rungume sa cikin rawar murya tace "Xan yi
missing din ka Yaya" kasa cewa komai yayi,
lkci daya idonsa ya canxa launi, rungume ta yyi shi ma yyi ya lumshe ido, kuka ta
dinga yi a kirjinsa, cike da karfin hali yace "Ae xa ki dinga xuwa gidana in sha
Allah..." Ta gyada masa kai kawai hawaye na sauka idonta, cikin sanyin murya tace
"Kayi hakuri da abinda nayi daxu, ban san it's wrong ba I wouldn't have done that,
kayi hakuri plss...." A hankali yace "Na hakura" gently ya janyeta jikinsa ganin
hawaye take har sannan yace "Toh ya isa haka mu je ki rakani gun mota" Bata iya ta
ce komai ba ya kama hannunta suka nufi gate. Tafiya kawai suke kamar ba su son
tafiyar har suka fita gate din gidan, suna isa motarsa ya juya yana kallonta har
idanuwanta sun yi jajir, sunkuyar da kanta tayi a hankali tace "Sai da safe, I am
wishing you a happy married life...." Yayi murmushin karfin hali yace "Thanks
imaan" Juyawa tayi ta fara tafiya yace "Imaan" ta tsaya sannan ta juyo jin bai ce
komai ba ta dawo inda yake tana kallonsa, yace "Shiga mu je xan siyo ma Inna abu ki
kawo mata ynxu" a hankali tace "Toh" sannan ta xaga ta bude front seat ta shiga, ya
shiga driver seat ya tada motar, the journey was silent har suka iso gun masu
gashin kaji, yayi parking ya kashe motar, ya sauka, ba a dau lkci sosai ba ya dawo
rike da leda uku na kaji da fresh milk, ya bude back seat ya ajiye leda guda sannan
ya bude side dinta ya mika mata leda biyu ta amsa ya xaga ya shiga driver seat,
gida ya koma bayan yyi parking ya juya yana kallonta yace "Sai da safe" ta sauke
idonta kasa tace "Allah ya kai mu..." Yace "Ameen, ki dau daya sai ki kai ma Inna
daya" D'an murmushi tayi ta bude motar ta fita, ta nufi gate ya bi ta da kallo har
ta shiga sannan yayi reverse ya bar layin. Washegari asabar tun da wayewar gari
Ammi da Aunty, Mama Hansai da matan kawu Bala suka dinga aiki a gidan trying to
make sure everywhere was neat, masu kujeru dama su ma sun xo sun dau kayansu, su
Maimoon, Ummi da Maryam kadai ke taya su aikin, Imaan kuwa na kwance dakinta wai
kai na ciwo, Rahma dama tare da ita Umma ta bar gidan da yammacin jiya.... Bayan
azahar Imaan na part din Inna tare da Maryam, Inna na kan darduma tana bada labarin
nan dai na irin yanda aka haifi Mujaheed tana tsaye bakin kofar asibiti tun safe
har dare, wahalan da tayi da shi tun yana tsumma, yanda ya girma a wajenta da fadan
da yasa ta dinga yi da jama'ah a anguwa, har lkcn da ya tafi kasar waje karatu....
Imaan dai na kwance sai game take a wayarta tana tabe baki don ita dai har ta
haddace labarin nan layi layi, Maryam sai dariya take ita da ba a ta6a ba ma
labarin ba, Inna na matsar kwalla tace "Har xuwa jiya da aka daura masa aure, Allah
sarki Mujaheed dina" Dariya kawai Maryam take har da kwanciya, Inna dai sai matsar
kwalla take tace "Duk cikin 'ya yan Ahmadu babu ya shi, gashi duk ya fi su kyau
wllh, ga tsafta ga mutunta na gaba da shi, sam Mujaheed bai san wani abu wai rashin
kunya ba, bai taba mayar min da magana ba, wllh jiya ban yi baccin kirki ba da
tunaninsa na kwana..." Sai kuma ta fashe da kuka sosai, sai a sannan Imaan tayi
murmushi bata dai ce komai ba, cikin rawar murya Inna tace "Da dakunan bangaren nan
nawa sun kai uku sai in ce su dawo nan da matar kawai ni dai in dinga ganin sa
kullum" Maryam dai sai dariya take, Imaan ta mike ta wuce daki ta dalilin kiranta
da ake a waya, Daga kiran tayi ta xauna gefen gado ta kai kunne hade da yin
sallama, ya amsa yace "How are you dear?" Tace "Alhmdllh" yace "Hope kin ji sauki
sosai" tana murmushi tace "Sure, sosai" yace "Ohk to ki dan fito ki amshi sako" ta
xaro ido tace "Na me?" A hankali yace "C'mon dear" tana murmushi tace "Toh bari in
fito" daga haka ta katse wayar ta fito parlor tana kallon Maryam tace "Mu je ki
rakani" Inna na goge hawayen idonta tace "Ina??" Imaan ta turo baki tace "Ae yanxu
xa mu dawo" Inna ta marairaice tace "Tou ni dai kar ku dade, mai tayani xaman gashi
yayi aure ya tafi..." Dariya imaan tayi ta fita Maryam ta bi bayanta, har suka isa
gate Maryam tambayarta inda xa su take yi amma ta ki gaya mata, suna fita gate din
Maryam tayi shiru ganin Sadeeq tsaye kusa da motarsa, murmushi yayi ganinsu, Maryam
tace "Hi...." Yace "Hello Maryam" tana murmushi tace "Happy Belated birthday
Sadeeq" yace "Thanks much... Hope an gama biki lafiya?" Tace "alhmdllh" yace "Maa
Sha Allah, Allah ya basu xaman lafiya" Maryam tace "Ameen" kallon Imaan da ta
jingina da motar ta rungume hannu yayi a hankali yace "Hello princess..." Ta d'an
yi murmushi tace "Ya gida" yace "Alhmdllh, ya Kaka?" Imaan ta langwabar da kai tace
"tana ciki tana ta missing ya Mujaheed" Yace "Allah sarki, ta kwantar da hankalinta
after a month sai ta koma gidan gaba daya koh" Yar dariya kawai imaan tayi tace
"Gaskiya ne" yyi murmushi ya bude back seat ya fiddo da wani kwali dake a rufe amma
ko bai fadi meye a ciki ba kowa ya sani, yana kallonta yace "Here..." Ta xaro ido
tace "Haba wannan ai yayi yawa" yace "Ni ma sun min yawa, take plss baby" Imaan
tayi murmushi ta d'an risina ta amsa tace "Toh Allah saka da alkhairi" hararanta
yyi tayi dariya bata ce komai ba, wani box mai kyau ya fiddo ya mika mata ta make
kafada tace "Bana so" hade rai yayi ya kalli Maryam dake murmushi yace "Kin ganta
koh?" Maryam tayi dariya ta mika masa hannunta tace "Bani in rike mata" Mika ma
Maryam box din yyi, Maryam tace "Allah ya saka da alkhairi" Yana murmushi yace "And
ban mance promise da na maki ba, kin bar min xabi or you want anything?" Yar dariya
Maryam tayi tace "Ehh na bar maka" yace "Toh shikenan, thank you" Kallon imaan yayi
yace "Dear, we will talk later ki gaida kaka" Imaan tace "Toh xata ji nagode"
Sallama yayi ma Maryam ma suka nufi gate, ya bude maxaunin driver ya shiga ya tada
motar, suna shiga gida Maryam ta kashe ma imaan ido tace "Yau xa mu ci cake mu yi
dam, amma me xa ki ce ma Ammi?" Imaan ta xaro ido tace "Part din Inna xan kai ai"
Maryam tace "That will save u long explanation" Washegari Sunday tun da sassafe
Inna ta gama shiryawa wai xa su gidan Mujaheed da Imaan, Daddy dake parlor xaune
yana kallon news yace "Toh ai kila ma basu tashi ba da sassafe xa ki je masu Inna"
Inna ta xaro ido tace "Sai kace rubabbu Bukar kace min basu tashi ba, Toh ni dai
gaskiya na shirya kuma yanxu xan tafi ina imaan din?" Daddy yace "Bata tashi ba"
Inna ta xauna saman kujera tayi tagumi tace "Naga abinda ya isheni.... baccin safe
ko baccin asara ni Asabe, karfe takwas ace mutum mai rai bai tashi yyi wanka ya
kintsa ya karya ya gyara gidansa ba? Kuma tun jiya nace mata ta shirya da safe xa
mu tafi tare tunda wannan yarinya Maryam dangin ubanta sun xo sun tafi da ita jiya
da magariba... Kai ku dai baku da tsari gaskiya... Meye kuma baccin safe??" Shi dai
Daddy bai ce komai ba, Ammi ta fito daga kitchen ta gaida Inna sannan ta tafi dakin
Imaan ta tasheta... Inna na ta xaune parlor ta tsuke fuska har imaan ta fito bayan
kusan minti talatin cikin atamfa riga da skirt na biki da aka masu bata sa ba,
sosai kayan suka amsheta, Inna tace "Ki dauko mayafi mu tafi idan munje can kya
karya gaskiya...." Ammi da Daddy suka kalleta, can Ammi tace "A'a inna da dai ta
karya ai bata da 6ata lkci wajen cin abinci, ta je gidan mutane da sassafe...." A
fusace Inna tace "Ke dai Aisha ki daina haka, ki dinga jin tsoron Allah, Gidan
Mujaheed din ne gidan mutane idan ba walakanci ba, gidan Mujaheed ne fa, ni dai ku
dinga tsoron Allah sai kace wanda xata gidan 6are? Ke dauko hijabinki mu tafi, shi
gidan yayan nata xaki ce ma gidan mutane saboda baki da mutunci..." Tana fadin haka
ta nufi kofa a fusace, Daddy ya tabe baki bai dai ce komai ba, Imaan ta sa hijab ta
dauko takalminta da wayarta tana kallon parent din nata a hankali tace "Sai mun
dawo" Daddy kadai ne yace "Allah ya kiyaye" Ammi kam bata ce komai ba sai aikin
gabanta take.

*Imaan isn't for free* it's 300 via


Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

52.....

Suna fitowa compound Inna ta kalli Imaan tace "Toh ko dai in je inyi ma Ahmadu
magana ya sa direba ya kai mu?" Imaan dai bata ce komai ba, Inna tayi tsaki tace
"Ayi ta maki magana kina ma mutane shiru idan ma baccin ne bai isheki ba idan munje
gidan Mujaheed din ba sai a baki daki daya ki kwanta kiyi ta yi ba, ai can ma gida
ne" Daga haka ta nufi part din Abba imaan na biye da ita, Aunty ce parlor tana goge
goge da su Maimoon, Aunty ta xauna ta gaida Inna, su Maimoon ma suka gaisheta, Inna
ta amsa tace "Gidan shiru ba wannan mata Rukayya koh" Ita dai Aunty bata ce komai
ba, Inna tace "Toh Ahmadu nake nema ya kira wannan mutumi me jan mota ya kai mu
gidan Mujaheed, tun asuba na gama shiryawa Imaan ta bata min lkci" Aunty tace "Toh
xauna Inna ki jira driver din an aike sa yanxu" Inna ta xauna tace "So dai ake in
makara kawai, Banda haka ni fa tun Asuba nayi wanka na" Imaan ta xauna a parlon
bayan ta gaida Aunty tana kallon series din da akeyi, ba a dau lkci ba driver ya
dawo, Aunty na kallon Inna dake xuba gyangyadi tace "Toh ya dawo fa inna..." Inna
ta bude ido da sauri ta mike tace "Toh tashi mu je imaan, shi Ahmadun baya nan ne?"
Aunty tace "Bacci yake" Inna tace "Ni dai ba wajena suka gaji baccin safe kamar
rubabbu ba gaskiya" daga haka ta fita imaan na biye da ita, a waje suka tadda
driver da mota, imaan ta bude ma Inna motar ta shiga tana amsa gaisuwar driver din
sannan imaan ma ta shiga, sai da suka hau saman titi Inna na kallon Imaan tace "Toh
kin gaya masa anguwar ne" Drivern na murmushi yace "Ae na san gidan kaka" Inna ta
washe baki tace "Ashe har ku kunje kun sa ma gidan albarka ku ma" Shi dai bai ce
komai ba yana murmushi, tafiyar kusan minti ashirin suka yi suka iso gidan
Mujaheed, Inna na kallon driver da yayi parking a waje tace "Kai ya haka ka danna
han a bude maka gate ka shiga mana, gidan jikana ne fa" Horn driver yyi mai gadi ya
fito yana kallonsa, can ya karaso gun motar yace "Daga ina?" Rike baki Inna tayi da
mamaki tana kallonsa tace "Naga abinda ya isheni, kai gidan jikana ne fa kake
tambayar daga ina? Na shiga uku wai ni yake tambaya daga Ina, ko in sauko in bude
get din da kai na ne" Mai gadin yyi kasa da kai yace "Yi hakuri Baaba" daga haka ya
tafi da sauri ya bude gate din, Inna ta ja tsaki tace "Mutane dai ba tsoron
Allah... wai daga Ina, ke ki ji fa gantalalle amma ba laifinsa bane na Mujaheed ne
da bai sanar masa kakarsa na da rai ba" Ita dai Imaan bata ce komai ba driver ne ke
bata hakuri, yana gama parking imaan ta bude motar ta fito, Inna na kallon driver
din tace "Toh yi wucewar ka yaro, mu da gida kuma sai bayan isha in sha Allah" Yace
"Toh baaba ku dawo lafiya" Inna ta nufi entrance din shiga gidan tana washe baki,
Imaan dai na biye da ita, Bubbuga kofa Inna ta shiga yi da karfi tana cewa "Salama
alaikum" Imaan tace "Kai inna kiyi a hankali mana..." Matsawa Inna tayi ta bude
baki tana kallonta, Imaan ta turo baki ta danna bell tace "Kawai kiyi ta bubbuga ma
mutane kofa da karfi" Inna xata yi magana aka bude kofar, Inna ta washe baki tana
kallonsa tace "Mujaheed...." Kallonsu kawai yake yana tsaye bakin kofar sanye da
jallabiya, Inna ta rike haba tace "Ashe da gaske ba ku tashi ba kenan" rabawa tayi
ta gefensa kamar yar yarinya ta shige parlon, Imaan ta juya tana murmushi, can dai
ta juyo a hankali, kallonta taga yana yi, ta sunkuyar da kai tace "Ina kwana Yaya"
Muryar Inna suka ji a parlor tace "Ina amaryar??" Mujaheed ya juya ya koma parlon,
Imaan ta bi bayansa, Xaunawa yyi yana kallon Inna yace "Ina kwana?" ta washe baki
tace "Lafiya lau Mujaheed, tun asuba da na tashi nayi wanka wllh, Banda imaan da ta
bata min lkci da tun gari bai gama wayewa ba xa ku gan ni" shafa kansa yyi bai dai
ce komai ba, Inna na kallon pillow da aka ajiye kan lallausan sabon rug din parlon
tace "Cewa nayi ina amaryar" Mujaheed yace "Tana sama...." Yana fadin haka ya tashi
ya wuce sama, Inna ta kara kallon pillow dake parlor murya can kasa tace "Toh waye
kuma ya kwana a parlor ni patuu" Imaan tayi murmushi tace "Toh ke ina ruwan ki"
Inna tace "Atohhh, ba ruwana kuwa" Cire Hijab Inna tayi ta linke tana kallon parlon
tana murmushi tace "Sabon gida ba dai sha'awa ba" Mikewa tayi ta nufi wani kofa ta
bude tana lekan ciki ta karasa ta ajiye hijab din nata a ciki ta fito ta rufe tace
"Dakinsu Hansai ne, shi ma sun xuba lafiyayyun kaya a ciki wllh masu tsada...."
tabe baki tayi ta tafi ta bude kofar kitchen tana lekan ciki ta xaro ido tace
"Waiii.... Ai kitchen din ma ba masaka tsinke da kayan kitchen na xamani, Ashe dai
ba gwalagwalan karya aka dinga yawo da shi ranan casu ba" Imaan dai ta hade rai sai
kallonta take... Mujaheed na haurawa sama ya bude dakin da Safeenah ke ciki, bacci
ya sameta tana yi, ya shiga ya kulle kofar ya karasa kan gadon ya d'an bugi gadon
yana kallonta, sai da ya buga gadon da karfi for d second time sannan ta bude ido
ta mike xaune tana kallonsa da wani expression, yace "Kin ma yi sllhn kuwa?" D'an
tsaki tayi tace "Haba don Allah sai ka wani buga gado ka tsorata ni kamar xaka tada
kato??" Daga head har toes yake kallonta, ta tabe baki ta kalli agogo tace "Sllh
dai dole inyi ko karfe nawa ne" da mamaki yake kallonta yace "A gidan ku haka kike
kai wa har karfe tara baki yi sllh ba Safeenah?" A fusace tace "Toh gajiyan bikin
fa? Plss Mujaheed that's not how to treat a new bride you are not romantic, haba
don Allah sai kace mun ta6a rayuwa gida daya...." Wani kallo kawai Mujaheed yake
mata, strictly yace "Look Safeenah I won't tolerate this, gidana ba na kafurai
bane, tun asuba na shigo na tashe ki kiyi sllh shine har yanxu baki yi ba, is this
ur home training?" Yar dariya tayi tana kallonsa daga sama har kasa tace "Kai ko
kunya baka ji ba don Allah??" tana kwaikwayonsa tace "Wai wani tun asuba na shigo
na tashe ki.. ban taba jin labarin ango irin ka ba sai yau da nake gani a xahiri a
gidana, wai ka shigo min da asuba, ain't you ashame of ur self plss" murguda baki
tayi ta sauka daga saman gadon da yar figigiyar rigar baccinta ta nufi bathroom, ya
bi da kallo kafin ta shiga bayin yace "Ki sameni downstairs yanxu idan kin yi
sllhn" daga haka ya juya ya fice daga dakin, Tv ya tarar Inna na kokarin kunnawa
tana cewa "Toh sai me idan Baki kunna min ba kamar yau na saba hada kayan kallo
kuma... Gidan Mujaheed kuma baxa ki saki jiki kiyi yanda kike so, ban da shi wa
gare ki da xa ki je gidansa ki sake jiki dama, ni dai ba ruwana, ki dinga abu domin
Allah Banda munafurci" Imaan dai sai kallonta take fuska daure, Inna na ganin
Mujaheed ta mike tace "Wai ka ji daga nace ta hada min kayan kallo shine xata ce
min daga xuwa gidan mutane, su waye kuma mutane, Mujaheed din koko Amaryar da bata
fito gaisheni ba har yanxu, ni dai ba ruwana, idan ma xa ki cire Hijabin nan na
jikinki ki linke ki ajiye ki tsayar da ranki waje daya ki saki jiki kamar kina
gidan Bukar to gwara ki cire don da kyar ma ba kwana xamu yi a nan ba gaskiya, ga
dai dakuna na kirga har hudu ranan" Mujaheed ya karasa ya kunna mata tv din yace
"Xata sakko yanxu ta gaishe ki ai" Inna ta koma kan kujera ta xauna ta tsuke fuska
tana kallon Tv, Xaunawa Mujaheed yayi kan kujera ya kalli Imaan ta gefen ido, Sai
turo baki take, Mujaheed ya kalli Inna yace "Amma kuma sai ki yi irin wannan
sammako Inna" Inna ta kallesa da sauri tace "Ni dai Ahmadu ne yace in taho da
sassafe, bayan jiya ya shigo da daddare mun yi magana" Imaan ta xaro ido tana
kallon Inna, Murmushi Mujaheed yyi yana gyada kai, Jin taku a stairs ya juya,
Safeenah ce ke sakkowa sanye da doguwar riga damamme, Still tayi tana kallonsu,
Inna ta kankance ido tana kallonta da kyau ita ma, Safeenah ta hade rai ta karasa
sakkowa ta shigo cikin parlon, Mujaheed ya kalleta yace "Meet my grandma and my lil
sis Imaan...." Inna na washe baki tace "Sannu Amarya, da fatan dai an tashi lafiya"
dauke kai Safeenah tayi ta tabe baki murya can ciki tace "Ina kwana" Inna tace
"Lafiya lau, sai dai ko sunanki ban sani ba" Mujaheed yace "Safeenah" Inna tace
"Toh madalla, to safeenah Mujaheed dai gashi nan a gabana aka haifesa, kuma ni nayi
wahala da shi tun yana tsummarsa, ke wahalar da nayi da shi wllh kare baxai ci ba,
Tabb banda nakudarsa me Rukayya tayi???" Hade rai Mujaheed yyi yana kallonta,
Safeenah tace "Toh maa sha Allah, ina d'an yi abu ne a sama Hajiya...." Xaro ido
Inna tayi kafin tace komai Mujaheed yace "Mind you, Inna is what we call her..."
Safeenah ta d'an tabe baki tace "Toh xan je in yi abinda ke gabana a sama Inna"
Inna tace "Ba xancen kije kiyi abinda ke gaban ki ba Yar nan, ko karyawa fa ba mu
yi ba, Imaan ma ina jin ko wanka bata yi ba don da naje ma bacci na tarar tana
yi...." Imaan na kallon Inna tace "Ni bance maki ban yi wanka ba inna" wani
matsiyacin kallon Safeenah ta jefa mata sannan ta kalli inna bluntly tace "Ba a kai
ga sauke min gara na daga container da ya kawo ba, ba komai yanxu haka s gidan"
Wani kallo Mujaheed ya dinga mata trying hard to control his temper, inna ta rike
ha6a tana kallonsa tace "toh me ku ke ci a gidan ba a sauke gara ba ni 'ya su?"
Safeenah tayi wucewarta sama, Mikewa Mujaheed yyi ya bi bayanta, yana shiga dakin
ya kulle kofar yana nunata da yatsa cikin tsawa yace "Let me give you this warning
Safeenah, idan baki son na fito maki da the other side of me you've got to respect
that woman to the fullest, she is my grandma kuma albarkacin ta yasa kike gidana,
wllh wllh xan yi taking action din da xai baki mugun mamaki idan baki maida
hankalin ki ba, sannan breakfast ni nace ki tashi ki fita kije ki girka masu yanxun
nan...." A tsawace ya kare maganan yana kallonta, Gaba daya ta gama tsorata sai
kallonsa take tana komawa baya, lkci daya hawaye ya kawo idonta sai kuma ta fashe
da kuka tace "Is this the real you dama Mujaheed?? me yasa tun farko baka yi
encourage dina wajen ganin nayi kokarin hakura da kai ba, you are always telling me
xaka koyi sona I shouldn't worry, dama ka aureni ne to make life a living hell for
me, kasan irin mutanen da na ki amincewa
da nace sai kai?? Kasan mutanen da na watsa ma kasa a ido nace sai kai, dama
laifine son mutum da xuciya daya?? Tun da aka kawo ni gidan nan ka ki ko da xama na
minti ashirin a dakina balle ka kwana, wllh ina sonka Mujaheed, ban aure ka saboda
komai ba sai saboda Ina son kasancewa da kai, ka dai san irin gidan da na fito
balle kace saboda wani abu naka na aure ka" dauke kai Mujaheed yyi xuciyarsa na
bugawa, right from time a rayuwar sa na duniya ya tsani ganin hawayen mace, a
hankali ya karasa inda take ya xauna gefen gadon ya jawota jikinsa cikin sanyin
murya yace "I won't make my home a living hell for you Safeenah, and sure I will
create a soft spot for you soon, but you've got to respect my family, duk abinda
nace bana so kuma plss try to avoid that, Kinga ke yan uwanki baxa su xo in masu
gaisuwar walakancin da kika ma grandma dita ba...." lamo tayi jikinsa tace "Amma
kana ganin wannan yarinyar fa bata gaisheni ba ma" Shiru ya d'an yi, Sai kuma yace
"Mind you sunanta Imaan, and kar ki damu xan mata magana" tace "Step sis dinka ce?"
Ya girgixa kai a hankali yace "She is my cousin sis" daga kai tayi tana kallonsa,
ya gyada mata kai, tabe baki tayi bata ce komai ba, yace "Toh for my sake kiyi
hakuri ki hada breakfast din even if it's just Irish and egg, sai ki dafa ruwan
shayi" Shiru tayi masa yace "Xa ki yi?" A hankali tace "Toh" murmushi yyi ya manna
mata kiss a goshinta, ta lumshe ido don ba kadan ba taji dadin hakan, ya mike yace
"Come out soon" daga haka ya nufi kofa ta bi sa da kallo, Allah yasan so ba na wasa
ba take ma Mujaheed, Bata taba yi ma d'a namiji irin son da take masa ba, kuma xata
iya yin komai a kansa. Mujaheed na dawowa parlor ya tadda Imaan kadai tana kallo,
tun da ta kallesa sau daya ta dauke kai, ya isa kusa da ita yace "Me yasa baki
gaida Safeenah ba?" Ta turo baki ta ki cewa komai, ya dafa kujeran da take xaune
yana kallonta da kyau yace "Look, duk kika xo gidan nan ko kika ganta a wani waje
dolenki ki gaidata coz she is my wife... Kin ji abinda nace??" Ta hade rai tace
"Toh ai ita ma ba da respect ta gaida Inna ba da ta sakko, so why will I greet her,
why??? beside she is suppose to tell me... Sannu da xuwa kafin in gaisheta, amma ko
kallona bata yi ba so nima naki gaisheta din ai ba wajenta muka xo ba...." Kallonta
kawai yake ganin yanda take maganar cike da tsiwa tana xare masa ido, ya dauke kai
ya d'an yi murmushi, can dai ya mike ya nufi kitchen jin muryar Inna kasa kasa ita
kadai tana magana, tsaye yyi bakin kofa yana kallonta tana duke tana fere dankali
tana cewa "Idan ba jaraba ba da safen ma ya wani bi figaggiyar mata kamar xabiya
daki bayan kwana da yayi a dakin daren jiya, to meye xasu shige daki kuma da safe
bayan nace masu ban karya ba ga 'yar mutane na taho da ita, ita ma bata karya ba,
dama da ya iyayenta suka yarda ta biyoni, ni dai ba ruwana..." Dariya sosai ta
basa, tana ganinsa tayi shiru tace "A'a har ka fito Mujaheed" yace "Dankali kike
ferewa da kanki kuma?" Inna tace "Yo baxan fere ba tunda na kwaso yunwar cikina
Mujaheed, ga Imaan ma bata karya ba da kyar Bukar ya yarda ta biyo ni... Abu dai da
raina da lafiya ta, ita wancan matar dake xaune parlor tace ba ruwanta baxata shiga
kitchen din mutane ba, ni ban gane ma wannan abun ba gaskiya" ya shafa kansa yace
"Yanxu Safeenah xata xo ta hada maku kayan karin" inna ta ajiye wukar tace "Toh
amma anya ka ce mata nice na raine ka kuwa...." Safeenah na sakkowa parlor ta dinga
yi ma Imaan wani kallo sak na tsana tana tafiya, suna hada ido Imaan ta tabe baki
ta dauke kai.... Tsayawa Safeenah tayi tana kallonta xuciyarta na tafarfasa tace
"Beware a gidana kike.... you had better respect ur self ki maida hankalin ki"
Kallonta Imaan tayi da sauri tace "Gidan ki ko gidan yayana? Gidan ku na can kin
baro sa malama don haka baki isa ki min warning a gidan Yaya ba...." Da sauri Inna
ta karasa fitowa kitchen jin muryar imaan, Mujaheed ma ya fito ya tsaya kallonsu da
mamaki, Inna tace "Lafiya?? me ya faru??" Imaan tace "Wai inna ki ji ce min take in
shiga hankalina wai nan gidanta ne, wllh ba abinda na mata daga sakkowarta ta fara
min fada tana min warning" sake baki Inna tayi tana kallon Safeenah tace "Ba
lafiya, ta shiga hankalinta kuma? Kinsan wacece ita kuwa yar nan, to bari kiji wllh
wannan da kike gani ta fiye ma Mujaheed ke so dubu dari, kaji min mata kamar zabiya
dai, ita da gidan yayanta kice ta shiga hankalinta sabida baki da tsoron Allah?? To
wllh a kan Imaan sai Mujaheed ya kora ki gidanku yanxun nan, gwara ma ki xageni da
ki ta6a min imaan gaskiya, duk da dai kin ma xageni tun daxu kawai dai ni me hakuri
ce na ja bakina nayi shiru, kaji min mokadaddiyar mata dai xata sa min jika a baki
in shiga uku???" Mikewa Imaan tayi kamar xata yi kuka ta nufi kofa tace "Ni sai kin
dawo Inna baxan xauna ba...." Inna ta saki salati tana tafe hannu tace "Na shiga
uku ni patuu, Mujaheed ya auri jaraba tunda ta ta6a imaan, ke me ya kai ki kinsan
wacece kuwa, ita kenan fa uban ya haifa a duniya, ko kallon banxa ba a mata balle a
mata fada... Shi Mujaheed din bai xaunar da ke ya sanar maki bane??" Bin bayan
Imaan Mujaheed yyi ganin har ta fice parlon.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

53....

Har Imaan ta sauka Balcony ta nufi gate Mujaheed ya rikota da sauri yace "Kee ina
xa ki??" Ta hade rai kamar xata yi kuka tace "Ni dai gida xan wuce bayan ta gama
xagina, Ni wucewa xan yi" Kallon Eyeballs dinta kawai yake, xata kwace hannunta ya
kalli gate, lkci daya ya jawo ta kusa da shi murya can kasa yace "Toh kiyi
hakuri...." ta turo baki ta ki cewa komai, ya dauke kai yayi murmushi yace "Toh
baxa ki hakura ba..." Bata fuska tayi tace "Xagina fa tayi..." ya xaro manyan
idonsa still smiling ya ja dogon hancinta yace "Ni ban ji inda ta xage ki ba, har
da sharri...." Kwace kanta take son yi xata wuce ya ki saketa yace "Ai fa nace kiyi
hakuri koh?" Kallonsa tayi fuska daure kamar xata yi kuka tace "Toh baka gaya mata
ni wacece bane?" Dariya sosai ta basa, and he couldn't help it don har sai da yyi
dariyan ganin maganan sak yanda inna ke yi, ya kamo duk hannunta biyu yace "Haba na
gaya mata mana lil sis, amma kiyi hakuri xan sake gaya mata da kyau, yanxu mu koma
ciki sai ki hada maku breakfast din mu rabu da ita...." imaan ta turo baki bata dai
ce komai ba, yana murmushi yace "Idan mun koma sai kice ma Inna kin hakura don ta
daina fada kin ji pls?" A hankali tace "Na ji" Yana kallonta sosai yace "Good girl"
daga haka suka koma parlon yana rike da hannunta, Inna kadai ce tsaye parlon tana
kallon stairs tana cewa "Ka ji min jarabbiyar mata ta ja Bukar ya kullace ni tunda
ni na fito masa da 'ya har xa a sa ta a baki... to wllh hir dinki ni ba ruwana, to
Wai ma ke baki da tsoron Allah ne?? duk hakurina yau sai da kika kai ni bango,
banda haka kin fito daxu kin gaida ni a tsaye sandandan kamar katon soja, ni dai
ban kula ki ba don babba da hakuri da kauda kai aka san sa, sannan na maki magana
bamu karya ba kince kwantenar karyar da aka maki na gara bai sauka ba, ko ina aka
taba gara a kwantena??? Ni dai duk ban kula ki ba ina ta hakuri shine yanxu xaki
ta6a imaan baki san ba a ta6a min ita ba, to haka xa mu yi dake tun ban dawo gidan
gaba daya ba?? Yau naga abinda ya isheni... Irin xaman da xa mu yi kenan ni patuuu
da wannan figaggiyar yarinyar" Mujaheed ya karasa gun Inna yace "Haba Inna daga
xuwa kuma, Imaan din fa ta ma ce ta hakura..." Inna ta kalli Imaan da sauri tace
"Wai??" Imaan ta gyada kai a hankali, Inna ta koma ta xauna tana share xufar
goshinta tace "Toh Alhmdllh... Sai ta sakko ta hada mana karin kumallo, gaskiya
Mujaheed Ina ga baka yi dacen mata ba, tun fa ba aje ko Ina ba ta fara nuna hali,
ko da yake ai ni me iya saita mata xama ne, ba haka na saita Rukayya ba ma Allah na
tuba" Mujaheed ya kalli Imaan ya mata alamar da ta tafi kitchen din, ta rungume
hannunta tace "Toh ni kadai?" Kallonta Inna tayi da sauri tace "Ke kadai me?"
Mujaheed ya nufeta yace "Toh mu je" Ba musu ta nufi kitchen din ya bi bayanta,
dukawa tayi gun dankalin da Inna ta fara ferewa, ya dau wukar ya mika mata yace "Be
careful with the knife...." Bata ce komai ba ta amsa ta fara fere dankalin, ya duka
kusa da ita yana kallonta, duk wanda ta gama ferewa sai ta sa a ruwan da ke kusa da
shi, shi dai kallonta kawai yake, pieces shidda ta gama ferewa tace "Ai dai wannan
ya ishemu ni da Inna..." Ya wara ido yace "Toh ni fa...." Kallonsa tayi da sauri
tace "Har da kai?" A hankali ya gyada mata kai, ta tabe baki ta ci gaba da ferewa,
wani kara tayi ta jefar da wukar sai ga jini a hannunta, ya daga ta da sauri yace
"Subhanallah..." yarfe hannun ta fara yi a rikice tace "Wayyoo Yaya zafi...." Pampo
dake kitchen din ya nufa da ita ya kunna yana tsaye bayanta ya shiga wanke mata
hannun yana kallon cut din that isn't deep, a hankali yace "Sorry lil sis...." Yana
gama wanke mata ya juyo da ita, hawaye ya gani idonta, lkci daya ya rikice yace
"Yana maki xafi sosai ne??" ta fashe da kuka a hankali tace "Ba kai bane kace in
kara bayan na gama namu da Inna" rungume ta yayi yace "Toh yi hakuri plss, we
should have use the potatoe peeler instead" ya daga kanta yana share mata hawayenta
da fingers dinsa, turo baki tayi tace "Ni dai sai dai kayi slicing din dankalin
baxan yi ba" murmushi yayi yana ci gaba da goge mata idonta a hankali yace "Toh
naji, sai ki kunna gas ki debi mangyada a pan" daga haka ya saketa ya koma gun
dankalin, fry pan da ta gani ta dauko ta bude jarkan sabon man gyada ta deba a fry
pan din sannan ta kunna gas ta daura, ta daura ruwan shayi ta sa lipton, ba dai
kayan kamshi tunda bata san inda suke ba, tsaye tayi bayansa tana kallonsa har ya
gama slicing dankalin ya mike ya ajiye bowl din a sink, ya juya yana kallonta yace
"Toh ya xa ayi?" Yar dariya tayi tace "Baka sani ba Yaya" ya buda hannu alamar bai
sani ba din, ta karasa inda yake ta wanke dankalin ta tsane duk yana kallonta, yace
"Ke da ba ki girki a gida ma...." Murmushi tayi tace "Ehh amma ai ina ganin Ammi na
yi, kuma dai na iya...." Shi dai bai ce mata komai ba, suna tsaye kitchen din har
dankalin da ta xuba a mai ya soyu ta kwashe a plate, tana kallonsa tace "Toh ina
eggs din?" Ya xaro ido yyi yace "Are you sure, kar kije ki tada min Asthma..." Ta
turo baki tace "It's just an ordinary egg, sai in sa onion fa, ba yaji ai" Yana
murmushi a hankali yace "Ohk...." Eggs din ya fiddo cikin few minutes ta fara
soyawa bayan ta yi chopping onion a board, duk yana lura da ita to make sure she is
fine din da gaske, can ya karasa kusa da ita ya tsaya bayanta a hankali yace "You
are uncomfortable Imaan" ita dai bata ce komai ba don da gaske tsarkewa numfashinta
yake yi ko don bata yi lowering gas din bane amma a gida ai tana soya kwai, ya rage
gas din sosai ya juyo da ita tana facing dinsa giving her support with his broad
shoulder, a hankali take sauke numfashin hade da shakar kamshin sa mai dadi, ya
dinga juya kwan a frying pan har ya ga ya soyu sannan ya kashe gas din, gaba daya
ya juye a plate din da ta dauko, ya kashe gas da ta daura ruwan xafi ganin yana
tafasa, daga kanta yyi yana kallonta a hankali yace "Are you okay?" Kai ta gyada
masa, yace "Ki tafi parlor xan kawo breakfast din yanxu" Bata ce komai ba ta nufi
kofa ya bi ta da kallo har ta fita, wani plate din ya dauka ya debar ma Safeenah
dankali da kwan ya rufe, sannan ya juye ruwan xafin a flask ya dauka da cups biyu
da spoon ya tafi parlon, Inna na xaune sai shar6an bacci take har da minshari, ya
d'an yi murmushi yana kallon Imaan dake xaune kasan rug ya ajiye flask din hannunsa
yace "Are you sure you are okay?" Ta gyada masa kai, kitchen ya koma ya dauko plate
din dankalin ya ajiye masu ya koma kitchen din, Tea mai kauri ya hada a cup sannan
ya fita da kayan shayin ya ajiye, plate din dankalin da ya bari a kitchen din da
cup din shayi ya tafi ya dauka ya fito, sama ya nufa imaan ta bi sa da kallo, can
ta tabe baki ta dauke kai, Safeenah na dakinta tana waya da Mahaifiyarta ta sanar
mata duk abinda ake ciki tun shigowar Inna gidan da sassafe, rai bace Hajiyan
Marafa tace "Ban da ma kin nace sai shi Allah na tuba me xa ki yi da d'an wajen
Rukayya, Ni fa da Rukayya kar ta san kar ne shi sa ban so auren ba, ke kuma kika ce
ba ki san xance ba kin samu miji, amma duk wannan mai sauki ne wllh tllh, ni nasan
ta yanda xan billo ma lamarin, ki kwantar da hankalin ki sai kace ba ni na haife ki
ba dai, ai in sha Allahu yanda nake xaune hankali kwance ba damuwar kowa gidan
ubanki haka ke ma xaki xauna gidan Mujaheed Safeenah in sha Allah" Safeenah na goge
idonta tace "Toh Mummy..." Hajiyan Marafa tace "Kar ki nuna masu komai, har ita
yarinyar me maki rashin kunya kar ki tanka ta, dama tunda Hajiya Rukayya tace min
bata san wannan tsohuwar ba a wajen dinner nasan karya kawai take, amma ba
damuwa... Ki kwantar da hankalinki dota babu mai sa maki ciwon kai in sha Allah a
gidan auren ki, xuwa gidan ki ma sai ya gagare duk danginsa har ita munafukar
uwartasa in dai ina numfashi, sannan kin ce har yau bai kwana dakin ki ba ko???"
Daga kai Safeenah tayi jin an bude kofa da sauri tace "Mummy xa mu yi waya anjima"
Bata jira cewar Mahaifiyar tata ba ta katse wayar, hade rai tayi ta kwanta ta juya
baya, Mujaheed ya ajiye abincin hannunsa ya xauna gefen gadon yace "Plss plss kiyi
hakuri Safeenah, nasan this is not proper at all cause this is just ur 2nd day a
gidana, but plss keep this in mind haka grandma dina take wllh, kowa ya santa kece
dai da baki santa ba, har ni ba barina tayi ba sai dai idan ban yi abinda xata yi
magana ba, Imaan kuma bata da matsala kawai ba ku fahimci juna bane, she's very
nice and sweet to stay with, ko a gida Grandma bata son a ta6a ta be it me or
anybody... Ranan xa a ga the other side of her in har aka ta6a imaan kinsan
takwararta ce, so plss you need not to worry beside just few hours fa xa su yi su
wuce, and I assure you baxan yarda a taka ki ko a raina ki ba coz you are my
wife...." Ita dai Safeenah bata juyo ba balle ta tanka sa.... Yace "Ga breakfast
din ki" still taki cewa komai, Juyawa yayi ya koma downstairs, kallon Imaan da ta
wani hade rai ya dinga yi har ya shigo parlon yace "Baxa ki hada shayin ba...."
Kamar jira take tace "Ni ba yunwa nake ji ba dama ai"

*For the sake of My lovely Naomi Baba Abbasss ga nyt update after enough read mores
daxu da safe, duk da dai ba wani kirki gareta ba oo* 😍

_You are reading imaan for free and still telling me nonsense and posting in
groups ur *Big Wahala*_ All I know Is that my book Imaan isn't for free. Gbamm!!

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

54....

Shiru Mujaheed yyi yana kallonta, can ya karasa kusa da ita yace "Saboda me baxa ki
ci ba?" Kin cewa komai tayi, yyi murmushi ya xauna kusa da ita ya jawo cup da flask
ya fara hada shayin, yana gamawa ya ajiye cup din shayin gabanta da plate din
dankali, dauke kai tayi xata mike ya rikota, ta shiga kokarin kwace kanta tana cewa
"Nace maka ni ba yunwa...." muryar Inna suka ji tace "Lafiya?? meye haka??" Saketa
Mujaheed yyi da sauri, Inna na xaro ido tace "Lafiya kake matse yar mutane
Mujaheed?" Ta gefen ido ya kalleta bai dai ce komai ba, Inna ta kalli Imaan tace
"Me kika masa?" Kamar xata yi kuka tace "Inna nace masa na koshi fa shine wai sai
na ci" Inna ta bude ido sosai tace "A'a toh ke kuma baki da tsoron Allah, kika
koshi a Ina? Uban me kika ci? Bata fa karya ba Mujaheed... Ni dai ba ruwana, ka
rabu da ita ka kada min nawa shayin in sha, ya wuce Allah ya masu hisabi da hanjin
cikin nata" Murmushi kawai Mujaheed yake ya gama hada ma Inna shayin ya ajiye
gabanta ya debar mata dankalin ta sakko kasa tace "Toh burodi fa?" Yace "Bari in
fita in siyo yanxu" Inna tace "Atoh, na taba ganin inda aka sha shayi ba burodi
dama" mikewa yayi ya fita parlon Inna ta bi sa da kallo ta rike ha6a tace "Ikon
Allah, aure mai saita mutum ya gyara sa, dubi fa wani biyayya na musamman da
Mujaheed yake yi yanxu daga ya kwana daki daya da mace, Ikon Allah ya fi gaban
haka.... Mujaheed ne xan aika da ya tafi babu musu?? Lallai kamar Rukayya ta tsine
masa, ai baxai ma je bane sai ya gama ja min rai ya gama min walakanci, ke ma dai
Bulasawa yayi yayi ya yunkuro ayi auren nan ko kya yi hankalin, kinsan fa da ace ke
ce kika yi aure da har na gama tarewa can gidan naki, toh wai yaushe ne wannan
kaddararren jarabawan sakandarin ne ni patuu, wllh su Ahmadu da Bukar dama can basa
tsoron Allah tun tasowarsu kamar dai ba ni na haifesu, Banda haka wani shegen
jarabawa ne ya isa ya hana sunnar manzon Allah S.A.W.... Ni dai ba ruwana" Imaan
dai bata tanka Inna ba sai fiffita shayin da Mujaheed ya hada mata take ta sha da
sauri kafin ya dawo, Inna ta saki baki tana kallonta da sauri tace "Ya haka xa ki
handame dankalin gaba daya Imaan, ba namu bane mu biyu" sosai ta ba Imaan da ta
cika baki da dankali da kwai dariya, ko sauraranta bata yi ba ta dinga turawa har
sai da ta ci kusan rabin plate din da kwai, Inna dai sai kallonta take baki bude,
Imaan ta dau wani cup ta dinga fiffita shayin har ya huce ta kwankwade da sauri ta
ajiye kusa da Inna tana goge bakinta, Inna ta rufe bakin da ta sake tace "Kunyar
Mujaheed din kike yanxu ko me?" Da sauri Imaan tace "Kunya Kuma??? Ni dai kar ma ki
ce masa na ci komai a nan, don ba abinda na ci" Bata jira cewar Inna ba ta koma
kujera ta xauna tana goge bakinta da kyau, Inna tace "Dama mana, ya xa ayi ki iya
cin rabin plate din dankali kamar jaka ai sai dai ni din..." Imaan dai bata kulata
ba ta mayar da hankalinta kan Tv, Da sallama Mujaheed ya shigo parlon rike da ledan
bread l, ya karaso ciki yana kallon empty cup din shayin da ya hada kafin ya fita,
Imaan ta wani daure fuska tana kallon TV, Inna tace "Toh ba kya daure fuska ba dama
kin handame komai kamar mayunwaciya, wllh Mujaheed yanda ka san ta shekara bata ci
abinci ba, dubi abinda ta bar min fisabilillahi, ko mage aka bar ma wannan xata
koshi balle mutum irina, yarinya dai sai ci kamar saniya" Imaan sai kallon Inna
take kamar xata yi kuka, Mujaheed dai yayi murmushi ya ajiye bread din hannunsa
yace "Toh tunda dai ba da kudin ki aka siyo kayan abincin ba kuma ba Amadun ki ko
Bukar suka siyo ba me xai dameki? Gidan yayanta ne fa" Bai jira cewarta ba ya wuce
sama, imaan ta dinga kallonta tana murmushi ranta fess, tabe baki Inna tayi ta bude
bread din ta yagi kato a ciki a hankali tace "Toh da ban haifesu ba xa su haife
ku?? da na sani ma in ki haifan nasu in ga ta tsiya, sai in ga ta yanda xa a same
ku gantalallu kawai marasu tarbiya" sakkowa kasa imaan tayi ta dinga 6a66aka
dariya, ita dai Inna bata ko kalleta ba ta tsuke fuska tana cin bread. Sai da tayi
nakk dama ta mike ta kai plate da cup kitchen duk ta wanke duk abinda aka bata ta
kife ruwan ya tsane sannan aka fara goge gogen kitchen din har wall din kitchen dai
sai da ta goge sannan ta fito ta share parlorn tasss, sannan aka fara goge goge,
tana goge sabbin kujerun da d'an kyallen da take goge goge tace "Babu wanda xai ce
datti baxai fito daga parlon nan ba, kaii aji tsoron datti, datti ba kyau...." Ita
dai Imaan kallonta kawai take, Inna ta gama goge goge ta wuce dakin su Hansai ta
kwanta saman gado, nan ta dinga sharar bacci uwa tana dakinta. Sha daya da kusan
rabi Mujaheed ya sakko parlon sanye da kananun kaya da suka amshe sa sosai, ya
dinga kallon Imaan yana tsaye kusa da stairs, can yace "Ina Innar" ba tare da ta
kallesa ba tace "Nima ban sani ba" juyawa yyi yana kallon Safeenah dake sakkowa a
bayansa kamar mai tausayin stairs din, riga da skirt ne jikinta na atamfa da suka
amsheta matuka, kayan ya haska ta ba kadan ba, she's really beauty.... fuskarta
babu walwala har ta karasa sakkowa, tunda suka hada ido sau daya Imaan ta dauke
kanta ta wani tamke fuska, ita ma Safeenar haka tayi tana jin wani mugun tsanar
imaan har xuciyarta, Mujaheed ya karasa ya bude dakin dake downstairs yana kallon
ciki, ganin Inna na bacci ya rufe ya dawo yana kallon Safeenah da fuskarta ke dauri
tana kallon direction daban yace "She is sleeping" kamar jira take ta Juya da sauri
ta koma sama, kallon Imaan yyi sai kuma ya bi bayanta, Imaan ta mike a hankali ta
tafi dakin da Inna ke kwance ta bude jakarta ta dau dari biyar da ta gani a ciki ta
rufe jakar sannan ta fito, kofa ta nufa direct ta fita parlon tana murguda baki,
Mai gadi ya tashi ya bude mata gate tayi ficewarta tana ce masa sai anjima yayi
mata Allah ya kiyaye, tana isa babban titi ta samu adaidaita ta shiga ta gaya masa
anguwarsu. Safeenah na shiga bedroom dinta Mujaheed ma ya shigo ya rufe kofar ya
juya yana kallonta yace "Toh girkin fa...." Xaunawa tayi gefen gado tana cire
dankwalin kanta dogon gashin ya sauka kasa, a d'an fusace tace "Toh wai ba cewa
kayi tana bacci ba, and you brought the idea of asking her first before cooking,
plss Mujaheed let me... Sannan gaskiya kada yarinyar nan ta sake xuwa min gidana
daga yau, am sorry to say this wllh I dislike her with passion, I don't know why
amma gaba daya naji na tsaneta with all my heart" Kallonta Mujaheed ya dinga yi da
wani expression, fuska daure yace "You are looking into my face and telling me u
dislike my blood, are you on ur right senses Safeenah??? meye damuwar ki da ita, to
bari ki ji, ba ki isa ki hana imaan shigowa gidan nan ba tunda ba gidan ki bane....
Kuma ki sakko yanxu ki girka ma grandmum dita lunch" a mugun fusace tace "It's
better ka fita ka tafi eatry ka samo masu lunch don wllh wlh baxan yi ba, Banda
hauka ma ni na taba jin inda ake tilasta amarya sai ta yi girki on her third day a
gidan miji, to baxan yi ba, ka fita ka siyo masu ko kasa blood din taka ta girka"
tana kai wa nan ta mike a fusace ta tafi can karshen gado ta xauna, shi dai
kallonta kawai yake trying hard to control his temper, underneath his breathe yace
"I will treat ur f**kup soon" daga haka ya fice daga dakin, ta bi sa da harara
murya can kasa tace "Xaka san blood din ka ce" Mujaheed na sauka downstairs ganin
Imaan bata parlor ya tafi kitchen nan ma bai ganta ba, dakin da inna ke kwance ya
shiga nan ma bai ganta ba, Inna ta d'an bude ido cikin muryar bacci tace "Azahar
yayi Mujaheed?" Yace "Imaan fa?" A firgice ta mike xaune tace "Wacece kuma Imaan"
bai ce komai ba ya fito dakin ya tafi compound nan ma bai ga alamanta ba, juyowa
yayi da mamaki xai dawo parlor ya kusa cin karo da Inna tana xaro ido tace "Ina
take?" Yace "Yanxu na sakko ban ganta ba" salati Inna ta saki ta fashe da kuka tace
"Ai ni na shiga uku daga fito da yar mutane ta min rakiya ta 6ata, toh Ina ta shiga
Mujaheed, ka rufa min asiri ita kenan Allah ya ba Bukar, har a koma ga Allah Bukar
baxai taba yafe min ba wllh, ka cece rayuwata Mujaheed a nemo ta" Wani kallo
Mujaheed ya dinga yi mata ta bangajesa ta nufi gun mai gadi da gudu tana hawaye
tace "Yaro wata yarinya fara yar doguwa siririya kamar xata karye ta fita ta get
din nan daxu??" Mai gadi yace "Ehh ta fita, har ma mun yi sallama" Inna ta saki
wani dogon salati a rude tana tafe hannu tace "Amma kai d'an banxa ne sakarai
gantalalle, ya xaka bar yarinya ta fita bayan tare kaga muka shigo, ita kenan fa
gun uban a duniya, mutane dai ba tsoron Allah, ya bar yar mutane ta fita ta shiga
gari, yanxu ta ina xan fara nemo Imaan ni patuu, ya ubangijina ka dubeni....."
fashewa tayi da kuka ta fice daga gate din da gudu ko Hijabi babu, Mujaheed dai ya
koma ciki ya dauko makullin mota ya fito ganin har Inna ta fice ya bude motar yyi
warming dinsa Mai gadi ya bude masa gate ya fita, kafin Inna ta isa titi ta tare
mutane sun fi biyar a hanya tana masu describing din Imaan ko sun ganta, duk aka ce
mata ba a ganta ba sai ta rushe da matsanancin kuka tana cewa "Bukar baxai ta6a
gafarta min ba har duniya ta nade" hakuri aka dinga bata tana tafiya tana kuka har
ta isa titi, Parking Mujaheed yyi ya sauke glass, ya wani daure fuska yace "Shigo
mu wuce" a fusace ta kallesa tace "In wuce gidan ubanwa ba yarinyar mutane, gidan
ka dai ya xama na jaraba daga xuwa Imaan ta 6ata...." A fusace yace "Wai imaan din
yarinya ce da xaki tsaya titi kina nemanta?" Ta xaro ido tace "Yarinya ce a gun
ubanta wlh, ita kadai fa garesa, wllh ba ruwana ka rabu da ni Mujaheed, me xanje
ince ma Bukar da Aisha idan na shiga mota...." Sai kuma ta rushe da kuka mai ta6a
xuciya, ganin mutane an fara taruwa kanta Mujaheed ya ja tsaki yaja motarsa ya bar
ta wajen, gida ya wuce direct, yana parking kofar gida ya shiga ciki, babu kowa
compound din ya tafi part din su Imaan, ya kusa minti daya tsaye a balcony kafin
yyi sallama murya can kasa ya bude kofar ya shiga parlon, imaan ce xaune parlon da
plate din abinci gabanta tana ci tana kallo, suna hada
ido ta mike da sauri har tana tuntube ta nufi dakinta da gudu ta shige ta kulle
kofa, Ammi ce ta leko daga kitchen, yyi kasa da kai yace "Ina yini Ammi" tace
"Lafiya lau, ya gida" yace "Alhmdllh" komawa kitchen tayi ya xauna saman kujera a
parlon, ba a dau lkci ba Ammi ta fito tace "Ya amarya fa..." ya d'an yi murmushi
yace "Tana lafiya" tace "To maa sha Allah, a xubo maka abinci?" Yace "A'a Alhmdllh"
dauke abincin da imaan ta bari a parlon tayi ta kai dinning ta ajiye ta dauko wani
plate ta rufe, Ammi tace "Ka dawo da Innar ne?" Yace "A'a, tana dai tahowa" Bai
rufe Baki ba sai ga Inna duk ta hada xufa tace "Ina Bukar yake?" Ammi na kallonta
da mamaki tace "Sannu da xuwa Inna" Inna tace "Ke tambayar ki nake Ina Bukar, ban
ga imaan ba wllh..." Ammi tace "Imaan kuma, ae ta dawo tun daxu" salati Inna tayi a
hankali tana tafe hannu tace "Ta dawo?? Amma wannan 'ya ta Bukar axxaluma ce wllh,
Allah kaga yanda yarinyar nan ta daga min hankali na dinga tona ma kai na asiri a
titi, Allah kaga yanda ta sa na bar jakata da dubu daya a gidan mutane na fito ba
shiri, Allah kaga yanda ta sa cikina ya rude a titi na dinga neman bayan gida...."
Sai kuma ta rushe da kuka ta fita parlon tana cewa "Bukar dai ya haifi jaraba, don
imaan jarababbiya ce, ko da yake uban nata ma fitinanne ne" Ammi dai banda murmushi
ba abinda take, ta kalli kofar dakin imaan tace "Imaan" sai da ta kirata sau biyu
sannan Imaan ta yi ma Sadeeq sallama a wayan da suke yi, ta fito da hijab har kasa
tana sunkuyar da kai, Ammi tace "Meyasa kika taho baki sanar da Inna ba?" Kamar
xata yi kuka tace
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

"Ammi bacci fa take ta yi, kuma ni na gaji ina son dawowa gida" Ammi tace "Toh ai
kin kyauta" Imaan ta saci kallon Mujaheed dake ta kallonta, ta juya da sauri ta
koma daki ta rufe kofarta. Some days later aka fara shirye shiryen saukan su Imaan
a gidan, during this period soyayya mai xafi imaan suke yi da Sadeeq amma ta waya,
gaba daya ya ki xuwa ta rasa me yasa sai dai ya kirata, kullum xancensa shi dai ji
yake kamar ya jawo kwanakin duk da bai fi saura wata biyu xa su xana jarabawan waec
ba, ko da xai xo gidan kuwa dama Inna yake xuwa gaidawa kuma ko ita imaan bata sani
sai ya tafi xai kirata yace ai ya xo gidansu, ranan asabar ya kama saura sati daya
saukansu, ranan kuma ya kama sati biyu da bikin Mujaheed, misalin sha daya da wani
abu na safe ya xo gida tare da Safeenah, ubansun lace ne jikinta sai mayafi da ta
sakale a wuya hannunta rike da handbag sai takalmi mai tsini da ta sa, tayi kyau
har ta gaji, sai xuba kamshi take, fuskar nan nata ya sha make up ba a cewa komai,
part dinsu ya nufa tana biye da shi, su Maimoon da Ummi suka yi welcoming dinta da
fara'a, ta amsa masu da siririyar muryarta tana murmushi, Maimoon ce ta tafi sama
ta kira Aunty, Aunty na sakkowa tace "A'a Aunty amarya ce a gidan namu, Sannu da
xuwa" Safeenah ta kalleta tace "Yauwa..." Aunty ta xauna tace "Fatan an tashi
lafiya" Safeenah tace "Lafiya lau ya gida" Aunty tace "Alhmdllh, ya naku gidan"
Safeenah tace "Lafiya lau" Aunty tace "Toh madallah..." Mujaheed dai sai kallon
Safeenah yake jin bata gaishe da Aunty ba, Bai dai ce komai ba ya kalli Aunty yace
"Abba fa?" Aunty tace "Tun safe ya fita" Mujaheed ya mike yace "Ohk bari mu gaida
Inna" Aunty tace "Toh shkkn sai kun dawo" yace "Yusuf ya dawo?" Aunty tace "A'a bai
dawo ba" kofa ya nufa Safeenah ta mike ta bi bayansa Aunty ta bi ta da ido har suka
fita ta girgixa kai ta mike ta je ta ci gaba da abinda take, suna fita Mujaheed ya
kalleta rai bace yace "Abinda kika yi kin kyauta kenan Safeenah, mum dita ce ita ma
fa?" Tsayawa tayi tana kallonsa da mamaki tace "Me nayi kuma?" Yace "Did you greet
her?" A fusace tace "Kai komai kace fada da bala'i, to ni ban ma sani ba, da muka
fito sai kayi correcting dina ba ka dinga min fada ba haba" Bai tanka ta ba ya ci
gaba da tafiya ta bi bayansa tana tabe baki, part din su Imaan ya shiga tana biye
da shi tace "Nan ne part din innar?" Ya kalleta yace "Part din uncle dina" Bai jira
cewarta ba ya shiga parlon da sallama, d'an tsaki tayi ta shiga ita ma, Ammi na
xaune parlon ta mike ganinsu tana masu sannu da xuwa da fara'a, Mujaheed ya xauna
ya gaisheta ta amsa tace "Sannun ku da xuwa" Safeenah da kallo daya tayi ma Ammi ta
gane ita ce Mahaifiyar Imaan coz it's soo obvious, ta wani daure fuska tana kallon
Tv, Ammi tun da ta kalleta sau daya taga bata gaisheta ba dama bata sake kallonta
ba, ta tafi kitchen tana cewa "Bari in kawo maku ruwa" wani kallo Mujaheed ya dinga
yi ma Safeenah da ta bude jaka ta fiddo chewing gum ta 6are ta jefa a baki tana
tauna, murya can kasa tace "Did you greet her Safeenah?" Banxa tayi masa tana taune
taunenta, Ammi ta fito ta ajiye ruwan kusa da shi, Yana kirkiran murmushi yace "Ae
daga gida muke ma" Ammi ta xauna tace "Ae ruwa ne" daukan bottle water daya yayi
yace "Daddy fa?" Ammi tace "Yana Abuja" Mujaheed yace "Toh xa mu je gaida Inna
yanxu" Ammi tace "Toh maa sha Allah, nagode kwarai" mikewa yyi ya nufi kofa
Safeenah ta mike ta bi bayansa Ammi ta bi ta da kallo, sai da suka sauka balcony ya
juya yana kallonta kafin yace komai ta wuce sa da sauri tana kas kas da cingam
fuska daure, gyada kai yyi ya dau hanyar part din inna ta bi sa a baya tana kyabe
baki, Inna na share parlornta ta daga kai tana kallon Mujaheed tace "Waye wannan"
Bai tanka ta ba ya cire takalmi ya shiga parlon, Safeenah ta cire takalmanta tana
kirkiran murmushi tace "Sannu da aiki Inna, kawo in karasa share maki" Inna tace
"A'a bar shi yi wucewar ki ciki, daga xuwa kuma sai ki hau shara ba ruwana, balle
ma na gama" tace "A'a don Allah ki bari Inna, ki kawo in karasa" ajiye tsintsiyar
Inna tayi ta mike ta amshe jakar hannunta tace "Toh ai nagode dama bayana kamar xai
cire wllh, ita wancan mata tana kwance daki wai ba lafiya, dadin abun ma an san
bata da lafiya kafin ta taho nan balle ace a parlon Inna, shi sa ban wani gigice
ba, Allah dai ya yaye mata wannan bala'i da ba a san kansa ba....." Mujaheed sai
kallon Inna yake sannan ya kalli kofar dakin bai dai ce komai ba, Safeenah ta gama
tattare parlon ta kwashe dattin da bai taka kara ya karya ba a Parker sannan ta
mike tana murmushi tana kallon Inna tace "A Ina xan xubda dattin?" Inna tace "Can
bayan window xaki tafi kwandon sharan yana nan xaki gansa fess na wanke wllh sai a
iya xuba tuwa a ciki a ci, sai ki xuba a hankali kar ya bata jikin kwandon har hypo
na sa yayin wankewa" Safeenah ta fita parlon ta sa takalminta mai tsini ta wuce
bayan window, Mujaheed na kallon Inna da sauri yace "Me ya sameta?" Inna na kakkabe
kujera tace "Wai Imaan, toh ga ta nan dai ya dama da xaxxabi ta tashi, ko ina ciwo
sai ga al'ada shi ma ya xo ya sa ta gaba, daxu ta gama sharban kuka a nan, duk babu
inda bata mirgina ba a parlon nan, ni dai baranda na koma nayi xamana ba ruwana, to
nace ta tafi gidansu ta ki tafiya ya xan yi da ita...." mikewa yyi da sauri tace
"A'a kar ka tasheta ka rufa min asiri, daxu wannan d'an albarkan Bulasawa ya xo
dubata ya taho da magunguna da allurai...." Tsayawa Mujaheed yyi yana kallonta,
Safeenah ta shigo parlon ta xauna kasan rug tace "Ina yini Inna?" Inna na murmushi
tace "Lafiya lau 'yar nan, amma ku daina cika powder a fuska, kin dai yi kyau wllh
powdern ne yyi yawa har kina naso..." Sunkuyar da kai Safeenah tayi tana ta
kirkiran murmushin karfin hali, Mujaheed xai shiga daki Inna tace "Kinga fitina ko,
Mujaheed nace kar ka tasheta, wllh allura aka mata ta samu bacci, ya xan yi da
raina idan ka tasheta yanxu?" Bai tanka Inna ba ya shiga dakin, Safeenah na
kallonta da sauri tace "Waye ba lafiya?" Inna ta marairaice tace "Wllh imaan, kamar
baxata yi ba yau, nace kar ya tasheta ya ki saurarata, duk ya rikice...." Mikewa
Safeenah tayi da sauri tace "Subhanallah bari in masa magana" daga haka ta shige
dakin.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

55....

Gefen Imaan dake bacci Mujaheed ya xauna a kan gadon Inna ya kai hannu forehead
dinta yana kallonta, Bude ido tayi a hankali, ya ta6a jikinta xai yi magana
Safeenah ta shigo dakin kamar an hankadota, rike kugu tayi tana kallonsu, duk da
mamakin ganinta da Mujaheed yyi bai nuna ba ya dauke kai daga kallonta, Imaan ta
mike xaune da kyar ta wani daure fuska, Mujaheed na kallonta murya can kasa yace
"Wani maganin kika sha?" Magungunan da Sadeeq ya kawo mata daxu ta nuna masa, ya
duka ya dau ledan ya fiddo drugs din yana kallonta yace "Wa ya kawo maki?" Shiru
tayi ta ki cewa komai, ya hade rai yace "Am asking you" turo baki tayi ta koma ta
kwanta, Safeenah dai sai kallonsu take rike da kugu, Inna ce ta shigo dakin tana
kallon Safeenah tace "Safara'u kike ko wa, ba kya fita parlor ki bar su suyi sirri
ba, kinsan fa komai nata ya sani, yanxu ganin ki sai ta ji kunyar gaya masa har da
ciwon mara a abinda ya dameta, don Allah ki dan koma daga parlo" Safeenah dai bata
ce komai ba sai murmushin karfin hali take tana sunkuyar da kai, Inna tace "Ae ba
wani abu bane, bbu abinda Mujaheed bai sani ba na Imaan, yanda kika san Yaya mace
haka ta mayar da shi tun bata kai haka ba...." Juyawa Safeenah tayi ta nufi kofa ta
fice Inna ta bi bayanta tana waigo imaan tace "Dama ki rufa min asiri kar ki bata
min xanin gado ki cuce ni, ba kowa gareni ba da xai wanke yanxu Mujaheed ba gidan
yake ba" D'an murmushi Mujaheed yyi har inna ta fita, Can ya wani hade rai yana
kallon Imaan yace "Wato kiran saurayin naki kika yi kika ce masa baki da lafiya
koh?" Kamar xata yi kuka tace "Ni bani na kirasa ba yaya" fuska daure yace "Toh wa
ya kirasa" a hankali tace "Inna" yace "Wa ya kira mata shi?" Imaan tace "Ni ban
sani ba ina daki" Ya kara hade rai yace "Shine kika ce masa kina period koh?" Xaro
ido tayi tace "Wllh ni ban ce masa ba Inna ce ta fada masa nima ai sai da naji
kunya fa" tana magana tana turo baki, yace "Toh wa yayi maki alluran?" Shiru tayi,
ya d'an mata tsawa yace "Answer me now" turo baki tayi tace "Inna ta min" sai kuma
ta rufe fuskarta da sauri a pillow tana dariya a hankali, kallon ta ya dinga yi
yana jin xuciyarsa na wani tukuki, a hankali ta dago tana kallonsa, ganin yanda ya
daure fuska ba shiri ta shiga taitayinta strictly yace "Sai kika bude masa kaya ya
maki allura yana kallon ki right?" Sosai ya bata dariya amma bata yi ba tana komawa
baya a hankali tace "Ni a cinya nace ya min, kuma a nan ya min fa yaya, bari in
nuna maka wajen ma" tana fadin haka ta dage gown din jikinta a hankali tana nuna
masa lap dinta, a hankali ya sauke idonsa yana kallon fresh lap din nata, lkci daya
yaji ransa yayi wani mugun baci xuciyarsa na tafarfasa, tayi murmushi ta rufe kafan
tace "Kagani ai" fuska a tamke yace "When xa ku fara exams na first term?" Ta buda
manyan idonta tace "Saura kusan four weeks ai Yaya" yace "Good ana gama saukan ku
dama idan Inna xata taho gidana ku taho tare" ta xaro ido tace "Saboda me Yaya?" A
tsawace yace "I am giving you instruction, don't question me" daga haka ya mike ya
juya ya nufi kofa rai bace, ta bi sa da wani kallo bayan ya fita, murya can kasa
tace "Tabb, waye xai je gidan ka, ni dai baxan je ba" Xaune ya tadda Inna kan
tabarma ta daura kafa daya kan daya tana ba Safeenah labarin irin wahalan da tayi
da Mujaheed tun daga ranan da aka haifo sa duniya.... Inna na kallon Safeenah da
kyau tace "Ko ke baki ga bakin d'an tsut ba??" Duk da irin yanda Safeenah ta dinga
dakewa coz at first she wasn't interested with the story gaba daya hankalinta na
daki ganin Mujaheed bai fito ba har sannan, amma bata san lkcn da ta fashe da
dariya ba har da sakkowa kasa tana kallon Inna, Inna ta hade rai tace "Ke Safara'u
ba batun dariya ba wllh, ya tsotsi uwar ne ba kadan ba sai dai Allah ya bata lada,
sai kin gansa wani narkeke da shi malam, don dama nonon Rukayya ba dai kyau ba
gaskiya" Dariya kawai Safeenah take har da kyakyatawa, Inna ta tabe baki tace "Uhn
ni dai ba ruwana" Mujaheed dai yayi still bakin kofar daki ya kasa karasowa cikin
parlon, Inna tace "Toh wllh da ya dawo wajena yana da shekara uku sai...." Katse ta
Mujaheed yyi fuska daure ta hanyar ce ma Safeenah "Tashi mu tafi" ita dai sai
dariya take, Inna tace "Ya haka ina bata tarihi Mujaheed" Mujaheed yace "Toh sai ki
jira idan an baki mai gadin gidan tarihi...." Inna tace "Meye laifina Mujaheed,
matar ka ce fa kuma sai mu xauna tana kallona Ina kallonta kamar kishiyoyi" Mikewa
Safeenah tayi tana dariya tace "Toh Inna mu xa mu koma xan xo ni kadai in sha Allah
sai ki bani karshen labarin" Inna na washe baki tace "Toh Safara'u shiga ku yi
sallama da Imaan din kiyi mata Allah ya sauwake" D'an dariyar dake fuskar Safeenah
ya dauke bata dai ce komai ba ta shiga dakin, tsayawa tayi bakin kofa tana kallon
Imaan dake xaune saman gado from head to toes, imaan ta wani daure fuska, Safeenah
ta ja tsaki tana yatsine fuska ta fice daga dakin. Dai dai nan aka yi sallama bakin
kofa, Inna ta mike da sauri tana amsawa tace "Bisimillah Bukar, Mujaheed ne kadai
da amaryarsa, shigo" Sadeeq ya shigo parlon yana murmushi, hannu ya mika ma
Mujaheed dake tsaye bakin kofa yana kallonsa, Mujaheed ya amsa still looking at him
suka gaisa, Inna na washe baki tace "Toh xauna Bukar" Xaunawa Sadeeq yyi kan
lallausan rug dake parlon, Inna na kallon Safeenah tace "Saurayin imaan kenan
Safara'u, tana gama sakandari nan da wata daya xuwa biyu dama xa a fara maganar
auren su, baki ga ba yaro mai kirki da sanin ya kamata wllh" Safeenah tana kallonsa
tace "Sannu da xuwa" Sadeeq ya mata godiya yana murmushi, Safeenah ta nufi kofa
tana kallon Mujaheed sannan ta kalli Inna tace "Toh Inna bari mu je sai na sake
dawowa" Mujaheed yayi ma Inna sallama ya fita Safeenah na biye da shi, sai da suka
d'an yi nisa ya tsaya yace "Ki tafi bangaren mu ki jira ni, I forgot i need to
discuss something with grandma" da mamaki ta dinga kallonsa, can tace "Toh sai mu
koma tare ai" ya wani hade rai yace "Wannan sirrinmu ne, do as I say plss" Bai jira
cewarta ba ya juya ya koma parlon Inna, ta bi sa da kallo da mugun mamaki, Inna ta
xubo ma Sadeeq abinci ta cika masa nama tam ta ajiye gabansa xata dauko ruwa kenan
Mujaheed ya shiga, cike da damuwa tace "Naga abinda ya isheni.... mai ya dawo da ku
kuma Mujaheed ba kun tafi ba, wllh shi kadai na ma girkin ban da ku...." Sadeeq bai
san lkcn da ya fara dariya ba, Mujaheed ya wani hade rai yana kallonta, tace "Ni
dai ba ruwana, mutane dai ba gaskiya meye kuma na dawowa bayan mun yi sallama kun
tafi" Mujaheed bai fasa karasawa cikin parlon ba ya xauna, Inna ta ajiye ma Sadeeq
ruwa da malt biyu tace "Toh ni ban san yanda xan yi da kai ba gaskiya Mujaheed, ko
in jiko maka garin kwaki ina ma da gyada wllh" Sadeeq ya hadiye dariyarsa yace
"Wllh Kaka ya min yawa xa mu ci wannan tare" Inna ta tsuke fuska tana kallon
Mujaheed tace "Katon ba sai ya cinye gaba daya ba kana xaune Bukar...." Sadeeq na
murmushi yana kallon Mujaheed da ya hade rai yace "Bismillah Dr" Mujaheed yace
"Alhmdllh, I am okay" Inna tace "To maa sha Allah, maxa maida hankali ka cinye
kayan ka Bukar, Ni dai nasan sai ka fita xai tsigaleni tass.... Toh wannan duk bai
dameni ba tunda Allah ya ga xuciyata kai na ma girki, ban san da xuwansu ba" Sadeeq
couldn't stop smiling ya dau spoon ya debi abincin ya kai baki bayan yayi
Bismillah, Inna ta xauna tace "Ita ma imaan d'an kadan na debar mata gashi can rufe
a kitchen, toh ni basu sanar min xa su xo ba da nayi girkin da su, meye a ciki don
dai ka ba mutum abinci, kawai fa ganin mutumi nayi gantsantsan a kaina mata na
tsaye bayansa, na ja bakina nayi shiru na basu hanya, shi sa na tafi kitchen na
adana maka abincin ka kada su gani su tafi da ni a baki suce na masu rowa, kasan
mutumin yau" Mujaheed dai bai tanka ta ba, ta gaji da xubanta tayi shiru, yana ta
xaune har Sadeeq ya gama cin abinda xai ci, bayan Inna ta tabbata da gaske ya koshi
ta kalli Mujaheed tace "Toh don Allah kayi hakuri ka ci sauran, kaga dai a nutse ya
ci abincin irin na yan gayu" Sadeeq ya fara dariya ya kasa kallon Mujaheed dake
kallon Inna ba yabo ba fallasa, Inna ta tabe baki ganin Mujaheed bai ce komai ba ta
dauke abincinta ta wuce kitchen ta rufe, dawowa tayi tana kallon kofar daki tace
"Toh imaan dakin xai bi ki fisabilillahi, ki fito mana" sai da Inna ta kara magana
imaan ta fito da hijab, Sadeeq ya dinga kallonta, rakubewa tayi jikin kujera tana
kallonsa a hankali tace "Ina yini" yayi murmushi yace "Lafiya lau, how are you
feeling now" tace "Na ji sauki" yace "Maa sha Allah, hope you've eaten?" Ta gyada
masa kai, Inna dai sai kallonsu take tana murmushi, imaan ta saci kallon Mujaheed
dake kallonta fuska daure, Dauke kai tayi da sauri, Sadeeq yace "Toh shkkn kaka na
cika alkawari tunda na dawo na ci abinci, ni xan koma" inna tace "Wllh na ji dadi
Bukar Allah maka albarka, tashi ki raka sa ke" Kudi ya fiddo aljihunsa dubu ashirin
ya ajiye kasa kan carpet da ya tashi yace "Kaka tukuicin girkin, naji dadi kuma
nagode" Inna tayi tagumi a hankali tace "Naga abinda ya isheni... Bukar dai baya
gajiya, abincin ma sai an bada tukuici?? Toh Allah maka albarka, ni dai na gode
baxan tsaya ina jayayya da kai ba kamar karamar yarinya, nagode" Yana murmushi ya
nufi kofa, Inna na kallon Imaan ta hade rai tace "Ke dai sususu ce wllh, baxa ki
tashi ki rakasa ba toh" imaan ta turo baki ta mike ta bi bayansa, Inna na kallon
Mujaheed tace "Toh kullum aikin kenan fa wllh, sai ya ajiye min damin kudi haka
kafin ya fita har na rasa yanda xan yi da kudi a dakin nan, ni fa ya fi min mutane
da dama a duniyar nan don yasan abinda ya kamata, ku ma dai ku ji tsoron Allah ku
dinga koyi da shi..." Mikewa Mujaheed yyi ya fice daga parlon. Tsaye Mujaheed ya
tadda su kusa da flower sai wani sunkuyar da kai imaan take shi ko sai kallonta
yake kamar lkcn ya fara ganinta, kamar mai counting steps dinsa ya dinga tafiyar
don basu lura da shi ba, murya can kasa Sadeeq yace "Plss ki kalleni dear let me
feel relieved, I've missed you alot,
but staying far away from you and just listening to ur voice is d best to me" Ita
dai ta kasa dago kanta, a hankali ya kamo hannunta ta dago manyan idanuwanta tana
kallonsa, yyi murmushin sa mai tsuma xuciyar wanda ya gani cikin cool voice dinsa
yace "I love you Imaan, I am always dreaming to be with you by my side as my
wife.... I wish xa ki ga yanda na kagu ki xama matata.... I just can't..." Sai
kuma yyi shiru ya lumshe ido, Imaan tayi still ganin Mujaheed da ya tsaya yana
kallonsu, da sauri ta xame hannunta daga na Sadeeq, Mujaheed ya dauke kai ya ci
gaba da tafiya gently, Ko Sadeeq bai juya ba yasan shi ne, kuma ya ki kallonsa, har
sae da Mujaheed yyi nisa sannan Sadeeq ya bi sa da wani kallo, can ya gyada kai
smiling, Imaan tace "Xan je in kwanta na gaji" yace "Sure dear, hope cramps din yyi
sauki?" Xaro ido tayi sai kuma ta rufe fuska da sauri, ya dinga kallonta yana
murmushi, ya kai bakinsa kusa da kunnenta a hankali yace "A day will come da xaki
san kunya baxae amfane ki ba" turo baki tayi har sannan ta ki kallonsa, murya can
kasa yace "I want just a favor from you... And don't deny me plss" tana kallonsa
tace "Na me?" Yana murmushi yace "I will text it to you idan na shiga mota ynxu coz
I am not ready to dig u out from underground now" xaro ido tayi tana kallonsa, ya
hade rai yace "And if you deny me, I won't be happy imaan" Bai jira cewarta ba ya
fara tafiya yace "Expect the text now, gobe I might come in the evening in sha
Allah" ta bi sa da kallo har yyi nisa sannan ta juya a sanyaye ta koma part din
Inna. Bayan magrib imaan na xaune dakin Inna bayan ta gama shirin bacci xata kwanta
ta tuna wayarta da text din da Sadeeq yace xai turo mata tun da rana, mikewa tayi
da sauri ta dau Hijab ta saka ta fito parlor tasan ma kila yana ta kiranta, Inna
dake xaune parlon tana cin abinci ganin ta nufi kofa ta tabe baki tace "In ji baki
mance komai naki a dakina ba Imaan" imaan tace "Xan dawo fa, wayata xan je in dauko
a gida" cike da damuwa Inna tace "Me kuma xa ki dawo ki min?? Tun safe fa kike nan"
Imaan bata saurareta ba ta fita parlon, daga nisa ta hango mutum na tahowa kamar
Yusuf kamar kuma Mujaheed, duk da Yusuf ta san ya daina xuwa part din Inna sai tare
da Abba, Tsayawa tayi har sai da ya iso kusa da haske taga Mujaheed ne, turo baki
tayi ta juya da sauri ta koma part din Inna, Inna da ta bar abincin da take ci ta
tafi tana share dakinta ta daga kai tana kallonta tace "Naga jaraba... Har kin
dawo??" Imaan ta bi ta gefenta ta shige dakin tana cewa "Ko ba Yaya bane" Inna ta
ci gaba da sharanta tace "Toh dama ki kakkabe min xanin gadona ki gyara gadon fess
ni ba gantalalliya bace, ba haka nake barin dakina ba in kwana tare da wari" Inna
ta mike ganin Mujaheed tace "Wannan shine anyi ba ayi ba, yanxu kayi auren ma baxa
mu sarara ba Mujaheed kullum kai ta mana sintiri a gida, ba daxu da rana ka xo ba
to me kuma ya dawo da kai, ko akwai ajiyar ka a parlon nan ne baka dauke ba har
yanxu" Bai tanka ta ba ya nufi kofar dakin ya bude ta bi sa da kallo baki bude,
imaan ta koma can karshen gado kamar xata yi kuka tana kallonsa, Ya wani mugun
daure fuska yace "You had better keep on running away from me coz wllh wlh am
promising you this... if I should get hold of you I won't take it likely with
you.... I will seriously deal with you" a fusace Inna tace "Naga abinda ya isheni,
don Allah Mujaheed ka rufa mana asiri, me ta maka kake kunduma mata xagi haka,
yarinyar da kamar baxata yi ba daxu Allah ya rufa mana asiri Bulasawa ya rufa mana
ya mata allura ya bata magani taji sauki shine yanxu xaka xo kana xaginta kana nuna
ta da yatsa kana gaya mata maganganu marasu dadin ji, to ni dai ba ruwana ka tafi
ka ba mu waje, ni na ta6a jin inda aka aurar da mutum kuma yyi ta sintirin dawowa
gida kamar dai da ajiyarsa da ya mance bai dauka ba, ni dai gaskiya na gaji da kai
kar ka sake xuwa min, tunda kayi auren ka kayi xamanka a gidanka ka bar min jikata
ta sarara...." Kawai Inna gani tayi ya shige dakin ta fasa ihu tana kwala ma Ahmadu
kira iya karfinta, ba kuma wanda xai ce ba wani mugun abun ta gani ba, Imaan ma duk
ta rude xata gudu bandaki ya fixgota kawai sai ji tayi xabga mata mari mai lafiya,
ta rike fuskarta a gigice, inna na ganin haka ta fice da gudu xuwa waje tana kiran
Abba, Mujaheed na kallonta da idonsa da suka kada cikin harshen turanci yace
"Muharramin ki ne mutumin nan da kika mika masa hannun ki ya kama, dama iskancin da
ku ke yi da shi kenan, yana tsaye kusa da ke kamar xai shige jikin ki kina jin dadi
koh? To wllh yanxun nan xan je in sami daddynki in sanar masa komai" a rikice imaan
ta rikosa ta dinga basa hakuri tana cewa "Yaya ni bani nace ya rike ni ba, don
Allah kayi hakuri baxan kara ba wllh, don Allah kayi hakuri" sosai xuciyarsa ke
tafarfasa yana kallonta, ta hade hannayenta hawaye na sakko mata tace "Don Allah
kayi hakuri baxan kara ba da gaske Yaya" tana fadin haka ta boye fuskarta a jikinsa
tana kuka, har ransa yake jin kukan nata, Bai san lkcn da ya jawota jikinsa ba
cikin sanyin murya yace "That's very wrong imaan, I've told you times without
numbers... that guy is just here to ruin ur life, to cause you heartbreaks, he is
after ur body... He is..." Kasa ci gaba yyi don sosai ransa ke tafarfasa, imaan dai
sai sauke ajiyar xuciya take tana kuka a hankali bata ce komai ba, nan ko ko kiris
bata yrda da abinda Yayan nata ke fada ba don ita tasan Sadeeq na sonta kamar yanda
ita ma take sonsa fiye da xaton mai karatu, dago kanta yayi yana kallon kwayar
idonta da ya rine murya can kasa yace "For my sake xa ki rabu da shi plss Imaan?"
Ta fashe da kuka cikin rawar murya tace "Ni dai ina son sa Yaya, kuma ai aurena xai
yi..." Kallonta Mujaheed yake ko kiftawa babu xuciyarsa na bugawa, da kyar tace
"Kayi hakuri plss Yaya, da gaske Ina son sa, but in sha Allah baxan bari ya sake
rike hannuna ba"

🌟⭐⭐⭐🌟assslamun alykum ina bawa masoya littafina imaaan hkrn xasujini shru xan dau
hutune xuwa bayan.sallah in allah ya kaemu tnx u fans imaaan inbaki biyaba karki
karanta🌟⭐🌟

_Maa Sha Allah, koma wacece ko wanene yayi wannan Broadcast din na sama👆🏻 ya
sani.... Da *NI* da *shi/Ita* xa mu hadu gaban Ubangiji, ba fa a kan komai ba sai
kan gantalallen Hausa Novel wanda baxai kare mu da komai ba, baxai amfane mu da
komai ba ranan gobe kiyama, wanda muke fatan ma ba xunubi muke kwasan ma kanmu ba
muke kuma rokan Allah ya yafe mana, wato irin xagi da cin mutunci da mai Broadcast
din ya ja min jiya wllh tllh xa ayi mana hisabi da koma wanene, don ni dai na yafe
duk xagi da na sha amma mai post din ya sani xa mu hadu gaban ubangijin da ya
halicce mu in sha Allah, and that's if he or she believes there is God_
Ni ba fitinanniya ba ni ba mafadaciya ba, ni ba mai sa ido ba, ni ba mai takura ba,
amma duk da haka ban tsira ba a media sai an cakale ni na mayar da martanin da bana
so dai, duk da babba da hakuri aka san sa amma a dai dinga jin tsoron Allah, mutane
dai ba gaskiya basa tsoron Allah, a dai dinga jin tsoron Ubangiji ni ba ruwana.

Least I forget akwai wani hoton dake circulating na wata mai pink kaya wai
Khaleesat Haiydar, to gaskiya ban san yarinyar ba ayi hakuri a daina turo min ana
tambaya ko ni ce don ba ni bace, plsss ba ni bace oo... this is not 2012 I am
begging you pple ba ni bace...😟 Ranan da na gama Imaan xanyi attaching pic dina a
karshen page din sai ku gani😁

One love fans😍

Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

56....

Saketa Mujaheed yayi har sannan bai daina kallonta ba sai kuma kawai ya juya ya
nufi kofa ya fita, ta bi sa da kallo tana share hawayen dake xubowa idonta a
hankali, komawa tayi gefen gado ta xauna a sanyaye, ko minti biyar ba ayi da fitar
Mujaheed ba Inna ta dawo dakin tace "Tashi mu tafi Ahmadu na kiran ki ya ji
ba'asi... Yau in sha Allahu xai mana iyaka da shi, kada ya sake shigo min tunda
yayi aure, Ina murna na rabu da shi kuma sai kullum ya wani xo min xalo xalo kamar
da ajiyarsa da ya mance min a nan???" Imaan tace "Ni dai ba abinda yayi min fa,
kuma bance ki je ki ce ma Abba komai ba, ai ni ce ban gaishesa ba shi sa, kuma na
hakura ni dai" Sake baki Inna tayi tana kallonta, Imaan ta mike ta nufi kofa tace
"Komai sai ki tafi wajen Abba baki jira kin ji abinda ya faru ba..." daga haka ta
fice a dakin ta bar Inna a tsaye. A hankali Imaan ta bude kofar parlon su ta shiga
gabanta na faduwa, da ta tuna abinda Mujaheed yace wai xai gaya ma Daddy sai
hankalin ta ya tashi, amma ta san baxai ma fada ba kawai tsorata ta yayi, Ammi ce
kadai xaune parlor tana kallo, ta xauna kasa a hankali ta gaisheta, Ammi na
kallonta tace "How are you feeling?" Tace "Na ji sauki Ammi" Ammi tace "Toh Allah
ya sauwake, ga abinci can kitchen idan xa ki ci" ta girgixa kai tace "Na ci a wajen
Inna" Ammi bata ce komai ba, hakan yasa ta mike ta nufi dakinta, a hankali ta nufi
inda wayarta ke ajiye ta dauka xuciyarta na bugawa don bata san abinda xata gani
ba, ta xauna gefen gado ta sauke ajiyar xuciya a hankali, can dai ta kunna wayar
tana kallon screen din taga message da missed call a gaban screen din, missed call
din ta fara shiga taga na sadeeq ne kuma just few minutes ago ya kirata, bude text
din tayi tana dubawa kamar idanuwanta xa su fito, ta maimaita text din ya fi sau a
kirga, can ta 6ata fuska kamar xata yi kuka, tafi minti goma a xaune, sai can kuma
tayi wa Maryam forward din message din, bayan ta tabbata ya tafi tayi deleting gaba
daya a wayar, ta d'an yi murmushi ta mike ta cire Hijab din jikinta ta linke ta
kashe wutan dakin ta kwanta. Washegari da ya kasance Monday Imaan ta ji sauki sosai
hakan yasa tayi shirin wucewa schl da safe, tana tattara few textbooks dinta da
xata tafi da su makaranta taga wayarta dake gaban madubi yyi haske, karasawa tayi
ta dau wayar taga text din Maryam ne ya shigo tana requesting ta hau WhatsApp su yi
chatting, reply tayi mata da cewa sai ta dawo schl daga haka ta ajiye wayar ta fita
dakin. Karfe hudu saura Imaan suka fito schl tare da Mariya dake ta mata labari tun
basu fito aji ba, tsaye su ka ga Sadeeq jikin motarsa ya rungume hannu idonsa sanye
da glasses, Sosai gaban Imaan ya fadi, Mariya ta wara ido tana kallonsa tace "Ya
Sadeeq Drivers fa?" Shi dai bai ce mata komai ba, Kallon Imaan Mariya tayi tana
murmushi tace "Sai gobe xan ci gaba Imaan" tuni kanninta biyu shiga mota yayan
nasu, Imaan ta gyada mata kai tana d'an murmushi tace "Allah ya kai mu" Har Mariya
xata shiga motar sai kuma ta kalli Imaan tace "Baxa ku gaisa da yayana ba" Imaan ta
kalli Sadeeq dake kallonta ba ko kiftawa, daga inda take tsaye a hankali tace "Ina
yini" ya gyada kai yace "Lafiya lau" daga haka ya xaga ya bude maxaunin driver ya
shiga ya tada motar suka wuce. Imaan na dawowa islamiyya that same day taga Miss
call din Sadeeq, kasa kiransa tayi da farko don bata san me xata ce masa ba, can
dai tayi dialing number a hankali ta kai kunne, yana fara ring ya katse ya kirata,
tayi gathering courage tayi picking, murya can kasa tayi masa sallama ya amsa yace
"You are ignoring my calls ko" ta xaro ido tace "A'a wllh, bana kusa da wayar ne ai
yanxu muka dawo islamiyya, jiya kuma Ina part din Inna wayar kuma na part din mu"
yace "Ohk, I tot u where ignoring it shi sa ma ban xo ba yau, ya jikin?" Ta
langwabar da kai tace "Na ji sauki" yace "Maa Sha Allah" shiru tayi ta rasa abun
cewa, can yace "Did you see my text or u don't just want to talk about it?" D'an
murmushin karfin hali tayi tace "Sure I saw it, I... but.. I can try doing as u
wish, but I can't perform the action in the text" Dariya yayi yace "Ohk then...."
Ta turo baki bata ce komai ba, yace "I will call you later xan fita masallaci" tace
"Allah ya kai mu" daga haka ya katse wayar. Ranan Thursday da safe bayan Imaan ta
gama shirin boko ta sami Ammi a kitchen a hankali tace "Ammi tunda ba islamiyya yau
idan na dawo schl plss Ina son in je in gaida Gwaggwo daga nan sai in kai ma Aunty
halima katin sauka" Ammi tace "Jiya ba ce min kika yi Thursday da Friday duk xa ku
je islamiyyar ba da yamma?" Imaan ta xaro ido tace "Ance sai Friday morning and
evening" Ammi ta tabe baki tace "Toh ki kira daddy ki gaya masa, ai ba ni xa ki
gaya ma ba" Murmushi Imaan tayi tace "Ae har na gaya masa jiya da daddare" Ammi
tace "Toh Allah ya kai mu" Imaan tace "Ameen" shayi ta hada a cup ta fita da bread
da egg dinta a plate xuwa dinning. Tana dawowa schl ranan ko abincin kirki bata ci
ba tayi wanka ta shirya cikin bakin abayanta ta sa Hijab har kasa ta fito parlor,
Ammi dake kallonta tace "Kar ki kai magrib a hanya Imaan" xaro ido Imaan tayi tace
"Ammi ni fa cewa Daddy nayi xan kwana" Ammi tace "Kwana kuma?" Imaan ta marairaice
tace "Ehh Ammi na gaya masa, ki kirasa ma" Ammi tace "Toh schl din fa?" Imaan tace
"A'a ai nace maki islamiyya xan je da safe da kuma yamma tunda Saturday ne saukan
ai" Ammi tace "Ba ruwana ni ban ce ki kwana ba da kin gaisheta ki kai ma Halima
kati ki juyo, am I clear???" imaan tayi shiru tana kallonta kamar xata yi kuka,
Ammi ta ci gaba da abinda take, a hankali Imaan tace "Toh sai na dawo" Ammi tace
"Dama kada ki kuskura ki kai magrib a titi ni dai na gaya maki" imaan ta nufi kofa
bata ce komai ba har ta fita parlon. Imaan na isa gidan gwaggwo dama gaisheta kawai
tayi tace "Ina sauri xan je gidan Anty Halima in kai mata kati in dawo...." Gwaggwo
na kallonta tace "Toh shikenan sai kin dawo, ya saurayin naki Sadeeq?" Yar dariya
tace "Yana nan, shi xai kai ni gidan Aunty Halima din ma, amma kar ki gaya ma Ammi
fa" Gwaggwo tace "Au tare ku ke shine bai shigo mu gaisa ba" imaan tace "A'a yanxu
dai ya kirani yana hanya" Gwaggwo tace "Toh Allah ya kawo sa lafiya, Mujaheed na
lafiya da amaryar sa dai koh?" Imaan ta turo baki tace "Nima dai ban sani ba"
Gwaggwo tace "Baki je gidan ba kenan" imaan tace "Mun je da Gwaggwo amma matar bata
da mutunci, ni dama baxan sake xuwa gidansa ba har abada" Gwaggwo tace "Ikon Allah,
toh Allah dai ya kyauta, amma ai babu xancen baxa ki kara xuwa gidan yayanki ba
Imaan" Imaan ta dau wayarta dake ring ganin Sadeeq ne ta mike tana kallon Gwaggwo
tace "Sai na dawo" Gwaggwo tace "Har ya iso" Kai ta gyada mata, Gwaggwo tace "Toh
Allah ya kiyaye, hanya a dai kula kin ji" Imaan ta nufi kofa ta fita parlon, yana
xaune mota ta karasa ta bude front seat, kallonta ya dinga yi, a hankali tace "Ina
yini" ya d'an yi murmushi yana shafa kansa murya can kasa yace "Lafiya lau Hijab
queen, you look beautiful in it always, but yau ma sai kin sa?" Shiru tayi tana
kallonsa, Yana mata murmushi yace come in" a hankali ta shiga motar ta rufe ba tare
da ta yarda sun hada ido ba, ya tada motar yace "Xa ki kai ma Halima card din first
koh?" Ta gyada masa kai, driving yake kamar bai son yi, lkci lkci kuma yana
kallonta ta gefen ido, shiru babu wanda yace komai cikinsu har suka isa gidan Aunty
Halima after 15 mins ride, ya juya yana kallonta a hankali yace "Be fast Imaan" ta
gyada masa kai ta sauka ta nufi cikin gidan ya bi ta da ido, jinginar da kansa yayi
jikin mota ya lumshe idanuwansa, can ya bude ya dau wayarsa yayi dialing number ya
kai kunne, ana dagawa, cikin cool voice dinsa yace "Selim... I think I am just
sorry, I had to disappoint you guys, may be some other times xa ku santa, kawai na
fasa deal din" Best dinsa Selim dake sauraronsa da mamaki yace "I don't get you
Sadeeq..." Sadeeq ya d'an yi shiru sai kuma calmly yace "I can't bring her to that
place, she's more than decent and innocent, though I have neva had bad intention
toward her... but, I am sorry for the disappointment, I will compensate this deal
for what ever amount you guys will require" Selim yace "You are sick, mu ne ba mu
san ciwon kanmu ba ko, mu ne ba mu san ciwon babes din mu ba, what's the use of all
this Sadeeq, after necessary arrangements da aka gama ka xo kana kawo mana wani
surutu, this is very unusual of you, haka on ur Birthday wai wani she's sick baxata
xo ba, wato mu namu Girlfriends din ne pure water....." Sadeeq dai tabe baki kawai
yyi bai ce komai ba, Yana jin friends din nasa dake guest inn din nasa suna surutu
daga karshe ya katse wayarsa, dialing number Mariya yayi, tana dagawa ya gaya mata
wani babban wajen cin abinci da xata je ta jirasa in the next 15 mins, yana gama
fada mata ya katse wayarsa. Imaan na fitowa gidan cousin dinta ta bude motar tana
kallonsa a hankali tace "Kayi hakuri I kept u waiting" murmushi kawai yyi bai ce
komai ba ta shiga motar, tada motar yayi suka bar layin, sai da suka hau saman titi
ya kamo hannunta da nufin xai mata magana, ba ita kadai ba har shi sai da yayi
shock hakan kuma ya sa ya saketa, har kuma suka isa wajen cin abincin bai ce mata
komai ba ita ma haka, ganin motar gidansu a haraban eatry din ya gane Mariya har ta
iso, Yana kallon Imaan yayi murmushi yace "Mu je" a hankali ta bude motar ta sauka
shima ya sauka ya rufe motar ya shiga gaba tana biye da shi har suka shiga wajen,
few mutane ne cikin hadadden wajen, Sadeeq ya hango Mariya xaune tana danna waya ta
cakare cikin English wears, ya kalli Imaan dake kallon Mariyar da mamaki ita ma, Ya
wara mata ido yace "Mu je" ba musu ta dinga bin sa har suka isa gun Mariya, Mariya
da tuni ta hangosa amma bata san tare da Imaan bane ta dai ga mace da Hijab, a
xuciyarta kuwa cewa tayi ohhh tot ya Sadeeq ya shiryu gaba daya jin kwana biyu
shiru ba ace min ga new catch ba balle mu hadu in gilla mata karya, ashe dai da
saura, ko wa kuma aka samu mai hijab har kasa, dariya abun ya bata don ita dai
tasan he is not a lover of hijab fa, haushi yake ji yaga mace ta sa hijab sanin da
tayi masa da, Suna isa inda take ya ja ma Imaan kujera yana kallonta, Imaan dake
kallon Mariya ta xauna, shi ma ya xauna, Mariya ta ajiye wayarta ta fara magana
kamar yanda ta saba duk sanda suka hadu da daya daga yan matan nasa, tana murmushi
tace "Sannu auntynmu, Yaya yace yau dai sai mun gaisa da future wif......" Shiru
tayi da mugun mamaki tana kallon Imaan, can ta kalli Sadeeq amma ta kasa cewa komai
xai xare ido take, cikin cool voice dinsa yace "Meet my soulmate, the future mother
of my angels in sha Allah...." Mariya was just lost of word, imaan kam ta sunkuyar
da kai, a hankali Sadeeq yace "Ko bata maki bane Lil sis?" Mariya na kikkifta ido
tace "I don't get this ya Sadeeq, are you for real??" gently yace "Sure, my future
wife in sha Allah, Imaan is her name" Tasowa Mariya tayi ta rungume Imaan cike da
murna tace "Waow, amma na ji dadi sosai wllh Yaya, but you two neva for once told
me, me yasa kuka boye min plss..." Imaan dai tayi murmushi bata ce komai ba,
waitress ce tsaye kansu tana tambayar me xata kawo masu, Sadeeq yace "Just drinks"
Sadeeq na kallon kanwartasa yace "Toh sake min ita kada ki fadar da ita" dariya
sosai Mariya tayi ta sake imaan ta xauna, tana kallonsu so happy, ba a dau lkci aka
kawo masu drinks din, Imaan dai sai kallon Mariya that couldn't hide how happy she
is, tana mitan irin deceiving dinta da suka dinga yi kullum sai yace mata bai gane
imaan ba ashe ma ya fi ta gane ta, Shi dai Sadeeq kallon Imaan kawai yake with
affection, sai a sannan yake da ya sanin ma amincewa da yayi xai kai ta guest inn
yayi proposing mata gaban gantalallun frnds dinsa da a yanda yake ya ma fi su kamun
kai... lol, after the proposal kuma party... party that they will be different type
of wines, a must drink... Kawai a gama kalle masa soulmate, lkci daya mood dinsa ya
canxa, Mariya ta xuba ma imaan drink a disposable cup ita ma ta xuba ta dauka ta
mika ma imaan tana murmushi tace "Here.... Future in-law...." Imaan ta amsa tana
murmushi, Mariya ma ta xuba ta fara sha tana kallon Sadeeq tace "You can serve ur
self" d'an murmushi yyi ya diba ya fara sha, Mariya na shan drink dinta ta fara
imagining to ya ake wannan soyayyar da Imaan, imaan dai da ta sani baxata ta6a
yarda Sadeeq yyi kissing dinta ba balle ya rungume ta, toh how is her brother
coping, Sadeeq that she know can't do with out that tabbb, tunanin hakan ya bata
dariya sosai, to ko ya ake wannan soyayya, Sadeeq ya ajiye sauran drink din
hannunsa yace "You two should tell me abinda ku ke so na saukan ku that's on
Saturday" Mariya tace "Good, muna komawa gida xan maka list dama, muna bukatan lot
lot of thingssss" dariya kawai yayi sanin both abinda ya kamata da wanda bai kamata
ba kenan xa a rubuta a list in dai Mariya ce, they spent just 30 mins a eatry din
daga nan Sadeeq ya mike yace "It's past six now xan mayar da ita gida" Mariya tace
"Ohk then, am very happy at this Yaya, Allah ya sanya alkhairi, plss" yace "Ameen"
daga haka suka fita eatry din Mariya na cewa "Plss this shouldn't take too long
ooo" Imaan dai taki yarda ta kalleta, Sadeeq dai yyi murmushi yace "Sure just in
few months time" Mariya ta dinga murna ita a dole Sadeeq xai auri kawarta, motar
gidansu da driver ke xaune yana ta jiranta ta nufa tana daga ma imaan hannu tace
"Sai mun hadu islamiyya gobe da safe in law" Sadeeq ya bude ma Imaan back seat yana
kallonta, shiru tayi tana kallonsa ita ma, ya d'an yi murmushi yace "You don't
worry ki shiga, I don't mind being ur Driver" ta d'an yi murmushi ta shiga motar a
hankali, ya rufe sannan ya shiga driver seat ya tada motar ya bar eatry din. Yana
driving yace "Gidan gwaggwo xan maida ki ko gida?" Tace "Gida, xan kirata ince na
wuce gida" yace "Ohk" suna isa layin ya tsaya 2 houses away, sannan ya bude motar
ya dawo baya ya shiga ya rufe yana kallonta, sunkuyar da kai tayi gabanta na
faduwa, tsoronta daya kada Mujaheed ace yana anguwar balle ya ganta cikin motar duk
da glass din is tinted, Sadeeq yana d'an murmushi yace "I think I don't have to
propose in midst of friends, just me and you..." ita dai bata ce komai ba tana
kallonsa, ya dauko wani karamin box ya bude yana kallonta, sunkuyar da kai tayi
gabanta bai bar faduwa ba, ya ciro ring din ciki wanda ba sai na fadi wani iri
bane, lol... ya kamo hannunta yana kallonta ya xura mata ring din, ita dai ta kasa
dago kai ta kallesa xuciyarta sai bugawa yake ga kamshin sa da ya cikata, Bata
ankara na sai ganin ya hade bakinsu tayi, tunda take bata ta6a tsorata na moment
din ba, coz it was something that had never happened to her all her life, lkci daya
ta fara turasa hawaye na sauka idonta, bai wani dau lkci ba ya saketa shi ma
xuciyarsa na bugawa, daura kansa yyi a kafarta cikin sanyin murya yace "I.. i.. am,
I am sorry Imaaan" ja baya tayi hakan yasa ya dagata ta bude motar ta daya side din
ta fice daga motar da sauri....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788
57......

Imaan na shiga parlonsu ta wuce dakinta direct ta kulle kofa ta fashe da kuka
sosai. Bayan kusan minti goma Ammi ta dawo daga part din su Aunty ganin takalman
imaan bakin kofa ta shiga parlon ta wuce dakinta, alwala tayi ta dawo parlor tana
kallon agogo don har sannan da saura lkcn sllhn bai yi ba, ta kalli kofar dakin
Imaan tace "Imaan" Da sauri Imaan dake xaune can karshen gado ta hade kai da gwiwa
ta daga kanta, Ammi ta sake kiranta, sakkowa tayi daga kan gadon tana goge idonta
duk da hawayen ya ki tsaya mata, ta nufi kofa ta bude ta fito parlor, Ammi na
kallonta tace "Yaushe kika shigo?" Da kyar ta bude baki tace "Ban dade ba" shiru
Ammi tayi tana kallonta da mamaki, Imaan ta sunkuyar da kai gabanta na faduwa
sosai, Ammi tace "Kukan me kike?" Ta girgixa kai tace "A'a ba komai" Ammi ta mata
wani kallo tace "Zo nan" sosai xuciyarta ke bugawa ta karasa ta duka kasa tana
kallon Ammi tace "Gani" cikin tsawa Ammi tace "What's wrong with you?" Duk yanda ta
so dakewa kasawa tayi, ta fashe da kuka sosai, duk yanda Ammi ta so boye tashin
hankalinta a lkcn kasawa tayi, Tayi kasa da murya tace "Nace me ya faru imaan,
kukan me kike yi, talk to me daughter" Cikin rawar murya tace "Da gaske Ammi ba
komai" Ammi ta wani hade rai tayi mata wani tsawa tace "Baxa ki bani amsa ba, kukan
uban me kike, me aka maki?" Imaan dai ta kasa cewa komai sai hawaye, mikewa Ammi
tayi hakan yasa ta tashi da sauri ta koma baya ta fashe da sabon kuka, tsayawa
kallonta Ammi tayi, can ta wuce daki da sauri ta dau wayarta ta shiga kiran layin
gwaggwo, ta kira ya fi sau a kirga gwaggwo bata dauka ba, kowa kuma yasan gwaggwo
haka take da waya, Ammi ta shiga kiran Halima, bayan sun gaisa Ammi tace "Halima
Imaan ta je gidan ki?" Halima tace "Ehh ta xo daxu amma ai ta wuce" Ammi tace
"Karfe nawa ta bar gidan naki?" Halima tace "Shidda dai kamar yayi, lafiya Ammi?"
Ammi tace "Lafiya lau, Ina tace maki xata daga gidan naki?" Halima tace "Bata koma
gida bane Ammi?" Ammi tace "Tambayar ki nake" Halima tace "Tace kila ta wuce gida
ko kuma ta tafi wajen gwaggwo" Ammi tace "Toh sai anjima" daga haka ta katse wayar,
Gwaggwo ta sake kira har ya gama ring bata dauka ba, ta kuma kira nan ma haka,
ajiye wayar tayi ta fito, ganin Imaan bata parlor ta wuce dakinta, jin tana
bathroom Ammi ta tsaya, gaba daya hankalinta ya tashi sosai, Imaan na gama alwala
ta fito, sosai ta tsorata ganin Ammi, ta sunkuyar da kai a hankali tace "Ammi ba
komai fa" Ammi tace "Daga gidan Halima kin koma gidan gwaggwo ne?" Ta girgixa kai
tace "A'a" Ammi tayi kasa da murya tace "Toh ki gaya min me ya faru" cikin sanyin
murya tace "Ba komai fa Ammi, kawai dai kamar bana jin dadi ne" Ammi tace "Baki jin
dadi kuma?" Ta gyada kai, Ammi tace "Ina ke maki ciwo?" Ta girgixa kai tace "A'a ba
inda ke min ciwo, kawai dai bana jin dadi" shiru Ammi tayi tana kallonta, can tace
"Toh ki yi sllh ki fito yanxu" imaan ta gyada mata kai Ammi ta juya ta fita, har
Imaan ta idar da sllh ta kasa daina hawayen da bata san dalili ba, tayi kokarin
daina hawayen amma hakan ya faskara, har sannan she is just shock, fashewa tayi da
kuka a hankali, ta jinginar da kanta jikin gado. Ammi na idar da sllh tayi ta
jiranta ta fito amma shiru, hakan yasa ta mike ita ma gaba daya ta rasa me ke mata
dadi, gashi ta kara kiran gwaggwo bata dauka ba tasan wayar na can karkashin
pillow, A hankali ta bude kofar dakin ta ganta xaune kan darduma ta jinginar da kai
da gado tana bacci, Ammi ta karasa inda take ta duka ta kai hannu jikinta ta ji ba
xafi, Bude ido imaan tayi ganinta ta ja baya, Ammi na kallonta ta xauna gefen gadon
tace "Tell me what's wrong with you plss imaan" D'an murmushin karfin hali tayi
tace "Ammi ba komai fa, i am better now" Ammi ta dinga kallonta kafin tace "Toh
fito ki ci abinci" tashi tayi a hankali ta dauke pray mat din ta linke ta bi bayan
Ammi xuwa parlor, Ammi ta xuba mata abinci a kitchen ta kirata, Mikewa Imaan tayi
daga xaunen da tayi a parlor ta tafi kitchen ta amso abincinta ta dawo parlor ta
xauna, Sosai Ammi ke studying dinta tana cin abincin sai dai bata ce mata komai ba,
ganin xata je ta ajiye abincin da ko rabi bata ci ba Ammi tace "Dawo ki cinye
abincin nan" kamar xata yi kuka tace "Ammi ya min yawa" Ammi tace "Dawo ki cinye na
ce" babu yanda ta iya haka ta koma ta xauna tana tura abincin da kyar, har ta cinye
taje ta ajiye plate din a kitchen ta dawo parlor tana kallon Ammi tace "Ammi ina
son xan kwanta" Ammi tace "Ishan fa?" tace "Ba bacci xan yi ba kawai xan kunna
kallo a ciki" Ammi bata ce mata komai ba hakan yasa ta wuce daki Ammi ta bi ta da
ido har ta rufe kofa. Ammi dai na ta xaune parlor har takwas da rabi aka yi sallama
bakin kofa, amsawa tayi Mujaheed ya shigo parlon, Ammi na kallonsa tace "Sannu da
xuwa" Ya d'an yi murmushi ya xauna yace "Ina yini Ammi" Ammi tace "Lafiya lau, ya
gida" yace "Lafiya Alhmdllh" tace "kwana biyu?" Yace "Alhmdllh" Ammi na kallonsa
tace "Baka da lafiya ne" yar dariya yyi yana shafa kansa yace "Aa, am okay, me kika
ga" ta girgixa kai tace "A'a ba komai, a xubo maka abinci" yace "A'a Alhmdllh"
shiru yayi yana kallon movie da ake yi a tv, can ya kalli Ammi yace "Abba yace
Imaan ta je" Ammi tace "Ohk, tana ciki Ina jin ta kwanta, let me wake her" ya kalli
agogo sannan ya kalleta yace "Bata da lafiya ne?" Girgixa masa kai Ammi tayi tace
"She's ohk" Ammi na kallon kofar dakinta ta kwalo mata kira, ta kirata yyi sau uku
amma shiru, can Ammi ta mike ta tafi dakin, kwance ta ganta ta rufa da duvet, Ammi
ta karasa ta cire duvet din da sauri Imaan ta rufe idonta, da mamaki Ammi ke
kallonta tace "Imaan kina son in bata maki rai a gidan nan yau ko, baxa ki gaya min
meye damuwarki ba, wani abun ya faru ne baxa ki gaya min ba" Imaan taki yarda su
hada ido ta mike xaune tana goge guntun hawayen idonta a hankali tace "Ammi kiyi
hakuri ni nace maki ba komai fa" Ammi tace "Wani abun ya hada ki da gwaggwo ne"
Imaan tace "A'a ni ban ma dade a gidanta ba, Ammi it's just mood swings" Ammi tace
"Toh xan kira daddyn ki yanxu kuwa in gaya masa, don baxan yadda ki sa min ciwon
kai ba ina xamana, wannan ai walakanci ne, ke yarinya ce xaki xauna kina kuka ki ki
fadin matsalar ki kice min mood swings, ko iskancin ki na da ne xai dawo yanxu,
kuma ki tashi ki fita Abba na kiran ki...." Juyawa Ammi tayi rai bace ta fita a
dakin tana mamakin hali irin na Imaan, tasan ko da rufeta xata yi da duka ta dage a
kan sai ta gaya mata kukan me take to taurin kanta baxai taba bari ta fadi ba, ita
kanta taurin kan Imaan na damunta ne ba kadan ba, parlor ta koma ta xauna tana
kallon Mujaheed tace "I don't know what's wrong with her, tun daxu take kuka, na
tambayeta meye matsalar ta taki gaya min, kuma kukan na iskanci ne da jin dadi,
dama ranta a bace ta bar gidan tunda nace kar ta kwana inda xata je...." Mujaheed
na kallon Ammi yace "Kuka kuma" Bude kofar dakin Imaan tayi ta fito kanta a kasa,
Mujaheed ya dinga kallonta har ta karaso cikin parlon ta xauna kasa tace "Ina yini
Yaya" yace "Lafiya lau, what's wrong?" Kin cewa komai tayi, Ammi sai kallonta take,
can kuma dai ta tashi ta wuce daki, Imaan ta hade kai da gwiwa, ya mike ya dawo
kusa da ita ya durkusa yana dubanta yace "What happened imaan, an maki wani abu
ne?" Ta dago kanta ta wani turo baki tace "Ba komai" shiru yyi yana kallonta, can
yace "Tashi mu je Abba na kiran ki" Mikewa tayi shima ya tashi ya nufi kofa ta bi
bayansa. Sai da suka yi nisa ya juya yana kallonta da kyau yace "Baxa ki gaya min
kukan me kike ba" tace "It's just mood swings" Bata jira cewarsa ba tayi wucewarta
ya bi ta da ido, can dai ya bi bayanta, Xaunawa parlon Abba tayi bata yadda sun
hada ido ta Abban ba ta gaishesa ya amsa yace "What did you want for ur Qur'anic
graduation?" Shiru ta d'an yi, can tayi murmushin karfin hali tace "Abba kawai a
min abinda aka ma su Maimoon" yace "To maa Sha Allah, you can go" Mikewa tayi ta
masa sai da safe ta nufi kofa Mujaheed ya bi ta da ido har ta fita, wanka imaan
tayi bayan ta koma part din su, tana saka kayanta text ya shigo wayarta ta kalli
screen din, dauke kai tayi ganin Sadeeq ne ya turo sakon ta karasa shirinta ta bar
wayar nan gaban madubi ta kashe wutan dakin ta kwanta, ta jima bacci bai xo mata ba
sai juye juye take daga karshe dai baccin ya dauketa. Washegari Friday duk da ynda
imaan ta dinga jin ciwon kai haka ta shirya ta wuce islamiyya, karfe sha daya kuma
ta dawo gida, har sannan dai bata wani dawo normal ba don scene din abinda ya faru
jiya ya ki barin memory dinta da ya fado mata kuma sai gabanta yayi mugun faduwa,
sai dai tana ganin motar daddy a parking space alamar ya dawo taji dadi har ranta.
Tana fitowa wanka ta dau wayarta da ta boye a press ta bude, missed calls din
Sadeeq taga ni har uku da text biyu bayan na jiya da daddare da bata bude ba, ta ki
bude text din tayi lock din wayar ta mayar cikin press dinta ta gama shiryawa
sannan ta fito parlor, Tana murmushi ta karasa ta gaida Daddy da ya fito parlor,
daddy na kallonta yace "Lafiya lau Mamana, are you okay" ta buda ido tace "Sure
daddy, ya hanya?" Yace "Alhmdllh, ya shirin walima" tayi yar dariya tace "Daddy Ina
yi" Ammi dake jera ma Daddy abinci a dinning sae hararanta take, Daddy yace "Ga
tsaraban ki can Ammin ki ta sa maki a fridge" cike da jin dadi tace "Toh nagode
daddy"
Da yammacin ranan Imaan ta tafi kai ma Inna abinci, sallama tayi ta shiga parlon,
Daddy ne xaune parlon sae Kawu Bala, ga Umma ma xaune ta sha xumbulelen hijab kanta
a kasa, ga wasu kawunnanta har biyu su ma a parlon, Inna dai na xaune kan tabarma
tayi tagumi tana sharban kuka, ganin imaan ta shigo cikin rawar murya tace "Wllh
bata fi wannan yarinyar muka aurota ba Talle" imaan ta gaishesu ta ajiye abincin
hannunta ta fita.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

58.....

Daddy ne xaune parlon Inna bayan su kawu Bala, Umma da kawunnanta sun fita, Inna ta
tace "Wlh wllh Bukar ka ji rantsuwar musulmi ko, to Rukayya ta ci albarkacin ka ne,
don ina jin kunyan ka ainun, amma idan ta sake ko da min kallon banxa ne a gidan
nan to aurenta da Ahmaduna ya kare ba ruwana, xan nuna mata ni na haifesa ba wani
shegen ya haifa min shi ba, yanxu ma ni wllh darajar ka da na Mujaheed ta ci, tunda
ni nayi wahala da shi kuma yana min biyayya, kai ma kuma kana min biyayya, matar da
ma ba wai son matar ka take ba amma ka dinga tsayawa tsakanin ka da Allah kan
lamuranta, ita bata ki ba ma ta cutar da Aisha ba wllh, kai kuma duk ka damu da
lamarinta, duniya dai ba gaskiya" Shi dai daddy bai ce komai ba yana sauraranta,
tabe baki tayi ta mike tace "Ni dai ba ruwana, kawai mata ta wani taho min da
rubabbun mutane su ban hakuri, wllh ta ci albarkacin Mujaheed da sai na masu koran
kare ba kunyar kowa xan ji ba, ba ruwana, matar da ba tsoron Allah gareta ba balle
a raga mata" Daddy dai ya bi ta da kallo har ta shiga daki sai ga ta ta fito ta
xauna tana kallonsa tace "Kana ji na Bukar, ni dai duniyar nan kaf ba wanda bai san
imaan takwarata bace, kuma kowa yasan ita kenan Allah ya baka, ita kenan jikata a
wajen ka, Toh ya dai fi babu ai, sabili da haka gaskiya ni dai ga dubu ashirin dina
da nake ta tarawa a samo tikeken rago da ya kusa d'an mariki a yanka mata na saukan
nan, Allah kuma yasa na tsoron Allah xata yi, yayi mata albarka ya hada ta da
mijinta na gari wato wannan yaro Bulasawa...." Shiru Daddy yayi yana kallon kudin
da take mika masa, tace "Haba ka amsa mana yaro, ka bar min hannu a sagale" d'an
murmushi yayi yace "Amma Inna kin fa san ba ita kadai xata yi sauka a gidan nan ba"
tace "Toh ai shi sa nace takwarata" ya girgixa kai yace "Ai Ummi ma takwarar ki ce"
Bude Baki tace "Yau naga abinda ya isheni, ji Bukar da wani xance, to cewa nayi ban
sani ba, ai xuciya ma na son mai kyautata masa, Ummi ko gaisuwar kirki tana min a
gidan nan balle in dinga tuna cewa takwarata ce, ni dai ba ruwana a dinga jin
tsoron Allah, yanxu meye ma'anar hakan da kafada salon Ahmadu ya ji ya kullace ni,
ni dai gashi ka tafi bakin ka a leko ka siyo mata tikeken ragon da nace a kawo
mata" mikewa Daddy yyi yace "Toh Allah ya saka da alkhairi, sai anjima" tace "Toh
kai dai ka ja bakin ka kayi shiru, abinda naman ma duk xa a tsakura ma kowa da kowa
a gidan" shi dai daddy bai ce komai ba har ya fita. Washegari asabar da wuri aka
tashi a gidan aka fara girke girke, Ammi da Aunty ne ke girkin a nan bayan kitchen
din su Aunty, abinci kala uku xa suyi, sae soye soye, tun daren jiya dama Ammi tayi
samosa da spring rolls, Aunty kuma tayi cakes da doughnuts, Umma sai kai wa da
kawowa take kamar dai me neman abu fuska a daure, ta shiga ta fita, babu dai wanda
ta ce ma sannu da aiki cikinsu, su ma babu wanda ya kalleta, Maimoon ne da Ummi
suka shigo kitchen ko wanne sanye da Sabbin dinkin da Daddy yayi masu na atamfa
gaba daya su uku masu saukan har da imaan, da Hijab dinsu ash colour yana jan kasa,
sosai suka yi kyau, Aunty tace "kun yi kyau sosai, amma kuna kallon agogo dai koh"
Ammi tace "Allah ya sa ita wancan ta gama shiryawan" Maimoon tace "Shayi kawai xa
mu sha sai mu je mu kirata" Muryar Umma suka ji bakin kofar kitchen din tana kallon
Ummi cike da masifa tace "Kin wuce kin cire kayan nan na jikin ki ga lace can na
dinka maki ko sai na 6ata maki rai???" Ummi ta kalli atamfar jikinta sannan tace
"Lace umma?" Xagi umma ta kunduma mata tace "Don uwarki xo ki fita ki cire kayan
nan, ko ubanki ne yayi maki" Ummi ta nufi kofa ta fita, Ammi dai sai aikinta take,
Aunty ta tabe baki ita ma ta ci gaba da aikinta, tsaki Umma ta ja ta bar bakin
kofar kitchen din, Maimoon ta hada masu shayin cup biyu ta fita, karfe bakwai da
kusan rabi Imaan ta taho part din su Maimoon sanye da nata atamfar da well ironed
hijab dinta har kasa, sosai tayi kyau Aunty tace "Iyye daughter tayi kyau sosai,
amma ko yar powder baxa ki shafa ba Imaan" Yar dariya Imaan tayi ta gaida Aunty,
Aunty ta amsa tace "Ki tafi daki ki dau powder Maimoon ki shafa kin ji?" Tana
murmushi ta juya ta fita ta wuce sama, dakin su Maimoon ta shiga ta dau powder
dinta dake gaban mirror ta shafa, ta goga chappete a lips dinta mai two colour,
sosai tayi wani sanyayyen kyau kamar warce tayi wani kwalliya, juyawa tayi ta fita
dai dai fitowar Umma dakinta, Sosai gaban Imaan ya fadi ta sunkuyar da kai har xata
wuce maganan Sadeeq ya fado mata, a hankali tace "Ina kwana" Umma na mata shegen
kallo tace "Kin sa6a gaisheni a gidan nan ne ko kuma gulma da kinibibi irin na uwar
ki, to ko da mistake kika sake gaisheni a gidan nan wllh sai na gaura maki mari
munafuka kawai sauran ciwo" Ita dai Imaan bata ce komai ba ta dinga sauka stairs,
Umma ta bi ta da kallon tsana karara, har wani tafarfasa xuciyarta yake... Imaan
na komawa kitchen Aunty tace "Ba gashi kin kara kyau abin ki ba, don kana da kyau
kuma baxa ka kara da wanka ba" Imaan dai murmushi kawai tayi, Aunty tace "Kin dai
karya koh?" gyada mata kai tayi, Aunty tace "Toh maxa ki tafi suna jiran ki a mota,
sai mun xo in sha Allah" Imaan har ta nufi kofa ta juyo ta marairaice tace "Aunty
xa ku taho da Inna?" Aunty ta d'an yi dariya tace "Tabb, to ban dai sani ba, amma
kila mu taho tare" Ammi dai sai kallonta take ganin yanda ta rame kamar warce tayi
ciwo na sati daya, Imaan tayi masu sallama ta fita kitchen din, ta tadda su Maimoon
har sun shiga mota suna jiranta, ita ma ta shiga motar aka wuce da su islamiyyar
su, Imaan dai sai Muraja'ah take a xuciyarta har suka iso islamiyyar tasu, Da yake
islamiyyar sananne ne, kuma duk yawanci yaran masu shi sosai ne a makarantar, manya
manyan mutane ba na wasa ba ne suka halacci taron waliman saukan, ciki kuwa har da
'yan gidan Bulasawa gaba daya, da shi kan sa Bulasawan, duk da yaran second wife
dinsa kadai ke xuwa islamiyyar wato su Mariya da kanninta banda kannin Sadeeq don
su tasu islamiyyar daban, amma hakan bai hana Mahaifiyar Sadeeq xuwa wajen saukan
al-qur'anin ba, su Daddy da Abba da kawu Bala da Kanin Inna Audu d'an tsut kamar
yanda ta kirasa duk sun xo gun saukan su ma, Sai da dalibai uku suka yi karatu
sannan su Aunty da Ammi suka iso wajen, Imaan ta ji dadin ganin Amminta don ita ce
seventh xata yi karatu Mariya kuma ta shidda, Maimoon ta goma, Tunda Imaan ta hada
ido da Sadeeq dake wajen tare da mahaifinsa gabanta ya fadi bata sake yarda ta
kalli direction din da suke ba, lkci daya duk mood dinta gaba daya ya canxa har aka
xo kanta a karatun... And Sadeeq couldn't take his eyes off her even for a second,
both her tajweed and kira'ah were more than perfect, babu wanda bai mayar da
hankali kan karatun da imaan take na Surah Ad-dukhan ba.... Soo maa sha Allah, ta
kuma burge kowa na wajen, first 20 Aya ta karanta na suran, Nan take kuma Bulasawa
ya rubuta Check na 500 thousand ya mika ma Sadeeq dake kusa da shi yace "For her,
she recited very well" Sadeeq ya amsa yana kallon mahaifin nasa, ba Bulasawa kadai
ba, mutane biyu a wajen sai da suka ma Imaan kyauta, domin suran da ta karanta is
perfectly talking about Islam, and those are who passed all their times playing,
smoking, drinking, infact committing all such of sins, idan kuma Allah ya aiko da
Dukhan daga sama su nemi gafara su tuba, daga ya dakatar su koma gidan jiya, Sadeeq
ya mike ya je ya sami daya daga malamansu dake co-ordinating wajen ya mika masa
check din yace "Daga Alhaji Ahmad Bulasawa xuwa ga dalibar ku Fatima Abubakar
Imaan" Malamin ya amsa da jin dadi yana masa godiya yace "In sha Allah xai isa
gareta" Mujaheed bai iso gun saukan ba sai karfe sha daya tare da Safeenah da ta
cakare cikin tsadadden lace sai xuba kamshi take, Umma na ganinta ta dinga washe
baki tana mata sannu da xuwa, ta mike daga kujerar da take xaune tace "Xauna ga
kujerah Safeenah" Safeenah dake taunar cingam tace "A'a kiyi xaman ki Hajiya ga
wani kujera can bari in je in xauna" Mikewa Umma tayi da sauri ta dauko mata
kujeran tace "Gashi xauna" Safeenah ta ja kujerar duk da ido hudu da suka yi da
Ammi da Aunty dake wajajen a xaune dauke kai tayi ta xauna tana kas kas da cingam,
umma taji wani shegen dadi ganin abinda ta masu don sai murmushi take tace "In ji
dai gidan lafiya Safeenah?" Safeenah na juya ido tace "Qlau wllh Hajiya" Da yake
dalibai 20 ke saukan kafin karfe sha biyu da wani abu na rana duk suka gama
karatun, A nan kuma malaman suka yi announcing kyaututtukan da Fatima Abubakar ta
samu da wasu daga cikin daliban, tunda Imaan ta ji wai Bulasawa da kansa yayi mata
kyautan kudi gabanta ya dinga faduwa, Umma dake wajen kuwa da taji amount din gaba
daya hautsinewa cikinta yayi a wajen, ta kasa xaune waje daya sai mutsu mutsu take,
Aunty kuwa sai murna take tana sa albarka, Mujaheed ya dinga kallon Imaan da ta ki
yarda su hada ido da kowa, hotuna aka shiga yi a wajen, kowa hoto yake son yi da
Bulasawa dake kokarin ganin ya bar wajen, Mariya ta ja Imaan daga wajensu Aunty
tace "Come let snap with my family plss" haka Imaan ta dinga bin ta har suka isa
inda familyn Bulasawan ke tsaye, Mariya ta ja ta xuwa gun Babanta tace "Abba xa mu
yi hoto da ita, she is Fatima by name" Bulasawa na kallonta yyi murmushi yace "Maa
sha Allah, keep it up Fatima" ta sunkuyar da kai tace "Nagode Abba" Photographer
dake wajen ne ya dinga masu hoto, Sadeeq dake tsaye gefe yana kallonsu ya dawo
gefen mahaifin nasa, Imaan na ganin haka ta fara kokarin sulalewa Mariya taki bari
ta wuce har sai da aka masu hoton su hudu, gaba daya hankalin Umma na kansu kamar
idanuwanta xa su fito, ko fasa auren Mujaheed da Safeenah da aka kusan yi kwanaki
bai daga mata hankali kamar abinda ke faruwa yau ba, Wai Bulasawa da kansa yayi
acknowledging Imaan, duk Aunty na lura da ita, Mujaheed dai na xaune shi ma sai
kallonsu yake, Imaan suna gama hoto da Bulasawa ya bar wajen bayan ya bada donation
dinsa na progress din islamiyyar, hotuna Imaan suka dinga yi da Mahaifiyar Mariya
da kanninta, Mariya
ta ja ta xuwa gun Mahaifiyar Sadeeq tace "Mummy xa mu yi hoto" Mahaifiyar Sadeeq
na kallon Imaan da lovely smile tace "Ur recitation was sweet.. keep it up" Imaan
na murmushi tace "Thanks Ma" Tsayawa imaan tayi kusa da ita aka fara daukansu hota
tare da Mariya, Sadeeq dai bai daina kallon Imaan ba, har dai suka gama hoto da
family dinsa ta tafi gun su Aunty, nan ma suka dinga hoto da su Abba da Daddy,
Safeenah bata yarda ko da wasa suyi hoto da imaan ba haka ma Umma, duk suka ga
Imaan na wajen basa shiga hoton, Imaan da Maimoon suka yi hoto da ya Yusuf da wasu
daga frnds dinsa, shi dai Mujaheed na xaune yana danna wayarsa, Imaan na kallonsa
ta isa kusa da shi ta durkusa a hankali tace "Yaya baxa mu yi hoto ba?" Daga kai
yayi yana kallonta da manyan idanuwansa, ta turo baki ta kama hannunsa tace "Ni dai
ka taso mu yi hoto plss" Ya d'an yi murmushi yace "To kira photographer din mu yi a
nan" Tace "Noo, background din baxai yi kyau ba, ba ga flowers ba" Safeenah dake ta
kallonsu ta karaso wajen kamar xata tashi sama ta xauna kujeran dake kusa da na shi
har tana neman faduwa, Imaan na kallonta ta mike daga durkushen da take ta d'an
tabe baki ta juya, Ba Safeenah kadai ba har Umma kallonsu take tayi mitsi mitsi da
ido gashi ba daman yin komai ga Daddy da Abba a wajen, Mikewa Mujaheed yyi ya kamo
hannun Imaan yace "Toh let go" Umma tayi still inda take ta bi su da kallo, gun
flowers din suka nufa yana rike da hannunta, Mariya ya mika ma wayarsa duk da
photographer dake kokarin daukansu yace "plss snap with my phone also" Imaan dai
sai murmushi take, suna tsaye kusa da flowers din aka dinga kashe masu hoto kamar
xata shige jikinsa, Mariya ma na daukansu da wayarsa Mujaheed couldn't help it but
smiled sweetly, ta jinginar da kanta jikin shoulder dinsa tana murmushin ita ma,
Safeenah ji tayi kamar xuciyarta ta fashe, ga wani tukuki da take ji a ranta, Umma
dai sai murmushin karfin hali take tana gaisawa da jama'ah tana kallonsu ta gefen
ido, Aunty dai na ta rarraba ma jama'ah abincin da snacks da suka kawo bayan sun
ware na malamai da daliban saukan, Ammi kuma ta dinga raba buckets da books, Su kam
familyn Bulasawa nan suka bar komai da suka kawo na sauka tun daga abinci, gifts,
da dai sauransu suka yi wucewarsu, tashin hankali gun Sadeeq ganin har suka wuce
imaan ta ki ko da kallon inda yake ba a cewa komai, tun da yake bai taba shiga
tashin hankali na wannan lokacin ba tun daga jiya har xuwa yau, saukan ma banda
Aunt dinsa ta tilasta sa da baxai xo ba, hatta Mahaifiyarsa sai da ta tambayesa
damuwarsa gun saukan ganin gaba daya he is moody yace mata ba komai har dai suka
bar makarantar bai ga fuskar tunkarar Imaan ba, ya dai je sun gaisa da su Abba da
Daddy, sai su Aunty da Umma, sannan suka bar wajen da family dinsa, kafin azahar su
Imaan suka bar islamiyyar a various cars xuwa gida, Tun da islamiyyar ta manya ce
babu dalibi cikin masu saukan da ke da niyyar bin d'an uwansa dalibi gidansu kamar
dai yanda ake yi yawanci, kowa kama gabansa yayi xuwa gidan iyayensa, ni ko nace ko
dadi... Lol. Imaan da Maimoon motar Mujaheed suka shiga ta dalilin wayar Mujaheed
din dake hannun Imaan don ita Mariya ta mika ma da xa su wuce, Safeenah ta wani
hade rai xaune a gaban motar Mujaheed na driving har suka isa gida, yana gama
parking Imaan na kallonsa a hankali tace "Yaya ka tuna promise da ka min few years
back?" Ya juya ya kalleta, d'an murmushi yyi yace "Ban manta ba" tana murmushi ta
sauka motar, Maimoon ta mika masa wayarsa ita ma ta sauka, Mujaheed xai sauka
Safeenah ta rikosa fuska daure, juyawa yyi yana kallonta, tace "Ban ga fa'idar
xuwan mu gidan nan ba bayan an gama sauka, I think it's better mu wuce gidan mu
Doctor" Makullin motar ya jefa mata a cinya yace "Ki wuce gidan sai na xo, I don't
think u have the right to tell me what to do and what not to do" daga haka ya rufe
motar ya nufi part din su ta bi sa da kallo kamar idanuwanta xa su fito.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

59.....

Karfe biyu imaan ta fito daga bedroom dinta bayan tayi wanka ta canxa kaya xuwa
daya daga sabbin kayan da Daddy yayi mata har kala biyar na waliman, sosai lace din
ya amsheta, Ammi ta gama jera abinci kan lallausan carpet dake parlor, Tana
kallonta tace "Ga abincin ku ke da Daddy" Imaan ta karasa ta xauna kan carpet din
tana bude warmers din tana murmushi, Daddy ya fito daga daki ya karaso cikin parlon
ya xauna saman lallausan carpet din shi ma yana kallonta yace "I am proud of you
sweetheart" Dariya tayi tace "Daddy bayan ni ba ku ban gift ba kai da Ammi" yace
"Let lunch first" Plate ta dauka ta xuba masu abincin da daddyn nata, Ammi dai na
xaune parlon har suka gama cikin abincin, daddy na kallonta yace "Hope you will
also pass ur up coming exams with flying colors by the grace of God" Imaan tace
"Sure daddy" Daddy yace "Maa sha Allah" Makullin mota ya fiddo aljihunsa ya ajiye
kusa da ita yace "And this is my gift" Imaan ya wara ido ta dau makullin tana kallo
yace "A car?" Ammi dai sai kallonsu take, cike da jin dadi Imaan ta rungume Daddyn
nata tace "I love you Daddy, Allah ya bar min kai, ya kara girma" Murmushi yayi
yace "Ameen, gobe xa a taho da motar but you won't ride anytime soon, may be after
ur waec" Imaan da ta rasa inda xata sa kanta sbda murna tace "Toh daddy, Allah ya
kai mu, nagode Sweet dad, Allah ya saka maka da alkhairi" Yace "Ameen, clear this
plates now" Mikewa tayi ta kwashe duk warmers da plate din ta kai kitchen, ta fito
daga kitchen kenan aka danna bell, Mikewa Ammi tayi ta wuce dakinta, Imaan ta tafi
ta bude Kofar, still tayi ganin Sadeeq tsaye hannunsa rike da leda, sosai gabanta
ya fadi lkci daya ta juya da sauri ta bar bakin kofar Daddy na kallonta yace "Who's
there?" Kasa basa amsa tayi ta wuce dakinta, bayan few seconds Sadeeq ya shigo
parlon da sallama murya can kasa, Daddy na ganinsa yace "Welcome son" Sadeeq na
kirkiran murmushi ya karasa ya ajiye ledan hannunsa ya xauna kasa shi ma ya gaida
Daddy da ladabi, daddy ya amsa da fara'a yana tambayarsa ya mutan gidan, yace
"Alhmdllh Daddy" Ammi ce ta fito daki sanye da hijab, ganinsa ta sunkuyar da kai
tace "Sannun da xuwa" ya kalleta yace "Ina yini Ammi" tace "Lafiya lau, ya gidan?"
Yace "Alhmdllh, fatan an watse taro lafiya" Ammi tace "Alhmdllh, mun gode Allah"
dakin imaan ta nufa ta bude kofar ta shiga ciki, xaune ta ganta can karshen gado ta
wani hade rai, Ammi tace "Wa kika ce ma Sadeeq xai xo gidan nan?" Kamar xata yi
kuka tace "Ammi ni wllh ban sani ba kawai ganinsa nayi" Ammi tace "Toh sai ki tashi
ki tafi ki kai masa ruwa da drinks ki dibar masa snack" Ammi bata jira cewarta ba
ta fita dakin ta wuce nata, Mikewa Imaan tayi ta dau hijab dinta fari har kasa ta
saka sannan ta fito, ta wuce kitchen ta hada ruwa da drinks sai glass cup a tray,
ta debi snack a wani plate ta daura a kan tray din ta fito, kanta a kasa ta iso
parlon ta duka gefensa ta ajiye, Mikewa Daddy yayi ya dau wayarsa yana kallon
Sadeeq yace "Let me make a call outside" Sadeeq yace "Toh sai ka dawo daddy" daga
haka daddy ya fita parlon, Imaan xata tashi ya rike hijab dinta cike da damuwa
murya can kasa yace "Plss listen to me Imaan, don Allah ba don ni ba ki tsaya ki
saurareni, am begging you plss...." Kasa cewa komai tayi ta xaune wajen ta hade kai
da gwiwa ta fara kuka a hankali, duk ya rikice mata ya duka on his kneels yace "Don
Allah kiyi hakuri ki yafe min Imaan, it's a mistake that will neva repeat itself
again, don Allah ki min rai kiyi hakuri, I have neva for once had the intention of
making you angry" ita dai ta ki cewa komai kuma ta ki dago kanta bata kuma fasa
kukan da take a hankali ba, cikin sanyin murya yace "Kin ji Fatima, ki yafe min don
Allah, wllh bani da nufin cutar da ke, I love you with every breathe of mine, I am
wishing u to be the mother of my kids, ban taba ma ya mace irin son da nake maki
ba, I Neva knew what true love is sai a kan ki, ni ba fasiki bane Imaan you can ask
Mariya, sure I do flex with friends and I am a player, but i am very selective when
it comes to mingling with girls, and mind you... ni ba maxinaci bane I can swear to
you by Allah who made me ban taba ba, I am a type of person that find my opposite
gender so irritating in every aspect, don't forget where I was born and raised,
sure it's strongly against the teaching of our religion but kema kinsan to hug or
kiss someone is part of our lifestyle back there, a haka na taso cikin su, I tried
my very best getting rid of that while here in Nigeria kuma Alhmdllh there is
improvement, wllh Imaan ban maki haka da niyyar in cuce ki ko in 6ata ki ba, mata
ma dake kawo min kansu ban bata su ba sai ke da nake son aure? Kuma yanayin da nake
shiga idan muna tare is something that I have neva experience all my life, that's
why kika ga ko xuwa wajen ki bana son yi duk irin son ganin ki da nake I try my
best staying away from u, plss Imaan kiyi hakuri ki yafe min, sharrin shaidan ne,
don Allah ba don ni ba ki dago kanki ki kalleni in baki hakuri, na kuma maki
alkawarin daga this very moment har xuwa ranan da Allah xai sa a daura mana aure
idan ke matata ce baxan sake xuwa gidan ku ba, baxa kuma inyi requesting mu hadu
ba, xa dae mu dinga waya kawai...." sai a sannan ta dago kanta hawaye na xuba
idonta, lkci daya idonsa ya kada shi ma cikin sanyin murya yace "Don Allah kiyi
hakuri Imaan" a hankali tana goge idonta tace "Na ji?" Kamar xai mata kuka har lkcn
yana durkushe kan kneels dinsa yace "Kin hakura" a hankali ta gyada masa kai, yayi
murmushin karfin hali yace "Toh nagode Imaan, Allah maki albarka" sunkuyar da kanta
tayi, ya dauko ledan da ya shigo parlon da shi ya ajiye gabanta yace "This is for
you, I am very proud of you today, Allah ya baki ikon amfani da karatun ki" ta kasa
cewa komai, ya mike yace "Ki ce ma Ammi na wuce, thanks much for forgiving me" Bata
iya tace masa komai ba ya nufi kofa ta bi sa da kallo, yana bude kofa kafin ya fita
murya can kasa tace "Nagode" ya juya ya kalleta yayi murmushi sannan ya fita ya
kulle kofar parlon, Bude ledan tayi taga tsadaddun turarruka ne a cikin ledan har
kala biyar. Daren ranan Imaan na dawowa part din Inna ta je kai mata abinci suka
hadu da Mujaheed xa shi gun Innar, Ya katse wayar da yake yi yana kallonta, ta wara
ido tace "Yaya baka tafi ba?" Yace "Ehh wait for me a parking space yanxu xan fito"
tace "Parking space?" Yace "Ehh" tace "Tohm" wucewa tayi shi kuma ya karasa part
din Inna, Parking space din nasu ta tafi gun motarsa ta tsaya ta jingina jikin
motar, Bayan kusan minti bakwai sai gashi, yana kallonta yace "I saw ur video...
reciting, kinyi kokari kadan, they are still some corrections in ur tajweed, so ban
ma san amfanin kyautar da aka dinga baki ba, may be dai Muryar ki ne yayi masu
dadi" on a serious note ya kare maganar, xaro ido Imaan tayi tana kallonsa a
sanyaye, lkci daya ta bata fuska ta sunkuyar da kanta, ko kallonta bai yi ba yace
"Matsa in bude motata" a hankali ta matsa masa daga jikin motar ya bude, ta fara
tafiya xata koma part dinsu, bin ta yyi da ido yyi saurin jawota, kuka ta fara yi a
hankali, ya dawo kusa da ita yana murmushi yana kallonta gently yace "I was only
joking Lil sis, ur recitation was superb, I love it, and that was what I expected"
turo baki tayi tana kallonsa ya ja hancinta yana kallon eyeballs dinta murya can
kasa yace "My future kids will have no problem with recitation of the holy Qur'an"
Bai yi xaton xata ji abinda ya fada ba coz his voice was so low, as if he just
murmured the sentence, ya ga ta xaro ido tace "Ehh?? Ur future kids that their
mother is already hating me from day one" sai kuma tayi murmushi tace "Ba ruwana,
idan dai sun xo gida xan dinga koya masu in sha Allah..." Yyi murmushin sa mai kyau
yana shafa kansa yana kallonta, Jan hancinta yyi bai dai ce komai ba ya bude back
seat ya fiddo Laptop sabo dalll, ya mika mata yace "My promise 3 years ago" wara
ido tayi ta rungume sa tightly tace "Waow... Nagode yayana, I love ittt, you kept
to ur promise" Mujaheed ya ji gaba daya kafafuwansa sun kasa daukansa ya jingina da
motarsa ya lumshe ido and hold her closely to himself, Saketa Mujaheed yyi da sauri
jin an bude kofar apartment dinsu, Imaan ma ta ja baya tana kallon direction din,
Umma ce ta fito tare da Hajiya Saude xata rakata, imaan na ganinta dama ta bar
wajen da sauri ta dau hanyar apartment dinsu, Umma ce ta fara hangota sai kuma ta
fara kalle kallen parking space din don ganin ita da waye tana ganin Mujaheed ta bi
bayan imaan da mugun sauri Hajiya Saude na biye da ita, fixgota Umma tayi tace
"Uban me kike yi gun Mujaheed, me ya kawo ki wajen sa, meye wannan a hannun ki??"
Umma ta kwace laptop din tana xaro ido tace "Meye wannan din ya baki?" Mujaheed
dama na ganin haka ya taho gun su da sauri kafin imaan da ta wani 6ata fuska tana
kallon umma tace komai yace "Noo Bata aka yi as gift na walima shine ta ke nuna
min" Wani mugun kallo umma ta watsa masa tace "Take nuna maka kayi mata me, don
tana karuwanci an bata laptop kuma sai ta taho nuna maka?" Da mamaki yake kallon
Umma yace "Haba Umma, why all this" tsawa ta masa tace "Questioning dina kake yi?
Sharri nayi mata ba iskancin take ba, ai wllh ko qur'ani xan iya dafawa in rantse
iskanci take yi, ance maku a banxa yaron nan ke kashe mata kudi, ai kawai sai dai
Allah ya shirya mana xuri'a, amma sai ta kawo wani shegen laptop ta nuna maka kayi
uban me da shi??" Imaan dai kallon umma kawai take hawaye cike idonta, Hajiya Saude
ta karbi laptop din tace "Lallai kam Allah ya shirya mana xuri'a amma dama waye bai
san 'ya yan masu kudin nan ba" Mika ma imaan laptop din tayi tace "Karbi, Allah
kuma ya shirye ki" Imaan taki amsar laptop din hawaye ya cika idonta, Umma tace
"Sake mata tsiyarta mu wuce idan baxa ta amsa ba" daga haka umma ta wuce, Mujaheed
ya sa hannu ya amshi laptop din hannun Hajiya Saude, ta bi bayan umma tana kyabe
baki, Imaan ta fashe da kuka tana kallonsa, Bin uwar tasa yyi da kallo xuciyarsa na
tafarfasa shi ma,
har suka fita gate, kamo hannunta yayi ya wuce bayan apartment dinsu da ita suka
tsaya cikin lallashi yace "Stop those tears imaan, she only said that to please her
self, eraze her talk off ur mind now" shessheka ta fara yi, ya hade rai yace "Baxa
ki daina kukan ba" goge idonta ta fara yi, ya sa hannunsa yana share mata idanuwan
nata, murmushi yyi murya can kasa yace "You are taking ur pride to it rightful
place in sha Allah Lil sis" turo baki tayi, sai ta basa dariya ya ja hancinta a
hankali yace "My pretty stubborn Lil sis" ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba,
Mika mata laptop din yyi ta amsa yace "Yi wucewar ki ciki, on Sunday sai ku xo
gidana tare da Inna in baki sauran gift din ki" make kafada tayi tana turo baki,
yace "Why??" Ta wani hade rai tace "I dislike ur wife, I don't know.... I just
don't like her" kasa cewa komai yyi yana kallonta, can a hankali yace "But it's
also ur home, gidana ai naki ne" tace "Toh ai ita bata san haka ba, ko baka gaya
mata bane" Dariya sosai ta basa don sae da yyi, ta tabe baki tace "Ni dai bana
sonta kwata kwata" ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh ni xan xo in dauke ku da kai
na" imaan tace "Toh, kasan me Sadeeq ya bani" shiru yyi yana kallonta, lkci daya
mood dinsa ya canxa, can dai yace "Waye shi?" ta wara ido tace "Lahh baka san sa ba
Yaya? Toh ai shikenan, sai da safe" daga haka ta wuce da sauri tana murmushi ya bi
ta da ido. Har titi umma ta raka Hajiya Saude suna tafe suna hira, Hajiya Saude
tace "Toh ke kin dage tana karuwanci ta ya kika san haka" Umma tayi dariya tace "Ni
kuwa xan fi kowa sani, ae ki bari kawai in Allah ya yarda sai uwarta Aisha ta ji
kunya, sai ta gwammace a juyarta ta dauwama bata rufe bakin mutane da sauran ciwo
ba" Hajiya Saude tace "Toh Allah ubangiji ya tabbatar da hakan, amma fa kamar
Familyn Bulasawan ma naga sonta suke" Umma da taji ranta ya wani baci tace "Toh ae
baxa su so d'an su ya auri warce ya lalata a waje ba, kuma muna nan sai Imaan tayi
ciki a waje ba a dakinta ba" dariya sosai Hajiya Saude ke ta yi, Umma ta ja tsaki
tace "Baki san ni bane, wannan yaron shine ajalin ita da uwarta, ba sai wani rawan
kai suke uban ya mata kyautar rabin miliyan ba"

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

60....

Imaan na gyaran dakinta da safe misalin karfe tara bayan ta gama shiryawa Ammi ta
shigo dakin tana kallonta tace "Jira kike in xo in fito da ke Imaan" Imaan tace
"Yanxu xan fito" Fita Ammi tayi daga dakin Imaan ta bi bayanta ta shigo parlon tana
kallon Inna dake xaune ta cakare cikin atamfa da hijab tayi tagumi, Imaan ta dau
well ironed hijab dinta tana kallon Inna, Inna ta ki kallonta ta tabe tobaki tace
"ku dai ba ku da tsari, baku da kirki, tun jiya ince maki xamu fita amma saboda
walakanci ki bari in xo in xauna kamar gantalalla ina jiran ki..." Imaan tace "Ni
shayi kawai xan sha, kullum sai ki sa mu dinga xuwa gidan mutane da asuba basu
tashi ba ana mana walakanci" Inna ta xaro ido tace "Ni babu wanda ya taba walakanta
ni, ki ji tsoron Allah, Ba kuma ruwan ki idan ma tsakar dare xan je gidan mutane,
wllh ki daina haka ba halin xaman gidan miji bane..." Imaan bata tanka ta ba ta
wuce kitchen ta hado shayi ta dau bread ta fito, sai da ta ji ta koshi sannan ta
ajiye sauran bread din, Inna dai ta wani tsuke fuska, Imaan ta dawo parlon tace "Na
gama" tsaki Inna ta ja ta mike ta nufi kofa tace "Mutane dae ba tsoron Allah a
xuciyarsu, jiya mu yi magana rimi rimi ki dawo nan uwar ki tace kar ki shirya, to
ta ma kanta ae, dama bafillatani kuma, kai dai kayi ta fatan ku rabu lafiya da shi,
ni dae ba ruwana"
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

Ammi dai na goge gogenta a parlor bata ce komai ba, Imaan na kallon Ammi a hankali
tace "Ammi sae mun dawo" Ammi ta masu Allah ya kiyaye ta ci gaba da aikinta.
Adaidaita Imaan ta tsayar masu a bakin titi, Inna ta shige adaidaitan ta xauna,
Imaan na kallonsa tace "Kabala xaka kai mu" da mamaki Inna tace "Kaji jaraba ko
yaro, ina ruwanta ita dai ba kawai ta shigo ka ja adaidaitan ka ba" Yayi dariya
yace "Ae da gaskiyarta Kaka, gwara ta tambaya ta ji ko xan je" Imaan ta wani hade
rai ta shiga, Inna tace "Bata da wayo ne, ai ku din ba wai tsoron Allah gare ku ba,
da mutum ya tsaya gaya maku inda xa shi sai don mugunta ku fasa xuwa can din, shi
sa nake shigewa kawai abu na in xauna, Atoh... ina xan iya da gantalallu" Murmushi
kawai mai adaidaitan yake yi yace "Gaskiya ne Kaka" Dai dai kofar gidan Ta Rasulu
mai adaidaitan ya tsaya, Inna tace "Kaga gidan aminiyata ta Rasulu kenan na xo,
kuma babu irin motar da babu a gidan 'ya ya na, kawai dai nayi ra'ayin hawa
adaidaita ne, ka ga kuma ni tsohuwa ce sai an bani ba wai miji gareni ba, kai koma
da mijin yanxu shi ma ta kansa xai yi ya ji da tsufansa, don haka ni dai ba wata
mai kudi bane, har naira 30 an sha kawo ni gidan ta Rasulu shekaru kusan goma da
suka wuce wllh..." Tana magana tana duba jakarta ta fiddo naira 70 ta mika masa,
yace "Kaka kudin ku dari biyu da hamsin ne" Inna ta wani xaro ido tace "Kai barawo
ne d'an nan, a kan tsohuwa kuma satan naka xai kare yau sabida baka tsoron Allah??"
Tuni Imaan ta shige cikin gate din gidansu Ta Rasulu, tana shiga parlon ta Rasulu
ta fito dakinta da sauri tana cewa "Shegu dawowa ku ka yi marasa xuciya??" Ganin
Imaan ce tace "A'a ke kuma daga ina?" Imaan ta xauna ta gaisheta Ta Rasulu ta amsa
tace "Ca nake mayun yaran nan da na kora ne suka dawo, duk sun dameni watakil ma
iyayensu basu tashi ba, ni kuma sai aka ce masu an hallito ni ne don wahalan jikoki
ya kasheni, to ni ko su Muhammadu da..." Shigowar Inna yasa tayi shiru tana
kallonta tace "A'a ashe tare ku ke Asabe" Inna na nuna Imaan tace "Ke din nan baki
da kirki wllh, kina ganin mutumi xai fara ci min mutunci kan kudi kika gudu kika
bar ni daga ni sai raina, ban ga amfanin biyo ni da kika yi ba ma don wllh sai a
iya kama ni a nakada min shegen duka a titi kiyi tsit abun ki, wa xai maka haka
banda bare dama, ae Bukar baxae min haka ba" Ta Rasulu na kallon Imaan ta rike ha6a
tace "Gaskiya kam naka baxai maka haka ba dama, toh ya ku ka kare da mai mashin din
Asabe" Inna tace "Yan arxiki suka taso suka basa dari biyu a nan waje ni ban ma san
su ba, ni dai nace Allah ya isa don 70 nayi niyyar basa tunda ba a kasa ake hako
kudin ba" Imaan ta wani daure fuska kamar xata yi kuka, Ta Rasulu tace "Ae yanxu
yawanci duk barayi dake fashi da makamai a da ne suka koma aikin adaidaita, amma
dai ai gwara haka koh? Da ace suna shiga gidajen mutane" Inna tace "Wllh nima nayi
tunanin haka don har sai da na tambayesa ko barawo ne shi, kuma baki gansa ba
bakikirin malam, ni dai da kyar idan yyi Imani lokacin da yake ganiyar fashi da
makaman" Ta Rasulu ta shimfida mata tabarma tace "Tunda ku ka rabu lafiya ai
Alhmdllh, ya su Ahmadu da Bukar" Inna ta xauna tace "Ahmadu yana nan lafiya, Bukar
kuma yana can gun neman na kai, maganar da kika ce sai na xo xa mu yi jiya da rana,
wllh gaba daya hankalina ya kasa kwanciya ni dai ina idar da sllhn asuba na fara
aikace aikace na gama na sa ruwan xafi nayi wanka, na fito na shirya, na kada shayi
da burodi na sha sannan na fito, wannan mata dake xaune ita ta 6ata min lkci banda
haka da tun sassafe ma xa ki gan ni gidan nan" Ta Rasulu tace "A'a gwara da kika xo
dama, to ni dai naje na samu mutumi kamar yanda muka shirya, kuma ga maganganu dai
ba dadi wllh, wannan yarinya dai dake xaune gaskiya ido yayi katutu a kanta, da
matsala ba kadan ba...." Inna tayi kwafa da karfi tana gyada kai tace "Ya tsole
kuwa idon don ubansa, ko ma na wasu shegun ne, su rasa wanda xa su sa ma ido sai
Imaan? Tabb lallai lalacewa ta tabbata wai jikar Patuu xa a sa ma ido " Ta Rasulu
tace "Atohhh, ga dai shi nan ya bada icce da xa tayi ta wanka da kuma na sha, da na
hayaki, duk na sati guda kuma ku rufa min asiri ko da kuskure kada tayi tsallaken
kwana bata yi ba don ni ba wahalalliya bace, ba ku ji kafata da na dawo ba kamar
xan daddatse su in huta, ni banda ma ta ki ce Imaan din ina ruwana da lamarinta,
tunda muke da uwarta ina ga in dai ta tako gidan nan to Asiya ce ta haihu, to ina
dalili, kawai albarkacin ki nake wannan wahalan, sannan abun tsoro da tashin
hankali fa ce min yayi na kusa da ita sosai ne ke son ganin ya tarwatsa rayuwarta,
ke kya yarda Asabe?? Wllh kar ki bari tayi wasa da Magungunan nan...." Inna tayi
tagumi tace "Amma dai me yasa yanxu ba a tsoron Allah ne ta Rasulu, mu xamanin mu
duk inda ka bi tsoron Allah ake kaca kaca ba wasa, kowa ya saka Allah a rai, yanxu
ko tsoron Allah yayi karanci, to ko dai gun aikinsa ne aka sa ma 'yar sa ido ince
ya hakura da aikin ya dawo mu xauna Allah xai rufa asiri??" Tsaki ta Rasulu tayi
tace "Ka ji ki da rikicin tsufa, ce maki aka yi fa na jikin ku ne ke son cutar da
ita" Inna tace "Ehh lallai xai cutar da kansa kuwa koma waye, xai san jikata yake
nufin cutar wa, to yanxu dai abinda xai faru yanxu shine... Kowa dai yasan ni yar
gaskiya ce sabili da haka baxan yi abinda bai kamata ba, shiryawa kawai xa mu yi ni
da ke mu koma wajen, in sha Allahu ko nawa ne ni xan biya a mayar da nufin sharrin
da ake ma jikata kan 'ya yan masu bin ta da sharrin, ba shkkn ba??" Ta Rasulu tace
"Haka ma xa ayi, yanxu dai bayan kwana biyu ki taho ki kwana nan don da asuba xa mu
fita amma gaskiya sai dai mu sami karyar da xan gilla ma Asiya da mijinta don sun
ce in daina jajibe jajibe, ni ko jajibe jajiben da nake na neman lafiyata ne da na
jikokina da na 'ya ya na, yanxu abinda duniyar baki daya ba gaskiya wa xai xauna,
bana bi ta nasu ba basu san komai ba su yara ne" Inna tace "Ai ki kyale yaran yanxu
mun dai haifesu ne bamu haifi halinsu ba, nima dai kafin in fito sai na gilla ma
Ahmadu karyar don ba lallai ya yarda ma in taho ba" Ta Rasulu tace "Atoh, wa xai
xauna" ita dai Imaan na xaune fuska daure sai kallon Tv take, inna bata bar gidan
ta Rasulu ba sai kusan karfe sha biyu, Ta Rasulu ta dauko naira Hamsin ta bata wai
su hau mota, Inna ta tabe baki tace "Da dai ba masu fashi da makamai suka koma yin
d'an sahun ba, ba ruwana ajiye gantalalliyar hamsin din ki ina da dari xan
lallabasa ya kai mu gida" Sabulun wanki kwaya daya ta Rasulu ta dauko ta mika ma
Imaan tace "Ga shi kya wanke 'yan kampai, ni dai bani da komai dakin duk maroka sun
xo na kwashe masu komai, gashi wata bai kare ba" Imaan ta amsa tace "Nagode" har
bakin titi ta Rasulu ta rakasu Inna na rike ledan Magungunan hannu bibbiyu tsabar
muhimmanci da ta basu, Ta Rasulu ta tsayar da adaidaita tace "Kai yaro nan nan
malali xa ka kai su, kaga dai ba miji gareta ba ya rasu, nawa xa ka kai ta?"
Mutumin yace "Dari uku Kaka" ta Rasulu ta buga adaidaitan tace "Toh je ka, mu ma
neman dari ukun muke kuma ba mu ta6a fashi da makamai ba mu dai" Mai adaidaitan na
dariya yace "Nawa xa ku bada Kaka?" Inna tace "To ko dai ya kai ni gidan Mujaheed
kawai, tun da ya tare sau daya naje gidan" Ta Rasulu tace "Toh shiga, ko nawa ne
Mujaheed din xai bada" Inna ta shiga tana kallon Imaan da tace "Ni gida xan wuce"
Inna ta kalli ta Rasulu tace "Kinga jarababba ko??" Ta Rasulu tace "Dalla shiga ku
je, duk saboda ke tsohuwar nan babu kokarin da bata yi amma baki gani, indan ta
uwarki ce ai sai dai a kashe ki mu taho muna kuka" Imaan ta shiga adaidaitan kamar
xata yi kuka, ta Rasulu ta juya tayi wucewarta, wani gidan mai me adaidaitan ya
shiga xai sha mai yana ba Inna hakurin xai siya fuel, Inna tace "Na Bulasawa ne?"
Yace "Ehh nasa ne" Inna ta washe baki tana kallon wagegen filling station din tace
"Ai d'a na ne wllh" da sauri mai adaidaitan ya juya yana kallonta, tana nuna masa
Imaan tace "Kaga surkarsa kenan, kuma jikata ce ni na haifi ubanta, ita kadai
garesa duniya" Mai adaidaitan yace "Allahu Akbar" Inna tace "Kai da kasan Allah
kenan yaro" dariya ya fara yi sosai, imaan dai gaba daya abin duniya ya isheta,
kamar ance ta kalli gefenta taga Sadeeq coming toward d tricycle, suna hada ido ya
sakar mata lallausan murmushi, sosai ta ga ya rame, ta sunkuyar da kanta da sauri,
ya iso kusa da napep din ya xaga gun Inna da fara'a yace "Kaka ina xuwa haka?"
Salati Inna ta saki tana kallonsa ta kalli mai napep tace "Toh ka gansa nan, ubansa
ne mai gidan man nan" Mai napep ya kalli Sadeeq da sauri, ya washe baki yace "Ai ko
ga kama" Inna tace "Atohh, ya xo checking ne da yake yau lahadi, kasan cuta tayi
yawa duniya yanxu" Sadeeq na murmushi ya gaisheta da ladabi ta amsa baki har kunne
tace "Wai gidan Mujaheed xai kai mu, Ashe gantalallen mashin din nasa ba mai shine
ya shigo xa mu siya" Sadeeq yace "Toh ku sakko in kai ku ga motata can" Inna fito
kamar jira take ta nufi motar ba tare da ta bi kan d'an sahu ba, Imaan ta bi ta da
kallo taji kamar ta nutse kasa, Sadeeq dai sai murmushi yake, yana kallon mai
adaidaitan ya ciro dubu biyu ya mika masa, karba yayi yana masa godiya, a hankali
Sadeeq na kallon Imaan yace "Come down plss, there is nothing to worry about"
sakkowa tayi daga napep din, ya nufi motarsa ta bi bayansa, Inna har ta shige baya
ta xauna, imaan na hararanta ta bude front seat ta shiga, har suka isa gidan
Mujaheed Imaan bata ce komai ba a motar, Inna ce dai ke hira da Sadeeq tana nuna
masa hanya, xai yi parking a waje tace "A'a danna hann, xa su bude maka" Sadeeq
yace "A'a Kaka ai ba kowa ke son a shiga gidan sa ba...." Inna tace "Ka ji ka
Bukar, gidan Mujaheed ne fa" murmushi kawai yayi ta bude motar tace "Kuma da
gaskiyar ka, don ba ko yaushe Mujaheed ke da kirki ba" Imaan na kallon Sadeeq tace
"We will talk later, thank you" Yana murmushi yace "I am happy I saw u after few
weeks" murmushi tayi masa, yace "Yaushe xa ku koma sai in dawo in dauke ku?" Tace
"Xa mu dai yi waya" yace "Toh shkkn, thanks
love" fita tayi ta bi bayan Inna, ya bi ta da kallo har ta shiga cikin gidan,
Imaan bata ko kalli Inna dake tsaye tana magana da mai gadi ba ta nufi entrance din
gidan ta murda kofa ta bude ta shiga cikin parlon da sallama murya can ciki,
Mujaheed ne xaune parlon yana operating laptop tare da Safeenah da ta makalkale
jikinsa kamar xa su dawo daya yana shafa dogon gashinta... Lkci daya Imaan ta juya
masu baya a hankali, sai kuma ta fice daga parlon, Inna dake tahowa tace "Basa nan
ne?" Imaan dai bata ce komai ba.

*Thanks for the prayers everyone, nagode kwarai, ga dai ni a garin wasu ko dadi,
lol*

*Imaan isn't for free* it's 300 via


Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

61

Mikewa Mujaheed yyi da sauri ya wuce sama, Safeenah ta wani tabe baki ta ki tashi
sai ma kwanciyarta da tayi kan kujerar, Inna na kallon Imaan da ke tsaye tana
kallonta tace "Lafiya kika fito ko basa nan ne?" A hankali Imaan tace "Nima ban
sani ba" Inna ta kutsa kai ta shiga parlon tace "Ina kuma xa su ranan lahadi su bar
kofa ba makulli kamar tababbu, ko dai baccin asaran suke..." Suna hada ido da
Safeenah dake kwance Inna tace "A'a Safara'u, to tace min ba kowa, anya Imaan na da
lafiya ma kuwa, Ina Mujaheed din?" Safeenah ta mike tana kirkiran murmushi tace
"Sannu da xuwa Inna" Inna ta xauna tace "Yauwa sannu Safara'u, ana ta shan iska
kenan, to ba kya sha ba gari duk xafi don ma dai akwai Ac, ai nima idan naji xafin
yayi yawa dama daga ni sai yar shimi da xani nake xama na parlor, kar xafi yyi min
illa..." Mujaheed ne ya dawo parlon sanye da jallabiya milk color kansa a kasa,
Inna na kallonsa ta washe baki tace "Ina kwana Mujaheed" ya karaso ya xauna yana
dube duben parlon yace "Ina kwana" tace "Lafiya lau, yau ba aikin kenan" Yace "Sai
da yamma" tace "Toh ai jiki da jini, in gaya maka daga gidan ta Rasulu nake mun je
mun yi sirrin mu shine nace bari in biyo mu gaisa kafin mu koma gida" magana take
masa amma gaba daya hankalinsa na kan kofa, Inna tace "Sai kuma wannan yarinyar
tace min baku nan, kai kaji walakanci..." Bata rufe baki ba kamar jira yake yace
"Tana Ina??" Inna tace "Oho ni dai ba na shigo ba, dama tun da muka fito take min
walakanci tana ganin mai adaidaita xai min rashin kirki ta gudu ta bar mu..."
Mujaheed bai ce mata komai ba ya mike ya nufi kofa Safeenah ta bi sa da kallon
gefen ido, Bai ga Imaan a waje ba ya karasa gate yana kallon mai gadi yace "Warce
suka shigo yanxu da kaka ta fita ne?" Yace "Ehh ta fita" Mujaheed ya fita gate din,
can ya hangota har ta kusa titi, ya fi minti daya tsaye yana kallonta kafin ya juya
a hankali ya koma cikin gidan, Inna na kallonsa tace "Ta ki shigowa ne halan? Rabu
da ita ban iya wahala ni dai ai ta aan hanya" Bai ce mata komai ba ya wuce sama
Safeenah da ta wani daure fuska ta bi sa da wani kallo. Bayan kusan minti talatin
Mujaheed ya sakko downstairs sanye cikin kananun kaya hannunsa rike da makullin
mota, Inna na xauna ga plate din farfesun kaji gabanta tana ta yaga tana ma
Safeenah hira, Safeenah dai na xaune sai kallonta take uninterested, Inna na kallon
Mujaheed tace "Ina kuma xa ka?" Yace "Ba dadewa xan yi ba...." Daga haka ya fita
parlon, da sauri Safeenah ta mike ta dau Hijab ta bi bayansa, Inna na cewa "Maxa je
ki ku yi sallama" Har ya shiga mota Safeenah ta samesa cike da shagwaba tace "Ina
kuma xuwa sweetheart, bayan ka min alkawarin baxa ka fita ba yau" Ya tada motar ba
tare da ya kalleta ba yace "Ba jimawa xan yi ba" Tace "Ohk then, bari in raka ka"
sai a sannan ya kalleta yace "I don't think it's necessary Safeenah" da wani
expression take kallonsa, yace "Forget about the previous plan on what to cook,
tunda grandma na nan kiyi tuwo kawai with vegetable soup, I will be back soon" tana
masa wani kallo bluntly tace "Wllh baxan yi ba, sai ka taho da tuwon daga inda xaka
yanxu..." shi dai ba kulata ba ya rufe motarsa ya gama warming mota ya danna horn
mai gadi ya bude masa ya fita. Mujaheed na isa gida yyi parking a waje, ya shiga
compound dinsu, tun da ya shiga yake kallon part din su Imaan, gently yake tafiya,
ya kalli apartment dinsu sannan ya wuce, yana isa part din su Imaan ya danna bell,
sai kuma ya bude kofar yyi sallama ya shiga, Ammi ta leko daga kitchen taga ko
wanene, gaisheta yyi ta amsa tana welcoming dinsa ta fito, Bai xauna ba yace "Dama
kawai na shigo mu gaisa ne" tace "Toh nagode, ya gida?" Yace "Alhmdllh" tace "Maa
sha Allah" ba tare da ya kalleta ba yace "Imaan na ciki ne?" Tace "A'a" da sauri ya
juya yana kallonta, tace "Yanxu na aiketa taje kai ma Aunty sako" Bai san lkcn da
ya sauke ajiyar xuciya ba yace "Toh, sai anjima" tace "Allah ya bamu alkhairi" fita
yyi parlon ya wuce part din su, Umma na xaune parlor da Rahma suna magana kasa
kasa, Umma na kallonsa da murmushi tace "A'a sannu da xuwa Mujaheed, yanxu ko nake
cewa bari driver ya dawo xa mu je can gidan Hajiya Balaraba daga nan sai mu biya
naka, tunda ku ka tare ban je ba" ya xauna ya gaisheta ta amsa tace "Toh ina
Safeenar?" Ya mike yace "Tana gida tace a gaishe ku" Umma ta bi sa da kallo ganin
sama xai wuce tace "Ina kuma xaka?" Yace "Xan dau wasu takardu a daki" Daga haka ya
haura sama, murya can kasa Rahma tace "Ita fa Mariyan ma ba kowa take kulawa ba
wllh Umma, bari dai Ummi ta dawo ki ji, ai ajinsu daya har schl" Umma tace "Toh ita
Imaan din ta ta6a xuwa gidansu Mariyan ne?" Rahma tace "Suna xuwa da Maimoon sosai
ma" Umma tace "Atoh, Da bata xuwa ai baxa su santa ba har su mata kyauta gun sauka,
har fa da yin hoto da uwar yaron da kishiyarta" Rahma tace "Imaan da bata kula maza
amma saboda taga d'an mai kudi ne she didn't think twice kafin ta fara kulasa, kila
ma a gidan nasu suka hadu" Umma tayi wani murmushi, murya can kasa tace "Toh xa ki
yi abinda nace maki din?" Rahma tace "Toh umma ai ba shiri muke da ita ba fa, gwara
ma Ummi" Umma tace "Toh yanxu ai xata dawo..." Dakin Aunty Mujaheed ya bude yana
kallon ciki, Maimoon ce xauna kasa kusa da Aunty dake xaune kan stool tana mata
kitso, Imaan kuma na xaune kasan rug tana kallonsu, Imaan na ganinsa tayi saurin
dauke kai, ya shiga ya rufe kofa idonsa a kanta, Maimoon ta gaishesa ya amsa, Aunty
ta sake kitson da take tace "Welcome son" Mikewa Imaan tayi tace "Toh Aunty ni xan
wuce" Aunty tace "Au kin fasa kitson kenan, dama nasan baxa ki yi ba, kice ma Ammi
xan shigo nan da anjima" Imaan dake murmushi don ita kanta tasan kawai dai tace
Aunty ta mata kitson ne amma ba yi xata yi ba, lokaci daya murmushin fuskarta yyi
fading ganin Mujaheed ya fita dakin, tana ganin haka ta hade rai ta koma ta xauna
tace "Toh tunda xa ki je shikenan, sai mu koma tare" Aunty tace "Toh shkkn"
Mujaheed ya fi minti biyu tsaye corridor ganin bata fito ba ya bude kofar dakin,
Aunty tace "Yau dai yan miskilancin na kusa ne ko doctor, Ina yini toh?" D'an
murmushi yyi yace "Ina kwana Aunty?" Tace "Atoh, ka shigo Ina welcoming dinka kayi
kamar baka ji ba kuma ka fita" ya shafa kai a hankali yace "An kira ni ne a waya na
fita" Aunty tace "Ohk, ya amarya?" Yace "Tana gaishe ku" Aunty tace "Toh muna
amsawa" duk irin yanda ya kafe imaan da ido bata yarda ta kalli direction dinsa ba,
har ya juya ya fita, Imaan bata bar part din Aunty ba sai da ta gama ma Maimoon
kitso suka koma part din su tare da Auntyn, har sannan kuma Mujaheed na xaune
parlor, ya bi su da ido har suka fita Imaan ta saci kallonsa suka hada ido da sauri
ta dauke kai ta shige gaban Aunty tana turo baki. Daren ranan Imaan na part din
Inna suna dakinta, Inna sai famar rura wutan dake kasko take da baki, Imaan kuma na
tsaye kamar xata yi kuka, Inna ta ajiye wutan tace "Ke dai ki daina haka imaan, ni
wllh idan kina bani wahala xan tattara lamarin ki in xubar a kwandon shara, ya xa
ki dinga ban wahala ina taimakon ki? Baxa ki cire kayan ba ki xo ki durkusa, kai
wllh Bukar dai ya haifi jaraba" Imaan tace "Toh wai ni kin manta bana son hayaki
ne, yanxu idan asthma dina ya tashi fa?" Inna tace "Meye kuma asma? Kiyi ta kira ma
kanki ciwo, Ke dai ki ji tsoron Allah, abinda nace d'an minini xan yarfa a wutan ki
shaka ko kadan ne sai ki fita da gudu, idan fa aka kashe ki ko digon hawaye na
baxan yi asara ba wllh" Imaan ta rungume hannu tace "Wllh bana so ni dai, gwara
inyi wanka da shi, haka kawai inje asthma na ya tashi inyi ta wahala" Inna tayi
tagumi tace "Kai ina shan wahala ni patuu, ni dai ba don ki kadai Allah ya halitto
ni ba wllh" tana fadin haka ta mike ta dau kullin magani ta wuce bayi tana cewa
"Sai ki cire kayan, idan ya kama ma in cuda maki maganin da kai na sai in cuda maki
baxan yi asaran kudi ne a banxa ba" Imaan na turo baki ta fara cire rigar jikinta,
tana cikin cire skirt taji an bude kofar dakin, xaro ido tayi ta fasa ihu ta
durkusa a kasa, da gudu Inna ta fito tana cewa "Shikenan ta fada cikin garwashi ta
kai ni ta 6aro gun Bukar...." Inna ta gwalo ido ta kalleta ta kalli garwashin wutar
don ta tabbatar bata fada ciki ba, Inna na nunata tace "Anya imaan xaki wanye
lafiya da duniya kuwa??" Imaan da ta takure gu daya tace "Ni dai Inna wllh kice
masa ya fita" da sauri Inna ta kalli kofa ganin Mujaheed tsaye ta xaro ido tace "Me
xan gani haka?? Kai ya haka xaka afko mana daki ba sallama, baka ganta a tu6e bane
Mujaheed, yaushe ka xama haka?" Shi dai bai ce mata komai ba ya juya ya fita, Inna
ta tafe hannu tace "Yau naga abinda ya isheni, toh tsaye ya gan ki da ya shigo?"
Kamar xata yi kuka ta gyada masa kai, Inna tace "Toh shi ya ga duhu wllh, tashi ki
shiga kiyi wankan ki, shi yaga duhu" Imaan ta mike ta dau towel ta daura tana turo
baki ta wuce bathroom, Inna tace "Kaji min gantalalle, Toh wani salon iskanci ne
wannan xai shigo maki daki kin tu6e?? Ni dai ba ruwana, don mutum yyi aure kuma sai
ya fiddo da fi'ilin iskanci iri iri, Toh wllh shi ya ga duhu" Tana fadin haka ta sa
makulli a kofar tace "Ba ruwana" Tun daga wannan rana da imaan ta ga Mujaheed xata
canxa hanya ta wani daure fuska..... Inna na parlor ta daura kafa daya kan daya da
yamma tana kallon wani film Ummi ma na parlon ta gama mata kitso kenan, Inna sai
tsine ma boss din film din da suke kallo take, duk ta cika parlon da muryarta, Ummi
sai dariya take tana cin soyayyen nama da Inna ta yarfa mata a plate, sallama aka
yi bakin kofa Inna ta amsa tana kallon kofar, Sadeeq ne ya shigo da leda a
hannunsa, Inna ta mike da sauri tace "A'ahh sannu da xuwa Bukar, kai ne da yamma
haka, Bisimillah" ya karaso yana murmushi ya xauna, Inna tace "Ya iyayen naka?" Ya
xauna yace "Alhmdllh, suna gaishe ku" Inna tace "Tohh ina amsawa wllh, Ummi tashi
ki debo masa ruwa a fridge da lemo, idan kuma baxa ki ba in tashi" Ummi dake
kallonsa ta gefen ido ta mike ta nufi kitchen, ba a dau lkci ba ta dawo ta ajiye
masa tray din drink da
ruwa ya kalleta yace "Nagode" Ummi ta koma ta xauna tana kallonsa, Inna na kallon
Ummi tace "Toh kiyi wucewar ki ai mun gama kitson ko? Allah maki albarka" Ummi ta
wani hade rai sai kuma ta mike ta nufi kofa, ko ba a gaya ma Sadeeq ba yasan kanwar
Mujaheed ce don kamar da suke ba na wasa bane, Inna ta tabe baki bayan ta fita tace
"Toh sai ta wani xauna cikin manya, ai bai dace ba" Sadeeq na shafa kai yana
murmushi yace "Dama Ina son xa mu yi magana ne Kaka" Inna ta gyara xama tace "Toh
Bismillah, Ina jin ka Bukar in ji dai lafiya" Yace "Lafiya lau, dama Kaka Abbana ne
ke min maganar aure tun da dadewa, na gaya masa yanda muka yi da ku a nan yana
ganin kamar kawai xance nake masa...." Inna ta katse sa tace "Aa ba xance kake masa
ba wllh su Ahmadu ne suka dakatar da kai, toh amma ni dama faduwa ta xo dai dai da
xama, ba ruwana yau xan kira Ahmadun a gama magana, in sha Allah xuwa nan da
Juma'ah ko lahadi xai ce ka turo magabatan ka, kwantar da hankalin ka Bukar in
Allah ya yarda komai ya xo karshe, Sakandari?? An dade ba ayi sa ba in har xancen
sakandarin xa su kara min, ni ba karamin aikina bane in tura ku kano gidan kawu
Salisu ku kai gaisuwan da sadaki can" ya d'an yi murmushi, tace "Allah ba batun
dariya ba, ai idan muka ci gaba da biye su Ahmadu da Bukar sai mu yi sa6o mu
hallaka, haka kawai su ja mana fushin ubangiji kiri kiri suna fiffita abun duniya
kan sunnar ma'aiki" a hankali Sadeeq yace "Toh nagode Kaka Allah ya kara girma"
Inna tace "Atohh, duk ya ake ciki xuwa gobe xan kira ka kaji" Yace "Toh xan koma
kaka" tace "Toh Allah maka albarka" ya ajiye mata ledan hannunsa yace "Ga turare na
kawo maki Kaka" Inna tace "Kamar kasan bbu komai dakina sai fankon gwangwanayen
turaren na jera gaban madubi" Yar dariya yyi ya nufi kofa ya bude, da sauri Ummi ta
ja baya, sai kuma ta fara tafiya ko takalmi bata tsaya sa wa ba, Sadeeq ya bi ta da
kallon mamaki bai dai ce komai ba ya fita ya sa takalmansa ya wuce, A gate ya kusa
cin karo da Imaan xata shigo compound din hannunta rike da pack din bottle water,
ta koma baya da sauri, ya wara ido ya fito murya can kasa yace "Baby" Ta sunkuyar
da kai tace "Ina yini?" yace "Lafiya lau, where are u coming from?" Tace "Na je
siyo ruwana ne" yace "Iyye bottle water kike sha kenan" murmushi tayi bata ce komai
ba, yace "Toh kawo in taya ki kai wa ciki" ta girgixa kai da sauri tace "A'a
nagode" Bata fuska yyi yace "Plss let me help" Bai jira cewarta ba ya kai hannu xai
amshi ruwan, hannunsa na ta6a nata ta sake ruwan ba shiri, shima kuma da sauri ya
janye hannunsa ruwan ya fadi kasa, dukawa yyi ya dauka yace "Ohh Subhanallah, sorry
plss" Murmushin karfin hali tayi ta shiga gidan ya bi bayanta, Xaune Imaan taga
Umma da Ummi kan fararen kujera a can Balcony dinsu Umma ta bata attention gaba
daya, Imaan ta dauke kai da sauri, shima Sadeeq hakan yyi har suka isa part din su
Imaan, imaan na kallonsa tace "When did you come?" Yace "Some minutes ago, am tired
Imaan na xo na sami grandma ne plss a ban ixinin in turo magabatana ko ba yanxu xa
ayi biki ba..." ita dai Imaan bata ce komai ba, ya ajiye ruwan hannunsa a kasa, ta
duka ta dauka tace "Toh nagode sai mun yi waya" daga haka ta wuce ciki, ya bi ta da
kallo sannan ya wuce yana murmushi. Abba ne xaune parlon Inna tare da Mujaheed da
xuwansa gidan kenan, har Inna ta kai aya a xancen da take Mujaheed sai kallonta
kawai yake, Abba dai kansa na kasa, can Abba ya daga kai ya kalleta bayan tayi
shiru yace "Toh ai jarabawan ma saura wata daya da sati biyu in sha Allah Inna"
Inna tace "Ku kuka jiyo wannan kuma ni ina ruwana, ya xa ku dinga maida ni karamar
mutum gaban yaron nan, gaskiya wannan karan bana son magana da yawa sabili da kar
raina ya baci, ga abinda nace in dai kuna tsoron Ubangijin ku, meye kuma wata daya
da rabi Ahmadu? Shi auren ake gudu kuma yanxu ana rirrike boko hannu biyu, Me yasa
ku ke haka?? Ni dai idan na isa da ku gwara a hada bikin ma da na wannan yaron
Isuhu tunda an ma kusa kai sadakinsa" Mujaheed dake kallonta har sannan yace "Don
dai an jira wata daya da kwanaki ban ga wani damuwa ba, hanxarin me yake??" Inna
tace "Amma gaskiya idan xan yi maganar arxiki Mujaheed ya daina shigo min parlona,
a daina xuwa min da shi" wani kallo Mujaheed ya dinga mata, tana kallon Abba da
karfi tace "d'an bakin ciki ne fa Ahmadu, ya xai yi aurensa yaje can yana morewa
da figaggiyar matar sa amma ya dinga yi ma yar Uwarsa bakin ciki, haka yake so tayi
ta xama a gida kamar ba mashinshini?" Mikewa Abba yayi yace "Toh shkkn, xa mu ba
yaron ranan da xai turo magabatan nasa in sha Allah" a fusace Inna tace "Yaushe?"
Abba yace "Nan da ko kwana uku in Allah ya yarda sai a hada bikin da Yusuf yanda
kika ce" Inna tayi murmushi tace "Toh Allah ya kai mu lafiya ya maku albarka"
kallon Abba da ya nufi kofa kawai Mujaheed yake har ya fita yana amsa maganar Inna
da Ameen, can ya kalli inna da ta mike ta fara kakkabe kujeru, yace "Kin kagu ta
bar gidan kenan??" A fusace tace "Ba ruwan ka, wai ma dai meye hadina da kai
Mujaheed??? Ni dai nasan na haifi Ahmadu amma wllh da babu abinda ya hada mu gwara
kayi ta kanka, kiri kiri ka dinga nuna ma jikata bakin ciki??" Yana murmushi ya
mike yace "In sha Allahu wannan auren da kike ta 6arin jiki a kansa baxa ayi ba,
kuma har tsayuwar dare sai na yi akan hakan" salati Inna ta saki tana kallonsa, sai
kuma ta fashe da kuka tace "Baxa ayi ba?? Ehh lallai ka zama dan iska Muhammad, ita
yar Bukar kake ma bakin ciki?? Me ta maka xaka mata wannan fatan" ko sauraranta bai
tsaya yyi ba ya fice daga parlon, a hankali yake tafiya don shi kansa bai ma san
lkcn da ya fada mata hakan ba. Abba na komawa dama ya kira Daddy ya gaya masa yanda
suka yi da Inna, Daddy dai bai iya yace komai ba, Abba yace "So yanxu na yanke
ranan Sunday as ranan da xa ace ya turo parent din nasa, kai kuma sai ka dawo
Saturday or Friday" Daddy ya sauke ajiyar xuciya yace "Toh shkkn Allah ya kai mu,
Allah yasa hakan ne mafi alkhairi" Abba yace "Ameen" daga haka suka yi sallama ya
katse wayar. Washegari Abba ya kira Sadeeq ya kuma basa izinin turo magabatan sa
ranan lahadi, Sadeeq was so happy, farin cikin da bai taba yin irinsa ba duk tsawon
rayuwarsa ya dinga yi ma Abba godiya kamar ya masa albishir da aljanna, Mujaheed
dai na xaune parlon shi ma don tun safe Abba ya kirasa, amma banda danna wayarsa
babu abinda yake, lkci daya ya dago yana kallon Sadeeq suna hada ido ya dauke kai,
ya mike ya kai wayarsa kunne yyi excusing kansa ya nufi kofa hakan yasa Abba ma ya
bi sa da kallo kamar yanda Sadeeq yyi.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

62....

Ranan lahadi kamar yanda Abba ya tsara hakan ce ta faru, don Mahaifan Sadeeq a
ranan suka xo gidan nema masa auren Imaan, Bulasawa ne sai kanninsa biyu, da
abokansa biyu, da kuma wani kawunsa suka taho gidan, shi dai daddy baya cewa komai
don har ransa bai son aurar da only child din tasa a lkcn, a da ya dau burin sai ta
kusa gama University amma yanxu gaba daya Inna ta gama ruguje plan din, kuma babu
yanda ya iya, dubu dari biyar iyayen Sadeeq suka bayar kudin gaisuwan da akwatuna
har guda takwas da sauran abubuwan da ake badawa a al'adance amma triple triple
suka kawo komai, sannan suka ajiye ranan da xa su dawo a saka rana, Umma tunda ta
sami labarin shigowar su gidan ta kasa xaune waje daya ta dinga safa da marwa a
daki, can dai ta kira Hajiya Balaraba duk ta sanar mata abinda ake ciki, Hajiya
Balaraba tace "Toh meye abun daga hankali Hajiya Rukayya, ke fa an gama baki
tabbacin babu auren nan, ba abu bane da xai taba yiwuwa, to meye abun damuwa kamar
baki yarda da bawan Allahn nan ba...." Hankali tashe Umma tace "Nasani Hajiya
Balaraba ba wai ban yarda bane, na ji fa har ynxu shiru shiru ba alamar komai, ko
xuwa gidan ma wllh yaron ya daina, ita kuma yarinyar gaskiya bbu wani linkage
tsakanin mu, bbu ta ynda xa a hadu har yau ban yi yanda aka ce min ba, ga lkcn na
ta wucewa..." Hajiya Balaraba tace "Bata tahowa bangaren ku ne?" Umma tace "Sae ta
yi wata ma bata shigo ba idan ba uwar bace ta aikota, shi ma iyakarta dakin Amina"
Hajiya Balaraba tace "Ke dai baki da dubara wllh, ga dai wajen da take xuwa kullum
wajen Hajiya Asabe, ke baxa ki hada wani dubaran ba daga can" Umma ta d'an yi shiru
kafin tace "Toh shkkn xan duba, can din ma ni ba haduwa muke ba ko na je gaishe da
tsohuwar, xa dai mu yi waya xa a shigo min daki...." katse wayar tayi da sauri jin
an bude kofa, Aunty ta shigo da farin ciki sosai tace "Hajiya an kawo kudin
gaisuwan Imaan dubu dari biyar, kayan na gani Ina so kuma akwatuna takwas daga
gidan Alhaji Bulasawa...." Umma ta dauke kai ta mike ta fara kakkabe gadonta tace
"Toh Allah dai yasa ba yaudara bane, mu dai namu ido, wani kudin auren kirki ne har
dubu dari biyar ba ma sadaki ba kamar xa a siyar da ita" Juyawa Aunty tayi ta fita
dakin, Su Bulasawa na barin gidan Abba ya sa su Ummi da Rahma da Maimoon su kwashi
kayan su kai part din Inna, Inna ta saki baki tana kallonsu suna shigo da kayan
tace "Meye haka kuma?? Meye wannan din" Maimoon na murmushi tace "Na Imaan" Inna ta
mike da sauri tace "Wa ya kawo?" Maimoon tace "Daga gidan su Sadeeq" tuni Rahama da
Ummi suka fice parlon xuwa dauko sauran, Inna ta saki wani kabbara sai kuma ta xaro
ido tace "Yaushe suka xo?" Maimoon tace "Basu dade da tafiya ba" Xaunawa Inna tayi
ta fashe da kuka tace "Allah sarki Bukar, ita kenan fa garesa, ita kenan Allah ya
basa gashi yanxu xai raba sa da ita... Yanxu ya xai yi da ran sa" Shigowar Abba
yasa tayi shiru tana share hawayen idonta, Abba ya xauna ya gaisheta, ta amsa cikin
rawar murya tace "Yanxu shkkn raba Bukar xa ayi da Imaan ni patuu??" Abba dai bai
bata amsa ba ya ajiye ledan hannunsa a kusa da ita yace "Kudin gaisuwar da suka
bada kenan" Inna ta xaro ido tana kallon ledan kudin tace "Nawa?" Yace "Dubu dari
biyar" Inna ta saki salati tace "Toh dama ku siya mata dankareren gwal ku ajiye kar
a ta6a mata ko biyar tunda ba wani xai mata xaman auren ba Ahmadu" Abba dai bai ce
mata komai ba ya mike yace "Xuwa anjima xa mu shigo da Abubakar" daga haka ya fita
parlon, Inna na murmushi ta daga hannu sama da karfi tace "Alhmdllh, Alhmdllh,
takwarata tayi goshi ni Asabe, Allah na gode maka Allah, Allah na gode maka, ka bar
min rai da lafiyar kai ta dakinta da hannuna in sa mata albarka" sai kuma ta fashe
da matsanancin kuka, Maimoon ta tabe baki ta ta fita xuwa debo wasu kayan. Bayan
Magrib Inna na share parlonta don ba a dade da fitar Aunty da frnd dinta sai frnds
din Ammi biyu ba sun shigo ganin kaya, Yusuf ne ya shigo parlon bai dai xauna ba
yana kallon Inna daga tsayen da yake yace "Ina yini" ta mike ta ajiye tsintsiyar
hannunta tace "Lafiya lau Isuhu, sannu da xuwa bari in bude maka kayan, wllh babban
akwatin babu atamfar kasa da dubu hamsin, gaba daya Holland da England suka xuba
mata, ba fa lefe ne kayan sun gani sun kyasa ne..." Xata fara sauke sauke yace "A'a
ba sai kin bude ba, dama Allah ya sanya alkhairi na xo maki, Allah yasa ayi muna da
rai da lafiya" Inna tace "Atohh, Ameen dai, dama ganin kaya ai sai mata, kuma ai
rana daya xa ayi bikin da naka idan Allah ya yarda, kai ka angwance kanwar ka ita
ma haka" shi dai bai ce mata komai ba ya nufi kofa yace "Sai anjima" tace "Mu jima
da yawa, Allah maka albarka, Ina nan ina lissafin wa enda suka shigo yi ma jikata
barka, har yan anguwar nan ina xuba ido in ga wa enda xa su shigo da wa enda baxa
su shigo ba, mutane uku dai sun shigo daxu, amma kaga Rukayya da Aisha ko keyarsu
ban gani ba kuma xan ji dalili gobe da safe, ita Imaan din ma ban ganta ba yau gaba
daya" shi dai tuni ya fita. Inna na xaune tana cin abinci aka bude kofa, Mujaheed
ne ya shigo parlon ta mike da sauri ta shige daki sai ga ta ta fito da katon bargo
ta rufa ma akwatin har tana neman faduwa, shi dai kallonta kawai yake, ta tabbatar
ko kalan akwatun ba a gani sannan ta koma ta xauna tana ci gaba da cin abincinta
tace "Wa alaikumussalam" Yana tsaye yace "Ina yini" tace "Lafiya lau" Bai kuma ce
mata komai ba ya juya fita parlon ta mike ta rufe kofar tace "Gaskiya xan kira
Ahmadu ya ja ma mutumin nan kunne ya daina shigo min nan, yaje can ya ji da xabiyar
matarsa, kwata kwata xuciyarsa ba shi da kyau, hassada bakin ciki duk sun taru sun
masa yawa, hooo ni patuu Allah ya ba ma Ahmadu Ya ya, sai dai Allah ya raba mu da
su lafiya" Imaan ta fito wanka kenan daure da towel taga wayarta na haske, ta tafi
gaban mirror ta dauka tana kallon screen din, pick din kiran tayi ta kai kunne tana
murmushi, shi yyi sallaman ta amsa a hankali, yace "Why ain't u picking sweetheart"
ta wara ido tace "Ina parlor ban jima da shigowa ba" Yace "Ohk, ya gida?" Tace
"Lafiya lau" yace "Kayan sun maki dear?" Ta d'an yi murmushi ta sunkuyar da kai
kamar yana gabanta tace "Ai bn gani ba" da mamaki yace "Why?" Nan ma dai murmushi
kawai tayi bata ce komai ba, murmushin shi ma yyi yace "Ina fa mancewa bafillatana
xan aura, to ya xa ki yi da ni da kunyar ki Imaan" ta turo baki tace "Nima bn sani
ba" Yar dariya yyi yace "Xa ki sani ne ma" ita dai bata ce komai ba, yace "I can't
wait imaan, in gan ni tare da ke as married couple" tace "Uhm ina son in shirya, I
just took my bath now" yace "You need a helping hand?" Ta xaro ido tace "Noo, sai
anjima" Bata jira cewarsa ba ta katse wayar, d'an murmushi tayi ta fara goge
jikinta. Umma ce xaune parlon gidan Mujaheed tare da Safeenah dake danna waya tana
mata sannu da xuwa, bayan sun gaisa tace "A kawo maki ruwa Hajiya?" Umma tace "A'a
Alhmdllh, ai daga gida nake, Mujaheed din na nan?" Tace "Yana gun aiki" Umma tace
"Toh madallah, na xo don Allah xa mu yi wata magana da ke ne mai muhimmanci"
Safeenah na kallonta tace "Toh ina ji Hajiya" Umma ta d'an yi shiru sai kuma tace
"Wannan yarinyar da tayi sauka kwanaki Imaan na xuwa gidan ki kuwa?" Safeenah na
yatsine fuska tace "Yauwa dama don Allah Ina son kawo maki wani kara Hajiya, kinga
ni dai da Mujaheed xai aureni ba wai ance min cousins dinsa xa su dinga xuwa min
without good reasons ba kuma ba tare da sanina ba, don haka, don Allah a dakatar da
wannan yarinyar daga xuwa gidana bana so, kada Watarana abu ya 6aci, sannan wannan
kakar tasa ita ma kusan kullum sai ta xo, don tare ma suke xuwa da cousin din tasa"
Umma ta xaro ido tace "Haba dai, kice suna xuwa nan sosai" Safeenah ta tabe baki
tace "Ai kam, ni dai na gaji, sannan idan Yarinyar ta xo tayi ta nuna min isa da
gadara a gidana ko gaisheni fa bata yi" Umma tayi dariya tace "Toh ai a kanta ma na
xo gidan nan yanxu haka, Kinga kenan faduwa ya xo dai dai da xama" Safeenah ta bude
ido sosai tana kallonta tace "Toh Ina ji" Umma ta gyara xama tace "Kin san d'an
gidan Bulasawa??" Safeenah ta d'an yi shiru sai kuma tace "Gaskiya a'a, ina dai
following din yaransa mata a Twitter" Umma tace "Toh d'an sa na fari ne ke neman
Imaan din da aure, jiya aka kawo gaisuwa dubu dari biyar, da akwatuna takwas da
sauran tarakace me yawa, wllh da kinsan abinda uwar yarinyar nan ta min a rayuwar
duniya da kin tausaya min ke ma ki taya ni bakin ciki da auren nan" Safeenah dake
gwalo ido tace "D'an Bulasawa fa?? Me ya gani tare da ita yake sonta?" Umma tace
"Toh wllh sauran ciwo ce ma, yau ciwo gobe lafiya tunda sickler ce" Safeenah na
gyara xama tace "Tabb, Shi sa take ma mutane wani gani gani kenan???" Umma tace
"Wllh don haka yanxu kawai so nake kada auren ya faru, ni dai ba shige shige nake
ba balle ace, ba ruwana da boka ko malam, kawai dai da yan dubaru xa a raba su,
kema kuma dole sai kin bada contribution" Safeenah tace "Toh ta yaya?" Umma tace
"Ba kince tana xuwa gidan nan ba, dama nima naji labarin suna xuwa da kakar, shi
yasa nace bari in xo in same ki" Safeenah tace "Ba dai ko da yaushe su ke xuwa ba
sai jefi jefi" Umma tace "When last suka xo??" Safeenah tace "xai yi kusan wata
daya, Umma tayi tagumi tana naxari, can ta kalli Safeenah da ita ma tayi shiru
xuciyarta fal takaicin wanda Imaan xata aura, wai yaron Bulasawa, Umma tace "Kinsan
me xai faru yanxu Safeenah" Safeenah ta kalleta tace "A'a" Umma tace "Ki jira sai
Mujaheed din ya dawo sai ki ce masa kwana biyu baki ga Inna ba, yaushe xata xo?? Ko
kuma kyalesa kawai bari in baki lambar Innar ki kirata sai bayan kun gaisa sai ki
tambayeta kwana biyu shiru shiru baki ganta ba yaushe xata xo??" Safeenah tayi
murmushi tace "Koh?" Umma tace "Ahaf jikinta na rawa xata xo, ai ita tana son a
dinga nuna ana ji da ita, kuma in xata xo da wuya ta xo ita kadai, Dole da Imaan
din take fita kinga shikenan Allah ya kawo mana ita har gida amma kar ki yarda ki
gaya ma Mujaheed kamar yanda nace da farko don akwai sa da kwakwalwa, nan da nan
xai gano
ki" Safeenah tace "I thought as much, ga wayar ki sa min lambarta" Umma ta amsa
wayarta ta saka mata lambar Inna daga nata wayar sannan ta mika mata, Safeenah ta
amsa ta kai kunne, Inna na dagawa ta rafka sallama, Safeenah ta amsa tace "Ina yini
Inna?" Inna tace "Lafiya lau, waye don Allah, ni dai aiki nake ta yi na bude ma
mutane akwatuna tun safe suna shigowa gani, kinsan duniya ba gaskiya yanxu sai a
samu rikakken barawo da xai boye abu ya wuce da shi shi sa nake sa ido" Safeenah
tace "Safeenah ce Inna" Inna tace "Waye Safeenah kuma?" Safeenah ta tabe baki tace
"Matar Mujaheed" Inna tace "Ayyo, Safara'u ce, Toh sannu kin ji labarin an kawo
kaya kenan?" Safeenah tace "A'a ban ji ba" Inna tace "Atoh wa xai gaya maki dama
d'a bakin ciki uwa bakin ciki, wllh har yanxu ban ga keyar Rukayya ba, Mujaheed
kuwa tunda ya shigo ya gaggasa min magana ban kara ganinsa ba sai jiya da aka kawo
kaya, bakina a leko na shiga daki da gudu na dau katon bargona na rufe ma yarinya
kaya da shi tun bai kai ga gama kirga guda nawa bane, akwatuna takwas ne da kyar
ake xuge xif din, Toh me xance banda in gode Allah, har da gwal na dankunne guda
biyu da xobuna biyu fa a ciki, ni dai ba ruwana duk me ma jikata bakin ciki Allah
shi yasan yanda xai yi da shi, ko ke wllh baki samu haka ba shi sa Mujaheed ya fito
kiri kiri ya nuna bakin cikinsa a fili, kwana nayi Ina al-ajabin abinda ya gaya min
ranan wllh, isuhu kuwa har nan ya xo ya min Allah sanya alkhairi...." Safeenah da
Umma sai sauraronta suke don a hands free Safeenah ta sa wayar, Umma ta wani
kankance ido tana kallon wayar, Safeenah ta tabe baki tace "Toh Allah ya kyauta,
yaushe xa ki billo Inna kwana biyu shiru" Inna tace "In billo a yashe ma yarinya
kaya in shiga uku Safara'u, ai ba xancen billowa sai na kai Imaan dakinta, sa ido
yayi yawa gwara in mike tsaye kyamm, toh ke baxa ki xo ganin kayan bane kike jira
in billo?" Safeenah ta kalli Umma, Umma ta gyada mata kai da sauri alamar tace xata
xo, Safeenah ta tabe baki tace "Toh xan shigo in sha Allah" Inna tace "Atoh, sai
kin xo, sai kiyi sauri don xuwa anjima xa a kai ma kakarta ta wajen uwa ta ga kayan
ita ma, sannan a maido min inyi gadin kayana" Safeenah tace "Toh sai anjima sai na
xo" Bata jira cewar Inna ba ta katse wayar tana kallon Umma da tayi tagumi,
Safeenah ta ja tsaki tace "Ai nima sai inda karfina ya kare wajen ganin auren nan
ya fasu wllh, wato shi sa yarinyar ke ganin kowa banxa, ita a dole xata auri yaron
Bulasawa to taga samu ta ga rashi tunda har labari ya xo kunne na kuwa" Umma tace
"Wllh da kin gama min komai a duniya idan har muka hadu muka tarwatsa lamarin nan,
Kinga wahalar da na sha gun uwar yarinyar nan wllh kwakwalwarki baxai dauka ba, ta
dalilin uwarta aka min kishiya, aka kuma sakeni...." Nan umma ta fara giggila ma
Safeenah karya da gaskiyar abinda ya hadata da Ammi, tana kai wa aya, Safeenah ta
gyada kai tace "Ki kwantar da hankalin ki Umma, ai tunda har labari ya xo kunnena
an gama komai, dama kwata kwata na tsani yarinyar tun daga ranan da na fara daura
ido kanta, ki manta da ko wani shiri da kike a da ki sa min ido" Umma tace "Atoh,
shkkn.. Amma fa baxan mance shirin da nake ba, don kunya ba kadan ba nake son Uwar
yarinyar ta kwasa a hannu, yanxu dai ki shirya anjima kije ganin kayan kada a dago
komai a rai" Safeenah tace "A'a rashin xuwan kawai ya fi, ban gani ba balle raina
ya kara 6aci" sai kusan yamma umma ta bar gidan ko digon ruwa bata sha ba, amma ko
a jikinta. Yau tun safe Mujaheed ke xaune garden din gidansa har wajen sha biyu na
safe, Safeenah ce ta shigo garden din cikin shiga ta alfarma tana taunar cingam
tana kallonsa tace "Doctor d'an baccin weekend din ma gaba daya baka yi ba yau, ni
dai yanxu fita xan yi, xan je can gida daga nan kuma in tafi gidan ku in gaida su
umma" Daga kai yyi ya kalleta calmly yace "Baxa ki ba" Safeenah ta gwalo ido tace
"Baxan je ba kuma, mahaifiyata da taka xan je gaidawa fa" ya mike a d'an tsawace
yace "Nace baxa ki fita gidan nan ba Safeenah..." Daga haka ya wuce ya bar ta wajen
tsaye, ta ja tsaki tace "Don kana fama da miskilancin ka kwana biyu sai ka sauke
kai na, Toh wllh sai na fita" Kiran Umma tayi da wayarta ba a dau lkci ba Umma ta
daga, ko gaisuwa babu Safeenah tace "Toh gashi dai ya ki bari na in fita wllh kuma
yau ya kamata mu yi abinda ya kamata, kusan sati daya kenan Mujaheed magana da kyar
yake min a gidan nan, ni ban damu ba don dama haka yake wani lkcn amma na wannan
karan yyi yawa, tun asuba yake xaune garden yau wllh kamar maraya, during weekdays
kuwa dama sai nayi bacci yake shigowa ya fice kuma da sassafe washegari, kwata
kwata na rasa gane kansa ban san me ke damun sa ba, ni duk wannan ba wani damuna
yyi ba don a sauki na, amma yanxu gaskiya ki kirasa ki masa magana don idan har ban
fito ba yau shirye shiryen mu ya ruguje ne kawai" Umma tace "Kyaleni da shi kawai,
mu ma nan ai ya fi satin bai xo ba, Ina ga halinsa na da ne ke kokarin dawowa" daga
haka umma ta katse wayar, Safeenah ta tabe baki ta wuce cikin gidan, tana ta xaune
parlor har bayan minti talatin ganin bai sakko ba ta mike ta wuce sama, ya fito
wanka kenan ta shiga dakin, yana mata wani kallo yace "Kin xata kiran da kika sa
mahaifiyata tayi min xai sa ko fita gidan nan ne yau??" Ta nufesa tace "Wai me ke
damun ka two days ne Mujaheed, dubi fa you look so pale, and ni dai nasan lafiyar
ka qlau" Ko kallonta bai yi ba ya bude press dinsa ta rungume sa ta baya tana shafa
chest dinsa cike da shagwaba tace "Ni dai wllh ka gaya min meye damuwarka mijina"
Bata jira cewarsa ba ta juyo da shi ta rungume sa gam tana shige masa and she
really turn him on....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

63......

Safeenah na gama shirinta ta daura dankwali ya xauna dass a kanta ta feshe jikinta
da turare, ta juya ta kalli Mujaheed dake kwance idonsa rufe, karasawa kusa da shi
tayi ta xauna gefensa tana ta6a dogon hancinsa ta kai bakinta fuskarsa a hankali
tace "Dear ni xan wuce fa" Bude ido yyi calmly yace "I said you are going no where
Safeenah" ta xaro ido tana kallonsa da mamaki don duk tunaninta ya hakura, can ta
marairaice tace "Haba dear, wllh fa ba dadewa..." Ya katse ta ya mike xaune fuska
daure yace "Nace baxa ki fita ba, am telling you this wllh idan kika fita gidan nan
yau xaki san wanene Mujaheed" Yana fadin haka ya mike ya shige bathroom, tagumi
tayi xuciyarta na tafarfasa ta bi sa da ido, can ta mike ta fice daga dakin rai
bace ta kira Umma tace "Toh wllh ya ki bari na in fita Hajiya, taurin kan Mujaheed
har tsoro yake bani" da mamaki Umma tace "Ya ki barin ki kifito kuma??? To ina Ina
xuwa..." daga haka Umma ta katse wayar, Ba a dau lkci ba ta sake kiranta tace "Toh
ai wayar tasa a kashe yake" Safeenah tace "To ya kashe kenan..." Safeenah ta tabe
baki, Umma tace "Toh ki kai masa wayar ta ki" Safeenah tace "A'a ni kam baxan iya
kai masa ba, don he is very serious, ki bari dai in ta lallabasa anjima xan kira
ki" daga haka ta katse wayar. Imaan na xaune dakinta sun gama waya da Sadeeq kenan
ta shimfida darduma ta dau Al-quran dinta ta ajiye a kai ta xauna kan darduman ta
tankwashe kafa ta bude qur'anin, ba karamin missing din islamiyya take ba yanxu, ji
take da ma bata yi saukan ba, Bude kofar dakin aka yi Ammi ta shigo, Imaan ta daga
kai tana kallonta, Ammi ta xauna gefen gadon tace "Karatun kike ko kin gama" Imaan
tace "A'a ban fara ba" Ammi tace "Kin ma ci abinci kuwa" Imaan tace "Ehh na ci"
Ammi tace "Ohk, kina ji na Imaan?" Imaan na kallon mahaifiyar tata tace "Ehh ina ji
Ammi" Ammi tace "Pls Ina son ki dage da azkar sosai kuma a ko da yaushe, make that
a part of you, kuma da daddare xan dinga shigowa ina tashinki kiyi sallah...." Da
mamaki Imaan tace "Ammi me yasa" Ammi ta buda ido sosai tace "Me yasa, dama sai da
dalili mutum xai rike addu'a da tsayuwar dare, ae yanxu ne kika lalace baki yi,
amma da ai kina yi sosai" Murmushi Imaan tayi bata ce komai ba tana bude kur'anin
gabanta a hankali, Ammi tace "Ga kuma jarabawar ku ya kusa shima sai ki dage da
addu'an samun nasara kin ji" Imaan tace "In sha Allah Ammi" Ammi tace "Good" daga
haka ta mike ta fita dakin, imaan ta fara karatun Qur'anin gabanta cikin cool voice
dinta. Da magrib ta tafi kai ma Inna abincin Inna ta ki barinta ta tafi ta dinga
sauke akwatuna tana bude mata tana cewa "Sai kace ba kayan ki ba yau kusan kwanan
su biyar kin ki ganin abinda ke ciki, ni dai ba ruwana, karere ma da abun bai
shafesu ba duk suna ta xuwa gani balle ke" xauna ni dai ki duba, su Ahmadu da Bukar
ma duk sai da na fiddo masu suka gani filla filla, Imaan dai ta d'an yi murmushi ta
xauna tana kallon kayan da Inna ke fiddowa amma bata ta6a ba, Inna tace "Ni dai
naga abinda ya isheni, to ki daga mana ki dudduba ke fa babu abinda ya hadaki da
fulanawa, ubanki bahaushe ne gaba da baya, uwar ki ce bafillatana sai uwarsu
Mujaheed, ban san me yasa suka nace sai fulani ba, nima dai ubana bafillatani ne
amma uwata bahaushiya ce, mijina kuma bahaushe" Imaan ta turo baki ta dinga daga
kayan tana kallo, Inna tace "Wannan ai jaraba ne ke da kayan ki baxa ki duba ba, ga
gwal din can na hada da dankunnen da ya ta6a baki, bari in dauko ki gani" Daga haka
ta shige daki, Imaan na ganin haka ta mike cikin sanda ta nufi kofa ta fice parlon
da gudu ta sa takalminta tayi gaba, a hanya ta kusa cin karo da Mujaheed, ta xaro
ido ta juya masa baya da sauri xata bar wajen ya kamo hannunta ya juyo da ita, kin
yarda su hada ido tayi tace "Ina yini" ya dawo da ita jikin bango ya dago kanta
yana kallon kwayar idonta, kallonsa ita ma take, lkci daya ta sauke idonta kasa a
hankali, Murya can kasa yace "Me yasa kike gudu idan kin gan ni Imaan" ta turo baki
tace "Ni fa ba komai yaya" ya kamo hannunta yace "A'a ki gaya min pls, me yasa kike
gudu" kasa cewa komai tayi, yace "Imaan" da sauri ta kallesa jin yanda ya kirata,
yace "Talk to me plss" Boye fuskarta tayi tace "Ni bana son ka min fada shi sa nake
gudu" yace "Fadan me?" Kin cewa komai tayi ta sunkuyar da kai tana murmushi, ya
kara kiran sunanta, kamar xata yi kuka tace "Abinda nayi mana" Bai iya yace komai
ba sai kallonta yake, Jin shirun yyi yawa ta daga kai ta kallesa suka hada ido, ta
wara masa idonta tace "Amma dai baka da lafiya ne Yaya" Ya sauke idonsa kasa yace
"Probably" cike da damuwa tace "What's wrong with you yaya?" Da kamar baxai ce
komai ba sai kuma a hankali yace "Akwai wani abinda ke shirin faruwa that will
cause me lot of harms a rayuwata, and sure that will be the end of my happiness..."
Da damuwa sosai tace "Subhanallah, what's that Yaya? Meye shi ka gaya min" jingina
yyi da bango bai iya yace mata komai ba, ta dawo tana facing dinsa ta kamo hannunsa
kamar xata yi kuka tace "Yaya don Allah ka gaya min meye shi, meye xai faru and how
are you to prevent it from happening" Taku da suka ji toward direction dinsu yasa
tayi saurin sake masa hannu bayan sun yi ido hudu da Abba dake tahowa xai tafi part
din Inna hannunsa rike da leda, Mujaheed ya ja baya da sauri, ita ma hakan tayi,
tunda Abba ya kallesu sau daya ya dauke kai, sai da ya isa daidai su.. Mujaheed ya
sunkuyar da kai cike da karfin hali yace "Sannu da dawowa Abba" Abba yace "Yauwa
Muhammad ya family" Imaan ta sunkuyar da kai ita ma tace "Ina yini Abba" Abba ya
amsa sannan ya wuce xuwa part din Inna. Imaan ta kalli Mujaheed tace "Yaya mu je
plss ka gaya min" Bata jira cewarsa ba ta kama hannunsa ta xaga baya da shi, ta
xauna kan wani dakali tana nuna masa gefenta tace "Oya xauna" murmushin karfin hali
yyi ya xauna, ya jinginar da kansa da nata yana kallonta ta gefen ido, tace "Toh
ina ji, tell me what's it kuma ka gaya ma su Abba kuwa??" Mujaheed ya jawota
jikinsa murya can kasa yace "No I didn't, and it's too late" kallonsa kawai Imaan
take, kafin tace komai yace "Kin ga kayan ki da aka kawo?" Rufe fuskarta tayi da
sauri a shoulder dinsa tace "Ni baxan iya ba" ya lumshe ido ya bude, a hankali yace
"Yanxu dai aure kike son yi ki tafi ki bar ni koh?" Ta xaro ido tace "Toh ae kai ma
kayi auren ka tafi ka bar ni" yace "Ance maki ina son auren nawa ne?" Yar dariya
Imaan tayi tace "Ehh baka sonta but you are enjoying ur marriage, kuma tana haifa
maka beautiful baby like her xaka fara sonta sosai" kallonta yake ko kiftawa babu,
cikin sanyin murya yace "Why did u say I am enjoying my marriage imaan, how did you
know??" Tana murmushi tace "Ae na gani..." da sauri yace "Kika ga me??" Taki yarda
ta kallesa tace "Abinda na gani" Bai san lkcn da ya rungume ta ba yace "Noo imaan,
I can neva enjoy my marriage with Safeenah, am only trying my best in fita
hakkinta, ni kadai nasan abinda nake ciki imaan, bana son Safeenah, warce nake so
na kokarin kubuce min which I won't allow in sha Allah" Imaan tace "Wai Aunty
Farida, she told me her wedding is next week ai, xan ma je tare da Maimoon" Ya
runtse ido yace "I have never loved farida, tausayinta kawai nake, kuma burina a
da in hada ta su xauna da wacce aka halitto ni domin ta, sbda lalurorinta, ita ce
macen da nake ma son da ni kaina ban san irinsa ba Imaan" da surprise imaan ke
kallonsa jin yace baya son Farida, a hankali tace "Who is this lady Yaya? Ni ban
santa ba, you've never tell me anything about her, ita ma a kd take?" lkci daya
idanuwansa suka kada sosai, cikin sanyin murya yace "Na fara mata so na yan
uwantaka, sannan na kasance mai tausayinta matuka, ni kaina ban ta6a tunanin
soyayyar da nake mata xai rikide ya koma so na aure ba, tun bata san kanta ba nake
sonta nake mata hidima, na kuma koya mata sa6o da ni...." Imaan dake ta kallonsa
ta xaro ido kamar xa su fito tace "Kamar dai yanda muka sa6a ko, To wacece kuma a
Ina take yaya?" Mujaheed ya dinga kallonta, Ta turo baki tace "Ni dai ka gaya min,
kuma tasan kana sonta kuwa?" Ya girgixa kai a hankali yace "Taki ganewa har yanxu"
Imaan tayi murmushi hade da tagumi tace "Toh nawa xaka biya ni sai ka hada ni da
ita in fallasa mata sirrin dake xuciyarka, Yayana kasan fa you are very
handsome..." Sai kuma ta fashe da dariya ta boye fuskarta a jikinsa tace "Wllh kana
da kyau, and you are a gentle man, tall, huge, your beards are cute, so babu macen
da xata iya resisting love din ka stop being afraid xaka rasa ta, kila da gudu ma
xata amince maka idan ka sanar mata, wa ya sani ma ko ita ma tana sonka, it's bcos
of ur handsomeness and ur personality wannan rubabbiyar matar taka ke rawan kai a
kanka, take ma mutane walakanci, wllh sonka take kamar ta mutu, bata san you are
only managing and just enjoying...." Sai kuma ta yi shiru da sauri, Bai san lkcn da
yyi wani murmushi ba har sannan yana kallonta ya dago kanta taki yarda su hada ido
yace "Enjoying what?" A rikice tace "A'a ba haka xance ba fa...." Ya lumshe ido
yana shakan kamshin gashinta daga cikin hijab din jikinta murya can kasa yace "I
will enjoy soon with my lil sis, amma ba da Safeenah ba...." imaan ta bude ido da
sauri ta kallesa tace "Wacece?" Ya bude ido shi ma yace "Ita warce nake so mana"
imaan tace "Toh are you paying me to help you out?" Yace "Ko nawa kike so kuwa,
amma before then sai kinyi kokarin sa su Abba a dakatar da maganar kawo sadakin ki
next week" da mamaki tace "Why? My being betrothed won't stop me from helping u out
yayana" Ya girgixa kai cikin sanyin murya yace "Shine babban abinda xai sa ki kasa
taimakona Imaan" Ta xaro ido tace "Yaya kai fa ka riga kayi auren ka, to ni baka
son nayi auren?" Ya kalleta yace "Auren dai kike son kiyi ki bar ni" dariya tayi
sosai tace "Kai ma ai ka yi" yace "Amma ai ina xuwa ganin ki kullum" tace "A'a ni
dai ba wajena kake xuwa ba, wajen Inna kake xuwa" yana kallon kwayar idonta a
hankali yace "Wllh duk ranan da na xo gida ban ganki ba bana iya bacci da daddare"
Da mamaki Imaan
ke kallonsa tace "Saboda me?" Ya sauke idonsa bai ce komai ba, tayi murmushi tace
"Kaga da matarka na sona sai in koma gidan ka in yi waec a can" ya kalleta da sauri
yace "A'a ba ruwanki da ita ki dawo kiyi waec din ki kawai" ta make kafada tace
"Bana so, Ni fa da gaske Yaya bana son matar nan taka, I so dislike her" Yyi shiru
bai ce komai ba, can tace "Yaya na fara jin yunwa fa, xaka bani lambar yarinyar ne
yanxu in kirata mu yi magana?" Ya girgixa kai yace "A'a sai dai in kai ki wajenta"
tace "When?" Yace "Ko xuwa gobe" tace "Toh Allah ya kai mu" da sauri ta daga
kafarta tana kakkabe hijab dinta tace "Wllh Yaya sauro a nan" Mujaheed ya kunna
fitilar wayarsa yana haska kafar yace "Sorry dear" yayi stretching legs dinsa ya
daura nata a kai bayan ya daga hijab din yana duba inda sauron ya cije ta, shafa
smooth leg din nata ya shiga yi yana kallonta, ta xaro ido ta buge hannunsa tace
"Aa ni bana so Yaya" a hankali yace "Why?" Ta turo baki tace "Uhn ni bana so" tana
fadin haka ta sauke kafarta kasa ta mike tace "Toh sai goben Yaya" ya mike yana
kallonta yace "Mu tafi eatry tunda kina jin yunwa?" Ta juyo da sauri tace "Da gaske
Yaya" yana murmushi yace "Sure, tafi ki jira ni gun mota a waje" tana murmushi tace
"Toh" daga haka ta wuce ya bi ta da kallo har tayi nisa, ya lumshe ido ya bude,
kamar mai tausayin kasa ya dinga tafiya har ya fita compound din ya sameta kusa da
motarsa tana jiransa, yana bude motar ta shiga front seat, shi ma ya shiga maxaunin
driver tana kallonsa tace "Yaya ni kaza nake son ci da drink kawai" yace "Ba sai
mun je eatry ba knn" tace "A'a can xa mu je" suna isa wani eatry babba yayi
ordering abinda tace, suna xaune wayarta a hannunsa tana kallon hotuna shi kuma sai
kallonta yake, hotunan da suka yi tare ne kadai a camera dinsa, sauran duk WhatsApp
images ne, hoton Safeenah ko kwaya daya babu a wayar tasa, Imaan ta daga kai suka
hada ido, ta xaro ido tace "Why are u staring at me that way?" Bai ce mata komai ba
yana kallon waitress dake ajiye masu gasasshen kaza daya da aka yayyanka sae kamshi
yake, Mikewa Mujaheed yyi ya tafi ya wanke hannu ya dawo, imaan har ta bude drink
din ta fara sha, ya xauna ya dau tsoka daya yana kallonta yace "Bude bakin" dariya
tayi tace "Cikin mutane??" Yayi shiru yana kallonta, a hankali ta bude bakin ya kai
mata naman dai dai lkcn da suka hada ido da Sadeeq dake xaune eatry din da wani
frnd dinsa.
*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

64....

Imaan ta sauke idonta kasa a hankali ta cire naman daga bakinta ta mayar ta ajiye,
kallonta kawai Mujaheed yake ganin abinda tayi yace "What happened?" Ta turo baki
taki cewa komai, Ido hudu suka yi da Sadeeq dake kallonsu har sannan shi ma, Sadeeq
na ganin haka ya mike ya iso inda suke yana murmushi ya dafa table din a hankali
yace "Good evening" sai a sannan Mujaheed ya sake kallonsa for d second time yace
"Same to you" Imaan dai ta kasa kallonsa sai bugawa xuciyarta yake, Ya ja third
chair dake wajen ya xauna yana kallonta da murmushi yace "How are you doing" Bata
iya ta kallesa ba cikin sanyin murya tace "Ina yini?" Yace "Lafiya lau, kina ta
enjoying da yayan ki" Mujaheed dai sai cin namansa yake ba tare da ya kallesa ba,
imaan ta ki cewa komai sai wasa da ring din finger dinta take, Sadeeq na murmushi
ya kalli Mujaheed yace "Ya family?" Mujaheed yace "Alhmdllh, do you care joining
us..." Sadeeq na kallon naman yace "Ohh Alhmdllh, I just finished eating now" daga
haka ya mike yace "Alright, xan wuce, i was about leaving na gan ku" Yana magana
yana ma abokinsa sign ya taso su wuce, Mujaheed yace "Ohk then" Daga haka Sadeeq ya
kalli Imaan yace "Toh malama, sai anjiman ku" ta kallesa suka hada ido, da sauri ta
sunkuyar da kanta a sanyaye tace "Toh sai anjima" juyawa yyi ya bi bayan frnd dinsa
da har ya nufi door din fita, Mujaheed ya kalli Imaan da ta wani hade rai ya dai ci
gaba da cin namansa bai ce mata komai ba, bayan few minutes a hankali tace "Ammi
xata fara nemana yanxu" ya kalleta yace "Toh wa xai ci maki naman da kika sa na
siya?" Ta turo baki tace "Ni bana ci kuma" Bai tanka ta ba ya kira waitress ya sa
tayi masa take away din kazar, ya tafi ya biya bill din ya dawo rike da ledan naman
ya dau drink dinsa ba tare da ya kalleta ba yace "Tashi in maida ki gida" Mikewa
tayi fuska daure ta bi bayansa don har ya nufi hanyar fita, bude front seat tayi
xata shiga suka yi ido hudu da Sadeeq dake tsaye gun masu suya dake wajen, dauke
kansa yyi ya ci gaba da yi ma mai suyan magana, A hankali Imaan ta shiga front seat
din, Mujaheed ya shiga maxaunin Driver ya tada motar suka bar haraban eatry din,
Har suka isa gida bai ce mata ba ita ma bata ce masa ba, Yana parking a waje ta
bude motar xata fita ya riko hannunta a hankali, kamar jira take ta fara shesshekan
kuka tana kallonsa, lkci daya ya rikice mata yace "Kuka kuma Imaan, what's wrong,
me ya faru..." Cikin rawar murya tace "Toh ba Sadeeq ya ganmu ba yanxu, Kuma...."
Sai kawai ta fashe da kuka sosai tana kallonsa, ya lumshe ido ya matso da ita kusa
da shi a hankali yace "Kuma me?" Tana shessheka tace "Let him not think something
different alhalin kai yayana ne kowa ma ya sani" shiru yyi yana sauraranta, jin
shirun yyi yawa ta daga kai a hankali tana kallonsa, yyi murmushin karfin hali yace
"Toh ba gashi kin fadi abinda ke kike tunani ba da sauran mutane, wato ni yayanki
ne, to shi ma you just assume hakan xai yi tunani ni yayanki ne, tunda Ammi da
Daddy ne suka haifeni sannan suka haife ki" ta turo baki tana kallonsa tace "Toh
kai ba yayana bane?" Yace "Ehh in dai Ammi ce ta haifeni" ta wani hade rai tana
kallonsa tace "Kamar ya?" Yace "Kamar yanda na fada" tace "To waye dama bai san kai
yayana bane" Yana shafa kansa yace "Waye dai bai san ni cousin din ki bane" ta xaro
ido tace "What did you mean??" Yace "I mean ki daina cewa ni yayanki ne so as
people will stop thinking we are from the same parent, we are only cousins imaan,
anything can happen" tabe baki tayi ta bude motar xata fita ya kamota yana kallonta
yace "Wait" tsayawa tayi har sannan bata daina kallonsa ba, ya bude ledan naman ya
dau daya ya kai bakinta, turo bakin tayi ta dauke kai cikin sanyin murya yace
"Plss..." Tace "Toh ba kace kai ba yayana bane" yayi murmushi yace "Ehh ni yayanki
ne, amma hakan ba yana nufin iyayen mu daya ba, yau idan aka ce in aure ki, baxan
ce A'a ai kanwata ce ita ba, kowa yasan there is marriage between us, so stop
confusing people" kallonsa Imaan take ko kiftawa babu, a hankali yace "Oya bude
bakin" ta sauke idonta kasa ta ki bude bakin kuma, ya kamo hannunta yace "Imaan"
kallonsa ta kara yi, ya jawota kusa da shi idonsa cikin nasa yace "Open ur mouth" a
hankali ta bude bakin tana kallonsa ya kai mata naman ciki, ta gutsura kadan ta
dauke kai, yana murmushi ya kai sauran baki yace "Toh shkkn kanwata" Bude motar
tayi tana son fita yayi saurin riketa yace "Since I got married nake missing din ki
sosai unlike before da nake gida that we are always fighting, from now on every
magrib idan kin je kai ma Inna abincin ki jira har sai na xo mun yi hira kadan
kafin na wuce kin ji" tayi murmushi tace "Toh ai da haka muke yi kafin ka canxa ka
fara ma mutane fada da ihu" ya kai tip din finger dinsa kan lip dinta murya can
kasa yace "Na daina yanxu dear, hira kawai xan dinga xuwa muna yi, sai in taho maki
da abun dadi" ta wara ido tace "To Yaya, xan dinga jiran ka" ya daure ledan naman
da drink ya mika mata yace "Good girl" ta amsa tace "Toh nagode, sai da safe" yace
"Sleep tight" ta fita motar tana murmushi ta wuce ciki ya bi ta da kallo. Parlor ta
tadda Ammi tana cin abinci, Ammi na kallonta tace "Me yasa kika dade, kuma ledan
meye hannun ki?" Imaan ta xauna tace "Yaya ne ya siya min" Ammi tace "Yaya kuma, a
kan me ya siya maki?" Tace "Ba komai, kawai dai ya siya min ne ya bani ai yasan ina
so" Ammi ta tabe baki ta ci gaba da cin abincin ta, Imaan ta bude ledan tace "In
debar maki Ammi?" Kamar jira Ammi take tace "A'a ki je kiyi ta fama" Imaan tayi
dariya ta mike ta wuce kitchen ta dauko plate ta juye naman taci taci ta sha drink
tayi nakk, sauran ta kai fridge tana kallon Ammi tace "Ammi sai da safe" Ammi tace
"Allah ya tashe mu lafiya, don't forget perform ablution before going to bed, kuma
kar ki manta kiyi addu'a, kin ma yi isha kuwa??" imaan tace "xan yi yanxu Ammi"
daga haka ta wuce dakinta, wanka tayi ta dauro alwala ta fito ta shirya cikin kayan
bacci ta sa hijab har kasa tayi isha da shafa'i, tana idarwa ta dau wayarta dake
gaban mirror tana dubawa, xaunawa gefen gado tayi ta shiga kiran Sadeeq don duk
dare sai ya kirata yau kuma bata ga call dinsa ba, har ya gama ringing bai dauka
ba, Ajiye wayar tayi a hankali ta hau saman gado ta kwanta ta rufe ido. Karfe biyar
saura na yammacin washegari Ammi na xaune parlor tana yankan pumpkin leaf aka bude
kofar parlon Mujaheed ya shigo da sallama, ya ajiye ledojin hannunsa na kayan shayi
ya gaida Ammi ta amsa tana masa sannu da xuwa yace "Daddy yace a kawo sakon" Ammi
tace "Ohk Yusuf baya nan kenan" Mujaheed yace "Ehh Ina ji" tace "Toh Allah yyi
albarka" yace "Ameen" har ya nufi kofa ya tsaya ba tare da ya juyo ba yace "Imaan
bata dawo schl ba?" Tace "Bata je yau ba" ya juya da sauri yace "Me yasa?" Ammi na
ci gaba da yanka leaf din tace "Yau ta tashi ba lafiya" Yace "Subhanallah, likita
ya xo dubata amma?" Ammi ta girgixa kai yace "Ynxu likitan ba wai yana xama bane,
yana Sokoto yau, amma gobe xai dawo, mun dai je asibiti" yace "Bacci take?" Ammi
tace "Ina ji" shiru yyi bai ce komai ba, Ammi ta kallesa hakan yasa ya nufi kofar
fita kamar mai counting steps dinsa yace "Toh Allah ya bata lfya" Ammi tace "Shiga
ka duba ko idonta biyu" Kamar abinda yake jiran ji kenan ya juya ya nufi dakin Ammi
ta bi sa da kallon gefen ido har ya shiga sai dai bai rufe kofar ba. Kwance ya
sameta ta rufa har kanta da duvet, ya xauna gefen gadon ya cire duvet din yana
kallonta, tun bai kai hannunsa jikinta ba ya ji temperature dinta is so high, ta
bude idonta da yyi ja tana kallonsa, kamar xata yi kuka ta fara kokarin mikewa
xaune tace "Yaya jikina xafi yake min sosai kuma Ammi ta ki bari in kunna fan ko
Ac" sai kuma ta fara kuka, ya jawota kusa da shi murya can kasa yace "Why did u
cover ur self?" Cikin rawar murya tace "Am feeling cold" yace "Kuma shine kike son
kunna fan" Bata ce komai ba sai kuka take a hankali, ya daga kanta yace "An maki
allura da ku ka je asibitin?" Kai ta gyada masa tace "My legs are still aching har
yanxu da bayana" yace "An shafa maki magani kuma?" Ta gyada masa kai tana goge
hawayen idonta, janyeta yyi jikinsa ya dau Magungunan dake ajiye side drawer har da
na shafawa, ya mayar da saura ya bude na tube din ya cire gaba daya duvet din, daga
kneel dinta ya fara shafa mata xuwa toes dinta, ta dinga kallonsa kamar xata yi
kuka tana rike hannunsa tace "Yaya xafi" daga kai tayi taga Ammi tsaye bakin kofar
dakin, Mujaheed ya juya ya kalli kofar, juyawa Ammi tayi ta bar bakin kofar, Imaan
tace "Ka bar shi haka kawai ya fara min sauki" Ya rufe tube din yana kallonta, jin
wayarta na vibrate ta juya da sauri ta dau wayar, Sadeeq ne ke kiranta, dagawa tayi
ta kai kunne tayi sallama a hankali, Daga daya bangaren ya amsa, ta gaishesa, yace
"How are you doing" cikin sanyin murya tace "Lafiya lau, why ain't you picking ur
calls" yace "Ba gashi Ina following calls that I have missed ba ynxu" shiru tayi,
shi dai Mujaheed kallonta kawai yake, Sadeeq yace "Ya Ammi?" A hankali tace "Lafiya
lau" yace "Maa sha Allah, we will talk later sai anjima" daga haka ya katse
wayarsa, ajiye wayar Imaan tayi Mujaheed na kallonta yace "Kiransa kika dinga yi
knn?" Bata san lkcn da ta fashe da kuka ba ta kife kanta da pillow tace "Kila fa
fushi yake da ni Yaya, it's very unusual bai kirani ba tun jiya" Kasa daina
kallonta Mujaheed yyi, tana shessheka tace "I called him sau biyu bai dauka ba, tun
ba yau ba nake ce masa kai yayana ne ko ya xatan karya nake masa, Yaya plss kai ka
gaya masa da kanka kila xae yarda, we are just close with you and nothing more, kai
yayana ne" Mujaheed na kallonta a hankali yace "We are just close and nothing more,
what if it's totally not so imaan kamar yanda shi yake tunani?" Ta daga kai da
sauri tana kallonsa tace "Toh ai ni da kai mun san ba haka bane Yaya, an taba ganin
inda Yaya ya auri Kanwarsa??? Hakan bai ta6a faruwa ba, don Allah Yaya make him
understand this, I am just sick of this, ni bai taba min haka ba" Mujaheed yyi wani
murmushi yana shafa kansa yace....

Sorry for the short chapter... don't forget i am still not home but I am managing
to type, in sha Allah xuwa karfe tara da wani abu ltr xa ku ji ni.
Thank you.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

65......

Mujaheed yyi wani murmushi yana shafa kansa a hankali yace "Saboda bai dau wayarki
ba shine kika fara leg and backache kenan??" Banxa tayi masa ta koma ta kwanta ta
juya masa baya, ya dinga kallonta ko kiftawa babu kafin ya mike ya nufi kofa yana
murmushi ta bi sa da harara har ya fita ya rufe mata kofa. Tun daga wannan rana
Sadeeq ya daina kiran Imaan gaba daya sai dai in ita ta kirasa, sosai ta shiga
damuwa ta rasa me ke mata dadi, ko abincin kirki bata iya ci, bata taba tunanin
akwai abinda xai daga mata hankali haka ba, ko da yaushe a sanyaye xaka ganta, tana
wanke wanke a kitchen ranan Thursday da yamma Ammi ma na kitchen din tana kwashe
shinkafar da ta dafa a warmer, tarwatsewan glass cup da ta ji yasa ta juya da sauri
tana kallon Imaan da ta koma baya tana xaro ido, don na biyu kenan ta fasa
tsayuwarta a sink din, Ammi ta daure fuska cikin tsawa tace "Are you stupid imaan,
tunanin uban me kike kika sake fasa min wani cup din?" Hawaye imaan ta fara yi tana
kallonta, Cikin tsawa Ammi tace "Get out kar in gaura maki mari my friend" juyawa
Imaan tayi da sauri ta fita, Ammi ta gama kwashe abincin ta tafi ta ci gaba da
wanke wanken, tana gamawa ta fita xuwa dakin Imaan, Kwance ta ganta ta rufe
fuskarta da pillow, har ta karasa kusa da ita ta xauna gefen gado bata sani ba,
Ammi tace "Imaan..." Da sauri ta dago a tsorace don bata ji shigowar ta ba, sai
kuma ta fara goge idonta tana sunkuyar da kanta, Ammi ta kamo hannunta cikin sanyin
murya tace "Tell me what's wrong with you plss Imaan, kina da wata da xaki fada ma
damuwarki ban da ni, am asking you this for the third time, kar ki yarda in kira
daddy yanxu kin san dawowa xai yi" Imaan ta fashe da kuka sosai ta rungume ta, lkci
daya jikin Ammi yyi sanyi, ta dago kanta cike da damuwa tace "Ki gaya min damuwarki
daughter" cikin rawar murya tace "Ammi mai sunan Daddy ne...." Da mamaki Ammi ke
kallonta lkci daya kuma gabanta ya fadi don right from time ta gudar ma only child
din tata heartbreak, cike da karfin hali tace "What about him???" Cikin kuka Imaan
tace "He is calling me no more, ko na kirasa baxai dauka ba sai washegari" Ammi
dake kallonta duk da tashi da hankalinta yyi ta dake tace "Me ya hada ku?" Shiru
Imaan tayi hawaye na sakko mata, bata ma san me xata ce ma Ammi ba, tasan ko hauka
take baxata ce don ya ganta da Mujaheed a eatry bane Mujaheed na bata nama a baki,
ta hadiye abu da kyar tace "Kila saboda yana ganina tare da Yaya ne always" Ammi
tace "Toh dole sai kin tsaya tare da Yaya, Ina ruwanki da shi da yyi aurensa, wato
yana ganinku kuna shashancin da ku ka saba kina xaunawa kusa da shi ko???" Imaan ta
fashe da kuka a hankali tace "Wllh Ammi na daina haka ai" Ammi bata iya tace komai
ba, imaan ta kamo hannunta cikin rawar murya tace "Ammi ko xa ki kirasa ki masa
magana don Allah" wani kallo Ammi ta mata tace "Ba mu gaji haka ba ai, ni ba
gantalalliya bace, kuma bari in gaya maki ba a ma namiji son hauka, kawai don bai
kula ki ba ki wani damu ki daga hankalinki kisa ma kanki wani cutar ki cuce ni?" Ta
rufe fuskarta a kafar Ammi tana shessheka tace "Ammi wllh da gaske Ina son sa" Ammi
ta dinga kallonta, can ta dago kanta cikin sanyin murya tace "Ki kwantar da
hankalin ki Imaan, amma bana son kina damuwa, kin basa hakuri kuma?" Imaan ta
girgixa mata kai, Ammi tace "Toh ki kirasa ko ki masa text ki basa hakuri, sai ke
kuma ki kama kanki ba ruwan ki da wani Yaya from now on kin ji abinda nace?" Imaan
ta gyada mata kai a hankali, Ammi tace "Kuma ban ce ki gaya ma Inna ba" a hankali
Imaan tace "Toh Ammi" Ammi tace "Ta shi mu je ki xuba abinci yanxu" ba musu Imaan
ta mike ta bi bayan Ammi suka fita dakin. Karfe shidda Imaan ta tafi kai ma Inna
abinci don bata ma son ta je da Magrib ta hadu da Mujaheed, turo baki tayi ganin
takalma bakin kofar, ta shiga da sallama ba tare da ta yarda ta kalli wanda ke
xaune a parlon ba ta ajiye abincin, Inna na washe baki tace "Toh kin kawo a dai dai
kuwa, kawo plate in dibar masa nasan baxai wuce shinkafa ba dai" Imaan ta saci
kallonsa lkci daya gabanta yyi mugun faduwa ganin Sadeeq xaune parlon cikin kananun
kaya idanuwansa sanye da glasses, suna hada ido ya dauke nasa idon, ta kasa fita
parlon, Inna tace "Baxa ki kawo kwanon bane in tashi da kai na" Yana murmushi yace
"Kaka da gaske fa na koshi, yanxu muka gama cin abinci da abokaina a gidan cin
abinci" Inna ta rike ha6a tace "Toh abincin gidan naku ba dadi ne Bukar har sai ka
fita gidan masu abinci?" Sosai Sadeeq yyi dariya yana kallonta yace "Kaka saboda
abokaina ne muka je can" Inna ta tabe baki tace "Atoh, na ji ance fa naman aladu
suke siyar ma mutane, ni dai da xaka yi hakuri ka daina xuwa idan ma girkin gidan
naku ne baka so sai ka dinga xuwa nan xan saka maka a kwano in ajiye, kazamai da
masu wari sun yi yawa a duniya yanxu kaje ka ci abinda xai hallaka ka wataran mu
shiga uku gaba daya" Shi dai dariya kawai yake Imaan ta juya ta fita parlon.... Dai
dai inda suke yawan tsayuwa da Mujaheed ta tsaya, ba a wani dau lkci ba taji foot
steps dinsa yana tahowa, yana kusa isowa wajen suka yi ido hudu, yyi slowing pace
dinsa amma kuma ba shi da alamar tsayawa, cikin sanyin murya tace "Plss ka tsaya
Abbana" Tsayawa yyi ya dawo gefenta ya rungume hannunsa a hankali yace "Toh na
tsaya daughter" Lkci daya hawaye ya kawo idonta ta sunkuyar da kai cikin rawar
murya tace "Don Allah kayi hakuri ka yafe min" Yace "Inyi hakuri a kan me" da kyar
tace "Abinda yasa kake fushi da ni" yayi murmushin karfin hali yace "Aa ban yi
fushi ba Imaan" tace "Wlh ka yi, don Allah kayi hakuri wllh hakan baxai kara faruwa
ba" Yace "Imaan don Mujaheed yayan ki ne kamar yanda kike yawan fadi ba yana nufin
same parent suka haife ku ba so I have all right to get angry, Shi din ba
Muharramin ki bane, da nine nace mu fita eatry ni da kudin gaisuwana ke kanki ba
yarda xa ki yi ba, not to talk of giving ur meat..." ta dinga goge hawayen da ya ki
tsaya mata tace "Plss kayi hakuri, baxan sake ba, abinda ma yasa ya kai ni wajen
ranan ya siya min kaza shine saboda I promise xan taya sa fada ma wata yarinya da
yake so cewar yana sonta wai ya kasa fada mata.... Wllh saboda nace ni xan yi ma
yarinyar magana ya sa ya siya min kaza don in maya" murmushi Sadeeq yyi yana shafa
kansa yace "Ya wuce Imaan... Xan wuce masallaci it's almost time" a hankali tace
"Ka hakura?" Yace "Tuni na hakura ai" mu je ki raka ni gate, har suka isa gate babu
wanda yace komai cikinsu, yana kallonta yace "Good night" ta gyada masa kai ya wuce
ta juya ta koma ciki. Tun daga sannan imaan tayi kokarin dinga avoiding Mujaheed,
ko parlonsu ya shigo dama tashi take ta wuce daki ko ta wuce kitchen, part din Inna
kuwa kafin yaje xata kai mata abinci ta maxa ta dawo, ana haka har ya rage two
weeks su fara exams kuma hakan yyi dai dai da saura sati biyu a kawo lefenta tare
da sadaki daga gidansu sadeeq, sosai ta dage da azkar kamar yanda Ammi ta ce mata
saboda yawan faduwan gaba da take, Ammi ma ta bata addu'o'in da xata dinga yi tana
kuma kokarin tashin ta duk dare tayi sllh. Yau Saturday Imaan ta fito parlor sanye
da hijab dinta har kasa hannunta rike da karamin jaka, duk da babu komai fuskarta
sai eye pencil da Chappete ba karamin kyau sanyanye tayi ba, Ammi dake xaune parlor
ta bi ta da kallo har ta durkusa kusa da ita tace "Ammi xa mu wuce" Ammi ta d'an yi
shiru kafin tace "Kar ki dade Imaan, ko minti goma plss kar ki yi ba mutuncin ki
bane, kina yin abinda ya kai ki ki juyo" Imaan ta d'an yi murmushi tace "Toh Ammi
in sha Allah" Ammi tace "Ko xa ku dawo napep xa ku hau kin ji abinda nace koh?"
Imaan tace "Toh Ammi" daga haka ta fita parlon, ta nufi part din su Maimoon, a
hankali ta bude kofar ta shiga da sallama murya can kasa, Umma ce xaune parlon, sai
Mujaheed dake xaune shi ma ya jinginar da kansa da kujera idonsa lumshe, Safeenah
ma na xaune parlon tana taunar cingam, Umma tace "Toh ni na ta6a jin rashin lafiya
haka, bari Abbansa ya shigo kila idan yyi masa magana xai yarda a dubasa, su dama
likitocin nan haka suke da shegen taurin kai sai dai su duba wasu ba dai a duba su
ba" Safeenah ta tabe baki tace "Wllh kuwa Hajiya, har ce min yake ba ruwana in
daina sa masa ido, Toh ya baxan sa ido ba mijina ba lafiya, ko abinci bai ci fa
Umma sai dai coffee da tea mun fi sati a haka" Umma ta rike ha6a tace "Ba lafiya
kuwa, bari Abba ya shigo wannan ai ba yi bane" Imaan da ta sunkuyar da kanta ta
nufi stairs tace "Ina yinin ku" babu wanda ya tanka ta a parlon har ta wuce sama,
Umma ta kalli Safeenah, Safeenah tayi wani murmushi tana kas kas da cingam,
Mujaheed tunda ya ji muryarta ya bude ido, ba a dau lkci ba Imaan ta sakko tare da
Maimoon dake sanye da hijab ita ma har kasa, suna shigowa parlor Umma ta bi su da
kallo, Maimoon tace "Sai mun dawo Umma" Umma tace "Yauwa" Imaan dai bata juyo ba
har ta fita, Maimoon ma ta fita, Mikewa Mujaheed yyi yana kallon Umma yace "Bari in
je in gaida Inna in dawo yanxu" Safeenah ta mike tace "Ehh bari mu je Umma yanxu
xan dawo sai mu fita kasuwan" wani kallo Mujaheed ya dinga mata fuska daure yace
"Da can baki san xa ki part din Inna ba sai da nace xan je??" Safeenah ta tabe baki
ta nufi kofa tana gyara mayafin jikinta ya bi ta da kallo, imaan da Maimoon na isa
bakin titi suka tsayar da adaidaita, Imaan na kallon Maimoon tace "Wllh ban san me
yasa gabana ke faduwa ba tun daxu Maimoon" Maimoon tace "Haba dai, to ki dinga
addu'a" Imaan tace "Ehh Ina yi" daga haka ta kalli mai adaidaitan da suka
tsayar....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

66.....

A hanya imaan ta sa mai adaidaitan ya tsaya gun masu fruits ta siya fruits kusan
kala hudu sannan suka koma adaidaitan, Tafiyar kusan minti ashirin suka yi suka isa
wani babban hospital wanda kai kana gani kasan na masu hali ne, sauka suka yi a
adaidaitan kafin Imaan ta basa kudi daga cikin jakarta Maimoon ta basa, hakan yasa
Imaan ta ciro wayarta kawai ta shiga kiran layin Mariya, ba a dau lkci ba Mariya ta
daga, Imaan tace "Muna waje" Mariya tace "Ohk to gani xan fito yanxu" Imaan ta
mayar da wayar jakarta suka shiga haraban hospital din, ba a dau lkci ba Mariya ta
fito ta nufo su tana murmushi suka gaisa da fara'a suna tambayarta me jiki, Mariya
tace "Da sauki sosai, mu shiga ciki" bin bayanta suka yi har xuwa special ward din
da aka kwantar da step sis din nata, da sallama suka shiga cikin babban ward din
mai dauke da gado daya sai kujeru da karamin Tv na bango, ga labulaye a duk windows
din, gadon ma kadai dake dakin ya isa ya bayyana cewa ward din na special people
ne, Mahaifiyar Sadeeq Hajiya Khadijah ce xaune saman kujera, sai Aunty da frnd din
Mum din Sadeeq da kanwarta, Aisha kanwar Sadeeq na kwance saman gadon tana bacci an
sa mata drip, sai autar su Sadeeq din dake tsaye hannunta rike da incense da
ashana, Imaan ta sunkuyar da kai ta karasa cikin dakin da ladabi ta gaida su,
Hajiya Khadijah ta amsa tana kallonta, Aunty da sauran mutanen ward din ma duk suka
amsa, Aunty na nuna masu kujera tace "Toh ku xauna" Maimoon ce ya fara xama, Imaan
kuwa sai da sister din mahaifiyar sadeeq ta sake maimaita mata ta xauna sannan ta
xauna har sannan kanta na kasa, Mariya na murmushi tana kallon stepmother dinta
tace "Mummy ita ce budurwar ya sadeeq warce xai aura fa...." Mummy na kallon Imaan
da kyau tace "Wannan ba warce ku ka yi sauka tare bane kwanaki har muka yi hotuna"
Mariya tayi dariya tace "Ita ce Mummy ashe dai xa ki gane ta" Aunty dai sai
murmushi take tana kallon Imaan da ta kasa dago kai gaba daya she was uncomfortable
ba kadan ba, Mummy ta d'an yi murmushi tace "Toh Maa sha Allah, Allah ya sanya
albarka..." Mariya tace "Ameen, amma fa tun kafin saukan suke tare Mummy" Mummy
tace "Toh maa sha Allah, hakan yyi kyau" Aunty na kallon Imaan tace "Ya su mamanku"
a hankali tace "Tana gaishe ku" Aunty tace "Toh mun gode Allah maku albarka" duk
suka amsa da "Ameen" a hankali Imaan ta dago kai tana bin ward din da kallo jin
numfashinta na d'an tsarkewa, kanwar Sadeeq ta gani xaune chair din dake kusa da
wanda ta xauna hannunta rike da incense har stick biyu ta kunna, Imaan ta kauda
kai, sai kuma cikin dubara ta dan rufe hancinta da hijab din jikinta, Lkci daya
Maimoon ta lura da hakan, ta taba ta murya can kasa tace "kiyi masu sallama mu wuce
kawai" kasa cewa komai Imaan tayi, su Aunty dai hiransu kawai suka ci gaba da yi,
Maimoon ta mike tana kallonsu tace "Toh mummy xa mu koma, ga wannan a ba mara
lafiya, Allah ya bata lafiya" tana magana tana ajiye ledan hannunta a table, Aunty
tace "Har xa ku tafi, to mun gode Allah ya saka da alkhairi" Mummy tace "Toh mun
gode, ku gaida gida da mutanen gida" tuni Maimoon ta kama hannun Imaan tana amsa
masu da Ameen, Mummy na kallon Imaan da murmushi tace "Toh ya sunan naki?" Maimoon
tace "Fatima Imaan" Imaan ta warce hannunta daga rikon da Maimoon ta yi mata ta
nufi kofa da sauri dai dai lkcn da aka bude kofar ward din Sadeeq ya shigo, bata
kai ga fita ba ta durkushe bakin kofa ta fara gasping for air tana tari, Mariya da
Maimoon suka nufeta da sauri, Su Aunty da Mummy ma duk suka mike suna salati suka
nufeta, Sadeeq ya xura wayarsa aljihu ya durkusa kusa da ita ya dagota yana
kallonta yace "Subhanallah, Imaan are you okay..." Mariya ta kashe incense din
hannun Step sis dinta, a nan kuma duk suka dago musabbabin tashin Asthma din nata,
ba karamin tausayi Imaan xata baka ba ganin yanda take struggling da numfashin nata
a kasa, gaba daya su Mummy da Aunty da mutanen dake ward din duk suka rikice,
Maimoon ta durkusa ta cire jakarta dake rataye shoulder dinta ta bude da sauri tana
bincika ciki ko akwai inhaler amma taga babu, ganin haka Sadeeq ya daga ta ya fitar
da ita daga ward din, Aunty ta bi bayansa ita ma hankali tashe Maimoon da Mariya ma
suka fita, cike da damuwa Mummy tace "Ai ba a san she is asthmatic ba, da Suhaila
bata kunna turaren ba, kuma duk sai suka yi shiru basu ce komai ba" Kanwar Mummy
tace "Wllh kuwa, irin haka ai magana xa su yi, gashi an ja mata wahala yanxu" Kawar
Mummy tace "Ikon Allah shi kuma Sadeeq ana neman mai lafiya ya jajibo ma kansa ciwo
Allah na tuba, dubi fa d'an hayakin da ya tada Asthma ni fatima Allah na tuba,
kenan wannan dai ko shara bata yi balle aje ga soye soye a kitchen, don in dai
wannan hayakin xai iya tada Asthma to fa babu abinda baxai tayar ba, Toh Allah dai
ya kyauta, Allah kuma ya bata lafiya" Mummy dai bata ce komai ba haka kanwarta da
ta mike ta bi bayansu Aunty. Sadeeq na xaune gefen Imaan dake kwance daya daga ward
din hospital din, ban da juye juye babu abinda take yi har sannan da kyar take
numfashi, Aunty sai sannu take mata tana kallonta cike da tausayinta, Mummy dai na
tsaye jikin window ta rungume hannu tana kallonta ita ma, Mariya har da d'an
hawayenta, Maimoon na kusa da sadeeq ta kama hannunta tana tofa mata addu'a a
hankali, wani likita ne ya shigo ward din yana kallon Imaan yace "Sit upright now"
Sadeeq ya mike don ta samu ta tashi xaune, da taimakon Maimoon ta xauna, likitan
yace "How are you feeling now" Bata iya tace komai ba, A hankali Sadeeq yace "She
said her chest..." Murmushi likitan yyi ya dafa Sadeeq yace "Anya kuwa Dr idan
emergency ya tashi gidan ku cikin dare xaka iya ta6uka abun kirki?" Aunty ta ta6e
baki tace "Haka nan yake wllh Dr, ni ban ta6a ganin likita haka ba, gaba daya mance
cewa shi likita ne yake in a situation like this" Dr din ya d'an yi dariya yace
"Gaskiya ne..." Ya maida dubansa gun Imaan da ta hade kanta da pillow yace "Amma an
ta6a maki allura idan Asthma din ki ya tashi ba inhaler a kusa?" Bata tare da ta
dago ba ta gyada masa kai da kyar, Yace "Toh Allah ya sauke, xai daina in sha Allah
mun baki magani ai... Allah ya baki lafiya" Ita dai bata ce komai ba, likitan na
kallon Sadeeq yace "Nan da few hours xa a sake shigowa duba ta Dr... Allah ya
tsare, sai a dinga kiyayewa" Sadeeq ya d'an yi murmushi yace "In sha Allah" daga
haka likitan ya fita yana kara gaida su Mummy, Sadeeq ya duka yana kallon Imaan,
murya can kasa yace "Sorry dear" ita dai bata ce komai ba, yace "Toh kwanta da
kyau" sai a sannan ta dago kanta a hankali ta kwanta tana sauke numfashi a hankali,
Mummy dai sai kallonta take haka ma Aunty, can Mummy tace "Toh Allah ya sauke, bari
in koma daya ward din" daga haka ta fita, Aunty ta ja kujera ta xauna, nan da nan
bacci ya dauke Imaan. Maimoon dake xaune kan kujera tare da Mariya suna kallon
Imaan ta fiddo wayar Imaan dake ring a jaka, number Ammi ta gani a screen, ta daga
ta kai kunne tayi sallama murya can kasa, a hankali Ammi tace "Imaan din fa
Maimoon?" Maimoon tace "Wlh Ammi ta sami attack ne a hospital din, amma da sauki
yanxu tana bacci ma" Mahaifiyar Mariya dake ward din har sannan tana duban Maimoon
tace "Kawo wayar" Mikewa Maimoon tayi ta tafi ta kai mata wayar, bayan sun gaisa
Aunty tayi mata bayanin abinda ake ciki tace "Amma da sauki Alhmdllh don har tayi
bacci, xuwa anjima in sha Allah xa a taho da su gida" Ammi tace "Toh maa sha Allah,
an gode sosai, Allah ya saka da alkhairi" Aunty tace "A'a ba godiya Hajiya, mu ma
mun gode" daga haka suka yi sallama Aunty ta mika ma Maimoon wayar, kusan la'asar
Sadeeq ya shigo ward din rike da ledan drugs, Maimoon da Mariya ne kadai dakin
Aunty ta tafi gun su Mummy, Har ya karasa gun Imaan kallonta yake ganin yanda ta
takure waje daya, ya kai hannunsa forehead dinta, sosai ya ji jikinta da xafi, ta
bude idonta da suka kada tana kallonsa, lips dinta ma yyi ja sosai, dukawa yyi da
damuwa yace "Are you okay imaan, har yanxu kirjin na maki ciwo ne" kokarin tashi
xaune ta shiga yi da kyar tana dafa bayanta, ya kama hannunta ya taimaka mata ta
tashi, ganin yanda ta rufe ido yace "Ina ke maki ciwo??" Murya can kasa tace "I am
feeling internal heat, kuma Ina jin sanyi, my back is aching" Shiru yyi yana
kallonta cike da tausayi, can ya juya ya fita suka dawo tare da likita, a dakin ya
tadda Mummy xata wuce gida ta dawo anjima shine ta shigo yi masu sallama, tana
tsaye kan Imaan ganin yanayinta tana kallonta tace "Wani abun na damun ki ne kuma?
Ko kina jin ciwo a wani waje ne?" Imaan ta girgixa mata kai da kyar bata ce komai
ba, likitan ya karasa ya kai hannu jikinta yana kallonta yace "Me kike ji a jikin
ki?" Imaan ta girgixa masa kai a hankali hawaye cike idonta tace "Kawai ina son xan
wuce gida" Sadeeq yace "Noo ki fada masa inda ke maki ciwo" da kyar tace "Joint
pain, kuma Ina jin xafi a jikina...." Likitan ya kai hannu forehead dinta yana
kallonta, yace "Yana maki haka ne?" Kai ta gyada masa, yana kallon kwayar idonta ya
d'an yi shiru sai kuma ya kalli Sadeeq yace "Is she a sickled cell patient?" A
hankali Sadeeq ya girgixa masa kai yace "She is only carrying the trait" Likitan
yace "Wani drugs kike sha a gida?" Cike da karfin hali tace "Suna da yawa" likitan
yace "Did you know their names?" Sadeeq yace "I will get drugs for her now, amma
ayi mata allura" daga haka ya juya ya fita ward din. Aunty ce ta sakko parlor sanye
da hijab hannunta rike da purse, ta kalli Mujaheed tana amsa gaisuwar da yake mata
a parlorn sannan ta kalli Umma tace "Xan fita sai na dawo Hajiya" Umma tace "Ina
kuma xa ki da magariba" Aunty tace "Xan je dubiya asibiti ne" da mamaki Umma tace
"Waye ba lafiya?" Aunty tace "Baki san su ba" Dai dai nan Abba ya shigo parlon yana
kallon Aunty yace "Ba ku tafi ba kenan" Aunty tace "Ehh yanxu xa mu fita" Abba yace
"Xuwa anjima idan anyi isha xan leka asibitin" Umma na kallon Abba tace "Wai waye
ba lafiya" Abba ya kalli Aunty yace "Bata sani ba ne dama?" Aunty bata tanka sa ba
ta nufi kofa, Abba ya girgixa kai yace
"Imaan ce suka je duba kanwar yaron nan dake nemanta a asibiti shine Asthma dinta
ya tashi, ita ma dai tana asibitin yanxu" Kallonsa kawai Mujaheed yake ko kiftawa
babu, Umma ta saki salati tana tafe hannu tace "Shine ake boye min, shi ciwon Amina
ke boye min fisabilillahi? Meye amfanin xaman munafurci Alhaji, wato ita ta ji xata
tafi dubata a asibitin ni kuma sai uwar yarinyar da Inna su kullace ni su xata naji
xuwa ne bana son yi, toh xuciyata bai kai haka lalacewa ba, kuma nima yanxu xan
shirya mu tafi, sai dai ita ta ji kunya, ban taba ganin munafuka irin Amina ba
wllh, duk ita ke hada ni da Aisha na lura" Shi dai Abba ko tanka ta bai yi ba ya
wuce parlon sa, Umma ta wuce sama da sauri don dauko hijab, Mikewa Mujaheed yyi ya
fita parlon ya bi bayan Aunty, tare ya gansu suna tahowa da Ammi dake sanye da
hijab ita ma, yana tsaye har suka iso, ya gaida Ammi ta amsa tana tambayarsa ya
aiki, yace "Alhmdllh, ya mai jiki" Ammi tace "Toh da sauki" a hankali yace "Toh mu
je in ajiye ku" Aunty tace "Toh ka kyauta" dai dai nan Umma ya fito parlon sanye da
hijab ita ma, tana kallon Aunty tace "Toh Amina xuciyata bata kai inda kike tunani
ba lalacewa, rashin lafiya Kuma da ke kan kowa kike boye min fisabilillahi??" Aunty
ko kallonta bata yi ba ta nufi gate, Ammi dai bata ce komai ba ita ma tafiyar take,
Umma tace "Munafurci dai bashi da amfani a rayuwa, kuma tare kika shigo gidan nan
kika ganmu da Aisha" daga haka ta kalli Mujaheed tace "Kai xaka kai mu ne" ba tare
da ya kalleta ba yace "Ehh" har suka shiga motar tasa babu wanda yace komai, Aunty
ta gaya masa asibitin bayan sun hau saman titi. Maimoon ce ta fito ta kai su har
ward din da imaan take, Mummy na xaune saman kujera kusa da gadon da imaan take
kwance tana bacci, sai kannin Sadeeq biyu da kanwarta da Mariya, Su Aunty na shiga
ward din Mummy ta fara welcoming din su, a ka shiga gaisawa fara'a, Umma dai sai
kallon Mummy take, Mummy tace "Jikin ma da sauki sosai, kawai drip din ne da bai
kare ba, don sunce biyu ne" Aunty tace "Toh Alhmdllh, Allah ya sauwake, ku kuma
Allah ya bada lada" Mummy tayi murmushi tace "Toh Ameen, Allah ya bata lafiya"
Mujaheed dai na tsaye daga bakin kofa yana kallon Imaan dake bacci tana sauke
numfashi a hankali, da sallama Sadeeq ya shigo ward din....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

67....

Sadeeq ya gaida su Aunty da ladabi, sannan ya gaida Umma ma dake ta kallonsa, Umma
tace "Lafiya lau, ya hidima?" Yace "Alhmdllh" Umma tace "Toh Allah ya bata lafiya,
ku kuma Allah ya sassaka da dawainiya, a haka nan dai ake kullum yau ciwo gobe
lafiya, an rasa gane kan abun dai, Allah dai ya rabata da wannan cuta da ya ki ci
ya ki cinyewa ni Rukayya" Mujaheed dake ta kallon mahaifiyar tasa ya karasa cikin
ward din xuwa gadon da imaan take tana bacci ya tsaya yana kallonta, ya kai hannu
goshinta ya ji babu xafi bacci dai take mai nauyi, Umma dai sai wani kallo take
masa ta gefen ido, Aunty na kallon Mummy tace "Toh Hajiya tunda kuna nan mu xa mu
koma, Allah ya saka da alkhairi, mun gode kwarai" Mummy na murmushi tace "Ah haba
dai ba komai ai yi ma kai ne, Allah dai ya bata lafiya, ya ba mu alkhairi" Ammi ma
tayi mata godiya hade da sallama, Umma da ke xaune ta ki tashi ta bi su da kallo
baki sake tace "Sai kace ana koranmu ko tashi yarinya bata yi ba balle mu ga
lafiyarta ku ce xa mu wuce?" Can ta tabe baki tana gyara xama tace "Atoh ku je ni
sai na xo" Ita dai Ammi bata ce komai ba har ta fita Maimoon ma ta fita, Mujaheed
dai sai kallon uwar tasa yake daga inda yake tsaye, Aunty dake ta kallonta ta dai
nufi kofa tana danna wayarta, suna fita ward din ta kai waya kunne bayan wani lkci
tace "Toh ga Matar ka can gaban surukai tana maganganu da bai dace ba a kan ciwon
'yar ka, mun fito yanxu xa mu tafi tace babu inda xata kawai dai don ta samu
sararin ci gaba da rashin kirkinta a wajen, idan ma xaka kirata to ka kirata ta
fito ward din nan, Banda ma kinibibi da can duk ciwon da Imaan take ta ta6a bin mu
asibiti...." Bata jira cewarsa ba ta kashe wayarta fuska daure, Ammi dai sai
murmushi take suna tafiya, ko minti daya ba ayi ba Abba ya kira Umma dake kallon
Mummy tana cewa "Mun gode fa, Allah ya saka da alkhairi ya bada lada, abun kam sai
addu'a yau ciwo gobe lafiya ana dai ta tafiya a haka..." Ring din wayarta yasa tayi
shiru tana kallon screen din, can ta daga ta kai kunne kafin tace komai Abba yace
"Rukayya ku dawo gida yanxun nan gaba daya" a hankali tace "Ko saboda me?" Strictly
yace "Nace ki dawo yanxu Madam" tace "Toh" daga haka ta katse wayar tayi tagumi
tana kallon Imaan bayan kusan minti uku ta mike tana murmushi tace "Toh, Hajiya
tunda sun ce mu tafi bari mu wuce don a mota daya muke, ma dawo da safe, Allah ya
saka da alkhairi" Mummy tace "Toh Ameen, Allah ya tashe mu lafiya, sai da safen" Da
ido Mummy ta bi ta har ta fita kafin ta dauke kai, Mujaheed dai na tsaye kusa da
gadon har sannan idonsa na kan imaan, Sadeeq dake tsaye ya ja kujera ya xauna,
Mummy na kallon Mujaheed da murmushi tace "Kanwarka ce koh?" Murmushin yyi shi ma
yace "Ehh kanwata ce" Mummy tace "To madallah, ga kujeru ka xauna" Yana kallon drip
din da aka sa mata yace "Am comfortable ma" tace "Toh yyi kyau" Mariya ce ta shigo
dakin rike da warmer din abinci ta ajiye tace "Bata tashi ba har yanxu?" Mummy tace
"Eh bata tashi ba" Mariya na kallon Mujaheed tayi murmushi tace "Ina yini Dr?"
Mujaheed ya mayar mata murmushin yace "Lafiya lau Mariya" Mummy na kallonsa tace
"Kai ma likitan ne kenan" shafa kai kawai yyi yana murmushi, Mariya tace "Ehh Dr
ne, a Chasel hospital yake aiki" Mummy tace "Maa sha Allah, that's good" Shi dai
Mujaheed bai ce komai ba, Sadeeq dai sai danna wayarsa yake babu yabo bbu fallasa,
Mujaheed ya kalli agogo yace "Xan je in yi isha, xuwa anjima xan dawo in sha Allah"
Mummy tace "Toh sai ka dawo" daga haka ya nufi kofa ya fita, Mummy na kallon Sadeeq
tace "Are they of the same mother?" Girgixa kai Sadeeq yyi har sannan yana danna
waya, Mummy tace "Stepmother dinta ce warce ta fita yanxu?" Sadeeq ya kalleta yayi
d'an murmushi yace "Not at all, mum din shi wanda ya fita ynxu ne" Mummy bata kuma
cewa komai ba. Karfe takwas da rabi Imaan ta farka daga baccin da take, har sannan
Mummy na xaune kusa da ita tare da Suhaila sai sadeeq dake xaune idonsa a kan
wayarsa, Aunty kuma na can gun Aisha Kanwar sadeeq dake kwance daya ward din, Mummy
na kallonta tace "Sannu, ya jikin?" Ta d'an yi murmushi tace "Na ji sauki" Mummy
tace "Toh Allah ya sauwake" Shi dai Sadeeq kallonta kawai yake, ta mike xaune a
hankali tace "I want to use the restroom" Mikewa Sadeeq yyi ya cire tube din ruwan
ta sakko daga saman gadon tana dafa gado sbda jirin da ta ke ji, Mummy dai sai
sannu take mata, Suhaila xata kama hannunta tayi murmushi tace "Xan iya" daga haka
ta wuce bathroom dake ward din tana dingishi, Mummy dai ta bi ta da kallo, Da
alwala ta fito bathroom din ta karasa kan gado ta dau Hijab dinta dake linke, Mummy
tace "Sllh xa ki yi?" Imaan ta gyada mata kai, Mummy ta kalli Suhaila tace "Ki tafi
can ward din ki dauko darduma" Mikewa Suhaila tayi ta fita, shi dai Sadeeq sai
kallon Imaan yake, ita kuwa bata yarda ta kallesa ba, Mummy ta nuna mata kujera
tace "Toh xauna kafin ta dawo" ba musu ta xauna saman kujeran, ba a dau lkci ba
Suhaila ta dawo da pray mat ta shimfida mata. Imaan na xaune pray mat din bayan ta
idar da sllh, Mummy ta bude warmer ta debi hadadden jollof rice da Mariya ta kawo
daga gida ta sa mata da enough meat, Mummy tana kallonta tace "Toh tashi ki hau
saman gado ki ci abincin" Mikewa Imaan tayi ta hau saman gadon ta mika mata abincin
ta amsa a hankali tace "Nagode" Suhaila tace "A hada maki shayi?" Girgixa kai Imaan
tayi tace "Wannan ya isheni" Bude kofar ward din aka yi Abba ya shigo da sallama
tare da Maimoon, Sadeeq ya mike har ya iso cikin dakin Abba yayi ma Mummy sannu ta
amsa tace "Sannu da xuwa" gaishesa Sadeeq yyi Abba ya amsa da fara'a yana
tambayarsa mai jiki, sannan ya kalli Imaan dake kallonsa yace "Sannu Mamana, how
are you feeling now" tana murmushi tace "Na ji sauki Abba, Ina yini" yace "Lafiya
lau, Allah ya kara lafiya daughter" Mummy tace "Ina yini Alhaji" Abba yace "lafiya
lau, ya masu jiki" tace "Alhmdllh da sauki sosai" yace "To madallah, Allah ya basu
lafiya, Allah kuma ya bada lada" Mummy tace "Ameen" Maimoon ta ajiye ledan fruits
dake hannunta tana kallon Imaan tace "Sannu" Murmushi imaan tayi mata, Abba yyi ma
Mummy sallama yace xai shiga ya duba sis din Sadeeq, Mummy tace "Tou mun gode
Alhaji" yana kallon Imaan yace "Sai da safe Mamana, Allah ya kara lafiya" ta amsa
da "Ameen, thanks Abba" tare suka fita da Sadeeq da xai kai sa gun sis dinsa. Basu
kai minti biyar da fita ba Mujaheed ya shigo dakin hannunsa rike da leda, Tun da
suka hada ido Imaan ta sunkuyar da kanta, ya karaso ciki yana ma Mummy sannu, Mummy
tace "Har ka dawo" yace "Ehh na dawo" Yana kallon Imaan da taki yarda ta kallesa
yace "How are feeling now" still bata kallesa ba tace "Na ji sauki" ya ajiye ledan
hannunsa a table, yana silencing wayarsa dake ringing, Mummy ta nuna masa kujera
tace "Toh ka xauna koh" ya d'an yi murmushi ya xauna saman kujeran, Imaan dai sai
juya abincin gabanta take, Mummy tace "Ba fa cin abincin kike ba" diba tayi ta kai
baki ta dago kai tana kallon Mujaheed dake kallonta, a hankali ta dauke kanta tana
cin abincin. Sai kusan karfe goma Sadeeq ya dawo dakin, Tun da ya kalli Mujaheed
sau daya ya dauke kai yana kallon Mummy yace "Xa a mayar da ke gida ne tunda
Suhaila da sis dinta na nan?" Mummy tace "Don't worry nan da anjima sai in tafi"
Yace "Ohk" karasawa yyi kusa da Imaan murya can kasa yace "Ba inda ke maki ciwo
ko?" Ta gyada masa kai kawai, yace "Ohk, xan je gida in dawo yanxu, I want to
freshen up" ta kallesa tace "Ohk" murmushi ya sakar mata ta sunkuyar da kanta, ya
juya yana kallon Mummy yace "Xan dawo ltr mum" daga haka ya nufi kofa Mummy tace
"Toh ai ba ku yi sallama da Dr ba" Juyowa sadeeq yyi ya kalli Mujaheed yace "Ohh I
didn't notice him, see ya ltr..." Mujaheed ya d'an yi murmushi yace "Alright" Daga
haka ya fice daga ward din. Imaan ta daga kai ta kalli Mujaheed taga kallonta yake
ta turo baki ta dauke kai, Mujaheed bai bar hospital din ba duk da kiran da
Safeenah da Umma suka dinga lafta masa, ya kuma ki dagawa, har sai da Umma ta kira
Maimoon tace ta kai masa waya, Maimoon na kallonsa ta mika masa wayar tace "Ya
M.A...." amsan wayar yyi ya kai kunne, cike da bala'i da masifa Umma tace "Mujaheed
wai Kanwar Uwarka ko ta ubanka ce kwance gadon asibiti???" Shi dai bai ce mata
komai ba, rai bace tace "Tun raina bai gama baci gaba daya ba ka kama hanyar gidan
ka yanxun nan, ka bar yar mutane can ita kadai tsakar dare kamar ni ce kwance ba
lafiya a gadon asibiti, ko meye hadin ka da sauran ciwon?" Mujaheed bai ce komai ba
ya katse wayar ya mika ma Maimoon ta amsa, Mujaheed bai bar asibitin ba duk da
fadan Umma sai kusan Sha daya da wani abu, shi ma Mummy ce tace masa amma ba shi da
family, Bai bata amsa ba sai murmushi da yyi ya mike yace "Toh sai da safe, Allah
ya bada lada" tace "Ameen" Imaan dake kwance ta rufe ido kamar mai bacci, ta bude
idon ta bi sa da kallo har ya isa kofa, sai kuma ya juya ya kalleta, da sauri ta
rufe idon, har xai fita sai kuma a hankali tace "Sai da safe" Yana kallonta yace
"Allah ya tashe mu lafiya" daga haka ya fita ya rufe kofar. Washegari aka sallami
Imaan karfe sha daya na safe, Stepmum din Sadeeq da su Suhaila ne suka kai ta har
gida, Ammi tayi masu godiya tare da Aunty, basu wani jima a gidan ba suka wuce
tunda tare suke da driver. Bayan sati daya da yayi dai dai da saura sati guda a
kawo lefen Imaan.... Umma ce xaune makeken parlon gidan Bulasawa tare da Hajiya
Balaraba sai Safeenah da ta ke ta taunan cingam ta ci kwalliya iya kwalliya tayi
kyau, ba don Suhaila da ta gansu bakin gate a tsaye ta dawo boko a motarta ba da
babu yanda xa ayi a barsu su shigo gidan don masu gadi sun ce ba a sanar da su xa
ayi bak'i ba, ynxun ma sun fi minti sha biyar xaune parlon suna jiran fitowar uwar
gidan Bulasawa, duk sun yi shiru kamar masu xaman makoki, can dai Hajiya Saude na
kallon Umma murya can kasa tace "Anya shawarar nan tayi kuwa Hajiya Rukayya??" Umma
na kallon Safeenah tace "Ni ban kawo hakan a kai ba fa, sai da Safeenah ta kawo
shawarar, kuma jikina ya bani da nasara...."
Safeenah ta tabe baki tace "Ku dai ba ni nace ayi haka ba?? ku kwantar da hankalin
ku kawai, na fa san abinda nake, haka kawai ga hanya mafi sauki kuyi ta kai ma
katti kudin ku suna cinyewa, har yanxu ban ga alamar abun da ake ta ce maku ba
gashi saura sati a kai lefe a sa rana, ga dai hanya straight...." Umma tace "A'a
wllh babu me cinye min kudi, ana biya min bukatata yanda ya kamata... So nawa
kuma??" Shigowar Mummy parlon sanye da hijab har kasa yasa duk suka yi tsit,
kallonsu ta dinga yi har ta karaso ta xauna saman kujera, Umma na murmushi tace
"Sannu da fitowa Hajiya" Mummy tace "Yauwa daga Ina?" Umma tayi yar dariya tace
"Lahh, baki gane ni ba Hajiya??" Mummy dai sai kallonta take don sarai ta gane ta,
can kuma ta girgixa kai tace "A'a ni ban gane ku ba, daga Ina?" Umma tace "Toh ni
dai sunana Hajiya Rukaiya, in dai kina jin Barrister Ahmad Yusuf na nan kaduna to
Mai gidana ne..." Mummy bata daina kallonta ba tace "Ohk..." Umma tayi kasa da
murya tace "Hajiya a matsayina na yar uwar ki musulma na xo maki taimako albarkacin
musulunci..." Da mamaki Mummy tace "Taimako kuma? Wani irin taimako nace maki ina
bukata??" Umma ta gyara xama tace "Hajiya don nace na xo maki taimako ba ina nufin
kudi ko wani abu gareni da xan baki ba don kin fi karfinsu, amma ki sani wllh wllh
taimakon nan sai ya fi maki kudi ko wani abu na kyale kyalen rayuwa... Hajiya kin
san shi aure ba abu bane da xa ayi na rana daya a gama ko na wata daya, A'a rayuwa
ce da ake fata ya xama na har abada, kin ga wannan yarinyar da d'an ki ke nema??"
Ita dai Mummy kallonta kawai take, Umma tace "Toh wllh wllh kin ji rantsuwar
musulmi sickler ce, sannan kin ga yanda kika ganta ita kadai, to har gun iyayenta
ita kenan takk... uwar ta fi shekara 13 bata haihu ba, kafin daga karshe taje ta
san abinda ta yi Allah ya bata yar, wanda da Allah ya tashi kamata ya hadata da
sickler, har yau kuma wllh tllh uwar ta hana uban karin aure kiri kiri, sannan babu
wanda bai san abinda take ba, daga ita sai yar suke yanda suka ga dama a daulan
uban, matar kanin mijina ne uwa daya uba daya, kin ga dai ba kishiyata bace ita
balle ace ina ma 'yar ta bakin ciki, ko daya wllh ba haka nake ba, gaskiya ce duk
inda take sai na fade ta, yanxu haka maganar da nake maki d'an kishiyata Yusuf ni
ce kan gaba gun nema masa aure gidan Alhaji Mukhtar Kiyawa da kika sani dai na nan
garin, wllh wlh mahaifiyar yarinyar nan ba mutuniyar kirki bace muguwar bafillatana
ce ta karshe, kije anguwar mu malali ki shiga gidajen layinmu kaf kiyi tambaya a
kanta xa ki sha labari, tayi kadan in mata hassada wllh balle ace ko hassada nake
mata, Bari ki ji Hajiya wllh a ta dalilin ta Mai gidana ya min kishiya, ta cusa
masa aminiyarta ina ji Ina gani ta aure min miji, ita kuma taki barin a mata
kishiyar har yau gashi ba haihuwa take ba, ita ma kuma ita kenan gun uwarta, sae
gashi ta haifi kwaya daya ita ma, kakar yarinyar ma gwaggwo ita kadae iyayen suka
haifa aka ce, kamar yanda baxan so Mujaheed da abinda xai cutar da shi a rayuwa ya
xame masa wahala ba haka baxan so ma duk wani matashi ko da ba ni na haifesa ba, a
wata wllh uban yarinyar na kashe mata kudi ya fi dubu dari biyu, kullum cikin abu
daya ake idan ciwon ya matsa mata kuwa ke kya ce baxata yi ba, shi sa nayo tattaki
in sanar maki ki ceci d'an ki, barin ma shi da yake d'an ki na fari....."

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

68......

Umma tayi shiru tana kallon Mummy tana jiran jin abinda xata ce, sai dai fa gabanta
faduwa yake, Safeenah da Hajiya Saude ma kallonta suke su ji abinda xata ce, Mummy
da tayi shirun kusan minti biyu ta sauke ajiyar xuciya daga karshe tace "Alright, I
will look into the matter, nagode da shawara" Umma tace "Atoh, banda mai sonka wa
xai kawo maka haka har gida, yanxu xamani ya lalace mutane basu son fadin gaskiya
ga ta nan dai kiri kiri ana ganinta, wllh bbu wanda bai san abubuwan nan da na gaya
maki ba amma sai mutune su yi gumm su xuba ido, to mu ba mu gaji haka a xuri'ar mu
ba gaskiya" Hajiya Saude tace "Wllh ko a gaban uwar yarinyar ce xa mu iya fadin
abinda Hajiya Rukayya ta fada maki a nan tunda ba tsoronta mu ke ba, gaskiya ne dai
sai mun fada, sam matar bata da hali, makirace ba ta wasa ba, yanxu haka ita gani
take ta ci nasara tunda bbu wanda ya isa ya fito ya fadi aibunta duk ta rufe bakin
kowa...." Mummy tace "Na ce maku xan yi shawara ai koh?" Umma tace "Toh Allah ya
baki ikon yin wanda baxa ki dawo kina da kin sani ba wataran, Allah kuma nuna maki
duk abubuwan da muke fada da idon ki, kai ko spy mace ne xa ki iya biya ta dinga
shigowa gidan namu taga wainar da ake toyawa, wllh wllh duk ta mallake gidan......"
Daga haka ta mike tana murmushi tace "Nagode da lkcn da kika bani Hajiya, Allah
ubangiji ya mana xabi nagari..." Tana nuna Safeenah tace "Yar wajen Hon Usman
Basiru ce wannan... Kuma surkata ce d'ana na fari ke aurenta, yanxu haka sun kusa
wata uku da aure" Mummy na kallon Safeenah tace "Maa sha Allah, that's nyc, Allah
ya bada xaman lafiya" Safeenah ta mike tana amsawa da Ameen, Hajiya Saude ma ta
mike nan suka yi ma Mummy sallama, Mummy tace "Toh nagode, sai anjima" Umma tace
"Mu jima da yawa Hajiya" kofa suka nufa kafin su isa kofar Sadeeq ya shigo parlon,
kallon Umma ya dinga yi da mugun mamaki da su Safeenah, Umma ta sunkuyar da kai ta
fita parlon su Hajiya Saude na biye da ita, Sadeeq na kallon Mummy ya karasa cikin
parlon ya xauna har sannan fuskarsa na dauke da surprise yace "Mum what is she here
for??" Mummy tace "It's not necessary you know Sadeeq" ya mike cike da damuwa yace
"Why will u say so mum, don Allah ki gaya min me ta xo yi?" Mummy ta mike tace
"Nace maka it's not necessary Sadeeq, I am busy upstairs pls" daga haka ta wuce ya
bi ta da kallo, a hankali ya koma kan kujera ya xauna ya jinginar da kansa jikin
kujeran ya rufe ido xuciyarsa na bugawa.
Bayan kwana biyu Sadeeq ya shigo part din mum dinsa ya ganta da sisters dinta da
few frnds a parlor suna xuba lafiyayyu kuma tsadaddun kayan lefen da aka yo daga
Dubai cikin boxes set shidda sau biyu, sosai boxes din suka yi kyau sannan they
look sooo unique kana gani kasan ba da kudin wasa aka siye su ba, Mummy na kallonsa
tace "Perfumes da kace xaka Karo fa??" Yana dai tsaye yace "Ohk suna wajen Aunty"
ta masa wani kallo tace "Wajen Aunty Kuma?? Me ya kai su can?" Shiru yyi bai ce
komai ba, Kawar Mummy Hajiya Farida tace "Toh Aunty ce ta nemo maka mata da xaka
bata kudin siyan turarurruka, kai sai samm baka san ciwon kanka ba Sadeeq, kila ma
har ka hada yarinyar da ita Auntyn koh?? tunda ga kanwar uwarka" Shi dai bai ce
komai ba, ya juya ya fita, Mummy ta bi sa da harara, Hajiya Farida tace "Ni fa ban
ji dadin da tasan yarinyar tun a asibiti ba wllh, Bai kamata ta san komai ba a
maganar auren nan"
Imaan na xaune dinning misalin karfe sha daya na safiyar lahadi tana answering
past questions din gabanta kasancewar gobe xa su fara waec, aka bude kofar
parlor.... Inna ce ta shigo parlon da sallama Imaan na kallonta har ta karaso ciki
tana tabe baki murya can kasa tace "Ko turaren wuta bana jin an sa ma parlon nan
yau, dama fa tsafta sai wanda Allah ya so da Rahama yake ba ma, mu dai mun gode
masa....." Imaan tace "Toh ba sai ki sa mana ba tunda ba mu sa ba" da sauri Inna ta
juya ta kalleta, Bata dai ce komai ba ta xauna saman kujera, Imaan ta ajiye pen din
hannunta ta shigo parlon tace "Ina xa ki je da sassafe haka?" Inna tace "Ina xan je
kuwa da ya wuce gidan Mujaheed, wa gare ni banda Allah sai shi, jiya fa haka ya xo
bashi da isasshen lafiya duk ya rame sai 'yan idanuwa, ya xama wani tsololo da shi
sai tsayi kamar pal waya, ni dai ba ruwana wllh, Mujaheed da ko ciwon kai da kyar
ka ji yana yi sai gashi duk ya xabge haka kamar ana cin namansa, ni ko nace anya
matar nan ba mayya bace aka lika masa ya aura kuwa?? Tun fa da aka yi auren yake a
haka yau lafiya gobe babu, toh ni dai yanxu gidan xan tafi idan ma Safara'u mayya
ce muna hada ido xan gane, mayu kuma wasu iri ne ba mu kara da su ba a duniya, Ni
wllh har dambe nayi da mayya, kuma da kyar idan Safara'u ba mayya bace" Imaan dake
kallonta da mamaki tace "Mayya kuma Inna" Inna tace "Oh oh Allah, to idan ba mayya
bace mecece, ce min yayi fa bai san me ke damunsa ba da na tsare sa jiya, wllh da
barbajin gaskiya a xancena, ni dai duk abinda ya samu Mujaheed ni ya sama kuma
baxan xuba ido haka ba, a kan Mujaheed sai duk in tada gidan nan Al-quran, ni bai
fiye min kowa sau dubu dari biyar ba aka ce maki, idan xa ki tafi ki shirya ki tafi
ki shirya mu tafi gidan yanxu in san abun yi, dama kuma ki taho da takadda da biro
duk yanda muka yi da shegiyar matar xa ki rubuta min, don tambayoyi xan mata na
dangin uwa da uba, a nan xa a gano tushen abun...." Xaunawa imaan tayi tana
kyalkyala dariya sosai, Inna ta wani hade rai tana kallonta tace "Amma ke kam baki
da da'a, Meye abun dariya a nan jikana na can rai a hannun Allah, Toh ni fa wllh a
kan Mujaheed sai ince a fasa kawo kayanki da sadaki yau ba ruwana, haka kawai
jikana ba lafiya xa a cika ma mutane gida da jama'ah... Bari ma in je in sami
Ahmadu yanxu tunda ke matar banxa ce baki da mutunci" wani kallo Imaan tayi mata
tace "Toh ni ce bani da lafiya da xa a fasa kawo kaya???" Inna ta saki baki tana
kallonta, can ta mike tana kwalo ma Ammi kira, Ammi ta fito da sauri tana amsawa,
rai bace Inna na nuna mata Imaan tace "Wllh jaraba kika haifa Aisha, mu dai kaf
danginmu babu butulu wllh ban dai san ya naku yake ba, gaskiya imaan butulu ce,
banda haka kiri kiri ta fito ta nuna ciwon d'an uwanta bai dameta ba saboda tana
6arin jiki tayi aure, baki ta6a xaunar da ita kin bata labarin irin bakar wuyar da
Mujaheed ya sha da ita tun tana tsummarta bane wai? Ni dai wllh a dinga jin tsoron
Allah, wllh baki xaunar da ita kin sanar mata ba da baxata fifita aure kan d'an
uwanta na jini ba, idan ban sa an fasa kawo kaya ba gidan nan yau a kan Mujaheed
ace ba ni bace, lefen banxa da hofi jikana ya fi lefe ne, wllh jiya baccin kirki
ban yi ba sai da safe bacci ya kwashe ni, ban tashi ba sai daxu na shirya a gurguje
na taho ta raka ni gidansa in ga abinda yake ciki, nace to ko ma matar ce mayya xan
je in ga" Imaan ta tabe baki tace "Ba fa inda xan je gobe Ina da jarabawa, ko kuma
ni likita ce da xan biki...." Inna ta fashe da kuka ta nufi kofa tace "Eh lallai
Imaan ta xama jarabar duniya, Bukar ya haifi jaraba, Allah ka mana iyaka da Butulu
duk inda yake.... Bari naje in samu Ahmadu ai na fi ki tsiya yau" daga haka ta fice
daga parlon, Imaan na turo baki ta juya xata koma dinning Ammi tace "Wuce ki shirya
ki bi ta ku tafi" ta juyo da sauri kamar xata yi kuka tace "Ammi karatu fa nake, ni
wllh bana son xuwa gidan Yaya..." Ammi ta hade rai tace "Musu xa ki tsaya yi da ni
kenan?" Lkci daya hawaye ya kawo idonta ta wuce dakinta, atamfa riga da skirt ta
fiddo ta saka bayan ta feshe jikinta da turare, ta goga chappete a bakinta ta sa
gogaggen Hijab dinta har kasa ta fito parlor rike da wayarta da karamin jaka, Ammi
dake xaune parlor ta bi ta da ido, a hankali tace "Ammi sai mun dawo" Ammi tace
"Allah ya kiyaye, you pray before leaving" Imaan ta gyada mata kai ta nufi bakin
kofa tana karanto addu'ar fita gida a ranta. Part din su Maimoon ta nufa ta bude
parlon ta shiga a hankali, ko karasawa cikin parlon bata yi ba ta dinga jin Muryar
Inna a parlon Abba tana cewa "Gaba daya Imaan ta banu ta lalace, sam bata da kirki
yanxu, amma abinda ya ban tsoro shine yanda aka boye mata wuyar da Mujaheed ya sha
a kanta, bata fa yarda da kowa a lkcn sai shi sai uwar, duk ta fitsare masa jiki,
har uban nata Bukar tsoron sa take... Toh meye kuma lkci daya sai yarinya ta xama
jarababba mara Imani, ni ka ma kira min Bukar din in ji ko su ke koya mata, dariya
fa ta dinga ba66akawa daga nace mata Mujaheed ba lafiya xan je gidansa, ni wllh na
gaji da imaan a gidan nan" shi dai Abba bai ce komai ba kansa na kasa yana
sauraranta, ta tabe baki tace "Ni dai ba ruwana, shi kuma Mujaheed gaskiya sai mun
tashi tsaye kansa don idan aka rasa sa ni nayi asara ba wani ba, idan ma auren ne
bai so gaskiya sai a raba yau yau din nan, ba ruwana a kai ni a baro in shiga uku"
Sai a sannan Abba ya kalleta yace "Xaxxabi fa kawai yake, amma ai yana jin sauki
yanxu..." Tsaki Inna ta ja tace "Tunda ba jikin ka bane ba dole kace yana jin sauki
ba Ahmadu, gansamemen mutumi da ya dinga min rawan sanyi jiya sai da na rufa sa da
katon bargo shine xaka ce yana jin sauki, ku dai ku dinga jin tsoron Allah, wlh ku
ji tsoron Allah, tunda ba wani ya min wahala da shi ba to ni xan je yanxu inji
abinda yake ciki, idan ma matar ce mayya duk xan gani" Da mamaki Abba yace
"Subhanallah, haba Inna ya kike irin wannan magana haka, wannan fa babban magana ne
ka ce ma mutum maye...." A fusace Inna tace "Na ce mata mayyar, idan ba mayyar bace
ina dawowa ai xan ce ba mayya bace, tsoron ubanwa aka ce maka xan ji banda Allah,
shi kadai ne abun tsoro dama, kuma ni da shi nayi imaani" dai dai shigowar imaan
parlon, kanta a kasa ta gaida Abba, Abba ya amsa yana tambayarta jiki domin jiya
yini tayi ciwon kafa, Inna tace "Ya jiki?? Ce maka aka yi bata da lafiya, Ga dai
bawan Allah me ciwo can a kwance xaka tambayi lafiyayyar mata ya jiki" tana fadin
haka ta tabe baki ta mike tace "Toh yanxu xa ka kirasu ka sanar masu d'an ka na
fari ba lafiya a bar kawo lefen da kudin aure sai wani satin koko?" Da sauri Imaan
ta kalleta, Abba yace "Haba Inna, ae wannan bai shafi ciwon Mujaheed ba, Ina
ruwansu da wannan, shi Mujaheed din yaro ne, don Allah ki yi hakuri ki bar xancen
nan Inna bai ma kamata ba, ga yanda dai muka yi da mutane kuma ki kawo wata magana
daban" Inna tace "Atoh ni dai duk abinda ya sami jikana Allah ya isa wllh...." Daga
haka ta fice daga parlon a fusace, Imaan tace "Abba sai mun dawo" ya gyada mata kai
kawai ta bi bayan Inna, har suka isa titi Inna bala'i take idan abu ya sami
Mujaheed ya sami kowa, ita dai Imaan sai turo baki take tana tsaye gefenta, Inna ta
tsayar da adaidaita ta shige yana tambayarta inda xata a fusace tace "Don Allah ka
rufa min asiri yaro ka ja mashin dinka mu je, meye kuma Ina xanje kamar yar
yarinya, jikana ne fa ba lafiya rai a hannun Allah gidansa na can unguwar dosa ana
ma kyautata xaton matar ce mayya, kuma kana ta cewa ina xan je" Mai adaidaitan bai
tanka ta ba, Imaan ta hade rai ta shige adaidaitan. Har suka isa gidan Mujaheed
mita take ita kadai daga imaan har mai napep babu mai ce mata komai, suna sauka
kafin ta fiddo hamsin ta mika masa Imaan ta basa dari biyar din hannunta don bata
ma son dogon xance, ya ciro dari biyu ya mika mata, Inna ta saki salati tace "Nawa
ka cire bawan Allah?" Imaan tace "Toh ai ba kudin ki bane Inna, kayi wucewan ka
kawai" Mai adaidaitan ya ja napep dinsa yyi gaba Inna ta dinga jaraba tana kiransa
barawo tuni imaan ta shige cikin gidan ta bar ta tsaye a bakin gate, dai dai
balcony ta tsaya ta rungume hannu tana jiran shigowarta, Can sai ga ta ta shigo
compound din tana cewa "Babu abinda kudin Bukar xai masa a rayuwar nan ta duniya,
iyaka ma ya gudu ne da wahala da Bala'i tunda bamu basa ba" bata ko kalli Imaan ba
ta murda kofar parlon ta bude ta shiga, Imaan ta turo baki ta bi bayanta, Umma ce
ta leko daga kitchen tana soya kwai da dankali, Inna ta rike ha6a tana kallonta a
hankali tace "Wacece wannan?" Umma dake sanye da hijab har kasa ta gaisheta a
dakile ta koma kitchen din, Safeenah ce ta sakko parlor sanye da doguwar riga na
material hannunta rike da tray na cup, ganin Inna ta dauke kai ta hade rai hade da
tabe baki tace "Sannu da xuwa" Inna tace "Ina Mujaheed din???" Safeenah tace "Yana
sama an sa masa drip" Inna tace "Ai ni na shiga uku, abun har ya kai an fara sa
drif... Toh aniyar kowa xai bi sa wllh babu abinda xai sami jikana" Kallon Imaan
tayi tace "Ke mu je in gansa..." Imaan ta nufeta, da sauri Safeenah tace "Inna a
can dakinsa yake fa...." Inna ta juya tana kallonta tace "Dakinsa kuma? Toh da ina
nace maki xan je banda dakin nasa? Ko nace maki dakin ki xan shiga Safara'u?"
Safeenah tace "A'a da naji kince ku tafi, idan ma tafiyar ne ke da kike matsayin
kakarsa ai sai ki tafi dakin" Inna ta gyara tsayuwa tace "Toh ita Imaan din fa??"
Safeenah ta d'an hade rai tace "Wannan ba hurumin ta bane gaskiya shiga dakin
mijina, bata da wannan hurumin, dakinsa sirrina ne da nashi" Salati Inna ta xabga
ta xauna kan kujera tayi tagumi tace "Naga abinda ya isheni ni Asabe... Safara'u
kinsan me kike cewa kuwa, wani sirrin ku ke da shi ke da Mujaheed da ba mu sani ba,
kinsan wacece kike kokarin hana shiga dakin nasa kuwa???" Umma ta fito kitchen bbu
yabo bbu fallasa tace "A'a inna, xancen gaskiya ayi ta, dakinta ne da na mijinta fa
kuma kice wata daban ta shigar masu, a kan wani dalilin?? sai kace dai a garin ga6a
ga6a muka taso, ko a musulunce
ai hakan haramun ne ma wata ta shigar maki turakan miji..."

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

69. Imaan

Mikewa Inna tayi ta bude baki tana kallon Umma tace "Rukayya ita imaan din ce wata
a gidan Mujaheed?? Ita Imaan din?? Ehh lallai ba shakka kin xama mahaukaciya, to
wllh tllh Imaan ta fiye ma Mujaheed Safara'u sau dubu dari, wacece kuma Safara'u
Allah na tuba?? Sannan yaushe kika san Allah da kike kokarin min wa'azi wai kar ta
shiga daki ta duba yayanta? Toh kwanciya tace maki xata yi a dakin idan ta je?? Ko
ko ce maki tayi bata da kwakkwaro kamar ki ne?? Ni dai na ga abinda ya isheni, ba
kunya ba tsoron Allah kin kwaso jiki xalalo xalalo kin xo gidan surka kina girki a
kitchen ita kuma tana sama wajen miji, anya Rukayya?? A'a tunda uwata ta haifeni
ban taba gani ko jin haka ba wllh, Toh ni duk ba wannan ba, don bai dameni ba...
Babban magana a nan shine gaskiya ban gane kan ciwon jikana ba, don wannan ciwo ba
na Allah bane, tunda ya auri wannan mata Safara'u yayi bankwana da lafiya, yau ciwo
gobe lafiya, yau fari gobe tsumma, To a kan me? Ita Safara'un yar wace gari ce in
ji tukun kafin in san abun yi" Umma ta dinga mata wani kallo tana jin kamar ta
tanka ta amma wata xuciyar na bata hakuri, fuska daure Safeenah tayi wucewarta
kitchen tana kas kas da cingam ta bar su nan tsaye, Inna ta gyada kai tace "Toh kya
ci uban ki kuwa ba dai jikana ba don kurwarsa daci ne da ita yarinya, in sha Allahu
sai dai ki ci uwarsa da ta jajibo ki ba shi ba, kuma xaman ki saura kiris a gidan
nan" daga haka ta ja hannun Imaan dake tsaye gefenta suka wuce sama tana huci, Umma
ta bi su da wani kallo xuciyarta na tafarfasa tasan dai ko hauka take baxata tanka
Inna ba, Inna ta bude kofar parlon dake sama ta shiga, Ganin Imaan ta ki shigowa ta
fixgota a fusace ta nufi dakin Mujaheed da ita, Imaan dai sai bin ta take, kwance
Mujaheed yake saman gado idonsa rufe, Inna na kallon empty robber din drip dake
sakale ta rike ha6a tace "Ka ji jarababbu mayu, wai an sa masa ruwa yana daki,
alhalin ga ruwa ya kare..." Bude ido Mujaheed yyi, Inna ta fashe da kuka a hankali
ta nufesa tace "Sannu Mujaheed, in sha Allahu babu abinda xai sameka in dai ina da
rai, asiri dai ya gama tonuwa na gano komai" shi dai gaba daya hankalinsa na kan
Imaan da tayi tsaye bakin kofa ta ki shigowa kuma ta ki yarda su hada ido sai wasa
da fingers dinta take, Inna ta xauna gefen gadon tana goge guntun hawayen idonta
tace "Kwana nawa da aurenta ka fara jin canji a jikin ka??" Shi dai bai ce mata
komai ba har sannan yana kallon imaan, Inna ta juya ta kalleta tace "Ke dai baki da
kirki wllh, halin ki abun tsoro ne gaskiya, baxa ki karaso ki gaida sa ba" sai a
sannan imaan ta kalli Mujaheed, suna hada ido tayi saurin dauke kai ta karasa cikin
dakin ta duka kasa kusa da gadon a hankali tace "Ya jikin Yaya?" Bai tanka ta ba,
Inna tace "Atoh, abinda ma da kyar ta biyoni Mujaheed, wllh Imaan bata da imaani,
har fa ce min tayi toh ita ce bata da lafiya da xance a fasa kawo kayan aurenta yau
sai wani satin sabida baka da lafiya...." Mujaheed dai ya kasa daina kallonta,
imaan ta wani hade rai tana kallon Inna, bude kofar dakin aka yi sai ga Safeenah ta
shigo da warmer a rufe da plate a hannunta, ko kallonsu bata yi ba ta karasa ciki
ta ajiye ta xauna kusa da kansa tana wani yauki tace "Baby ka tashi ka ci ko kadan
ne sai ka sha drugs dinka plss, bacci ma ya kamata kayi ka huta bayan ka gama cin
abincin tunda sai ltr xa a sa wani drip din" Imaan ta dinga hararanta ta gefen ido,
Inna ta tsuke fuska ta rungume hannu tana karanto addu'a a xuciyarta tana tofawa a
duk angles din dakin, Mujaheed ya mike xaune ya cire duvet din jikinsa yana kallon
Safeenah yace "You don't worry anjima xan ci, na sha tea yanxu" tace "Toh ayi maka
pepper soup din ko appetite dinka xae dawo?" Da kamar baxai ce mata komai ba sai
kuma yace "Ohk" Ta mike tana wani cat walking ta nufi kofar fita tana karkada jiki,
Imaan ta wani tabe baki ta dauke kai fuska daure, Safeenah na fita Inna ta mike ta
dau abincin ta bude window ta xaxxage gaba daya downstairs ta juyo tana kallon
Mujaheed murya can kasa tace "Mayya ce Mujaheed...." Bude baki yayi yana kallonta
da mamaki, ta kyabe baki ta cire Hijab dinta ta linke tace "Jira in je in soya maka
wani gaskiya, Allah ba batun wasa ba an gano mayya ce amma kada kace mata komai
tukun, a hankali ake kama barawo, anjima ta Rasulu tace min xata xo nan....." Bai
san lkcn da yyi murmushi ba bai dai ce mata komai ba, kofa Inna ta nufa fuska daure
ta fita xata kitchen ta masa girki, Imaan na ganin haka ta mike da sauri ta nufi
kofa yace "Fatima" tsayawa tayi sai dai bata juyo ba, jin bai ce komai ba a hankali
ta juyo tana kallonsa, taga kallonta yake, sosai gabanta ya fadi, kamar xata yi
kuka tace "Na'am" jin yyi shiru ta karasa kusa da gadon ta durkusa tace "Ga ni" ya
sauke idonsa daga kallonta yace "Ya preparation na exams?" A hankali tace "Lafiya
lau, how are you feeling now?" Yana kallonta yace "Dama kin san bani da lafiya
ashe?" Tace "Aa ni Inna ce ta gaya min daxu Allah ban sani ba" Bai ce komai ba
hakan yasa tace "Xan je in taya Inna" yace "Promise me baxa ki wuce gida ba daga
nan" murmushi tayi ta boye fuskarta da gado don abinda ke ranta kenan, ji tayi ya
kamo hannunta ta dago da sauri yace "Kar ki tafi yanxu Imaan" ta turo baki tace
"Bayan Umma tana nan, kuma matar ka sai wani hararana take yi, ni dai wucewa xan
yi" yace "Toh kiyi xamanki a nan" ta xaro ido tace "Kaga Inna ta wuce fa, salon
idan matarka ta shigo ta xageni ko" yace "Kina dai son wucewa kawai" tana murmushi
tace "Toh naji baxan wuce ba, amma me ke damun ka Yaya? Ji fa ka rame sosai" Ya
jinginar da kansa da gado murya can kasa yace "Ban sani ba" ta langwabar da kai
tace "Kana likita kuma baka sani ba, or is about our last talk, I mean about the
lady..." Shiru yyi yana kallon Ac dake aiki a dakin, murya can kasa yace "Yau xa a
kawo kayan ki koh?" Dariya tayi ta boye fuskarta tace "Uhm nima ban sani ba" jin
bai ce komai ba ta dago tana kallonsa, kallonta taga yana yi da manyan idanuwansa,
ta sunkuyar da kai tana murmushi tace "Ehh yau ne" yace "And u are happy" ta turo
baki ta ki cewa komai, sauke kafafuwansa yyi daga saman gadon ya nufi press dinsa
ya fiddo gogaggen shirt xai saka a kan singlet da 3 qtr din jikinsa, Bude kofar
dakin aka yi sai ga Safeenah, da wani expression ta dinga kallonsa sai kuma ta
kalli Imaan a nutse tace "Malama tashi ki fitar min dakin miji, naga alama
karuwancin naki ba iya waje ya tsaya ba har gida" Imaan na mata wani kallo tace
"Karuwanci kuma? To sai dai in kece karuwa....." Bata rufe baki ba Safeenah ta
sauke mata mari tana wani huci tace "Ni kike ce ma karuwa a dakin..." ita ma bata
kai karshe ba taji saukan wani wawan mari da yasa ta ji dumm a kunnenta, da kyar ta
juya tana ganin stars ta kallesa cikin rawar murya tace "Mujaheed. .." ya kuma
wanke ta da wani mahaukacin marin ya fixgota yana huci yace "Kinsan warce kika mara
Safeenah??" Safeenah ta xaro ido a tsorace tana kallonsa, sai kuma ta rushe da kuka
cikin tashin hankali tace "Yanxu a kan wannan matsiyaciyar ka mareni Mujaheed, a
kan wannan sauran ciwon....." Hankada ta yyi iya karfinsa don har sai da ta fadi
kasa timm, Yana nuna ta calmly yace "Kece matsiyaciya ba ita ba" Safeenah ta mike
da sauri ta fice dakin da gudu tana kuka, Imaan da hankalinta yyi mugun tashi tana
kallonsa cikin rawan murya tace "Yaya me yasa ka mareta, ai xan iya ramawa da kai
na, why did you slap her, you shouldn't have, beside umma fa na gidan" Mujaheed ya
rikota cikin daga murya yace "Did you know what I felt da ta mare ki imaan?? Kinsan
abinda naji?? Me yasa xata daga filthy hand dinta ta daura a fuskarki??" Ta dinga
kallonsa da manyan idanuwanta ko kiftawa babu, yyi kasa da murya yana sauke
numfashi a hankali yace "Wlh da ni ta mara baxan ko daga kai in kalleta ba, why
will she slap you Imaan???" Kallonsa kawai imaan take ganin yanda idanuwansa suka
kada sosai, lkci daya ya rungume ta ya lumshe ido, a hankali ta kwantar da kanta
kirjinsa tana jin yanda xuciyarsa ke bugawa tana shakan daddadan kamshinsa, gently
ya dinga tafiya tana jikinsa har ya isa kofa ya sa makulli. Inna na kitchen tana
aikin suyan dankali da kwai, Umma ma na kitchen din fuska daure tana dauraye kayan
miya da xa ayi ma Mujaheed pepper soup, lkci lkci take xabga ma Inna harara ta
dinga addu'ar da ma man gyadan dake kan gas din ya kware a jikinta kowa ya hutu a
duniyar, Inna ta kwashe dankalin karshe a mai tana tabe baki tace "Ba ruwana, ni
sai in sa Ahmadu ya tattaro min kayana ma in dawo nan gaba daya, don dai in masa
girkin abincin da xai ci ransa kadai kar a cucesa, ni a ma kira min Ahmadun in gaya
masa jikin Mujaheed ba sauki masu kawo lefen nan su dakata kawai lefe bai fi jikana
ba gaskiya" Umma ta kalleta da sauri, sai kuma tayi kasa da murya tace "Lallai kam,
ace duk yanda suke da Imaan baya nan xa a kawo lefe da kudin aurenta, abun bai yi
ba gaskiya, daxu daxun nan da safe na gama maganan nan" Inna tace "Atohh, ko tsari
babu wllh, Ahmadu ya ki saurarata da yake kunnen kashi garesa, ni bari a kara
kiransa in jaddada masa halin da na xo na samu Mujaheed a san abun yi" tana fadin
haka ta fice kitchen din, Umma ta kashe gas ta bi bayanta da sauri, jakarta ta
dauka ta bude ta dau wayarta ta mika ma umma tace "Kira min Ahmadun" Umma ta nemo
lambar Abba ta kira ta sa a hands free ta mika mata, Abba na dagawa Inna tace "Toh
wllh Ahmadu Mujaheed na nan rai kwakwai mutu kwakwai, ko magana bai iya yi balle ya
ci wani abun, idan xa a ji ta nawa to a dakatar da masu kawo kayan nan xuwa sati
mai xuwa, aure bai fi rai ba ku ji tsoron Allah Ahmadu....
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

Mujaheed rai garesa" Abba dake ta saurarenta yace "Sun kira suna tahowa nan da
wani lkci, don haka babu fa'idar fasa komai, sannan ba wai jimawa xa ayi ba balle
kice, da sun tafi xa mu taho da Abubakar da likita tunda yaro Mujaheed din ya xama"
Inna tace "Toh kuwa kun xama abun tsoro wllh, Allah ya mana tsari da ku" daga haka
ta mika ma Umma tace "Kashe min wayata maxa, ni dai ina ganin jarabawan rayuwa"
Umma ta katse wayar gaba daya rai ba dadi, don tun safe da ta ji labarin xa a kawo
lefen Imaan ta gane xancenta bai yi tasiri ko kadan a gun uwar Sadeeq ba, tun
sannan ta kasa xaune sai da ta taho gidan Mujaheed don fada ma Safeenah abinda ake
ciki, tana xuwa kuma ta iske Mujaheed kwance wai ba lafiya an sa masa drip, abinda
ma ya tsayar da su basu fita ba kenan amma da tuni sun baxama neman duk abinda xai
sa a fasa shigo da lefen Imaan gida, a hankali Umma tace "Ba a kyauta ma Mujaheed
ba amma gaskiya" Inna tace "Toh wa gareni da xan ma magana ya ji, ai Ahmadu ya
dauko hanyar lalacewa shi ma, shi dama Bukar bana sa shi a lissafi kwata kwata"
Umma tace "Toh ko xaki ma shi yaron magana, naga kuna shiri sosai" Inna ta mika
mata wayar tace "Yauwa duba xa ki ga Bulasawa ki kira, ae yana da fahimta, kawai ce
masa xanyi Imaan tace tana jin nauyinsa don Allah in masa magana a dakatar da kawo
kayan don yayanta bashi da lafiya yana kwance har da karin ruwa leda uku" Umma ta
amshe wayar da sauri tace "Toh hakan ma yyi wllh" tana kiran number Sadeeq ta sa
handsfree ta mika ma Inna, Inna ta karbe wayarta ta nufi kofar ta fice parlon gaba
daya, Umma ta bi ta da wani kallo tana murmushi, dai dai nan Safeenah ta sakko kasa
tana kuka sosai har lkcn tana rike da kuncinta, hankali tashe Umma ta nufeta da
sauri tana cewa "Lafiya Safeenah me ya same ki?" Cikin kuka sosai tace "Hajiya a
kan wannan shegiyar yarinyar Mujaheed xai sa hannu ya mareni har sau biyu, Mujaheed
ya rasa warce xai mara sai ni? Mujaheed slapped me???" Bude baki Umma tayi tana
kallonta da mugun mamaki tace "Shi Mujaheed din ya mare ki??" can ta juya ta wuce
sama kamar xata tashi sama, Sosai Imaan ta rikice jin muryar Umma tana bubbuga
kofar dakin kamar xata cire tana kiran sunan Mujaheed, Lkci daya hawaye ya kawo
idonta ta rikosa cikin rawar murya tace "Wayyo Yaya ka gani ko" Xaunar da ita yyi
gefen gado ya duka kusa da ita murya can kasa yace "Relax now, ba shigowa xata yi
ba na rufe kofar" Inna ce ta shigo parlor tana tabe baki tana kallon wayarta, ganin
Safeenah na rusa kuka ta isa kusa da ita ta duka tana kallonta da mamaki, can tace
"saboda na xubda girkin da kika masa shine kika xauna nan kina kuka? Ke kya yarda a
cuci wani naki??" Bata jira cewarta ba ta wuce sama, tana isa parlon Mujaheed ta
dinga kallon Umma dake ta jijjiga kofa, hankali tashe tace "Lafiya?? Makalewa suka
yi a ciki??" Umma ta ki cewa komai xuciyarta kamar ya fashe ta huta, da karfi Inna
tace "Mujaheed???" Mikewa Mujaheed yyi daga durkushen da yyi gaban imaan da taki
kwantar da hankalinta jin muryar Inna ya nufi kofar ya bude a hankali, mari Umma ta
sauke masa tana huci tace "ita Safeenahr ka daga hannu ka mara???" Wani salati Inna
ta xabga tana kallonta tace "Kina da hankali kuwa Rukayya, Mujaheed din kika mara
hka???" Muryar Safeenah suka ji tana cewa "Wllh baxan xauna gidan nan ba yau in har
sabida wnn matsiyaciyar Mujaheed ya mareni wllh baxan xauna" Mujaheed ya daga kai
yana kallonta fuska daure yace "Ki tafi gidan ku sae na neme ki, kar ki kara ko
minti biyar gidana...." Inna tace "Fakat, maxa tattara ina ki ina ki kiyi wucewar
ki mayya" gwalo ido Umma tayi tana kallonsa kamar yanda Safeenah ma tayi, cike da
karfin hali Umma tace "Safeenar kake cewa ta tafi gidansu Mujaheed??" Bai yarda ya
kalleta ba a takaice yace "Ehh Umma ta tafi gidansu" juyawa Safeenah tayi da sauri
ta fita parlon, Umma ta kasa cewa komai tana kallonsa with shock can ta juya fuu ta
wuce, Inna tace "Tunda kema mayyar ce sabida me baxa ki ji haushin koran Safeenah
ba, in sha Allahu xamanta ya xo karshe a gidan Mujaheed...." Shiru Inna tayi tana
kallon Imaan ganin hawayen idonta tace "Me aka maki kike kuka?" Kin cewa komai tayi
ta juya masu baya, Inna na kallon Mujaheed tace "Kasan yau xa a kawo kayanta da
lefe, nace su Ahmadu su jira ka ji sauki ayi komai da kai sun ki saurarata... Yanxu
ga dai waya ka Kira min Bulasawa na kirasa daxu ban ji yyi magana ba kila kiran ma
bai je ba" Imaan ta juya da sauri tana kallon Inna tace "Me xa ki ce masa??" Inna
tace "Wannan ba matsalar ki bace sirri na ne da shi" Mujaheed dai na rike da wayar
yana kallonta, ganin haka Inna ta kwace wayarta ta juya ta fita xuwa gun mai gadi
don ya kira mata Bulasawa, ganin ana wangale gate din ta tsaya sai ga motar Abba,
parking Abba yyi ya fito tare da Daddy da kawu Audu da wani frnd din Daddy daga
cikin motar, Inna ta bude baki tace "Kaddai ku ce har sun kawo kayan ni Asabe??"
Abba yace "Sun kawo har ma sun tafi, an saka biki nan da wata guda dai dai da lkcn
da xa su gama xana jarabawa, sun kuma bada sadakinta dubu dari takwas" Inna tace
"Toh da kyar idan Mujaheed xai yafe maku, don wahalan da yyi da ita ku da ku ka
haifeta ma baku yi ba, amma sbda butulci ku amshi kudin auren yarinya ba shi sbda
cuta ta kamasa?? Toh aji tsoron mutum" daga haka ta juya ta wuce ciki fuska
tsuke....

*Maa sha Allah, I will take a break till after sallah in sha Allah, thank everyone
for being patient with me all this while following the book Imaan, ayi sllh lfya*

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

🌟⭐imaan ⭐🌟

70.....

Tun da Inna ta fita parlon Mujaheed ke kallon Imaan dake tsaye ta wani hade rai
tana kallon bakin kofa ita a dole Inna ta tafi kiran Sadeeq a fasa kawo kaya, satan
kallonsa tayi ganin ynda yake kallonta ta turo baki ta juya xata fita yyi saurin
rikota yana kallon eyeballs dinta yace "Don't say anything about what happened
between u and my wife to Grandma" kin cewa komai tayi ta kwace hannunta ta fice
daga parlon nasa ta sakko downstairs, a nan kuma ta ji shigowarsu Abba compound din
gidan da maganganun da suke yi da Inna, Inna ta dawo parlor tana girgixa kai tace
"Tunda uwata ta haifeni ban ta6a ganin irin haka ba, su Ahmadu dai sun shiga uku
sun lalace tirrrr, yanxu ko Mujaheed kadai bai isa ya karbi auren imaan ba, amma
kawai mutane don ba shi da lafiya kuyi masa wannan rashin mutunci, to da kyar idan
girman ku bai fadi a idonsa ba gaskiya" Imaan dai sai kallonta take, Inna ta xauna
fuska ba annuri tace "Tirrr" Abba yyi sallama bakin kofar parlon ya shigo sannan
Daddy da Kawu Audu, Gaishesu Imaan tayi Abba ya amsa yana kallonta yace "Ina
Mujaheed din?" Inna ta tabe baki ta dauke kai tana girgixa kafa, Imaan xata wuce
sama Abba yace "Ina matar gidan?" Inna ta kallesa da sauri tace "Wace matar gida?
Matar gida da ya kora daxu, koko wata daban kake nufi?? ai tuni yace ta wuce
gidansu ba wanda bai san mayya bace, daga nan dama ni dai daukansa xan yi mu koma
gida ya xauna bangarena ayi ta masa magani har yayi garau" Kawu Audu da ya buda ido
sosai yace "Mayya kuma Yaya?" Inna tace "Xancen kake so D'an tsut, tun fa da aka yi
auren nan yau lafiya gobe ba lafiya a haka yake kamar mai laulayi, to ina dalili da
raina kuma da lafiyata snn ba gantalalliya ba...." Ta kalli Imaan tace "Ke tafi ki
kirasa su gane ma idonsu yanda ya koma" Daddy yace "Ni ban fahimci xancen ki ba
Inna, ita matar yace ta tafi gidansu ko wa?" Inna na kallon Imaan tace "Ke tafi ki
kirasa su gansa bana son dogon surutu da Bukar, don ba hankali isasshe garesa ba
wllh, kuma a gaskiya kada Bukar ya sani a bakin duniya ni ba ni na koreta ba da
bakinsa yace ta tafi to tunda ba ubanta ya gina masa gidan ba ba dole ta tafi ba,
har Rukayya fa a nan na sameta tana masu girki a kitchen daxu..." gaba daya dai sai
kallonta suke don har sannan babu wanda xai ce ya fahimci xancenta, Imaan dai ta
wuce sama tayi knocking kofar parlor din Mujaheed, sai da ta kara knocking har sau
biyu sannan ya bude door din bedroom dinsa, tace "Abba yana kiran ka a kasa" yana
gyada kai a hankali yace "You know what Imaan??" Tana kallonsa tace "What??" Yayi
wani murmushi yace "I want you to keep this at d back of ur mind... all this ur
pretence and everything you are doing... Billah ranan da xan rama yana nan xuwa, I
will make u regret all this you are doing in sha Allah" on a serious note ya fadi
haka, ta buda ido sosai tana kallonsa da mamaki tace "Pretending kuma? What am I
pretending yaya? Ni ban gane ba" yace "Bana son ki gane dama" tabe baki tayi ta
juya ta bar wajen ya bi ta da kallo har ta fita sannan yyi wani murmushi. Inna na
kallonsu Abba tace "Ni fa ko rantsuwa nayi da kyar inyi kaffara Ahmadu, wai ya xa
ku maida ni yarinya da bata san abinda take bane, komai na fada ku karya ta ni ne??
nace maku yarinyar nan mayya ce ita ta kama min jika yake ta ciwace ciwacen da ba
na Allah...." Katse ta Daddy yyi ya mike yace "Ke dai Inna ki daina haka, don Allah
ki rufa mana asiri ki daina, ni fa gaskiya ba ruwana idan kika jawo wata maganar,
ya xa ki dinga kiran yar mutane da mayya kai tsaye, Haba inna.... kin san wannan ba
magana bace karama kuwa??" Tagumi Inna tayi a hankali tace "Naga abinda ya isheni
ni patuu... Me yasa Bukar ke min haka a rayuwa" Daddy yyi yace "Ni gaskiya nake
gaya maki, kiyi hakuri ki daina wannan abinda kike ba shi da amfani, duk wanda kika
ji bai maki ba sai kice masa maye?? Haba don Allah, ke kin xata maita karamin abu
ne, wllh ki daina haka bai kamace ki ba kwata kwata, haka kawai ki dage kina ce ma
yar mutane mayya ki dauko mana wata maganar, this is very wrong wllh" Shi dai Abba
kansa na kasa, Inna dai bata kuma cewa komai tayi tagumi, kawu Audu yyi kasa da
murya yace "Hajiya yanxu da xa a kai maganan nan gaba...." Tsawa tayi masa tace
"Kai d'an tsut ka fita harkata, idan an kai sa gaba uwaka xa ayi?? kada wanda ya
sani a bakin duniya gaskiya, da kansa ya kori matarsa ni ban koreta ba...." Shiru
kawu Audu yyi bai kuma cewa komai ba, Mujaheed ne ya sakko parlon cikin kananun
kaya, Abba ya daga kai yana kallonsa ko kiftawa babu ganin yanda ya rame, Daddy ma
kallonsa ya dinga yi da mamaki, ya karasa parlon yyi kasa da kai ya gaishesu, Daddy
yace "What's wrong with Muhd?" Ya d'an yi murmushi yyi kasa da murya yace "It's
just malaria amma da sauki sosai Abba" Daddy yace "Are u under medication?" ya
gyada kai yace "Sure sir" Kallonsa kawai Abba ke yi shi dai ya kasa cewa komai,
Daddy yace "But did you have any problem Mujaheed, wannan anya Malaria ne kadai..."
Inna ta tabe baki ta mike murya can kasa tace "Har da kamun mayya ko kun ki ko kun
so" daga haka ta nufi kofa fuska daure, Daddy ya bi ta da kallon gefen ido, sai
bayan da ta fita parlon gaba daya Abba yace "Me ya hada ka da matar ka kace ta tafi
gida??" ya shafa kai a hankali yace "Abba...." Sai kuma yyi shiru, Daddy yace "Bama
son jin komai my friend, get her back immediately, am I clear??" Mujaheed ya
kallesa ya kasa cewa komai da farko, can a hankali yace "In sha Allah Abba" Kawu
Audu yace "Toh xa mu je asibitin ne yanxu??" Mujaheed ya kallesa yace "A'a ina
amsan medication a gida kawu, ai da sauki sosai yanxu" Kawu Audu yace "Toh Allah ya
kara lafiya Muhd, Allah ya yaye maka" Mujaheed yace "Ameen" Mikewa Abba yyi yace
"Ka dai ji abinda aka ce maka yanxu, get her back today, sannan I want you to try
all possible means of stoping ur grandma from coming to this house" murmushin
karfin hali Mujaheed yayi yana kallon Abban nasa, daddy yace "That's just it" Daddy
na kallon Imaan dake xaune yace "Ke kuma mai nuna mata hanyar xuwa gidan ko?"
Mujaheed ya kallesa da sauri yace "A'a Abba ta san hanya ai...." Imaan ta sunkuyar
da kai bata ce komai ba, Daddy yace "Toh tashi mu wuce" Mikewa tayi ta nufi kofa,
Daddy yace "Allah ya kara lafiya M.A" Mujaheed yyi murmushi yace "Ameen" Abba yace
"Anjima ka taho gida tare da matar taka" yace "Toh in sha Allah" Kawu Audu yace
"Sai ayi ta hakuri ka ji?" Murmushi kawai yyi ya sauke kansa kasa, har bakin mota
ya rakasu, Imaan ta shiga bayan motar tana kallonsa tace "Allah ya kara lafiya" ya
gyada mata kai kawai bai ce komai ba, Daddy ya shiga front seat, Abba ya shiga
maxaunin driver yana kallon Mujaheed yace "An kawo kudin auren kanwarka, we will
talk later idan ka xo gida" A hankali Mujaheed na gyada kai yace "Toh Allah ya
sanya alkhairi...." Abba yace "Ameen" Mujaheed ya kara masu sallama suka bar
compound din ya juya kamar me counting steps dinsa ya koma parlor ya xauna saman
kujera ya jinginar da kansa jikin kujerar ya lumshe ido yana jin xuciyarsa na masa
xafi. Umma na barin gidan tare da Safeenah dama bata yarda Safeenah ta tafi gidansu
ba, ta lallabata da kyar suka wuce gidan Hajiya Saude, Hajiya Saude ta sauke ajiyar
xuciya bayan Umma ta koro mata duk yanda aka yi, ita dai Safeenah sai hawaye take
tana jin da yau xa a mika mata wuka daga ita sai Imaan a daki babu fa abinda xai
hanata ta kasheta, bata taba jin tsanar mutum kamar yanda take tsanar Imaan ba, wai
a kanta Mujaheed ya daga hannu ya mareta har sau biyu, for what??? Hajiya Saude
tace "Kuma har sun kawo lefen koh???" Umma na share xufar da ke keto mata cikin
tashin hankali tace "Wlh muna hanya Ummi ta kirani wai ga kaya an kawo, akwatuna
har sha biyu da sadaki kusan miliyan daya, ni abun duk ya kwabe min wllh" Hajiya
Saude ta bude baki tana kallon Umma, can tace "Amma wannan uwar yaron anyi
tsinanniya, wato hauka ta manna mana wai xa tayi shawara" Umma tayi tagumi bata ce
komai ba, Hajiya Saude tace "To yanxu meye abun yi kuma??" Umma tace "Auren nan fa
ko ana ha maza ha mata baxa ayi sa ba in dai ni Rukayya ina da rai, wato sun ma ci
bulus kenan da uwarta idan na hakura aka yi auren" Hajiya Saude tace "Gaskiya kam
gashi daga ita ba wata balle ace a hakura xuwa wani lkcn" Umma ta mata wani kallo
tace "Toh ko da wasu 'ya yan an gaya maki haka nan kawai xan bar imaan ta tafi
gidan da xata huta, duk fitsara da rashin kunyar da kakarta ta dinga sa wa ta dinga
min ya tashi a banxa ya tafi a banxa kenan, inaaa ai sai dai idan ban haifu cikin
uwata Hadiza ba, Imaan sae dai ta ji labarin jin ddin aure amma ba dai ita ta ji
ba" Safeenah ta tabe baki tace "Ni dai babban damuwata ta daina xuwa min gidana
gaskiya, a kanta har Mujaheed ya daga hannu ya mareni kuma ki hanani gaya ma
Hajiyata" Umma tace "Haba Safeenah bai kai ki gaya ma Hajiyar Marafa ba, kin santa
da xuciya ki bar ni da shi kawai, kema kinsan haka nan baxai mare ki ba, wllh sai
yayi da ya sanin abinda ya aikata, muna nan da ke" Safeenah ta yi tsaki bata ce
mata komai ba, Umma tace "Tunda shawarar da kika bada aka yi amfani da shi kwanaki
bai yiwu ba yanxu baki da wata shawarar da xa ki kara ba mu?" Safeenah tace "Don an
kai lefe da kudin aure ba yana nufin anyi aure bane...." Shiru tayi ta bude jaka
jin wayarta na ring, ta fiddo wayar tana kallon screen din, Kallon Umma tayi tace
"Shi yake kirana" Umma ta xaro ido tace "Haba?? To dauka ki ji uban me xai ce maki"
Safeenah ta wani daure fuska ta daga kiran ta sa handsfree tayi shiru, sallama yyi
cikin sanyayyen muryarsa, cike da masifa tace "What did u want from me Mujaheed?"
Ya d'an yi shiru sannan yace "I want to say I am sorry, kiyi hakuri tsautsayi ne"
ta fashe da kuka tace "Tsautsayi ka daga hannu ka mareni a dakina a kan wata can,
kuma a gabanta??" Yace "Nace kiyi hakuri, and take note Imaan ba wata bace kanwata
ce, I see no reason xaki daga hannu ki mareta in kyale ki..." Safeenah ta bude baki
ta xaro ido tana kallonsu Umma, tace "Wato kirana kayi ka sake min rashin mutunci
kenan Mujaheed?" Murya
can kasa yace "Not at all Safeenah, Kinsan Imaan ba lafiya sosai gareta ba, kuma
ga grandma dinmu a gidan, da ban yi haka ba anything can happen... ni nasan halinta
ke baki sani ba, so don't ever, I mean ever.... try giving her a bad look talkless
of you laying ur hand on her face, xan iya maki fiye da abinda kika yi...." Sai
kuma ya kwantar da murya yace "Yanxu dai I didn't call to talk long plss kiyi
hakuri da abinda ya faru idan ma kince xa ki rama shkkn sai ki rama a kai na, but
If you try touching my lil sis I will not take it likely with u" Bude baki Safeenah
tayi da mugun mamaki tana kallon Umma da ta gwalo ido tana sauraransa ita ma, a
hankali Safeenah tace "You called to warn me Mujaheed?" Yace "Not at all, na kira
ne in baki hakuri, and tell me where you are now??" Umma tayi kasa da murya sosai
tace "Kice kina gida wajena" Safeenah ta tabe baki fuska daure ta ki cewa komai,
yace "Am asking kina Ina" alama umma ta dinga mata ta gaya masa tana can gida, ta
harareta ta dauke kai tana wani cika tace "Ina gidan ku" Mujaheed yace "Good I am
happy baki tafi gida ba, later da yamma xan shigo in sha Allah, I need rest now..."
Daga haka ya katse wayarsa. Safeenah ta ja wani tsaki tana kallon Umma a fusace
tace "Ni dai Hajiya kin
bari kawai na tafi gidanmu Hajiyarmu ta san abinda ake ciki, aure ko wata uku ba
ayi ba an fara mari na sbda wata shegiya, dubi fa hakuri ya kira ya bani amma dubi
irin maganganun da ya dinga min da warning?? Infact wai ma me yasa baya ji da
kanninsa haka yanda yake ji da ita?" Umma ta tabe baki tace "Uwar ce ta asirce min
shi, tun yarinyar na yar karama tana yar yaye yake bauta da ita ke kya ce don shi
aka haifota, nayi nayi in rabasa da ita amma inaaa, da yake kinsan lkcn a wajen
kakar tasu yake, ita kuma yarinyar kullum sai an kai ta can sai ya maida ta gida da
yamma, idan ba karyar kakarsu ba ma cewa tayi da sunansa ta fara magana, amma duk
karya ce wllh, a haka dai ta taso ta makalkale ma d'a na sai kice shine Abubakar
ubanta, idan kuwa xai dawo hutu gida daga Uk uban tsaraban da yake yo mata hankali
baya dauka, kanninsa ko quarter dinsa basa samu wllh, wai ma don abun ya ragu sosai
yanxu, ae ba karamin tashi tsaye nayi ba gaskiya, ban yi da wasa ba kam, kwanaki da
dadewa fa mijin da Seeyama ke aure yanxu ya so hada imaan din da, kinsan abokinsa
ne kuma yaron ga kudi ga hankali amma sbda shi shashasha ne wai da Imaan xai hada
sa, ni ko na ruguje xancen gaba daya, shine yaron ya dawo ma Seeyama, yanxu wnn
auren ma da ake son a mata shine gaba a kan komai ina jin, kuma bbu mamaki ya ma
san yaron Bulasawan..." Safeenah da ke ta kallon Umma tace "Toh ni dai gaskiya tayi
aurenta ta tafi gidan mijinta ta kyale min miji haka" Umma ta bude baki tace "Tayi
aure kuma? To ai tunanin xata auri yaron Bulasawa ne yasa take raina mutane take
ganin ita wata ce, wllh shi yasa take maki kallon hadarin kaji, kallon kowa take
kasa da ita sbda tana tunanin yaron Bulasawa ne xai aureta, amma bata san she is
mistaking ba, wllh wllh ba mijinta bane yaron in dai ina numfashi, ke kinsan ko
gaisheni yarinyar nan da kike gani bata yi kuwa?? Uwarta kuwa jin ta take ita wata
ce yanxu a dole ga ta surkar Bulasawa, to xa su kwashi kunyar su kuwa a hannu wllh
ba cika baki ba" Safeenah ta tabe baki tace "To ae don an kai sadaki da lefe an sa
rana ba shine yake nufin an daura auren ba, in dai ni take ma wani gani gani wllh
ta tari aradu ba gamo... Sai na kunyatata in ga ta tsiya in ga karshen auren nata
da shi Sadeeq Bulasawa din" Umma tace "Atohh, ni dai dama nace idan aka yi auren
nan to fa ban haifu cikin uwata ba, daga ita har uwarta da kakarta sai sun kwashi
kunyarsu a hannu ina kallo" Hajiya Saude tace "Kuna ta surutu ni ko har na gama
yanke shawarar what next... Kuma in Allah ya yrda naji kamshin nasara...." Umma ta
kalleta da sauri tace "Toh ba mu mu sha" Hajiya Saude tace "Amma duk da haka sai
mun koma wajen mutumin nan ko xuwa gobe"
Bayan Magrib Mujaheed yayi parking kofar gidansu ya fito ya kulle motar gaisawa
suka yi da mai gadi dake bakin gate, Mai gadin na kallonsa yace "Likita ba lafiya
ne" Mujaheed na kallonsa yyi murmushi yace "Alhmdllh, na ji sauki" daga haka ya
shiga compound din, direct part din Inna ya nufa walking slowly, a hankali ya
murda kofar parlon ya shiga, ido hudu suka yi da Imaan dake xaune parlon tare da
Inna da ke ta fiddo kayan cikin akwatunan lefen da aka kawo bakinta har kunne, Ta
Rasulu ma sai aikin fiddo ubansun kayan take tana cewa "Toh ga dai kaya ba laifi an
xuba karyar naira, ko da yake suna da shi ne, Ni fa nasan har uwar Bulasawan nan a
da wllh, don akwai wata makociyata kawar kanwarta da suke uwa daya tana ma uwar
Bulasawan aikatau, lkcn ma kudin bai bunkasa haka ba, toh sai makociyar tawa ta ja
ni wataran muka je gidan kawar kanwarta wai xata kai mu gidan kakar shi mijin Imaan
wato uwar Bulasawa, sunan uwar tasa Hajiya Salamatu, tana nan wata doguwa fara,
duka duka bata fa wuce mu ba amma kirkinta ragagge ne...." Inna dai sai kallonta
take kasa kasa, ta Rasulu ta tabe baki tace "yo ragagge mana, a lkcn Ina goyon
Shamsu daga ya mata fitsari a cafet, ga abinci mai lafiya da xuka xukan kaji an
xubo mana xa mu ci in gaya maku abincin da ban ci ba knn don matar nan cewa tayi in
tafi gida in canxa masa kaya xarni ya isheta, nan ko bata san har da kashi yyi ba
ina ta boyewa ne har sai mun ci abincin, ni dai har da d'an kwalla na na bar gidan
ina dukan shamsu, kafin in dawo kuwa su shafa'u suka side kwanon tass da ke kinsan
dangin mayu ne, ni dai abincin ko a halshe na" Maimoon dai sai taya su fiddo kayan
take bata ko kalli ta Rasulu ba, Duk suka kalli Mujaheed da ya shigo parlon ya
tsaya yana bin akwatunan da kallo, Inna ta washe baki tana kallonsa tace "Mujaheed
takwarata tayi goshi wllh, ko atamfar dubu ashirin Ina jin babu a nan, gwalagwalai
kuwa mun kirga biyar da ta Rasulu, to me xance ma Allah banda in gode masa?" Imaan
dai sai danna wayarta take, Mujaheed yace "Toh Allah ya sanya alkhairi" Inna tace
"Ameen, kuma kayi hakuri da abinda iyayenka suka maka, ka dai fi su nesa ba kusa
ba, in sha Allahu idan Allah yasa aka daura auren nan lafiya kai xaka kai Imaan har
dakinta kayi mata fada sosai sannan mu taho gida mu bar ta" Dariya Maimoon ta dinga
yi tana kallon Imaan da taki dago kanta, Inna ta tsuke fuska tace "Ke ba batun
dariya bane, magana ta gaskiya shi xai kai ta gidanta... Ke kinsan wahalar da yyi
da ita ne kuwa" Ta Rasulu tace "Wahala kuma ai ya tashi a banxa tunda ba shi xai
aureta ba, kyansa ace wannan uban shakuwar da suka yi kawai ya aureta suje can su
xauna tare, abinda ma ya fi kowa saninta a duniyar, ba shikenan sai su haifo
santala santalan 'ya yansu su xube ma Aisha tayi ta bari barin da bata yi ba da, ku
dai xumuncin ku duk kame kame ne ba shi da wani karfi Allah na tuba, Banda haka ba
sai ayi tuwona maina ba ko don Rukayya ta hadiye xuciya ta mace, ita kenan fa gare
Bukar a duniyar...." Tagumi Inna tayi kamar xata yi kuka tace "Ni dai naga abinda
ya isheni ni Asabe... Wa ya gayyato min wannan mata??? Huuu gaskiya ta Rasulu kin
lalace, ke kinsan uban sa6on da kika buga yanxu ki ja mana girgixan kasa kuwa? Kai
wasu dai kyansu dawanau wllh" Ta Rasulu tace "Sa6o don nace da Mujaheed ya auri yar
uwarsa Imaan? Ke dai baki son gaskiya, kuma baki tsoron Allah, Asabe kinyi watsi
da tsoron Allahn ki tun tale tale, kai tun kina gidan Alhaji isuhu, kawai jin ki
nake idan kince wasu basu tsoron Allah" Inna da ta wani tsuke fuska tace "To bari
kiji, wllh da Mujaheed ya aure min jika gwara tayi ta xama ba aure ina kallonta, me
xata ci da sauran Safara'u Allah na tuba?? Me xata yi da surka irin Rukayya
ta6a66iya, ke ma dai wllh muguwa ce ta Rasulu, waye kuma Mujaheed da xa ki ce ya
aurar min Imaan in shiga uku in lalace, Ina Imaan xata kai sa, ke dai wllh
fitinanniya ce tirrrr" Mikewa Imaan tayi ta wani hade rai ta nufi kofa, Inna ta
hade rai tace "Atoh maxa yi tafiyar ki Imaan kada a sa min ke a bakin duniya, Toh
ni dai tunda kin gama ganin kaya tashi kiyi tafiyar ki ta Rasulu ba ruwana kar ki
kawo mana rudani a lamarin mu, tunda ke rudaddiya ce, tashi ki tafi haka a gaida su
Muhammadu" Ta Rasulu tace "Toh banda Mujaheed din dama wa xai iya da ciwace ciwacen
Imaan Allah na tuba, ni fa tunda Uwar Bulasawa ta kore ni da d'ana ta hanamu abinci
na tsaneta har yau" Inna tace "Toh ae ba ni da Ahmadu ta kora ba ta Rasulu, kuma
ko da ni ta kora ma xuciyata me kyau ce fesss na yafe mata duniya da lahira, ke dai
kawai kiyi ta kanki ta Rasulu, bikin ma ni bance lallai sae kin xo ba kar ki kunya
ta ni don Allah ki rufa min asiri kiyi xaman ki a gida kin ji???" juyawa Mujaheed
yyi ya fita parlon, Inna ta bi sa da harara tace "Waye kuma Mujaheed da xan hada
jikata da?? Kai Allah dai ya isa da wannan tunanin naki gaskiya" Washegarin ranan
Imaan suka fara jarabawan waec, karfe biyu saura suka tafi yin first paper dinsu,
xuwa hudu da wani abu suka gama suka fito, tunda suka fito Maimoon ke kallon Imaan
da ta nemi dakali ta xauna, Maimoon ta karasa kusa da ita tace "What happened
Imaan?" Imaan ta kalleta a hankali tace "Kamar bana jin dadi" Maimoon tace "Toh
sannu yanxu driver xai xo sai mu wuce gida" Mariya ta nufo su tace "Amaryar mu how
was today's paper?" Imaan tace "Alhmdllh" Mariya tace "ki taso ku gaisa da Ya
sadeeq yana waje, yace in kira ki" Imaan ta d'an turo baki tace "A'a ni dai kice
masa baki gan ni ba plss" Mariya tace "C'mon ki taso mu je plss how will I say ban
gan ki ba" Maimoon ta dago Imaan tace "Mu je kila ma Driver ya xo" Maimoon na rike
da hannunta suka fita wajen gate din makarantar, a hankali Imaan ke tafiya har suka
isa gun motar Sadeeq ta tsaya, ya dinga kallonta daga glasses din idonsa yace
"What's wrong?" Mariya tace "Nima na tambayeta daxu tace ba komai" bude motar yyi
ya fito yana kallonta daga sama har kasa yace "Me ke damun ki?" Kamar xata yi kuka
tace "Ina yini?" Yace "I said what's wrong?" Ta sunkuyar da kai tace "I am not
feeling fine" Back seat ya bude mata yace "Shiga in ajiye ki gida" ta buda ido
sosai tace "Driver dinmu na xuwa" kallonta kawai ya tsaya yi, hakan yasa ta kalli
Mariya, Mariya tace "Ki tafi xa mu taho yanxu" Sadeeq yace "Kema shiga mu je may be
baxata yi tunanin guduwa xan yi da ita ba" dariya Mariya tayi tace "Toh kuma driver
yana hanya, ku tafi kawai xa mu jira shi da su Ummi" ta fadi haka tana nuna masa
Ummi dake can tsaye sai kallonsu take suna kallon direction dinta kuma ta dauke kai
da sauri, a hankali Imaan ta shiga bayan motar, Mariya kuma ta shiga front seat, ya
rufe motar ya xaga ya shiga maxaunin Driver ya tada motar suka bar kofar
makarantar, tun da suka dau hanya yake kallonta ta madubi, ita ko ta jinginar da
kanta ta rufe ido, har suka isa gida, parking yyi bakin gate yana kallonta ta
madubi still, can ya bude motar ya fito ya dawo baya ya xauna, sai a sannan yasan
bacci take da gaske, ya kai hannu forehead dinta ta bude ido da sauri ta koma baya,
yyi kasa da murya yace "Ina ke maki ciwo?" Ta sunkuyar da kai tace "Ina jin
xaxxabi" yace "Tun yaushe??" Tace "Da safe" shiru yyi bai ce komai ba, can ya sauka
motar yana kallonta yace "Come down" a hankali ta fara sakkowa motar ya kama
hannunta don taimaka mata, xata kwace hannun ya ki saketa, Bata yarda ta kallesa ba
ta fito motar, yana kallonta yace "Anjima xan xo maki da drugs" tace "Toh nagode"
saketa yyi ta juya xata shiga gate suka yi ido hudu da Mujaheed dake kallonsu yana
xaune gun mai kiosk dake layin, ta dauke kai da sauri ta shiga gate din, duk da
hada idon da Sadeeq yayi da Mujaheed shigewa motarsa yyi ya tada ya bar layin.

Thanks for d call and text fans...

Allah maimaita mana.... Ameen.


*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

71......

Da daddare Imaan na parlon Inna a kwance ta dalilin kiranta da Sadeeq yyi xai kawo
mata magunguna ita kuma bata son fita kofar gida shi sa ma ta taho part din Inna ya
sameta a nan, ko tsinke Inna bata bari a parlonta ba cikin kayan da aka kawo na
Imaan gaba daya ta kai su daki, dakin ma makulli take sa masa sai in xata shiga ta
bude idan ta fito kuma ta kulle ta daure makullin a ha6ar xaninta, Inna dake xaune
ta gama cin abinci kenan ta daura kafa daya kan daya ta ta6e baki tace "Ni dai da
ki tashi ki lallaba ki koma can bangaren ku ki jirasa, bana son wannan juye juyen
da kike min kamar macijiya gaskiya, ni bana son abinda xai gigitani da daddaren
nan, Bukar kuma ba kirki ne da shi ba tsaf xai iya cewa a parlona ciwon ya tashi in
shiga uku" Ita dai Imaan bata kulata ba, dai dai nan aka yi sallama kofar parlon,
Mikewa Inna tayi tana amsawa tace "A'a Bisimillah Bukar, sannu da xuwa" Sadeeq ya
shigo parlon, inna ta kinkimo lallausan carpet dinta da ta nade saboda masu shigowa
kallon lefe kar su 6ata mata ta shimfida masa, yana murmushi ya xauna ya gaisheta,
ta amsa tace "Tun daxu take xaxxabi nace ta tafi gidansu iyayenta su sani ta ki, to
dama wannan mutumin Mujaheed da yana nan ne yasan kan xaxxabin, to ban gansa ba
kuma nasa Maimuna ta kira min shi nace ga kanwarsa ba lafiya amma shiru bai xo ba,
ita kuma lkcn da ba shi da lafiya har cewa tayi a fasa kawo lefenta da kudin aure
sai ya ji sauki, su Ahmadu dai ne basu yarda ba, kowa da imaninsa kawai a rabu da
shi, shi ya sani...." Sadeeq dake fiddo drugs da ya kawo bai dai ce komai ba, can
ya kalli Imaan da ta juya masu baya, Inna tace "Atoh, tsorona daya kada uban yace a
nan xaxxabin ya tasar mata kuma ni daxun nan ta shigo min wllh" a hankali yace "How
are you feeling?" Shiru Imaan tayi bata ce komai ba, Inna tace "Idonta biyu wllh"
Imaan ta hade rai ta juyo sannan ta mike xaune, ledan maganin ya nuna mata yace "Ur
drugs with prescription, sai ki sha yanxu" Inna ta tafi kitchen ta dauko ruwan gora
da cup tace "Toh tashi ki sha" Sadeeq yace "Ni xan koma Kaka" Inna tace "A'a abinci
fa? uwarta ce tayi, da ke ni dama idan ba girkinta ba bana cin na kowa sai in
Amina, tuwo ne da miyar agushi yaji kayan hadi, sai kamshi yake xubawa in xubo
maka?" Yana d'an murmushi yace "Naci abinci kafin in taho kaka" tace "Toh ko in
juye maka ka tafi da shi?" yace "Ai kuma ni da abinci sai gobe idan Allah ya kai
mu" Inna tace "Atoh, haka naga Mujaheed ma yake yi, shi in dai karfe tara yyi bai
ci abinci da daddare ba to ya gwammace ya kwana haka bai ci komai ba, kaji fa
abinci ma sai an masa ka'ida, Ni ko nace aikin banxa, yo ko tsakar dare cikina ya
bukaci hakkinsa bana tashi in san yanda nayi na sallamesa ba? Wlh akwai hisabi mai
tsanani tsakanin mutum da yan hanjinsa, in dai ka cuce su to ranan gobe kiyama abun
baxai maka kyau ba, shi sa ba ruwana ko biyun dare ne naji yyi kugi xan tashi in
san abun yi, abinda ga kayan shayi kaca kaca a gidan" Sadeeq ya mike yana murmushi
yace "Sai da safe kaka, xa a kiyaye" tace "Toh Allah ya bada ikon kiyayewa" Yana
kallon Imaan yace "Sleep tight, Allah ya kara sauki" a hankali tace "Ameen, amma ba
wanda xai sani bacci coz I am having 10 o clock paper tomorrow" yace "Not at all,
xa ma ki iya tashi cikin dare kiyi karatun ki" daga haka ya nufi kofa Inna tace
"Toh baxa ki tashi ki daddage kiyi masa rakiya ba Imaan?" yace "A'a ta sha magani
ta kwanta kaka, sae da safe" Inna tace "Atoh, Allah ya tashe mu lafiya, ka gaida
iyayen naka, Allah yayi albarka" yace "Ameen kaka nagode" daga haka ya fita parlon
ya rufe kofar. imaan sun fara jarabawa da sati guda aka fara shirye shiryen biki a
gidan kasancewar biki biyu ne da nata sai Ya Yusuf... yau Friday Imaan na dawowa
exams karfe sha daya ta tafi part din Inna, bakin tap ta sameta tana wanke gaba
daya buckets dinta da iron sponge da detergent, Imaan ta shiga parlor ta xauna, Sai
kusan sha biyu Inna ta shigo tana cewa "Haka kawai, naga bokitai suna son komawa
kamar takashin kare, Allah ubangiji ya min tsari, na wanke su tass na shanya kayana
ni dai, kuma duk Maimuna ce me min amfani da abokitai gashi sun dauko hanyar
dafewa, gaskiya xan kira ubanta ya mana iyaka, idan nata xai siya mata to sai ya
siya mata ta rabu da nawa..." Tana kakkabe kujerunta tace "Toh ya jarabawan yau?"
Imaan tace "Alhmdllh" Inna tace "Toh Allah ya baku sa'a, sai kiyi kokarin ganin kin
cinye jarabawan kin fi kowa, to kin ci abinci kuwa?" Imaan tace "Ni bana jin yunwa"
Inna ta tabe baki jin yanda take amsa mata ta gama kakkabe kakkabenta ta dauko
tsintsiya, Imaan na kallonta tace "Inna Yaya yana xuwa?" Inna na gyara tsintsiyar
hannunta tace "Yaya? Waye kuma Yaya?" Imaan bata ce komai ba, Inna ta tabe baki ta
fara sharanta tace "Wai Yaya, to ajiyar Yaya kika bani Imaan? Ina xan ga wani Yaya
mutumi na gidansa, ni har na mance rabon da ya tako min nan ma, toh mutumi ya fara
sanin dadin aure me xai xo ya min kuma? A'a ni kam kusan sati kenan ban gansa ba"
Imaan dai sai kallonta take, Inna ta kalleta tace "Sako xaki bada a ajiye masa?"
Imaan ta turo baki tace "A'a kawai na daina ganinsa ne" Inna ta tabe baki tace "Toh
ba sai ki shirya ki tafi gidansa ba ko akwai wanda xai hanaki? Ni dai har abada in
taka cikin gidansa tunda iyayensa ba so suke ba, to me Mujaheed xai bani wanda
Allah bai ban ba? A'a ba ruwana ta kai na nake yanxu, ni ko naje gidan nasa fa ko
yar kudin motar nan baya bani, kullum a gantale nake dawowa idan naje wllh, to sai
kace uwata tace min je ki kya gani" Imaan tace "Toh ki kirasa" Inna ta kalleta da
sauri tace "In kirasa? Ke uban me ya hanaki kiransa, gafara xai min Mujaheed din
koko?" Imaan ta hade rai bata ce komai ba, Inna ta ci gaba da sharanta tace "Ni dai
kar ki dameni don Allah, waye kuma Mujaheed Allah na tuba" can kuma ta mike ta
dauko wayar ta mika mata tace "Toh kirasa dai mu ji" Karban wayar Imaan tayi, tayi
dialing number sa ta sa handsfree ta ba Inna, har ya gama ring bai dauka ba Inna ta
ajiye wayarta ta ci gaba da abinda take. Ranan lahadi warce Anty ta kira domin yi
ma Imaan gyaran jiki ta iso gidan duk da bikin saura sati uku, sati ukun kuma xata
yi tana gyara Imaan, kudi ba na wasa ba Aunty xata biyata, matar ta so ace Imaan ko
fita baxata dinga yi ba during the period amma hakan baxai yiwu ba sbda exams da
take, Tunda Umma taga sananniyar mai gyaran jikin da aka dauko hankalinta yayi
mugun tashi, duk gaba daya she is soo confused, sun koma gun mutumi kamar yanda
Hajiya Saude tace amma ita fa taga abu sai gaba yake ga biki saura sati uku har xa
a fara gyara amarya, tsabar yanda ta sa abun a rai har wani rama tayi abincin kirki
bata iya ci, hatta bacci gagaranta yake yi ynxu, ga uban kayan abinci da drinks da
aka fara jibgewa a gida na bikin... Anty ce xaune parlor tare da mata mai gyaran
jiki tana sake jadadda mata irin gyaran da take so tayi ma Imaan, Matar tace "Baki
da matsala Hajiya, ni tsakani da Allah nake aiki na" Anty tace "Toh sai abu na
biyu, a wajen kakanta xa a ke gyaran, amma fa kinsan yanda tsoffi suke sai ana yi
ana hakuri da kauda kai don Allah..." Dariya matar tayi tace "Ae muna da su Hajiya
wannan ba damuwa bane in sha Allahu" Umma dake kitchen ta shirya xata fita amma ta
kasa fita duk tana saurarensu, Anty tace "Toh mu je in raka ki bangaren kakar
tata..." Mikewa matar tayi rike da Babban jaka, Anty ta dau mata dayan suka fita
xuwa part din Inna, sai a sannan Umma ta fito tana danna wayarta, ta kai kunne,
Mujaheed dake bedroom dinsa ya fito wanka yana shiryawa ya kalli wayar Safeenah
dake gaban mirror yana ring, karasawa yyi ya dau wayar yana kallon screen din, har
kiran ya katse kallon wayar yake ganin number Ummarsa, can ya ajiye wayar sai gashi
ta sake kira, dauka yyi ya nufi kofa suka kusa cin karo da Safeenah xata shigo
dakin, karbe wayar tayi a hannunsa tace "Ka gaji da kwanciyar kayi wanka kenan..."
Bai tanka ta ba ya juya yana ci gaba da buttoning din shirt din jikinsa, ita kuma
ta fita dakin ta koma nata don daxu da ta shigo ganin ko ya tashi ne ta bar wayar a
dakinsa, ta daga kiran ta kai kunne tace "An tashi qlau Hajiya?" Umma tace "Lafiya
lau, ya jikin Mujaheed?" Safeenah ta tabe baki tace "Ya warke fa kawai yana
pretending ne sbda bai son ina xuwa inda yake tunda ina takurasa sai ya ci abinci
ko makamancin haka, wllh har yanxu na rasa gane kan Mujaheed, gaba daya ya ki gaya
min damuwarsa duk da dai da sauki yanxu, in dai ya fita aiki ne baya dawowa sai
nayi bacci..." Umma tace "Ke ki rabu da shi haka nan yake ba a taba gano inda ya
dosa, wani lkcn kuma tsabar miskilanci ne, ni da na haifi kayana kuma, kema ki fita
harkansa kawai idan kika ga yana shan kamshi sai ki ga kun dawo dai dai..."
Safeenah ta tabe baki tace "Ni ko ina xan sha masa kamshi ya hango wata a waje,
gwara inyi ta lallabasa a haka...." Umma tace "Toh ni ba wannan ba, Safeenah
shirye shirye dai sai gaba yake a gidanmu don yau ma aka dauko mai gyaran jiki xata
fara mata gyara..." Safeenah tace "Saura sati uku fa Hajiya, ba sai a xuba ido ba a
ga ikon Allah, idan fa mutum ya fiye axar6a6i da kyar ya dinga ganin abubuwa yanda
yake so, ke dai kawai ki xuba masu ido ki daina damun kan ki, auren nan ance ko an
daura bai fi na minti goma ba in ma an daura kenan to me xai dameki, ni ban cika
yarda da irin mutanen nan ba amma gaskiya mutumin nan da alama yana da gaskiya
sosai, duka duka nawa ya amsa wajen mu..." Umma ta sauke ajiyar xuciya tace "Ban
son in sakankance ne da maganar mutumi a xo ayi abun nan Ina ji Ina gani, wllh da
na shiga uku, shi sa gwara in buga nan in buga can, yanxu ma xan je gidan Hajiya
Balaraba" Safeenah ta tabe baki tace "Toh ni dai sai mun yi waya xan hada ma mijina
breakfast ya tashi" Bata jira cewar Umma ba ta katse wayar ta ajiye ta ja tsaki
tace "Ance maki ba don abinda Mujaheed yyi min sbda yarinyar da irin rainin da take
min xan bata lkcina a kan abinda ya dame ki ne, nima ta kaina nake shi sa na xage"
shiru tayi tana imagining ace da gaske d'an Bulasawa ya auri Imaan, Tabb har
takasu ma xata iya dinga yi ita surkar Bulasawa, kawai wataran sai a wani xo da
motoci kusan biyar gidanta a sunan Imaan ce ta xo gaida Yayanta, ta sakko daga
motar da gwalagwalai iri iri tana yatsine yatsine tana mata kallon banxa, tabbb, da
sauri Safeenah ta kauda tunanin a ranta tana cewa Allah ya kiyaye hakan ma baxae
faru ba, in sha Allahu talaka bawan Allah xa ki aura ki xo gidana in taka ki yanda
nake so in walakantaki, murmushi Safeenah tayi wai ta hango imaan ta xo ce ma
Mujaheed basu da abinci a gida shi kuma yace ta debo mata a nasu ta bata, Safeenah
ta tabe baki tace "Ae Kyawunta ma baxai bari wannan mafarkin nawa ya xamo gaskiya
ba, Allah dai yasa idan an rabata da yaron Bulasawan ba wani mai kudin xai kuma
xuwa mata ba don wannan shine anyi ba ayi ba...." Safeenah ta d'an yi murmushi a
ranta tace muna wargaza auren nan xa mu yi mata maganin bakin jini in sha Allahu,
ita da aure sai dai taga wasu na yi, shiru tayi tana tunanin to kada kuma fa ta
rasa miji wataran iyayen suce a hadata da yayanta tunda da aure tsakaninsu....
sosai gaban Safeenah ya fadi ta xauna gefen gado da sauri xuciyarta na bugawa, lkci
daya ta girgixa kai tace "A'a gwara dai a rabata da d'an Bulasawan kawai, duk
tsiyarta kuma baxata sake samun kamarsa ba sai dai kasa da shi" murmushi Safeenah
tayi ta mike ta fita dakin dai dai fitowar Mujaheed daga bedroom dinsa, rungume sa
tayi tana shigewa jikinsa tace "What should make for breakfast sweetheart?" Tabe
baki yyi ya kauda kai. Sosai Imaan tayi wani fresh tayi kyau ta dalilin gyaran da
aka fara mata, har wani sheki da glowing skin dinta yake, duk ta gifta ka dama
kamshin da xaka ji na musamman ne, a haka kuma take fita tayi jarabawa kullum, tun
biki na saura sati biyu dama wayarsu ya ragu sosai da Sadeeq, yawanci kuma ita ke
kiransa ma, shi ko sai dai ya bi miss call dinta. Yau Wednesday Imaan na dawowa
daga exam bayan tayi wanka ta sauya kaya Inna ta xubo mata abinci da yaji nama ta
ajiye mata a kusa da ita tace "Ni dai wai yaushe xa ku gama wannan kaddararren
jarabawan ne ki nutsu waje daya a maki gyaran nan cikin kwanciyar hankali, wannan
ae fitina ne ana gyara yana bin iska tunda kullum sai kin fita..." Imaan na kallon
abincin da Inna ta ajiye mata tace "Ni fa bana jin yunwa" Inna ta kalleta da sauri
tace "Ni dai na shiga uku da wannan 'ya ta Bukar, ko kumallon kirki fa baki yi ba
daxu, a haka xa a kai ki gidan Sadeeq din nan da sati biyu a rame duk k'ashi a
wuya?? Ni dai ba ruwana bari Amina ta shigo tunda Aisha ta sallama mata ke gaba
daya" Imaan ta tura abincin xata kwanta kan kujera a fusace Inna tace "Ni fa bana
son a dameni gaskiya sai ince ki tattara kayanki ke da mata mai gyara ku koma
bangaren ku yanxu nan, ya xan dinga maki magana kina walakanta ni, dama katuwar
mata mai gyaran jiki ce tace ki ci abinci kafin ta dawo taje siyo wasu kayayyaki a
kasuwa ta dawo, to idan ta dawo ba ki ci ba fa..." Imaan tace "Inna to ko dai yaya
ba shi da lafiya ne har ynxu?" Bude baki Inna tayi tana kallonta da mamaki, can ta
xauna tayi tagumi a hankali tace "Naga abinda ya isheni ni Asabe, waye kuma Yaya??"
Imaan ta turo baki ta dauke kai, Inna tace "Wai akwai abinda ya hada ki da Mujaheed
ne bayan kasancewar Ubansa wan ubanki? Akwai wani dangantaka tsakaninku ne dama da
ban sani ba? Wato kwana biyu shiru bai shigo ya takura ki ba shine duk kika damu
tunda ke gantalalliya ce, toh sai ki tashi ki tafi gidansa, Toh wai ma ina ruwanki
da wani yaya ke da xa ki yi aure nan da kwana sha biyar? Ko dai akwai ajiyar ki a
gunsa ne bai baki ba kafin a kai ki daki in kirasa ya baki?" Imaan ta wani hade rai
tace "Toh kawai daga tambaya? Naga ya dade bai xo ba kuma ba haka yake ba" Inna
tace "Toh idan lalacewa yyi ya fara hakan fa?? Ko idan ya xo me xai bani banda ya
tsokane ki ya cuce ki ya wuce don ma naga tunda yayi aure yyi hankali ya daina sa
ki kuka, Ke dai ki dinga jin tsoron Allah kiyi ta kanki ba ruwana, to ni ko
shekaranjiya na sa Ummi ta kira min shi katon ya ki dauka, wa ya sani ko fushi yake
na daina xuwa gidansa, sai kace gidan aljanna Allah na tuba, ni dai ba ruwana wllh"
daga haka Inna ta shige daki, imaan ta bi ta da harara ta jinginar da kanta da
kujera bata ce komai ba.... Ana saura kwana 7 biki Imaan ta gama jarabawa
kasancewarta science student, Maimoon da Mariya kuma nan da kwana shidda xa su gama
jarabawan don art class suke, yau kusan kwana hudu basu yi waya da Sadeeq ba, bai
kirata ba ita ma bata kirasa ba, tana bedroom din inna bayan la'asar hannunta rike
da hisnul Muslim wayarta ya fara ring, daukar wayar tayi tana kallon mai kiranta,
ganin number Sadeeq ta daga ta kai kunne tayi shiru, shirun shi ma yyi na kusan
second goma sannan yace "How are you?" Murya can ciki tace "Am good" yace "Ina
waje" ta kalli agogo bata dai ce komai ba, yace "Or are you busy?" Tace "Ni ba bari
na ake ina fita ba..." Ya d'an yi shiru sannan yace "What did you mean?" Tace "Bana
fita" yace "Ohk gida ake biyo ki da papers din ki kenan?" Turo baki tayi tace "Waye
ubana da xa a biyo ni gida da papers?" Yace "What exactly are you trying to say?"
Kin cewa komai tayi, Yace "Ohk then kar ki fito..." Xai katse wayar frnd dinsa
Saleem dake tsaye gefensa jikin motarsa ya amshi wayar ya kai kunne yace "Haba
amarcy ba dadewa fa xa kiyi ba, ki d'an fito pls, just few minutes" a hankali Imaan
tace "Toh" Saleem ya katse wayar yana kallon Sadeeq yace "Amare fa lallaba su ake
basa laifi Dr" Sadeeq dai bai ce komai ba yana rungume da hannunsa, Saleem yyi
murmushi yace "To saki ran kafin ta fito mana" Nan ma dai Sadeeq bai tanka sa ba,
Hijab Imaan ta saka sai dai ba har kasa ba, ta fito parlor ta sanar ma Inna sadeeq
na kiranta a waje, Inna dake xaune parlon tare da mai mata gyaran jiki suna hira
sai kallon takwarar tata take, can a hankali cikin sanyin murya tace "Ashe dama
haka kike da kyau ban sani ba Imaan?" Dariya sosai mai gyaran jiki ta shiga yi tana
kallon Inna dake sa ta nishadi tun xuwanta, kwata kwata bata gajiya da fadan Inna
da labaranta masu kai da marasu kai, ga uwa uba tsaftarta, komai na Inna burgeta
yake, Imaan bata san lkcn da tayi murmushi ba bata dai tanka Inna ba ta nufi kofa
ta fita, Inna na kallon mai gyaran jikin tace "Allah kuwa yar nan, dubi fa yanda
take walkiya da kyalli, ga kamshi kaca kaca ta ko ina a jikinta, duk inda ta gilma
sai ya kamu da kamshin da take yi, ni dai xan kara maki dari biyu da tsinkin sabulu
a kudin da xa su biyaki, gaskiya kin fito min da jikata, kai har dambun nama xan
maki ni dai" Matar dai sai dariya take tana ma Inna godiya, Imaan na isa part dinsu
ta shiga don daukan hijab mai tsayi, Ammi ta fito daga kitchen jin an bude kofa,
Imaan ta gaisheta sannan ta nufi dakinta, Ammi ta bi tada ido, ba a dau lkci ba ta
fito sanye da hijab har kasa, tana kallon Ammi a hankali tace "Ana kirana a waje
ne..." Shiru Ammi tayi tana kallonta, hakan yasa Imaan ta sunkuyar da kanta, Ammi
ta karaso kusa da ita ta sa ta xauna saman kujera ta xauna kusa da ita tace "What's
wrong with you Imaan?" Imaan ta kalleta da sauri tace "Ba komai fa Ammi" Ammi tace
"Noo there is something kar ki ji komai ki gaya min..." Imaan ta girgixa mata kai a
hankali tace "Da gaske ba komai Ammi...." Ammi tace "Toh shikenan, but don't forget
baki da wanda ya wuce ni a duniya, idan baki gaya min damuwar ki ba ban san wanda
xa ki gaya ma ba" Imaan ta sunkuyar da kai tana murmushi tace "Idan akwai xan gaya
maki ai Ammi" Ammi tace "Toh ki kwantar da hankalin ki and keep praying, kar ki
gaji da addu'a, kuma ki dinga cin abinci sosai kin ji" murya can kasa Imaan tace
"Toh nagode Ammi" Ammi tace "Ko me kike bukata ki kirani a waya ki sanar min" Imaan
tace "Toh bari in je ana jirana" Ammi tace "Toh ki kame kanki" mikewa Imaan tayi ta
nufi kofa Ammi ta bi ta da kallo har ta fita ta kulle kofa. Tunda Imaan ta iso part
din su Maimoon Umma dake xaune tare da Hajiya Balaraba kan fararen kujeru take
kallonta ko kiftawa babu, ta sunkuyar da kai ta gaishesu a hankali Hajiya Balaraba
ce kadai ta amsa a dakile, tuni kamshin da take ya daki hancinsu gaba daya, har ta
fita gate basu daina kallonta ba, Da ba don Saleem da ya ki barin sa ba da tuni
Sadeeq ya bar wajen ganin har bayan minti goma bata fito ba, tana fitowa sau daya
ya kalleta ya ci gaba da danna wayarsa, Saleem ya mata murmushi har ta iso inda
suke ta tsaya a gefe a hankali tayi masu sallama sannan ta gaishesu kanta a kasa,
Saleem ya amsa yace "Hope an gama exams lfya?" Tace "Alhmdllh" Sadeeq ya maida
wayarsa aljihu yana kallonta ta cikin glasses din idonsa a takaice yace "Wani
shirin xa ku yi a nan gida?" Shiru tayi da farko, sai kuma ta kallesa taga wani
direction yake kallo daban, tace "Nima ban sani ba" yace "Ohk then, on Thursday xa
ayi dinner...." Yana magana ya bude mota ya fiddo hadadden IV mai yawa sosai ya
mika mata ta risina ta amsa, shi dai bai yarda sun hada ido ba, yace "I think
that's all, dama sbda IV din na xo, if there is anything I will call and let u
know" daga haka ya bude driver seat ya shiga, ita dai sai kallonsa take, Saleem na
mata murmushi yace "Toh mun gode amarya, ki shiga ciki xa mu koma" tayi murmushin
karfin hali ta juya ta nufi gate, Saleem ya xaga ya shiga front seat, Sadeeq ya
tada motar suka bar layin, suna hawa kan titi Saleem yace "Plss ka rage wnn xuciyar
Sadeeq... I don't like the way u treated her gaskiya" Sadeeq dai sai driving dinsa
yake bai ce masa komai ba, Saleem ya tabe baki ya fiddo wayarsa yana dannawa,
Sadeeq yace "Raina min hankali take" Saleem yace "Meye abun rainin hankali" a d'an
fusace Sadeeq yace "Baka ji abinda tace ba kenan, wai bata san abinda xa su yi ba a
gida na biki, wato babu events da xa su yi kenan take nufi, which is a lie" Saleem
ya tabe baki yace "Duk wannan xumudin da ka dinga yi kwanki kafin a saka bikin duk
naga babu shi yanxu Sadeeq" Sadeeq ya rage gudun da yake yana shafa kansa a hankali
bai dai ce komai ba....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

72......

Ranan lahadi da karfe sha daya Mama Hadiza ta iso gidan tare da autar ta Maryam, a
part din su imaan suka sauka as usual, sai bayan azahar sannan suka taho part din
Inna, Inna dake xaune ta gama hada ma Imaan kwadon rama da ya ji kayan hadi a bowl
kenan tayi masu kallo daya ta dauke kai ta rufe bowl din raman ta ajiye a gefe,
Maryam ta tabe baki ta xauna tana kallon TV, Mama Hadiza ta xauna kusa da Inna tana
murmushi tace "Sannu Innata" ba tare da Inna ta kalleta ba tace "Yauwa, a rufe min
kofata kada k'uda su biyo bayan ku su shigo min parlor" Mama Hadiza ta mike ta rufe
kofar ta dawo ta xauna tana murmushi tace "Ina yini Inna? Fatan mun same ku lafiya"
Inna tace "Lafiya lau, ai naji labarin tun sassafe ku ka shigo nan dai ne ba ku xo
ba sai yanxu" Mama Hadiza tayi dariya tace "Mun d'an kintsa ne Inna, ya shirye
shirye?" Inna tace "Atoh suna can suna yi, ko shawara ma basa yi da ni wllh ban ya
ake ciki da maganan bikin ba, nasan dai ta Rasulu xata gayyato kawayenmu gaba daya
sai a kafa mana katon rumfan nan da kujeru mu xaxxauna a tsakar gida" Mama Hadiza
ta sunkuyar da kai tana murmushi, Inna na kallon Maryam tace "Toh ita wancan har
yau ba manema ne yarinya ta xama sangamemiya ban ji ana batun aure ba Hadiza, kina
gaba tana biye da ke fa a baya" Maryam ta hade rai ta gaisheta, Inna tace "Lafiya
lau, baki da samarin ne?" Maryam dai bata ce komai ba ta dauke kai, Mama Hadiza dai
sai murmushi take tana kallon uwartata, Inna ta tabe baki tana gyara daurin
dankwalinta a hankali tace "Ni dai ba ruwana" Mama Hadiza tace "Toh Ina amaryar,
ango dai shi ya dauko mu airport daxu?" Inna tace "Isuhu ai ya lalace ya daina
shigo min nan kwata kwata sai dai mu ci karo a tsakar gida, Ita kuma Imaan suna can
bandaki tare da mata mai gyaran jiki, ke kya ce canja mata fata xata yi, ni kada
garin neman ido a rasa gira a kona min jika in shiga uku, iyayin matar yyi yawa
wllh, gashi duk tayi ta ajiye min kaya ta ko Ina kamar tababbiya, ni ko in tattara
in jibge mata su a kan katuwar jakarta, ni dai na gaji wllh" Dariya Mama Hadiza ta
dinga yi, can tace "Mujaheed fa inna?" Inna ta kalleta tace "Ai Mujaheed ya daina
xuwa gidan nan, ni na fi wata ma ban gansa ba, ba laifin xaune balle na tsaye ban
san me na masa ba ya dauke kafa" Mama Hadiza ta fiddo wayarta a jaka tace "Toh
yanxu ai dole ya xo, jiya ma mun yi waya da shi kafin in taho..." Tana magana tayi
dialing number Mujaheed, har ya gama ring bai dauka ba, Inna tace "Atoh, ko dai an
sace wayar tasa ne, nima har na gaji da kira ba a dauka fa" Imaan ce ta fito daki
sanye da Hijab har kasa, ta wara ido ganin Maryam ta nufeta da sauri ta rungume ta
cike da jin dadin ganinta, Maryam ta wara ido tace "Waoww sis kinga yanda kike
glowing kuwa? Wllh kin yi kyau sosai" Imaan na murmushi ta koma gun Mama Hadiza ta
durkusa ta gaisheta, Mama Hadiza ta jawota jikinta smiling broadly tace "Maa sha
Allah, my daughter kinyi kyau sosai, ya shirye shirye" Imaan ta boye fuskarta
jikinta a hankali tace "Lafiya lau mama" Inna tace "Ai dama ita Imaan da kyanta,
wannan gyaran kyanshi dama Ummi, ita ce mummunan gidan, gaskiya ban san inda
Rukayya ta samo ta ba..." Dariya Mama Hadiza tayi tana kallon Inna, Inna tace
"Allah kuwa" Mama Hadiza na kallon Imaan tace "Toh tafi ki goge jiki ki shirya"
Imaan ta mike tana murmushi ta wuce daki Maryam ta bi ta da kallo don kyau ba na
wasa tayi ba. Imaan na xaune tare da Maryam a bedroom din Inna bayan la'asar,
Maryam dake ta kallonta a hankali tace "Kina nufin ba events da xa ayi Imaan?"
Imaan ta bude hannu tace "Nima ban sani ba sai dai ki tambayi Maimoon, daxu dai ya
kawo IV, su xa suyi dinner" Maryam tace "Toh dress code fa? Kuma wani kayan yace xa
ki sa?" Imaan tace "Oho ni bai gaya min ba" Maryam tace "Kamar ya, ba ku shirye
shiryen tare ne?" Imaan ta tabe baki kamar baxata ce komai ba, sai kuma tace "Ni ko
waya fa bama yi" da mamaki Maryam tace "Saboda me?" Imaan tayi shiru tana kallonta,
Maryam ta kamo hannunta tace "Talk to me, what's happening?" Imaan ta sauke idonta
tace "Nima ban sani ba, baya kirana sai dai in ni na kirasa, kuma ba xuwa yake ba"
Maryam ta xaro ido tana kallonta da mamaki, Imaan ta d'an yi murmushi tace "In xubo
mana abincin ynxu?" Maryam tace "Plss mu yi magana ki ajiye batun abinci, toh ke
kina ga babu abinda kika masa Imaan?" Imaan ta girgixa kai a hankali tace "Ba
abinda na masa wllh, he just changed all of a sudden, I don't know why...." Sai
kuma tayi shiru lkci daya hawaye ya kawo idonta, Maryam ta kasa daina kallonta lkci
daya jikinta yyi sanyi, can cikin sanyin murya tace "Kuma kin tambayesa abinda kika
masa? Kila kin yi offending dinsa baki sani ba" Imaan tace "That doesn't warrant
him to change his attitude, ko don yaga few days ya rage a daura mana aure shi sa
yake min haka" sai kuma ta fara kuka a hankali, Maryam taji gaba daya hankalinta ya
tashi ta rungumeta tace "Plss kar kiyi kuka, we have to find out why d sudden
change of attitude, be strong plss" Imaan dai bata ce mata komai ba, bayan wani
lkci ta mike a hankali tace "Bari in xubo mana abinci" daga haka ta fita dakin.
Bude Ido Sadeeq yyi don ganin wanda ya shigo masa bedroom dinsa that is almost out
of bound for everybody except his mum, Mikewa xaune yyi yana kallonta, Mummy tace
"Sai yaushe xaka kai masu kayan da ka bari parlor na ga lokaci na ta wucewa Abba,
today is Tuesday, or do they have any other alternative?" Yace "Mum xan ba Mariya
ta kai anjima" Da mamaki Mummy tace "Mariya kuma, kaga ina involving din su a
harkata a gidan nan?" Sadeeq ya koma ya kwanta yace "Kawarta ce fa Mum, ta san
gidansu ai, I don't think I am going out today" Mummy tace "You tell me what's
wrong with you this days Sadeeq, meye matsalar ka" Mikewa xaune yyi yace "Mummy
frankly speaking gaba daya naji bana son auren nan kuma, am I even supposed to get
married now? Isn't it too early? Sure Ina sonta amma bana son auren ynxu gaskiya"
Wani kallo ta dinga masa, kafin tace "You are stupid..." tashi yyi ya wuce bathroom
ya rufe kofar gbam, ta fi minti biyar tsaye dakin mamaki fal xuciyarta kafin ta
juya ta fita. Sadeeq ne xaune parlon Dad dinsa da yammacin ranan, tun shigowar sa
parlon bai yarda ya daga kansa ba, Mummy ma na xaune parlon sai kallonsa take,
Alhaji Ahmad Bulasawa dake tsaye ya gama duk fadan da xai yi kamar xai ari baki
daga karshe ya xauna yana kallon Sadeeq da kyau yace "If you think I have a son
that will tarnish my image here in my mother's land... you are mistaken Abubakar,
ban haifi wannan d'an ba, kindly get out from my sight now, aure ba fashi tunda ba
wani ya nema maka yarinyar ba, kuma ba wani yace ka fito da xancen aure ba yanxu" A
hankali Sadeeq ya mike ya nufi kofa ya fita parlon Mummy ta bi sa da kallo, Alhaji
Ahmad yace "In sha Allah daurin aure babu fashi ranan juma'ah..... No one is
tarnishing my image" direct Sadeeq part din Step mum dinsa ya wuce, Aunty na
dakinta ya sameta, ta ajiye abinda take yi tana kallonsa tace "Ango kayi scarce, ya
shirye shirye" ya karasa kusa da ita ya xauna ya rike kansa, da mamaki tace "Me ya
faru Abba?" Da kyar ya dago yana kallonta da idanuwansa da suka kada yace "Pls
Aunty kiyi ma Abba magana a daga bikin nan, wllh naji gaba daya am not ready to be
a family man, wani lkcn sai ayi amma ba yanxu ba" Bude baki Aunty tayi tana
kallonsa, da wani expression tace "Are you alright Sadeeq? Kana da hankali kuwa,
biki saura few days kace a daga, waye kake son maidawa kananun mutane, ubanka dai
koh? Kai ma kasan Abban ka will never support this, wani laifi fatiman tayi maka
ne?" Ya girgixa kai a hankali yace "Ni bata min komai ba, kawai naji bana ra'ayin
aure yanxu, ba cewa nayi a fasa ba, a daga kawai nake so... " Aunty ta saki baki
tana kallonsa with much surprise, can ta girgixa kai tace "Don Allah ka rufa mana
asiri, kada ka maida mu kananun mutane a idon jama'ah Abba, haba Sadeeq this is
very unusual of you, me ya same ka haka, ko dai gantalallun frnds dinka ke xuga
ka??" Rasa ma me xai ce mata yyi, can ya mike kawai ya fice daga dakin ta bi sa da
kallo baki bude. Mummy ta gama hada duk kayan da suka ma Imaan kala uku masu tsada,
daya na dinner biyu kuma na events idan xa su yi a gida, immediate din Sadeeq Annur
ta samu a dakinsa ta mika masa tace "Gashi ka kai ma yayanka yana garden, kace nace
ya tafi ya kai masu yanxun nan" daga haka ta fita dakin. Bayan Magrib Sadeeq yyi
parking kofar gidansu Imaan ya kashe motar ya fito ya dau ledan kayanta dake bayan
motar, ya fi minti biyar tsaye jikin motarsa ya ki kiranta a waya, can kawai ya
shiga cikin gidan kamar mai counting steps dinsa, direct part din Inna ya nufa,
yayi sallama bakin kofar parlon, Inna ce ta amsa sannan ya shiga, Mama Hadiza dake
xaune parlon tana cin abinci suna hira da Hajiya Bilki mai gyaran jiki, ta rufe
abincin ta ajiye gefe ganinsa, Inna ta mike ta shimfida masa darduma tana masa
sannu da xuwa, sauke kansa yyi kasa yana d'an murmushi ya ajiye ledan hannunsa ya
xauna a hankali ya gaida su gaba daya, Mama Hadiza ta amsa tace "Sannu da xuwa
Sadeeq..." yace "Kun xo lafiya mama?" Tace "Alhmdllh, ya shirye shirye?" Yace
"Alhmdllh" Inna tace "Kaga yanxu kuwa ta fita taje raka wannan yarinya Maryam su
gaisa da Ahmadu ko a kira maka ita a waya?" Yace "A'a kaya ne dama na kawo mata"
Inna tace "Atoh ai shkkn sai in ajiye mata, kana dai cin abinci kuwa Bukar naga kai
ma ka fige kamar amaryar taka" murmushi yyi ya sunkuyar da kansa yace "Ina ci Kaka"
da damuwa Inna tace "Aa ku dai yi hakuri ku kwantar da hankalin ku ko kwa yi kyan
gani da biki don Allah..." Shi dai bai ce komai ba, Bude kofar parlon aka yi
Mujaheed ya shigo da sallama, sanye yake cikin kananun kaya hannunsa rike da
makullin mota, Tunda ya shigo Mama Hadiza ke kallonsa, yyi murmushi yana shafa
kansa ya karasa cikin parlon, sai da ya fara ba ma Sadeeq hannu sannan ya xauna
kusa da Mama Hadiza a hankali yace "Kun xo lafiya mama?" Ta rike ha6a tace "Kayi
rashin lafiya ne ba a gaya min ba Muhd?" Yace "Ae naji sauki yanxu,
kwanaki ne nayi rashin lafiya, tare da Maryam ku ka xo?" Inna dake kallonsa da
kyau tace "Toh dai yau ga ni, ga Mujaheed, ga Hadiza da katuwa mai gyaran jiki, ga
kuma yaron nan Sadeeq, sai Mujaheed ya ji tsoron Allah ya fito ya gaya ma kowa
abinda na masa a parlon nan yanxun nan... Don ni ban san abinda na masa ba, idan
Mujaheed bai saka min da abun kirki bautar da na masa ba yana yaro ai baxai guje ni
ba yanxu da tsufa na, Hadiza yau kusan wata shidda kenan ban sa Mujaheed a ido ba,
ba laifin tsaye balle na tsaye, ba lafin fari balle na baki, ko na kirasa baya
dauka to ni dai gaskiya ya fito ya fadi abinda na masa ko in bar sa da Allah..." Ko
kallonta Mujaheed bai yi ba sai juya makullin hannunsa yake, Hajiya Bilki dai sai
dariya take kasa kasa, Mama Hadiza ta kasa cewa komai sai kallon Inna take ganin
yanda ta ci serious ta tsuke fuska, Sadeeq dai idonsa na kan wayarsa da yake
dannawa, cikin rawar murya Inna tace "Ko don nace matarsa mayya ce ya kullace ni
ban sani ba, toh banda haka me na ma Mujaheed, wllh ban masa komai ba, ko wani kaga
xai mance da ni haka a rayuwa kai ba mai tare min bane balle kai da kanka, gashi
duk ka wani fige kamar kazar Hausa kuma ace yarinya ba mayya bace.... Ni dai ba
ruwana" Mujaheed na kallon Mama Hadiza yace "Ba ku taho da su El-Ameen ba?" Mama
Hadiza ta sauke ajiyar xuciya tace "Xa su taho tare da babansu xuwa jibi, xai xo
daurin auren shi ma" Inna ta bude baki tace "Toh shi Mujaheed ba mutum bane da ya
ki xuwa nasa daurin auren?" Mama Hadiza tayi murmushi tace "Inna kar ki manta Imaan
ita kadaice gun Yaya, banda haka ma da ba lallai nima in xo ba tunda yaushe na xo
bikin Mujaheed, to wannan dalilin yasa babansu Maryam ma xai xo daurin auren
nata...." Inna ta tabe baki tace "Ku dai ku dinga tsoron Allah, ku dinga abu saboda
Allah, wato shi Mujaheed bai cancanci a xo nasa ba sai na Imaan, to ubansa ya sha
Mama ya bar ma ubanta, duk babu wani banbanci" dariya kawai Mama Hadiza tayi bata
dai ce mata komai ba, shi dai Sadeeq idonsa na kan wayarsa, Maryam ce ta fara
shigowa parlon Sadeeq ta fara gani ta gaishesa da fara'a, ya amsa yana murmushi
yace "Kun xo lafiya Maryam?" Tace "Alhmdllh Dr, ya shirye shirye" yace "Lafiya lau"
ta wara ido ganin Mujaheed tace "Ya M.A..." Imaan ta shigo parlon hannunta rike da
fruit salad da Ammi ta bata ta kawo ma Mama Hadiza, ganin Mujaheed xaune parlon ta
tsaya tana kallonsa ko kiftawa babu, daga kai yyi ya kalleta, bata san lkcn da ta
ajiye bowl din hannunta ta nufesa da sauri ta xauna kusa da shi tana kallonsa ta
wara ido tace "Yaya..." Ya shafa kansa kamar baxai ce komai ba sai kuma ya d'an ja
hancinta yace "Kanwar Yaya..." dariya ya bata, ganin yanda take dariya yyi murmushi
yana kallonta, rungumesa tayi a hankali tace "I missed you" Kallonsu kawai Sadeeq
yake, Mama Hadiza ta dinga ma Imaan wani kallo amma imaan ko sanin tana yi bata yi
ba, Inna tayi tagumi ta rasa abun cewa sai yan idanuwa, Can a fusace tace "Ke dai
gantalalliya ce wllh, katuwa da ke ki fada jikin mutumi wai Yaya, yanxu fa ke matar
wani ne, da ba don mijin naki ya san alakar ki da Mujaheed ba me kike tunanin xai
faru yanxu? Kawai mata daga shigowa ki dare kan mutumi kice Yaya???" Da sauri Imaan
ta sake Mujaheed ta juyo, sai a nan suka yi ido hudu da Sadeeq, sosai gabanta ya
fadi ta xamo kasa tana kallonsa, Mama Hadiza dai ta kasa cewa komai amma gaba daya
kunya ya isheta, Inna tace "Toh waye kuma Yaya Allah na tuba ke ba yarinya ba
yanxu, mutumi yyi aurensa kema xa ki yi naki, ai kuma sai a hakura haka sai 'ya
yanku su ci gaba da xumuncin, ni dai ban taba ganin haka ba...." Sadeeq ya d'an yi
murmushi ya mike yace "Kaka ni xan koma yanxu" Inna tace "Au to baka sha ko ruwa ba
Bukar" yace "Ae daga gida nake Kaka" Inna tace "Toh shikenan Allah maka albarka,
kuma ka dinga cin abinci kaji" yace "In sha Allah" Yana kallon Mama Hadiza yyi kasa
da kai yace "Mama xan koma, Allah huce gajiya" Mama Hadiza tace "Toh ka gaida mutan
gidan Sadeeq na gode kwarai" kofa ya nufa, Inna na kallon Imaan tace "Ae sai ki
tashi kusa da mutumin nan ki tafi ki sallami mijin ki koh" Kin tashi Imaan tayi,
Mama Hadiza na ganin Sadeeq ya fita tace "Baxa ki tashi ki fita ba shashashar
yarinya, kawai ki kama ki rungume mutum a gabansa sbda baki da natsuwa" a fusace
Inna tace "A'a ke kuma bana son fadan rashin gaskiya, wa gareta da xata rungume
banda Mujaheed din, a haka suka taso abun su dama can, shi ma mijin ai ya sani, ko
ce maki aka yi bai sani ba, sarai ya san yayanta ne bata da kamarsa a duniya ko kun
haifa mata wani yayan ne ban da shi Mujaheed din?? Ni bana son fadan rashin gaskiya
wllh, kinsan yaushe rabon mu sa Mujaheed din a ido ne? kuma ta gansa baxata nuna
farin cikinta ba, kullum sai ta min xancensa don ma Ina gwaleta kamar bai dameni ba
alhalin kullum da daddare sai nayi mafarkinsa, kawai mata daga xuwa ki hau yar
mutane" Hajiya Bilki ta dinga dariya tana kallon Inna, a hankali Imaan ta mike ta
bi bayan Sadeeq Mujaheed ya bi ta da ido.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788
73.....

A hankali Imaan ke tafiya tana kallon Sadeeq da har ya kusa gate sbda saurin da
yake, kafin ta fita kofar gida har ya shiga motarsa ya wuce, ta bi motar da kallo
sannan ta juya a sanyaye ta koma part din inna, Mama Hadiza dai har lkcn ta ki sake
fuska don ba karamin 6ata mata rai abinda Imaan tayi yyi ba, tana shigowa parlon
kuwa ta dinga hararanta fuska daure, Imaan na ganin haka ta sunkuyar da kai ta wuce
bedroom din Inna duk jikinta yyi sanyi, Inna ta bi ta da kallo sai kuma ta kalli
Mama Hadiza tace "Toh ba shikenan ba har ta sallamesa ta dawo, amma kina neman
maida karamar magana babba sbda rashin tsoron Allah, ai shi Sadeeq din ya fi kowa
sanin tsakaninsu da Mujaheed, kuma yaro ne mai hankali da natsuwa, tunda nake ban
taba ganin yaro natsatstse irin sa ba, gashi kwata kwata abun sa bai rufe masa ido
ba, kyauta yake kamar bai san ciwon dukiyar ba, to bayan ni har ku ma baxa ku huta
ba aka ce maki Hadiza??" Ita dai Mama Hadiza bata ce komai ba tayi tagumi, Inna ta
tabe baki tace "Ni dai ba ruwana... A dinga kyakkyawan xato domin Allah, sai kace
warce ta fada kan wani kato can a titi, wannan ae yayanta ne Mujaheed" Mujaheed ya
mike yana kallon Mama Hadiza yace "Toh na gaishe ki Mama Allah ya huce gajiya sai
na shigo gobe" Inna na kallonsa tace "Amma kai dai Allah ya xuba maka shegen rowa
Mujaheed kamar uwarka, banda haka ina laifin ka riko mata Yar gasasshen kazar nan
da yar lemo... ka wani shigo gansansan daga kai sai kai, inda Isuhu ya fi ka kenan
gaskiya" Mujaheed dai bai tanka ta ba ya nufi kofa, tace "Toh nayi magana daxu baka
ce komai ba, ina fa da labarin abinda kayi ma Seeyama lkcn bikinta, to ita Imaan ko
don ba ubanku daya ba, naga har yanxu shiru baka yunkuro ba, kyansa dama kawai ka
bata kudin ni nasan abinda xan mata da shi, kar ka siya mata komai ba abinda Ahmadu
da Bukar basu yi mata ba, kudin xai fi mata amfani gaskiya" ya juya ya kalleta yace
"In xan bata abu ae ba sai kin sani ba Hajiya, sai kace mahaifiyarta bata
kusa....." Daga haka ya fice daga parlon Inna ta rike ha6a tana kallon Mama Hadiza
tace "Ke me yake nufi kenan? Kaddai baxai ma yar uwarsa komai ba bikinta sukutum da
guda?? To bari dai in xuba ma saurautar Allah ido, amma wllh in har Mujaheed bai
bada gudunmawa mai kauri bikin Imaan ba lalacewa ta samesa duniya da lahira, kuma
ban san da wani idon xai kalli ubanta ba" Washegari laraba da safe driver ya ajiye
su Imaan saloon, Mai wajen da kanta tayi mata gyaran bayan ta gano amarya to be ce,
Banda kallonta babu abinda ake yi a saloon din, don gaba daya she looks so new,
tayi wani haske da fresh sai glowing ko ina na jikinta yake kamar balarabiya, dubu
ashirin Abba ya basu na gyaran gashin su uku don Ummi da Rahma basu yarda sun biyo
su ba, da kyar Maryam ta lallaba Imaan ta yarda ayi mata kitso a gashinta, imaan
har ta mance rabon da tayi kitso, haka aka ta daure aka rangada mata kitsonta
kanana mai kyau, sai kusan azahar suka kira driver ya xo ya maida su gida. Sosai
gida ya cika da jama'ah na kusa da nesa duk da sai Juma'ah ne bikin amma kai kana
ganin jama'ahn gidan kasan only child ce xa ayi ma aure, kuma ga biki ya hade biyu,
gaba daya yan uwan Ammi suna gidan, daga su har 'ya yansu, Aunty ma duk yan uwanta
na kusa da nesa sun iso, Bakin ciki kamar xai kashe Umma, kwata kwata taki yarda ta
fito daga dakinta har da sa makulli daga ciki abun duniya ya taru ya mata yawa,
anya auren nan baxa ayi sa ba kuwa?? Tambayar da ta dinga yi ma kanta kenan, wata
xuciyar na assuring dinta baxa ayi ba ta xuba ido kawai. Su Imaan na komawa gida da
awa daya mai lallin da Aunty ta kira ta xo gida yi mata lalle, Inna ta gama xuba ma
imaan pepper soup din da Aunty ta aiko mata da abinci kenan mai lallin ta shigo
tare da Maimoon, Maimoon tace "Inna mai lalli ce" Inna ta kalli mai lallin da
damuwa tace "Naga jaraba, ko abinci fa bata ci ba kika xo lalle baiwar Allah....
Tun safe take garari a titi wai gyaran gashi ynxu kuma daga ta fito wanka na xuba
mata abinci sai ki xo kice kin xo lalle baiwar Allah, ba fa ta ci komai ba" Mama
Hadiza dake parlon ta kalli mai lallin tace "D'an yi hakuri ta ci abinci yanxu ta
gama Aunty..." Mai lallin tace "Toh xan jirata a waje" daga haka ta fita, Inna ta
harari Mama Hadiza ta gefen ido ta dau abinci ta tafi daki kai ma Imaan tana cewa
"Abu dai munafurci munafurci ba a son fadin gaskiya, na ma mata maganar gaskiya kin
kwantar da murya kina mata magana salon ta min kallon fitinanna" Imaan ta gama saka
kaya kenan Inna ta shigo tace "Ki ci abincin ki a nutse kafin ki fito wani shegen
lalli, ba ruwana da gantalewa, ko lallaba maki lallen bana yi da kaina ba cikin
dare" daga haka Inna ta juya ta fita. Maryam na kallon Imaan dake tsakuran abincin
da Inna ta ajiye mata tace "Ki bani number Sadeeq in kirasa ai shi ya kamata ya
baki kudin lalle da kitso ba su Abba ba" Imaan ta kalleta, sai kuma tayi murmushi
tace "A'a just leave him... There is no need ai Abba riga ya bada" Maryam tace
"Like seriously tun xuwan mu kasar nan ban ga ya kiraki ba Imaan, there is
something wrong somewhere bai kamata kiyi shiru ba gashi jibi daurin aure ki cuci
kanki" Imaan ta tabe baki tace "Am not saying anything Maryam, kika san uxurinsa"
Maryam tayi shiru tana kallonta da mamaki, Imaan ta mike ta rufe abincin don gaba
daya ta kasa ci, tun last week tayi loosing appetite dinta gaba daya, a hankali
Maryam tace "Baki ci komai ba a abincin Imaan" Imaan tace "Mai lallen tana ta
jirana, anjima xan ci" daga haka ta fita dakin, Maryam ta bi ta da kallo, bayan few
minutes ta dau wayarta ta shiga duba number Sadeeq, tana gani tayi dialing, har ya
gama ring bai dauka ba, ta sake kira nan ma bai daga ba, kwashe lambar tayi a nata
wayar ta ajiye ta mike ta shiga gyara ma Inna daki, tana gamawa ta dawo ta xauna ta
dau nata wayar tayi dialing number din Sadeeq, ba a dau lkci yana ring ba ya daga,
shiru tayi da farko sai kuma tayi masa sallama, ya amsa, tace "Sadeeq?" Yace
"Yes..." tace "Why the sudden change of attitude toward ur financee Sadeeq?" Ya
d'an yi shiru kafin yace "Wait! Who is this?" Tace "You answer my question
first..." Yace "I don't think you are in the rightful place to..." A d'an fusace
tace "Kar ka gaya min magana malama, wato kai a silly thought dinka ka riga da ka
sameta xaka fara walakantata tun bata shiga gidanka ba ko?? to wllh karya kake
Imaan ta fi karfin haka, you are mistaken malam, domin ka kawo sadaki kuma jibi
daurin aure ba yana nufin har ta xama taka ba...." Ya katse ta shi ma yace "Toh ki
ce mata tayi xuciya ta gaya ma iyayenta ta fasa auren kawai, sai su maido min da
sadakina.... I think this will be better than you calling and saying nonsense on
phone to me madam" daga haka ya katse wayar, Maryam ta dinga kallon wayar da mugun
mamaki nan ko xuciyarta cike yake da tantamar anya Sadeeq din da ta sani ne wannan,
Anya Sadeeq din da ya siya mata latest phone da take mafarkin mallaka kwanaki da
suka xo Nigeria kawai don tayi masa addu'ar Allah ya bar sa da Imaan ne wannan,
mikewa tayi very shock ta fita dakin, a parlor ta tadda imaan mai lalli na mata
lallin, Inna ta matsar da kujerunta gaba daya ta lullube su, ta kwashe carpet dinta
kada a goga mata lalli a cuceta kamar yanda tace, Xaunawa Maryam tayi tana kallon
Imaan, lkci daya taji tausayinta ba kadan ba ya kamata, kawai mikewa tayi ta fice
daga parlon daga karshe.... Sai kusan Magrib Imaan ta wanke lallenta da yyi kyau ba
kadan ba ta tafi part din su dauko Hijab don Inna ta wanke mata gaba daya wanda ta
taho da, Shirye shiryen Mothers day da xa ayi gobe kawai ake yi a gidan, bata ga
kowa part din su ba ta wuce daki ta dauko hijab ta fito, Muryar Maryam taji tace
"Imaan" da sauri ta kalli direction da taji muryata ta ganta xaune ita kadai a
dinning, karasawa tayi tana kallonta tace "Me yasa kika ce baxa ki yi lallen ba?" A
takaice Maryam tace "Nothing" Imaan tace "Amma fa jiya kince xa ki yi" Maryam tace
"Fasawa nayi, xauna mu yi magana Imaan" Imaan ta ja kujera ta xauna tana kallonta,
Maryam ta d'an yi shiru sai kuma tayi kasa da murya tace "You know what imaan?"
Imaan ta girgixa mata kai gabanta na faduwa, Maryam tace "Plss ina son ku xauna da
Inna kiyi mata magana yanda xata fahimce ki, ki ce mata don Allah tayi ma su Abba
magana a daga bikin nan xuwa wani lkci" Kallonta kawai imaan ke yi, Maryam ta
girgixa kai tace "This is not the Sadeeq you know before imaan, ki rufa ma kanki
asiri ki yi ma Inna bayani ita kadai xata iya ma su Abba magana su daga bikin nan,
wllh idan kika auri wannan Sadeeq din you are going to live a miserable life in his
home, gaba daya gadara yake yana ganin ya gama samun ki, dama boye maki real him
yyi tun farko, kinsan yanda muka yi da shi a waya daxu da na kira in ji dalilin
Change of attitude dinsa?" Imaan da har hawaye ya kawo idonta ta girgixa mata kai a
hankali, Maryam tace "Ce min yyi ince maki idan kin isa ki fada ma su Abba kin fasa
auren a dawo masa da sadakinsa" Sosai gaban Imaan ya fadi ta dinga kallon Maryam
xuciyarta na bugawa, Maryam ta girgixa kai cikin sanyin murya tace "I am not in
support of you marrying Sadeeq any longer Imaan, ba shi da mutunci ko kadan,
hallaka ki kawai xai yi Imaan, kiyi hakuri ko min son da kike masa ki samu Inna ki
gaya mata abinda ke faruwa a san abun yi tun da sauran lkci..." Imaan ta fara kuka
a hankali, cikin sanyin murya tace "But I love him Maryam, shi ma yana sona, I just
don't know what came over him..." Sai kuma ta fashe da kuka sosai ta hade kanta da
dinning cikin rawar murya tace "May be stress yasa yake jin haushi haka, ni dai
nayi masa uxuri, this is not the Sadeeq I use know, nasan idan munyi aure xa mu
koma yanda muke da in sha Allah...." Da mugun mamaki Maryam ke kallonta tace "Are
you on ur right senses Imaan, Ina gaya maki ga abinda mutumi yace kice idan kunyi
aure xa ku dawo yanda ku ke da???" Imaan ta dago tana kallonta hawaye na sakkowa
idonta tace "Ina sonsa a haka Maryam, kawai ki taya ni da addua Allah ya maida sa
yanda yake da, beside
bayan duk bak'in da suka taho from different places sai ace an fasa aure, idan shi
bai fito ya fada masu ya fasa ba I see no reason why I should do so Maryam" Mikewa
Maryam tayi tana mata wani irin kallo tace "Baki da hankali wllh" Imaan ta tashi da
sauri tace "Plss this should be between us, ban ga dalili me karfi da xai sa ince
na fasa auren nan ba, don Allah forget you even called him, ai ni xan xauna da shi
ba ke ba, I know he loves me, nima kuma Ina sonsa, so plss mu bar maganan nan a
nan" daga haka Imaan ta bar dinning din Maryam ta bi ta da kallo baki bude. Daren
ranan Imaan bata yi bacci ba, gaba daya she is just disturbed nd restless, ta mike
xaune daga karshe ta kalli Inna dake sllh kamar dai yanda ta saba duk dare, kallon
agogo tayi taga biyu da minti biyar, wayarta ta dauka tana kallo, sai kuma ta shiga
text message, cikin minti goma ta gama rubuta ma Sadeeq text, da farko tambayarsa
tayi ko tayi masa wani laifi ne ya gaya mata, daga karshe kuma ta basa hakuri cikin
tausasan lafazi ta tura masa, tagumi tayi tana kallon wayar duk da bata expecting
reply don tasan bacci yake at that time, text taga ya shigo wayar nata gabanta ya
fadi sosai, ta dinga kallon wayar kafin ta dauka ta bude text din tana kallon
content dinsa, "if you think you notice any change of behavior da bai maki ba a
tattare da ni, ki yanke hukunci da kika ga is the best, wanda xai yi suiting din
ki" ta karanta text din ya fi a kirga amma ta kasa apprehending, can ta yi dialing
numbersa har ya gama ring bai dauka ba, ta kuma kira bai dauka ba, ta tura masa
text na cewar ya dau call dinta don Allah, ba a dau lkci ba reply ya shigo yace
"Good night" Ta dinga kallon reply din sannan ta ajiye wayar ta mike ta shige
bathroom ta rufe kofa, kuka ta fara yi a hankali tana jin xuciyarta na mata xafi,
tayi kukan da ta dade bata yi ba amma maimakon taji d'an sanyi a ranta sai k'una da
radadi, bubbuga kofa Inna tayi tace "Me kike yi a bandaki tun daxu Imaan, lafiyan
ki??" Imaan ta fara wanke fuskarta da sauri, Inna bata fasa bubbuga kofar ba hakan
yasa imaan ta bude kofar kanta a kasa, Inna ta gwalo ido tace "Kukan uban me kike?
Ni fa bana son a gigitani gaskiya, ni ba karamin aiki na bane ince ki bi dare ki
koma gidan ku, lafiya kike kuka a bandaki" Imaan bata tanka ta ba ta fara alwala,
Inna tace "Naga jaraba, don xa a maki aure kuma sai ki shige bandaki kiyi ta kuka
salon cuta ta kama ki" inna na tsaye tana kallonta har ta gama akwala ta fito ta sa
hijab dinta ta hau saman darduma, Inna ta tabe baki tace "Ni dai ba ruwana" daga
haka ta tafi ta xauna ta ci gaba da addu'o'in da take. Washegari tun sassafe Umma
ta bar gida ana girke girke, ko danginta daya babu a cikin mutanen da suka cika
gida, Ummi da Rahma ma duk ta sa sun shirya sun bar gidan, Aunty mamaki ta dinga yi
na irin xuciyar umma, tunda take bata taba ganin mata mai nuna bakin ciki kiri kiri
a fili irin Umma ba don cikin anko hudu da suka yi da Ammi ko daya ta ki yi, su
Ummi ma ta ki barin su dinka nasu da aka masu. Mama Hadiza ce xaune parlon Inna
tare da Aunty misalin tara na safiyar ranan Thursday din, Inna na kallonsu tace
"Toh dama so nake ku rufa min asiri ku tattara 'yarku ku maidata can bangaren ku,
tun daren jiya take kuka ga idanuwa can sun kumbure, toh ina dalili wani abun ya
sameta a bangarena, dama aure hauka ne, wannan mata mai gyaran jiki ba irin
lallashin da bata mata ba amma kamar ana tunxurata, to tunda uwarta ta sallama maku
ita shi sa na kira ku, ku tafi da ita can nayi kokari haka kuma Allah ya gani"
Aunty ta mike ta tafi dakin inna tana kallon Imaan dake kwance, murmushi tayi ta
xauna kusa da ita ta dagota tace "Haba daughter, kuka kuma haka?? Ko kina da damuwa
ne?" Imaan bata ce komai ba ta sunkuyar da kanta, Aunty tace "Kiyi hakuri kar ki
sake kuka kinji, it's always like this for every lady Imaan" Imaan ta fara wani
sabon hawayen, Aunty ta rungume ta tana lallashinta, Mama Hadiza ta shigo dakin ita
ma ta dinga kwantar mata da hankali, sai da suka tabbatar tayi shiru gaba daya
sannan suka fita dakin, Aunty ta hado mata shayi mai kauri ta kai mata.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

74.....

Bayan azahar mai make up da aka yi hiring ta xo tayi ma Imaan very light make up da
ya fito da ainahin kyanta na 'yar fillo, ta saka wani lace mai tsadan gaske da
Daddy yyi mata da head din da xata saka, ko tsinke ba a taba ba a lefenta dama,
gaba daya kayan da xata yi fitan biki Daddy ne yyi mata su, tayi kyau har ta gaji
barin ita da dama bata make up, kowa sai kallonta yake cike da sha'awa, Aunties din
Sadeeq da Step mum dinsa duk sun xo gun mother's day din, Mariya da frnds dinsu na
islamiyya da boko duk sun xo suma, da Ammi da Aunty ankon lace suka yi, ko kai ka
gansu sai sun burge ka, karfe uku da wani abu Umma ta dawo gidan ita ma ta shirya
cikin tsadadden lace ta shigo cikin jama'ah ana ta gaisawa, sosai hakan ya ba Aunty
mamaki sai dai bata ce komai ba, bayan kusan awa daya sai ga Safeenah ta xo gidan
cikin shiga ta alfarma da sisters dinta biyu, can kuma sai ga wasu daga kawayen
Umma, gida ya cika da frnds din Aunty da Ammi masu ji da kansu cikin ankonsu na
mothers day da Aunty ta fitar, irin rawan da Safeenah tayi sai abun ya baka mamaki,
don xagewa tayi ba kadan ba kamar dai bikin masoyiyarta, sosai hakan ya ba Imaan
mamaki, ita dai tana xaune ana ta abubuwa a wajen, duk Ammi na lura da imaan
throughout the program bata da walwala kana gani kasan tana da damuwa, biyar da
wani abu Ammi ta samu ta kebe da ita a backyard din apartment dinsu tana kallonta
tace "Imaan ba nace ki kwantar da hankalin ki ba, or do you have any problem da
baki son fada min ne" Imaan ta girgixa mata kai cikin sanyin murya tace "Ba komai
Ammi...." Sai kuma ta sunkuyar da kanta hawaye ya fara taruwa idonta, Ammi tayi
tunanin kila duk fargaban da ko wace amarya ke yi da xulumin barin gida ne ke damun
yar tata, hakan yasa ta jawota kusa da ita ta shiga kwantar mata da hankali cikin
taushin murya, Imaan dai sai gyada mata kai take hawaye na sakko mata, Ammi ta
rungumeta tace "Bana son wannan kukan Imaan, today is ur happy day, ki saki ranki
pls" a hankali imaan tace "Na daina" Ammi tace "Good ki shiga ciki ki xauna, karfe
nawa yace xa ku tafi dinner din?" ta girgixa kai tace "Ban dai sani ba kila bayan
Magrib" Ammi ta bude mata kofar kitchen tace "Go in and get some rest before then,
or are you feeling pain anywhere?" Imaan ta girgixa kai tace "A'a" Ammi tace "Toh
shiga ciki ki xauna" shiga kitchen din tayi sai kuma ta juyo a hankali tace "Ammi
Daddy na fa?" Ammi tace "Ya dawo two days ago ai, don kina part din Inna ne" Imaan
tace "Toh" daga haka ta wuce dakinta, wayarta da ta sa a jaka ta fiddo tana dubawa
taga text na Sadeeq, sosai gabanta ya fadi ta bude message din tana kallon content
dinsa, "I am sorry to let u know that... tonight dinner isn't going to hold anymore
due to some reasons, ki sanar ma mutanen gida, thanks" ta karanta message din ya fi
sau biyar sannan ta ajiye wayar a sanyaye, lkci daya ta ji wani hawaye me xafi na
xubo mata, xaunawa tayi gefen gado ta cire head tie dake kanta, Maimoon ta kira a
waya daga karshe ta sanar mata babu dinner din ta gaya ma su Ammi don a sanar ma
mutane da xa su tsaya sbda dinnern, Maimoon tace "What?? Sbda me??" A hankali Imaan
tace "Ke dai ki gaya masu kawai ni ina daki yanxu" daga haka ta katse kiran, Aunty
ce ta shigo dakin tana kallonta tace "Imaan shi Sadeeq din yace maki babu dinner
kuma?" Imaan ta kalleta trying her best to look alright tace "Ehh daxu yyi min text
Aunty, he said he is sorry for the inconvenience" Aunty tayi shiru tana kallonta
can tace "Toh shkkn Allah ya so babu wanda ya tafi can din ma" daga haka ta fita
dakin, kowa a gidan yayi mamakin me yasa aka ce an yi canceling dina, ciki har da
Umma dake tsakar gida tace "Ahhh gaskiya mu dai ba a kyauta mana ba, mu da muka sa
ran mu yi yanda muka ga dama yau abu namu maganin akwabe mu, ni fa har na hango an
dire ma kowa full chicken a table da lemon masu kudi, gaskiya an shiga alhakin
mutane da yawa..." Safeenah tace "Ikon Allah, to bari mu san inda dare ya mana dama
dinner din nake xaman jira a tafi, ni ban ma taba jin inda aka fasa dinner ba sai a
bikin gidan nan" Ammi dai ko kallonsu bata yi ba tana sallaman wasu frnds dinta da
gifts da aka raba na mothers day, Mama Hadiza tace "Toh ai gwara hakan, Allah na
tuba meye abun birgewa a dinner, albarka ake so a aure dama ba tsiya ba, dinner sai
kace fadan Allah, ai ni wllh ya burgeni da yace bbu dinner kowa sai ya ci kajin a
gidansa...." Umma dai bata kalli inda take ba ta shiga sallaman neighbors dinsu da
xa su tafi, Mama Hadiza ce ta tafi sanar ma Inna babu Dinner don suna can ana shiri
da ta Rasulu da taxo da yamma, Inna ta gwalo ido tana kallon Mama Hadiza tace
"Subhanallahi shi Bulasawan wiwi ya sha da xai ce an fasa shagalin?" Mama Hadiza
dai bata ce mata komai ba ta fita, Inna ta kalli Ta Rasulu da har ta fiddo kayan da
xata saka da mayafi tace "Yau naga gantalallen mutumi ta Rasulu, wai ki ji ba casu"
Bayan isha Imaan na xaune can karshen gado tana ta bin frnds dinsu da Mariya dake
ta hira a dakin da kallo, ko kadan bata san abinda suke cewa ba don gaba daya she
is absentminded, Maryam dai na xaune one side tana danna wayarta amma gaba daya
mood dinta wasn't good, Maimoon ce ta shigo dakin ta nufo Imaan ta mika mata wayar
hannunta, Imaan ta amsa a hankali tace "Waye?" Maimoon tace "Ya M.A" Imaan ta kai
wayar kunne tayi sallama, cikin sanyin murya Mujaheed ya amsa mata daga daya
bangaren, tace "Ina yini Yaya?" yace "Lafiya, can you pls come out now?" Tace "Kana
Ina?" Ya d'an yi shiru sai kuma yace "Ki sameni bayan apartment dinmu" tace "Toh"
daga haka ya katse wayar, ta mika ma Maimoon wayarta ta sauka daga kan gadon ta dau
hijab dinta har kasa ta saka, Maryam na kallonta tace "Where are you going to?"
Imaan tace "Yaya ke kirana" daga haka ta fita bayan tace ma su Mariya tana xuwa, ta
kitchen dinsu ta fita, ta dinga tafiya kamar mai tausayin kasa har ta kai
Bangarensu Maimoon, tsaye ta gansa yana facing bango har ta iso kusa da shi bai
juyo ba, a hankali tace "Ga ni Yaya" juyowa yyi yana kallonta, lkci daya ya sauke
idonsa, ya fi minti biyu bai iya yace komai ba, sai kuma cikin sanyin murya yace
"Sure I was suppose to ask you what u want for ur wedding but I didn't Imaan, but I
don't know if you will appreciate this little that I have for you..." Imaan dai sai
kallonsa take, wani round box mai kyau dake hannunsa ya bude yana kallonta ya fiddo
bracelet sai kyalli yake kana gani kasan na menene ya kamo hannunta a hankali ya
saka mata a wrist cikin sanyin murya yace "Am hoping you will love it lil sis" lkci
daya hawaye ya kawo idonta ta fada jikinsa tana shessheka tace "Nagode Yayana"
rungumeta yyi cikin breaking voice yace "I am... wishing u all d very best in ur
marriage lil sis, Allah ya ba ku xaman lfya, but.. but i want to let you know this
Imaan....." Sai kuma ya kasa ci gaba ya runtse ido, saketa yyi ya janyeta jikinsa
ya juya xai bar wajen tace "You want to let me know what Yaya?" Bai juyo ba sbda
bai son taga hawayen idonsa yace "I want to let you know that, kiyi ma mijin ki
biyayya, be the best wife you can..." Daga haka ya wuce ta bi sa da kallo tana goge
hawayen idonta tace "Toh nagode Yaya" a hankali ta juya ta koma apartment dinsu
hawayen da take ta gogewa ya ki tsaya mata. Kamar Daren jiya wannan Daren ma Imaan
bata yi baccin kirki ba, sai kallonsu Mariya da Maimoon da Maryam dake ta baccinsu
take, daga karshe ta tashi ta dauro alwala ta dinga sllh har sai da taji bacci ya
xo mata, nan kan darduman ta kwanta nn da nan kuma bacci yyi awon gaba da ita. Da
asuba Ammi ta shigo ganinta kwance kasa ta tada ta tana kallonta tace "A kasa kuma
Imaan maimakon ki tafi dakina?" Imaan ta mike xaune tana murxa ido tace "Sllh nayi
ne daxu" Ammi tayi shiru tana kallonta, can tace "Toh ku tashi ku yi sllh lkci yyi"
daga haka ta fita dakin, Da safe gida ya xamo ba masaka tsinke duk inda ka bi
jama'ah ne, tun asuban fari dama ake ta girki a gidan don Aunty tace da kansu xa su
yi abinci ba sai an wani kira masu yi ba, Umma ma dai na cikinsu, da ita aka dinga
yin komai tun asuban, Ba karamin tilasta Imaan Ammi tayi ba ta sha shayin da ta
hado mata sannan mai make up tayi mata make up kamar jira, yau ma dai wani ubansun
lace din ta saka da ya fi na jiya, Maryam kam cewa tayi kanta na ciwo don ma kada
a tilasta ta saka kaya, da ta tuna yanda suka yi da Sadeeq jiya sai ranta yyi mugun
baci, in kuma ta tuna abinda Imaan ta gaya mata wai ba ruwanta sai tayi wani
murmushi tana tausayin Yar uwar tata, Maimoon da Mariya suka cakare cikin ankonsu
na ranan aka dinga hotuna. Karfe sha daya Yusuf ya fito dakinsa xuwa parlon Abba ta
dalilin kiransa da yyi a waya, gaisawa yyi da mutanen dake parlon nasu don tun safe
yake daki da few frnds dinsa, da sallama ya shiga parlon Abbansa yana kallonsa ya
xauna yace "Gani Abba...." Abba xai yi magana Daddy ya shigo parlon da sallama,
Yusuf ya gaishesa, Daddy ya amsa gaisuwarsa sannan ya xauna yana kallon Abba yace
"Ina hanya ka kirani Barrister..." Abba ya kalli Yusuf yace "Kaje waje ku shigo
tare da Sadeeq, ya kira yana waje...." Yusuf yace "Sadeeq Bulasawa?" Abba yace
"Ehh" mikewa Yusuf yyi ya fita, Daddy ya kalli agogo sannan ya kalli Abba yace "Why
is he here?"

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

75.....

Tare Yusuf suka shigo parlon Abba da Sadeeq, Sadeeq yyi kasa da kai ya cire glasses
din idonsa ya xauna saman rug ya gaishesu cikin sanyin murya, amsawa suka yi a tare
suna kallonsa, Yusuf ya xauna shi ma yana duban Sadeeq da ya ki dago kai, calmly
Abba yace "Hope all is well Abubakar?" Sadeeq bai ce komai ba kuma bai dago kansa
ba, daga daddy har Abba kallonsa kawai suke, Yusuf ma haka, Can Sadeeq ya dago
kansa ba tare da ya yarda sun hada ido da ko daya daga cikinsu ba a hankali yace "I
am sorry I am saying this late, ina son don Allah ku min alfarma ayi hakuri da
daurin auren nan yau saboda wasu dalilai...." Kallon mamaki Abba da Daddy suka
shiga yi masa, Yusuf da ya xaro ido shi ma ya dinga kallonsa, Sadeeq ya shafa kansa
murya can kasa yace "I think I am not ready for marriage now, I am sorry I am
saying this at the die minute, but this is just d fact, ku yi hakuri...." Yusuf na
masa wani kallo ya mike a mugun fusace yace "How dare you say such at this time,
who do you think you can take for granted here...." Abba da gaba daya Sadeeq ya
gama kulle masa kai cikin cool voice yace "What exactly are you trying to tell us
here now Sadeeq.... What do you mean?" shiru Sadeeq yyi bai ce komai ba, can ya
kallesu yace "I think it's good a fasa auren nan sai wani lkcn, ku min afuwa...."
mikewa Daddy yyi cikin tsawa yace "You are very stupid...." Abba ya mike da sauri
ya nufi d'an uwan nasa sanin xuciyarsa yana kallonsa a nutse yace "keep calm
Abubakar, keep calm..." Mikewa Sadeeq yyi kansa a kasa yace "I am sorry..." Daga
haka ya nufi kofa ya fita daga parlon, Yusuf ya bi sa da kallo da mugun mamaki,
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" shi ne kalmar da Abba ya dinga furtawa ya kasa
tsaye waje daya, daddy ya koma ya xauna a hankali trying his best to be calm, Abba
ma ya koma ya xauna har lkcn yana nanata Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, silent
din kusan minti biyar ne ya biyo baya a parlon, kowa da tunanin da yake a ransa,
can Abba ya daga kai ya kalli daddy, lkci daya wani tausayin d'an uwan nasa ya rufe
sa, how will such thing happen to his only child, cikin sanyi Abba yace "Look
Abubakar you need not to worry, haka Allah ya tsara kuma Alhmdllh, I am sending
them their pride price immediately, sannan plss do not say anything to anybody
about this yet...." Daddy dai bai ce komai ba ya jinginar da kansa da kujera ya
lumshe idonsa, Yusuf duk jikinsa yyi sanyi ya ma kasa kallon iyayen nasa ya rike
kansa kawai, Abba ya mike walking round as if looking for a solution, sosai xaka ga
damuwar dake tattare a fuskarsa, Daddy ya mike daga karshe calmly yace "Bani
sadakinsu in mayar masu yanxu Barrister" sanin halin daddy yasa Abba yace "Xan
maida da kaina Abubakar, ba sai ka je ba" duk ynda daddy yyi Abba ya basa sadakin
kin basa yyi hakan yasa ya koma ya xauna xuciyarsa na tafarfasa, he just can't
believe this is happening to his daughter, can Abba xauna ya dau wayarsa ya shiga
kiran layin Alhaji Ahmad Bulasawa, sai da ya kusa katsewa ya daga, bayan sun gaisa
Abba ya d'an yi shiru sai kuma a nutse ya shiga tambayar Bulasawa dalilin da yasa
xa su yi masu abinda suka yi, Alhaji Ahmad Bulasawa dake sauraronsa keenly yace "I
really don't get you Alhaji, me ke faruwa, anyi wani abu ne??" Mamaki ne ya cika
Abba jin abinda Bulasawa ke cewa, bbu bata lkci ya shiga yi masa bayanin ynda suka
yi da Sadeeq yanxun nan, cikin daga murya Bulasawa yace "He is seriously stupid,
wato abinda ya xo yace maku kenan, to wllh ko ya ki ko ya so aure ba fashi, my
reputation is above everything, ana saukowa masallaci dama daurin aure na nan bbu
fashi in sha Allah, till we meet there...." Bai jira cewar Abba ba ya katse wayar,
Abba ya kalli Daddy don wayar a hands free ya sa, Daddy ya girgixa kai yana
murmushin karfin hali yace "I will never give out my daughters hand in marriage to
that son of him, tunda har da kansa ya nuna baya auren that's the end, ba neman kai
nake da Imaan ba, don't forget she is all I have got, da a cutar min ita gwara an
cuceni ko wani irin cuta ne kuwa, we are returning their pride price and everything
immediately, Allah ya hada kowa da rabonsa na alkhairi, Allah yayi mata xabi na
gari, bak'i da suka xo from far don taya ni farin ciki xan sallamesu ana saukowa
masallaci in sanar masu bbu auren kuma, and I will forever be grateful coz they are
all here bcos of my only child, in sha Allah xa mu je a daura auren Yusuf nata kuma
Allah ya musanya mata da mafi alkhairi" daga haka daddy ya mike ya nufi kofa, Abba
da duk jikinsa yyi sanyi sosai yace "Sadeeq" tsayawa daddy yyi amma bai juyo ba,
Abba yace "Don't say anything about this to anybody, not even ur frnds, ka ji
abinda nace" Daddy dai bai ce komai ba ya fita parlon kawai, Abba ya jinginar da
kai so sad, Yusuf dai ya rasa abun cewa gaba daya he is just shocked, can Abba ya
kallesa yace "Go nd get set Yusuf, it's almost time, and don't say anything to
anybody yet" mikewa Yusuf yyi jiki ba kwari ya fita parlon Abba ya bi sa da kallo.
Gida ana ta shagalullukan biki bbu abinda yasan me ke faruwa, Imaan dai tana
bedroom dinta baccin da bata yi jiya ba duk ya dameta, daga karshe ta kwanta ta
dinga bacci, bbu wanda ya tasheta cikin mutanen dake dakin don da ganin yanda take
baccin ma kasan gaba daya she is restless sai juye juye take. Abba ya dau sadakin
da su Bulasawa suka kawo ya tafi gidan da kansa don mayar masu don sosai ya gamsu
da abinda d'an uwansa yace na cewar bbu xancen aure kuma tunda Sadeeq din ya fito
da kansa ya nuna ya hakura to gwara kowa ma ya hakura ko don gudun kada ya jefa
Imaan cikin wani hali, kuma hakan shine abu na karshe da xai so ma only child din
d'an uwansa, ko kadan Bulasawa bai ji dadin kudin da Abba ya maido ba don kin karba
yyi, Abba yayi masa bayani a nutse yanda xai fahimce me yasa suka yi haka ya kuma
nuna masa dole su yi hakan don ceto imaan, ba irin kiran da Bulasawa bai ma Sadeeq
a waya ba amma ya ki dagawa, Abba na murmushi yace "Toh kaga Alhaji, kawai Allah
yyi masu xabi na gari, tunda kaga haka auren ba alkhairi bane garesu" Bulasawa dai
ya kasa cewa komai amma gaba daya shi ma ransa ya sosu, Abba yyi masa sallama daga
karshe ya bar parlon nasa bayan ya sanar masa xuwa gobe ko jibi xa a maido masu
lefe, shi dai Bulasawa har Abba ya fita bai iya yace komai ba, can ya dau wayarsa
ya shiga Kiran mahaifiyar Sadeeq, tana dagawa strictly yace "ki sameni parlona
ynxu, kuma duk inda Abba yake I want him immediately, in sha Allahu kuma baxai
kwanan min a gida ba yau, and he is returning all my asset that is with him today,
I have nothing to do with him any longer" Bai jira cewarta ba ya katse wayarsa.
Karfe daya saura Abba suka wuce masallaci tare da frnds dinsa da kawu Bala, sae
kawu Audu, bayan ya samu waje yyi parking ya kira Daddy don ya ji yana iya, daddy
ya sanar masa yana hanyar xuwa mosque..... Ana sakkowa masallaci aka daura auren
Yusuf da Hafsat a kan sadaki dubu dari biyu, auren da jama'ah da dama suka shaida,
sae kuma daurin aure na biyu da ake jiran waliyyan ango amma shiruu, wanda hakan
yasa aka fara dago kila babu auren ne tun kafin su Abba su sanar da hakan, Abba na
kallon daddy dake kusa da shi murya can kasa yace "Abubakar xan daura ma 'ya ta
aure yanxu, auren da ina da tabbacin kowa xai yi alfahari da shi in sha Allah, ko
ba ynxu ba kuwa, da raina baxan ta6a yarda ka ji kunya a idon duniya ba, kuma ikon
da nake da shi a kan Imaan yasa xan daura mata auren huce takaici duk da banda ni
da kai da Yusuf sai Bala bbu wanda yasan abinda ake ciki" Daddy dai sai kallonsa
yake don tun idar da sllh ya ki cewa komai, Abba yace "Ka je a kai ne waliyyin
ango, Bala kuma dama shine waliyyin amarya..." Yana fadin haka ya fiddo kudi a
aljihunsa ya mika ma Daddy yace "This is 200k, sadakin da xaka bada...." Abba na
fadin haka ya koma gun su kawu Bala da abokansa, ko kadan daddy bai yi welcoming
idea din Abba ba, kwata kwata bai son ma imaan dole, bai son tashin hankalinta ya
xama biyu, na rashin masoyi ga kuma aure without her consent, gashi bai san da wa
Abba xai hadata ba idan kuma yace xai yi magana Abba sai yaga kamar ya nuna masa
bashi da iko da imaan, gaba daya he was just confuse haka ya tafi dai don yin ynda
Abba yace, Daddy bai taba xaton sunan da yaji an kira na angon ana daura auren,
haka ya dinga kallon Abba ko kiftawa bbu, Yusuf kansa was more than shock ya kasa
daina kallon iyayen nasa, can ya lumshe ido ya bude xuciyarsa na bugawa.... Abba ya
sakar ma Daddy cool smile ganin kallon da yake masa, maimakon Daddy ya mayar masa
sai ya dauke kai kawai. daga karshe dai Yusuf fita yyi to avoid gaisawa da frnds
don gaba daya shock ya xame masa biyu..... Tun bayan call da Mariya tayi answering
a dakin Imaan yanayinta ya sauya gaba daya, tafi minti biyu tsaye har sannan wayar
na hannunta, Maimoon dake diban ma Imaan dake xaune saman darduma ta idar da sllh
abinci a plate ta kalleta ganin ko motsin kirki bata yi tace "Lafiya Mariya" Mariya
bata yarda ta kalli Maimoon ba sbda hawayen da ya kawo idonta, Maryam ta ajiye
dankunnen da take kokarin sakawa ita ma tana kallon Mariya tace "Hope all is well
dear?" Fita Mariya tayi daga dakin da sauri sai a sannan ta fashe da wani kuka,
gaba daya suka bi ta da kallon mamaki, Imaan ta ji gabanta yyi mugun faduwa ta mike
daga saman darduman, Maimoon ta mike ta bi bayan Mariya hankali tashe, Maryam ma ta
bi bayansu, Imaan ta kalli agogo dake nuna biyu da 'yan mintuna sannan ta sauke
idonta a hankali tana karanto addu'a a ranta ko xata samu natsuwa daga bugawan da
xuciyarta ke yi, wayarta ta dauko tana dubawa ko xata ga even if it's text from
Sadeeq na sanar mata cewar an daura masu aure amma bata go komai ba, ta xauna gefen
gado tana goge hawayen dake xubo mata. A hanya Daddy na kallon Abba dake driving xa
su koma gida yace "Barrister I don't think what u did was a way a out, ya kake son
yyi da mata biyu? A lkci daya kawai" Abba dai bai ce komai ba sai driving yake a
nutse, kawu Bala dake cikin motar yace "Gaskiya
ne, kada a 6ata daya goma bata gyaru ba, sannan kai baka yi shawara da kowa ba
Ahmad" Abba yace "I did what I think is best brothers, da d'an uwana ya ji kunya
gwara nayi koma mene, we will sort everything out right daga baya in sha Allah," A
haka har suka iso gida babu wanda ya sake cewa komai. Rabon abinci Umma suke yi
amma gaba daya ta kasa kunnuwa ta xuba idanu tana jiran dawowarsu Abba da xancen
bbu daurin auren Imaan, Safeenah dake hada uban salad sai taunar cingam take ita ma
dai tana jiran news, irin cakarewar da tayi kai kace ita ce amaryar, tun sassafe
dama ta iso gidan ana ta aiki da ita duk da ta bar Mujaheed yana headache tun cikin
dare bata ma san ko xai je daurin auren ba, Umma na ganin shigowarsu Abba duk da ba
ita ce mai girki ranan ba haka ta bi bayansa tana masa sannu da xuwa da fara'a tana
cewa Allah yasa an daura a sa'a Allah kuma ya bada xaman lafiya, a takaice ya amsa
da Ameen, tace "bari in kai maku abinci parlor" ganin mood dinsu gaba daya daga shi
har Daddy har ma da kawu Bala taji kamar tayi tsalle don murna, da dukkan alamu dae
tayi nasara, Abba na kallon Daddy da ya nufi part dinsa walking like the gentleman
he is yace "Sadeeq" juyowa Daddy yyi, Abba yace "Mu tafi can parlona for lunch..."
Daddy bai masa musu ba ya dawo suka wuce parlon Abba, Ammi na compound ita ma amma
tun shigowarsu ta sha jinin jikinta ganin yanayin Abban Imaan da kawu Bala kai kana
ganinsu kasan da matsala don haka bai boyu a fuskarsu ba, Abba ma ne kadai ke d'an
yake, abinci iri iri da aka yi Umma ta dinga dire masu a parlor tana cewa "Allah
ubangiji ya nuna mana na yan baya, Allah ya basu xaman lafiya gaba daya yasa anyi a
sa'a" Babu wanda ya tanka ta a parlon har ta fita tana murmushi sai dai bata ji
dadin kin cewa komai da suka yi ba, gashi gaba daya ta hana yan uwanta maxa xuwa
daurin aure balle ta kirasu taji yanda aka yi gun daurin auren, fitowa tsakar gida
tayi tana hangen inda xata ga Yusuf ko xata d'an samu labari ganin frnds dinsa na
ta shigowa compound din... Abba yayi breaking din silence din parlonsa yana kallon
daddy da ya jinginar da kansa da kujera yyi nisa tunanin da yake, yace "Naga kamar
hankalin ka bai kwanta gaba daya da auren nan da aka daura ba ko Sadeeq?" Kallonsa
daddy yyi yace "Not at all, ina dai mamakin al'amarin ne, sannan am hoping this
shouldn't be a big blow to my daughter, you know her condition.... Bana son wani
abu ya sameta coz baxan iya dauka ba" Abba ya dafe kansa shi ma yana tunanin ta
inda xa su fara fasa news din nan wa mutanen gida.... Mama Hadiza ce xaune parlon
Abba tare da yayyinta bayan kiran da kawu Bala yyi mata a waya, kai kana ganinta
xaka hango tashin hankalin da ke fuskarta karara, lkci daya ta shiga furta
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Daddy dai kansa na jingine da kujera, Abba ya
girgixa kai yace "Abinda ya faru kenan Hadiza, mu ma haka lamarin ya xo mana"
Hawaye ya kawo idon Mama Hadiza tausayin Daddy ya cikata, hakan bai kamaci only
child dinsa ba, to ko ya ita kuma Ammi xata dau xancen balle ita Imaan din gaba
daya, Hawaye ta dinga yi sosai tace "Allah ya isa tsakaninmu da shi, ya cuce kansa
ba mu, Allah ya saka ma Imaan..." Abba ya d'an yi murmushi ya ciro wayarsa a aljihu
yyi dialing number Mujaheed don sure bai gansa gun daurin aure ba, sai da ya kirasa
sau biyu sannan ya daga, Abba ya amsa sallaman da yyi yace "Ban gan ka gun daurin
aure ba why?" Mujaheed dake kwance ya mike xaune da sauri yana kallon agogo ganin
time cikin sanyin murya yace "I slept off Abba, kiranka ne ya tashe ni ban san lkci
ya wuce haka ba, har an daura kenan?" A takaice Abba yace "A'a ana jiran ka, I want
to see you home now my frnd..." Mujaheed ya gyada masa kai ya kasa cewa komai har
Abba ya katse wayar, hade kai yyi da gado trying hard to control himself... Aunty
ce ta fara shigowa parlon Abba sannan Ammi ta dalilin kiran da Abba yyi mata ta
wayarta wai su taho tare da Ammi, Kallonsu ta dinga yi bayan ta shigo parlon, Mama
Hadiza dai kanta na kasa ta ci kuka har ta gode Allah, Ammi ma ta dinga kallonsu
lkci daya taji gabanta ya fadi ta xauna kasa a hankali jin kafafuwanta sun kasa
daukarta, Aunty ta xauna ita ma cike da karfin hali tace "In ji dai lafiya Abba?" A
takaice Abba yace "Lafiya lau" Kawu Bala yace "Lafiyar kenan Amina..." Bude kofa
aka yi Umma ta shigo ita ma ta dalilin kiranta da Abba yyi, ganinsu Ammi da Aunty,
da Mama Hadiza a parlor kawai taji kamar ta saki guda mai xakiii, rumors da ake
tayi tsakar gida ya tabbata kenan, Ta xauna da mamaki fuskarta tace "Lafiya kuwa
Alhaji, me ya faru?" Ko rufe baki bata yi ba Yusuf ya shigo parlon tare da Inna da
ta cakare cikin super abunta an daura dankwali sai xuba kamshi take ta daura mayafi
a kan dankwalin, tana murmushi baki har kunne tace "Toh Allah ubangiji dai yasa an
daura a sa'a Allah ya kauda idon makiya, ya kuma sa gidan xamanta ne, ku kuma Allah
maku albarka ya baku lada" Kawu Bala ne ya amsa da Ameen kansa a kasa, shi dai
daddy kansa na jingine da kujera, inna ta nemi kujera ta xauna tace "Toh wani
shawarar kuma xa ayi yanxu aka tara mu a nan, ga dai bak'i can na baro" Abba yayi
murmushin karfin hali yace "Mujaheed muke jira Inna" Inna tace "Ae dole, shi ne
ubanta na hudu a nan ai...." Bude kofa aka yi sai ga Mujaheed ya shigo parlon sanye
da shadda fari kal sai walkiya yake, duk suka dinga kallonsa ya nemi gefen Yusuf da
kansa ke kasa ya xauna ya gaishe da iyayen nasa gaba daya da ladabi duk suka amsa,
Abba ya kalli Aunty a hankali yace "Go and get Imaan immediately" Mikewa Aunty tayi
ta fita ita gaba daya ta gama shan jinin jikinta don gani take ba alkhairi yasa aka
tara su parlor ba, ba alkhairi xa su ji ba. Aunty na rike da hannun Imaan da ke
lullube cikin mayafi suka shigo parlon Abba, ta xaunar da ita gefenta, imaan bata
iya ta dago ba balle ta ga mutanen dake cikin parlon gabanta dai sae faduwa yake,
Umma dai har ta fara lissafin nawa xata kai ma mutumin nan kyauta don nuna masa
farin cikinta, gaba daya ta kasa boye how happy she is ah wajen duk da ynda ta
dinga dakewa, tunda Imaan suka shigo da Aunty Mujaheed ke kallonta ko kiftawa babu,
Abba ya bude wajen da addu'a sannan a hankali yace "Bbu amfanin tsaya jan xance ko
wani boye boye, kuma ina son kowa a nan ya dau abinda ya faru yau a matsayin
kaddara wanda aka ce ta riga fata, mu ma ba haka muka so ba, kowa ma ba haka xai so
ba, sai dai kawai mu kara gode ma Allah don shi ya san dai dai, a takaice dai bbu
xancen auren Fatima da yaron nan Sadeeq yanxu..." Ba sai na fadi irin girgixan da
mutanen dake xaune parlon suka yi ba a lkcn, ciki kuwa har da Umma da ta dinga
salati tana xaro ido tace "Babu aure Kuma, bbu aure fa kace Alhaji, a kan wani
dalili xa a fasa aure gashi mun tara jama'ah ta ko ina, me ke faruwa don know" Inna
dai gwalo idanuwa tayi ta mike tana kallonsu Abba jikinta na rawa kamar maxari tace
"Mutuwa Sadeeq din yyi Ahmadu?" Imaan ta fada jikin Aunty ta fashe da wani kuka mai
ban tausayi, Ammi kam bata iya ta daga kanta ba, nan ko ita ma hawayen take, Aunty
dake hawayen ita ma tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, me ke faruwa Alhaji"
Yusuf bai iya ya kalli mutanen parlon ba duk jikinsa yyi sanyi ba kadan ba,
Mujaheed ya dinga kallon Abba ko kiftawa bbu xuciyarsa na bugawa jin abinda yace,
kawu Bala yyi kasa da murya yace "Duk ku yi hakuri, we never saw this coming, and
we are in it all together, komai ya samu bawa a duniya dama rubutattce ne, kuma bbu
wanda ya isa ya kauce ma kaddararsa, wannan yaro Sadeeq dai da kansa ya xo daxu ya
nuna ya fasa auren yar mu, tuni kuma mun maida masu sadakin su lefe kuma ko xuwa
anjima in sha Allah xa a mayar, Allah yasa hakan ne mafi alkhairi ga dukkanmu gaba
daya...." Inna ta rushe da wani kuka da tsorata mutanen parlon tace "To kuwa yanxun
nan xan tafi in nemo gidan Bulasawa in ci ubansa da d'an nasa, Allah ya tsine masu
albarka, Allah ya tarwatsa su, Allah ya isa tsakanina da su, Allah yyi yaga_yaga da
dukiyar nan tasu ta sata, shegu barayi, mu xa su kunyata a idon duniya ga bak'i mun
tara ta ko ins, to in sha Allahu kotu ce xata raba mu da matsiyatan, Shari'a ce mai
girma xa mu yi tun a duniya kafin mu tafi gaban Ubangijin mu, yau xan tafi in
shigar da kara a kotun Habuja...." Abba yace "Don Allah ki sauraremu Inna, dama an
taba aure dole?? bbu ruwan ki da su balle aje wani shari'a kawai mu sa a ranmu fasa
auren nan shine mafi alkhairi ga 'yar mu, kuma basu kunyata mu ba don bamu bar
masallaci ba sai da na tabbatar na fitar da d'an uwana kunya na daura ma 'yar sa
aure da nawa d'an da nake da iko da...." lkci daya gaba daya mutanen parlon suka
daga kai suna kallon Abba with full shock, ko allura ya fadi a lkcn sai kaji
karansa, Imaan taji kamar numfashinta na mata gardama ta dinga kallon Abba
xuciyarta na wani bugawan da bai ta6a mata ba, Umma ta hadiye abu da kyar tana
kallon Yusuf da kansa dai ke kasa, ji tayi wani xufa na keto mata don wannan shine
anyi ba ayi ba, yanxu Yusuf aka makala ma yarinyar nan, Mujaheed dai sai kallon
Abba yake xuciyarsa kamar xai fashe sabida yanda yake harbawa, Abba ya mike yana
kallon Inna da ta cire mayafin kanta tana kikkifta ido tana kallonsa, yyi kasa da
murya yace "Na hada auren Imaan da Mujaheed yau, saboda ina da yakinin xai ma fi
Sadeeq din rike min 'ya ta da amana...."

*Table_shaker/Media shaker* ✍🏻

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

76.....

Kusan a tare Ammi da Umma suka mike tsaye a parlon suna kallon Abba da wani irin
shock, can Ammi ta kalli Daddy xuciyarta na bugawa lkci daya hawaye suka dinga
sakko mata tana girgixa kai, Tuni Umma ta isa gaban Abba cikin kidimewa bakinta na
rawa haka ma ko ina na jikinta tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, la ilaha
ilallahu Muhammadur rasulillahi sallallahu alaihi wassalam, ban fahimce ka ba
Alhaji? Ban gane ba wllh tllh, Wani Mujaheed din ka hada da Imaan??? Wani Mujaheed
din kake nufi, wai d'a na kake nufi?? Ka min bayani don girman Allah Alhaji, wani
Mujaheed ne wannan??" Aunty ta kasa rufe bakin da ta bude tana kallon Abba a mugun
sanyaye ko motsi ta gagara yi daga xaunen da take, Mama Hadiza tayi tagumi tana
kallon Inna da bakinta ke hangame tana kallon Abba a tsorace da alama magana dai ya
makale mata gaba daya, sai a sannan Imaan ta gama fahimtar abinda Abba ya fada few
seconds ago, don tun bayan maganarsa taji komai na kanta ya kwance ta kasa
apprehending, da kyar ta gano me yake nufi bayan maganganun Umma, ja baya ta dinga
yi a hankali tana jin wani sanyi na ratsa ko ina na jikinta numfashinta ya dinga
sama sama kamar xai dauke, can ta juya a hankali ta kalli inda Mujaheed yake xaune,
kan kneels dinsa ta gansa ya rufe fuskarsa da both palms dinsa.... wani ihun da
yasa duk mutanen parlon suka juya kallonta ta fasa da karfi, sai kuma ta mike da
gudu ta fice daga parlon kamar mahaukaciya, Umma ta durkusa kan gwiwowinta bibbiyu
duk jikinta na 6ari ta rushe da wani matsanancin kuka mai cike da tashin hankali ba
na wasa ba tace "Alhaji ka min bayani yanda xan gane don girman Allah, ko akwai
wani Mujaheed din ne banda nawa a gidan nan, ka fahimtar da ni fisabilillahi, don
nasan Mujaheed guda ne a gidan nan kuma d'a na ne, kuma da matarsa... Wani Mujaheed
din ka hada da Imaan???" Ammi da ta kasa controlling kanta ta fashe da kuka sosai
tashin hankali karara muryarta tace "Abubakar ban amince da auren nan ba, ban yarda
ba, nace ban yarda ba, warware auren nan xa ayi, ban amince da shi ba...." tana
fadin haka ta fice parlon da sauri tana kuka, Muryar Inna suka ji da karfi tana
xaga parlon tana cewa "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'una, la ilaha ilallahu
Muhammadur rasulillahi sallallahu alaihi wassalam, hasbunallahu wa ni'imal wakeel,
la ilaha illa anta subhanaka innee kuntu minazzalimin, wayyoo Allah ni patuu, Naga
abinda ya isheni waye kuma Mujaheed?? Lalacewa ta samu Bukar da Ahmadu, Allah ka yo
min agaji naga abinda ya isheni kankat a duniya yau, jama'ah waye kuma Mujaheed,
daga ina kuma aka samosa??" Umma dake durkushe ko ina na jikinta na rawa ta dinga
gyada kai kamar idanuwanta xa su fito tana kallon Inna ganin abinda ta dinga yi a
parlon, gaba daya a birkice take don bata ma san tana gyada kan ba, Mikewa Aunty
tayi tana goge hawayen idonta ta fice daga parlon duk jikinta a sanyaye, daga Abba
har Daddy da su kawu Bala kallon Inna dake ta xagaye parlon suke, har daga karshe
ta tsaya cak waje daya ta juyo tana kallonsu, sai kuma ta rushe da matsanancin kuka
tana nuna su tace "Amma Allah ya hada ni da gantalallun 'ya ya, waye kuma Mujaheed
Allah na tuba, to wllh kafin in tada gidan nan cikin minti kalilan a warware auren
nan don jikata ba rasa manema xata yi ba, ban amince da auren nan ba, kun cuce ni,
kun ci amanata kun ja mana fushin Ubangiji a gidan nan yau, lalacewa ta sami 'ya
yana ni Asabe...." sai kuma ta fashe da kuka tace "Tunda uwata ta haifeni ban taba
ganin haka ba" Umma ma ta fashe da kuka mai ta6a xuciya tace "Innalillahi wa inna
ilaihi raji'un, na shiga uku na lalace ni Rukayya, dama Mujaheed dina ake nufi ban
sani ba, dama d'a na aka hada aure da Imaan, na mutu na lalace kuwa" kuka take
sosai ba na wasa ba ta daura hannu a ka ke kya ce uwarta ce ta mutu, Ba Abba kadai
ba har Daddy was so shocked at reaction din kowa a parlon, Abba ya sunkuyar da
kansa ya ma rasa abinda xai ce, Inna ta xauna kan kujera ta kara fashe da wani
sabon kukan tace "Idan ba a raba auren nan ba yanxun nan ni dai xan ce na bar ku da
Allah inyi tafiyata kano Ahmadu da Bukar, Bala da d'an tsut" Abba ya dago yana
kallonta, lkci daya gaba daya mood dinsa ya canxa ganin yanda Inna ke kuka, Umma na
jin abinda Inna tace ta tsayar da kukan da take har sannan jikinta na 6ari tana
kallonsu Abba taji me xai ce, a hankali Mujaheed ya xame hannunsa daga fuskarsa da
ya rufe yana kallon Umma da idanuwansa da suka rine, Mikewa Abba yyi ya wuce
bedroom dinsa without thinking twice, Mujaheed ya bi sa da kallo, lkci daya ya mike
ya fice daga parlon without anybody noticing him except Mama Hadiza da ta bi sa da
kallo, sai ga Abba ya fito daki rike da takarda da biro, tunda Umma take bata ta6a
sanin akwai abu wai shi relieve ba sai a wannan lkcn da taga abinda ke hannun Abba,
ko da relieve din na ciwo ne tasan bai kai wannan da taji dadi ba yanxu, Abba ya
kalli inda Mujaheed ke xaune kafin ya wuce daki yace "Ina Mujaheed din??" Da sauri
Umma ta juya tana kallon direction din tace "Gashi nan Alhaji" Xaro ido tayi ganin
babu shi a wajen, da karfi Umma tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un.... Ina
yake??" sai kuma ta mike kusan a guje ta fita parlon, Inna ta fashe da kuka tana
kallon inda yake xaune kafin ya fita tace "Toh me yasa ya fita ga takarda da biro
ka dauko me yake nufi da tafiyar da yyi da auren yar mutane a kansa?? To wllh sai
ka bi sa Ahmadu, maxa ku bi sa" Abba dai ya kasa cewa komai har sannan yana tsaye
da takarda da biro a hannu yana kallon bakin kofa da mamakin fitan da Mujaheed
yyi.... Safeenah na xaune compound ana ta hadin salad sai murmushi take ita kadai
tun bayan da taga Imaan ta fito parlor ta wuce apartment dinsu da sauri kamar warce
aka kora, sai dai fuskarta a rufe yake bata ga expression din fuskar ba, can kuma
taga Ammi ma ta fito ta wuce apartment din nasu, ita ma dai ba wani ganin fuskarta
tayi sosai ba don saurin take, sai kuma ga Aunty ma ta fito babu walwala ta nufi
apartment din su Imaan ita ma, lastly sai Mujaheed, kansa a kasa ya nufi gate, ta
mike ta bi bayansa da sauri fuskarta dauke da damuwa tace "Dear wai me ke faruwa
ina ta jin kananun rumors wai kamar an fasa auren Imaan, what's happening?" Bai
tanka ta ba tafiyarsa kawai yake, da sauri ta dinga binsa tana kallon idonsa da
mamaki tace "Did you cry Mujaheed?" Murmushin da bata ta6a sanin sa da shi ba ya
sakar mata a hankali yace "Not at all, ki je ki ci gaba da aikin ki" sosai taji
dadin murmushin Mujaheed dinta, coz ita dai tun da suka yi aure da kyar idan ta
ta6a ganin ko da murmushin sa, ta mayar masa da murmushin tace "Toh dear, amma
akwai bikin kuwa har yanxu? Naji sai kananun xance fa ake wai kamar Sadeeq din yace
ya fasa??" Still walking yace "Akwai biki, kije ki ci gaba da abinda kike" bai jira
cewarta ba ya fice daga gate din gidan kamar dai wanda ake jira a waje sbda saurin
da yake, ya shige motarsa yyi zoom off ya nufi main road, Safeenah ta bi motarsa da
kallo tana murmushi sannan ta juyo ta dawo cikin gidan, Umma ta hango tana tahowa
kusan a guje, a rikice Umma ke kallonta tace "Safeenah ya fita gidan nan ne? Kin
gansa?" Da mamaki Safeenah ke kallonta tace "Lafiya? Me ke faruwa? Waye ya fita"
Gaban Umma yyi mugun faduwa ta yi still tana kallon Safeenah xuciyarta na bugawa,
Safeenah tace "Wai me ke faruwa ne?" Cike da karfin hali Umma tace "A'a dama sako
xan basa...." Safeenah tace "Ya wuce a mota ai yanxu" Umma ta saki wani salati ba
tare da ta san tayi hakan ba ta fita gate din da sauri, Safeenah ta bi ta da kallon
mamaki, har titi sai da Umma ta tafi bbu hijab ko xata ga Mujaheed, amma babu
alamar sa, nan ta fashe da matsanancin kuka cikin tashin hankali tace "Toh ina kuma
ya tafi bai tsaya ya rubuta takardan ba ni Rukayya..." Sai kuma ta juya da sauri ta
koma gida tana goge idonta, wayar Safeenah dake xaune tsakar gidan ta amsa ta xaga
bayan gidan da sauri, Safeenah dai sai bin ta take da kallo, a xuciyarta kuwa
tunani take to me ke faruwa kuma da matar nan ta rude haka ko dai an daura auren ne
bayan full assurance da aka basu baxa ayi ba kuma su ma sun ga alamar hakan, ita
duk ba wannan ba murmushin da Mujaheed yyi mata ne ya tsaya mata a rai, ta d'an yi
murmushi tana tunanin what to cook for him today, Umma na xagawa tayi dialing
number Mujaheed hannunta na rawa, Mujaheed dake driving ya kasa controlling tears
dake sakko masa har lkcn ya kalli wayarsa, ganin Safeenah ya d'an yi murmushi ya
dau wayar ya katse sannan ya kashe phone din gaba daya ya ajiye, salati umma ta
rafka jin waya a kashe da ta sake kira, ta fashe da kuka tace "Ai ni na shiga uku
na banu na lalace, me hakan ke nufi ko ba shi da caji ne?" Hannunta na rawa ta sake
kira amma a kashe, tayi xaman dirshan a kasa tana shessheka tace "Kila dai ba shi
da caji ne, amma da yasan takarda Abba yaje daukowa a daki da baxai wuce ba sai ya
tsaya ya rubuta masu, nasan bai sani bane" cikin rawar murya take maganar tayi
dialing number Hajiya Saude da har ta haddace lambarta ta kai kunne, Hajiya Saude
na dagawa umma ta sakar mata wani kuka da karfi tace "Saude na shiga uku, abu bai
yi ba, Saude da nasan xa ayi haka da na bar d'an Bulasawa ya auri tsinanniyar nan,
wllh ni yanxu ma sai in taho ki rakani mu koma gun mutumin ya warware abun yaron ya
dawo hankalinsa ya xo su yi auren, Saude da yaron yace masu ya fasa auren sai wai
Ahmad ya sa aka daura da Mujaheed dina, Mujaheed fa Saude, da d'a na Mujaheed aka
daura auren, Mujaheed aka daura ma aure da sauran ciwo, yar wajen Aisha Saude...."
Cikin rikicewa da tashin hankali Hajiya Saude ta dinga cewa "Mujaheed kuma,
Mujaheed fa kika ce, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Mujaheed din ki??? La
ilaha ilallahu Muhammadur rasulillahi sallallahu alaihi wassalam, mun shiga uku
Rukayya, Mujaheed kuma" Umma na kuka sosai tace "Wllh shi Saude, ko Safeenah ban
yarda na gaya ma ba ban san ya xata dau wannan labarin da nake ji ya ma fi mutuwata
ciwo ba, wllh da auren nan da Ahmad ya daura da d'an cikina da ma mutuwa nayi hakan
bai faru ba,
wayyo Saude xama bai gan ni ba, gani nan fitowa mu koma gun mutumi a warware komai
na hakura duniya da lahira in ma Bualsawan da kansa ke son auren Imaan wllh tllh na
hakura Allah ya basu xaman lafiya da xuri'a dayyaba, gani nan fitowa Saude ai lkci
bai kure mana ba, da sauran lkci" Bata jira cewar Saude ba ta katse wayar tana kuka
kamar ranta xai fita ta daura hannu a ka, da ta tuna Safeenah sai taji xuciyarta ya
tsinke har ranta take jin da ma da gaske mutuwa tayi da wnn bakar rana da take
gani, Wai only son dinta da take ji da take alfahari da aka daura ma aure da yar
makiyiyarta sauran ciwo...." Hade kai tayi da kasa tana kuka tana cewa "Ya Allah
kasa mafarki nake ba gaske ba, Allah ka warware wannan auren kada in mutu, wayyo
Allah ka dubeni" sai kuma ta mike kamar mahaukaciya ta shiga gidan ta kitchen,
kanta a kasa ta wuce sama ta dau hijab a daki ta saka har da nikab sannan ta fito
ta sake bi ta kitchen ta fice daga gidan ta nufi titi da shegen sauri tana hadawa
da gudu tana cewa "In sha Allahu, xa a warware komai na hakura in ma uban Sadeeq ne
Imaan ta aura ba komai"

_Hajiya Sadiya Chamo wakar biki yyi sweeeet😉 Mujaheed yace ince maki ki turo
account number, amma fa su a duniyar su basu da banks irin na Naija, to ko ya xa
ayi wannan abun?? Ya dai ce ince ki turo...._🥰

*I really appreciate the prayers and well wishes yesterday fans soyayyata gare ku
babu mix wllh, masu Ihisani😍 ina godiya kwarai Allah ya kara budi da daukaka, Allah
ya sa ku gama da duniya lafiya, Allah ya raya kids ya raba ku da iyayen ku lfya...*

_If you are yet to patronize Imaan... Do so for the love u are having for the book
and the writer for the sake of Allah.... nima sai in ji dadi_😃🥰
it's just 300 via....
Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah.

Next Update around 9 or so in sha Allah. Tnx.

77.....

Duk yanda Maryam tayi da Imaan ta gaya mata abinda ya faru ganin yanda take kuka
kamar ranta xai fita tun shigowarta kin ce mata komai Imaan tayi, Maimoon da
hankalinta ya tashi ba kadan ba ta cire mayafin da Imaan ta rufe fuskarta da shi
tace "Wai meye haka Imaan, what's happening, talk to us plsss"
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

Fadawa kan gado imaan tayi ta kara rushewa da wani kukan tana shessheka, Maryam ta
dinga kallonta tana fatan Allah yasa ba tunanin da take bane ya tabbata wato Sadeeq
yace ya fasa auren, lkci daya jikinta yyi sanyi ta xauna gefen gadon ta ma rasa
abinda xata ce tayi tagumi tausayin Imaan ya cikata, Hawaye Maimoon tafara yi tana
dago Imaan tace "Don Allah me ya faru Imaan ki gaya mana, wani abu ya sami Sadeeq
din ne? Ki mana magana don Allah" Mikewa Maryam tayi ta fita dakin a sanyaye hawaye
na sakko mata. Aunty ce tsaye bedroom din Ammi ta jingina da bango ta rungume hannu
tana kallon Ammi gaba daya ta rasa abun cewa, Ammi dai na xaune gefen gado ta ci
kukanta har ta gode Allah tayi tagumi, cikin sanyin murya Aunty tace "plss I don't
want you to react again Ummi Imaan, kiyi hakuri and keep calm ki ga next action da
xa a dauka, bana son ki sake cewa komai" Ammi ta kalleta tana girgixa kai tace "I
should keep calm fa kika ce Amina?? Why will I?? am sorry to say this duk da
Mujaheed ba shi da wani aibu kuma shi din tabbas namijin aure ne amma aurensa da
Imaan will be the last thing I could imagine on Earth, Amina kin mance wacece uwar
Mujaheed? Kin manta wacece Rukayya? Me yasa su Alhaji xa su yanke hukunci haka babu
knowledge dinmu, why will they do such, me yasa xa a aura ma 'ya ta Mujaheed bayan
ba rasa masoya xata yi ba, duka duka nawa Imaan din take ma gaba daya, me yasa xa
su min haka...." Hawaye sosai Ammi ke yi tana girgixa kai tace "Yau da ba Rukayya
ta haifi Mujaheed ba da xan fi kowa farin ciki da wannan hadin nasu, I will be
happy Amina, amma a wannan circumstance din na fi kowa jin takaici da bakin ciki, I
hate the thought of my daughter been an inlaw to Rukayya, fatana kada 'ya ta ta
kwana yau a gidan nan da auren Mujaheed a kanta, Mujaheed ya fi karfinta, Rukayya
xata iya karasa kashe min 'ya ta ne idan aka bar wannan auren, don Allah Amina ki
min favor din fahimtar da Abba illar wannan auren da ya hada" Ammi na kuka sosai
tace "she is all I've got a duniyar nan, idan na rasata shkkn that's just the end,
ya xan yi Amina? wannan karan wllh baxan yi shiru a cutar min da Imaan ba, auren
nan babu alkhairi babu alamarsa Mujaheed ya sakar min 'ya ta ko kuma in dauketa mu
bar gidan nan, ba matarsa bace Imaan" kuka sosai Ammi ke yi tana jin xuciyarta na
mata xafi, Aunty ta kasa cewa komai ita ma hawayen na sakko mata, Mama Hadiza ce ta
shigo dakin ta tsaya tana kallonsu kafin ta karaso calmly tace "Aisha I never
expect ur reaction a parlon yayana ba, ban taba xaton ko a mafarki xa ki yi abinda
kika yi ba, you look into my brothers face and tell him baxa ki iya barin d'an sa
yyi xaman aure da 'yar ki ba, ko da kuwa Rukayya shaidan ce a siffar mutum don
nasan saboda ita kika yi wannan furuncin wllh bai kamata ki yi ma Ya Ahmad haka ba,
bai kamata ba, bai kuma cancanci haka daga gare ki ba, kuma ni kin ban mamaki don
ba Ahmad kadai ba har ni da Ya Sadeeq kika ci ma fuska don Mujaheed d'an mu ne,
kuma ko albarkacin abinda Mujaheed yyi ma Imaan a rayuwa ba gori ba bai cancanci ki
rufe ido a gabansa yana xaune ki nuna baki son hadin nan ba, ita Inna dama bana ma
kawota a lissafi don nasan wacece ita amma kiri kiri ki kunyata d'an uwana da yake
tunanin yana da iko da Imaan kamar yanda Ya Sadeeq ke da iko da ita" Ita dai Ammi
bata ce komai ba hawaye kawai take don gaba daya ba wani sauraron Mama Hadiza take
ba, ta dade bata jita cikin tashin hankalin da take a lkcn ba, Cikin sanyin murya
Aunty tace "Mama Hadiza put ur self in her shoes, she spoke out of frustration,
kiyi hakuri ko wace uwa iyakar abinda tayi xata yi wllh, bbu wanda bai san Rukayya
ba bbu wanda bai san halinta ba, wace uwa ta gari ce xata so Rukayya a matsayin
surkar 'yar ta, think of it mama Hadiza..." Mama Hadiza tace "Don't tell me that
Amina, Imaan ba da Rukayya xata xauna ba, wllh da Yaya Ahmad yyi breaking min news
din nan nayi farin ciki ba kadan ba, amma me?? lkci daya farin cikin nawa ya koma
ciki tuna uwar Mujaheed da nayi, ni ina da yakinin wllh tllh nan gaba sai kun fi
kowa murnan hadin nan da ya Ahmad yyi yau, barin ma ke Aisha..." Mikewa Ammi tayi
tana goge idonta tace "Kiyi hakuri Mama Hadiza bana tunanin xan amince da wannan
auren na fi ku sanin wacece uwar Mujaheed, na kuma san abinda xai faru, Kar ki ce
na maki rashin kunya but Imaan is all I've got sannan ga condition dinta, baxan so
wani abu ya samar min ita ba, da wanne xata ji? Kishiya ko Uwar miji, wanda ba sai
an fito fili an fada ba kowa yasan kishiyar nan ba mutunci gareta ba har ke kin
shaida, imaan is too young and sick for this, don Allah kiyi hakuri ki ma
yayinnanki magana a warware auren nan they are not meant for each other, Allah
ubangiji ya mata wani xabin mafi alkhairi" Ammi na magana hawaye na sakko mata ta
shige bathroom, Aunty ta lumshe ido ta bude tana jin tausayin aminyartata da 'yar
ta, Mama Hadiza ta fi minti biyu a tsaye kafin ta juya ta fita dakin. Kawu Bala
dake ta girgixa kafa daga inda yake xaune parlon Abba bayan fitar Inna da kusan
minti goma yace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, where are we to start from
now??" Shi dai Daddy ya jinginar da kansa da kujera tun xamansa parlon har sannan
bai ce uffan ba, Kawu Audu yace "Masalha daya shine a warware auren nan kawai shine
kwanciyar hankalin kowa don Asabe ba kyau... ayi hakuri kawai a warware auren Allah
yasa hakan yafi alkhairi" Abba dai sai kallon Daddy yake da ya ki cewa komai ya
rungume hannu, Abba ya mike yace "Sadeeq tun a lkcn da na baka sadaki a masallaci
ya kamata ka fito fili ka nuna min baka son na hada auren 'yar ka da d'a na, bai
kamata ka min shiru a lkcn ba, da ka fito da abinda ke ranka da duk abubuwan dake
faruwa yanxu bai faru ba, but anyway yanda na hada auren nan haka xan rabasa ba da
jimawa ba in sha Allah, ka tashi ka tafi ka ba uwarka hakuri, kai ma kuma ina baku
hakuri da matarka, in dai a kan na aura ma Imaan son dina ne xa a raba auren yanxu
sai kowa ya saki ransa...." Kallonsa kawai Daddy yake ya kasa cewa komai, Kawu Bala
yace "A'a bai kai haka ba Ahmad.... Don't misunderstand him plss" ko saurarensa
Abba bai yi ba ya nufi kofa ya fice yana dialing number Mujaheed, Daddy ya bi sa da
kallo, Kawu Bala yace "Haba sadeeq idan ma baka yi na'am da auren nan ba bai kamata
ka fito fili ka nuna ba, Ahmad yyi iya kokarinsa ne na ganin ka fita kunyan jama'ah
da aka tara, ko shawara bai yi da d'an sa ba yana ganin ya isa da shi ya yanke
hukunci amma kuma a samu matsala daga bangaren ka" Daddy ya sauke ajiyar xuciya
kamar baxai ce komai ba sai kuma ya girgixa kai yace "Noo, not at all...." kawu
Audu yace "Banda abin ka xumunci bai kara karfi ba hakan da aka yi?? jini daya wasa
ne Sadeeq? ita Asabe fa dama ba a saiti take ba wani lkcn sai dai Allah ya gyara
mana ita, don me xaka dau maganganunta ka kunyata D'an uwan ka, shi Mujaheed da aka
ma aure without his consent dubi fa yanda ya nuna kamar ba komai amma sai ku
Sadeeq, to Allah na tuba ina laifin wannan hadin banda rikicin Asabe da yawa yake??
Ku kan ku xa ku yi farin ciki da auren nan nan gaba, Mujaheed bayan hankali da
natsuwa da sanin ya kamata ga ilimin muhammadiyya ga boko, uwa ba ya rike ibada ba
da wasa ba, ai ya xo wajena na gani, haba wnn ai abun kunya ne kuke sai kace ba
jini ba, kuma duk Asabe ce daburtattciya, kai Asabe dai ba kyau" Daddy ya girgixa
kai a hankali yace "Ko kadan ni ban ga aibun hadin nan ba, Mujaheed d'a na ne, na
kuma san waye shi, na kuma san tarbiyarsa, infact tarbiyata ne Mujaheed, but 6acin
ran fa?? You all can see the reaction displayed by his mum ga kuma maganganun da
Inna ke yi tana cewa ta bar mu da Allah, for what?? Ni tun a masallaci nasan xa ayi
haka, Yusuf da ya fito ya nuna yana so ma ga abinda ta mana balle wannan?" Mikewa
yyi yace "Am coming" daga haka ya fita ya bi bayan yayan nasa. Ta Rasulu ta rike
haba ta hangame baki tana kallon Inna da ta gama tsara mata sa6on da su Ahmadu da
Bukar suka yi tana sharban kuka sosai, tsofaffin parlon suka dinga salati ana
nanatawa ana tafe hannu, cikin rawar murya Inna tace "Allah ya isa tsakanina da
Sadeeq da ya yaudari jikata ya kuma ja mana rudani a gida har ya kai ga Ahmadu da
Bukar da su d'an tsut suka tafka babban sa6o suka aura ma Imaan Mujaheed wai a fita
kunya, basu san kunyar aka shiga ba tsumu_tsumu, da wani idon xa mu kalli jama'ah"
Ta Rasulu tace "Ikon mai mana ruwan sama, to yanxu kice duk uban kayan da muka tafi
muka mata jere a rusheshen gidan Bukari komawa xa mu yi mu kwaso a kai gidan
Mujaheed kenan?" Gwalo ido Inna tayi tana kallonta, sai kuma ta fashe da kukan
takaici tace "Ke dai Allah kadai yasan yanda xai yi dake, kuma gaskiya na yafe
kawancen nan namu, waye kuma Mujaheed, me Imaan xata yi da shi fisabilillahi ta
Rasulu? Anya kinsan Allah kuwa" Ta Rasulu tace "Al-quran baki son gaskiya Asabe,
yau ko Bala ne ya haifi Mujaheed baxa ki tambaye ni wanene shi ba balle Ahmadu ne
ya haifesa, to ita Imaan din wacece da Mujaheed baxai aureta ba Allah na tuba, wllh
ban taba ganin shegen gantalallen xumunci irin naku ba, 'ya 'ya uwa daya uba daya
ki dinga nuna bambanci haka, daga an rufa ma yarinya asiri kada aji kunya an lika
ma Mujaheed sai ya xama laifi??" Inna tace "Gaskiya Allah ya isa sanin ki da nayi a
duniya Ta rasulu, Allah kuma ya saka min...." Ta Rasulu ta mike tace "Oho dai
gaskiya ce sai na fada, Bulasawan da ya so kunyata ku ma ba don...." Inna ta katse
ta da sauri tace "Waye kuma Bulasawa Ta rasulu? Tsinannu xa ki ce manyan barayin
duniya, uban waye bai san sata suke yi ba? Waye bai san abinda Bulasawa yyi a
Nigeria ba, an fa sha kamasa dumu dumu yana sata wllh, ni dai Allah ya dubi jikata
ya rufa mata asiri da aka fasa auren, da ina xan shiga idan aka aura mata d'an
gagarumin barawo, mu ma duk kallon barayin xa a dinga mana kawai, in sha Allahu sai
naje na ci uban yaron a gidan satan su da suka gina, bari dai komai ya lafa a sakar
min jika wllh wllh sai na je" Ta Rasulu tace "Dama idan xa ki tafi sai ki rike
kudin satan da ya
dinga baki kina boyewa ki mayar masu da abun su" Inna ta saki salati tayi tagumi
tace "Duka duka nawa ya ban, sau uku fa kadai ya ban dubu uku sai shegen iron dinsa
gashi can ko budewa ban yi ba, ance maki ni gantalalliya ce mara tsoron Allah??"
Shigowar Ammi yasa Inna tayi shiru, Ammi ta xauna parlon kanta a kasa, Inna ta
share guntun hawayen idonta tana kallonta, cikin sanyin murya Ammi tace "Inna xan
tafi gidanmu tare da Imaan...." Inna ta katse ta da sauri tace "Akan me??" Ammi
tace "Idan aka raba auren in sha Allah xamu dawo, amma yanxu...." Inna ta katse ta
mike tace "Yau naga fitinanniyar bafillatana, don an aura ma Imaan Mujaheed sai
kice xaki tafi gida da Imaan, meye da Mujaheed din kamar warce aka aura ma barawo,
jikana ne fa shi ma?? Ni fa na haifi Ubansa na haifi Uban Imaan.... yau naga ikon
Allah, to wllh kiyi ta tafiyar ki amma bbu inda xaki da jikata don an aura mata
d'an uwanta, wahalan da yyi da ita ko ke kinyi idan ba rashin tsoron Allah ba??"

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

78......

Mikewa Inna tayi ta shige daki tana cewa "Ni dai ba ruwana, kiyi tafiyar ki ke
kadai amma bbu inda imaan xata je, kawai Allah ya rufa mana asiri mu kuma mu ki
rufa ma kanmu?? kaji min mata dai" Ta Rasulu na kallon Ammi tace "Haba Shatu, ke ma
fa Mujaheed din nan d'an ki ne, ko yana da wani mugun hali ne wanda ke kika sani ba
mu sani ba??" Inna ta leko daga daki tace "Ina fa ta Rasulu kawai samun waje irin
na bafillatani, mai mugun hali ai a bayyan 'yar ta imaan yake, ni wllh sai ince ma
cutar Mujaheed aka yi da aka hada sa da Imaan bayan ga matarsa Safara'u, Imaan fa
ko girki bana jin ta iya, banda Mujaheed din wanene xai iya da ita, kuma daga an
rufa ma juna asiri sai ki nemi ki tona mana, ni dai ba ruwana kiyi ta kanki Aisha,
ko kinfi Ahmadu da Bukar sanin abinda suke ne, kawai mata kina nema ki lalata mana
xumuncin mu sbda rashin tsoron Allah" Mikewa Ammi tayi ta fice daga parlon, Inna ta
rike ha6a tace "Yau naga bafillatana dai..." Ta Rasulu ta tabe baki tace "Ni dai
ban taba ganin irin wannan xumunci ba tunda uwata mai salati ta haifeni, gida duk
ya rikice daga hada aure na xumunci" Inna tace "Wllh idan xuciya ta debeni sai in
iya ce ma Mujaheed ya ki sakinta mu ga ta tsiya, idan an bi komai a hankali kuma
Allah ya dora mu kansa ai sai ya saketa tunda a gaskiya Imaan ta fi karfin sa sai
irin su Bulasawan dama, amma mata kya xo kice min xa ki tafi da Imaan...." Ammi na
komawa part dinsu ta shiga dakinta ta sa Hijab ta dau purse ta fito ta bude dakin
Imaan, Mama Hadiza ce xaune dakin ta rungume Imaan dake kuka kamar ranta xai fita
cikin tashin hankali take cewa "Yayana ne shi fa Mama, ya xa ayi ace wai an daura
mana aure da yaya, wayyo na shiga uku mama dama Yaya na auren kanwarsa?? don Allah
ki gaya ma su Abba Yaya na ne, wllh ni dai yayana ne...." Mama Hadiza ta kasa ce
mata komai, jin har jikinta ya dau xafi sosai ta dago kanta tana kallonta fuska
daure tace "Wato ban isa ince kiyi shiru kiyi ba koh?" Maryam dai na xaune dakin
tayi tagumi, Maimoon sai hawaye take duk jikinta a sanyaye tana kallon Imaan da duk
ta fice hayyacinta, Mama Hadiza ta sake Imaan ganin Ammi ta mike ta fita daga
dakin, Ammi ta karasa cikin dakin tana kallon 'yar tata tace "Dauko Hijab din ki"
tashi Imaan tayi ta dau hijab dinta tana shessheka tace "Ammi plsss kice ma Daddy
su yi hakuri wllh yayana ne shi, ba aure tsakanin mu, don Allah kar su ce sun daura
mana aure" Fixgo hannunta Ammi tayi suka fita daga dakin trying hard to control her
tears, Imaan ta dinga bin ta tana kuka sosai har suka fito compound dake cike da
jama'ah sai dai fa duk an hada groups ana kananun surutai tunda har sannan ba a
fito ance ga abinda ke faruwa ba a gidan, sun dai ga families din na ta kai komo
bbu annuri, mutane dai dai ne yanxu basu san an fasa auren Imaan da d'an gidan
Bulasawa ba, sai dai duk bbu wanda yasan an daura auren da Mujaheed, Safeenah ce
tsaye rike da plate din abinci ta cika uban nama tana kallon Mama Hansai dake ma
wasu yan uwanta da wasu mutane dake xaune sun hada group bayanin abinda ke faruwa
fa a gidan, duk aka saki baki ana kallonta, tana girgixa kai tace "Toh Yaya Ahmadu
na ganin haka sai kawai ya daura auren da d'an sa tunda an riga an tara jama'ah
kada a ji kunya, shine fa hankalin kowa ke tashe a gidan, kusan dai bbu wanda yyi
na'am da auren nan da aka hada...." Hajiya Bari'a kawar Aunty dake wajen ita ma a
xaune ta ce "Wani d'an nasa a ciki, shi angon ko kuwa??" Mama Hansai ta tabe baki
tace "Kila da da angon ma aka auran da duk matsalolin dake faruwa yanxu bai faru
ba, da d'an ita Hajiya Rukayya aka daura auren, wato dai Mujaheed....." Safeenah
dake tsaye tana ta saurarenta ta sake plate din hannunta a hankali, lkci daya ta
fixgo Mama Hansai tana gwalo kwala kwalan idonta tace "Wani Mujaheed din????" Mama
Hansai ta juya da sauri tana kallonta don bata ma san ita ce matar Mujaheed ba,
Cikin yanayi na tashin hnkli da rikicewa Safeenah ta dinga jijjigata tana cewa
"Wani Mujaheed din kike nufi, ki gaya min wani Mujaheed? mijina aka daura ma aure
da Imaan din???" Mama Hansai dai sai xaro ido take ta kasa cewa komai, Safeenah ta
saketa a hankali tana tariyo reaction din Umma daxu da irin gigicewan dake tare da
ita har da fita waje babu hijab, da kuma Mujaheed da ya fito parlon mahaifinsa
hawaye a idonsa, wani karan da ya tsorata mutanen compound din Safeenah ta saki da
karfi, dai dai fitowar Ammi da Imaan, Safeenah na hada ido da Imaan dake kuka Ammi
na rike da hannunta ta sulale wajen sumammiya, duk aka yo kanta ana salati masu
debo ruwa na debowa, masu fiffita nayi, Ammi dai tuni ta ja Imaan suka fice
compound din gaba daya.... Gidan Gwaggwo Ammi ta wuce tare da Imaan, parlor suka
tadda gwaggwo suna jimami da yan uwanta biyu a parlon, Ammi ta gaisheta da mutanen
parlon ta wuce ciki Imaan ta na biye da ita kanta a kasa, Gwaggwo ta bi su da kallo
can ta mike ta bi bayansu, gefen gado ta tadda Ammi a xaune tayi tagumi, Imaan kuma
ta kwanta kan gadon tana kuka a hankali, Gwaggwo ta xauna kan carpet dake shimfide
dakin tace "Toh me kuma ku ka xo yi nan Aisha ko baku yarda da kaddara bane? Komai
bawa ya ga a rayuwa fa rubutattce ne daga Allah, dama can Allah ya rubuta Sadeeq ba
mijin Fatima bane, abun da ciwo amma hakuri kawai duk xa mu yi, daxun nan Muhsin ya
bar gidan nan shi ma duk abun ya damesa gashi ko sanin inda Sadeeq din yake bai yi
ba wayoyinsa ma duk a kashe wai, ni ban taba xaton haka daga Sadeeq ba, ko me ya
samesa haka Allah ma fi sani, amma gaskiya wannan ba lafiya ba ranan daurin aure ka
xo kace ka fasa ba laifin tsaye balle na xaune, ban taba ganin haka a xuri'ar mu
ba... Na kuma samu labarin hadin da yayan mijin ki yayi Allah ubangiji ya sa hakan
shine mafi alkhairi, ai matar mutum kabarinsa...." Ammi ta katse ta tace "Alkhairi
fa kika ce Gwaggwo, wllh auren nan ba alkhairi babu alamarsa, in dai basu sakar min
'ya ta ba barin garin nan xan yi da ita, Allah baxai taba sa 'ya ta ta hada jini da
irin Rukayya ba, bana fatan haka kuma in sha Allahu hakan baxai ta6a faruwa ba...."
Gwaggwo ta bude baki tana kallon Ammi da mamaki, can tace "To ai baki da iko da
'yar su Aisha, ke har xa ki bude baki kiyi wannan mummunan furucin kin mance
halaccin uban yaron nan, gaskiya ban san ki da mance alkhairi da rike sharri ba,
Ina ce saboda ke Ahmadu har sakin Rukayya sai da yyi wanda sai da tafi shekara uku
bata gidan, ko don ubansa ke kya bude baki kiyi wannan furucin Ammi, meye aibun
Mujaheed yaro mai hankali da nutsuwa to wllh ni ko ranan laraba sai da ya shigo
gidan nan gaisheni, da kyar ayi wata daya ko sau daya bai shigo min ba, kaji min
Aisha dai, 6ata masu xumunci kike son yi ko me? Ke dai ba kawai kiyi ma yar ki
addu'a da fatan alkhairi da xaman lafiya gidan mijinta ba tunda ga yanda abubuwa
suka kasance, da Rukayya Fatima xata xauna ko Mujaheed? Haba Aisha sai kace ba
matsayin uwa kike gare Mujaheed ba, gaskiya banji dadin rashin hankalin nan naki
ba, daga ubansa yyi kokarin fidda ke da mijin ki kunya sai ki rufe ido ki nuna masu
ke baki da hankali baki da kirki??" Ammi ta girgixa kai tana murmushin takaici tace
"Dama ba lallai kowa ya gane abinda nake nufi ba ba kuma lallai kowa ya ga abinda
nake hangowa ba, Rukayya ta wuce tunanin ku gwaggwo, wllh Rukayya...." Katse ta
gwaggwo tayi ta mike tace "Toh sai ki mayar masu da 'yar su ki dawo mu xauna ba
shikenan ba, ai bamu da iko da ita, maida ta ki kwaso kayan ki mu xauna nan tunda
ke shashahsa ce..." Daga haka ta fice daga dakin. Duk kiran da Abba ya dinga yi ma
Mujaheed layinsa gaba daya a kashe suke, daga karshe gidan nasa kawai Abba ya wuce
nan mai gadi ya sanar masa bbu kowa a gidan, yayi reverse kenan xai bar layin kiran
Daddy ya shigo wayarsa, da kamar baxai daga ba sai kuma ya daga, Daddy yace "Kana
Ina Barrister?" Abba yace "Ina hanya" Daddy ya fada masa eatry da yake son su hadu
a lkcn don bbu inda xa su xauna su ke6e su yi magana, Abba yace "Alright" kusan a
tare suka isa eatry din, Daddy ya sa waitress ta kawo masu just table water, Abba
ya bude ruwan ya sha kusan rabi sannan ya ajiye sauran, Daddy na kallonsa yace
"First of all I will like to say I am sorry Barrister, duk da dai you misunderstood
me amma ina mai baka hakuri still, ko kadan Barrister Auren Imaan da Mujaheed da ka
hada ba wai ban yi farin ciki da hadin naka bane, abun farin ciki ne sosai don ko
bbu komai mun kara karfafa xumuncin mu, babban damuwata a auren nan shine
mahaifiyar mu... nasan baxata ta6a na'am da hadin ba, Dole xata yi maganganu da bai
kamata ba a kan mu, sannan Barrister bamu san ko shi Mujaheed din xai yi na'am da
auren ba, we don't know ko yana da ra'ayin mata biyu, infact duka duka yaushe yyi
auren ba, beside bai ta6a fitowa ya nuna yana son Imaan ba banda so na 'yan
uwantaka unlike Yusuf da ya nuna interest a kanta da farko, Barrister what if mun
shiga hakkinsa shi Mujaheed din?? Wani irin xama kake ga xa su yi baya sonta ita ma
kuma haka?" Murmushi Abba yyi yace "Ae shi yasa nake ta neman sa ta waya domin ya
xo ya datse auren amma ban samesa ba, yanxu haka daga gidansa nake baya nan, but in
sha Allahu kar ka damu xa a raba auren" Daddy yace "It's not a matter of a saketa
or not barrister, in har shi yayi na'am da auren shikenan, sai kuma mu san yanda xa
mu yi da Inna, Imaan kuma I am hoping she learn to live with him as husband in sha
Allah, Rukayya da Aisha kuma I don't think xa su iya saka xumuncin mu ya sa mu
tangarda, in har Mujaheed yayi na'am da auren kuma Inna ta hakura shkkn Allah ya sa
hakan shine mafi alkhairi gare su gaba daya, I think you don't need to add anything
to what I just said now barrister mu bar xancen haka...." Daga haka Daddy ya kira
waitress don ta kawo masu abinci coz it's almost Asr. Tun da Safeenah ta farfado
take bin duk mutanen dake xagaye kanta da kallo kamar me son tuna abinda ya faru,
lkci daya ta mike a xubure kamar warce aka tsikara ta fasa wani ihu tace "Shi mijin
nawa aka aura ma Imaan, innalillahi wa inna ilaihi raji'un, na shiga uku Hajiya
Rukayya
ta kai ni ta baro ta cuce ni, ta cuce ni, ta cuce ni, mijina ne ya auri Imaan daga
karshe, wayyo na shiga uku...." Da gudu Inna ta karaso wajen ta Rasulu na biye da
ita ta dalilin labari da aka je aka basu a bangaren ta wai Safeenah ta suma a
tsakar gida, Inna na kallon Safeenah tace "Mu ma duk haka muka ji da aka mana
kishiya Safara'u, sai dai duk na ki ya fi ciwo ke da kika tika rawa a bikin kishiya
jiya, yau kuma tun safe kike ta yanke yanken kabeji da salak......" Safeenah ta
fashe da matsanancin kuka tana jijjiga kanta kmr tababbiya tace "Wllh wllh baxan
xauna da kishiya ba kishiyar ma Imaan, don ni kadai aka yi Mujaheed a duniya, don
ni kadai aka yi sa, sai na nuna ma Rukayya ba ni ta yaudara ba, baxan fallasa ta ba
yanxu sai ta fara sanin su waye family dinmu, sai ta san an aura ma Mujaheed Imaan
ne saboda mugun halinta da bakin halinta wllh idan ban nakada ma Rukayya duka ba
ban Haifu cikin Mansura ba....." Gate Safeenah ta nufa da gudu kamar mahaukaciya
tana rusa kuka tana kiran mummyn ta, Inna ta bi ta da kallo da sauran mutanen wajen
da suka bude baki da shock, Inna tayi wani dariya irin ta boss tace "Toh wllh babu
tsinannen da ya isa ya raba auren nan da raina, auren nan mutu ka raba takalmin
kaza, maxa a tafi a kwaso kayan da aka kai gidan barayi a fito da kayan Safara'u a
feshe dakin a xuba na jikata, dama idan ba shi Mujaheed din ba waye ya dace da
Imaan banda toshewar basirar mutane? Dama can hange hangen Imaan da kwadayin abun
duniya yasa ta hango xuri'ar shegu barayi suka kuma yaudareta suka gudu, ni fa tun
ba yau ba nake tunanin hada auren jikokin nan nawa biyu kawai dai Allah bai bani
basiran yin magana bane amma yanxu kam faduwa ta xo daidai da xama bbu shegen da ya
isa ya raba auren nan, ko shi Mujaheed din yyi yunkurin sakin Imaan ni sai in iya
tsine masa ya bi duniya" tana gama fadin haka ta nufi part dinta tana cewa "Ku kira
min Ahmadu da Bukar na canxa shawara gaskiya, wnn ai abun arxiki suka hada...." Sai
kusan Magrib Umma ta dawo gida duk tayi xuru xuru tun safe banda ruwan shayi babu
abinda ta xuba a cikinta, xuwa lkcn duk an watse a gidan sai yan uwa na jiki da
suka rage, tana shiga dakinta ta dau wayarta don kiran Mujaheed taga missed calls
din Hajiyan Marafa yyi goma sosai gabanta yyi mugun faduwa ta dinga kallon wayar,
ta xauna gefen gado, Ummi ta biyota daki tace "Umma Hajiya Baturiya yayar Aunty
Safeenah fa ta xo har sau uku daxu..." Umma ta hadiye abu da ya makale makogwaronta
da kyar ta hade rai tace "Toh sai aka yi Yaya? Neman me suke min?" Ummi tace "Nima
ban sani ba" Umma tace "Toh fita waya xan yi" Ummi na fita dakin Umma tayi dialing
number Mujaheed ta ji sa a kashe, mikewa tayi hankali tashe tace "Me Mujaheed ke
nufi da kashe wayarsa ne??" Hijab ta kuma sakawa ta fita gidan don xuwa gidan
Mujaheed ta iskesa. Tsaye ta ga Inna tsakar gida kusa da apartment din su Ammi inda
take shiga ba nan take fita ba, Aunty da Mama Hadiza sai Mama Hansai da few
relatives na tsaye dai suna kallonta, rai bace ta ci gaba da cewa "Wllh idan bata
yi hankali ba sai ince kar ta sake dawowa gidan nan ta sha xamanta gidansu, kuma a
kai ni yanxun nan in dauko jikata ai ba uban wani yyi mata ciki ta haifeta ba, ta
dauwama a gidansu kar ta sake dawowa gidan d'a na, mata kawai sai bakar xuciya,
Bukar dai ya auri jaraba don Aisha jaraba ce wllh, shi jikan nawa take nuna ma k'i
haka ba kunya ba tsoron Allah bata jin kunyata ba balle na ubansa sannan Bukar, shi
Mujaheed din ne bata so sbda rashin tsoron Allah kamar wani barawo?? to kuwa har
Bukar bata so tunda bata son d'an d'an uwansa, kawai ni dai Allah ya hada 'ya yana
da fitinannun mata a duniya... Maxa a kai ni gidansu in dauko jikata yanxun nan"
tana fadin haka ta tafi dauko Hijab, Daddy da Abba da shigowarsu gidan kenan su ma
suka tsaya from afar suna kallon mahaifiyar tasu.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

79.....

Sai kusan karfe goma da rabi Umma ta dawo gida daga gidan Mujaheed duk tayi wani
wujiga wujiga da ita, tun magarib da ta fita ta je gidan nasa take ta xaune cikin
compound wai ko xai dawo amma shiru har karfe goma da wani abu bbu shi bbu alamarsa
hakan yasa ta baro gidan hankali tashe tana hawaye ga Hajiyan Marafa sai kiranta
take a waya ba kakkautawa, daga karshe ma kashe wayar tayi gaba daya, direct part
din Inna ta nufa tana share xufar fuskarta, kowa ya ganta yasan tana cikin tashin
hankali ne ba na wasa ba, xaune ta samesu da Mama Hadiza, Mama Hansai da Ta Rasulu,
sai Aunty, Umma ta rakube jikin kujera tana kokarin boye hawayen idonta kar su
gani, ta gaishe su gaba daya, duk suka amsa banda Inna dake cin abinci, Umma tayi
kasa da murya kamar ta kirki tace "Inna daga gidan Mujaheed nake yanxu, tun
magariba nake gidan amma shiru shiru bai dawo ba ban san dalili ba, tsorona kada
wannan hadin ya ja mana matsala mai karfi a xumuncin mu tunda Aisha kirikiri ta
fito ta nuna bata so, ita ma Imaan din da kanta ba so take ba, shi kansa Mujaheed
nasan tashin hankali ne yasa ya shiga duniya, kuma daxu naji ke da kanki kince sai
an raba auren, to Mujaheed fa har ynxu bbu labarinsa wllh yanxu haka ma daga
gidansa nake Inna...." cikin rawar murya ta kare maganar tana kallon Inna, Inna ta
tura abincin gabanta ta kalli Ta Rasulu tace "Kin ji bala'i koh? Rukayya ni xa ki
ma sharri kice nace a raba aure da raina a duniya ba wai na mutu ba, ni dai nasan
daxu a parlon Ahmadu nace ba ayi shawara da ni ba na kuma nuna bacin rai na sosai,
amma bayan wannan ban san komai ba, ban kuma ce komai ba, yo dama ai Mujaheed shine
dai dai Imaan ganewa ne ba ayi ba da wuri, shi fa Sadeeq din nan dama ubansa ne mai
kudin ba shi ba, kuma da kyar ma idan Mujaheed bai fi sa kudi ba, kudin uban yaron
ke rarumowa ya xo nan yana mana burga yana yaudaran jikata wllh, lkci daya kuma
Allah ya toni asirinsa, ai wannan auren da kike gani Rukayya mai raba sa kilan
mutuwa kawai xai yi a banxa a hofi, kawai ni dai abinda na sani shine dolen
Mujaheed ya hada akwatuna irin wanda su Bulasawa suka kawo mana da gwalagwalai idan
ko ba haka ba wllh sai in ce a raba auren baki na a leko don jikata ba gantalalliya
bace, sannan da kyar idan baxae karo Sadaki ba, ke dai da Aysha da wuya ku ga
annabi wllh, ban ta6a ganin mutane irin ku ba a duniya, ita ta tashi ta gudu da
yarinya kamar mahaukaciya ba don su Ahmadu da suka dakatar da ni ba wllh da naje da
dauko jikata da daddaren nan" Umma da hankalinta ya kai kololuwa gun tashi ganin
Inna ta juya xance gaba daya on like da safe da ta dage sai anyi saki ko tayi ma su
Abba Allah ya isa, tasan kuma ai shkkn aikin gama ya gama tunda Inna ta canxa
labari don dama wajenta kadai take da hope, ynxu kuma bbu hope din, mikewa tayi ta
fice daga parlon da sauri, bata yi nisa tana tafiya ba ta xauna nan kasa kan hanya
ta rushe da kuka sosai tace "Na shiga uku na lalace na cuci kai na, yanxu d'a na
aka makala ma sauran ciwo ina ji ina gani?? Wllh sai na raba auren nan ko ta halin
yaya, Mujaheed baxai taba hada jini da xuri'ar Aisha ba, da auren nan ya rayu gwara
in mutu kawai, in sha Allahu sai ya saketa sai dai idan ba ni na haife sa ba, wato
yana ma son auren kenan tunda har ya gudu ba labarinsa....." ta kuma fashewa da
matsanancin kuka xuciyarta na mata xafi, ko mutuwar ubanta bata ji ciwonsa irin
yanda take jin ciwon wannan auren ba, ji tayi dama ayi backward din komai ta bar
Sadeeq ya auri Imaan, ko bakomai xata yi mingling da manyan mutane da dangin
Bulasawa ayi hotuna su kai Imaan kantamemen gidanta, yanxu Imaan ta auri Sadeeq ba
ma lallai taga irin rayuwar da suke da Sadeeq din ba balle ta ji haushi ko ya
dameta, ita da ganin Imaan sai in ta xo gida, amma wnn wai yaron cikinta ne xai yi
rayuwa da Imaan din tana ji tana ganin komai da idanuwanta, tashi tayi tana kuka
sosai ta wuce apartment dinsu tana cewa "In sha Allahu sai ya saketa, sai in bani
nayi nakudar sa ba, in sha Allahu bbu aure tsakaninsu, d'a na ya fi karfin sauran
ciwo, ta ina xai fara rayuwar aure da ita ta talauta min shi da ciwonta" ranan dai
Umma yanda taga rana a gantale haka ta ga dare, babban damuwarta da tashin
hankalinta me xai faru idan gari ya waye, tasan da kyar idan Hajiyan Marafa baxa su
taho gidan tare da duk yaranta su risketa ba, tasan Safeenah ta gama sanar masu duk
abinda ya faru da yanda ta dinga kokarin hana auren Imaan da Sadeeq, Umma ta mike
xaune ta rike kanta tana kiran Allah ya kawo mata dauki xuciyarta, ni kam nace
lallai ma. A bangaren Ammi kuwa sllh ta dinga yi daren ranan don ita ma neman
baccin tayi ta rasa rabonta da shiga tashin hankali haka har ta manta, da dadewa ta
sha addu'ar kada Allah ya kaddaro masu rana irin ta yau tun daga lkcn da ta lura
shakuwan Mujaheed da Imaan ya fara wuce hankali ya dauka, shi yasa ma ta dinga taka
ma Imaan burki sai gashi lkci daya bbu notice abinda take gudu ya faru, da yau
Yusuf aka hada da Imaan me xai dameta, sai ma ta fi kowa farin ciki da hadin amma
Mujaheed kam ya fi karfin 'yar ta. Imaan na cikin duvet ita din ma ba bacci take ba
sai juye juye kawai take, xuwa lkcn kukan ma ta kasa wani mugun xaxxabi take ji
sosai, duk joints dinta ciwo suke mata ga headache da backache, tasowa Ammi tayi ta
nufo ta bayan ta idar ganin juye juyen da take, ta cire duvet din jikinta tana
kallonta kafin tace komai taji xafin da jikinta yyi ba kadan ba, Imaan ta mike
xaune da kyar ta jigina da gado a hankali tace "Ammi bana jin dadi" Ammi tayi shiru
tana kallonta, can ta mike ta wuce kitchen ta hado mata shayi sanin da daddare bata
ci abincin kirki ba ta kwanta, ta dawo ta mika mata shayin tace "Ki sha in samo
maki paracetamol yanxu" Imaan ta karbi cup din hannunta na rawa, Ammi ta fita xuwa
dakin gwaggwo, sllh ta sameta take yi ita ma, ta bude gun da take ajiye
magungunanta ta dau pain reliever da man xafi da ta gani ta fita, duk yanda Ammi
tayi da Imaan ta sha shayin kin sha tayi wai amai take ji, hakan yasa ta bata
paracetamol din ta shafa mata magani duk jikinta ta sa ta kwanta sannan ta lullube
ta. Da safe Abba bai hakura da kiran layin Mujaheed dake kashe har sannan ba, lkci
daya jikinsa yyi sanyi a nan kuma ya fara considering d'an nasa, to ko shi ma baya
son auren ne, yasan dai ko Mujaheed baya so xurfin cikinsa ma baxae bari ya fada
ba, shigowar Umma ya sa ya ajiye wayar hannunsa, Umma ta duka kan kneel dinta tana
kallon Abba dake kallonta shi ma, Cikin rawar murya tace "Alhaji na xo neman
alfarma ne a gun ka ba wai don na isa ba don ni din a ko da yaushe mai laifi ce na
sani amma don Allah kar ka biye ta halina kayi ma girman Allah ka saurareni kuma ka
min alfarmar da na xo nema" Abba na kallonta yace "Ina jin ki" tayi kasa da kai a
sanyaye tace "Alhaji wannan auren da ku ka hada kayi ma girman Allah ka raba sa, na
farko Aisha ba son auren take ba, ita Imaan din ma haka, shi kuma Mujaheed sbda
tashin hankali kaga ba shi ba labarinsa, ban san inda ya shiga ba, don Allah ka yi
min rai kayi abinda ya kamata a wannan batu..." Abba yace "i don't have any say on
this matter any longer Rukayya, Sai abinda Inna ta ce, yanda tace haka xa ayi...."
Umma ta fashe da kuka tana kallonsa tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, wllh
Alhaji Mujaheed dina baya son auren nan, tun jiya fa har yau wayarsa a kashe bamu
san inda yake ba" Abba ya mike yace "Yana lafiya in sha Allah" mikewa Umma tayi
tana shessheka ta fita tana tunanin meye mafita, don ita da Mujaheed yayi aure da
Imaan fa gwara ko da bata mutu ba ta yarda ta rasa komai nata a duniya. Karfe tara
Abba da Daddy suka isa gidan gwaggwo, Gwaggwo ta fito daki bayan mai aikinta ta
kirata, da fara'a ta amsa gaisuwar su tana masu sannu da xuwa, Gwaggwo ta xauna
saman kujera tace "Ya aka ji da taro da hidindimu??" duk suka amsa da Alhmdllh an
gode Allah, Gwaggwo tace "Toh madallah Allah maku albarka, Allah kuma yasa abinda
ya faru shine mafi alkawari gare mu gaba daya" Abba yace "Ameen, dama xuwa muka yi
mu baki hakuri a bisa wannan hukunci da muka yanke baki da masaniya, abubuwan ne
suka xo a haka gwaggwo, ayi mana afuwa...." Gwaggwo tace "A'a ba komai wllh Ahmad,
ai duk an xama daya, wannan aure kuma da ku ka hada Allah yasa shine mafi alkhairi,
Allah maku albarka, su kuma Allah ya basu xaman lafiya, kada ku biye shiriritan
matan ku, abinda ya dace shi ku ka yi, anjima in sha Allahu ni da kai na xan maida
Fatimar gida, idan Allah ya yarda" Abba yace "Toh Alhmdllh Allah ya kara girma
gwaggwo, ita Hajiya Aishar fa??" Gwaggwo tace "Ta d'an fita siyo mata magunguna da
yake jiya da xaxxabi ta kwana amma da sauki sosai yanxu, bacci ma take" Abba yace
"Toh Allah ya sauwake, xa mu koma Gwaggwo, mun gode kwarai, Hajiyar ma tace a
gaishe ki" Gwaggwo tace "Toh Ina amsawa, Allah ya maku albarka" duk suka amsa da
Ameen suka mike, Daddy ma yyi mata sallama suka fita parlon, a bakin gate suka hadu
da Ammi ta dawo pharmacy, kallo daya tayi masu ta dauke kai ta gaida Abba, Abba ya
amsa yace "Ya mai jikin ta kara ji Aisha" Ammi tace "Alhmdllh da sauki" shi dai
Daddy kallonta kawai yake, Abba yace "Toh Allah ya bata lafiya" Ameen ta mayar masa
ta shige gate din gidan, murmushi Abba yyi ya bude front seat, daddy ya xaga ya
shiga maxaunin driver suka bar anguwar, Abba yace "In sha Allahu xa su sakko gaba
daya, kuma xa su fi kowa farin ciki da wannan aure nan gaba" Daddy bai ce komai ba
har suka hau saman titi, sai kuma yace "How do we reach Muhd, I am disturb about
him barrister" Abba dai bai ce komai ba don shi ma bai san inda xai samo Mujaheed
ba balle su ji ta bakinsa a kan auren. Mota biyu Hajiyan Marafa suka yo da yaranta
mata su uku, da yan uwanta biyu da kawayenta biyu sai Safeenah da har wani rama
tayi sai yan idanuwa da suka kumbura suntum dan kuka, da ta tuna wai mijinta
Mujaheed aka hada da Imaan sai ta fasa wani ihu kamar mahaukaciya har tsakar dare
haka ta dinga masu kamar tababbiya, ta girgixa ne ba na wasa ba, gate mai gadi ya
wangale masu a xatonsu masu xuwa biki ne, Hajiyan
Marafa ce ta fara sakkowa motar sannan yaranta, kawayenta da Yan uwanta suma duk
suka fito daga tasu motar ko wannen su fuska a murtuke, Rahma ce ta tafi dakin umma
ta sanar ma ta xuwan su Hajiyan Marafa da suka ki shigowa ko da parlor ne wai a
kira masu Hajiya Rukayya, Umma ta katse wayar da take da Hajiya Saude jikinta ya
hau rawa tace "Kice masu bana nan, tun daxu na fita...." Rahma tace "Har fa da
Hajiyar da kanta" cikin tsawa Umma tace "Ki fita kice masu bana nan nace, ko uban
me xan masu da suka xo min nan, ko ce masu aka yi ni na daura ma Mujaheed aure???"
Rahma ta fita dakin umma ta mike da sauri ta sa makulli hannunta na rawa, xaunawa
tayi gefen gado xuciyarta na bugawa, Allah kadai yasan abubuwan da xa su fada yau,
saukin abun ma Abba sun fita tun daxu da kaninsa, Aunty da Mama Hadiza dama suna
can part din Inna tun safe, dialing Number Hajiya Saude ta kara yi ta sanar mata
Hajiya Mansura ta xo tare da tawagarta a motoci, Hajiya Saude tace "Innalillahi wa
inna ilaihi raji'un... Toh yanxu ya ake ciki??" Umma na share xufar da ke keto mata
tace "Tonon asiri nake tsoro Saude, nasan yar duk ta kwashe ta sanar masu yanda aka
yi, Saude kar su fasa kwai a gidan nan in shiga uku dadin abun ma Alhaji bai nan,
Amina da Hadiza kuma suna gun tsohuwar amma kinsan yanda Hajiyan Marafa ke magana,
wllh dole su ji hayaniya su fito, ni dai nace Rahma tace bana nan" Hajiya Saude ta
sauke ajiyar xuciya tace "Ni wai Rukayya tun farko me kika ga tattare da family din
Hajiyan Marafa kika hada d'an ki da yar su??" Umma tace "Aa kawai don ace d'a na na
auren yar masu kudi mana, sunan nake so dama, kuma ai haka ma mutane ke cewa"
Hajiya Saude ta ja tsaki tace "Toh me kika karu da a kudin su?" Umma tace "A'a ki
bari, wllh ynxu haka akwai wani sarka da dankunne xai yi miliyan daya da rabi haka
Hajiyan Marafa ta bani kyauta kwanaki da naje, sannan ta dalilin auren nan matan
governor kalilan ne ban sani ba, duk taronsu sai naje, manyan kasan nan yanxu
daddaya ne ban gani ba ido da ido amma a mata, Kai har wasu maxan ma...." Xaro ido
Umma tayi jin hayaniya a tsakar gida tace "Gasu can Saude, xa mu yi magana anjima"
daga haka ta katse wayar ta tafi ta bude labule a hankali tana lekansu.... Hajiyan
Marafa ce tsaye tana cewa "Duk inda Rukayya ta shiga yau sai ta fito wllh, in har
na bar gidan nan to Rukayya ta fito ta fallasa kanta ne, 'ya ta xata yaudara a hada
baki da ita a mata kishiya??? Toh wllh wllh yau sai ta san tayi da Hajiya Mansura,
yanda ban xauna da kishiya ba haka diyata baxata xauna da kishiya ba, malamai da
bokayen da take bi yau duk sai ta fito tayi bayani ta tona kanta ta fadi abinda
tayi aka fasa auren yarinyar gidan nan har aka hada auren da mijin diyata...."
Hajiya Baturiya yarinyar Hajiya Marafa ta fari cikin tsawa da daga murya tace "Ta
fito da bakinta ta fadi abinda tayi aka fasa auren da aka lika ma mijin Yar uwata,
ta fito nace idan ba haka ba yau wllh wllh sai mun tada gidan nan in ga shegen da
ya tsaya ma mutan gidan....." Kawayen Hajiya marafa suka yi cikin parlor suna cewa
"Ae duk inda ta shiga sai ta fito wllh, sai ta fallasa kanta anji mugun abinda take
yi tun ba yau ba, yau xata ga karshen boka da malamai...." Mama Hadiza ce ta taho
compound din da sauri jin hayaniya Aunty na biye da ita a baya, Umma dake jin su a
daki ta daura hannu a ka ta dinga xagaye dakin hawaye na sakko mata tana salati
tana fatan kada su Abba su shigo gidan, wani rashin tunanin ne ya kai ta hade kai
da Safeenah har ta san sirrinta haka tasan abinda take ciki, tare fa suka dinga
xuwa gun Malamin ashe abu xai juyo kansu yanxu ga Safeenah ta fallasa ta gun uwarta
da bakinta ba shiru yake ba, ta xauna gefen gado ta fashe da kuka tace "Innalillahi
wa inna ilaihi raji'un, me ke faruwa haka ni Rukayya, Allah ka rufa min asiri kada
'yan gidan nan su jiyosu su fito, da na shiga uku yau kuwa" muryar Mama Hadiza da
ta ji tana tambayar lafiya yasa ta mikewa da sauri tana xaro ido ta ji cikinta ya
hautsine, Hajiya Baturiya tace "Kafff xuri'ar mu babu wanda ya taba xama da kishiya
don haka baxa a fara kan kanwar mu Safeenah ba, karya ake Safeenah ta xauna da
kishiya, Rukayya ta fito ta fadi abinda tayi gaban kowa yanxun nan..." Mama Hadiza
tace "Tohhh, iko sai Allah ku kuma da abinda ku ka xo kenan??" Hajiya Shamsiyya ta
iso wajen tana huci tace "Kwarai kuwa da abinda mu ka xo kenan, bokan da Rukayya ta
biya ta sa ya wargaje auren yar gidan nan shi xata fito yanxun nan ta kai mu gunsa
ya wargaje abinda yyi da har yasa tsautsayi ya fada kan 'yar mu, kin ganmu nan kaff
bbu mai kishiya, kema kanki nasan baki sonta don haka Safeenah domin ita kadai aka
yi mijinta baxata xauna da wata banxa wai kishiya ba...." Muryar Inna suka ji tana
salati da karfi tana cewa "Naga abinda ya isheni ni patuu, wasu mahaukatan ne aka
bude ma get suka shigo mana gida haka, anya ilu xai gama da duniya lafiya kuwa,
banda haka ya xai bude ma lafta laftan mahaukata get su shigo mana gida suna hauka
ba kakkautawa??? Ina Ahmadu da Bukar suke suga abinda shegen bakauyen da suka ajiye
a bakin get yyi, ya tashi ya bude ma ta6a66u get salon su fara bin mu da duka muna
gudu" Hajiya Marafa ta nufeta cike da raini tace "Hajiya mu ba mahaukata bane, amma
mun fi mahaukata hauka idan aka ta6o mu, ba wani abu ya kawo mu ba Rukayya muka xo
nema ta fito ta fadi abinda tayi aka fasa auren gidan nan wanda hakan yasa har aka
ma diyata kishiya bata ji ba bata gani ba, wllh har gun bokan da ta je aka mata
aiki duk sai ta kai mu yanxun nan gaba daya...." Inna ta xaro ido cike da masifa
tace "Auzubillahi wacece wannan Kuma?? Waye kuma boka ni patuu?? Rukayyar ce ta san
wani boka?? Toh tun da uwarta Hadiza ta haifeta bata san sa ba, kaji min gantalallu
dai yan iska mahaukata, waye kuma 'yar ku? Safara'u ko wa? Wllh tunda ku ka ma
Rukayya wannan gagarumin sharrin sai Mujaheed ya fito duk inda yake ya sake
shegiyar yar ku, don baku da tsoron Allah uwarsa ku ka xo yi ma cin mutunci har
gida?? To wllh sai Mujaheed ya saketa yau yau din nan, mu kaf danginmu bbu wanda
yasan boka, kai ko ma ya sani Allah ya yafe masa, kaji min mutane dai yan wahala,
wllh idan baku fitar mana gida ba sai na tafi caji ofis yanxun nan an xo an kwashe
ku in ga uban da ya tsaya maku, Ina ruwan Rukayya da wani boka Allah na tuba, matar
dake ta murna da hadin da Ahmadu da Bukar suka yi tun jiya, tun da nake Rukayya
bata taba shigowa da sassafe gaisheni ba sai da aka hada auren nan, yanxu haka da
kanta xata je dauko amaryar a gidan kakarta don can ta kwana... Kaji min mutane
dai?? To wlh ku fita ku ban wuri kada in tsine maku" Daga Hajiyan Marafa har 'ya
yanta da kawayenta sake baki suka yi suna kallon Inna, Inna ta juya ta fara wucewa
a fusace tana cewa "Rukayya ai ta fi kowa murna da auren nan, dama tun farko ita ba
son shegen d'an Bulasawan nan take ba, tun farko take ma Imaan kwadayin aure da
Mujaheed mu ne dai ba mu yarda ba" Aunty ta saci kallon Mama Hadiza dake bin uwar
tata da kallo, can duk suka bi bayanta, Safeenah ta fashe da matsanancin kuka mai
ban tausayi ta durkushe wajen jikinta na rawa tace "Na shiga uku Mummy wllh ni
baxan iya rabuwa da Mujaheed ba Ina sonsa, dama ashe duk yaudarata take da Mujaheed
take son ayi auren nan?? Wayyo mummy ku taimakeni kada ya sakeni wllh ina son sa"
Hajiyan Marafa ta dinga huci ta ma rasa abun cewa tana kallon Safeenah, sai da Inna
tayi nisa ta kalli Mama Hadiza murya can kasa tace "Ba boka ba har gun masu tsafi
Rukayya xuwa take wllh tllh"

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

80....

Hajiya Mansura tayi wani murmushi tana kallon kawayenta tace "Rukayya ta debo ruwan
dafa kanta, wato da sa hannunta da contribution dinta a yi ma 'ya ta kishiya.... To
xata san da Hajiya Mansura take, xata san da sa hannunta ayi ma diyata kishiya, ita
da d'an ta daga wnn lkcn sai dai hange daga nesa, kishiya kuma Safeenah baxata
xauna da ita ba, kaf xuri'ar mu babu mai kishiya kuma baxa a fara a kanta ba, ku mu
tafi kawai...." Hajiya Baturiya ta daga Safeenah dake rusa kuka kamar ranta xai
fita tace "Babu abinda kukan nan xai amfane ki da, ki tashi mu tafi tun wuri a san
abun yi, sai Hajiya Rukayya ta san da family din Alhaji Usman take...." Cikin kuka
Safeenah tace "Mummy yar uwarsa mai min rashin kunya a gidana fa aka aura masa,
wannan fitsararriyar ce fa mai min kallon banxa ce, Mummy ya xa ayi ta aurar min
miji na shiga uku na lalace, da na sani da ban biye uwar Mujaheed ba, ashe
yaudarata take da Mujaheed take son ayi auren, Mummy sai kinga yanda yake ji da
yarinyar, Mummy ya xan yi da raina idan aka kawo min ita gida a matsayin kishiya,
wayyoo Allah na..." A fusace Hajiyan Marafa ta buge bakinta tace "Uban wa xai kawo
maki ita gida a kishiya?? ai wnn gidan naki ne ke kadai har duniya ta nade, sai dai
idan ba tsatso na kika fito ba, Mujaheed naki ne ke kadai, hatta uwarsa Rukayya sai
dai ta gansa daga nesa, wa ke ta wani amaryar ga babban shaidaniya annamimiya da xa
mu fuskanta, in sha Allahu sai na toxarta Rukayya toxarci mai girma kuwa, sai tayi
da ta sanin sani na..." Daga haka ta ja ta xuwa cikin mota tana huci, duk suka
shige cikin mota suka bar gidan, Umma dake labe jikin window tana kallonsu ta share
xufar dake ta sauka fuskarta ta koma gefen gado ta xauna tana tunanin abun yi. Inna
na kallon Mama Hadiza da Aunty tayi wani murmushi tace "To kun dai jiye ma kunnan
ku komai, ni tun ba yau ba nasan Rukayya na xuwa gun boka da malamai, amma wllh
tllh in har da sa hannunta a rugujewar auren jikata ita ma nata auren na lilo
tangal tangal yanxu...." Sai kuma Inna ta fashe da kuka sosai tace "Allah dai ya
hada Ahmadu da jaraban duniya, Rukayya jaraban duniya ce, wato hade kai tayi da
surka suna xuwa gun boka bbu kunya ba tsoron Allah, Ni dai wlh in har aka binciko
min aka gano cewar ita ta wargaza auren Imaan akwai tashin hankali a gidan nan
gaskiya, don da kai na xan yi fatali da kayanta waje, dama darajan Mujaheed kawai
take ci a wajena" Mama Hadiza ta sauke ajiyar xuciya tace "Ni na ma rasa abun cewa
wllh..." Inna tace "Yo ba dole ba, kuma fa tana ciki tana jin su, wa ya sani ma ko
xawo ta dinga saki a dakin, ni dama ciki suka shiga suka kamata su lakada mata duka
da cacan bakin da suka dinga yi tsakar gida" Mama Hadiza tace "Toh Inna kin san
halinta kuma me yasa xaki kare ta a wajensu?" Inna tace "Ka ji ki ke kuma, ke baki
ga yanda jikinsu yyi sanyi ba, ai ynxu mance batun kishiyar da aka ma Safara'u xa
su yi su fuskanci Rukayya su yi fata fata da rayuwarta, ai bamm na hada mata...."
Dariya sosai Aunty tayi tana kallon Inna, Inna tace "Lallai ba ku san ni ba kenan
har yanxu, Ahmadu da Bukar kawai nake jira su dawo daga gidansu bafillatanar can da
ta gudu min da jika su ji wnn abun al-ajabin, dama Ta Rasulu sai da tace min bata
yadda da fasa auren nan da Bulasawa yyi ba, shi sa ma yau da sassafe ta tafi don
xuwa binciko mana m ke faruwa, na rantse da Allah in har da sa hannun Rukayya a
fasa auren nan sai nayi sanadin karshen xamanta a gidan nan..." Tana fadin haka ta
tashi ta wuce daki, Mama Hadiza ta girgixa kai tace "Rukayya tayi asara duniya da
lahira, yanxu meye amfanin surkai su xo tsakar gida suna maki cin mutunci haka, ni
wllh Mujaheed nake tausayi bai yi sa'ar uwa ba kwata kwata, tun fa ba yau ba ake
abu daya da matar nan ta ki sa Allah a ranta, anya Rukayya xata gama da duniya
lafiya kuwa??" Aunty dai bata ce komai ba amma ita ma mamakin maganganun Hajiyan
Marafa da tawagarta kawai take... Karfe sha biyu saura Gwaggwo ta shiga parlon
Inna da sallama, Imaan dake sanye da Hijab har kasa da Nikab na biye da ita a baya,
Inna dake xaune parlon tare da Mama Hansai ta amsa sallaman, Imaan ta wuce daki
walking slowly, Inna tayi ma Gwaggwo kallo daya tana sakace hakori ta dauke kai,
Mama Hansai ta shimfida mata darduma tana mata sannu da xuwa, Gwaggwo ta xauna
bayan sun gaisa da Hansai tace "Sannu Hajiya Asabe" Inna ta kalleta tace "Yauwa
sannu Hajiya Biba, amma a gaskiya ki dinga sa 'yar ki a hanya, kwata kwata Aisha
bata ji bata maida ni bakin komai ba, ya xata maida kanta mahaukaciya daga anyi abu
don fitar da mu kunya gaba daya, kema kuma baki son gaskiya don da kina son gaskiya
tun jiya ya kamata ki tiso keyarta ki koro su, nan nan nace mata kada ta je ko ina
amma yarinyar nan ta ki saurarata, gaskiya raina ya baci matuka don tun tsakar
daren jiya nayi niyar tahowa gidan in sameta su Ahmadu suka hanani" Gwaggwo dake ta
saurarenta tace "Allah ya kyauta, a dai ta hakuri..." Inna tace "Atoh, tamkar yar
ciki na na dauketa amma dubi iya shegen da ta min, kowa a gidan na ya girgixa da
auren nan, to amma abinda hakuri bai yi ba rashinsa xai yi? ni fa har cewa nayi sai
Mujaheed ya rubuta takarda amma d'an banxan ya gudu da dukkan alama yana so, to
yana so mana tunda tun jiya bbu shi bbu alamarsa ya shiga duniya" Gwaggwo tace "Toh
Allah dai yasa hakan ne mafi alkhairi, ga ta nan dai na kawota, ba ma ta jin dadi
amma tunda nayi ma iyayenta alkawarin dawo da ita shi sa na maido ta yanxu" Inna ta
yo waje da ido tace "Kuma bata da lafiya sai ayo min nan da ita, ta fito ta koma
barin su ai Hadiza na can" Gwaggwo ta mike tace "Ni dai xan koma Hajiya Asabe Allah
ya sanya albarka" Daga haka ta nufi kofa, Inna tace "Toh ko ruwa baxa ki sha ba"
Gwaggwo tace "A'a nagode, sai anjima" daga haka ta fita parlon, Inna ta tabe baki
tace "Aisha dai ta lalace wllh" tana fadin haka ta tashi ta tafi daki gun imaan,
kwance ta sameta ko nikab din fuskarta bata cire ba, Inna ta tuge nikab din ganin
yanda idonta yyi jajir ga jikinta yyi xafi ba kadan ba tace "Ae ni na shiga uku,
fasa auren da Bulasawa yyi yasa kika rame haka kika sa ma kanki ciwo Imaan?" Imaan
ta mike xaune da kyar hawaye na saukowa idonta ta kamo hannun Inna cikin rawar
murya tace "Don Allah Inna ki taimakeni, wllh shi fa Yayana ne taya xa ace ya
aureni???" Inna ta marairaice tace "Nima dai shi na gani, wnn uban sa6o har ina ni
patuu, sai kuma ace kinyi ciki kin haifa masa 'ya ya ko? To ta ina xa fara wannan
ta6aran ni Asabe??" Imaan ta fashe da kuka sosai ta rufe kanta da pillow tana
shessheka, Inna ta xauna gefen gado tayi tagumi tace "Anya su Ahmadu da Bukar suna
da hankali kuwa ni Patuu? A ina suka ta6a ganin anyi haka tukun??" Imaan dai kuka
kawai take kamar ranta xai fita, Inna tace "Naga abinda ya isheni...." Mama Hadiza
ce ta shigo dakin bayan sun hadu da gwaggwo a compound sun gaisa ta sanar mata ta
dawo da Imaan, Inna na ganinta ta mike tace "Hadiza anya su Ahmadu na da saiti
kuwa, ta ina Imaan da Mujaheed xa su yi aure ne wai ban gane ba, yayanta ne fa
Hadiza?" Mama Hadiza tace "Kamar ya Inna?" Inna tace "Toh abinda tace min kenan wai
yayanta ne kuma haka ne wllh yayanta ne" Mama Hadiza na kallon imaan tace "Halan
baki je islamiyya bane Imaan???" Inna ta daure fuska tace "Kaji wata magana,
yarinyar da ta haddace kur'ani har sauka tayi aka bata kyaututtuka kice bata je
islamiyya ba Hadiza??" Mama Hadiza na kallon Imaan fuska daure tace "Ta ina
Mujaheed ya xama Muharramin ki? Ko kin fara hauka ne? Idan an kai ki gidan sai ku
ci gaba da xaman yaya da kanwa a can, amma na sake jin kince yayanki ne sai na bata
maki rai wllh, shashasha kawai...." Murya can kasa Inna tace "Atoh dai, nima ban
san ta ina ya xama yayanta ba, ubanta Bukar ubansa Ahmadu, uwarta Aisha uwarsa
Rukayya" ko kallon Inna Mama Hadiza bata yi ba ta juya ta fice daga dakin, Inna ta
xauna gefen gado tayi tagumi tace "Gashi har yanxu shiru bbu Mujaheed din babu
labarinsa, ko shima yana can yana ta damuwar an hada sa da kanwarsa ne" ita dai
Imaan bata ko kalleta ba sai kuka take a hankali. Har Inna ta gama tsarinta
kallonta kawai Abba da Daddy suke yi, Inna tace "Wllh kuwa Ahmadu, motocin da suka
shigo sun yi biyar ga dai Hadiza shaida, to shine nace gaskiya idan maganganun
iyayen Safara'u ya tabbata kashin Rukayya ya bushe a gidan nan kuma xamanta ya xo
karshe, ynxu dai muna bin komai a hnkli ne don ba mu gama tabbatarwa ba tukun, duk
da dai gaskiya tun ba yau ba nasan Rukayya na shige shige" Abba dai kansa na kasa,
Daddy kuwa har xuciyarsa bai yrda da xancen Inna ko na second daya ba, can ya mike
yace "Inna lkcn Asr yyi xan tafi masallaci ynxu" Daga haka ya nufi kofa Inna ta bi
sa da kallo sannan ta kalli Mama Hadiza tace "Irin na xauna ina shirga masu karya
din nan, to in sha Allahu a gabansa asirin Rukayya xai tonu dumu dumu..." Abba ya
kalleta yace "Allah ya kyauta, xa mu xuba ido mu ga inda matsalar yake kafin a dau
mataki" Inna tace "Atoh dai nima haka nace a hankali xa mu bi komai har mu gano
gaskiya, ba wani gaggawa" shi dai bai ce mata komai ba, tace "Toh wai ni jama'ah
ina xancen jikana ne, tun jiya fa har yau shiru, ko gidansa xan dau mayafi in
tafi?" Abba yace "Daxu mun biya gidan baya nan" salati Inna ta saki tana kallonsa
tace "Toh me ya samesa?" Mama Hadiza tace "Gun aikinsa fa?" Abba yace "Sadeeq ya je
baya nan" cike da damuwa Inna tace "Toh anya lafiya kuwa??" Mikewa Abba yyi shi ma
dai duk abun ya damesa sosai, yace "Bari in tafi masallaci Inna" daga haka ya fita
parlon yana tunanin to Ina Mujaheed xae tafi tun jiya. Daren ranan Inna ta fito
tsakar gida tana salati tana kiran Abba da karfi, Daddy ne ya fito part dinsa ya
sakko yana tambayar me ya faru, Ko saurarensa bata yi ba balle ta kallesa ta karasa
part din Abba tana kwalo masa kira, Yusuf ne ya fito parlon Aunty na biye da shi,
yace "Lafiya Inna? Me ya faru" Daga sama har kasa ta kallesa tace "Kai rabu da ni,
kai ne Ahmadu, ni ba duk xatona kana gun amaryarka ba ashe kana gidan nan har yanxu
baka shigo ka min jajen abinda
ke faruwa ba...." Ganin Abba tace "Wllh Ahmadu na kasa gane kan Imaan, abinci fa
na tilasta ta ci sai gashi ta dinga amai kamar xata mutu ga jikinta duk xafi kamar
garwashi, ka ga dai yanda nake tsaye kyam to bata iya tsayawa haka, kada wani cuta
ya kamata fa in shiga uku ka taho mu je ka kaita asibiti, a gaskiya bata da lafiya
sosai wllh" shi dai Daddy na tsaye bayanta yana kallonta, Abba yace "mu je to" daga
haka ya fara tafiya Inna ta bi bayansa Aunty da yusuf na biye da su, kafin su je
har Mama Hansai ta kintsa Imaan da duk ta wani langwabe, Abba yasa ta sa hijab suka
wuce asibiti.... Daren ranan asibiti Imaan ta kwana tare da Aunty sbda karin ruwan
da ake mata, tausayinta sosai Aunty take ji don abun ya hade mata biyu ne, ga
heartbreak ga kuma unexpected marriage, ga shi duk ta wani rame, wajen karfe daya
Imaan ta farka daga baccin da take, Aunty dake xaune kan farin kujera ta jinginar
da kanta da gadon ta dago jin motsin ta, mikewa tayi tace "Sannu Daughter, ya
jikin?" Imaan ta kamo hannunta lkci daya hawaye ya kawo idonta cikin sanyin murya
tace "Aunty don Allah baxa ki taimakeni kiyi ma su Abba magana su yi hakuri kada su
ce ya Mujaheed ya aureni ba??" Aunty na kallonta da tausayi tace "You need much
rest imaan ki kwanta ki yi bacci ko na hada maki shayi?" Imaan ta girgixa kai
hawaye na sakko mata tace "Aunty kice wani abu plss" Aunty tace "Imaan meye da
Mujaheed din da baki son auren sa?" Imaan ta xaro ido tace "Aunty yayana ne fa"
murmushi Aunty tayi tace "Eh yayan naki, ae da aure tsakanin ku ko, Mujaheed is
good ba shi da wani flaws da xai sa ki daga hankalin ki, ke da ma kika fi kowa
sanin sa, kinsan halinsa ya san naki so what more, in just few days time da xa ku
yi tare am telling you sai kun gode ma iyayen ku da suka hada ku aure, but wait
ynxu ki gaya min me yasa baki son auren, amma kada ki ce min yayan ki ne, don ke
kika laka6a masa wannan matsayin, tell me yana da wani abu ne da ba ki so" ta fashe
da matsanancin kuka tace "Wllh Kunyan sa xan dinga ji Aunty, ni kunya nake ji...."
Sosai ta ba Aunty dariya, Aunty ta rungumeta tana murmushi bata dai ce komai ba,
cikin rawar murya Imaan tace "Allah kunya xan ji Aunty" Aunty tace "Toh ki kwanta
yanxu ki huta sosai, gobe sai mu yi magana" da haka ta lallaba ta ta kwanta, amma
imaan bata yi bacci ba daren ranan, da ta tuna wai ynxu Mujaheed fa mijinta ne sai
taji kamar ta bace duniyar gaba daya da wannan abun kunyan kawai, washegari sai da
rana aka sallamosu suka dawo gida. Sadeeq ne durkushe gaban Mum dinsa dake xaune
tana kallonsa da mamaki, ya hade kansa da kneels dinsa hawaye na sakko masa yace
"Mummy I don't know what just came over me, don Allah ki tausaya min ki ba Abbana
hakuri ya sami iyayen Imaan ya basu hakuri I cant imagine loosing her, don Allah ki
taimakeni ki masa magana ya same su sai a daura mana auren" Mummy tace "Anya kana
da hankali kuwa Sadeeq??" Ya dago kansa yana kallonta hawaye na sakko masa yace
"Sure mum, ni ban san me yasa nayi abinda nayi ba, help me speak to dad plss" mummy
tace "Kaje ka samesa da kanka Sadeeq I won't invole my self coz har ynxu ur Dad is
angry with me bcos of what u did" tashi yyi ya nufi kofa ta bi sa da kallon mamaki
don tun shekaranjiya sai yau ya shigo gida kamar an jefo sa, mikewa tayi duk
jikinta yyi sanyi sosai tana tunanin to me ya sami son dinta, ita tun farko tasan
ba yin kansa bane fasa auren nan da yyi, then who is after her son? Waye yyi masa
haka? Girgixa kai tayi tace "I will surely find out...." Tana fadin haka ta fita
dakin. Inna na xaune parlonta ta sa Mama Hadiza gaba bayan Magrib wai sai ta samo
mata layin Mujaheed kawai ita dai, Mama Hadiza ta kira for the third time da damuwa
tace "A kashe fa wayar yake Inna ba a kunna ba har ynxu, gashi kina jin ance
switched off" Inna ta xaro ido kamar xata rusa kuka tace "Anya Hadiza Mujaheed ba
kashe kansa yaje yayi ba kuwa??" Sai kuma ta fashe da kuka tana kallon Mama Hadiza
tace "Da mun shiga uku mun lalace" Mama Hadiza ta hade rai tace "Haba Inna ya kashe
kansa a kan me kuma?" Sallaman da suka ji bakin kofa yasa duk suka yi shiru, Imaan
dake kwance daki duk tana jin su ta mike xaune da sauri xuciyarta na bugawa jin
muryar wanda yyi sallaman, Inna ta kalli Mama Hadiza tace "Waye kuma wannan yake
min sallama?" Mama Hadiza ta amsa sallaman tana kallon bakin kofa, Sadeeq ne ya
shigo parlon kansa a kasa, Mama Hadiza ta dinga kallonsa da mamaki, Inna ta mike da
sauri tace "Naga abinda ya isheni, waye kuma wannan Hadiza?? Wa yake nema a parlon
nan" A hankali ya durkusa gabanta cikin raunin murya yace "Don Allah ku yi min rai
kaka kar ku raba ni da Imaan, ban san me ya sameni nayi abinda nayi ba, don girman
Allah ku yafe min kaka, wllh Ina son Imaan baxan iya rayuwa ba ita ba don Allah
kaka ki taimakeni kada su Abba su ce baxa su bani ita ba..." Hawaye sosai yake yana
kallonta hankali tashe, Mama Hadiza ta bude baki tana kallonsa, lkci daya taji
tausayinsa sosai ba kadan ba don gaba daya a hargitse yake ga wani rama da yyi ba
na wasa ba, Inna ta xauna ta rushe da kuka tayi mitsi mitsi da ido tana kallonsa
cike da masifa tace "Amma dai kai gantalalle ne wawa, da can uban me ya hau kanka
ka yaudari jikata ka sa mata cuta ka gudu?? kunyata mu fa kayi a idon duniya
makiyan mu na ta mana dariya ta ko wani lungu da sako, uwar me xa mu maka ka xo
mana nan d'an nan, wllh maxa ka fita kada Bukar ya gan ka don ba ruwana, gwara ma
Ahmadu...." A rikice ya kamo hannunta yace "Wllh kaka ban san me ya sameni nayi
haka ba, don girman Allah kar a raba ni da Imaan xan iya rasa rai na" Imaan ta mike
ta shige bathroom ta dinga kuka kamar ranta xai fita, Inna ta gwalo ido tana
kallonsa tace "Baka san abinda ya same ka kayi haka ba kuma?" Kuka sosai yake mata
yace "Wllh ban sani ba Kaka, ban san me ya faru ba, ban san me yasa nayi haka ba,
Kar ku hana ni Imaan don Allah, nasan ke kadai xa ki saurareni kaka" Inna ta fashe
da kuka tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Lalacewa ta sameka baka rike
Allah da karfi ba Bukar, ni dama nasan da akwai abu a kasa don wannan ba halinka
bane, yanxu ni ya xanyi da kai an riga an daura ma mutumi auren yarinya??" Dago kai
yyi da sauri yyi still yana kallonta ko kiftawa babu, Mama Hadiza ta sauke wani
boyayyen ajiyar xuciya tace "Ka bari iyayenta su dawo xa a san abinda xa ayi
Sadeeq...." Sadeeq ya kalleta yace "Don Allah ki sa baki Mama I can't imagine me
loosing her, u just can't imagine it" Mama Hadiza tace "You don't worry ka tafi
gida, in sha Allah xa a san abun yi" Inna na matsar kwalla tace "Ehh ka tafi xa a
san abun yi, ae kai din mutumin kirki ne" xuciyarsa na bugawa yace "Toh anjima xan
iya dawowa Kaka?" Mama Hadiza tace "A'a ka bari dai gobe dare yyi yanxu, I will
talk to my brothers..." mikewa yyi ya isa gabanta ya durkusa hawaye na sakkowa
idonsa a hankali yace "Nagode sosai Mama, Allah ya kara girma" Mama Hadiza ta kasa
cewa komai wani tausayinsa ta dinga ji har ranta, cikin sanyin murya tace "Don't
worry ka tashi ka tafi Sadeeq" mikewa yyi a sanyaye ya nufi kofa wiping off his
tears ya fita parlon, Inna ta kalli Mama Hadiza ta fashe da kukan takaici tace
"Kinga maganan iyayen Safara'u a fili ko Hadiza? Kinga magana ya fara fitowa koh,
wllh ni dama nasan da kyar Sadeeq yyi ma jikata haka, yaro ne fa mai hankali da
natsuwa, ubansa ma ga dattako da sanin ya kamata sannan ga kudinsa na halak, duk
satan da ake a kasar nan ko biyar bai taba sata ba wllh inda ya burgeni kenan,
komai nasa na halas ne babu Haram, gaskiya a duba lamarin nan a tausaya ma yaron
nan, yanxu dai jiran dawowar ta Rasulu nake inji bayani a nan kuma xa a san ni
tababbiya ce a gidan nan, kaff sai na tada gidan nan wllh idan abinda muke xargi
gaskiya ne, kuma don Allah da Mujaheed na son auren nan xai gudu? Ni nasan yana can
abun duniya ya ishesa baya son auren, ya kwantar da hankalinsa kawai da rai na babu
me cutar sa yyi masa auren dole wllh, me xai ci da Imaan Allah na tuba" Mama Hadiza
dai bata ce komai ba amma gaba daya kanta ya gama kullewa, bata ma san surutun da
Inna take ba don tausayin Sadeeq ya dameta. Misalin karfe sha daya da rabi na dare
Inna na kwance parlor sai sharar bacci take ga darduman ta da Hijab da carbi a
gefenta tayi shirin tashi tayi sllhn dare anjima, kukan da Imaan ke yi tun bayan
wucewar Sadeeq yasa taki kwanciya a dakin bayan tace mata aniyarta ta bi ta, shine
tayi kwanciyar ta a parlor, murda kofar parlon aka yi a hankali ya shigo ya ya
kulle kofar ya tsaya nan bakin kofa yana kallonta, bayan few seconds ya nufi
bedroom dinta walking gently ya bude kofar yana kallon ciki, Imaan na kwance ta
rufe har kanta da duvet sai dai ba bacci take ba, duk a xaton ta Inna ce ta bude
kofar dakin hakan yasa ko motsi bata yi ba, murmushi yyi ya rungume hannunsa ya
jingina da kofa yana kallonta ko kiftawa babu, a hankali ya rufe kofar dakin ya
nufi kan gadon, Imaan ta bude ido sosai daga cikin Duvet din da take jin kamshin
turaren da take ji....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

81.....

A hankali ya sa hannu ya sauke bargon daga saman kanta bayan ya xauna kusa da ita,
ido hudu suka yi, ta mike xaune a mugun firgice ta xaro ido tana komawa baya da
karfi tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, innaaa" sai kuma ta fara kokarin
sauka daga kan gadon ko ina na jikinta na 6ari, yyi hanxarin rikota ya maido da ita
kusa da shi ganin xata kurma masa ihu ya hade ta da jikinsa ya sa hannu ya rufe
bakinta, da karfinta ta dinga struggling din kwatar kanta hawaye na sakko mata amma
ta kasa, gaba daya kuma ta ki yarda ta kallesa, shi kam sai kallonta yake daga
karshe ya xame hannunsa bakinta ya rungumeta hade da lumshe ido murya can kasa yace
"Imaaan..." Ta fashe da kuka sosai tana tura sa tace "Bana son haka yaya ni ka sake
ni plsss, meye haka kke yi, ka sakeni bana soo....." Unexpectedly taji warm lips
dinsa a kan neck dinta, ta wani xaro ido ta fasa ihu cike da shock tace "Wayyo
Innaa....." Muryar Inna suka ji daga parlor cikin rikicewa take cewa "Kai amma
gaskiya ban taba ganin shaidaniyar yarinya irin wannan 'ya dai ta Bukar ba, me na
maki xaki gigitani haka fisabilillahi ina bacci Imaan? Me na maki?? To fito don
ubanki ki tafi bangaren ku baxa ki kwanar min a nan ba wllh tllh, maxa fito min
dakina, kuma ke da Allah tsorata ni da kika yi, gaskiya ke da Allah" Mujaheed ya
saketa da sauri ya koma baya ganin tana jan numfashi da kyar, jinginar da ita yyi
da gado yana kallonta yace "Hey relax now...." Kin yarda su hada ido tayi tana
kokarin daidaita numfashinta, tashi yyi ya kunna fan din dakin ya dawo ya xauna ya
dago kanta yace "I said relax..." Murda kofar dakin Inna tayi jin sa a rufe cike da
masifa tace "Bude min dakina ki fito ki kama gaban ki ba ruwana, Allah ya saka min,
daga yau kada ki sake yo min nan dama don koran kare xan maki muguwar yarinya
kawai" Imaan dai sai sauke numfashi take hankali, lkci daya ta mike tsaye hawaye na
sakko mata xata tafi gun kofar ta bude duk don ta samu ta gudu Mujaheed ya kamota
ya mayar da ita kan gadon ta fashe da kuka jikinta na rawa tace "Inna kice masa ya
bar ni in bude kofar" Inna dake tsaye har sannan ta wani xaro ido tace "Auzubillahi
waye ya shiga dakin?? Waye ya shiga??" cikin rawar murya Imaan tace "Yayaa..." Inna
ta d'an yi shiru kafin tace "Yaya? Waye kuma Yaya?" Imaan dai bata ce komai ba sai
goge idonta take xuciyarta na bugawa tana komawa baya, Mujaheed ya kafeta da ido ko
kiftawa baya yi yana kallonta, Inna tace "Shi Mujaheed din d'an iska ya xama xai
tsallakeni a parlor ya shigar maki daki kina kwance? Ko wiwi ya sha daga inda ya
taho??" Mujaheed ya mike yana murmushi ya shafa kansa ya nufi gun kofar ya bude,
Imaan taji 6ata taba son k'in ganinsa irin na moment din nan ba, ko kallonsa bata
son yi balle ta ji muryarsa, gaba daya ta ji ta tsane sa, Yana bude kofar Inna ta
kallesa daga sama har kasa sannan ta kalli Imaan da ta takure waje daya tana hawaye
tace "Ya kai minti nawa da shigo maki" Imaan taki cewa komai sai hawaye da
shessheka, Inna ta kara kallon Mujaheed tace "Iskancin naka ya kai ka dinga biyo
dare kana shigewa dakin mutane Mujaheed?? Toh dama neman ka ake ruwa a jallo, tunda
dai ka gama guje gujen ka mara tushe sai mu tafi gun su Ahmadu ka rubuta ma jikata
takarda ka mika ma ubanka da ya daura maku aure ya bata, don gaskiya Imaan bata isa
aure ba, idan ma ta isa to a gaskiya ka fi karfinta, Ina xata kai lafcece irin ka?
Ko baka ga yanda take bane, sannan wannan yaro Sadeeq dai ya dawo daxu ashe ba yin
kansa bane.... Don haka mu je dama kai kadai ake jira" Mujaheed yyi wani murmushi
yace "Ke ma xa ki iya rubuta takardan ki bata ai...." Inna tayi misti mitsi da ido
ta tsaya kallonsa ko kiftawa babu, can kawai ta fice daga dakin, ya bi ta da ido
har ta fita parlor gaba daya bayan ta cire makullin jikin kofar parlon, yana jinta
ta sa makulli ta waje ya juya yana kallon Imaan, ganin ta mike xata shige toilet da
gudu, yyi hanxarin cafkota ta kwala wani ihun jikinta na rawa tace "Na shiga uku
don Allah Yaya ka bariii...." Ya ajiyeta saman gado ta ja duvet tana rufe jikinta
tana kuka, yana kallon idanuwanta duk da ta ki yarda ta kallesa yace "Listen to me
now..." Kin tsayawa waje daya tayi tana komawa baya tana kuka, ya wani hade rai
yana kallonta yace "I said stay still now" da kyar ta xauna waje daya ganin ba da
wasa yyi maganan ba amma ko da mistake taki kallonsa sai hawaye take xuciyarta na
bugawa, ya dinga kallon lips dinta sannan a hankali cikin sanyin murya yace "isn't
this our Destiny Imaan?" Sai a sannan ta kallesa da sauri, ta xaro ido cikin rudewa
tana girgixa masa kai tace "Noo it's not plss, Yaya this not destiny, we are meant
to be only brother and sister not husband and wife, this is not destiny plsss, kai
yayana ne wllh, ni kuma kanwarka ce ko ka manta, bayan wannan babu wani alakar da
ya dace da mu Yaya, wllh Yaya wannan abun kunya...." Bai jira ta kai karshen abinda
xata fada ba ya bata shock of her life at that moment ta hanyar hade bakin sa da
nata...... Iyakar rikicewa Imaan ta rikice a wnn lkcn don har daukewa numfashinta
sai da ya kusa yi, don kansa ya kyaleta, amma fa shi ma ya kasa kallonta, murya can
kasa yace "Am I still ur Yaya?" Shock bai bar ta ta iya basa amsa ba banda rawa
babu abinda jikinta yake tana ja baya, dai dai nan kuma aka bude kofa a can
parlor.... Inna ta shigo masu dakin tana kallonsu tace "Yana nan har yanxu Ahmadu"
mikewa Mujaheed yyi ya saci kallon Imaan da har sannan ta kasa kwakkwaran motsi
kuma taki cewa komai ya fita dakin ya ga Abba tsaye bakin kofa, Yyi kasa da kai
kafin yace komai Abba yace "Where were you all this while??" A hankali Mujaheed
yace "Ina nan Abba...." Abba yace "mu je to" Inna ta dau Hijab ta nufi kofar xata
fita Abba yace "Ina kuma xa ki Inna" da mamaki tace "A'a ba magana xa ayi ba ya
sakar min jika, Ahmadu na fa ce maka yaron ya xo mana da Hadia jiya yana ta kuka
kamar xai mutu, nasan Hadiza ta gaya maka komai, wllh ba yin kansa bane kuma ko
waye yyi masa haka xa mu binciko in sha Allahu kashin ko ma waye ya bushe...." Abba
yace "A'a kiyi hakuri kiyi kwanciyar ki yanxu dare yyi, gobe da safe sai a xauna
kowa da kowa ayi magana a nutse" Inna tace "A'a da yanxu da goben ai duk daya ne
Ahmadu, ni dai gaskiya mu je ayi magana ayi ta ta kare yanxu, kada wani abu ya sami
Imaan kaga auren nan ba sonsa take ba" Da kyar Abba ya lallaba Inna a bari gobe da
safe ayi magana, shi dai Mujaheed na tsaye kansa a kasa amma gaba daya hankalinsa
na kan abinda yyi Imaan, shi kansa bai yi xaton xai iya hakan ba, Bai san lkcn da
yyi wani murmushi ba yana shafa kansa, muryar Inna ya ji tace "Kaga mahaukaciya ma
ya mayar da ni, dariya yake min ko Ahmadu, to wllh sai ya sakar min jika tunda ba
sonsa take ba baxa a mata dole ba" Abba yace "Allah ya kai mu goben" daga haka ya
kalli Mujaheed yace "Mu je" Mujaheed ya kalli kofar dakinta sannan ya bi bayan
Abba, slowly suke tafiyar yana gefen Abba, Abba yyi breaking silence din yace "You
are not happy with what I did koh Muhd?" Mujaheed ya kallesa murya can kasa yace
"Not at all Abba" Abba yace "Toh ina ka shiga kwana biyun nan" Mujaheed ya sunkuyar
da kansa yana murmushi yace "Ina gidan a bachelor frnd of mine, bana son tashin
hankalin gidan ne" Abba na gyada kai yace "Gaskiya ne, jiya Hadiza ta sameni ta min
bayanin yanda suka yi da yaron nan Sadeeq, kasan Hadiza ba komai take ba ma
listening ear ba, but tunda har ta sauraresa... sure da wani abu a kasa, Ur mum
isn't still okay with this Union, grandma din ka har yanxu ba mu gane inda ta dosa
ba gaskiya dama she has always been a confusionist, Hajiya Aisha bata gidan nan
yanxu haka all because ita ma bata son auren, I caused all this Muhd, kai ma ban yi
shawara da kai ba naji ra'ayin ka, so I think raba auren nan shi xai fi komai sauki
a gidan nan" sauraronsa kawai Mujaheed yake kansa a kasa, Abba na gyada kai yace
"Gobe da safe duk xa mu hadu, ita ma Aishar xa a kirata ta xo don a gabansu xa a yi
komai...." Shi dai Mujaheed bai ce komai ba har suka isa apartment dinsu, Abba yace
"You spend the night here sbda gobe da safe xa a kira meeting din" murya can kasa
Mujaheed yace "In sha Allah" daga haka Abba ya wuce parlonsa, Mujaheed ya wuce sama
walking gently. Daren ranan gaba daya bai yi baccin kirki ba, haka ma Imaan da kiss
din da ya mata ne ya tsaya mata cak a rai, da ta tuna sai gabanta yyi mugun faduwa
kuma sai ta mike xaune to calm her self down, ta goge bakinta ya fi a kirga amma
har lkcn ji take kamar it's happening fresh, ko Sadeeq da yyi mata wanda ya fi wnn
ma bata ji abinda take ji ba yanxu, da ta tuna Yaya ne yyi mata sai hankalinta ya
kara tashi ta fara hawaye, anya yayan da ta sani ne wannan kuwa, har xuciyarta taji
gaba daya tsoronsa ma take... Washegari misalin karfe tara na safe Ammi ta shigo
gidan ta dalilin kiran Gwaggwo da Abba yyi tun sassafe, Aunty na xaune parlon sai
Umma da duk ta fige damuwa yyi mugun mata yawa, amma da ta tuna Mujaheed ya dawo
kuma tana da yakinin yau xai yi saki sai ta samu relieve, Aunty suka gaisa da Ammi,
Ammi ta nemi waje ta xauna, Umma dai bata yarda ta kalleta ba, bayan nan Yusuf ya
shigo yana rike da makullin motarsa ya xauna ya gaida parent din nasa, Abba ya
shigo parlon tare da Daddy duk suka xauna, Daddy ya amsa gaisuwar Yusuf yana
tambayarsa matarsa, Kawu Bala ne next din shigowa nan kuma aka yi ta jiran Inna da
Imaan sai Mujaheed, Inna ta wangale kofa ta shigo, Imaan na biye da ita sanye da
hijab har kasa, kanta a kasa ta xauna kasa kusa da inda Inna ta xauna, Abba ya
gaida Inna Daddy ma ya gaisheta sannan kawu Bala sauran ma duk suka gaisheta, sama
sama ta dinga amsa gaisuwar tana kalle kallen inda xata ga Mujaheed, Imaan ta gaida
su Abba sannan ta gaida su Aunty, Umma dai ta ki yarda ta kalleta sai kallon kofa
take tana jiran shigowar Mujaheed dinta, Inna tace "Naga Ikon Allah, toh shi ina
mutumin yake, ni fa ban gama tsaftace bandaki na ba na yo nan gaskiya Ahmadu...."
Bude kofar parlon aka yi Mujaheed ya shigo suka hada ido da Imaan da ke kallon
direction din, da sauri ta sunkuyar da kai gabanta na faduwa ta matsa kusa da Inna
kamar irin xuwa yyi ya dauketa, sanye yake cikin kananun kaya ya sauke kansa kasa
bai yarda ya kalli kowa parlon ba ya karasa kusa da Yusuf ya xauna sannan ya gaida
occupant din parlon kansa a kasa, Shiru ne ya biyo baya a parlon, Umma dai sai
kallonsa take ganin wani fresh da yyi abun sa, hakan yasa ta kara jin hankalin ta
ya tashi, wato bai damu ba kenan??? kawu Bala ya bude wajen da addu'a sannan ya
kalli Abba, Abba ya sauke boyayyen ajiyar xuciya calmly yace "Abubuwa da dama sun
faru tun bayan wannan aure da na hada ba tare da shawara da kowa ba few days ago,
domin haka nake mai kara ba ma kowa a parlon nan hakuri bisa bacin rai da aka shiga
da dai sauran su, to bayan wannan ina son jin views din ku a parlon nan akan auren
nan kafin mu san abun yi, Ni da Sadeeq da Bala ba mu da abin cewa tukun sai mun ji
naku ra'ayin in sha Allah, but before then... jiya Hadiza ta xo min da wani batu da
yake bukatar a duba sa sosai...." Inna dai sai girgixa kafa take, Abba na kallonta
yace "Inna xa mu so mu fara jin ta bakin ki a kan auren Imaan da Mujaheed da na
hada...." Inna ta katse sa da sauri tace "Me kuwa xan ce Ahmadu, ka ji ta bakina
kamar Yaya? wllh Imaan bata son auren nan don ma ka ji, da a shiga hakkinta fa? Tun
xamanin kakannin mu aka daina auren dole, toh tunda ta ce bata so gaskiya ni ban ga
amfanin auren ba, kada in je in rasa ta a banxa, yanxun nan ya rubuta mata saki ta
san inda dare yyi mata, amma gaskiya ba wai bana son auren bane tunda duk jikokina
ne, to da wani abu ya samar min jika fa? Ko bacci fa bata yi bata cin abinci, A'a
wllh ba ruwanaa" Mujaheed dai sai kallon Inna yake kasa kasa, Umma taji kamar ta
goya Inna don murnan furucin ta, Mama Hadiza dai ko kallon Inna bata yi ba sanin
awa daya yyi kadan tace ai bbu auren da ya fi na Imaan da Mujaheed daraja a duniya,
Abba ya sauke ajiyar xuciya ya kalli Mama Hadiza yace "What did you think Hadiza?"
Mama Hadiza ta d'an yi shiru sannan cikin sanyin murya tace "Barrister in har su
yaran basu son auren nan abu mafi sauki da kwanciyar hankali shine a raba, xumunci
ba abun wasa bane, kada wnn aure ya 6ata xumunci gaskiya...." Abba ya gyada kai
cikin gamsuwa bai dai ce komai ba, can ya kalli Umma yace "Meye ra'ayin ki
Rukayya?" Umma ta fara matsar kwalla tace "Ba shi da fa'ida auren nan Alhaji, ita
yarinya ba so take ba uwar yarinya ba so take ba, toh wani aure kuma Allah na
tuba...." Abba yace "Ke ma kuma ba so kike ba koh?" Umma dai bata ce komai ba sai
matsar kwalla take, a hankali tace "Alhaji raba auren nan shine kwanciyar hankalin
kowa..." Abba ya kalli Aunty yace "Amina ur view?" Aunty ta sauke ajiyar xuciya
tace "Duk yanda Allah ya tsara dai dai ne Alhaji, in barin auren in kuma raba
auren..." Abba ya kalli Yusuf yace "Engineer..." Yusuf ya d'an yi murmushi bai ce
komai ba, Abba ya kalli Imaan da kanta ke kasa yace "Mamana baki son auren nan ko?"
Ta fashe da kuka kamar jira take ta gyada masa kai tana shessheka, Abba ya kalli
Ammi yace "Hajiya Aisha??" Ammi ta kallesa tace "Gwara raba auren Barrister...."
Abba ya kalli Mujaheed yace "M.A...." Mujaheed ya kallesa, ya d'an yi shirun kusan
second biyar sannan yace "Baxan iya sakinta ba Abba...." Duk aka xaro ido a parlon
ana kallonsa, Imaan ta fashe da matsanancin kuka ta fada kan Inna da ta hangame
baki tana kallon Mujaheed ita ma, Abba na kallonsa kamar yanda Daddy ma ke kallonsa
yace "Ko saboda me?" Mujaheed ya sunkuyar da kai a hankali yace "Saboda ina son
kasancewa tare da ita...." Umma ta fashe da kuka kamar yar yarinya tace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, kana son kasancewa da ita fa kace Mujaheed?
Ita Safeenar fa???" Abba dai ya kasa cewa komai sai kallonsa yake, Inna tace "Ehh
lallai lalacewa ya tabbata a duniya, Innalillahi wa inna ilaihi raji'un..."
Mujaheed yyi kasa da murya yace "Ku yi hakuri Abba ni baxan iya sakin Imaan ba..."
Daga haka ya mike ya fice daga parlon, kawu Bala ya sauke ajiyar xuciya yana gyada
kai yace "Allah sarki..." Inna ta mike ta fashe da kuka tace "Ahmadu duk kai ka ja
mana wannan bala'in muna xaman xaman mu, kawai ka tashi sbda tsautsayi ya afka ma
bawan Allah Sadeeq ka daura ma mahaukaci aure da jikata, wllh Mujaheed ya fara
haukacewa banda haka ko kunya babu yace baxai saketa ba yana son kasancewa da ita,
to tayi masa uban me idan sun kasance tare, ai ni naga abinda ya isheni bai ishi
Allah ba, amma ba komai da kansa xai gaji ya saketa don wllh Imaan baxata tare
gidansa ba, to ta tare tayi masa uban me?? Wllh ta kwaso kayanta gaba daya ta dawo
bangarena ni ban yadda da auren ba, dama dai Sadeeq bai dawo bane sai in hakura ta
tare gidan Mujaheed din, amma bawan Allah ya dawo kuma yace baxai iya sakinta
ba...." Tana fadin haka ta daga imaan dake kuka kamar ranta xai fita suka bar
parlon, Ammi ta share hawayen idonta ta mike ta fita parlon Aunty da duk jikinta
yyi sanyi ta mike ta bi bayanta, Mama Hadiza ta sauke ajiyar xuciya tace "Toh Allah
yasa barin auren shine mafi alkhairi" a hankali Daddy ya amsa da "Ameen" shi dai
Abba ya kasa cewa komai, Umma da ta sakko kasa tana kuka sosai tace "Toh Alhaji ya
xa ku yi da yaron da naji ance ya dawo???? An fa ce ba yin kansa bane, don Allah ku
duba lamarin nan kada ku xama kananun mutane" Kawu Bala yace "Sae yayi hakuri,
Imaan ta masa nisa, ita din matar aure ce yanxu" Umma ta mike tana kuka sosai ta
fita waje da sauri ko xata ga Mujaheed amma babu shi babu alamarsa. Mama Hadiza ce
ta kira Sadeeq ta sanar masa ya xo bayan ta amshi lambarsa gun Yusuf, suna xaune
parlon Abba har lkcn sai ga shi, Kallonsa kawai Daddy yake don ba karamin ramewa
yyi ba, duk ya fice hayyacin sa, a sanyaye ya xauna parlon ya gaishe su gaba daya,
duk suka amsa suna kallonsa, cikin raunanin murya ya fara basu hakuri yace "I don't
know what came over me Abba, wllh ba halina bane, don Allah ku yi hakuri ku yafe
min, I am ready to marry Imaan now, Kar kuce xa ku raba ni da ita don Allah, wllh
baxan iya rabuwa da ita ba...." Hawaye cike idonsa ya kare maganar, Kawu Bala yace
"Sadeeq komai ya faru a rayuwa rubutattce ne daga Allah, Allah kuma ya kaddara
Fatima ba matar ka bace, don yanxu haka maganar da nake maka Fatima matar aure
ce...."
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

Sadeeq ya daga kai a hankali yana kallonsa xuciyarsa na bugawa, double ya dinga
ganin parlon daga nan kuma bai kara jin komai ba bai kara ganin komai ba a
parlon.... Tun da Inna taji abinda ya faru da Sadeeq tayi kukanta mai isarta ta
buga ma ta Rasulu waya taji ko xata xo ranan, ta Rasulu tace "Ai ki bari Asabe
maganar babba ce, in sha Allahu gobe da sassafe xan shigo nima yanxu na dawo garin
wllh" Inna na matsar kwalla tace "Toh sai kin xo, don ba lafiya ta Rasulu" daga
haka ta kashe wayar ta ajiye tace "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un, Allah ka
rufa ma Rukayya asiri ya kasance bata da hannu a abubuwan dake faruwa, idan ko ba
haka ba sai dai wata ba ita ba a gidan nan...." Imaan dai na kwance kujera tayi
lamo, tunda taji abinda ya faru da Sadeeq kuma wai suna asibiti take kuka, da ta
tuna furucin Mujaheed sai taji gabanta yyi mugun faduwa jikinta yyi sanyi, Inna
tace "Na fa ce ki kwantar da hankalin ki sai dai Mujaheed yyi ta yawo da auren ki a
kansa amma har abada ke da tarewa shegen gidansa, to ki tare kiyi masa me a gidan,
ko kuma yyi maki me Allah na tuba? Da kansa xai gaji ya kawo maki takardar ki ya
bamu hakuri" ita dai Imaan bata ce komai ba tana jin xuciyarta ja mata xafi. Abba
ne tsaye ward din da Sadeeq yake tare da Daddy sai Alhaji Bulasawa da wani frnd
dinsa, Alhaji Bulasawa na tsaye kan Sadeeq sai kallonsa yake duk da bacci yake,
kana ganin Alhaji kasan kasan damuwa ne sosai tare da shi, Can ya juya ya kalli
Abba a karo na farko tun shigowarsu yace "Alhaji can you pls do something about
this pls, I don't want anything to go wrong with my son, and yana da matsalar
xuciya dama from the beginning, though it's not critical but the condition he is
now can make it, don Allah ina bukatan taimakon ku ba wai don na isa ba, ku duba
wannan lamarin" Da damuwa sosai yyi maganar, Abba dai kallonsa kawai yake ya kasa
cewa komai, Daddy ya ja kujera ya xauna ya jinginar da kansa hade da lumshe ido,
Abba ya sauke idonsa yace "In sha Allah xa a duba ka kwantar da hankalin ka
Alhaji...." Alhaji Bulasawa yace "Toh na godiya" Mummy ce ta shigo ward din tare da
Mum din Mariya, ganin Sadeeq ta fara kuka ta ki karasawa ciki, mum din Mariya ta
karasa a sanyaye tana kallon Sadeeq din.... A haraban hospital din Abba ya kira
layin Mujaheed to see if he can reach him, luckily kuwa ya shiga, Mujaheed na
dagawa Abba yace "Muhd Ina son ganin ka a gida yanxu" Mujaheed ya d'an yi shiru
sannan yace "Ina Zaria yanxu Abba, da Magrib xan shigo" Abba yace "Am expecting
then" daga haka ya katse wayar ya xauna saman kujera yana kiran Allah a xuciyarsa,
Mujaheed ya d'an yi murmushi ya ci gaba da abinda yake a office dinsa. Da daddare
Imaan na parlor xaune ta sa pepper soup din da Aunty tayi mata a gaba amma ko spoon
daya bata kai baki ba, Inna na bathroom dinta tana aikin wankewa tunda daxu da safe
bata samu ta wanke ba, Bude kofar parlon aka yi Imaan ta daga kai da sauri Mujaheed
ya shigo, tashi tayi kamar warce aka tsikara xata gudu yyi maxa ya rikota, ta fashe
da kuka jikinta na rawa tace "Yaya don Allah ka bari bana so..." Ya juyo da ita
yana kallonta, ganin yanda hawaye ke xuba idonta ya xaunar da ita ya xauna gefenta
a hankali yace "Listen to me now Imaan..." Taki yarda ta kallesa har sannan jikinta
rawa yake, murya can kasa yace "Kema kina son in sake ki koh?" Ta kallesa ta fashe
da matsanancin kuka tana gyada masa kai, shiru yyi na kusan second goma, a hankali
yace "Toh shikenan tunda haka kike so, but I don't have paper and pen here, mu je
waje sai in dauka a mota in rubuta takardar in baki..." Daga haka ya mike, ita dai
tayi shiru tana kallonsa amma hakan bai sa ta daina hawaye ba, ya kalleta yace "Toh
mu je mana, ba dai haka kike so ba??" Mikewa tayi a hankali ta dau Hijab dinta ta
saka sai kuma ta tsaya, yace "Mu je...." slowly ta fara tafiya ya bi bayanta yana
murmushi, ita dai Imaan tafiya kawai take yana biye da ita yana kallonta har ta
fita gate, satan kallon part din su yyi sannan ya fita gate din shi ma.....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

82.....

Imaan ta tsaya jikin motar sai dai bata yarda ta kallesa ba, ta gefen ido ya dinga
kallonta ya bude driver seat ya dauko takarda da biro, jinginar da takardar yyi
jikin motar ya fara rubutu a kai, satan kallansa tayi ganin rubutu yake kan
takardar ta ji gabanta ya fadi, lkci daya ta sunkuyar da kanta tana jan fingers
dinta, ya gama rubutu a takarda ya linke yana kallonta yace "Hope you are now
happy?" Bata yarda ta kallesa ba ta gyada masa kai kawai, ya d'an yi shiru sannan
yace "But I want to let you know one thing Imaan before handing this paper over to
you" ita dai kanta na kasa, jin yyi shiru bai fadi one thing din da yace xai gaya
mata ba ta kallesa taga kallonta yake, da sauri ta sauke kanta kasa xuciyarta na
bugawa, ya bude motar ya shiga a hankali yace "Xagaya ki shigo ki ji abinda xan
gaya maki..." Ta girgixa kai tace "Ka gaya min a nan" yace "I want to say it while
looking at u in the eyes, so that baxai yi fading memory din ki da wuri ba, ko da
ba ma tare you won't forget it Imaan, it's almost a piece of advice..." Ta hade rai
tace "Ni dai ka bani takardar in wuce" ya girgixa kai yace "Baxan baki ba idan baki
shigo kin saurareni ba, I assure you wannan maganan da xan maki wataran xai maki
amfani" Kallonsa tayi sai dai bata ce komai ba, kuma bata xaga ta shiga motar ba,
yace "Duk lkcn da kika shirya jin abinda xan gaya maki I will give you ur divorce
content, but not today anymore..." Daga haka ya ja kofar motar xae rufe, ta fashe
da kuka ta rike kofar da sauri tace "Toh ka rubuta min abinda xaka gaya min a wani
takardan ka bani gaba daya mana" Ya wani hade rai yace "Cinye ki xan yi idan kika
shigo motar? Kinsan Allah baxan baki takardan nn ba idan baki shigo kin saurareni
ba" Dauke kai tayi kamar me naxari sai kuma ta xaga a hankali ta isa daya side din,
d'an murmushi yyi ya rufe side dinsa ya jinginar da kansa da kujera, tana xagayowa
ta bude front seat ta shiga ta xauna ta d'an saci kallonsa taga murmushi yake,
still tayi da farko, sai kuma ta sake kallonsa, lkci daya ta yunkura xata sauka
motar ya wani fixgota ya jawota ya rufe kofar gbam ya sa ma motar lock, a mugun
tsorace ta dinga jijjiga kofar tana cewa "Meye haka Yaya??" Bai ko kalleta ba ya
tada motarsa ya bar layin, kuka ta dinga yi tana kallonsa a rikice tace
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Yaya don Allah ka bari, where are you taking
me to, plss ka tsaya ka bude min mota in sauka, wayyo innaa...." Driving kawai yake
bai ko kalleta ba, ta fixgosa cikin kuka tana jijjigasa tace "Don Allah ka bude min
in sauka Yaya, ina xaka kai ni??" da hannu daya ya mayar da ita kan kujera ya wani
hade rai ba tare da ya kalleta ba idonsa a kan titi yace "Kika sake rikeni sai na
falla maki mari..." Ba karamin tsorata tayi ba jin babu wasa tattare da shi, hakan
yasa bata sake rikesa ba ta dinga kuka tana kiran Inna tana bubbuga kujeran motar,
Sun yi nisa sosai ya daura mata well folded takardan hannunsa kan cinyarta yace "As
I promised, here is it...." Kuka kawai take tana kallonsa kamar ranta xai fita,
yace "Dauki takardan ki bude ki karanta, ba saki kike so ba, to gashi na rubuta
maki" kin ta6a takardarn tayi, ya juya ya kalleta fuskar daure, da sauri ta dau
takardan hawaye na xuba idonta tana shessheka, yace "Open it now" hannunta na rawa
ta fara warware takardan tana kallon abinda ya rubuta kamar hakw.... "Xan sake ki
on one condition, the condition is... Xa ki haifa min yara guda biyar duk masu kama
da ke, duk yaron da yyi kama da ni bbu shi a cikin lissafin, just 5 of ur look
alike...." Ji tayi gabanta yyi wani mugun faduwa ta sake takardar tana kallonsa,
wani murmushi yyi yana kallon titin gabansa yace "Yes... Sai ki shirya conceiving
daga daren yau" ta hade kai da gwiwa ta fashe da kuka da karfi tana kiran Inna,
driving kawai yake yana murmushi, wani hotel ya kai su, yana parking harabar hotel
din ya juya yana kallonta, har lkcn kuka take sosai, ya bude motar ya fita ya
xagayo ta inda take ya bude seat din yana kallonta yace "Come down..." Kin dago
kanta tayi bata kuma fasa kukan da take ba, xaro ido tayi ta dago da sauri jin
daukarta xai yi ta hadiye kukan da take cikin rawar murya tace "Wllh xan sakko
Yaya, wllh xan sakko" Ya daure fuska yace "To sakko" ta hadiye abu da kyar ta fito
motar tana shessheka tana bin haraban hotel din da kallo gabanta na bugawa tayi
kasa da murya pleadingly tace "Don't Forget from the beginning kai ka koya min
daukan ka matsayin yayana, kar ka manta a matsayin Yaya na dauke ka tun ban san kai
na ba, why will u bring me to a hotel all of a sudden plss?" Yace "To show u ni ba
yayanki bane, and after today I don't think xa ki kara kirana yayan ki" xaro ido
tayi tana kallonsa, ya kulle motar xai kama hannunta ta fixge da sauri ta kara
fashewa da kuka, kallonta ya tsaya yi sai kuma yace "Daukar ki kike son inyi kenan
koh?" Ta girgixa masa kai cikin tashin hankali tace "A'a yace "To mu je" tafiya ta
fara yi toward direction din entrance din hotel din yana biye da ita, tana waigowa,
he couldn't just stop smiling, amma da ta juyo sai ya hade rai, kujera ya nuna mata
bayan sun shiga reception din hotel din yace "Sit" kin xaunawa tayi tana hawaye, ya
kama hannunta ya tafi da ita gun kujerar ya xaunar da ita yana kallonta, hade kai
da gwiwa tayi tana jin kamar ta kurma ihu ko xata ji dadi, ya juya ya koma gun
ma'aikatan babban hotel din, bayan kusan minti goma ya dawo inda take ya duka dai
dai kanta yace "Tashi mu je...." Ta daga kai da sauri cikin rawar murya tace "Don
Allah Yaya kayi hakuri ka mayar da ni gida Ina rokon ka don Allah ba don ni ba"
D'aga ta yyi ya kama hannunta suka wuce sama xuwa room din da aka basa don kar ma
ta ja masa attention din mutane, a door ta tsaya bayan sun shiga ciki, ya kulle
kofar ya cire makullin jiki yana kallonta calmly yace "Ke da gida kuma sai deal din
mu ya tabbata, I mean 5 kids...." Durkusawa tayi on her kneels tana kuka sosai tace
"Don Allah ba don ni ba ka mayar da ni gida Yaya xa a dinga nemana fa" Ya durkusa
gabanta shi ma a hankali yace "A neme ki bayan kina tare da mijin ki??" Kallonsa ta
dinga yi ko kiftawa babu kamar yanda shi ma yake kallonta... Inna ce xaune parlon
Daddy ta yafa xaninta a kai, kai kace bayerabiya ce, fuskar nan nata a tsuke, Daddy
da shigowarta parlon tana rafka uban sallama ya sa ya fito daga daki ya xauna yana
kallonta yace "Ina yini Inna?" Ta kallesa tace "Lafiya lau Bukar... Kana ji na??"
Daddy yace "Ina jin ki?" Tace "Toh... Ka san dai ni na haife ka, kai kuma ka haifi
Imaan koh??" Shiru Daddy yyi bai ce komai ba, a fusace tace "Ka min shiru Bukar ko
ba haka bane?" Yace "Haka ne" tace "To madalla, Bukar yau da ba don kai ba wllh ba
bbu uwar da na hada da wannan yarinya Imaan, kawai ni dai nasan na haifeka kai kuma
Allah ya baka ita, to ya xan yi tunda d'an da na haifa ya haifeta, ya xan yi
nace??" Shi dai Daddy kallonta kawai yake, Rai bace ta ci gaba "Yanxu ace Imaan
xata bar bangarena baxata jira in gama tsafatace bandakina in fito ba tace min to
Inna ni na tafi? sbda walakanci sai ta tsallake kamar tababbiya tayi wucewarta ga
farfesun da wannan mata Amina tayi mata ta bar min shi a bude a parlor duk dattin
duniya ya fada kai, sannan ta bar min kofa a bude domin ba ma sauro daman shigowa
su cuce ni, wllh raina yyi mugun bacewa don ni ba haka na ma Iyayena ba kai ma kuma
ba haka ka min ba, to wacece kuma imaan fisabilillahi xata min haka, a wangale fa
ta bar min kofar Bukar kaji abinda yafi min ciwo kenan, ni nace lallai dole sai
Imaan ta xauna bangarena dama?? To wllh ta fito ta tafi ta kwashe tsummokaranta
dake kwambodi na kada in watsa su titi ba ruwana, ni xata kawo ma raini ta
walakanta, dama tun da yamma naga take takenta, Banda Ahmadu da ya jaza mana wnn
bala'i na aura mata katon d'an sa uban me dama xan ci da ita a sashina??" Daddy
dake ta kallonta yace "To ai bata xo nan ba..." Inna tayi shiru ta kalli kofar
dakinta, sai kuma tace "Bata nan kuma?" Daddy yace "Bata xo nan ba" mikewa Inna
tayi da mamaki ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fita, part din Abba ta wuce,
tana daga tsaye bakin kofa tana kallon Aunty da ta mike ganinta tace "Amina
yarinyar nan bata yo nan ba?" Aunty tace "Wai imaan?" Inna tace "ita" Aunty tace
"A'a bata xo nan ba gaskiya" Inna ta gwalo ido ta shigo parlon da sauri tace "Bata
xo ba kuma Amina?" Jin muryar Inna Abba ya fito daga parlonsa, Inna ta nufe sa da
sauri tace "Ahmadu ban ga imaan ba tun daxu wllh" Abba yace "Imaan kuma?" Inna da
har jikinta ya fara rawa tace "Ehh na shiga wanke bandaki na fito naga babu ita a
parlor sai farfesu" Su Maimoon suka fito tare da Maryam da tayi hijira bangaren
Inna tun ran Friday, Aunty na kallonsu Maimoon tace "Ku tafi can apartment dinsu ku
duba ko tana can" fita suka yi parlon gaba daya, Abba na kallon Inna ganin yanda ta
rikice yace "Bari a dubota can bangaren su, amma ina xata je dama Inna" Inna ta bi
bayansu Maimoon da sauri, tana tsaye bakin kofa sai xaxxare ido take tana jiran
fitowarsu, Maimoon ce ta fara fitowa tace "Bata nan fa Inna" Wani salati Inna ta
rafka da karfi sai kuma ta fashe da matsanancin kuka tace "Innalillahi wa inna
ilaihi raji'un, bata ciki fa ku ka ce???" Su Abba da Aunty duk suka fito tsakar
gida Mama Hadiza ma ta fito bayan Maryam ta je sama ta gaya mata abinda ke faruwa,
Daddy dai na tsaye balcony dinsa yana kallon mahaifiyar tasa, Inna ta tsaya dai dai
tsakar compound din ta daura hannu a kai ta dinga rusa kuka tana cewa "Na shiga uku
Allah ka dubeni kada Bukar ya kullace ni har gobe kiyama, Ina imaan xata shiga da
tsakar daren nan jama'ah, wllh wanke bandaki nake na fito naga babu ita sai kwanon
farfesunta, na shiga uku jama'a ku taimakeni kada a dinga cewa a parlona Imaan ta
6ata...." Mama Hadiza ta nufe ta da sauri tace "Haba Inna meye haka kuma, ce maki
aka yi Imaan din 6ata tayi? Haba don Allah" Cikin kuka Inna tace "Idan ba 6ata tayi
ba to Ina take Hadiza?? Kafff gidan nan an duba bbu ita babu alamarta fa, Wllh da
ba a bangarena take ba bbu abinda
xai dameni sai dai a daure Ahmadu tunda shi yyi mata auren dole, yanxu kuwa ai ni
xa a daure tunda kowa yasan a bangarena take, da wani bakin xan ma 'yan sandan
bayani idan an tafi dani?? Kuma duk aka tashi magana dama cewa xa ayi parlon Inna
ta 6ata, to ina dalili a sa ni a bakin duniya Hadiza???? Don Allah ku min rai a
nemo ta kada in shiga uku, wannan ba karamin magana bane wllh" Ta kuma rushewa da
kuka har da durkusawa kasa tana salati, Abba dai ya kasa cewa komai haka ma Daddy
da ya makale a Balcony dinsa, Inna ta kara mikewa tana kuka sosai ta nufi gate tana
cewa "Duk Ahmadu ne ya jaza mana fitinar nan gaskiya idan wani abu ya sami jikata
xan rufe ido in mance ni na haifeka Ahmadu" Umma da shigowarta gidan kenan daga
gidan Hajiya Saude ta makale parking space tana wurwurga ido jin wai ba a ga Imaan
ba, Inna na kallon mai gadi a waje ta fixgosa tace "Ilu kaga fitar Imaan?" yace
"A'a ban gani ba Baaba..." Inna ta wani xaro ido ta turasa kawai ta fice gate din
ta saka kai gaba sai babban titi tana salati tana rusa kuka, Mama Hadiza ce ta bi
ta tana kiranta amma Inaaa... Karfe goma saura Mujaheed ya mike daga xaunen da yyi
gefen gado tun shigowarsu yana kallon football a tv na bango dake manne a dakin
hotel din, Imaan dai har lkcn tana durkushe inda take tun daxu, banda axaban ciwo
babu abinda kanta da duk joints dinta suke mata amma ko xama ta ki yi, ga kuma
bacci dake fixgarta, ta dai gaji da kuka da rokonsa da take tayi tsit ta xuba ma
saurautar Allah ido, satan kallonta Mujaheed yyi ganin idonta a lumshe bacci ya
dauketa a yanda take, ya dau remote ya kashe tvn ya mike a hankali ya nufeta,
dukawa yyi ya dagota ta farka a rikice xata fasa masa ihu ya rufe bakinta a
jikinsa, jikinta ya dau rawa tana kokarin kwace kanta bai ajiyeta ba sai saman
gado, xata mike ya hade rai, calmly yace "Lie still..." Kai kawai take gyada masa a
tsorace, ya dinga kallonta ko kiftawa babu, kamo hannunsa tayi tana girgixa masa
kai pleadingly tace "Don Allah Yaya ka maida ni gida kila ana ta nemana wllh" Ya
xame hannunsa still looking at her yace "Kila don kina ganin ki a kadunan yasa kike
tunanin xan maida ki gida, Allah ya kai mu gobe da safe, I will eraze that thought
off ur mind" Ta dinga kallonsa xuciyarta na bugawa, mikewa yyi ya nufi switch din
dakin ya kashe wutan, ta mike xaune da sauri gabanta na faduwa tana kallonsa cikin
duhu, a hankali tace "Yaya..." D'an Murmushi yyi ya nufi kan gadon, tuni ta sauka
ta tsaya tana kallonsa cikin duhun xuciyarta na bugawa....

*Naji kuma xan iya, though it's short... Thanks for the prayers*
*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

83......

Mujaheed bai yarda ya kalleta ba ya ciro wayarsa a aljihu ya xauna saman gadon ya
kunna wayar, ita dai tana tsaye tana kallonsa gabanta na faduwa, number yyi dialing
ya jingina da gadon, Safeenah dake kwance saman gadon hajiyarsu an cire mata drip
kenan har ta fara bacci ta mike xaune da kyar tana kallon wayarta dake gaban mirror
yana ring, Hajiya Baturiya tace "In ma xa ki rabu da wayar nan kiyi baccinki ki
rabu da shi..." A hankali tace "Toh idan shine fa Anty?" Hararanta Hajiyan Marafa
ta dinga yi daga inda take xaune, yayarta Sajida tace "Wlh idan kika ja ma kanki
wani ciwon Safeenah iyaka namu muyi ta maki fatan samun lafiya, me aka yi aka yi
Mujaheed da xa ki nemi hallaka kan ki a kansa? Mutumi da har yau bai kira ki ba
balle ki san abinda ake ciki, wa ya sani ma ko da saninsa aka yi auren ma tunda
uwarsa ce kan komai" Safeenah ta kalleta da sauri tace "A'a wllh bai san da auren
ba, nasan shima hankalinsa ne ya tashi shi yasa muka ji sa shiru" Hajiyan Marafa
tace "Na rasa wannan bala'in ni dai, haka kawai ki dauki namiji ki sa a rai kina
neman ja ma kanki wani ciwon??" Safeenah ta sauka saman gadon da kyar ganin basu da
alamar dauko mata wayar, tana isa gaban mirror din ta xaro ido tana kallon wayarta
tace "Wllh shi ne Mummy..." Da sauri ta daga wayar kafin ya katse ta kai kunne,
kawai sai ta fashe da kuka sosai, Mujaheed yyi shiru yana sauraronta na few
seconds, can yace "Let me assume baki son kiran nawa kenan..." Da sauri tace "Me
yasa ka kashe wayar ka all this while Mujaheed, me yasa baka yi tunanin halin da
xan shiga ba a wannan lokacin, don Allah ka ce min karya ne baka min kishiya ba,
kace min karya ne ni kadai ce matar ka Mujaheed, I can't imagine my self sharing
you with any lady wllh baxan yarda ba, ni ce kadai matarka a duniya" Ya daura kansa
saman pillow dake kusa da shi yyi kasa da murya yace "Yanda kika samu labarin auren
nan haka nima na samesa Safeenah, I know nothing about it, ban san komai a kan
auren nan ba..." Kuka take sosai tace "Wllh Mujaheed na isheka duniya da lahira me
xa kayi da wata matar kuma, kayi min rai kada ka min kishiya, ka barni ni kadai a
gidan ka, na isheka duniya da lahira, don Allah kace min babu xancen auren nan kuma
plsss..." Bai san lkcn da yyi murmushi ba a hankali yace "Marriage or no marriage
Safeenah you still remain my first, ke ce matata ta farko, then why worry?" Imaan
dake tsaye tana kallonsa tunda ta fahimci da warce yake waya ta wani daure fuska ta
juya masa baya tana jin wani irin haushi a xuciyarta, kuka kawai Safeenah take
kamar ranta xai fita tace "Kana nufin da gaske kenan auren na nan Mujaheed, Kuma
wai da cousin dinka da ta raina ni?? Nooo plss wllh baxan iya sharing mijina da ita
ba, I can never, you are meant for me alone, tell ur parent u don't need a second
wife plss, ban rage ka da komai ba..." Murmushi yyi sosai yace "Thank God you know
I don't need a second wife, then why disturb ur self?? I just have to obey my
parent that's all" Juyowa Imaan tayi a hankali tana kallonsa, yace "I will call you
tomorrow, get set before 9:00am xan xo" daga haka ya katse W
wayar yana satan kallon Imaan, missed calls din Mama Hadixa ya gani kusan shidda,
tun yana waya yake jin shigowar kiran nata, murmushi yyi ya shiga gun text message
ya tura mata text kamar haka, "Am sorry I did what is wrong Mama, but I think this
the only way out don baxan iya sakin Imaan ba" yana tura mata ya kashe wayar gaba
daya yana kallon imaan dake tsaye har lkcn tana kallonsa, kwanciya yyi saman gadon
ya lumshe ido, ta goge hawayen dake sauka idonta har lkcn tana kallonsa, da ta tuna
abinda yace ma Safeenah sai taji wasu hawayen sun taho mata, tana ta tsaye har
bayan kusan minti talatin, jin kafafuwanta sun gaji ga bacci da ta fara ji ta
durkusa a hankali tana ta6a tiles din dakin taji sanyi, ta dauke hannunta ta mike
tsaye tana kallonsa, bayan kusan minti biyu ta xauna gefen gadon a hankali tana
satan kallonsa, jin bai motsa ba duk da ba ganin fuskarsa take ba ta gane kilan yyi
bacci, kamar me tsoron gadon ta kwanta a edge ta juya masa baya ta rufe ido, a
hankali ya juya yana kallonta bayan few minutes, mirginawa yyi side dinta, cikin
bacci kawai taji sa kusa da ita, Bude ido tayi a tsorace xata mike ya riketa, cikin
rawar murya tace "Wayyo Yaya plss ka bari, meye haka" yace "Waye yayanki?" Jikinta
ya dau rawa tana girgixa kai tace "Ba kowa wllh" yyi kasa da murya drawing her
closer to himself yace "Who am I to you now?" Hawaye ne ya shiga sakko mata ta ki
cewa komai, ya daura forehead dinsa kan nata ta rufe ido da sauri, yace "Talk to me
now" a hankali tace "Yaya kai na fa ciwo yake min da bayana tun daxu...." ya
kwantar da kanta a hankali kan chest dinsa cikin sanyin murya yace "Tell me... Me
yasa kike son in sake ki bayan destiny da ya hada mu Imaan? Baki tunanin kilan dama
we where meant for each other, isn't this great? everything just happened all of a
sudden, so fast, baki tunanin wannan wani al'amari ne babba, why kike so na sake
ki?" wasu hawaye masu xafi suka dinga xubo mata ta lumshe idonta ta ki cewa komai,
a hankali yace "Talk to me pls" ta bude idonta tace "Saboda kai na dauke ka a
matsayin yayana ne..." ya d'an yi shiru sannan yace "Kenan ba aure tsakanin mu?" Ta
girgixa kai cikin rawar murya tace "Akwai...." Yace "Toh me yasa kika bar sa a
matsayin babu a xuciyar ki?" Tace "Saboda Ina maka kallon yayan da muka fito ciki
daya, I grew up looking at u as my blood brother, I've neva tot of living together
with you as..." Sai kuma tayi shiru, ya d'an yi murmushi yace "Ni kuma ban taba
maki wannan kallon ba, Ina maki kallon cousin dita ce da xan iya aure ta haifa min
kyawawan yara masu shagwaba da son jiki irin nata, masu dogon hanci da karamin baki
irin nata, masu asthma da ....." Dukansa ta yi a kirji kamar xata yi kuka tace "Ni
bana sooo...." Yana murmushi ya rungumeta sosai cikin sanyayyan muryarsa yace "In
sha Allah our kids will be more than healthy..." ta dago da sauri ta kallesa tace
"Ni fa baxan xauna da kai ba as my husband, I just can't... Bayan ga matarka da ka
gama ce ma kai baka son auren" Kallonta kawai yake ko kiftawa babu, xuciyarsa ya
dinga raya masa yyi mata abinda yyi parlon Inna jiya amma kuma kawai sai ya ji
nauyin yin hakan, saketa yayi, yyi kwanciyarsa yana murmushi yana tunanin ranan da
xai nuna mata shi ba yayanta bane, soon but not in a hotel room, xamowa kasa tayi,
tana turo baki tana kallonsa, daga karshe dai ta duka nan kasa ta kwantar da kanta
saman gado a haka bacci ya dauketa, mikewa yyi jin alamar tayi bacci ya xaga ya
dagata sama ya kwantar da ita saman gadon ta riko hannunsa cikin muryar bacci tace
"Yaya I am feeling cold..." kwanciya yyi kusa da ita ta shige jikinsa, yyi murmushi
yana kallonta ya cire mata hijab din jikinta keeping her more closer to himself,
gaba daya scent dinta ya cikasa, ya lumshe ido trying to force him self to sleep,
but the thought of imaan by his side, sooo close... as his sunnatic wife couldn't
let him, gashi da yyi yunkurin gyara kwanciyarsa just to maintain sai ta kara shige
sa, and he wish everyone was happy with this surprise marriage, da ya fi kowa murna
da farin ciki a duniya, duk ya tuna Ummarsa sai ya ji gabansa ya fadi, don tun da
aka daura auren bai yrda ko na second daya sun hadu ba. Sai kusan karfe biyu da
wani abu na dare bacci ya daukesa, duk da sanyin da yyi yawa a dakin bbu me jin
hakan a cikinsu.... Da asuba kiran sllh ya farkar da Mujaheed, ya kalli Imaan ya
gyara mata kwanciya xai mike ta rikosa, kunna kananun wutan dakin yyi yana kallon
fuskarta yaga bacci take, xai tashi ta kara rikesa, murmushi yyi ya ja dogon
hancinta hakan yasa ta bude ido a hankali, ya kai hannu goshinta ta wani hade rai
tana kallonsa ta mirgina da sauri daga wajen, sauka yyi saman gadon ya shiga
bathroom, tashi tayi ta jawo hijab dinta ta saka ta kashe Ac din dakin ta koma can
karshen gadon ta kwanta tana tunanin lkcn da ta hau saman gado ta kwanta, yana
fitowa ya kalleta yace "Baxa ki yi sllh ba" shiru tayi bata ce komai ba fuska
daure, ya fita dakin, sai a sannan ta mike ta wuce bathroom din, har ya dawo
masallaci tana xaune saman darduman da ta gani a dakin tana azkar, ya xauna gefen
gadon yana kallonta, ita dai bata yarda ta kallesa ba, ya dawo kusa da ita a
hankali yace "Good morning wife" Bata fuska tayi tace "Ni ba wife din ka bace" Ya
wara ido yace "Ohh don ban nuna maki ke wife dita bace jiya da daddare koh?" Dauke
kai tayi ta ki cewa komai, ya gyada kai Yana murmushi yace "Xan yi maganin ki,
abinda dare da yawa" Yana fadin haka ya mike ya hau saman gadon ya kwanta hade da
lumshe ido. Karfe bakwai da wani abu suka bar hotel din, Imaan dai sai kallon hanya
take tana jiran ta ga inda xai kai ta, ganin sun dau hanyar kano ta xaro ido a
tsorace tana kallonsa kamar xata yi kuka tace "Yaya don Allah ka bari, where are
you taking me to plss, wllh nasan ana ta nemana gida ka mayar da ni don Allah" Yana
kallon titi a hankali yace "Kaf gidan nan yanxu bbu mai iko da ke, so they are all
supposed to know that kina wajen mijin ki su xuba mana ido kawai, su da xa mu dawo
masu da cute kids in sha Allah, sai mu ba Umma daya mu ba Ammi biyu mu ba Aunty
daya sai mu tausaya ma Inna ita ma mu bata guda daya duk da lalata mana ita xata yi
yanda ta lalata ki...." hawaye Imaan ta fara yi tana kallonsa tace "Don girman
Allah ka mayar da ni gida Yaya, stop this joke" gently yace "You think I am joking
ko? Xa ki sha mamaki kam" Ta dakatar da kukan da take tana kallonsa ganin he is so
serious, Bai kalleta ba driving kawai yake da d'an gudu, tayi kasa da murya tace
"Don Allah kar ki min haka Yaya, kar ka raba ni da Ammina..." sae kuma ta fashe da
kuka, yace "Idan ban raba ki da ita ba ynxu ae ita xata raba ni da ke, ni kuma
baxan yarda a raba ni da ke ba coz I want to live with my lil sis in one roof"
Tafiyar kusan minti hamsin yyi ya shiga garin Zaria, Imaan dai gaba daya she is
shock ganin da gaske fa Mujaheed yake, wani babban gida yyi Parking ya fito yana
rike da mukullin gidan ya bude gate din ya dawo motarsa, ya shiga gidan yyi parking
a space na mota hudu dake babban compound din ya kashe motar ya fito yana kallonta,
bin gidan kawai take da kallo kusan a tsorace, ya rufe side dinsa ya xaga ya bude
inda take yace "Come down" ta hade hannunta tana girgixa masa kai tace "Am begging
you ka mayarda ni gida don Allah Yaya, Kar ka min haka" sakko da ita yyi daga motar
ya rufe yana rike da hannunta ya nufi entrance din shiga gidan ya sa makulli ya
bude, parlor ne babba, kuma bbu abinda bbu a ciki amma duk komai ya d'an yi kura,
ya kulle kofar parlon ya sa makulli sannan ya wuce stairs, Imaan ta durkushe wajen
jikinta a sanyaye ta ma kasa kukan, lkci daya ta mike tana xaro ido da karfi tace
"Yayaaa" sai kuma ta nufi stairs da gudu tana ci gaba da kwala masa kira, Mujaheed
ya fito daki da sauri yana saukowa stairs suka kusa cin karo, rungumesa tayi
jikinta na rawa tace "Kamar na ga wani abu yana tafiya wllh Yaya, I saw an insect"
Jan ta yyi xuwa sama ya bude bedroom yace "Tafi ki yi wanka na hada maki ruwa" a
tsorace tace "Ni dai Yaya wllh kamar cockroach na gani fa" yyi murmushi ya kama
hannunta xuwa bathroom yace "Toh muje in raka ki kiyi wankan" bin bayansa ta dinga
yi tana kallon kasa ko xata kara ganin wani, yace "Toh cire kayan" Hijab dinta ta
cire ta ajiye gefen gado, ta fara kokarin cire dogon rigar baccin jikinta, shi dai
kallonta kawai yake har ta fara dage rigan, sai kuma tayi still ta kallesa, ganin
yanda yake kallonta tayi wani kara ta sauke rigar kasa ta durkushe tace "Wayyo
Yayaaa bana son haka" Yana murmushi ya durkusa shi ma yace "Baki son me??" Bata
yarda ta kallesa ba ya mike ya tafi gefen gado ya xauna yace "Toh ki shiga kiyi Ina
jiran ki a nan" mikewa tayi ta shige bathroom din ta rufe kofa har da sa makulli.
Fita dakin yyi ya ya dawo parlor, ya bude kofa ya fita ya kulle ta waje sannan ya
bar gidan, few shoppings yyi ya siyo har da breakfast ya dawo gidan, ya ajiye
ledojin hannunsa a parlor ya wuce sama ya bude dakin, tsaye ya ganta jikin window
wayarsa kare a kunnenta idonta sha6e sha6e da Hawaye, jin an bude kofa ta juya tana
kallonsa ta katse wayar tana shessheka, ya tsaya nan bakin kofar ya dinga mata wani
kallo, a hankali ta dinga share hawayen idonta, ya karasa cikin dakin ya fixge
wayar yana duba screen din ya ga number Daddy, barin wajen take so tayi ya fixgo
hannunta fuska daure yace "What did you tell him??" Ta fashe da kuka tace "Ni dai
Yaya don Allah kayi hakuri ka mayar da ni gida, ni bana son ka baxan xauna da kai
ba..." Call duration din kiran ya duba yaga kusan 7 mins, ya hade rai sosai yace "I
asked what did you tell him??" Ta make masa kafada cikin rawar murya tace "Ni nace
masa ya xo ya daukeni baxan xauna a nan da kai ba, nace masa ni bana sonka" Kiran
Daddy na ya shigo wayar, ta goge idonta da sauri xata amshi wayar ya mata wani irin
kallo ya juya ya fita ta bi sa da ido hawaye na sauka idonta, Yana fita dakin ya ji
ya ma kasa daukan kiran, ganin ya kusa katsewa ya daga a hankali ya kai kunne amma
ya kasa cewa komai, Daddy
yace "Are you there Imaan?" Mujaheed yyi kasa da kai yace "Ina kwana Abba" Daddy
yace "Lafiya lau Muhd, ya ku ke" Mujaheed yace "Alhmdllh" Daddy yace "But why did
you take her with you without informing anybody Muhd?" Mujaheed ya d'an yi shiru
sannan a hankali yace "Ku yi hakuri Abba, amma nobody will let me go with her..."
Daddy yace "Ita kuma dayar matar taka fa? Kar ku shiga hakkinta, you know what is
right from wrong..." Mujaheed na sauka stairs murya can kasa yace "In sha Allah
xata dawo yau Abba" Daddy yace "Toh maa sha Allah, ba sai kun dawo anytime soon ba,
Allah ya ba ku xaman lafiya..." Mujaheed yyi murmushi yace "Toh Ameen nagode
Abba...." Daddy yace "Tace kuna Zaria koh?" Mujaheed yace "Ehh" Daddy yace "To maa
sha Allah, hope there is no problem?" yace "Sure Abba" Daddy yace "And what about
ur work?" yace "Xan dinga tahowa daga nan din, I took two weeks leave..." Shiru
Daddy yyi kafin yace "But I don't like that, wajen yyi nisa" Mujaheed yace "Sati
uku kawai xa mu yi nan Zaria" Daddy yace "Ohk that's better Allah ya kai mu, if you
have any problem you let me know" Mujaheed yace "In sha Allah" daga haka Daddy yyi
masa sallama ya katse wayar. Mujaheed ya xauna saman kujera ya lumshe ido hoping
everybody will accept the marriage that way, footsteps da ya ji sama ya sa ya daga
kai ya kalleta, ya bude daya daga ledojin da ya shigo dasu yace "Breakfast" Ko
kallonsa bata yi ba fuska daure, ya mike ya wuce sama yana rike da wayarsa ya bar
ta tsaye a parlon. Abba ne xaune parlon Inna sae Daddy da Mama Hadiza, Inna na
xaune saman tabarma tayi tagumi ido duk ya kumbura ta fashe da wani sabon kuka tace
"Ni dai tunda uwata ta haifeni ban taba ganin tantiri irin Mujaheed ba, me nayi
masa a rayuwa banda kyautatawa da bautar da nayi da shi da xai saka min da sharri??
Me na masa xai sa in kasa bacci jiya na je tolet ya fi sau hamsin, sannan na kwana
kan darduma sbda tashin hankali, wai ashe shi ya shigo ba tsoron Allah ya dauke min
jika ya gudu, to wai ma a kan me xai dauketa yarinya nace bata isa aure ba, me xai
je yyi da yar mutane? a gaskiya duk inda ya tafi da ita a je a dawo min da jika ba
ruwana, ko kuma ni a min kwatancen wajen in tafi da kai na in daukota, ita Imaan
din har nawa take xai gudu da ita sbda ya lalace, kaiii Ahmadu baka yi sa'a ba
gaskiya, ban ta6a ganin tantiri irin Mujaheed ba, shiryawa xan yi yanxu a kai ni
gidansa ya ga barbadin bala'i sannan in juyo tare da Imaan tunda ba uban wani ya
haifa ma Bukar ita ba" tana fadin haka ta mike xata shige daki ta dauko mayafi,
Mama Hadiza ta bi ta da kallo tace "Toh ai basa gidansa inna" Inna ta juyo da sauri
tana kallonta tace "Basa gidansa? To ina ya kai ta?" Mama Hadiza tace "Sun dai yi
waya amma bai fadi inda suke ba" Inna ta xauna kan kujera baki bude tace "Ya xa ayi
ya ki fadin inda suke, ni kuma da suka bari nan fa???" Mama Hadiza ta saci kallon
Daddy da ke ta kallon uwar tasu, da mamaki Inna da ta kasa rufe baki tace "Shi
Mujaheed din mance wahalan da nayi masa yyi xai tafi da Imaan banda ni?" Bbu wanda
dai ya tanka su cikinsu. Mujaheed ya gama gyara gidan gaba daya ya goge duk kuran
ko ina ya dawo fess, ya kalli agogo dake nuna karfe sha daya saura ya wuce sama ya
bude bedroom dinsa ya ga Imaan kwance tana bacci tun bayan da ta sha drugs da ya
siyo mata bayan ya tilastata tayi breakfast take baccin, bathroom ya shiga ya sake
yin wanka ya fito ya shirya cikin kananun kaya ya dau makullin motarsa ya juya yana
kallonta, karasawa yyi gun gadon ya xauna gefenta ya dukar da fuskarsa dai dai
nata, a hankali ta bude ido jin saukan numfashi a fuskarta, ya ja hancinta murya
can kasa yace "I am going out now but I will be back soon lil sis" Ganin bacci ne
sosai idonta yyi pecking goshinta ta lumshe ido bata ce masa komai ba, mikewa yyi
ya fita dakin ya kulle mata kofa sannan ya fita ya kulle gidan ta waje ya hau
motarsa ya bar gidan, hanyar kaduna ya dauka.... Direct Marafa ya nufa bayan ya
shiga garin kaduna, yana isa gidansu Safeenah yyi parking a kofar gida ya fito daga
cikin motar ya shiga cikin gidan, bbu kowa parlon sai Sajidah, daga sama har kasa
ta kallesa ta ci gaba da danna wayarta, ya xauna saman kujera ba tare da ya sake
kallonta ba ya ciro wayarsa ya kunna, sannan yyi dialing number Safeenah, tana
dagawa yace "Ina parlor ki fito" Safeenah dake shiryawa ta fito wanka ta xaro ido
tana kallon Uwarta dake waya, Safeenah ta dade bata ji farin cikin da take ji ba a
lkcn, ta xauna gefen gado bayan ta sa kayan tana kallon Hajiyarsu dake waya tana
cewa "Ehh dama shine abu na farko da nake son ayi mata, Ehh sunanta Rukayya, xa mu
yi waya anjima" daga haka ta katse wayar, Safeenah ta xaro ido tace "Hajiya
Mujaheed ne fa a parlor" Hajiyan Marafa tace "Mujaheed Kuma? To me ya xo yi??"
Safeenah ta bata rai ta mike ta nufi gaban madubi ta feshe duk jikinta da turare
sannan ta dau karamin gyale ta fita, tana shigowa parlor ganinsa a xaune ta nufesa
da sauri ta fada jikinsa ta rungumesa gam, sai kuma ta fashe da kuka tace "I've
missed you a lot Mujaheed, don Allah ka xo ne mu koma gidanmu mu ci gaba da xamanmu
mu kadai??" Yace "Tafi ki hada kayan ki" ta xaro ido tace "Da gaske??" Yace "I am
waiting" gaba daya su Hajiya Baturiya dama sun kwaso kayanta daga gidan Mujaheed
bayan abinda ya faru, ta mike da sauri ta tafi daki tana kallon Uwarta tace "Mummy
yace in hado kayana wllh" Hajiyan Marafa tace "Babu inda xa ki je sai an gama aikin
da ake yi..." Safeenah ta fashe da kuka tace "Ni dai wlh Mummy ki Bari in bisa gida
fa xa mu wuce ya ma saki yarinyar Ina ji, don Allah ki bar ni mu je" Hajiya Marafa
tace "Cewa nayi ki bari sai an gama aikin da ake yi tukun, ke ana kokarin kwatar
maki yan ci kin kasa ganewa sbda son miji" Safeenah tayi kamar xata yi kuka tace
"Ni dai Hajiya tafiya xan yi daga karshe sai in dawo idan an gama aikin, amma ni
kam da baku bata kudin ku ba ni kadai na isa Hajiya Rukayya a duniyar nan, wllh sai
na rabata da d'anta, Auren ma da aka masa Ina jin babu shi yanxu" daga haka ta fita
xuwa dakinta ta hau hada kayanta a jaka, cikin few minutes ta gama ta jawo jakar
downstairs, Mujaheed ya dinga kallonta har ta iso parlon, Sajida ta dinga mata wani
kallo tana girgixa kafa, Mujaheed yace "Hajiya fa?" Safeenah ta koma sama da sauri
ta shiga dakin uwarta tana murmushi tace "Hajiya wai ki fito ku gaisa" Hajiya
Marafa tace "Bai kai wannan matsayin ba, banda ma kin nace ina mu Ina hada xuri'a
da Rukayya? Waye bae san Rukayya da abinda take yi ba, in sha Allahu ta ja ma kanta
abinda ba shikenan ba tunda har ni tayi ma haka, xan kuma nuna mata mu bama xama da
kishiya, Ana gama aikin da ake dama xan tako gidan da kai na" juyawa Safeenah tayi
ta fita dakin tana cewa "Bayan nace maki babu auren yanxu wace kishiya kuma, ai sai
dai mu gwada mata hankali kawai..." Tana dawowa parlor ta kalli Mujaheed tace
"She's in the bathroom mu je kawai dear" mikewa yyi ya nufi kofar fita ta bi
bayansa tana kallon Sajida tace "Sai mun yi waya Aunty Sajida" ko kallonta Sajida
bata yi ba har ta fita, sai da suka shiga mota Mujaheed yace "Zaria xa mu je"
Safeenah ta xaro ido cike da farin ciki tace "Ae ya fi dear nah, gwara mu yi nisa
da gida kawai, after some months sai mu dawo kaga bbu wanda xai kara tada wani
maganar, wllh hakan ya fi, har naji hankali na ya kwanta sweetheart" shi dai bai ce
mata komai ba ya tada motarsa don duk hankalinsa yyi kan Imaan da ya bari tana
bacci....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

84....

_And I dedicate this particular page to the entire members of_ *Murmushin Novels*
group....

I Khaleesat Haiydar is wholeheartedly saying a big fat *Thank you* to the entire
members of the above👆🏻 named group... nagode nagode, Allah ya bar kaunar, I really
appreciate it sisters, Allah ubangiji ya kara maku budi da daukaka, ya bar xumuncin
mu, ya sa ku gama da duniya da iyaye lafiya, Allah ya saka da alkhairi, Billah Ina
yin ku har raina, sannan.... _Inna na gaisuwa tace sai kun xo mata kwalema da
share share a fitar da duk dattin da suka makale mata kada su cuceta, sannan tace
in maku tuni da tsoron Allah a duk inda xa ku kasance duba da yanda duniyar ta
lalace yanxu mutane ba tsoron Allah, domin kuwa lkcnsu tsoron Allah ake kaca kaca
ba wasa, don haka ku ji tsoron Allah a duk inda xa ku kasance, sannan ku xamo masu
tsafta domin sace xuciyoyin masu house_... Lol, gaskiya I am happy da abinda ku ka
min jiya, I love u all...

And my lovely fans that partronized my book happily without thinking twice, ku ma
ina yin ku har raina wllh, Ina son ku, _Inna tace kuma tana gaishe ku, kuma ku rike
Allah, to wa gare ku da xa ku rike dama banda Allahn? Sannan ayi ta ma iyaye
biyayya domin a rabu lafiya da su kamar yanda Ahmadu da Bukar ke mata biyayya..._
lol

Mujaheed na gama parking a compound ya kashe motar ya bude ya fito, gate ya tafi ya
kulle ya dawo, Safeenah da ta fito motar tana mika ta sauke ajiyar xuciya tace "Har
hankalina ya kwanta dear, i prefer here than kaduna unlike kwanaki da muka xo naji
duk ban son garin, yanxu kam I like it here..." Shi dai bai ce mata komai ba ya
nufi entrance din gidan rike da takeaways din da yyi a hanya, tace "But wait,
foodstuffs din fa Dear, ka bar su a booth, my bag is there also..." ba tare da ya
juyo ba yace "we will take them in later..." Bin bayansa tayi suka shiga gidan, ya
xauna saman kujera bayan ya ajiye ledojin abincin hannunsa ya jinginar da kansa da
kujeran don duk ya gaji sosai, ko kadan shi dama bai son driving me nisa, Safeenah
na murmushi ta tsaya bayan kujeran tana massaging shoulders dinsa a hankali tace
"Bari in je sama in hada maka ruwan wanka baby, nasan ka gaji, shi sa nace ka bani
driving din inyi ka ki...." Shi dai bai ce komai ba yana sauraronta, tana gama
fadin haka ta cire mayafinta ta ajiye saman kujera xata wuce sama ya bi ta da kallo
yace "A'a kar ki damu baxan yi wanka ba yanxu" ta juyo tana kallonsa tace "Oh
really, amma idan kayi ai xaka fi samun relieve ae dear, anyway mu je sama in maka
tausa toh" cike da shagwaba ta fadi hakan, bai ko kalleta ba ya mike ya dau ledan
abinci daya yace "Ni fa I am okay, I just need rest...." Ta langwabar da kai tace
"To mu je ka kwanta my dear...." Bai ce komai ba ya nufi stairs, jin tana biye da
shi ya tsaya a staircase din sannan ya juya yana kallonta yace "Tot you said you
are hungry ga abinci can kuma kin bari downstairs" ta tabe baki tace "No apple din
da na ci daxu a hanya ya isheni, nima hutawa xan yi, all my body is just aching"
Bai ce komai ba ya ci gaba da tafiya tana biye da shi har suka isa corridor din
dakuna hudun dake jere, tsayawa yyi dai dai kofar dakin da yake amfani da, ya d'an
saci kallonta ganin dakin ta nufo yace "You use the other room Safeenah" Da mamaki
take kallonsa, sai kuma tace "Why? Beside tunda muke xuwa gidan nan na taba amfani
da wani dakin banda wannan da muke using tare? Baka taba ce min inyi amfani da wani
daki ba ai" Ya juya yana kallonta da kyau yace "Ohk we are not sharing it this time
around, you choose from any of the other rooms, this is a master bedroom" wani
kallo Safeenah ta dinga yi masa daga sama har kasa, can tace "What's wrong with you
Mujaheed, why are u behaving this way?? dama mun ta6a raba daki tunda muka yi aure
da kai? Ko kuma wani sabon walakancin ka tsiro?" Ya shafa kansa murya can kasa yace
"Plss Safeenah I am tired bana son magana, I told u I need rest, idan baxa ki shiga
any of the rooms ba ki koma parlor" yana fadin haka ya shige dakin ya sa makulli,
Safeenah ta wani xaro ido tana kallon kofar da mugun mamaki, ta fi minti daya tsaye
tana tunanin wannan kuma wani sabon walakancin Mujaheed ya kirkiro mata? Tabdi ai
ko wahala kawai xai daukar ma kansa don maganin sa xata yi ba na wasa ba, da wannan
tunanin ta sauka downstairs a fusace xuciyarta na tafarfasa, don sosai ranta ya
baci... Mujaheed ya ajiye ledan hannunsa yana kallon Imaan dake bacci har lkcn,
takawa yyi ya isa kusa da ita ya xauna gefenta, a hankali ya kai hannu forehead
dinta ya ji temperature dinta normal, Bude lumsassun idonta tayi tana kallonsa,
sai kuma ta dauke kai a hankali ta matsa daga kusa da shi ta juya masa baya, yace
"Kinyi sllh?" Kin basa amsa tayi ta turo baki, idonsa ya sauka kan darduman da ke
shimfide dakin alamar tayi sllhn, yace "Tashi ki ci abinci" ta hade rai tace "Ni
baxan ci ba" yace "Koh??" K'in cewa komai tayi, ya sa hannu ya daga ta, ko ba a
fada masa ba yasan next reaction dinta hakan ya sa ya maxa ya juyo ta ya rufe
bakinta ya hade rai sosai yana kallonta, ta 6ata fuska kamar xata yi kuka cikin
sanyin murya tace "Ni dai ka maida ni gun Ammina" Mikewa yyi ya dagota ya dawo da
ita kasa kan darduman da ta bari a shimfide fuska daure yace "Ga abinci nan ki
dauka ki ci" ganin kallon da yake mata ta jawo ledan a hankali hawaye na taruwa
idonta ta bude ta ciro take away din shinkafa da kazar da ya siyo mata sai table
water da five alive drink, spoon ta dauka ta debi shinkafar ta fara ci a hankali,
shi dai kallonta kawai yake ko kiftawa babu, can yyi murmushi ya tafi kan gado ya
kwanta hade da lumshe idanuwansa, bayan kusan minti biyar ya bude ido to see if she
is eating the food, kazan abincin ya ga ta dauka tana ci as if her happiness depend
on it don ba cin wasa take ma kazan ba, suna hada ido ta juya da sauri bayan ta
cire naman a baki, murmushi Mujaheed yyi ya mike xaune ganin ta ajiye kazan yace
"Wa kika ajiye ma?" Ta turo baki tace "Ni baxan ci ba" kallon bakin da take turo
masa kawai yake.... Inna ce xaune kan kujera a parlonta tana saka gogaggun kayanta
a sabon Ghana must go din da ta sa Mai gadi ya siyo mata aka bude kofa hade da
sallama, Daga kai tayi tana amsa sallaman ta ajiye set din riga da xanin hannunta
tace "Sannu da xuwa Ta Rasulu" Ta Rasulu ta cire Hijab din jikinta ta linke da kyau
ta ajiye tace "Ke kuma ina xa ki da gana mas gau?" Inna ta tabe baki tace "Kayana
nake hadawa ta Rasulu, sam bani da 'ya yan nuna ma duniya, shine naga gwara kawai
in tafi gidan Bala in xauna, duk me xa a min a can xan fi shanyewa tunda nasan ba
jinina yyi min ba" Ta Rasulu ta xauna tace "Me kuma suka maki 'ya yan??" Inna tace
"Fisabilillahi ta Rasulu ina laifina don nace duk inda xa a nemo min Mujaheed a
nemo min shi in ji dalilin da xai dauke min jika ya gudu kamar d'an fashi, ta
Rasulu babu lefe babu sadaki babu komai kawai ya samu tsaleliyar yarinya a bagas ya
tafi da ita ko uban meye ma'anar haka oho, wato ga sadaka an basa, to wllh ubansa
Ahmadu ma yyi kadan balle shi sa karan kada miya, Jikata tafi karfin ayi sadaka da
ita, kawai yaro tantiri dai ya shigo min gida ina wankin bandaki ya arce min da
jika tsakar dare kawai sbda yana shan wiwi, to ta Rasulu shan wiwin nasa kuma sai
ya kare a kai na? Don wannan ni ya ci ma mutunci ba kowa ba wllh, snn ace ayi shiru
a xuba masa ido yaje ya lalata min jika? Kinga Hadiza, Ahmadu da Bukar duk
gantalallu ne Allah na tuba, sam bbu wanda ya dau wani kwakkwaran akshan a kan
batun nan, yanda kika san abun kirki Mujaheed yyi ko kuma shi halitto min jika,
idan kika bibiya ma duk sun san inda ya tafi da ita marasu imani, daxu fa har
gidansa naje a unguwar dosa basamuden da ya ajiye bakin get yace min ai gidan fanko
ne bbu kowa ciki, ni dai ba yarda ba na shiga na gama xagaye na naji shiru bbu
alamar kowa shine fa na fito na dawo gida na sa aka siyo min jaka nake xuba kayana,
haka kawai yara sun gama rainani sun maida ni shashasha, tsakanin Imaan da Mujaheed
fa gantalallen kaza, ni dai ban ta6a ganin ya siyo mata ko da tsinke ne ya bata ba
kamar dai yanda wnn yaro d'an albarka Bulasawa ke yi, to wannan mutumi xan dau jika
in ba ma, wllh baxata sa6u ba, maxa ya dawo min da Imaan ba yanxu xata tare ba...."
Ta Rasulu na girgixa kai tace "Toh shi Mujaheed ko dai hau ne ya fada masa xai
aikata wannan barna haka? Ina ya tafi da yar mutane bai bada hakokkin aurenta ba,
haka kawai ya cuce ta yyi mata ciki a banxa" Inna ta rushe da kuka tace "Imaan ina
ta isa daukan ciki ke kuma ta Rasulu, da kuwa ya cuceta, duka duka nawa take? Ai
kamata yyi a xaunar da shi a karanta masa illan hakan, ina laifin ta d'an kara
gwabi, to ga dai Safara'u har yau shiru sai dai ta ci tayi kashi, ban gane kan abun
ba" Ta Rasulu tace "Yanxu dai kiyi hakuri ki maida kayan nan, tafiya ba taki
bace...." Inna tace "A'a gidan Bala xanje gwara inje suyi ta taka ni baxai min ciwo
ba don bbu abinda na hada da su na dai san uwarsu kishiyata ce ta aure min miji ban
ji ba ban gani ba" Ta Rasulu tace "Asabe nace maki bbu xancen tafiya, ga abun al-
ajabi na xo da shi..." Inna tayi shiru tana kallonta, Ta Rasulu tace "Toh dai asiri
mummuna aka lafta ma Bulasawa yace ya fasa auren Imaan...." Inna tayi tagumi tana
kallon ta Rasulu a hankali tace "Sai aka ce maki wani la'anannen ne yyi asirin Ta
Rasulu?" Ta Rasulu ta tabe baki tace "Toh me shi a gidan nan yake tare da ku wllh,
ba a dai ambato min suna ba, amma a nan me shi ke kwana yake tashi, amma ke wa kika
xarga Asabe?" Inna tace "Allahu Akbar, Rukayyar Ahmadu ce" Ta Rasulu tace "Nima ita
na raya" Inna ta bude baki tayi mitsi mitsi da ido tayi shiru tana kallon Ta
Rasulu, can tace "Ikon Allah, wato kaikayi ne ya koma kan mashekiya ba shakka, kin
lura duk ta fi kowa daga hankali a auren da aka daura da Mujaheed???" Ta Rasulu
tace "Wllh kuwa, biri yyi kama da mutum, ni naga ma duk ta rame ta xabge tayi baki,
yanxun nan mun hadu da ita xan shigo ita xata fita, wllh duk a birkice take, sai
naga ma kamar hadin bauta tayi" Inna ta gyada kai tana wani murmushi tace "Toh
Alhmdllh da wnn magana ya fito fili, amma kinsan wani abu? Wllh yanxu a idon
Ahmadu, Bukar da Hadiza bbu me tada fitina a gidan nan sai ni, nice dai fitinanniya
gantalalliya" Ta Rasulu tace "Ke ma xai wllh ai wannan magana barinsa xa mu yi a
ciki mu yi ta kallon ikon Allah, iyaka a tashi tsaye sosai da nema ma yarinyar nan
Imaan tsari...." Inna tace "Ke da kika san komai, ai bbu wanda xai fara gwaleni a
kan xancen nan sai Bukar, shi Ahmadu dama baxai ce komai ba amma ni nasan kallon
jarababbiya yake min baxai dai yi magana ba, ita kuma wannan mata Hadiza sai dai ta
xuba min idanu, a takaice dai Bukar ce min xai yi in daina haka shi ba ruwansa, to
ya xan masu Ta Rasulu? To wllh tunda Rukayya ta ma jikata haka sbda bakin ciki da
hassada tata ta kare duniyar nan gaba daya, kuma kwanaki kadan ya rage mata gidan
d'a na wllh, ke dai kawai ki xuba min ido ni kadai na isheta sai ta gwammace kida
da karatu, aure jikokina kuma mutu ka raba, ni nasan da tasan auren xai dawo kan
Mujaheed da bata san yanda tayi ta hana ba, kuma mutuwa xata yi a banxa idan tace
xata raba auren nan...." Ta Rasulu tace "Atoh, kuma fa har yanxun ba wai saduda
tayi ba, ance min tana nan tana kokarin raba auren nan, da kyar fitan da tayi yanxu
ba gun bokanta
xata ba, wllh sai mun tashi tsaye an yi kokarin nisantar da Imaan sosai daga
sharrinta, in sha Allahu in dai da ran mu sai ta fito da bakinta tana tona kanta,
kada ki kuskura ko da wasa ki gaya ma ko Hadiza tunda lalacewa ta sami yaran naki,
mu dai da muka san komai sai mu yi ta kan mu" Inna tace "Dama ba gantalallen da xan
gaya ma, iyakata da su su ban kudi in rufa ma jikata asiri, sannan in sha Allahu a
gaban Bukar asirin Rukayya xai tonu shi da baya ta6a ganin laifinta..." Ta Rasulu
tace "Toh ynxu ya isilin bawan Allahn nan Bulasawa?" Inna ta marairaice kamar xata
yi tace "Wai daxu aka sallamesu asibiti inji Ahmadu, ni dai xan shirya in siya lemo
ko kwaya biyar inje har gida in duba sa wllh, dama can Imaan ba matarsa bace bani
da rabon cin kaji da xabi dai" tana magana tana matsar kwalla, Ta Rasulu tace "Kya
ci da kudin ki" cikin rawar murya Inna tace "A'a ki bari Ta Rasulu, wani hanin ga
Allah baiwa ne, kuma ni da Bulasawa mutu ka raba har gidansa xan dinga xuwa kai
masa xiyara...." Daddy ne tsaye jikin motarsa kofar gidansu Ammi, ya fi minti goma
yana jiran fitowarta, jin an bude gate ya daga kai har ta fito, ta gaishesa, yana
kallonta yace "Ban san ki da haka ba Aysha, wannan ba halin ki bane, why are u
behaving this way pls?" Bata tanka sa ba, yace "Ko ba don ni ba don barrister ya
kamata ki hakura haka nan, kar ki manta jininsa fa ya aura ma Imaan, sannan don't
forget yayana ne shi din, jinin nasa kuma d'a na ne, beside all this Aysha Mujaheed
bai yi deserving haka daga gare ki ba, wai kin mance wanene Mujaheed ne?" Ammi da
hawaye ya kawo idonta ta girgiza kai tace
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

"I am thinking of my daughters future, ban san rayuwar da xata yi tare da kishiya
da uwar miji warce bata sonta duk da kai ba yarda da rashin son da take mata kake
ba, kila sai ranan da xaka gani a xahiri, nasan abinda imaan xata iya jurewa da
wanda baxata jure ba, this is too much for her, ga condition dinta...." Daddy ya
sauke ajiyar xuciya yace "Baki yarda da kaddara ba kenan, Haba Aysha sai kace ba
musulma ba, where is ur faith? All you need to do is wish ur daughter a peaceful
and better married life, plss ki shiga kiyi ma gwaggwo sallama we are going home
now" Girgixa masa kai tayi tace "No ka tafi gobe in sha Allah xan dawo" yace
"Sure?" Tace "In sha Allah" yace "Toh Allah ya kai mu, we will talk later on phone"
daga haka yyi mata sallama ya shiga mota ita kuma ta wuce ciki. Mummyn Sadeeq ce
xaune makeken parlonta tare da aminiyarta Hajiya Batula, Hajiya Batula tace "To ke
wa kike tunanin xai aikata hakan Hajiya" mahaifiyar Sadeeq Hajiya Khadijah, tayi
murmushin karfin hali tana gyada kai tace "Ni nasan wacece ita tunda aka ce daga
family din yarinyar take, sarai nasan wacece, kuma Billahil azeem xata san ita ce
silan heartbreak din d'a na" mikewa tayi ta nufi window fuskarta a murtuke, da
mamaki Hajiya Batula tace "Ba shakka, amma koma wacece ita din gaskiya ta xama abar
tausayi yanxu, ta rasa wanda xata ma asiri sai Abba? Don me bata bar asirin iya
'yar su ba kadai, Wannan shine biggest mistake of her life, don da ta sani da bata
fara ba" Mummy dai murmushi kawai take, aka bude kofar dakin duk suka juya, Sadeeq
ne ya shigo dakin, Uwarsa ta dinga kallonsa don ba karamin rama yyi ba, yyi kasa da
kai ya gaida aminiyar mum din tasa cikin sanyin murya sannan ya xauna saman kujera
yace "Mummy, Ina son xan tafi Uk...." Katse sa tayi tace "Kaje kayi me a UK
Sadeeq?" A hankali yace "I need rest Mum..." Shiru tayi tana kallonsa, lkci daya
hawaye ya kawo idonta ta dauke kai tana kallon waje ta window.... Mikewa xaune
Mujaheed yyi jin ringing din wayarsa, ya dauka yana kallon Screen din, Call din
Umma ya gani, ya ji gabansa ya fadi sosai, yyi ta kallon screen din har ya katse,
ta sake kira, kasa kin dagawa yyi, ya daga a hankali ya kai kunne yyi shiru, ko
sallama babu tace "Mujaheed??" Yyi kasa da murya yace "Na'am, Ina yini Umma" Tace
"Kana Ina ne?" Ya d'an yi shiru sannan yace "Ina gida" tace "Wani gidan?" Nan ma
yyi shiru, cikin tsawan da ya ji har tsakiyar kansa tace "Baxa ka bani amsa ba ina
tambayarka?" A hankali yace "Gidana Umma" strictly tace "Wani gidan naka a ciki?"
Yace "Zaria" Tace "Toh" tana fadin haka ta katse wayar kitt, ya dinga kallon phone
din xuciyarsa na bugawa, Imaan dai na xaune kan darduma har lkcn ta gama jujjuya
shinkafar takeaway din gabanta ta bar sa, kazar ma tunda ya kamata tana ci ta ki ci
kuma, sauka yyi saman gadon ya tafi ya bude kofar dakin ya fita, Safeenah na xaune
parlor tana waya da Hajiyar su, murya can kasa tace "Haukatar da ita kuma Mummy,
A'a gaskiya... idan aka yi haka ai bata kwashi takaicin da ya kamata ba, a dai yi
wani abun daban Mummy" Safeenah tayi shiru tana sauraron uwar tata, sai kuma tace
"Mummy na fa ce maki babu auren nan wllh, tunda muka xo bai ce min komai a kai ba,
sun raba da suka ga bai so...." jin taku a stairs ta katse wayar da sauri, ta gyara
xama ta wani hade rai tana kallon tv dake aiki, Mujaheed ya shigo parlon yana
kallon ledan abincin da bata ta6a ba ya dauka yace "Ain't you eating?" yi tayi
kamar bata ji sa ba, ya tafi kitchen ya wanko plate ya dawo parlon, ido hudu yayi
da Imaan dake sakkowa stairs a hankali tana kallon Safeenah dake xaune idonta a kan
tv har lkcn....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

85......

Ganin direction din da Mujaheed ke kallo bbu ko kiftawa Safeenah ta juya da sauri
tana kallon wajen ita ma, sake remote din hannunta tayi a hankali ta mike tana
kallon Imaan da idanuwanta kamar xa su fito, da mugun mamaki da shock take kallon
nata, lkci daya ta juya cikin tashin hankali tana kallon Mujaheed xuciyarta na
bugawa kamar xai fito, walking slowly ya karasa cikin parlorn ya xauna saman kujera
ya bude takeaway din dake cikin leda ya diba abincin a plate ya ajiye sannan ya
daga kai ya kalli Safeenah dake kallonsa har lkcn with full shock, sai kawai ta
fashe da wani matsanancin kuka jikinta na rawa ta nufesa ta rikosa tace "Tell me,
what is she doing in our home Mujaheed? Why is she here? Wa take nema??" Juyawa
Imaan da ta hade rai tayi xata koma sama, Mujaheed yace "Don't go back, dawo nan"
k'in tsayawa tayi tana ci gaba da tafiyar ta da sauri, cikin daga murya yace
"Imaan!!" ta tsaya fuska daure amma ta ki juyowa, har ranta taji xafin ganin
Safeenah, ga wani faduwa da gabanta yake yi, Mujaheed ya mike tsaye yana kallonta
yace "I said come back here Imaan..." Safeenah na jijjigasa cikin tashin hankali
sosai tace "Mujaheed answer my question, ka gaya min me yarinyar nan take a gidana,
ka gaya min nace, wa take nema??" Imaan ta juyo walking slowly ta dawo parlon tana
kallon Safeenah fuska daure, Safeenah ma ta dinga kallonta xuciyarta na bugawa har
lkcn tana rike da Mujaheed, Imaan ta murguda mata baki ta dauke kai tana jiran jin
kiran me Mujaheed yyi mata, Safeenah ta nufeta da sauri tana huci bakinta na rawa
tace "Me kike yi a gidana??" Imaan ta rungume hannunta tace "Abinda kike yi, and
point of correction ba gidan ki bane ke kadai, nima nan gidana ne...." Wani kara
Safeenah tayi kamar mahaukaciya jikinta na rawa tace "Karya kike wllh, karya kike,
nan gidan mijina ne, gidana ne nan, baki da space a gidan nan yarinya, this is my
husband's house" Imaan tayi wani murmushi tace "Koh? To sai ki tambayi mijin ki
dalilin da ya sa ya kawo ni nan" Sai kuma ta saci kallon Mujaheed da ya ki kallonsu
gaba daya, murya can kasa tace "And here is also my husband's house...." Bata rufe
baki ba Safeenah ta wani cakumota da karfi jikinta na rawa, Mujaheed ya taho da
sauri ya janye Imaan yana ma Safeenah wani mugun kallo, ya fixgota shi ma cikin
tsawa yace "What is this u are doing? Baki da hankali ne xaki fixgota haka? Ciwo xa
ki ji mata?" Safeenah na kallonsa with shock ta fashe da matsanancin kuka ta xube
kasa tace "Na shiga uku na lalace, Mujaheed kayi ma Allah ka gaya min me take a
gidan nan Plss, tell me what brought her to my home" Wani dogon tsaki Imaan ta ja
tana hararanta xata bar wajen Safeenah ta mike yi kanta gadan gadan, cikin xafin
nama Mujaheed ya fixgota for the second time yana mata wani kallon da ya sa
hanjinta ya kada, strictly yace "This should be ur last attempt in this house, I
will neva take it likely with you idan kika sake maimaita hakan, Me kike son yi
mata da??" Safeenah na kuka sosai tace "Wllh baxan xauna da yarinyar nan ba mutuwa
xan yi, ka taimakeni ka gaya min me take yi a gidanmu, wayyo Allah na na shiga
ukuuu..." Mujaheed ya saketa, calmly yace "Aure ya kawota gidan nan, ita din xabin
mahaifina ne gareni, kamar yanda ke kike xabin mahaifiyata, at that time I've neva
for once say no to my mother na karbi auren ki hannu bibbiyu, the only difference
btwn my marriage with you and that of Imaan is that, ke naki I was aware and
present during the nikka.... Don haka kamar ynda ban ma Mahaifiyata musu a kan
auren ki ba, to baxan ma mahaifina musu a kan auren Imaan ba, and I am assuring you
that in sha Allah xan xamo mai adalci tsakanin ku, i will try my very best, but
Imaan matata ce yanxu kamar yanda kike matata...." Imaan dake tsaye tana jiran
ganin abinda Safeenah xata mata, ta kara jan wani dogon tsaki ta wuce sama kamar
xata tashi sama, Mujaheed ya bi ta da ido, Safeenah ta sulale kasa ta rushe da wani
kuka da karfin gaske, cikin tashin hankali tace "Innalillahi wa inna ilaihi
raji'un, na cuce kai na, don Allah Mujaheed kar ka min haka don kaga Ina sonka,
babu mai kishiya cikin 'yan uwana wllh tllh, plsss kar kace min kishiyata ce ita, I
can't stand it, xuciyata bugawa xata yi wllh...." Dukawa yyi yana kallonta smiling
calmly yace "Kin yi breaking record..." Tun da Imaan ta koma daki ta kasa xaune ta
kasa tsaye, ta kalli kofa ya fi a kirga, tsayawa tayi jikin window ta fara kukan da
ita ma bata san dalilinsa ba, wani tukuki taji xuciyarta na mata, tana ta tsaye har
bayan kusan minti goma, aka bude kofar dakin, juya baya tayi da sauri ta goge
idonta tana kallon waje fuska daure, ya rufe kofar yana kallonta yace "She is my
wife imaan, aside that kuma ta girme ki sosai, kada ki sake mata tsaki, that's very
disrespectful of you...." juyowa tayi tana kallonsa da wani expression, ya karasa
kusa da ita kafin yace komai, cike da masifa tace "Wllh sai na mata din, da ta
girmeni sai kuma ta haifeni? Ni ina ruwana da ita a gidan nan xaka ce min she is ur
wife ko da nace maka ban sani bane? What's my business with that??" Sai kuma ta
fashe da kuka ta nufi bathroom da sauri ya rikota yace "No I am only reminding you
Imaan" fadawa jikinsa tayi tana kuka sosai tace "Ni wllh Yaya bana son gidan nan, I
don't want to stay here, na tsane ta da gaske, baxan xauna ina ganinta ba kullum, I
don't like her, bayan ta gama xagi na saura kadan to dokeni kuma kaje kana ta bata
hakuri tun daxu fa.." tana fadin haka ta kara rushewa da kuka har da shessheka tana
shigewa jikinsa, rungumeta yyi yana sauraronta da mamaki, sai kuma yyi murmushi a
hankali yace "Toh ya kike son ayi?" Cikin rawar murya tace "Ni dai mu tafi wani
gidan kuma kar ta bi mu wllh..." Yace "Kin hakura xa ki xauna da ni kenan yanxu?"
Still tayi da farko, lkci daya kuma ta janye jikinta daga nasa da sauri ta juya
masa baya tana imagining abinda ta fada, murmushi kawai yake yana kallonta, ta turo
baki tace "Ni baxan xauna da kai ba" daga haka ta wuce cikin bathroom da sauri ta
rufe kofar, juyawa yyi ya fita dakin still smiling. Lallashi bbu irin wanda
Mujaheed bai ma Safeenah ba domin a rayuwarsa ta duniya ya tsani kukan mace, kukan
ma wai sabida shi, amma kamar yana dada tunxurata, da ta tuna biye ma Umma ya ja
mata wannan masifa da tashin hankali sai ta kara rushewa da kuka tana tunanin me
xata ma Umma taji dadi a ranta, gani take kamar ta kusa farkawa da mummunan
mafarkin nan da ke neman fasa mata xuciya, sai lkcn ta san meye kishin abinda kake
so, gashi ta kasa ko da kiran Hajiyarta ta sanar mata ai fa kishiya na nan daram,
tsoro take kada tace mata ta dawo gida don har xuciyarta take jin baxata iya rabuwa
da Mujaheed ba har abada, rabuwa da Mujaheed mutuwar ta kenan a ganinta, ta rikosa
tana kuka sosai tace "Wllh ina sonka Mujaheed, Ina son kasancewa da kai amma baxan
iya xama da yarinyar nan ba idan ma record din gidanmu xan yi breaking ba da wannan
yarinyar ba gwara ka saketa ka auri wata na yadda, Allah da gaske ban son ganinta
ko na second daya, yanxu kana nufin kun hada gado da yarinyar nan?" Mujaheed ya
saketa ya mike yace "Baki son ganina kenan idan baki son ganinta, don she is me"
Bai jira sauraronta ba ya shige toilet din dakin yin alwala, har ya fito kuka take
tayi dai dai a kasa kamar warce uwarta ta mutu, ya nufi kofa ya fita dakin, bedroom
din sa ya nufa ya bude a hankali yana kallon ciki, fitowar Imaan kenan daga
bathroom ta dauro alwala ita ma, ta wani hade rai ta dau hijab dinta ta sa tana
shimfida darduma, cire makulli yyi ta ciki ya kulle dakin da makullin sannan ya
tafi masallaci bayan ya saka makullin a aljihu. Mujaheed na dawowa masallaci ya
shiga dakin da Safeenah take, kamar yanda ya bar ta haka ya dawo ya sameta, Yana
tsaye dakin yace "Baki ma yi sllhn ba kenan?" Banxa tayi masa tana kuka sosai, ya
tabe baki yace "Xa mu fita in siyo mata few wears coz gaba daya kayanta na gida"
Safeenah ta mike da sauri tana xaro ido tace "Xaku fita fa kace Mujaheed??? Har
xaka fara walakanta ni kenan kake nufi, xaku fita kake ce min fa" yace "You heard
me right, we are going to the market, kuma don't forget cikin one week dinta
muke..." Kallonsa kawai Safeenah take kamar idanuwanta xasu yo waje xuciyarta na
bugawa, yace "Her one week started from yesterday" Bai jira cewarta ba ya fita
dakin ya kulle kofar, imaan na xaune saman darduma ta hade kanta da gado ya sameta,
Yana kallonta yace "We are going out now" Ta dago da sauri tana kallonsa tace "I am
going no where plss" Yyi shiru yana kallonta, sai kuma yace "Ohk dama shopping xamu
je ki yi, bari mu je da Safeenah tayi maki kawai" Mikewa tayi da sauri tace "Tayi
mani a kan me? What's my business with her? Ko ita xata sa kayan da xata min
shopping??" Bata jira cewarsa ba ta nufi kofa ta fice, murmushi yyi ya bi bayanta,
waje ya sameta tsaye jikin motar, ya bude lock din motar ta bude front xata shiga
suka yi ido hudu da Safeenah dake lekosu ta window tana kuka kamar ranta xai fita,
Imaan ta ji dadin hakan har ranta, ta kalli Mujaheed sai kuma ta nufe sa da sauri
tace "Toh ai baka gama saka buttons din ba" Bata jira cewarsa ba ta fara buttoning
din masa shirt dinsa, kallonta yake da mamaki, ta turo baki taki yarda su hada ido
har ta gama sannan ta juya ta koma gun motar ta shiga ta rufe tana satan kallon
windown dakin Safeenah tana d'an murmushi, Mujaheed ya bude gate sannan ya dawo ya
shiga driver seat yana kallonta murya can kasa yace "Kema bari in gyara maki Hijab
din ki" Bai jira cewarta ba ya jawota kusa da shi yana gyara mata hijab duk da bbu
abinda ya samesa, xata turasa sai kuma ta tuna kila Safeenah na nan tana kallonsu,
hakan yasa ta tsaya ta matsa kusa da shi amma bata yarda sun hada ido ba,
unexpectedly taji bakinsa cikin nata, ta xaro ido a mugun tsorace xata kwace kanta
ya ki saketa. Siyayya ba na wasa ba Mujaheed yyi ma Imaan, duk ita ke daukan kome
taga yyi mata, tun daga inner wears, dogayen riguna, kananun kaya, amma fa gaba
daya fuskarta a daure yake sbda abinda yyi mata daxu,
da ta tuna sai ta goge bakin, sau dayawa sai ta dau kayan da yyi mata kyau sai ta
juya gunsa da sauri tana nuna masa kayan tace "Yaya wannan xai min kyau koh??" sai
kuma ta tuna sabon relationship dinsu, a hankali take juya masa baya tana turo baki
bar wajen fuska daure, shi dai sai dai yyi murmushi yana biye da ita, bayan sun
gama da boutique suka shiga shopping mall, gun turarruka ta nufa shi kuma ya tafi
gun kayan shayi don siya masu, Tana cikin daukan turare suka yi ido hudu da farida
dake duba wani turaren a wajen ita ma, xaro ido imaan tayi da mamaki ta nufeta da
sauri tace "Anty Farida" Rungume ta Farida tayi cike da murnan ganinta tace "Imaan,
what are you doing in Zaria?" Imaan na murmushi sosai tace "Ni da Yaya ne Aunty
Farida, dama Zaria gidan ki yake?" Farida da lkci daya fara'arta ya d'an ragu, a
hankali tace "Ehh nan nake, me kika xo yi nan din ke?" Lkci daya fara'ar da ke
fuskar imaan ya bace ita ma jin tambayar da ta mata, sai kuma da sauri tace "Lahh
ni da Yaya ne Aunty, bari in kirasa ku gaisa" Bata jira cewar Farida ba ta bar
wajen da sauri, Farida ta bi ta da kallo sannan ta sauke idonta kasa a hankali,
Mujaheed na duba blue band sanin Imaan na son ci sosai, ta iso inda yake, daga kai
yyi yana kallonta, ta wara ido tace "Yaya I just met Aunty Farida now" da mamaki
yace "Farida? Where is she?" Imaan tace "Wajen perfumes" sai kuma ta kamo hannunsa
kamar xata yi kuka tace "Don Allah Yaya don't tell her that we are married plsss"
da mamaki yake kallonta trying hard not to laugh yace "Why???" Hankali tashe tace
"Wlh abun kunya ne wannan Yaya, ya xa ayi ace wai kai mijina ne bayan kowa ya san
kai yayana ne, don Allah kar ka gaya mata wllh xan ji kunya sosai" Murmushi yyi
yace "Toh na ji, mu je...." Tana rike da hannunsa suka tafi inda Farida take, shi
dai bin ta kawai yake yana kallonta har suka iso wajen, Imaan na kirkiran murmushi
tace "Aunty ga yayan, shi ma yyi aure few months ago, wajen matar ma na xo in mata
kwana biyu"

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

86.....

Farida na murmushi tana kallon Mujaheed tace "Ina yini Dr?" Mujaheed ya mayar mata
murmushin yace "Lafiya lau Farida, kwana da yawa?" Tace "Alhmdllh ya aiki" yace
"Lafiya lau, dama Zaria kike?" Tace "Ehh a nan nake" Ya gyada kai yace "Maa sha
Allah, toh ya mai gidan?" Tace "Yana lafiya lau, tare muke yana waje" Mujaheed yace
"Toh maa sha Allah" Imaan dai sai kirkiran murmushi take tana kallon Faridar,
Farida tace "Yaushe kika ce xa ki koma kaduna?" Imaan ta wara ido tace "Nan da sati
daya idan Allah ya yarda" Farida tace "Amma xa ki xo gidana ai koh?" Imaan tace
"Ehh xan ce Yaya ya kawo ni, ki ba mu address" Farida na murmushi tace "Toh bani
number wayar ki" Imaan tace "Na bar sa a gida, bari ki bani naki inyi saving a
wayar Yaya" daga haka ta karbe wayar hannun Mujaheed ta mika mata, Farida ta amsa
ta sa number ta sannan ta mika ma Imaan, Imaan ta amsa tayi saving number da Aunty
Farida sannan tace "Nagode Aunty sai kin ganni soon" Farida na murmushi tace "Toh
nagode Imaan" daga haka tayi mata sallama, tayi ma Mujaheed ma sallama sannan ta
bar wajen, Imaan ta ci gaba da daukan turarrukan da take so, Mujaheed na bin ta da
ido har ta juyo, suna hada ido ta turo baki tayi gaba ta bar sa a wajen, murmushi
yyi ya bi bayanta, suna isa counter ya biya kudin abubuwan da suka siya gaba daya
aka kai masu mota, har suka isa gida babu wanda yace komai cikin motar, Yyi parking
yana kallonta yace "Ke baki ji kunya ba da kika ce mata wajen matata kika xo?" ko
kallonsa Imaan bata yi ba ta dau ledan turarruka da body cream sai toothbrush da
toothpaste dinta xata fita motar yace "Xa ki san hutu kika xo yi gidana" ita dai
bata tsaya ta sauraresa ba ta wuce ciki, ya fita motar ya tafi ya kulle gate ya
shiga cikin gidan, direct sama Imaan ta wuce ta tadda Safeenah tsaye corridor
idonta yyi jajir sbda kuka, da alama dai jiran haurowanta sama take, tun da suka
hada ido Imaan ta dauke kai fuska daure, Safeenah na kallonta da kyau tace "Mijina
kika yadda aka aura maki dai koh???" Imaan ta juya tana kallonta tace "Mijin mu dai
malama...." Tana fadin haka tayi maxa ta shige dakin ta sa makulli, xuciyar
Safeenah ya dinga tafarfasa tana tunanin me xata ma Imaan taji sauki, wani
murmushin takaici tayi ta juya ta koma ciki, Mujaheed na shiga parlor ya fiddo
wayarsa dake ring, ya d'an yi jim yana kallon Screen din don number Daddy ne,
xaunawa yyi saman kujera sannan ya daga ya kai kunne murya can kasa yyi sallama,
Daddy amsa daga daya bangaren yace "Ya ku ke Muhd?" Mujaheed yace "Alhmdllh Abba,
Ina yini?" Daddy yace "Lafiya lau, su Hadiza xa su kai ma Imaan kaya can gidan
naka, how about the key to the house?" Mujaheed yace "In sha Allah xan kawo
makullin Abba" Daddy yace "Alright, Hadiza tace baka daukan kiranta why?" mujaheed
yyi murmushi sai dai bai ce komai ba, Daddy yace "Kar ka damu ka dauka kaji me xata
ce maka, may be Sunday ma su je tare da Inna" Mujaheed yace "Toh Allah ya kai mu,
nagode" Daddy yace "Ba matsala dai koh?" Mujaheed yace "In sha Allah" Daddy yace
"If there is any you let me know, amma kasan Ummar ka an kwantar da ita asibiti
kuwa?" Mujaheed yyi shiru da farko, sai kuma yace "Not at all Abba" Daddy yace
"Ohk, Alhmdllh da sauki sosai, later xa a sallamosu" Mujaheed yace "Toh Allah ya
sauwake, nagode Abba" Daddy yace "Madallah" daga haka ya katse wayar, mujaheed yyi
dialing number Umma, bayan wani lkci ta dauka, a hankali ya gaisheta ta amsa, yace
"Ashe baki ji dadi ba Umma?" A takaice tace "Wannan ba matsalar ka bace Mujaheed,
kuma shirun da kaji na maka ba yana nufin na hakura da aurenka da tsinanniyar
sauran ciwon nan bane, in sha Allahu ina kara jin sauki xan taho zariar ayi ta ta
kare duk uban da xai faru sai dai ya faru amma wllh baxa kayi aure da yar Aisha ba
in dai ina numfashi a duniya, kai koma bbu raina baxa ka yi ba wllh, don ma kaji da
kyau, kwata kwata ban amince ka hada daki da ita ba...." Tana gama fadin haka ta
katse wayar kitt, Mujaheed ya fi minti goma xaune kansa a jingine da kujera ya
lumshe ido, a hankali ya mike daga karshe ya wuce sama, dakin Safeenah ya shiga, ya
sameta tana xuge jaka bayan ta ciro Hijab, ko kallonsa bata yi ba ta saka hijab
din, ta daga trolley dinta tana ja ta nufi kofa, yace "Ina xa ki" ganin bata da
niyyar tsayawa balle ta basa amsa ya fixgota, ta fashe da matsanancin kuka kamar
jira take tace "Let me Mujaheed, gidanmu xan wuce don wllh baxan xauna da yarinyar
nan ba, I can't stay under the same roof with her, na tsaneta, na tsaneta...."
Katse ta yyi yace "Kin tsane ni kenan, good and fine, you dare cross this house da
sunan wucewa gidanku to a bakin auren ki wllh, kin ji na rantse" daga haka ya
saketa ya fice daga dakin, ta bi sa da kallo baki bude, lkci daya ta xube kasa ta
dinga kuka kamar ranta xai fita. Bayan Magrib da takeaways din abinci Mujaheed ya
shigo gidan, ko kadan bai yarda damuwar da ke tattare da shi ya bayyana fuskarsa
ba, sama ya wuce ya sa makulli ya bude kofar dakin da Imaan take, ya sameta saman
darduma ta idar da sllh, ya ajiye mata leda daya yace "Daxu baki sha drugs din ki
ba why?" Shiru tayi masa, yace "Imaan" ta dauke kai tace "Am not sick" ya fi second
goma yana kallonta sannan ya juya ya fita, mikewa tayi da sauri ta nufi kofarta ta
kasa kunne, ta ji ya bude kofar dakin Safeenah ya shiga, tabe baki tayi ta koma ta
xauna gefen gado fuska daure. Xaune ya samu Safeenah kasan dakin ta jinginar da
kanta da gado ga wayarta a gefenta, kana ganinta kasan ta gaji da kuka, ya ajiye
ledan hannunsa ya karasa ya xauna gefen gadon yace "Kin yi sllh?" Bata ko kallesa
ba balle ta amsa, yace "Let talk Safeenah...." Still bata ce komai ba wasu hawayen
na xubo mata, yayi kasa da murya yace "Yanxu ya kike son ayi Safeenah?" Ta daga kai
tana kallonsa cikin rawar murya tace "Am very serious Mujaheed baxan iya xama da
yarinyar nan ba a gidan nan" Ya d'an yi shiru sannan yace "Mind u, sunanta Imaan ba
yarinya ba" A mugun fusace ta mike tace "What ever" ya dauke kansa yace "Idan baxa
ki iya xama da imaan ba baxa ki iya xama da ni ba kenan ae" Wani kuka ta sakar masa
tana kallonsa, ya mike ya isa gabanta ya kamo hannunta a hankali yace "I have
decided in raba maku gida, ke sai ki xauna nan, ita kuma....." Ta wani xaro ido da
karfi tace "Ka raba mana gida?? Ka raba mana gidan don ka ji dadin cutata, to wllh
baxai yiwu ba" Bai san lkcn da yyi murmushi ba yace "To baxan raba ba, don kada in
cuce ki, amma Ina son don Allah ba don ni ba ki kwantar da hankalin ki, mu xauna
lfya gaba daya, I will neva give imaan space din raina ki... Plss Safeenah kiyi
hakuri ki kwantar da hankalin ki, wannan kaddaranmu ne gaba daya, bana son kina
kukan nan don I am feeling guilt inside me, gaba daya we never saw this coming,
ain't you proud being my first? Kowa xata shigo gidan nan fa a bayan ki take kin
sani, so why disturb ur self, kuma duk yanda kika ce ayi haka xa ayi, don haka kiyi
hakuri wife...." Rungumesa tayi tana kuka sosai tace "Wllh kishin sharing dinka da
wata mace nake Mujaheed, ji nake kamar xuciyata xata fashe saboda kishi" ya rufe
bakinta yace "Aa baxa ki yi sharing dina ba..." Da haka dai Mujaheed ya dinga
lallaba Safeenah har ta d'an hakura ta ci abincin da ya shigo mata da shi, jin lkcn
isha yyi ya mike ya fita dakin xuwa masallaci, for once xae huta da koke kokenta ko
hankalinsa xae kwanta ya samu relieve, he hate it when a lady cries..... Yana
dawowa masallaci ya sameta parlor tayi jigum, shi dai ya san yana tausayinta sosai,
kuma babu abinda ya fi unexpected kishiya ciwo, kishiyar kuma warce tun asali basa
shiri, ya karasa parlon ya xauna saman kujera kusa da ita yace "Kin yi sllhn" shiru
tayi bata ce komai ba fuska bbu walwala, ya kalli movie din da ake a tv ya dau
remote yace "Bari in kai maki wannan series din naki da kike kallo kullum...." Daga
haka ya canxa tashar ya jawota jikinsa a hankali, wani sabon hawaye ne ya fara
sauka idonta, yace "I don't like this tears plss Safeenah, yanxu baxa ki hakura ba
for the sake of the love you are having for me??" Cikin rawar murya tace "Ae nace
maka na hakura" yyi pecking goshinta yace "Toh kar ki sake kukan nan" daga masa kai
kawai tayi, tayi lamo jikinsa, suna ta xaune a haka har kusan karfe goma, jin
footstep a stairs Mujaheed ya daga kai da sauri suka yi ido hudu da Imaan, dauke
kai Imaan tayi, Safeenah na jin tafiyarta ta kara shige masa, Imaan bata sake
kallonsu ba ta wuce kitchen rike da takeaway din da ya kai mata daki, tana ajiye
ledan hannunta ta jingina da cabinet din kitchen din xuciyarta na bugawa, tafi
minti biyar sannan ta fito ta wuce sama da sauri ba tare da ta yadda ta sake
kallonsu ba, Mujaheed ya bi ta da kallon gefen ido... Sha daya saura Mujaheed ya
tafi sama tare da Safeenah bayan an gama series din, ya bude mata kofar dakinta
yana kallonta yace "Good night" shiga dakin tayi bata tanka sa ba ta nufi kan gado
tayi rub da ciki, ya bi ta da kallo sannan ya rufe kofar a hankali, Safeenah ta
sulalo daga saman gadon tana kuka kamar ranta xai fita, wato a dakin Imaan dai xai
kwana kenan yau, tunanin hakan yasa taji kamar ta kurma ihu ko xata samu saukin
xafin da take ji a xuciya. Mujaheed ya bude dakinsa yana kallon ciki, ganin Imaan
ta kashe wutan dakin ya luluba switch din ya kunna, kwance ya ganta ta rufe har
kanta da bargo, ya rufe kofar dakin ya rage kayan jikinsa ya shiga bathroom, wanka
yyi ya fito ya saka pyjamas dinsa sannan ya kashe wutan dakin ya karasa kan gado ya
cire blanket din jikinta murya can kasa yace "Did you perform ablution before lying
down?" Duk da imaan na jinsa taki cewa komai idonta a rufe, ya kai hannu fuskarta
ta mike a fusace tace "Meye haka na fara bacci xaka shigo min daki ka tasheni
Yaya?" Ya d'an shafa kai yace "Dama shigowa nayi in ce maki sai da safe, and to
make sure kin sha drugs din ki" tana kallonsa da idanuwanta da suka yo waje tace
"Ina xaka?" Yace "Wajen matata da kika xo hutu wajenta mana kanwata....." Bai jira
cewarta ba ya juya ya nufi kofa ta bi sa da kallo kamar idanuwanta
xa su yi magana, ko kiftawa babu har ya fita dakin ya kulle kofar a hankali not
making any sound, Imaan ta cire bargon jikinta ta sauko daga kan gadon da sauri....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

87.....
Imaan har ta isa kofa sai kuma ta dakata bakin kofar, ta durkushe kasa ta hade kai
da gwiwa lkci daya ta fara kuka tana jin xafi a ranta, ta fi minti goma wajen kafin
ta mike a hankali ta koma saman gado ta takure waje daya ta rufe fuskarta da pillow
tana shessheka, har karfe daya bata yi bacci ba, daga karshe ta mike a hankali ta
shiga bathroom ta dauro alwala ta fito ta shimfida darduma ta dau Hijab ta fara
sallah, bata san iya lkcn da ta dauka tana sllh ba, daga karshe ta kwanta saman
darduman don har rufewa idonta yake sbda bacci, lkci daya kuma baccin ya dauketa.
Da asuba Mujaheed ya bude kofar dakin a hankali ya shiga ya kulle sannan ya kunna
wutan dakin, kwance ya ganta saman darduma ta rufe fuskarta da hijab, ya isa
gabanta ya durkusa yana kallonta ya sa hannu ya sauke hijab din daga fuskarta,
bacci ya ga take yi, yyi murmushi ya ja dogon hancinta gently, a hankali ta bude
idanuwanta ta daura kansa jin kamshin da ya cika hancinta, sanye yake da jallabiya
ya sakar mata good morning smile ta dauke kai da sauri ta hade rai, yace "Me yasa
kika kwanta kasan tiles da sanyin nan?" Bata tanka sa ba, ya mike yace "It's time
for subhi prayer" still bata ce komai ba ya juya ya nufi kofa, a hankali ta juya
tana kallonsa har ya bude kofar ya fita ya kulle, Mikewa xaune tayi lkci daya
hawaye ya kawo idonta. Har gari ya washe imaan na xaune saman darduma tana azkar
duk da baccin dake fixgarta, amma sai da ta gama ta mike ta hau saman gado nan da
nan bacci ya dauketa, ba ita ta tashi ba sai kusan karfe tara, ta fi minti goma
xaune gefen gadon sannan ta ja tsaki ta mike ta shiga gyaran gadon, tana gamawa ta
cire kayan baccin jikinta ta linke ta dau sabon towel da ya siya mata jiya ta
daura, sannan ta dau brush da maclean ta shiga bathroom, tana daure da towel bayan
tayi wanka ta fito ta dau hijab dinta ta koma bandakin ta fara Hijab din da
detergent, har ta gama sannan ta dauraye bandakin ta fito, ta gama shafe shafenta,
ta feshe turare ta dau daya daga sabbin abaya ta saka ta kara feshe jikinta da
turare sannan ta dau bucket da hijab dinta ke ciki ta fita xata shanya a waje, tun
da ta fito daki ta ke jin kamshin soye soyen da ya cika gidan, ta tabe baki har ta
sauko downstairs, Mujaheed na xaune parlor cikin kananun kaya, Safeenah na kusa da
shi duke a kasa tana setting breakfast da ta gama girkawa, ta wani cakare cikin
riga da wando da ya fito da ainahin komai nata, ta daure gashinta da ya xubo har
shoulders dinta, labari kawai take masa yana kallonta yana kallon Tv, kai kana
ganinta kasan farin ciki ne fal ranta a moment din, murmushi Mujaheed yyi jin
abinda tace yace "To me yasa kika fara ci?" Safeenah da tun sakkowar Imaan suka yi
ido hudu, ta wani juya ido cike da shagwaba tace "Saboda mijina na ci mana, ae duk
abinda kke so dole in so sa ni ma..." Mujaheed kawai gyada mata kai yake yana
murmushi, ta mike ta xauna kusa da shi ta sakale hannu wuyarsa tace "To ka mance
lkcn da kake cewa sai na ci?" Ya d'an bude ido yana kallonta yace "Ni??" Maimakon
ta basa amsa sai kawai ta saka mashi baki a nasa, dauke kansa yake son yi da mamaki
amma ta ki barin yyi hakan, irin kiss din da ta san yake so ta shiga masa, tun yana
basarwa har ya fara give up sai dai bai mayar mata ba, Tun da Imaan taga haka bata
sake yarda ta kalli direction din su ba, sai dai da kyar take daga kafarta har ta
isa kofar parlon ta bude a hankali ta fita xuciyarta na bugawa, Jin sound din bude
kofa Mujaheed yyi saurin mikewa xaune yana kallon kofar amma tuni ta rufe, Safeenah
tayi lamo jikinsa yana kallonta yace "Wa ya fita?" Ta langwabar da kai tana juya
ido a hankali tace "Mu nawa ne gidan yanxu?" Janyeta yyi jikinsa bai ce komai ba,
tana murmushi ta xamo kasa tace "Should I make the coffee for you now?" A takaice
yace "No" ko kallonsa bata yi ba ta shiga hada masa coffee din a mug, Duk da yanda
Imaan ta so kar tayi kukan da ke cinta a rai amma hakan ya faskara, tana gama
shanya hijab din ta xauna saman dakali ta hade kai da gwiwa ta fashe da matsanancin
kuka tana jin xuciyarta na mata xafi, ita kanta bata san dalilin abinda take ji a
ranta ba a lkcn, bata yi minti biyar wajen ba ta mike a hankali tana goge idonta,
ba karamin sanyi ta ji ba kukan da ta yi, ta dau bucket tana tafiya a hankali har
ta isa entrance din gidan, nan kuma gabanta ya shiga faduwa coz she can't imagine
seeing what she just saw for the second time, baxata iya withstanding dinsa ba,
slowly ta bude kofar just to keep them alert, sannan ta shiga parlon amma bata
yarda ko da wasa ta kalli inda suke ba xuciyarta na bugawa har lkcn, ta wuce sama
kamar me counting steps dinta, Mujaheed ya bi ta da kallon gefen ido, Safeenah dai
tana aikin hada shayinta da xata sha xuciyarta fess tana satan kallonta, Bayan
kusan minti bakwai Mujaheed ya mike Safeenah tace "Ina kuma xaka ga breakfast na
xuba maka darling" Ba tare da ya kalleta ba ya fara tafiya yace "Mu kadai xa mu yi
breakfast din??" Ta mike da sauri ta sha gabansa ta riko hannunsa tace "Haba dear,
shine sai ka je kiranta da kanka, ai ko ni sai in je in kirata dama ba mu gaisa ba
yau, But you know what baby?? wllh duk naji abubuwan da ka gaya min jiya da daddare
kuma in sha Allah I will adhere, I will try my best mu xauna lafiya da ita, na
yarda wannan kaddara ta ce, kuma babu bawan da ya isa ya wuce kaddarar sa, na ji na
yarda xan dau Imaan matsayin kanwata kamar yanda kace, don haka give me the space
to start doing this from today, xan je mu gaisa in kirata yanxu, daga nan ba sai mu
fara fahimtar juna ba?" Tana masa lallausan murmushi tana murxa hannunsa ta kare
maganar, shi dai kallonta kawai yake, bata jira cewarsa ba ta sake sa ta wuce sama
tana murmushi, a hankali ta bude kofar dakin Imaan ta shiga bbu ko sallama, Imaan
dake kwance ta rufe fuskarta da pillow tana shessheka a hankali, ta ki dagowa duk
da taji an bude kofa dakin, Safeenah tayi wani dariya tana kallonta daga head xuwa
toes, Imaan ta bude ido da sauri jin dariyarta xuciyarta na bugawa ,sai dai still
bata dago kanta ba, Cike da isa Safeenah tace "Kinga consequence din auren mijin
wata koh??" Imaan dai bata dago ba kuma bata ce komai ba, Dariya Safeenah ta fara
yi sosai tace "Ban taba ganin amaryar da miji bai dokinta sai a kan ki, har xai
tsallake ki ya tafi gun uwar gidansa ya kwana a faranta masa rai, kina gidan kuma
kwanan ki, isn't this a big shame to you? To what will one expect bayan kowa yasan
tusa masa ke kawai aka yi ya aure ki, kuma shi din mijina dama a ko da yaushe mai
biyayya ne, yyi biyayya ya aure ki ba don yana so ba sae don bbu yanda xai yi, to
abinda baki sani ba mijin wata mijin aro ne, yanda kika shigo gidan miji na a
xabure haka xa ki fita a xabure ki bar min gidan mijina, don ko mahakaci yasan wllh
tllh tusa masa ke aka yi, baya yin ki ko na second daya, da yana yin ki ko yaya ne
baxai ki kwana dakin ki ya tafi dakin first wife dinsa a daren ki na farko gidansa
ya kwana ba, don haka tun yanxu yarinya ki fara sanin matsayin ki gidan nan, I
think that is all I have to say to you now, and can you kindly come downstairs for
breakfast, he instructed I come and get you don baxai iya hawa sama kiran ki
ba...." Imaan ta goge idonta da pillow ta mike xaune tana kallon Safeenah tana
murmushi tace "Xan nuna maki ke ce kika auri mijin wata ba ni ba, kuma aron nasa ma
ni ko na second daya baxan baki ba, nan ba da jimawa ba xa ki san ba tusa masa ni
aka yi ba, shine ma mai tusa kansa gareni, kuma xan nuna maki ke aka tusa ma
Mujaheed yyi biyayya ya aura ba ni ba, sai ma kinsan ni ce silar auren ki da
Mujaheed xa ki dawo hankalin ki...." Safeenah tayi wani dariya lkci daya ta daure
fuska tana huci tace "Karya kike wllh, ke dai ce kika aura mijin wata mijin aro,
Mujaheed ba class din ki bane bbu abinda xai ci dake, tsautsayi ne kawai ya ja
auren ku, amma wllh ba mijin ki bane shi din...." Tana magana hawaye ya cika idonta
duk da daurewan da tayi kada hakan ya faru, tana girgixa kai tace "Wllh ba mijin ki
bane shi din, ke kin kasance makwadaiciya me son abun duniya, kuma kyan ki ire iren
su Bulasawan, don su xa su fi iyawa da sauran ciwo, tsautsayin da ya hana d'an
gidan Bulasawa auren ki shi xai kara sa mijina ya sake ki shi Bulasawan ya aure ki
kuje can ku karata, in sha Allahu nan ba da dadewa ba xa ki bar min gidana da
mijina ki tafi, ba D'an gidan Bulasawa ba, in har xa ki iya auren shi Bulasawan ma
da kansa ki tafi ki auresa, banxa kawai ragowar ciwo...." Imaan tayi murmushi tace
"Son da mijinki ke ma ragowar ciwo wllh da kin samu just 10% na kalan son daga
garesa da ba haka ba, mark my words.... sai kin xama abun tausayi a gidan nan in
dai ni ce, banxa kawai jahila mahaukaciya..." Safeenah da ta yo waje da ido jikinta
na rawa tace "Ni kike xagi???" Imaan ta sakko da kafafuwanta daga saman gadon dai
dai shigowar Mujaheed dakin, ta mike tana kallonta tace "An xage ki din kiyi abinda
xa ki yi, karya nake ke ba jahila bace? Ko kin ta6a leka islamiyya??" Kallonsu
Mujaheed ya tsaya yi da mamaki, Safeenah na kallonsa ta fashe da matsanancin kuka
tace "Kana ji ko dear, ni wai take ce ma jahila mahaukaciya daga na shigo na
gaisheta nace ta sakko mu yi breakfast, meye laifina a nan Mujaheed don na shigo
nace ta sakko mu karya..." Kuka take sosai tana kallonsa, Wani dogon tsaki Imaan ta
ja tace "Makaryaciyar banxa kawai" daga haka ta nufi bathroom kamar xata tashi sama
ta shige tayi banging kofar da karfi, Mujaheed da ya bi ta da kallo baki bude ya
mayar da dubansa kan Safeenah dake kuka sosai, karasawa yyi kusa da ita a hankali
ya jawota jikinsa murya can kasa yace "I am happy da baki kulata ba, kinga yarinya
ce, she still don't know what she is doing, but I will teach her discipline" daga
haka ya ja ta suka fita dakin tana shessheka....
Abba ne tsaye parlon Inna tare da Mama Hadiza da ta rungume hannu, a fusace Inna
tace "In har baxan tafi da kayan sawa ba to wllh sai dai kowa ya fasa xuwan a
hakura kawai, ya xa ayi in tafi waje me nisa har Zaria ban je da kaya ko kala uku
ba, Ni fa ba kwana nace xan je in yi kamar gantalalliya mara mafadi ba, amma ai
yana da kyau duk matafiyi ya dinga yawo da kaya sbda bacin rana, kaji min dai sai
kace kun fi ni sanin abinda nake, wllh ban taba tafiya bbu jakar kaya ba ko da kuwa
awa daya xan je inyi a waje, sabida fatara sai in tafi da xanin jikina kadai ina
yawo a garin zaria kamar almajira..." Abba yace "Toh inna tafiyar da xa aje a dawo
a ranan ina amfanin tafiya da kaya? Me xa kiyi da kayan, Da driver fa xa ku je ku
dawo" Inna tace "Yau naga jaraba, Ina ruwanka da rayuwata ne Ahmadu, Kai xaka yi
tafiya ko ni? Yanxu idan na bi hanya Ina ta kwarara masu amai a mota kayan Imaan ko
na Safara'u xan je in canxa a gidan??" Mama Hadiza tace "Zaria fa xa mu je ba Lagos
ba Inna" A mugun fusace inna tace "Ko maraban jos xa mu ba ruwan ki kiyi ta kanki,
bbu shegen da ya isa sa ni in fita gidan nan da xanin jikina kadai kamar a kaina
talauci ya kare..." Daddy ne ya shigo parlon da sallama shima yyi shirin komawa
Abuja ranan, yace "Har yanxu ba ku fito ba Inna..." Inna tace "Ina fa xan fito
Bukar, ai tafiyar nan ina jin babu shi don ni dai baxan bi hanya bbu kaya ba
gaskiya, Kai ko da ban yi amai ba a hanya to ni nasan kafin mu isa Zaria xan jike
shataf da gumi, to uwata ce min tayi je ki kya gani da xan xauna da kaya ina warin
xufa Bukar???" Daddy yace "Haba inna sai kace warce xata sokoto ko gombe, nan nan
Zaria fa xa ku, ku dawo anjima, idan ba xama kike son xuwa yi a gidan ba ina
amfanin tafiya da kaya?? Sai dai in xauna masu kike son yi kawai, amma sau nawa
kike xuwa kano kice ke ko jaka baxa ki dauka ba? Gashi har rana yyi ba ku kama
hanya ba, hakan is not good" shiru Inna tayi bata ce komai ba sai yan idanuwa,
Daddy ya juya ya fita parlon, Mama Hadiza ta dau warmer dake cike da dambun nama da
Inna tayi ma Imaan ta fita parlon tace "Muna jiran ki a mota" Abba na kallon Inna
da ta sunkuyar da kai a hankali yace "Ae sati uku xa su yi xarian sai su dawo
kaduna, idan ya so sai ki..." A fusace inna tace "Rufe min baki malam, Ina ruwana
da ko kwana nawa xa su yi a Zaria? Ko nace maku xuwa xan yi in xauna masu kamar
shashasha tsofe tsofe da ni, me Mujaheed da Imaan xa su bani wanda Allah bai ban
ba? Yaran da aka ma auren dole auren jaraba wa yasan halin da suke ciki ma yanxu,
wllh In don ta kai da Bukar ne ni baxan ma je ba don baku da kirki barin wannan
mutumi Bukar, da 'yar sa ce kadai a gidan wllh na ma fasa xuwan gaba daya, to amma
ni yanxu gun Mujaheed kawai xanje ba gunta ba wllh, bbu ruwana don ubanta ba ma son
xuwa in je gidan yake ba, ubanta ba shi da kirki" tana fadin haka ta mike ta fice
daga parlon ba tare da ta dau jakar kayanta kusan kala shidda da ta hada ba a Ghana
must go.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

88....

Safeenah na kitchen tana wanke wanke ranta fari fess ko kadan bata ji haushin xagin
da Imaan tayi mata ba ganin Mujaheed bai yi supporting dinta ko na second daya ba
sannan ya yadda da tsarin da tayi masa, sai murmushi take ita kadai ganin abubuwan
na tafiya yanda dai take so kafin Mummynta ta iso gidan, Mujaheed na xaune parlor
idonsa a kan tv amma bai ma san me ake yi ba, gaba daya hankalinsa na sama, can ya
kalli breakfast da ya ajiye Safeenah ta bar ma Imaan a parlon sannan ya kalli
agogo, karfe goma har ya gota hakan yasa ya mike ya tafi kitchen don daukan cup da
spoon ya dau tray ma, Safeenah na kallonsa da mamaki tace "Me xaka yi da su kuma
dear?" Yace "Imaan haven't Breakfasted..." dauke kai tayi ta wani hade rai tana
dauraye plate din hannunta tace "Toh ai idan tana jin yunwa da ta sakko tunda mun
ajiye mata mun fita hakkinta, may be she isn't hungry yet" shi dai ba kalleta ba
balle ya tanka ta ya fita kitchen din, shayi ya hada cikin cup a parlorn don kayan
shayin na ajiye har lkcn, ya dau plate din dankali da kwai ya daura kan tray da cup
din shayin sannan ya wuce sama, duk Safeenah na lekansa daga kitchen ko kiftawa
bbu, lkci daya gaba daya mood dinta ya canxa ta ajiye plate din hannunta ta fito
kitchen din ta bi sa da kallo xuciyarta na tafarfasa, Mujaheed ya murda kofar dakin
ya shiga ciki sannan ya kulle, xaune ya sameta ta jinginar da kanta da gadon dakin,
ya ajiye plate din hannunsa yana kallonta, ta mike ba tare da ta yadda ta kallesa
ba xata shige bathroom ya rikota, fashe masa da kuka tayi tace "Ni wllh ka mayar da
ni gidanmu baxan kara kwana gidan nan ba, idan ba haka ba inyi wucewata da kai na"
Ya rungumeta yace "Da aka yi maki me?" Kwatar kanta take son yi a fusace amma ya ki
saketa, yyi murmushi murya can kasa yace "Upon rashin kunyar da kika ma matata ba
mu ce maki komai ba kuma kike kuka??" Turasa tayi iya karfinta tace "Ae dama ni ba
matar ka bace sai ita...." sosai ta basa dariya ya dake bai yi ba yace "Daga
kanwata kuma kin dawo matata, when hakan ya faru ban sani ba?" Struggling ta dinga
yi xata kwace kanta amma ya ki saketa, ta fashe masa da kuka sosai tace "Wllh duk
abinda kake min sai na gaya ma Abba da Inna, har...." Xaro ido tayi ganin abinda
yake mata da sauri tace "Ha'an meye haka Yaya??" Ya lumshe ido bai ce mata komai ba
yana ci gaba da kissing duk jikinta as if his life depend on it at that moment,
turasa ta dinga yi jikinta na 6ari, lkci daya ta tsorata cikin rawar murya tace "Ka
sakeni plss bana so Yayaaa, what's this you are...." ya kankameta making the affair
more deeper and hotter, daga haka kuma bai kara bata chance din magana ba, iyakar
tsorata Imaan tayi a lkcn, it's something that just came all of a sudden, duk
wannan abun kuma yaki bude ido balle ma ya kalleta, gaba daya kafafuwanta suka kasa
daukarta ganin durkusawa take son yi ya kwantar da ita saman gado, going further
from where he stopped, lkci daya ya bude idonsa da suka sauya kamanninsu yana
kallonta, ya dagota da sauri yace "Imaan, Imaan..." Kokarin jan numfashi take tana
komawa baya, ya riketa yana kallonta shi ma yana sauke numfashin, har sai dai ya ga
ta nutsu gaba daya numfashinta ya dawo normal, sai kuma ta fixge hannunta hawaye
cike idonta ba tare da ta yadda sun hada ido ba xata sauka saman gadon kana ganinta
kasan a tsorace take, ya mike xai riketa ta fashe masa da kuka jikinta na rawa tana
komawa baya tace "Don Allah Yaya ka bari, wllh bana son haka, kayi hakuri plss" yyi
kasa da murya yace "To sakko kiyi breakfast" xuciyarta na bugawa har lkcn taki
kallonsa, kamar yanda shi ma bai yarda ya kalleta ba, ganin tray din breakfast din
dake kasa lkci daya ta hade rai tace "Ni baxan ci ba" da sauri Kuma a tsorace ta
sauka daga kan gadon kafin ya iso kusa da ita tace "Wayyo Yaya don Allah kayi
hakuriii" Yana kallonta da lumsassun idanuwansa yace "Toh xauna kiyi breakfast" ta
make kafada tace "Ni dai ka siya min wani baxan ci wannan ba wllh" tana fadin haka
ta juya masa baya, murmushi yyi yana shafa kansa yana kallonta daga sama har kasa,
murya can kasa yace "Koh..." Ba tare da ta juyo ba tace "Ehh ni dai ka siya min
baxan ci Wannan jagwalgwalon ba" walking gently ya karasa kusa da ita tana jin
tafiya ta juya ta bar wajen da sauri tace "Yayaaa" murmushi kawai yake yana shafa
kansa yace "Toh shkkn bari in je in siyo ma kanwata wani abinci..." Da sauri tace
"Ae tare xa mu je in nuna maka abinda nake son ci" duk wannan abun taki yarda ta
hada ido da shi, a hankali yace "To mu je" har xata bi ta gabansa sai kuma ta koma
baya da sauri kamar xata yi kuka tace "Yayaa" ya buda ido yace "What?" A hankali
tace "Kar ka ta6a ni plss" Yana murmushi yace "Ehh baxan ta6a ki ba yanxu sai
anjima da night koh?" sosai gabanta ya fadi, kamar xata yi kuka ta kallesa a karo
na farko, shi ma yana kallonta yace "Ba sai in je in ta6a warce take son in ta6a ta
ba..." Wani kallon da yyi mugun basa dariya tayi masa, tace "It's not new ai, tunda
jiya ma a dakinta ka kwana" Da mamaki yake kallonta yace "Dakinta kuma?" Bata ko
kallesa ba ta fice daga dakin ya bi ta da kallo, sannan ya duka ya dau tray din da
ya shigo da shi ya fita dakin, Safeenah na xaune parlor har ta gaji da kallon
stairs sai ga imaan ta sakko, ko kallonta Imaan bata yi ba ta tafi waje dauko Hijab
dinta da ta shanya tunda shi kadai take da a gidan, Safeenah ta bi ta da kallon
tsana xuciyarta na kuna, fitowar Mujaheed ya sa ta mike fuska daure, yyi mata kallo
daya ya wuce kitchen, bin bayansa tayi tana kallon tray din da ya ajiye yace "I
will be back soon..." Da sauri tace "Ina xa ka?" Yace "I want to get her something
to eat..." Safeenah ta daure fuska sosai tace "Wannan fa?" Yace "Tace baxa ta ci
ba" Safeenah tace "Toh bari in shirya, nima ai ba wani breakfast din kirki nayi ba
coz kasan bana cin dankali" Ya buda ido yace "Dankalin kuma da kika ce na koya maki
ci daxu??" Ko tankasa bata yi ba ta tafi dauko Hijab a sama, bin ta yyi da kallo
yana shafa kai, can ya dau makullin motarsa ya fita ya tadda imaan tsaye jikin
mota, yace "Xa mu je da Safeenah, she will be coming out...." Bata jira ya kai
karshe ba tace "Toh ku je" daga haka ta wuce sa xata koma ciki ya rikota da sauri
ya jawota jikinsa a hankali, murya can ciki yace "Haba wife..." Kamar xata yi kuka
tace "Wllh baxata bi mu ba, sai dai in fasa xuwa ai ba kwanan ta bane" sosai ta
basa dariya ya daura fuskarsa saman kanta yace "Kwanan ki ne kenan kanwata?" Tana
kallon entrance din shiga gidan tace "Ehh" murya can kasa yace "So we are sleeping
together today?" Tace "Ehh" lumshe ido yyi yace "Da gaske?" Tace "Ehh" yace "Baxa
ki ji tsoro ba?" Tace "Ehh" Magana yake mata amma duk hankalinta na kofar tana
jiran fitowar Safeenah, Mujaheed yace "Ke fa kika ce min Ehh da bakin ki" ta kara
cewa "Ehh" dago kanta yyi yana kallon kyakkyawan fuskarta sanin she isn't listening
to him, dai dai nan Safeenah ta fito sanye da hijab hannunta rike da waya, A
hankali ya sake Imaan jin footstep dinta, ya karasa gunta yace "You say what u want
to eat sai in siyo maki kawai" tana masa wani kallo tace "Why??" Imaan na kallonta
da kyau tace "Saboda ba kwanan ki bane, ki jira after a week sai ki bisa a mota not
today" Da mamaki Safeenah ke kallon Imaan sannan ta kalli Mujaheed, Mujaheed yace
"Don't worry i will get you pizza, guess that is what u want for breakfast" daga
haka ya nufi gate ya bude sannan ya dawo ya bude lock din motar, Imaan ta bude
front seat taki yarda su hada ido da Safeenah ta shiga motar ta rufe door din,
Mujaheed ya shiga maxaunin driver ya tada motar ya fita compound din sannan ya
sauka ya rufe gate ya koma cikin motar suka bar layin, ya rasa me yasa yake
murmushi shi kadai, Imaan dai bata yarda sun hada ido ba, sun dan yi nisa murya can
kasa yace "But ain't we suppose to take our bath before coming out?" Imaan ta
kallesa da sauri tace "Bath? ai ni nayi wanka" yyi murmushi yace "Ohk tot ba ki yi
ba ai" dauke kai tayi ta hade rai ta ki cewa komai, A wani babban eatry ya siya
mata abincin sannan ya siya ma Safeenah ma, ita dai bata ce masa komai ba, bayan
sun bar eatry din tace "Yaya ka bani waya in kira Anty Farida in ji ko gidanta bbu
nisa sai ka kai ni in gaisheta" yace "Not today" 6ata fuska tayi kamar xata yi kuka
tace "Yaya plss, ni dai ina son in je" Bata jira cewarsa ba ta fara laluba
aljihunsa tana neman waya, buda ido yyi sosai yana kallonta har ta cire wayar and
he couldn't stop looking at her, ta bude wayar ta fara shiga gallery, hotunan
Safeenah da take dauka a wayar ta gani sun fi a kirga, lkci daya tayi marking dinsu
gaba daya ta jefa su a kwandon delete, sannan ta shiga contact, tana nemo lambar
farida tayi dialing ta kai kunne, Bayan few seconds Farida tayi picking call din,
bayan sun gama gaisawa Imaan tace "Aunty ki turo address din Yaya xai kawo ni yanxu
ae kina gida koh?" Farida tace "Ehh Ina nan, bari in turo" imaan ta katse wayar
tana kallon mujaheed dake driving idonsa a kan titi, yace "Xa mu yi baki daga kd
fa" Imaan tace "Su waye?" text din farida na shigo wayar hannunta ta bude tana
kallon address din sannan ta nuna masa, ya kalli wayar sannan yace "Baxa ki bari
gobe in kai ki ba?" A takaice tace "Noo" yyi murmushi ya dau hanyar unguwar da
Farida ta turo, tafiyar kusan minti sha biyar suka yi suka iso layin, yyi parking
dai dai house number din, Imaan tayi dialing number din Farida tana dagawa tace
"Aunty ina waje" Farida tace "To ki shigo ciki ina ce tare ku ke da Mujaheed din?"
Imaan tace "Ehh tare mu ke" Farida tace "Toh ku shigo sai su gaisa da Mai gidan
yana nan" Imaan tace "Toh" sannan ta kalli Mujaheed, yace "Ki shiga ki fito ina
jiran ki" tace "Baxa ka shiga ba?" Yace "Yes" ta hade rai tace "Ayya, ita fa da
kanta tace xa ku gaisa da mai gidanta, or are you feeling anything deep down?" Ya
kalleta da mamaki yace "Like what?" Ta wara masa ido tana murmushi tace "Like kishi
or so" Yar dariya yyi bai shirya yin hakan ba yace "Not when I am having you" turo
baki tayi tace "Not when you have
ur wife dai" ya ja hancinta yace "And you are the wife koh" ta make kafada tace
"Ni ba matarka bace, matarka na gida" daga haka ta fita motar, ya sakko shi ma yana
kallonta yace "Toh xa mu raba wannan gardaman anjima da daddare" da sauri ta
kallesa amma bata ce komai ba ta nufi gate din gidan ya bi bayanta yana murmushi,
Mai gadi ne ya bude masu gate din suka shiga, Mujaheed ya tsaya compound din gidan
yace "I will wait here" Imaan ta tafi kofar shiga parlon ta danna bell, Farida ta
bude kofar ganinta tayi murmushi sosai tace "Welcm imaan ina yayan naki?" Imaan ta
mayar mata da murmushin tace "Wai baxai shigo ba yana waje" Farida tace "Na xata da
aunt din ta ki xa ku xo ai" Imaan tayi yake tace "Ya ajiyeta a wani anguwa ne"
Farida da ta hango Mujaheed tace "Dr ka shigo mana xa ku gaisa da Mai gidan ne"
Mujaheed yace "Ohk" daga haka ya fara tahowa, Farida ta kama hannun Imaan suka
shiga ciki, tarba sosai Farida da mijinta suka yi masu, Mijinta Dr Khaleel na
kallon Mujaheed yace "Toh ya madam baku xo da ita ba su yi xumunci da Farida.. "
Mujaheed ya d'an yi murmushi yana kallon Imaan, Imaan ta d'an marairaice masa tana
girgixa masa kai a hankali alamar kada yace komai, Farida dai sai kallonsu take
haka ma mijin nata, Mujaheed ya shafa kansa still smiling yace "Gata nan xaune ai"
Farida ta dinga kallon Imaan da mamaki ko kiftawa babu, Mijin yace "Maa sha Allah,
auren xumunci kenan ku ka yi, Farida ce min tayi sistern ka ce" Mujaheed ya gyada
masa kai yace "Sure, auren gida ne" Farida dai sai kallon Imaan da taki dago kai
take ta kasa cewa komai, Nan dai Mujaheed da ko a jikinsa suka dinga fira da mijin
Farida, Farida ta mike daga karshe tana kallon Imaan a hankali tace "Mu tafi ciki
Imaan" mikewa Imaan tayi Mujaheed ya bi ta da kallo yana murmushi ta balla masa
harara kamar xata yi kuka ta bi bayan Farida, suna shiga daki Farida ta kulle kofa
ta juyo tana kallon Imaan da sauri tace "Da gaske mijin ki ne Mujaheed yanxu
Imaan?" Imaan ta kasa cewa komai lkci daya hawaye ya kawo idonta, Rungume ta Farida
tayi cike da murna tace "Kai, amma i am very happy for Imaan, kinyi dacen miji
Imaan...." Imaan dai bata ce mata komai ba hawayen dake idonta ya sakko Farida na
kallonta da mamaki tace "Kuka kuma? Baki son auren ne Imaan?" Imaan ta xauna gefen
gado tana goge hawayen idonta tace "Fasa aure na aka yi aka hadani da Yaya..."
Farida ta dawo gefenta tana kallonta cike da mamaki da kuma tausayi tace "Allah
sarki, ban ji labarin ma Imaan, but put this in mind Mujaheed shine mafi alkhairi
gare ki shi yasa hakan ya faru Imaan, kin fi kowa sanin halin Mujaheed fa..." Imaan
ta fashe da kuka tace "To amma yaya na kuma Anty Farida?" Farida bata san lkcn da
tayi dariya ba sosai ta kamo hannunta tace "Toh ai ya fi dadi irin wannan auren
Imaan, Kinga sai kiyi ta xuba masa shagwaba kamar yanda kike masabda hujja
yanxu...." Imaan ta marairaice tace "Allah Aunty kunya fa nake ji" Farida tayi
murmushi tace "Imaan kenan, kin san da dadewa na taba tunanin anya ba sonki
Mujaheed yake ba, coz care din da yake baki is too much, kuma har muka rabu da
Mujaheed ban taba kin yarda cewar baya son ki ba, ni nasan akwai abu a xuciyarsa
game da ke, may be saboda mum dinsa yayi ta boyewa, amma ban taba jin kishin ki dai
dai da na rana daya ba, cikin kaninsa ma duk mun fi sabawa da ke, sai ranan da ya
xo gidanmu na karshe yake ce min kilan wataran ya hada ni da kanwata, nasan kuma ke
yake nufi a lkcn" Imaan dai sai kallonta take, Farida tace "Amma sun rabu da matar
da Ummarsa ke son ya aura koh??" Imaan ta tabe baki tace "Tana nan, tare ma muke
yanxu, wllh Aunty Farida bana sonta" Farida ta xaro ido tana kallonta, can tace
"Tana nan?? To yau kwananku nawa da auren?" Imaan tace "Gobe Friday sati daya, amma
yau kwanan mu daya a Zaria" Farida tace "Kwananki nawa da tarewa?" Shiru Imaan tayi
sannan a hankali tace "Just two..." Farida tayi murmushi tace "Toh ai babu xancen
wani kunya tsakanin ki da Yaya yanxu koh?"

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah


Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number
07087865788

89.....

Murmushi Imaan tayi ta rufe fuskarta jikin Farida a hankali tace "A'a akwai mana
Aunty" Farida ta dinga kallonta kafin tace "Toh kuwa idan kika tsaya jin kunya
kishiyar ki xata kwace maki Yaya kina ji kina gani" Imaan ta dago tana Kallonta,
Farida tace "Kwarai kuwa, kunyar me xa ki ji kuma bayan kun riga da kun xama daya
yanxu" Imaan kamar xata yi kuka tace "Wllh Aunty kunyarsa ni dai nake ji ban san ya
xan yi ba" duk da ta ba Farida dariya, Farida ta daure fuska tace "Kunya bayan ya
riga ya kwana dakin ki?" Imaan ta girgixa kai tace "A'a ni bai taba kwana daki na
ba" Farida tace "Kika ce kwanan ki nawa da tarewa yanxu?" Imaan ta buda ido sosai
tace "Aunty jiya fa muka xo nan garin" Farida tayi shiru sannan tace "Kuma bai
kwana dakin ki ba?" A hankali Imaan tace "Ehh kila dakin matarsa ya kwana jiya, don
daxu da safe ta shigo tana ce min wai bata ta6a ganin amaryar da miji bai kwana
dakinta ba ranan farko sai dakin uwar gidansa, har tana ce min mijin wata na aura,
kuma mijin wata mijin aro ne" da mamaki Farida ta dinga kallonta, can tace "Toh shi
me ya hanasa kwana dakin na ki?" Imaan ta tabe baki tace "Ni nasan sbda jiya da
muka hadu da ke a mall nace maki hutu na xo gun matarsa, shine da ya shigo da
daddare yace min to xai tafi wajen matarsa ni kuma ban ce masa komai ba har ya
fita..." Farida tayi murmushi tace "Toh ki maida hankalin ki imaan, idan ba haka ba
kuwa you will regret it duk da ban san kishiyar nan taki ba ga dukkan alama makira
ce, kuma Mujaheed da na sani dai baxai taba kwana dakinta yasan ba ranan ta bane,
Mujaheed yana da addini sosai ya san me yake, sai dai idan ya canxa ne daga yanda
na san sa a da, yanxu ki bude kunnuwan ki sosai ki ji abubuwan da xan gaya maki,
idan kuma ki ka ki aiki da su toh kina tare da dana sani wanda ba shi da amfani, ko
tantama babu ke Mujaheed ya fara so kafin first wife dinsa, that is if yana ma
sonta kenan.... Imaan if I am not mistaken babu abinda ya shiga tsakanin ki da
Mujaheed har yanxu koh?" Imaan ta sunkuyar da kai bata ce komai ba, Farida tayi
murmushi tace "Toh ki saurari duk abinda xan gaya maki yanxu...." a hankali Imaan
ta kalleta tace "Toh" Farida bata fito bedroom dinta ba sai kusan sha biyu na rana
shi ma don Imaan tace mata yunwa take ji bata yi breakfast ba shine ta fito hada
mata breakfast, Har lkcn Mujaheed na parlor tare da Dr Khaleel da bai gajiya da
labari, shi dai gaba daya hankalinsa yyi kan Imaan sanin bata yi breakfast ba har
lkcn, Farida tayi murmushi tana kallonsu tace "Sannun ku da hutawa" Mujaheed na
kallonta yace "You tell imaan lkci ya wuce fa, this is after 12" Farida tace "Haba
nan da bayan azahar ba sai ku wuce ba Dr, ni ban gaji da ganin kanwata ba, kayi
wucewarka kawai anjima xa mu maida ta gida...." Dr Khaleel na kallon Mujaheed yace
"Ba yini ku ka xo yi mana ba dama Dr?" Mujaheed yyi murmushi yace "Xa mu yi bak'i
ne daga kaduna, suna ma hanya yanxu" Farida dai bata tanka sa ba ta shiga kitchen,
eggs ta soya ma Imaan, ta hada mata shayi mai kauri, ta debar mata pepper soup din
da tayi da safe sannan ta dau bread duk ta daura su kan tray ta fito kitchen din,
ganin abinda ke hannun Farida hankalin Mujaheed ya kwanta don shi damuwarsa kenan
dama, daki Farida ta kai mata abincin ta ajiye saman carpet, Imaan ta sakko kasa,
Farida tace "Bari inje in daura white rice, nayi stew daxu da safe" Imaan tace
"Toh" daga haka Farida ta fita dakin, a hankali Imaan ke shan shayin hannunta, da
ta tuna wasu daga abubuwan da Farida ta gaya mata sai tayi murmushi ita kadai, wani
kuma ta turo baki, wani kuma idan ta tuna a ranta tace tabdi, da tuna wai Safeenah
xata iya kwace Yaya ya daina kulata sai ta hade rai, shayi kadai ta shanye cikin
abubuwan da Farida ta kawo mata, sannan ta mike ta dau tray din ta fita don kai wa
kitchen, tunda ta fito Mujaheed ke kallonta, suna hada ido ta sunkuyar da kai ta
karasa cikin kitchen din ta ajiye tray din, Farida dake wanke wanke tace "Toh baki
ci egg din da yawa ba ai Imaan" Imaan tace "Aunty na koshi wllh" Farida tace "Toh
nasan Mujaheed xai ce xa ku wuce yanxu, ki tafi daki ki harhada duk abinda na baki
a leda, kin xo da jaka ai?" Imaan ta girgixa mata kai, Farida tace "Ohk toh ki tafi
dakin ina xuwa yanxu" Imaan na fitowa parlor suka kara hada ido da Mujaheed da ya
mike tare da mijin Farida xa su wuce masallaci don lkcin sllh yayi, Yana kallonta
yace "After prayer xa mu wuce" ba tare da ta kallesa ba tace "Toh" sannan ta wuce
ciki, ba a dau lkci ba Farida ta shigo dakin, daya daga sabbin jakanta na aure ta
ciro ta kwashe gaba daya kayan da ta debar ma Imaan ta xuba a ciki tace "Hope you
remember all what I said??" a hankali Imaan ta gyada mata kai, Farida tace "In sha
Allah may be next tomorrow xan xo gidan naku kin ji?" Imaan ta marairaice tace
"Aunty me yasa baxa ki xo gobe ba?" Farida tayi murmushi tace "A'a gwara dai jibin,
in sha Allah xan xo kanwata" Imaan tace "Toh Allah ya kai mu, Aunty ban xo da
Hijabs dina daga gida ba, did you have hijab to give me in dinga sllh da shi, am
having just this one I am wearing" Farida tace "Ohk" mikewa tayi ta bude daya daga
akwatunanta ta fiddo sabon hijab a leda tace "Sai dai bai kai kasa ba nasan ke har
kasa kike sa wa" Imaan tayi murmushi tace "Nagode Aunty bari in yi sllh kafin ya
dawo...." daga haka ta mike ta shiga bayi don dauro alwala. Sai karfe daya Imaan
suka bar gidansu Farida bayan Farida da mijinta sun rakosu har bakin mota, a back
seat Imaan ta ajiye warmer din abincin da Farida ta tilasta mata sai ta tafi da shi
sannan ta bude front seat ta shiga, Mujaheed ya kara sallama da Dr khaleel ya ja
motar, Imaan na daga ma Farida hannu, sai da suka hau saman titi ya kalli jakar
hannunta yace "Jakar meye Wannan?" Ta turo baki tace "Ta bani kyauta ne, ta ga ban
xo da jaka ba" murmushi yayi bai ce komai ba, bayan few minutes yace "Idan kika
gama haifa min yara na sai in maki lefen ki ko?" ko kallonsa bata yi ba ita dai
tana rungume da jakar hannunta don Farida tace mata kada ta yarda ya ga abinda ke
ciki, Sai da suka kusan gida Mujaheed yace "Ammi fa tana gida, ta xo" Imaan ta
kallesa da sauri tace "Ammi?? Da gaske Yaya?" Yace "Ehh" murna ta fara yi kamar yar
yarinya a motar, ganin murmushin da yake ta dakatar da murnar ta marairaice tace
"Don Allah Yaya kace min wllh don ni ban yadda ba, kila ba da gaske kake ba" shi
dai murmushi kawai yake, lkci daya ta daure fuska, yace "Toh Ammi baxa ta iya xuwa
ganin ki ba kenan" turo baki tayi tace "Nasan Ammina baxa ta iya xuwa ba" yace
"Why?" Tace "Ni dai nasan she can't" yace "Toh idan muka je kika ganta me xan
maki?" Ta kallesa da sauri sai kuma tayi murmushi tace "Idan muka je naga da gaske
ta xo xan baka dubu goma" ya gyada kai still smiling yace "Idan kuma ba mu ganta ba
fa?" Ta turo baki tace "Sai ka siya min waya" ya wara ido yace "Uhn???" Tace "Ehh"
yyi murmushi yace "Toh ban yadda ba dubu goma da kika ce yyi kadan" tace "Toh me
xan baka?" Ya shafa kansa yace "Dubu goma with kiss and hug" Ta wara ido, sai kuma
ta rufe fuska tace "Toh naji" yace "Kin ji kika ce fa?" A hankali tace "Ehh" Yana
murmushi yace "In dai muka je muka ga yan gida ai duk daya ne koh?" Ta girgixa kai
da sauri tace "Noo, ni dai Ammina nace" parking yyi kofar gida ya kashe motar ya
sauka ita ma ta fito tana rike da jakarta, ta bude back seat ta dau warmer din
abinci bata ko kalli takeaways da yyi masu da safe ba ta nufi gate, shi ya kwashe
ledojin ya rufe motar sannan ya bi bayanta, still Imaan tayi ganin motar gidansu a
compound din, ta juya ta kalli Mujaheed dake tahowa yana murmushi, lkci daya ta
nufi cikin gidan da sauri ta bude kofa, sai kuma ta tsaya tana kallon Mama Hadixa
da Inna dake parlon, Mujaheed ya bude kofar shi ma ya shigo, imaan ta ajiye warmer
din hannunta ta nufi Mama Hadixa dake murmushi ta fada jikinta cike da farin ciki
tace "Oyoyo Mama, yaushe ku ka xo" Mama Hadiza ta rungumeta tace "Daga ina ku ke?"
Imaan na washe baki tace "Mun fita ne Mama, yaya ya kai ni gun Aunty Farida, kin
tuna ta?" Mama Hadiza tace "Nan take aure ita ma?" Imaan ta gyada kai tana murmushi
tace "Ehh Mama" Mama Hadiza tace "Maa sha Allah, amma kina cin abinci kuwa daughter
naga kin rame" Imaan ta sunkuyar da kanta tana murmushi, ita dai Inna na xaune
fuska a murtuke ta kura ma Tv ido, Mujaheed na murmushi ya karasa parlon ya ajiye
ledan hannunsa ya xauna kusa da ita ya mata side hug yace "Nasan dai wajena kika xo
koh inna?" Inna tace "Toh dama wajen wa xan xo idan ba kai ba Mujaheed, ga damun
nama can cikin cooler na maka" Dariya ya fara yi yana kallonta, Imaan ta daga kai
daga kwance da tayi jikin Mama Hadiza ta kalli Inna, mikewa tayi ta dawo kusa da
ita tana murmushi, cike da masifa Inna tace "Don Allah yar nan ki rufa min asiri ki
ja baya ba wajen ki na xo ba Allah shaida...." Mama Hadiza ta dauke kai tana
dariya, Imaan ta turo baki xata bar wajen Mujaheed ya rikota yana dariya shi ma
yace "Inna Imaan ce fa ko baki ganeta bane" Inna tace "Wacece kuma Imaan??" Dariya
kawai Mama Hadiza da Mujaheed ke yi, Imaan xata bar wajen Mujaheed ya rikota ya
xaunar da ita gefensa, rufe fuskarta tayi jikinsa da sauri ta fara kuka, Mujaheed
ya d'an kalli Mama Hadiza dake dariya har lkcn, murya can kasa yace ma Inna "Tunda
kuka kika xo sa min matata, tashi ku yi wucewar ku mun yafe xuwan" Inna tayi kamar
bata ji sa ba fuska a murtuke, Mama Hadiza tace "Babu kowa gidan ne? Ina ce kace
min Safeenah ta dawo" Mujaheed ya kalli sama yace "She is home, bata fito bane?"
Inna tace "Au kana nufin tana ciki??? Toh xan hau sama wannan mata Hadiza ta
hanani, wai gidan mutane" mikewa Mujaheed yyi ya wuce sama imaan ta bi sa da kallo,
Inna na kallonta tace "Toh bbu abinci gidan Mujaheed din ne kika rafke haka?" Imaan
ta hade rai ta dauke kai, Mama Hadiza tace "Debo ruwa kitchen in wanke ma Inna
garden eggs dinta" mikewa Imaan tayi ta dau ledan garden eggs din dake ajiye kusa
da babban trolley na kayanta da Mama Hadiza ta taho mata da shi ta wuce kitchen
tana kallon hanyar stairs,
Inna ta kalli Mama Hadiza tace "Wllh duk ta rame, kin ga abinda nake ta gudu kenan
koh, dama duka duka imaan din nawa take xa a ba katon nan? Ni dai ba ruwana wllh"
Mama Hadiza tace "Rashin kwantar da hankali ne da damuwa fa Inna, da alama kuma ta
fara hakura" Inna ta tabe baki tace "Ni dai ba ruwana" Har Imaan ta gama wanke
garden eggs din ta xuba su a bowl ta dawo Mujaheed bai fito parlor ba, sai kallon
stairs take, Inna tace "Ko yar mantina bbu gidan ne, daga kaduna fa muke" Mama
Hadiza ta saci kallonta bata dai ce komai ba. Mujaheed na tsaye dakin Safeenah dake
kwance saman gado fuska daure tana taunar cingam, kana ganin idanuwanta kasan kuka
ba na wasa ba ta ci, yana kallonta yace "You are looking into my face and telling
me baxa ki sauko ki gaida iyayena ba Safeenah??" A mugun fusace ta mike xaune tace
"Ehh, ko dole ne Mujaheed? Don Allah ka rabu da ni ka fita, ni dai abinda na sani
duk wanda ya shiga hakkina a gidan nan Allah ya isa, kuma matakin da xan dauka wllh
sae ya girgixa kowa, ni gaida iyayena kake da xan gaida naka" da mamaki ya dinga
kallonta, trying hard to control himself, can ya juya ya fice daga dakin ta bi sa
da wani mugun harara tana kas kas da chewing gum, yana sakkowa downstairs Imaan ta
wani hade rai tana cin garden egg din Inna da ta dauka, Inna na kallonsa tace
"Safara'un bata nan ne...." Imaan ta cafke tace "Tana daki" Inna ta xaro ido tace
"Tana daki??? Duk uban sallama da bubbuge bubbugen kofar da na dinga yi tana ji ta
min shiru??" mikewa Inna tayi ta wuce sama, Mama Hadiza tace "Don Allah Inna ki
bari ki dawo ki xauna, ni bana son hka" ko sauraronta Inna bata yi ba, Mujaheed dai
ya bi ta da kallo haka ma Imaan da taji mugun dadi har ranta, Inna ta bude dakin
farko da ta gani sai ga Safeenah kwance saman gado waya kare kunnenta tana jin bude
kofa ta katse wayar da sauri, Inna ta saki baki tana kallonta, can tace "Amma ke
dai barbadaddiya ce Safara'u, ashe kina cikin gidan nn kiji shigowar dangin mijin
ki kiyi mukus a daki kamar Mayya, Ni fa na haifi Uban Mujaheed din, Hadiza kuma
kanwar Ubansa ce, ashe ke salubabbiya ce Safara'u?" Safeenah tun da ta kalleta sau
daya ta dauke kai tana cin chewing gum, Mama Hadiza ce ta hauro sama, Inna tace
"Wllh ga ta nan Hadiza ina mata magana ko gaisheni ma bata yi ba tana min cin
cingam din karuwai, anya wannan matar aure ce kuwa? Toh dadin abun dai ko kashi mai
rai bata ta6a haifa ma Mujaheed ta ajiye ba balle Ahmadu ya samu barbadaddun jikoki
kamar ta, kuma in sha Allahu Imaan ce xata cika gidan nan da 'ya ya muna nan da
ku...." Mikewa Safeenah tayi ta daina cin gum din bakinta tana kallon Inna, duk
xamansu da Mujaheed bata ta6a kawo haihuwa a rai ba sai ynxu da Inna ke mata gori,
Safeenah tayi wani murmushi tace "Warce uwarta juya ce xata cika gida da 'ya ya?"
Mama Hadiza tace "ke karamar mara kunya kama kanki kada in baki mamakin da bakiyi
tunani ba, mara tarbiya kawai shashasha, tunda kika mana haka to har uwar da ta
haife ki ma xaki iya walakantawa haka" Safeenah tayi wani murmushin rainin hankali
ta mike ta shige bathroom tana cewa "Ae na xama kandagaren bakin tulu, babu yanda
aka iya da ni, Mujaheed dai ko an ki ko an so nice ta farko gidansa ba a isa a
canxa wannan ba" key ta sa ma bandakin, inna ta juya ta fita tana kwala ma Mujaheed
kira.... Mujaheed na ganin Mama Hadiza ta wuce sama dama ya mike ya koma kusa da
Imaan da ta hade rai, dauke kai tayi ya juyo da ita yana murmushi yace "Our
deal...." Mikewa take son yi ya ki bari ta tashi nan ya rungumeta giving her a
romantic kiss, ga mamakinsa bata yi yunkurin stopping dinsa ba, sai dai yana jin
yanda xuciyarta ke bugawa, muryar Inna da ya ji ya sa shi saketa da sauri ya matsa
daga kusa da ita, masifa kawai Inna take kamar xata ari baki, Sakkowar Mama Hadiza
ya sa Mujaheed ya mike, Mama Hadiza na kallonsa rai bace tace "Har mu yar iskar
yarinyar nan xata walakanta haka Mujaheed??" Mujaheed ya kasa cewa komai, Inna ta
xauna a hankali tace "Ni har xagina ma tayi ban kulata ba" Mujaheed yace "Ku yi
hakuri don Allah Mama..." Mama Hadiza tace "In sha Allahu a dalilina bbu abinda xai
sami aurenta na dai san xata gani a kwaryarta, the main point here is imaan baxata
xauna gida daya da ita ba, sam baxai yiwu ba, tun wuri ka fara shirin raba masu
gida" Inna tace "Atoh, jikata baxata xauna da mayya irin Safara'u ba wllh, yarinya
shegiya kawai mara tarbiya ni take tauna ma cingam tana balan balan da shi?? To
wannan lafceciyar uwar tata tayi ma haka ba ni ba" Shi dai Mujaheed bai ce komai ba
amma sosai ransa yyi mugun baci, Mama Hadiza ta xauna har lkcn ranta a bace tana
girgixa kai tace "Uwar ka dai ta cuce ka wllh, domin wannan ba yarinyar aure bace,
kwata kwata bata da kirki" Inna tace "Atoh, gwara da kika gane ma idonki, da ni ce
na koma gida nake fada karyatanin da kuka saba xa ku yi, barin mutumin nan Bukar, a
sannu xa ayi walkiya halin kowa ya fito nan ba da dadewa ba kuwa, ni dai abinda na
sani shine duk wanda ya kuskura ya ma jikata wani mugun abu to wllh wllh watan
mutuwarsa a duniyar nan ya tsaya cakkk don baxan yadda ba sai na hallaka sa" ita
dai Mama Hadiza bata ce komai ba. Mikewa tayi daga karshe tana kallon Imaan tace
"Mu tafi sama am not staying long here...." Imaan ta mike a hankali ta bi bayanta,
Mujaheed ya bi ta da kallo, sai da suka isa stairs ta juya ta kallesa langwabar
mata da kai yyi, ta make kafada ta bi bayan Mama Hadiza, dakin da take suka shiga,
Mama Hadiza na bin dakin da kallo tace "Nan ne dakin ki?" Imaan tace "Tun da muka
xo a nan nake" Mama Hadiza ta xauna gefen gado tana kallonta tace "Babu matsala
koh?" Shiru Imaan tayi, Mama Hadiza tace "Kar ki ji komai ki gaya min meye matsalar
ki kinga soon xa mu wuce" Imaan ta durkusa kusa da ita a hankali tace "Mama kawai
dai sai matarsa ta yi ta tsokanata haka daxu da safe ta shigo min daki tana xagina"
Mama Hadiza ta bude ido sosai tace "What?? Ta shigo tana xagin ki a kan me?" Imaan
tace "Wai na auri mijinta, kuma take cewa bai kwana dakina ba sai nata" Mama Hadiza
ta kankance ido tana kallonta rai bace tace "Shi Mujaheed din me ya hanasa kwanciya
dakin ki?" Murmushi imaan tayi kamar baxata ce komai ba sai kuma tace "Ni ce nace
bana so" Mama Hadiza tace "Ashe ke wawuya ce ban sani ba, kuma Ina maki kallon me
ilimi ashe ba haka ba imaan?" Imaan ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba,
maganganu sosai Mama Hadiza tayi mata yawanci duk babu banbanci da wanda Farida
tayi mata sai abinda baka rasa ba, ita dai kanta na kasa, Mama Hadiza tace "Idan ma
xaki cire wannan kunyan ki cire ni dai na gaya maki, idan ko ba haka ba kin dinga
kwasan takaici da gori kenan gun jakar kishiyar nan taki in har kika yarda ta gano
abinda ku ke ciki" Imaan ta goge hawayen dake sulalowa idonta a hankali tace "Toh
Mama" cikin kwantar da murya Mama Hadiza ta ci gaba da bata shawara sannan ta daura
da nasiha, Imaan na kallonta a sanyaye tace "Mama yaushe Ammi xata xo ita?" Mama
Hadiza tace "Ke ma kin san baxata xo ba, amma nan da wata daya ai xai kai ki gida
na sani" Imaan tace "Toh" Mama Hadiza ta bude jakarta ta ajiye mata abubuwan da ta
kawo mata ta yi mata bayani sannan ta mike tace "You keep them safe sai ki fito
parlor" daga haka ta fita dakin, Imaan ta mike ta xubasu a jakan da Aunty Farida ta
bata sannan ta fita dakin ta harari kofar dakin Safeenah ta sauka kasa, Inna na
xaune kan carpet ta bararraje tana cin shinkafa da miyar da Farida tayi, Mama
Hadiza ta xauna tace "Ina Mujaheed din?" Inna tace "Ya je siyo maki abinci, ni dai
ga wani nan na samu" Inna na kallon Imaan tace "In har kika yarda kika ba mayyar
kishiyar ki daman raina ki baki dinga cin ubanta ba to gaskiya an cuce ni da aka sa
maki sunana, irin gallazawar da nayi ma uwarsu Bala da Hansai ai sai Allah, komai
sai yanda nace ayi xa ayi a gidan nan, keee!! wllh ki kara kaifin bakin ki da
fitsara..." Inna na nuna mata bakinta tace "Kinga bakin nan nawa, to shi ya kwace
ni a kuruciyata, kwata kwata ban daukan nansans" Dariya Imaan ta fara yi, Mama
Hadiza dai tayi murmushi tana kallon uwar tata, Inna ta ci gaba da cin abincinta
tace "Wacece kuma Safara'u da cikin mintuna kalilan baxa ki kwace Mujaheed a
wajenta ba, shi fa Mujaheed wllh tun ba yau ba dama yake son auren ki, irin son da
yake maki ba ni har tsoro ya dinga bani lkcn, duk ina lura da shi yyi ta wani
takura ki yana sa maki ido d'an banxan, gashi yyi ta latse min ke kuma sbda bashi
da tsoron Allah, ashe dai kayansa ce ke, ohh Allah mai girma gashi yanxu har kin
tare gidansa kin kwana" Imaan ta rufe fuskarta da kujera tana murmushi, Mama Hadiza
ta fara dariya tana kallon Inna, inna ta tabe baki tace "Ni dai ba ruwana, ashe
dama Allah ya riga ya kaddara shi din dai ne mijinki, tohh ya muka iya Mujaheed dai
jikana ne kuma bbu wanda ya fi ni saninsa gaskiya...." Shigowar Mujaheed ya sa Inna
tayi shiru tana ci gaba da cin abincinta, Mama Hadiza dai sai kallonsa take tana
murmushi, ya ajiye ledan hannunsa yana kallon Imaan da ta ki dago kanta, Inna ta
kallesa ta gefen ido ta tabe baki, xaunawa yyi yana kallon Mama Hadixa yace "Ga
abinci na siyo maki Mama" Mama Hadiza tace "Toh nagode" Mikewa inna tayi tana
kallon Imaan tace "Mu je in ga dakin ki" Imaan ta mike ta nufi sama Inna na biye da
ita Mujaheed ya bi su da kallo, Inna ta dinga bin dakin da kallo bayan sun shiga
sannan tace "Kina dai sane har yanxu Mujaheed bai maki lefe ba dai koh? Kuma
sadakin ma Ahmadu ne ya bada sbda lalacewa, To ba ruwana kada ki yarda ya kai ki ya
baro ki sai ya hada maki lafiyayyen lefe irin na Bulasawa gaskiya, don ba sadaka
aka basa ke ba" Imaan tayi dariya bata dai ce komai ba, inna tace "Allah kuwa kar
ki yarda ya shigar maki daki bai maki lefe ba ya kai ki ya baro ba ruwana" Imaan
sai murmushi take Inna ta xauna gefen gado tace "Ita kuma Safara'u kar ki kuskura
ki raga mata, ko mi ta maki ki rama ke dai kar ki yarda ta kai maki hannu, da kinga
haka ki ja bakin ki kiyi shiru ki gudu tunda ba karfi ne dake ba, Ni fa nayi dambe
yyi sau dari da uwar Bala
damben mu na karshe sai da na tsaga mata goshi, da tabon ta mutu, Allah dai ya ji
kanta ya gafarta mata, lafiya muka xauna da ita wllh matar kirki..." Shigowar
Mujaheed dakin yasa inna ta ja bakinta tayi shiru, sai kuma ta mike tana kallon
Imaan tace "Ke mu je" imaan ta mike tana murmushi ta fita dakin Inna na biye da ita
suka koma parlor suka xauna. Karfe biyar saura Mama Hadiza tace "Toh inna ya kamata
mu kama hanya yanxu...." Inna ta katse ta tace "Haba Hadiza da maraicen nan mutum
ya kama hanyar kaduna yanda duniya bbu gaskiya ga yan kinnappin da yan fashi kaca
kaca a titi??" Mama Hadiza tace "Shi tafiyar minti araba'in din ne dare yayi
Inna??" Inna tace "Ni fa tun ina gidan mijina in dai la'asar ya gota to bana bin
babban titi" Imaan dai sai murmushi take, Mama Hadiza tace "Abinda nan da yan
kwanaki ma xa su dawo kadunan Inna" a fusace Inna tace "Toh me kike nufi? Nufin ki
xama nake son yi masu a gida tsofe tsofe da ni koko? Da ba don maraice yyi ba me
xan xauna in yi Hadiza?" Mama Hadiza ta mike ta dau handbag dinta tana kallon Imaan
tace "Tafi ki ce ma Mujaheed xan koma" dai dai nan Mujaheed ya sakko parlon, yace
"Mama ba dai tafiya ba?" Mama Hadiza tace "Wucewa xan yi, sai ayi ta hakuri kuma"
Mujaheed ya saci kallon Inna da ta hade rai tana kallon Tv sai kuma ya kalli Mama
Hadiza yace "Is she staying here" Mama Hadiza tace "Don Allah ni dai mu je ku raka
ni in wuce" daga haka ta nufi kofa, Mujaheed ya kara satan kallon Inna sannan ya bi
bayanta, Imaan na kallon Inna murya can kasa tace "Kar ki tafi Inna kiyi xaman ki a
nan kin ji" Inna ta tabe baki tace "Yanxu xuwa xata yi ta 6ata ni gun 'yan uwanta
su kullace ni ko don ba ni na haife ku yasa suke min walakancin nan oho, bari dai
in tafi kada a sa ni a bakin duniya, amma duk abubuwan da na gaya maki kar ki
kuskura ki watsar don xa su maki amfani, in sha Allahu nan da kwana biyu tun da
naga gida ko shawara da su Ahmadu baxan yi ba sai dai su ga wayam bbu ni, tashi mu
je ki rakani...." Imaan ta mike kamar xata yi kuka ta bi bayanta, fuska daure Inna
ta shige bayan mota Mama Hadiza dai bata ce komai ba, Mujaheed ya sauke wani
boyayyen ajiyar xuciya, Imaan ta fara hawaye Mama Hadiza tace "Meye haka? Bana son
shashanci fa" juyawa tayi ta koma ciki tana share hawayen idonta.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788
90.....

Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

Mujaheed na komawa parlor bayan su Mama Hadiza sun wuce ya dau trolley din da suka
kawo ma Imaan ya kai mata daki, xaune ya sameta ta jinginar da kanta jikin gado
tana hawaye, ya ajiye jakar ya isa kusa da ita ya xauna yana kallonta, Hade kai
tayi da gwiwa tana kuka a hankali, ya dagota yace "Ohk I am taking you home next
week in sha Allah, yayi hakan?" Tana kallonsa cikin sanyin murya tace "Da gaske?"
Yayi murmushi ya ja hancinta yace "Ehh mana, ko Yaya ya ta6a maki karya ne" Ta goge
idonta tace "Toh Allah ya kai mu" yace "Baki yi lunch ba har yanxu" tace "Bayan
abincin da na ci gidan Aunty Farida, I am not hungry" mikewa yayi yace "Let me get
something outside" Bai jira cewarta ba ya isa kofa ya cire makulli ya fita ya kulle
dakin ta waje, turo baki tayi ta mike ta kwantar da jakar da ya ajiye mata ta bude
zip din, gogaggun kayanta ne kusan kala goma sai Hijabs har kala Biyar a babban
jakan da inner wears, sai turarurrukanta da man shafa, rufe jakar tayi a hankali ta
ja sa gefe ta ajiye sannan ta koma gefen gado ta xauna. Sai kusan karfe shidda
Mujaheed ya bude dakin yana kallonta daga bakin kofa yace "Come downstairs" sai da
ya bar bakin kofar sannan ta mike ta fita dakin tana kallon dakin Safeenah ta sauka
downstairs, xaune ta samesa parlon da pineapple da aka yi slicing a plate, ta
karasa ta xauna tana kallon movie da ake a Tv, yace "Baxa ki sha ba?" Kallon
abarban tayi sannan ta dauke kai, ya mike ya dau plate din ya nufeta ya xauna kusa
da ita, a hankali ta dau daya ta sa a baki, yyi murmushi yana kallon eye balls
dinta ta hade rai tace "Ni dai ka daina kallona" ya jawota jikinsa yace "Ohk na
daina" suna nan haka har kusan Magrib suna kallon movie da ake yi a TV, Jin
footstep a stairs duk suka juya, Safeenah ce ke sakkowa sama fuska a murtuke, suka
hada ido gaba daya da ita, a hankali Imaan ta kwantar da kanta saman shoulder
dinsa, Safeenah bata sake yarda ta kallesu ba ta wuce kitchen, Mujaheed dai bai
sake kallonta ba Imaan ta bi ta da harara, Mujaheed dake lura da ita yyi murmushi
ya daura lips dinsa a cheeks dinta murya can kasa yace "Me ta maki?" Hade rai tayi
ta kallesa, ya wara ido ya rungumeta yace "Toh yi hakuri" lamo tayi jikinsa, bayan
kusan minti biyar sai ga Safeenah ta fito kitchen din ko ba a fada ba kasan yunwa
take ji, suka kara hada ido da Imaan ta dauke kai da sauri ta wuce sama kamar xata
tashi sama, shi dai Mujaheed bai ce komai ba, jin ana kiran sllh ya mike yace "Me
xa ki ci sai in taho maki da shi when I am coming back from mosque" tace "Ae akwai
abincin da muka siyo" yace "Noo ae ya huce" d'an murmushi tayi tace "Almubazzaranci
Kuma?" Shiru yyi yana kallonta, tace "Sae ka dawo" daga haka ta mike ta wuce sama,
a hankali yace "Imaan" ta juya tana kallonsa yace "Ki sa makulli daki idan kin
shiga" Kai kawai ta gyada masa ta wuce sama shi kuma ya fita, imaan ta kusa idar da
sllhn Magrib taji ana murda kofar dakin, tana idarwa ta nufi kofar a hankali tace
"Waye?" Muryar Safeenah ta ji tace "Idan ba tsoro ba uban me yasa kike sa makulli a
kofa, banxa matsoraciya karuwa kawai...." Imaan tayi murmushi tace "Sbda bani da
lkcn biye ma jahila in daura ma kai na xunubi shi yasa nake rufe kofata, when ever
I have ur time I will leave my door open, wahalalliya kawai" Bubbuga kofar Safeenah
ta dinga yi da mugun karfi tana kunduma mata mugayen ashar tana cewa "In kin haifu
cikin uwarki ki bude kofar nan yanxu ki ga abinda xai faru, wllh in doke ki in doki
banxa in ga uban da xai tsaya maki" Dariya Imaan tayi tace "Allah ya baki lfya,
kina ta6a ni xa ki sha mugun mamaki idan kika ga mijin ki ya tsaya min, mate din ki
masu ji da karfi boxing suke yi why not ke ma ki fara da ki zo nan kina xubar da
mutuncin ki gun 'yar cikin ki" Safeenah tayi wani kara ta kunduma mata wani xagin
tace "Ki bude kofar idan ke ba shegiya bace" Imaan tace "Shegun biyu a nan ai,
jarababbiya kawai" daga haka Imaan ta koma gefen gado ta xauna tana murmushi,
Safeenah sai buga kofar take kamar xata cire, imaan bata sake kulata ba har ta bar
kofar tana ci gaba da zage xage, sai kusan bakwai da rabi Mujaheed ya shigo gidan,
ya kwankwasa kofar Imaan, mikewa tayi ta isa gun kofar ta tsaya, ganin ba a bude ba
Mujaheed yace "Imaan" bude kofar tayi yana kallonta yace "Have u prayed" Bata basa
amsa ba ta nufi kan gado ta xauna ta fashe da kuka, da mamaki ya karasa kusa da ita
yace "What happened???" Cikin rawar murya tace "Ko ba matarka bace ta xo tana ta
xagina tana bubbuga kofa wai xata dokeni, har da ce min karuwa" sae ta kuma fashewa
da kuka sosai amma ba hawaye, mikewa yyi ya fice daga dakin, ta bi sa da kallo tana
turo baki, Bude kofar dakin Safeenah yyi ya sameta xaune gefen gado waya kare
kunnenta tana hawaye, katse wayar tayi lkci daya ganinsa, Yana kallonta da kyau
cikin daga murya yace "Let me drop u this warning Safeenah, even by mistake, I mean
mistakenly kika sake yi ma Imaan kallon banxa a gidan nan balle ki gaya mata magana
mara dadi I will show u the other side of me, I will show you the bad side of me,
Billah xa ki iya min komai in shanye in kyale ki amma banda ta6a Imaan, idan kuma
kin xata wasa nake try anything silly for the second time wllh i will make you
regret it" Wani murmushi tayi tace "Toh mu xuba mu ga" daga haka ta shige bandaki
tayi banging kofar ta rufe. Imaan har ranta taji dadin samun Safeenah da Mujaheed
yyi kuma duk tana jin abinda yace mata don a bude ya bar kofar, parlor ta sauka don
warming din abinci ranta fess. Karfe goma Imaan na xaune gaban mirror tana shafa
cream din gashinta a kai aka bude kofar dakin ta juya da sauri, ganin Mujaheed ta
ci gaba da shafa man da take, Karasawa yyi kusa da ita ya mika mata wayar hannunsa
ta karba tana kallon screen din kafin ta kai kunnenta, ya juya ya fita dakin, tana
murmushi tace "Ina yini Aunty?" Daga daya bangaren Aunty tace "Lafiya lau Imaan ya
ku ke?" Imaan tace "Alhmdllh, Aunty yaushe su Maimoon xa su xo?" Aunty tace "Idan
kun dawo kaduna xa su xo daughter" a hankali Imaan tace "Toh Aunty" Aunty tace "Ki
kwantar da hankalinki kinji Imaan, What happened is the best for you in sha Allah,
kuma Babu ruwanki da abokiyar xaman ki" imaan bata iya ta ce komai ba, Aunty tace
"Toh sai da safe" Murya can kasa tace "Nagode Aunty" daga haka Aunty ta katse wayar
Imaan ta ajiye a sanyaye ta ci gaba da abinda take, daga karshe ta mike ta hau
saman gado ta kwanta, Mujaheed ya shigo dakin ya dau wayarsa dake gaban mirror ya
dawo kusa da ita ya xauna yace "Ain't you taking the fruits again?" Girgixa masa
kai tayi, yace "Toh in kira maki Ammi?" Mikewa xaune tayi da sauri tace "Ehh pls"
yayi dialing number Ammi ya mika mata sannan ya shiga bathroom, Ammi na dagawa daga
daya bangaren Imaan taji dadi har ranta, sallama Ammi tayi, A sanyaye Imaan tace
"Ina yini Ammi?" Ammi tace "Lafiya lau Imaan, ya kike?" Imaan tace "Alhmdllh, Ammi
Daddy na fa?" Ammi tace "Yana Abuja" Imaan ta yi shiru, Ammi tace "Kiyi hakuri
Imaan, Allah plans best, Allah yasa hakan shine ma fi alkhairi gare ki, ki kwantar
da hankalin ki" Imaan ta d'an yi murmushi cikin sanyin murya tace "Ae nayi Ammi"
Ammi tace "That's good...." Imaan tace "Toh me yasa Ammi ba ku xo da su Mama Hadiza
ba?" Ammi tace "In xo in maku me?" Murmushi kawai Imaan tayi a hankali tace "Ina
missing din ki ne" Ammi tace "Idan kin xo gida xa ki gan ni ai" Imaan tace "Toh
Ammi" Ammi tace "Babu ruwan ki da kula abokiyar xamanki kin dai ji me na ce maki
komai ta maki kar ki tanka, ki yi hakuri" Imaan tace "Toh Ammi" Ammi tace "Toh sai
da safe" Imaan ta kalli kofar bathroom tace "Baxa ku gaisa da Yaya ba Ammi?" Katse
wayar Ammi tayi, Imaan ta dinga kallon screen din sannan ta ajiye wayar ta kwanta
ta lumshe ido, tana ji Mujaheed ya fito yayi shirin bacci sannan ya dawo kusa da
ita ya dau wayarsa da ta ajiye gefenta yana kallon fuskarta, yace "Tashi ki sha
drugs din ki" A hankali ta bude idonta tana kallonsa, ya mike ya dauko mata
Magungunan ya ajiye mata sannan ya fita downstairs dauko ruwa, har ta bude
Magungunan kafin ya dawo, ya mika mata ruwa a glass cup ta amsa ta sha maganin, ya
fita da cup din ta koma ta kwanta haka kawai gabanta ke faduwa, ya shigo ya kashe
wutan dakin ya kwanta daya side din yace "Did u perform ablution before going to
bed?" Bata amsa masa ba ta juya masa baya, Bayan kusan minti goma ya mirgina a
hankali ya dawo kusa da ita, juyowa tayi da sauri tana kallonsa cikin sanyin murya
tace "Yaya" Jin yanda xuciyarta ke bugawa murya can kasa yace "Are you okay?" Ta
girgixa masa kai lkci daya hawaye ya kawo idonta, kallonta ya dinga yi cikin duhun,
a hankali ta rufe ido ta daura kanta jikinsa cikin sanyin murya tace "Bacci nake
son in yi" d'an murmushi yyi ya rungumeta, ya kwantar da murya yace "Kiyi baccin
ki, don't be afraid" Bata ce komai ba tayi lamo jikinsa har lkcn yana jin yanda
xuciyarta ke bugawa, sai da ya ji saukan numfashinta alamar bacci ya fara daukanta
bayan wani lkci ya daura lips dinsa forehead dinta ya lumshe ido cikin sanyin murya
yace "I... i love you" Bude ido tayi da sauri, ya kankameta yace "Bacci nace kiyi
kanwata" Bata san lkcn da tayi murmushi ba ta lumshe ido ta mayar da kanta...
Wajajen karfe biyu na dare Imaan ta farka ta gansa tsaye yana sallah, mikewa xaune
tayi ta sauka saman gadon ta shiga bathroom ta dauro alwala ita ma ta fito ta bude
jaka ta dau daya daga Hijabs dinta. Washegari da karfe goma na safe Mujaheed na
tsaye bakin kofar kitchen bayan sun gama breakfast Imaan na wanke plates din da aka
yi amfani da, ko na minti daya bai yarda ya bar ta ita kadai ba, ko me xata yi
outside her room yana tare da ita, kuma tun da gari ya waye Safeenah bata sakko ba
shima bai je dakinta ba, Kamar ance ya juya ya ganta ta sakko stairs yafe da mayafi
ta nufi kofar fita, ya bi ta da kallo ganin xata fita, calmly yace "Where are u
going to?" Ko kallonsa bata yi ba har ta fice daga gidan, Imaan ta tabe baki tana
ci gaba da aikin da take. Sha biyu saura Mujaheed ya fita gidan don siyo ma Imaan
dake masa complain
din ciwon kafa maganin tube da take shafawa, tun wayewar gari take ce masa kafarta
na ciwo, yana fita dama yace ta saka makulli kofarta, Safeenah ce xaune parlor tana
ta communicating da 'yan gidansu da suka shigo garin zaria tana masu kwatancen
gida, bell taji aka danna daga karshe, ta mike taji sanyi har ranta ta isa kofar ta
bude tana cewa "Ashe kun ma kusa...." Umma ce tsaye bakin kofar, Safeenah ta dinga
kallonta daga sama har kasa, a takaice tace "Daga Ina kuma wa kike nema??" Umma ta
bude baki tana kallonta da mamaki tace "Wa nake nema Safeenah??" Cike da rainin
wayo Safeenah tace "Kinga.. tun ina danne xuciyata muna magana a mutunce ki juya
asirin ki a rufe ki bar gidan nan Hajiya Rukayya...." Umma ta katse ta tace "Ehh
lallai kin cika yar iska mara mutunci Safeenah ni kike gaya ma haka a gidan d'a na?
Ni????" Safeenah tayi wani dariyar rainin wayo tace "D'an ki? D'an ki fa kika ce?
To wllh you are mistaken, kuma xaki san a da Mujaheed yake d'an ki, a da kike da
iko da shi ba yanxu ba, bari ki ji abinda baki sani ba... Ke da Mujaheed sai dai
hange daga nisa, sai kin san mu gidan mu ba bokaye muke bi ba matsafa masu shan
jinin mutane muke bi, kuma tun muna magana ta fatar baki cikin mutunci ki juya ki
ja tsummar kazamar rayuwarki ki bar gidana, shaidaniya annami...." Wani wawan mari
Umma ta sauke mata tana huci, ta kuma sauke mata wani, Safeenah ta dafe kuncinta ta
yo waje da ido da karfi tace "Ni kika mara Hajiya Rukayya?? Ni kika mara?" Umma na
nuna ta cikin bacin rai tace "Na mare don uwarki, sakayyar da xa ki...." Umma bata
rufe baki ba Safeenah ta sauke mata nata tagwayen marin masu lafiya, Umma ta gigice
ta dafe kuncinta cikin shock tace "Ni kika mara Safeenah?" Cikin tsawa Safeenah
tace "An mare ki Rukayya kiyi abinda xa ki yi, nace na mare ki, uban waye ke da
baxan mare ki ba, meye a ciki don na mari shugabar bokaye da malaman garin kaduna?"
Duk wannan abun Imaan na tsaye stairs tana kallonsu don da karfi Safeenah ke
magana, lkci daya Umma ta shako Safeenah da karfi tana huci tace "Yau sai dai wata
ba ke ba don ubanki, yau sai dai Mansura ta haifi wata" Safeenah ta cakumota ita
ma, nan suka fara dambacewa bakin kofar suna ba juna kashi ba kakkautawa, Safeenah
ta samu nasaran hayewa kan Umma ta dinga dukanta iya karfinta tana huci tana cewa
"Sai na illata ki yau yanda baxa a gane ki ba idan kika bar gidan nan, ta dalilin
hassadan ki da bakin ciki da mugun hali aka min kishiya kika dinga ja na gidajen
bokaye da malamai don a lalata auren yarinya da saurayinta har aka fasa auren aka
makala ma mijina, kin cuce ni, kin cuce ni, kin yaudare ni, Allah ya isa tsakanina
da ke, axxaluma, wllh sai na illata ki yau duk abinda xai faru sai dai ya faru...."
Kasa motsi Imaan tayi da farko ta makale jikin stairs tana kallonsu, ganin duka ba
na wasa take ma Umma ba ta sakko da sauri tayi kan Safeenah, Safeenah na ganin haka
ta raba hankalinta biyu wanda hakan ne ya ba Umma da jini ke fita bakinta da hanci
damar hankadeta da karfi daga kanta ta shako wuyarta, Mari me lafiya Imaan ta wanka
ma Safeenah ta fixgo gashinta da karfi tace "Yau na tabbata ke jaka ce, jahila kuma
mahaukaciya.... " Safeenah tayi wani kara xata fixgo Imaan Umma ta danneta kasa,
nan suka hade da Imaan suka dinga jibgarta tana ihu, Imaan bata ta6a sanin tana da
karfi haka ba, don dukan Safeenah take kamar an aikota, hakan yyi dai dai da
shigowar Hajiya Baturiya da Hajiyan Marafa da wata kawarta, a rikice Hajiyan Marafa
ta dinga salati tana komawa baya, Imaan na ganin haka ta daga Safeenah da sauri,
tana jan Umma da ta mike ita ma su bar wajen, Hajiyan Marafa ta durkusa gaban
Safeenah da jini ke xuba bakinta tana salati da karfi tana cewa me xan gani haka,
Hajiya Baturiya tayi wani kukan kura kamar mahaukaciya tayi kan Umma da ta nufi
stairs da gudu tare da Imaan.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

91.....

Imaan da har wani rawa jikinta yake ta bude kofar dakinta bayan sun haura sama
kamar kiftawar ido ta shige, kiris ya rage Hajiya Baturiya ta cafke Umma, Umma ta
shige dakin da mugun sauri ta tura kofar da karfi Imaan na taya ta suka sa makulli,
wani mahaukacin bubbuga kofar Baturiya ke yi tana kunduma ma umma munanan ashar
tana cewa sai ta illata ta yau, Imaan dai na tsaye tana kallon kofar gabanta na
faduwa sosai ta dinga sauke numfashi, bayan kusan minti biyar ta juya a hankali ta
ga Umma xaune bakin gado ta rike kai sai sauke numfashi take ita ma, dauke kai
Imaan tayi ta tafi gun window ta tsaya, har lkcn Baturiya da Hajiyar Marafa basu
fasa bubbuga kofar kamar xa su balla ba suna tsine ma Umma suna cewa idan ta isa ta
fito, Imaan dai sai kallon kofar take tana tsoron kada ya balle su shiga uku, don
ba bugun wasa suke ma kofar ba, jin budewar gate ta juya da sauri tana kallon
compound ta window, Mujaheed ne yayi parking ya fito daga motar hannunsa rike da
leda, wani ajiyar xuciya Imaan ta sauke, lkci daya ta ji hankalinta ya kwanta, jin
su Baturiya basu hakura da buga kofa ba suna tsine tsine ta nufi kofar tace "Lallai
da gaske kun cika dangin mahaukata gantalallu, mu kuma ba mahaukata bane shi sa
baxa mu kula ku ba, kuma aniyar ku ta bi ku" Muryar Safeenah taji da karfi tana
cewa "Wllh wllh sai dai matsiyaciyar uwar ki ta haifi wata yau, sai kin san kin
ta6a ni yau, sai nayi rugu rugu dake na illata ki, na lalata maki kamanni na maki
wannan alkawarin" Imaan tayi wani dariya har da tafe hannu tace "Nasan darajan
iyaye ni baxan xage iyayen ki ba, duk da sun gama xagin kansu tass a idona, don
tunda nake ban ta6a ganin gantalallu marasa aikin yi irin family din ki ba, kuma a
kanku tsiya ya kare, ga alama na gani" Imaan na fadin haka ta juya tana murguda
baki ta koma gun window, xage xage suka dinga yi in Unison kamar barbarians ko
wacce na fadin abinda xata ma Imaan, Umma dai har lkcn tana xaune ta rike kai,
Muryar Mujaheed Imaan taji da mamaki yana cewa "What's happening here?" Babu warce
ta tankasa cikinsu, sai dai duk sunyi tsit sai kas kas din chewing gums, Hajiyan
Marafa da kawarta da Baturiya suka ja gefe suka tsaya ko wannensu na huci, Mujaheed
ya daure fuska sosai yana kallon Safeenah cikin daga murya yace "I am asking you
Safeenah me ke faruwa a nan?" Safeenah dake tsaye da kumburarren baki tana masa
wani shegen kallo cikin tsawa tace "Ban sani ba Mujaheed" Kofar dakin Imaan ya nufa
da sauri yana bubbugawa yace "imaan? Imaan?" Fashewa Imaan tayi da kuka sosai ta
iso kusa da kofar cikin rawar murya tace "Yaya cewa fa suka yi xa su kasheni"
Mujaheed ya kalli Safeenah da sauri yace "What?? Hauka kika fara yi Safeenah?"
Hajiyan Marafa tace "Uwarka Rukayya ce mahaukaciya ba 'ya ta ba Mujaheed, nace
uwarka ce mahaukaciya.." kallonta kawai Mujaheed ke yi ko kiftawa bbu, lkci daya
idanuwansa suka sauya kala, ya dauke kai cikin daga murya yace "Open the door
Imaan" a hankali Imaan ta murda makullin kofar ta bude kadan ba duka ba, Safeenah
na ganin haka tayi kanta da gudu xata fincikota tana huci, cikin zafin nama
Mujaheed ya hankadeta a tsawace yace "What are you trying to do??" Shiga dakin yyi
ba tare da ya shirya yin hakan ba ganin Hajiyan Marafa da Baturiya sun tunkaro
kofar da sauri, ya rufe kofar ya sa makulli, Imaan ta makale bayan kofar xuciyarta
na bugawa, still Mujaheed yyi ganin Umma dake xaune rike da kai gefen gado, da
mamaki yace "Umma...." Sai a lkcn Umma ta dago kai tana kallonsa tace "Mujaheed
kada auren Safeenah ya kara minti biyu a kan ka, ka sallameta yanxun nan" tana
magana hawaye ya fara sauka idonta kamar an bude famfo, sai kawai ta rushe da kuka,
Mujaheed ya nufeta with shock ya duka gabanta yace "Me ke faruwa Umma? Me Safeenahr
ta maki??" kuka kawai Umma ke yi tana girgixa kai, irin kukan takaicin nan,
Mujaheed da ya rude gaba daya ya mike da sauri yana kallon Imaan dake makale jikin
bango har sannan yace "Tell me what happened Imaan, me ke faruwa??" Imaan ta sauke
idonta kasa, kamar baxa ta ce komai ba sai kuma tace "Dambe tayi da Umma..." Da
karfi yace "What?? Safeenar tayi dambe da Umma?" umma na kuka tace "Kwarai kuwa
Mujaheed, Safeenah ta xageni ta daga hannu ta mareni sannan ta hau ni da kokuwa"
kuka ne ya ci karfinta, ta rike kai tana rusa kuka sosai, lkci daya idanuwan
Mujaheed suka kada sosai, ya juya ya nufi kofar ya bude ya fita, bai gansu corridor
din rooms din ba ya sauka downstairs da sauri, Ganin yanda Umma ke kuka Imaan ta
nufeta a hankali tace "Kiyi hakuri Umma" Umma bata kalleta ba kuma bata daina kukan
da take yi ba tana girgixa kai, Imaan ta sauke kanta kasa ta nufi kofa walking
slowly, dai dai staircase din karshe ta tsaya tana leko parlon kamar munafuka,
Hajiya Baturiya na xaune tare da Hajiyan Marafa da kawarta sai Safeenah banda
kundume kundume babu abinda suke suna kara fadin abinda xa su yi ma Umma yau,
Safeenah na ganin Imaan ta mike kamar mahaukaciya ta nufeta dw gudu, Imaan na ganin
haka ta juya da sauri xata gudu ta koma sama ta ci karo da Mujaheed dake sakkowa a
bayanta, shigewa jikinsa tayi jikinta na rawa, ya shiga sakkowa stairs din a
hankali yana rike da Imaan, Safeenah dai na tsaye tana huci tana kallonsa don tunda
take bata ta6a ganin irin expression din fuskarsa ba tare da shi, can ta sauke
idonta kan takardar hannunsa har ya iso gabanta ya mika mata takardan looking
straight into her eyes da idanuwansa da suka dawo kamar garwashi, kin amsawa tayi
tana kallonsa da idanuwanta da ta gwalo xuciyarta na bugawa, ganin bata amsa ba ya
isa kan kujera ya ajiye yana mata wani kallon da ya firgitata cikin muryar da bata
ta6a saninsa da shi ba yace "I don't want to see you in my house in the next 30
mins Safeenah...." Ba ita ba har Imaan sai da ta d'an yi shock jin furucin sa,
Hajiya Marafa ta mike da sauri ta isa gun takardar ta dauka ta warware, Ita dai
Safeenah na tsaye ta kasa ko da motsi tana kallon Mujaheed, lkci daya Hajiyan
Marafa ta ajiye takardan bayan ta gama karantawa ta nufesa da mugun sauri tana
kallonsa cikin daga murya tace "Mujaheed ita 'yar tawa xaka ma sakin walakanci??
Ita Safeenahr ka saka" Bata jira amsar sa ba ta sauke masa wani lafiyayyen mari,
Mujaheed ya dinga kallonta ko kiftawa bbu, wani marin ta kuma sauke masa ta
cakumosa tana kunduma masa xagi tana huci tace "To wllh karya kake, nace karya
kake, baka isa bane, bbu saki a auren mu...." don kanta ta sakesa bayan ta gama
jijjigasa, ya sauke idonsa sannan ya nufi inda ta jerar da takardan ya dauka da pen
din ya fara wani rubutun a kai, cikin few seconds ya nufi Safeenah dake tsaye kamar
Status tana bin sa da kallo ya kamo hannunta ya sa mata takardan cikin cool voice
dinsa yace "Na sake ki saki daya, saki biyu, saki uku, within the next 30 min ki
tattara duk wani abu naki ki bar min gida na, xa mu hadu a court da ku for
insulting my own mother" Imaan ta dinga kallon Mujaheed ko kiftawa bbu very shock
as well, Muryar Umma suka ji a stairs, a hankali tace "Allah ya maka albarka" Wani
kara Safeenah tayi cikin gigicewa ta nufesa tana cewa "Wllh ina sonka Mujaheed, ka
saurareni ka ji abinda yasa na aikata abinda na aikata, wllh mahaifiyar ka ce ta ja
min komai, ni ban san boka ko malam ba, wllh ita ta cuceni ta kai ni don mu raba
auren Imaan da Bulasawa, sai ga shi Allah ya nuna mana ishara an aura maka Imaan
din, she is the cause of everything happening here, don Allah ka saurareni Mujaheed
wllh baxan iya rabuwa da kai ba xan iya rasa raina, Ina sonka Mujaheed...." Calmly
Mujaheed yace "Ko da gun masu tsafi ta kai ki I can't change her from who she is,
she still remains my mother..." Duk da wajen Umma Hajiyan Marafa ta yi niyyar nufa
kamar wata xararriya amma ganin Safeenah ta sulale kasa yasa ta tsaya gun 'yar tata
ta durkushe kusa da ita ta dagota ta fasa wani ihu, Hajiya Baturiya da kawar
Hajiyan Marafa duk suka taho gun cikin rikicewa, Mujaheed da idanuwansa suka koma
kamar garwashin wuta ya kama hannun Imaan da ta kasa motsi suka bar wajen, tuni
Umma ta koma sama tana goge hawayen dake sakko mata ba kakkautawa, xaune suka tadda
Umma gefen gado ta rike kai, Mujaheed ya isa kusa da ita ya durkusa cikin sanyin
murya yace "Kiyi hakuri Umma, I am sorry all this happened, don Allah Umma kiyi
hakuri..." kuka ta fara yi sosai ta kasa ce masa komai, Imaan dake tsaye kusa da
mirror ta sunkuyar da kanta ita ma hawaye ya cika idonta, Mikewa yyi yana kallon
Imaan yace "Get set we are leaving now" Yana fadin haka ya fita dakin, Imaan ta
nufi Umma dake kuka har lkcn ta durkusa a hankali tace "Umma kiyi hakuri" Umma dai
bata ce mata komai ba.... Su Hajiyan Marafa sun kwasa gaba daya sun je kai Safeenah
da ta ki farfadowa duk ruwan da suka dinga xuba mata hospital, Bayan Umma ta fita
dakin ta koma parlor ta xauna Mujaheed ya shigo yana kallon Imaan dake rufe jakarta
bayan ta dau Hijab, xaunawa yyi gefen gado, ganin mood dinsa ta nufesa ta xauna
kusa da shi a hankali kafin tace komai ya kamo hannunta yace "Pls Imaan let this be
a secret between us, kar ki ce ma kowa komai a gida plss" ganin yanda idanuwansa
suka rine ta rungume sa a hankali tace "In sha Allah Yaya, sorry about all what
happened" sun fi minti biyu a haka sannan ta xame jikinta tana kallonsa, mikewa yyi
cikin sanyi yace "Am waiting for you outside" daga haka ya nufi kofa ta bi sa da
kallo cike da tausayin sa har ya fita, tasan shi daya yasan abinda yake ji ynxu,
ace mahaifiyar ka ga abinda take yi kuma tasan bbu karya a xancen Safeenah, shi ma
kuma yasan haka, but dole uwa uwa ce. Bayan few minutes Mujaheed ya bar gidan tare
da Imaan da Umma after making sure bai bar komai nata a cikin gidan ba, duk a
compound ya bar mata su kuma ya kulle gate dinsa ta waje, Imaan na xaune gaban mota
abubuwan da suka faru na sake dawo mata fresh, Umma dai tayi jigum bayan mota,
Mujaheed kuma ya maida hankalinsa gaba daya kan driving din da yake sai dai kana
ganinsa kasan yana tare da damuwa sosai, a haka suka shigo garin kaduna wajajen
la'asar.... Imaan
bata san lkcn da tayi wani murmushi ba lkci daya farin ciki ya baibayeta ganinsu a
layinsu, Mujaheed na isa gate yyi horn Mai gadi ya bude masa gate yana daga masa
hannu, bai iya ya tanka sa ba har ya shiga compound din yyi parking, Imaan ta bude
motar a hankali ta sauka, bayan ya sauka, Umma ma ta sauka motar kanta a kasa,
Imaan sai kallon apartment dinsu take tana jin kamar ta tafi da gudu, bbu wanda
take son gani lkcn sai Amminta, maimakon mai gadi ya rufe gate sai ganin motoci har
uku suka yi sun shigo compound din, Mujaheed ya dinga kallon motocin haka ma Umma
da ta daga kai tana kallo, Bude first car din aka yi mahaifiyar Sadeeq ta fito
motar cikin shiga ta alfarma sae ga wasu wa enda da alamar kawayenta ne su ma sun
fito, Umma ta dinga kallonta ko kiftawa babu, lkci daya cikinta ya hautsine, tun da
Imaan ta gansu jikinta yyi mugun sanyi, Umma na hade hanya ta nufi entrance din
parlor da sauri....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

92.....
Mama Hadiza xata fito parlor suka kusa cin karo da Umma bakin kofa, Bin ta da kallo
Mama Hadiza tayi ganin saurin da take yi kanta a kasa har ta shige parlor, Mama
Hadiza ta tabe baki ta fito compound din, imaan dai ta kasa kallon direction dinsu
kamar mara laka ta nufi apartment din su xuciyarta na bugawa, Mujaheed ya gaishe
su, Hajiya Khadijah ta amsa a takaice, bai kara kallonsu ba ya wuce ciki walking
slowly, Mama Hadiza na kallonsa ta amsa gaisuwar da yake mata, bai tsaya ba ya
shiga parlor ya rufe kofar, Mama Hadiza ta nufi su Hajiya Khadijah tana masu sannu
da xuwa duk da bata san su ba tace "Toh ku shiga ciki mana" Hajiya Khadijah tace
"Mai gidan mu ke nema, Allah ya sa dai yana nan" Mama Hadiza tace "In ji dai lafiya
Hajiya?" Hajiya Khadijah tace "Lafiyar kenan dai, wajen sa muka xo" Mama Hadiza
tace "Ai kam bai nan...." Hajiya Khadijah ta d'an yi shiru sannan tace "Kaninsa
fa?" Mama Hadiza tace "Wai lafiya Hajiya? I am their sister" Hajiya Khadijah tace
"Sorry I didn't introduce my self, ni mahaifiyar Sadeeq ce, kin gane yanxu kuwa?"
Mama Hadiza ta bude ido tace "Ohh Allah sarki sannu da xuwa Hajiya, to mu shiga
daga ciki mana, sannun ku da xuwa" Hajiya Khadijah tace "Yauwa mun gode, amma tunda
basa nan da mun tafi gun kakar Imaan din koh?" Mama Hadiza tace "Ehh toh mu je can
din, ai tana nan" Hajiya Khadijah tace "Toh nagode" a tare suka tafi part din Inna
da frnds dinta da Mama Hadixa dake gaba suna biye da ita, Mama Hadiza ce ta fara
shiga parlon Inna da sallama, sannan su ma suka shiga, Inna ta fito daki rike da
tsintsiya ta dinga bin su da kallo, sannu suka shiga yi mata gaba daya, bata tanka
su ba ta nufi bakin kofa bayan sun shigo ta duka ta dau doormat tana kakkabewa a
waje tace "Sannu kuma sai kace me ciwo ni patuu" Mama Hadiza tace "Inna mahaifiyar
Sadeeq ce..." Mikewa Inna tayi da sauri tana kallon Hadiza tace "Wacece mahaifiyar
tasa?" Mama Hadiza ta nuna mata, inna ta saki kabbara tace "Sannu baiwar Allah,
lallai kin iya haihuwa, ynxu ke ce mahaifiyar wnn yaro me kirki da mutunta babba?
Eh lallai Allah ya baki..." Hajiya Khadijah ta gaida ta with respect, frnds dinta
ma duk suka gaisheta, Inna ta amsa tana washe baki tace "sannun ku da xuwa bari in
debo maku ruwa" daga haka ta wuce kitchen ta dau faranti ta daura lemo biyu da ruwa
biyu ta kawo ta ajiye masu tace "Gashi ku dau daddaya ku sha, Allah ya maku
albarka" Hajiya Khadijah tace "Toh mun gode Kaka, dama gun mai gidan na xo bai nan,
shi ma mahaifin Imaan din yana Abuja aka ce min" Inna ta d'an yi shiru, sai kuma
tace "Lafiya kuke nemansu?? Ba an mayar maku da kaya kunce a bar shi ba, to gasu
can dai a daki ko tsinke ba a ta6a ba har ynxu a ciki" Hajiya Khadijah tace "A'a ba
wannan ya kawo mu ba Kaka" Inna ta sake fuska tana murmushi tace "Toh madallah, me
ya kawo ku kenan?" Hajiya Khadijah tace "Xuwa nayi, ga ni ga matar gidan nan, ga
Mai gidan, ga mahaifin Imaan da mahaifiyarta su tambayar min ita ko mai ni da
Sadeeq muka ta6a mata xata shiga ta fita ta hana aurensa da Imaan, idan kuwa tace
babu... to Billahil Azeem xan dau mummunan mataki a kanta, in dai ina numfashi
maganan nan baxai tafi a haka ba sai ta san ita ce silan bakin cikin d'a na, kafin
in dau mataki nace bari dai in xo ku tambayar min ita ko Sadeeq ya ta6a mata wani
abun ne...." Inna dake wurga ido tace "Ban fahimce ki ba 'yar nan? Wace matar gidan
a ciki kike nufi??" A takaice Hajiya Khadijah tace "Uwargidan wan mahaifin Imaan,
ita nake nufi" Inna tayi wani dariya murya can kasa tace "Toh Alhmdllh, ke ma dai
an gano maki ita ta raba auren d'an ki da Imaan kenan? To na ji dadin xuwan ki
gidan nan, na kuma ji dadin yanda kika tsaya kan d'an ki ba wasa, yanxu abinda xai
faru 'yar nan hakuri xa ki yi har xuwa ranan lahadi duk inda uban Imaan yake dama
xan kirasa ya dawo don a kan idonsa xa ayi komai, sannan Ahmadu ma bbu inda xai je
ranan, duk xa mu hadu, ga ni, ga ki, ga autata Hadiza, ga uban Imaan, ga
bafillatana uwar Imaan, ga ita matar da ku ka xo nema ga kishiyar ta, to sai ayi
magana me ma'ana gaban kowa, da kanta xata bude baki ta fadi me tayi har yasa aka
fasa wannan aure mai albarka kaca kaca..." Hajiya Khadijah tace "Toh nagode Kaka,
Allah ya kara girma" Inna tace "Ameen yar nan" mikewa Hajiya Khadijah tayi ta ma
Inna da Mama Hadiza da ta kasa cewa komai sallama ta nufi kofar, frnds dinta ma
suka masu sallama duk suka fita, Inna na murmushi tana kallon Mama Hadixa tace "Toh
Alhmdllh ba a bakina aka fara jin wannan xancen ba, Rukayya dai ta shiga uku ta
lalace in matar nan ta fallasa ta gaban kowa har shi Bukar, sai kuma in xuba ido in
ga matakin da Ahmadu xai dauka, shi kuma Bukar xan ga da wani bakin xai yi magana
idan ya ji wannan abun al-ajabin" sai kuma Inna ta fashe da kuka sosai tace
"Rukayya dai ta cuce mu, ta cuce mu, ta cuci jikata yanxu wannan mata da ta fita da
ita ce surkar Imaan fa" Mama Hadixa ta sauke ajiyar xuciya ta dai kasa cewa komai
duk jikinta yyi sanyi, a nan ta gane dalilin da yasa Umma ke ta sauri daxu. Tun da
Umma ta shiga daki take kuka kamar ranta xai fita banda bugawa babu abinda
xuciyarta ke yi, ta leka compound daga windown dakinta ya fi a kirga amma bata ga
alamar mahaifiyar Sadeeq da Mama Hadiza ba, tasan kila suna can bangaren Inna,
tunanin hakan yasa cikinta ya kara hautsinewa, don tasan shkkn mahaifiyar Sadeeq ta
gama fada masu har gida ta je ta sameta ta 6ata Imaan da mahaifiyarta, sai xaga
dakin take tana salati hawaye na bin idonta, da ta tuna ai sai dai su Abba su ji a
bakin Inna ba dai directly daga bakin uwar Sadeeq din ba sai hankalinta ya d'an
kwanta, gwara innan ta fada masu da bakinta, sun kuma santa da karin xance ko xa su
yarda ba duka ba... Ammi ta dinga kallon Imaan bayan ta shigo parlor da mamaki tace
"Daga Ina kike?" Imaan ta karasa da sauri ta rungumeta tana murmushi tace "Daga
gida Ammi, Ina yini" Ammi ta daga kanta tana kallonta tace "Ina Mujaheed din?"
Imaan tace "Tare muke, ya shiga gida" Ammi ta dinga kallonta sannan ta saketa tace
"Toh sannu da xuwa" Imaan ta xauna saman kujera still smiling tace "Nayi missing
din ki Ammi, Daddy yana Abuja koh" Ammi tace "Ehh yana can, bari in sauke abinci"
daga haka ta koma kitchen, mikewa Imaan tayi a hankali ta nufi dakinta. Bayan
Magrib Imaan na xaune tana cin abinci sai dai gaba daya hankalinta yayi kan
Mujaheed ta rasa dalilin da yasa hakan, may be don ta san he is still sad ne and
there will be no one to console him, a hankali ta dinga cin abincin duk da yanda
tayi missing girkin Ammi amma turawa kawai take bbu appetite, Ammi ce ta fito
parlor daga dakinta rike da wayarta tana kallonta ta karaso cikin parlon ta xauna
tace "Imaan what's happening?" Imaan ta kalleta da sauri tace "Na me Ammi?" Ammi
tace "Me yasa ku ka taho gida?" Imaan ta d'an Bude ido tace "Ya kawo ni ne kawai
Ammi fa" Ammi tace "Ya kawo ki kiyi me?" Imaan tace "Ba komai, anjima xa mu koma"
Ammi tace "Yanxu daddy ya kirani wai Inna ta kirasa ya taho gida ranan lahadi"
Shiru Imaan tayi tana kallonta, dai dai shigowar Mujaheed parlon da sallama Imaan
ta kallesa, ya karaso parlon yana kallon Ammi ya xauna kansa a kasa yace "Ina yini
Ammi?" Ammi tace "Lafiya lau, sannu da xuwa" yace "Ya gida" tace "Alhmdllh" Yace
"Abba yana Abuja" tace "Ehh ya tafi" yace "Toh Allah ya dawo da shi lafiya" Ammi
tace "Ameen" daga haka Ammi ta mike ta koma cikin daki, Mujaheed ya kalli Imaan
dake ta kallonsa, sunkuyar da kanta tayi tace "Have you eaten?" A hankali yace
"Yeah" ta kallesa tace "Nasan baka ci ba" ya d'an yi murmushi yana shafa kansa yace
"Na ci mana" kallonsa ta dinga yi, ya mike yace "Dama Ammi na shigo gaidawa" Imaan
tace "Xa kaje wajen Inna ne?" Girgixa mata kai yayi ya nufi kofa, ta d'an saci
kofar dakin Ammi sannan ta mike da sauri ta bi bayansa. Har ya sauka balcony tace
"Yaya" juyawa yayi ya kalleta, ta isa kusa da shi tana kallonsa, a hankali tace
"Plss in debo maka abinci ka ci??" Ya matso da ita kusa da shi ya ja hancinta yace
"Wanda na ci fa?" 6ata fuska tayi tace "Wllh baka ci ba, ni dai ka jira in debo
maka" murmushi yayi a hankali yace "Toh debo min" Da sauri ta juya ta koma ciki, ya
bi ta da kallo, direct kitchen ta shiga ta bude warmer din da Ammi ta xuba
shinkafar da ta dafa, duk da bashi da yawa sosai haka ta debar masa ta sa masa stew
da nama hudu, ta rufe warmer din ta juya xata fito taga Ammi tsaye bakin kofar
kitchen din, ji tayi kamar ta nutse kasa kawai ta huta, Ta kasa kallon Ammi ta fara
kame kame bakinta na rawa tace "Dama, dama abinci xan kai masa, Ammi shi ya
tambayeni" Ammi bata ce komai ba ta karasa cikin kitchen din, Imaan bata yarda ta
kalleta ba har ta fita kitchen din da sauri, tana shigowa parlor ta duka kusa da
plate din abincinta ta dau nama biyu ta kara a nasa tana satan kallon kofar kitchen
din sannan ta mike ta fita, bata gansa a waje ba, ta dinga bin compound din da
kallo amma babu alamar sa, part din su ta nufa kamar me counting step dinta ta
shiga parlon da sallama murya can ciki, babu kowa sai Tv dake aiki, taji dadin
hakan sosai, sama ta wuce ta nufi dakinsa tana kalle kalle ta bude kofar, xaune ta
samesa gefen gado yana danna wayarsa, daga kai yayi yana kallonta, ta shiga ta
kulle kofar dakin ta karasa kusa da shi ta ajiye masa abincin ta hade rai tace
"Shine ka wuce koh?" Jawota yyi jikinsa a hankali yace "Ba gashi kin kawo min har
daki ba" Tana kokarin mikewa tace "Xan tafi kar Ammi ta dinga nemana" ya ki saketa
yace "Ai a nan xaki kwana" xaro ido tayi ta kallesa sai kuma tayi dariya tace
"Tabdi, ni dai ka sakeni in wuce Yaya" yace "Toh wuce da abincin ki baxan ci ba"
shiru tayi tana kallonsa, sai kuma ta 6ata fuska tace "Ni wllh sai ka ci" yace "In
dai ba nan xaki kwana ba kuma ki bani abincin a baki to baxan ci ba" xaro ido tayi
tace "Toh babu spoon din bari in je in dauko a kitchen" ya matseta yace "Guduwa xa
ki yi" tace "Ae nasan idan na gudu baxa ka ci ba, spoon xan je in dauko in dawo"
yace "Toh je ki dauko" mikewa tayi ta nufi kofa sannan ta juya ta kallesa
ta wara masa manyan idonta tana dariya tace "Kai ma ka xo part dinmu ka kwana
mana" daga haka ta fice dakin.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

93.....

Karfe sha daya saura na dare Umma ta shigo dakin Mujaheed sanye da hijab dinta har
kasa, yana xaune ya jinginar da kansa da gado ya daga kai ya kalleta sannan ya
dauke kai, he looks so frustrated har lkcn kuma bai ci abincin da Imaan ta kawo
masa ba, Umma ta kulle kofar a hankali ta karaso cikin dakin tana kallonsa ta xauna
saman kujera, kana ganinta kasan tana tare da damuwa ba na wasa ba, and she looks
so sick, bai ce mata komai ba hakan yasa a hankali ta fara magana tace "Kana ji na
Muhd?" Kai ya gyada mata ba tare da ya kalleta ba still yace "Ina ji" Maimakon tayi
magana sai ta fara hawaye, sai kuma ta fashe da kuka sosai, shi dai bai yarda ya
kalleta ba bai kuma ce komai ba, tana girgixa kai cikin sanyin murya tace "I don't
know where to start from Mujaheed, ban san ta inda xan fara ba, amma lallai ka sani
duk abinda Safeenah ta fada gaskiya ne bbu karya ko daya a ciki, she said nothing
but the truth, kuma ba komai yasa na aikata hakan ba Mujaheed sai k'in da nake ma
Aisha, I've gone through a lot in my husband's house all bcos of that woman, ita ce
ta jefa ni cikin halin da nake ciki na sa6on ubangiji na, ta dalilinta na dinga
aikata abubuwan da na aikata, amma kuma da na san Allah xai yi Ikonsa ya juya abun
nan ya dawo kai na Abban ka ya baka auren Imaan wllh wllh da ban fara abinda na yi
ba, I wouldn't have done what I did, I still can't imagine you having kids with
Aisha's daughter, ban san ya xan dau lamarin nan ba idan ka haihu da Imaan Muhd,
har yau bana son auren nan naka da ita na fada da babban murya, bana so, bana so
har cikin raina, kuma baxan ta6a so ba, da auren nan ya dore wllh gwara ko raina ne
ubangiji ya dauka..." Kuka take yi sosai cike da tashin hankali, ta cigaba cikin
rawar muryar tace "Amma nasan babu yanda xan yi yanxu, ba abinda xan iya akan auren
nan da bana so, sai dai kawai in xuba ido in ci gaba da k'in auren, kuma ni baxan
ce xan sa maka baki a auren ba, I will neva do that coz you've always been obedient
to me from the first, ko me na sa ka in ma kana so, in ma baka so yi kake yi with
respect, baka ta6a min musu ba Mujaheed, kawai abinda na sani babu ruwana da matar
ka da abinda xata haifa, babu ruwana da su har abada, put it at the back of ur mind
baxan ta6a son auren nan ba kawai adalci xan maka, Baxan ta6a daukan 'yar wajen
Aisha surka ba, baxan dau 'ya yan da xata haifa a jikokina ba, Wanda Ina ma fatan
kada Allah ya bata 'ya ya da kai, lastly I want to say I am sorry for all the shame
and frustration I've caused you before and is still causing you now, don magana na
gaba sosai, you just have to take heart and pretend everything is fine" daga haka
ta mike tana goge idonta ta bar dakin Mujaheed ya bi ta da kallo, jinginar da kansa
yyi a hankali da gado ya lumshe idanuwansa hawayen dake makale idonsa suka sakko
kasa. Imaan na kwance daki sai dai ba bacci take ba, she's just imagining ko
Mujaheed ya ci abincin da ta kai masa ko bai ci ba, a hankali ta mike xaune ta
sauka saman gadon ta nufi press dinta, ta fi minti biyu tsaye kafin ta bude ta ciro
jakar islamiyyarta ta koma kan gado ta xauna ta bude jakar a hankali, takardar da
ya ta6a jefo mata ta window da dadewa ta ciro daga cikin jakar ta dinga kallon well
folded takardan sannan ta warware tana kallon rubutun ciki, ko layi daya bata kai
ga karantawa ba ta daga kai da sauri jin an bude kofa, Ammi ce ta shigo dakin ta
kulle kofar, kallonta Imaan ta dinga yi har ta karaso kusa da gadon ta xauna a gefe
tana kallon takardar hannunta ta amsa, Imaan ta sunkuyar da kanta gabanta na
faduwa, Ammi ta gama karanta Content din takardan ta ajiye gefe sannan a hankali
tace "Imaan" imaan ta daga kai tana kallonta, Cikin sanyin murya Ammi tace "From
all indication you are now happy getting married to Mujaheed right?" Imaan ta sauke
kanta kasa bata ce komai ba, Ammi ta girgixa kai tana murmushin karfin hali tace "I
am surprised har xa ki hakura lkci daya haka Imaan, I am very surprise at you, amma
ki sani har gobe baxan ta6a alfahari da auren ki da Mujaheed ba, never!" Kuka Imaan
ta fara yi a hankali bata ce komai ba, Ammi tace "And since you accepted him lkci
daya sbda ya maki dadin baki irin na maxa, to ki sani duk abinda xai je ya dawo
iyaka in maki addu'a Imaan, tunda kina ganin auren ki da Mujaheed alkhairi ne har
kika hakura cikin sanyi, kuma cikin kankanin lkci Allah yasa hakan..." Daga haka
Ammi ta mike ta nufi kofa Imaan ta bi ta da kallo tana hawaye, kafin ta fita tace
"Ammi shi fa Yaya babu ruwansa kema kin sani, kuma ai ni ban ce na hakura ba.."
Ammi ta juya ta kalleta sannan tayi murmushi a hankali tace "Ae bance da ruwansa ba
Imaan, Allah ya raba ki da sharrin uwarsa, ki je ku karata da shi..." Daga haka
Ammi ta fita dakin. Washegari Friday Umma taji shiru shiru dai Abba bai kirata ba
kamar yanda take ta jira, har dai ya fita gidan da safe, da yamma xuwa parlonsa
tayi bayan ya dawo duk da ba ita ce da girki ba amma shiru bai ce mata komai ba sai
ma tambayar ta da yyi me Mujaheed suka xo yi gida jiya, don throughout ranan ita
kanta bata ga Mujaheed ba, Tayi murmushin karfin hali tace "Kila sun xo gaishe mu
ne, amma Ina jin ai sun koma, don duk yau ban gansa ba" Abba bai ce komai ba ta
mike ta fita tana mamakin mai ya hana Inna ko Mama Hadiza yi masa magana a kan
xuwan Hajiya Khadija gidan, ko ba komai dai ta ji hankalinta ya kwanta, kila basu
yarda da uwar Sadeeq din bace, ta dinga fatan Allah ya sa maganar ta tafi a haka,
tsabar tashin hankali ko mutum daya bata fada ma damuwarta cikin kawayenta ba, tana
fitowa Parlor Maimoon tace "Umma Maman Surayya ta xo neman ki tana sama" Umma ta
wuce sama da sauri jin Hajiya Saude ta xo nemanta, xaune ta same aminyar tata a
gefen gadonta, Umma ta kulle kofa tana dubanta ganin yanayinta tace "Lafiya Hajiya
Saude?" Hajiya Saude ta fashe da kuka sosai ta ajiye takardan hannunta tayi tagumi
cikin rawar murya tace "Na shiga uku Rukayya tawa ta sameni Babansu Surayya ya
sakeni...." Umma ta xaro ido tace "Ya sake ki kuma Saude? Garin Yaya, me ya faru?"
Hajiya Saude ta dinga girgixa kai hawaye na sakkowa idonta tace "Surayya ta cuceni
ta kunyata ni gaban kishiyoyina Rukayya, hotel ta bi saurayi karban waya abokin
Babanta ya ganta, in takaice maki har hoto yayi mata, ya xo har gida ya nuna ma
uban, tun jiya ake abu daya bbu tashin hankalin da ban gani ba, bayan uban ya kusa
karyata da duka naga abun yyi yawa sai na nuna bacin rai na shine fa kamar wasa
bawan Allahn nan ya rubuta takadda ya bani, dama kwanaki ya min daya bayan wanda
yyi min shekaru biyar da suka wuce, yanxu fa duk ya katse igiyoyin, ki tashi
Rukayya ki rufa min asiri ki raka ni mu tafi gun mutumin nan baxai rasa abun yi kan
matsalar nan ba, fita gidan ubansu Surayya ba nawa bane..." Umma dake ta kallonta
baki bude tace "Toh ina ga wllh tawa matsalar ma ta fi taki Saude...." Nan Umma ta
kwashe duk yanda aka yi daga jiya xuwa yau ta labarta ma Saude tana matsar kwalla
ita ma, tana girgixa kai tace "Saude ban san wani tuggun Hajiya marafa da tsinannun
ya yanta xa su hada min ba nan ba da jimawa ba don nasan baxa su kyale xancen nan
haka ba, ga uwar yaron nan da muka je har gida muka sameta ban san tsarin da ta xo
tayi ma Inna da Hadiza ba, gashi har yanxu shiru Ahmadu bai ce min komai ba ko gaya
masa ne basu yi ba oho, ya xan yi Saude? Wllh daren jiya ban rutsa ba kuma gaba
daya na kasa tashi inyi sllh, yanxu haka xancen da nake maki tun safe bbu abinda na
saka a ciki na sai ruwan da nake ta Sha, ga dukkan alama ma xaxxabi xan yi" Saude
na matsar kwalla don ita ba ta Umma take ba ta kanta take tace "Wllh na ki me sauki
ne Rukayya a kan nawa, iyaka fa idan an tada maki maganar uwar yaron ki rantse ki
kuma rantsewa kiyi ta rantsewa kice baki je gidanta ba, rantsuwa ai ita ce kankat,
sai a bar ki da mahaliccin ki a bar ki da rantsuwar ki kawai, ni dai ki tashi ki
rakani gun bokan nan idan aure na ya mutu da sufyanu ai nawa ya kare a duniya, na
shiga uku na lalace gidan uban wa xan tunkara ina marainiya da ni" Umma ta girgixa
kai tace "Saude sai dai kije Balaraba ta raka ki gaskiya, don har abada ni da sake
komawa gun bokan nan, saninsa bai amfana min komai a rayuwata ba, kullum ni kenan a
gantale ban ta6a nasara na a xo a gani ba, meye amfanin raba auren da yayi aka aura
ma d'a na?? Shegen mutumi kawai katon arne dama yasan bai san gaibu ba ya dinga
amshe min kudi gashi daga karshe ya tarwatsa min rayuwa dubi irin matsalar da na
tsunduma kai na fa yanxu???" Hajiya Saude ta mike tana kallonta tace "Lallai kin
kasance butulu Rukayya, duk yanda na tsaya maki bamu gun wannan bokan ba mu gun
wancan Malamin da walakancin da xa ki saka min kenan??" Umma ta mike tace "Don
Allah Saude ki fita kiyi tafiyar ki nima a yanxu da kika gan ni wllh ta kaina nake
matsalata ta fi naki wllh wllh..." Hajiya Saude tayi wani murmushi tace "Toh nagode
kwarai Rukayya xan tafi, amma ki sani wllh kema sai kin girbe abinda kika shuka,
duk ta'asa da barnar da kika dinga aikatawa xaki gansu a kwaryar ki kwanan nan,
wannan da ya sameki shi ake ce ma wasa farin girki" daga haka Hajiya Saude ta fice
daga dakin kamar xata tashi sama tana goge hawayenta. Daren ranan Imaan na parlon
Inna xaune idonta a kan tv dake aiki sai dai bata san abinda ake yi ba gaba daya
hankalinta baya tare da ita, Inna kuma tana can bakin tap tana aikin gurje gurjenta
har ta gama ta shigo ta fara kakkabe kujerunta tana kallon Imaan tace "Ae yarinya
jibi akwai fasa mugayen bama bamai xa ayi a gidan nan, iyaka dai bam din ya
tarwatsa wa enda xai tarwatsa mu kuma muyi ta kanmu mu kara rike Allah, ke kuma
Alhmdllh yanda wannan mutumi Mujaheed ya dauke ki haka ya maido min ke sbda
tsayuwar dare da na dinga yi, abinda na nasani a nan gaskiya shine in har Mujaheed
bai fita hakkin ki na aure ba wllh wllh babu inda xa ki bi sa, in su Ahmadu sun
mutu to ni suma nayi, ba da ni xa ayi wannan ta6arar da abun kunyar ba, ko ya ta6a
shigar maki daki ya kwana ne??" Imaan dai sai kallon tv take, Inna ta yi mata tsawa
tace "Keee..." Da sauri Imaan ta juya ta kalleta, Inna tace "Toh wllh Bukar kika
share ba ni ba, kwana biyu da baki gidan nan bakina tsit bbu shegen da ya sa ni
magana, to dama wake sani maganan banda ke da Mujaheed din...." A fusace Imaan tace
"Toh wai ni nasan da ni kike ne" Sai kuma ta rufe fuskarta da kujera ta fara kuka
ta mike ta shige daki da sauri, Inna ta tabe baki tace "Toh ni ina ruwana idan ya
kai ki ya baro ki, duk da baxan ma yadda hakan ya faru ba tunda ba ubansa ya
halitto min ke ba, haka kawai ya same ki a banxa, to shi ne banxa ba ke ba" Imaan
ta kwanta saman gado tana turo baki a hankali tace "Ko Ina ruwanta ma..." Bayan few
minutes ta jawo wayar Inna dake saman gadon ta dinga kallon wayar sannan tayi
dialing number din Mujaheed, sai da ya kusa katsewa ya daga kamar xata yi kuka tace
"Yaya Ina ka tafi yau?" A hankali yace "Anjima xan dawo, where are you?" Tace "Ina
part din Inna" d'an murmushi yayi yace "Are you missing me?" Da sauri tace "A'a fa,
kawai naga ban ganka bane, kuma ban san ko ka ci abinci ba..." Yana murmushi yace
"Toh xan shigo yanxu, me xan kawo maki?" Rufe fuska tayi a hankali tace "Kaza mana"
Muryar inna taji tace "Yau naga jarababbiyar mata, shi Mujaheed din kika kira da
katin wayata?? Toh gaskiya sai dai in bar ki da Allah don ba Mujaheed ya saka min
katin ba, ba kuma uban Mujaheed ya saka min ba Bukar ne ya sa min kafin ya wuce,
wannan wani irin jaraba ce ni patuu? Uwar me kika hada da Mujaheed din xa ki kira
sa a wayata, ni dai na shiga uku da wahalar ki" imaan ta katse wayar ta jefar kan
gado ta juya mata baya fuska daure, Inna ta dauke wayarta tace "Waye kuma Mujaheed
da xaki kirasa da wayata muguwa kawai..." Daga haka ta fice daga dakin. Imaan na ta
kwance daki taji an bude kofar parlon Inna, mikewa xaune tayi tana kallon kofar
dakin.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

94.....

Mujaheed ya xauna parlon yana kallon Inna da ke juya furan gabanta tana kallon
ledan hannunsa, yace "Ina yini" tana murmushi tace "Lafiya lau Mai gida, sannu da
xuwa" Bai tanka ta ba, ta dau cup ta kusa cika masa da fura da nono ta mike ta basa
tace "Dama saboda kai na dama furan nan" amsa yyi ya ajiye xata dau ledan da ya
ajiye ya dauke da sauri yace "Ce maki aka yi ledan ki ne?" Tace "to sai nace maka
ci xan yi Mujaheed? Haba sai kace gantalalliya kuma, duba abinda ke ciki kawai
nayi" daga haka ta koma ta xauna fuska daure, Imaan ta tsaya bakin kofar daki tana
kallonsu, Mujaheed ya kalleta bai dai ce komai ba ta fito ta dau ledan tana kallon
Inna tace "Toh ni ina nawa furan?" Bata rufe baki ba Inna tace "Baxan bada ba"
Dariya Mujaheed yyi ya dau nasa ya mika mata, ta kalli Inna tana murmushi ta amsa,
mikewa inna tayi ta nufi kofa ta bude tace "Tashi ka fita ka ban waje Mujaheed..."
Mikewa yyi yana kallo Imaan yace "I will call you with her phone...." Ta turo baki
tace "She won't let that ai" Mujaheed yace "Hide the phone" shirun da suka ji inna
tayi bata ci gaba da masifa ba yasa suka kalleta matsar kwalla suka ga tana yi,
Mujaheed ya danne dariyarsa, Imaan ta ta6e baki ta dauke kai, cikin rawar murya
inna tace "Dama banda 6are wa xai xage ka?" Mujaheed ya kalli Imaan yace "Don't
forget to hide the phone" Imaan tace "Ohk I will do so" Mujaheed ya nufi kofa yana
murmushi yace "Sae da safe inna" daga haka ya fita ta kulle kofarta ta sa makulli,
Imaan xata shiga daki a fusace inna tace "Kada ki fara don ba uwarki Aisha bace mai
min gyaran daki kije ki xubar min da kasusuwan kaji ki cuce ni" Imaan ta tabe baki
ta dawo parlor ta ajiye ledan da cup din furan da Mujaheed ya bata ta tafi kitchen
dauko plate kafin ta dawo inna ta dauke cup din furanta da sauri ta juye a bowl ta
rufe tana cewa "Baxan bayar ba wllh" Har Sunday Imaan na part din Inna bata tafi
bangarensu ba don haka kawai ita dai ta ji tana kunyar Amminta, har Inna ta gaji ta
kyaleta kiran da Mujaheed ke mata ta wayarta iyaka tace masu idan katin ta ne to su
da Allah. Karfe goma saura Imaan na parlon tana kallo Inna kuma na shan shayi Daddy
ya shigo parlon, Mikewa Imaan tayi da sauri daga xaunen da take cike da farin cikin
ganinsa sai dai kuma ta samu kanta da kasa xuwa ta rungumesa kamar yanda ta saba,
murmushi yyi ganinta yace "Ba ku tafi ba Mamana?" Inna ta cafke tace "Ehh ni nace
bbu inda xata, ba sadaka aka ba Mujaheed ba da xai ki yi mata lefe, in dai bbu lefe
to baxata bar gidan nan ba Bukar, kai haka aka baka uwarta bbu lefe???" Daddy dai
bai ce komai ba ya xauna saman kujera, Imaan ta duka ta gaishesa tana murmushi,
yace "How are you doing?" Tace "Alhmdllh Daddy, ya hanya?" Yace "Alhmdllh" kallon
inna yayi yace "Ina kwana?" Inna tace "Lafiya lau Bukar, Allah maka albarka" yace
"Ameen, ya gida?" Tace "Toh ga gida dai mun gode Allah" yace "Toh ga ni na dawo
Inna" Inna tace "Aa ba xance gaka ka dawo ba, ka tashi ka tafi ka huta kafin a neme
ka kuma...." Shiru yayi yana kallonta can ya mike yace "Toh sai anjima" tace "Allah
ya kai mu" Imaan ma tayi masa sai anjima ya fita parlon. Karfe sha biyu Mama Hadiza
ta shigo parlon Inna dake ta xuba kamshin turaren wuta tare da mahaifiyar Sadeeq da
Hajiya Salmah aminiyarta, Inna ta fito daki ganinsu ta washe baki tace "Toh
Alhmdllh, sannun ku da xuwa" Hajiya Khadija ta xauna da kawarta sannan suka gaida
Inna, inna ta amsa ta dauko masu ruwa ta ajiye tana kallon Mama Hadiza tace "Toh
duk ki kirasu ta waya ai koh?" Mikewa Mama Hadiza tayi ta shiga daki, ba a dau lkci
ba ta fito, Inna ta shimfida tabarma ta xauna Mama Hadiza ma ta nemi waje ta xauna,
Aunty ce ta fara shigowa parlon sannan Ammi, duk suka dinga kallon mahaifiyar
Sadeeq sannan aka gaisa, tun da Abba ya kira Umma yace ta tafi parlon Inna taji
xuciyarta ya tsinke, wato sai yau xa ayi mata maganar da take tunanin babu shi jin
shiru shiru, dakewa tayi ta sa Hijab ta fito xuwa part din Inna shawarar da Saude
ta bata na mata ringing a kai, har dai ta iso parlon Inna fuskarta a daure, bata
ta6a jin faduwar gaba irin yanda ta ji a moment din ba lkci daya jikinta ya mace ta
kasa karasowa cikin parlon tana kallon Hajiya Khadija ko kiftawa babu, Inna na
kallonta tace "Sannu da xuwa Rukayya shigo mana..." Umma ta kalli Inna sannan ta
kalli Abba da Daddy dake parlon su ma, ganin Umma ta ki shigowa Inna tace "Haba
Rukayya sai kace yarinya kin wani makale jikin kofa, ke fa ake jira tun daxu, don
Allah ki rufa mana asiri ki shigo...." Lkci daya Umma ta kara daure fuska ta shiga
parlon ta nemi gefe daya ta xauna tana kallon direction din kofa, Inna ta kalli
Abba tace "Toh ko dai a kira Mujaheed ne, Ina son ayi komai kan idonsa" Daddy yace
"A'a ba sai an kirasa ba" Inna tace "Tohh ai shikenan" Hajiya Khadija na kallon
Umma da kyau tace "Kafin in fara magana Ina fatan kin gane ni dai Hajiya?" Umma ta
kalleta a takaice tace "Ina fa xan gane ki? Jama'ah ai da yawa" Wani murmushi
Hajiya Khadija tayi tace "Ehh dama ba lallai ki gane ni ba, kilan idan na fara
magana a kan abinda ya kawo ni xa ki gane ni" Hajiya Khadija ta kalli Inna tace
"Kaka wannan matar da kike gani kusan watanni biyu da suka wuce ta ta6a takowa har
cikin gidana ta sameni da wani batu da xan fadi kowa ya ji yanxu" kallon Hajiya
Khadija gaba daya occupant din parlon suka dinga yi with interest, Inna ma sai
gwalo ido take tana sauraron Hajiya Khadija, Hajiya Khadija tace "Wannan mata ta
sameni har gida tare da surkarta da kawarta, a kan maganar auren d'a na Sadeeq da
'yar gidan nan Imaan, a bakinta nake jin cewa Imaan sickler ce ba lafiyayya ba, har
kudaden da mahaifinta ke kashe mata duk wata a kan ciwonta sai da ta fada min,....
Bana son inyi nisa don maganganun bbu dadin ji, bbu irin bacin da matar nan bata yi
ma mahaifiyar yarinyar nan a gabana ba, babu kunya tace min in har na yarda d'a na
ya aureta to fa xa su mallake min shi kamar yanda suka mallake mahaifin yarinyar,
matar nan da ku ke gani ta fi minti ashirin tana magana na batanci a kan yarinyar
nan Imaan da mahaifiyarta a parlona, munafukar kawarta na taya ta, daga karshe nace
masu to nagode xan yi shawara a kan batun nasu, muka rabu da su a haka... abu biyu
na gano tare da baiwar Allahn nan a lkcn, na farko Hassada... na biyu kuma kiyayya
mai tsanani, na kuma ga alamar xata iya yin komai domin ta tarwatsa rayuwar imaan
da mahaifiyarta, she can go to any extent doing that, kwata kwata bata tsoron Allah
matar nan, muguwa ce, Ni kuma da na fi ta bayan sun bar gidana da few weeks na sa
aka kai lefen Imaan, shine ganin bata samu nasara ta wajena ba ta shiga gun bokaye
ta yi ma d'a na asirin da yasa yaji bai son auren kwata kwata, ta raba da sa imaan
sbda son xuciyarta...." Gaba daya mutanen parlon kallon Umma suke babu ko kiftawa
with shock, shi dai Daddy tunda ya kalleta sau daya bai sake kallonta ba ya
jinginar da kansa da kujera ya lumshe ido, Ammi tayi murmushin karfin hali hawaye
cike idonta tana girgixa kai, Mahaifiyar Sadeeq na kallon Umma da kyau tace "Ki
saurareni da kyau, ke dai kin gan ni ne kawai amma baki san wacece ni ba, you know
nothing about me, before going further don Allah Ina so ku tambayar min ita me
Sadeeq yayi mata?" Bbu wanda ya iya cewa komai cikin parlon, Mama Hadiza ta dinga
girgixa kai tana kallon Umma da ta tamke fuska tana kallon Maman Sadeeq, can Umma
ta mike tana kallonta da kyau tace "Hajiya ni kika gani a gidan ki? Ni Rukayyar? Ni
kuwa?? A Ina na san ki da har xan je gidan ki? Ni din?? Kinsan abinda kike cewa
kuwa? Uban me xai kai ni gidanki da ban ma san hanyar gidan ba, to wllh wllh wllh
karya take min Alhaji, na rantse ban san matar nan ba ban ta6a ganinta ba Allah
shaida, wllh ban santa ba ban san me nayi mata take son 6ata min suna haka ba,
innalillahi wa inna ilaihi raji'un..." Bude baki Hajiya Khadija tayi tana kallon
Umma da mugun mamaki, Aunty tayi wani murmushi tana girgixa kai, umma ta fashe da
matsanancin kuka tace "Idan na yarda da kazafin nan da sharri da kika biyoni har
gida kika min Allah ya tsine min, wllh sai an bi min hakkina ko nawa ne xan kashe,
wllh baxan yarda da wannan sharrin da bakin fenti da kika goga min ba" Inna ta
hangame baki tana kallon Umma dake kuka sosai tana huci, Umma ta isa gaban maman
Sadeeq cikin daga murya tace "Wllh wllh baxan yadda ba, ni Rukayyar ce naje gidan
ki na 6ata imaan da uwarta?? To wllh tun a duniya xa a fara mana shari'a dake, ba
Bulasawa ba in ma mai kudin duniya kike aure wllh sai an bi min hakkina, me na maki
xaki 6ata ni haka gaban mijina, uwarsa da kanninsa?? Me na maki? A ina na ta6a
sanin ki?" Wani murmushi kawai Hajiya Khadija take tace "Amma tunda nake ban taba
ganin makira, annamimiya, makaryaciya, kuma warce bata tsoron Allah irin ki ba, ke
shaidaniya ce a siffar mutum, ke din annoba ce a cikin jama'ah..." Bata rufe baki
ba Umma ta nuna mata yatsa a goshi tana huci tace "Uwarki ce shaidaniya annoba ba
ni ba" a hankali Hajiya Khadija ta mike tana kallonta tace "Ni ki nuna ma yatsa
kika xagi uwata??" Umma na huci tace "An nuna maki din, kiyi abinda xa ki yi idan
kin isa, haka kawai mata ki shigo min gida ki min wannan kafurin sharrin haka mai
muni" murmushi kawai Hajiya Khadija tayi tace "First na bari ne ki gama rantse
rantsen ki kafin inyi reminding din ki gidana akwai Cctv camera, sannan secondly
sai kin san kin nuna min yatsa a goshi" Inna ta mike tana salati tace "Rukayya kin
ja ma kanki babban bala'i da bamu san iyakarsa ba tunda kika daga rubabben shegen
yatsan ki kika dunguri goshin wannan baiwar Allah, wllh kin debo ruwan dafa kan ki,
bbu abinda ya sha kan Ahmadu balle ni...." Mikewa Abba yyi ya fita daga parlon,
Umma na kallon Inna cike da masifa tace "In sha Allahu baxan ga bala'i ba, a kan me
mata xata shigo har gidana ta min irin wannan kazafin inyi shiru? Wllh baxan yarda
ba duk inda xa mu tafi sai dai mu tafi" Hajiya Khadija ta mike tace "Ki saurareni,
sai na nuna maki ke a makiran ma karama ce, sai na nuna maki karshen ki tun a
duniya,
kuma sai kin san ba a cutar min da Sadeeq, da acuce sa gwara an cuceni" daga haka
Hajiya Khadija ta fice daga parlon kawarta ta mike ta bi bayanta, inna ta saki
shewa tana kallon Umma dake xufa tana huci tace "Anyi walkiya mun ganki axxaluma
diyar shaidan, dama tun ba yau ba nasan mugun abinda kika aikata ma jikata ya dawo
kanki aka aura ma d'an ki, d'an Albarka, Toh Alhmdllh ba a bakina aka ji wnn
mummunan labarin ba, in kin cuce wani kin kwana lafiya to wani ko dare ma baxa ki
isa ba kiji in gaya maki, Sai dai in maki fatan Allah ya raba ki da wannan mata
lafiya, in dai jikata mutum yace xai cuta ya shiga uku ya lalace a duniya kuma yyi
ta ganin ba dai dai ba kenan, kuma kinyi asara duniya da lahira tunda kika rike
boka da malamai maimakon Allah da ya halicce ki...." Shigowar Abba yasa inna tayi
shiru tana huci, yana kallon Umma ya mika mata takardan hannunsa yace "Bana son ki
kara kwana gidan nan yau Rukayya...." Umma ta dinga kallonsa da idanuwanta Kamar xa
su fito xuciyarta na bugawa can ta karbi takardan da sauri ta warware tana kallon
content dinsa, wani kuka ta saki a parlon tana kallon Daddy hankali tashe ta nufesa
tace "Saki na fa yayi baban Imaan.... Wllh saki har biyu yayi min baban Imaan"

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

95.....

Shi dai Daddy bai ce komai ba sai kallon Umma yake, Inna tayi mitsi mitsi da ido
tana jiran ta ji yyi magana, kawai ya mike ya fita daga parlon, Umma ta fashe da
matsanancin kuka ta xauna kasa tace "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un, na shiga
uku na lalace" Inna ta wangale kofa da sauri tace "A'a rufa min asiri ba kya shiga
uku a parlona dake tare da albarka kaca kaca ba Rukayya, tashi ki tafi kiyi ta
kanki, Allah ubangiji yyi mana tsari da irin ku a duniya, Allah ya saka ma d'a na
Ahmadu da xuwa gurin boka da malamai da kika dinga yi da dukiyarsa, Allah sarki
Mujaheed, a duniya dai kam bai y sa'ar uwa ta gari ba, amma da sauki tunda ga shi
da Kaka mai tsoron Allah ba kama hannun yaro, sannan ga Amina matar ubansa ita ma
matar kirki, Imaan kuma Allah ya isa tsakaninta dake cutar da ita da kika yi, Allah
ya isa mata ya saka mata, in sha Allahu sai Allah ya saka mata" Kuka kawai Umma
take tana kallon Inna, Inna ta washe baki tana kallon su Mama Hadiza tace "Yo Mutum
ma ya rike Allah hannu bibbiyu ya ya kare da duniyar balle ita da ta rike boka"
Ammi ta mike a sanyaye ta fita parlon wiping off her tears, Umma ta hade kanta da
kujera tana kuka sosai tace "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un..." Inna tace "Ni
dai ki tashi ki bar min parlona Rukayya kada ki ja min wata fitinar, kada ki ja min
fushin ubangiji ki tashi ki tafi" mikewa Umma tayi ta fita parlon tana kuka kamar
ranta xai fita, Aunty tayi tagumi duk jikinta yayi sanyi tana kokarin maida hawayen
idonta, Mama Hadiza ma dai ta kasa cewa komai don duk da sanin halin Umma da tayi
amma gaba daya hakan taji bai mata dadi ba, bata taya xaton hukuncin da yayan nata
xai dauka kenan ba, Ina laifin ma saki daya, bbu wanda ta fi tausayi kamar
Mujaheed, don ko ba komai mahaifiyarsa ce. Part din Daddy Umma ta shiga da sauri
bayan ta bar parlon Inna, Daddy na xaune parlor har lkcn ya kasa gaskata abubuwan
da ya ji daga bakin mahaifiyar Sadeeq game da Umma, yasan tabbas Maman Sadeeq
baxata tako har gida tayi ma Umma sharri ba gashi tace xata kawo evidence tunda
akwai Cctv camera, but he is trying hard not to believe it kada tsanar Umma yyi
masa yawa a xuciya, Ammi dai tunda ta shigo bata ce masa komai ba ta shiga daki duk
iya daurewan da tayi kada ta xubda hawaye ta kasa ta dinga kuka tana tunanin me
tayi ma Umma a rayuwa haka irin wannan kiyayya da take mata da only child dinta,
ita dai Allah shaida ba ita tace Abba ya ga Aunty yace yana so ba, tun suna yara
suke tare da aunty ba wai rana tsaka kawancensu ya fara ba, dama kuma tun farkon
aurenta da Daddy Umma ke mata hassada saboda a wadace take da komai kasancewar bata
da kowa gabanta, babu abinda daddy ya raga ta da shi duk da rashin haihuwarta da
tsangwamar Inna jefi jefi, ita kuma Umma tana da yara sannan makarantansu masu
tsada ne sosai tun a lkcn, sai gashi Abba ya kara auren aminiyarta wanda hakan yasa
abu ya kara ca6e masu da Umma, Umma na tunanin hada baki tayi da Amina ta aure mata
miji don kusan ko da yaushe Amina na tsohon gidansu ta xo gun Ammi, Ammi ta girgixa
kai hawaye na sakko mata tana tantama anya da gaske akwai mutane masu irin halin
Umma a duniya kuwa ko ko ita kadai ce dai, don kiyayyar da tsanar yayi yawa, Sai
gashi that not been enough tilon 'yar ta an aura ma jinin Umma, tasan dai dai da
second daya Mujaheed bai ta6a supporting mahaifiyar sa a kan abubuwan da take ba,
but kuma ai dole yyi mata biyayya domin ko uwa ce, gashi yanxu an kara sakinta for
the second time ta dalilin Imaan, bayan sakin da aka mata years back ta dalilin ita
Ammin, ko saboda haka ai baxata ta6a barin Imaan ta xauna lafiya gidan Mujaheed ba,
tunanin hakan yasa Ammi ta kasa daina kukan da take. Tun da Umma ta shigo parlon
Daddy yyi mata kallo daya ya dauke kai, durkusawa tayi gefensa hawaye na bin
kuncinta cikin rawar murya tace "Don girman Allah ka ceci rayuwata Abban Imaan, ka
dubi Allah kayi ma d'an uwanka magana ya janye batun sakin nan, wllh bani da inda
xan je in ji dadi da ya wuce gidan nan kayi min rai Abban Imaan kada a raba ni da
'ya yana, duk abubuwan nan da suka faru wllh sharrin shaidan ne da rudin duniya, na
kuma yadda nayi laifi, ka yafe min ba don halina ba ka sama min mafita Abban Imaan"
daddy dai ya jinginar da kansa da kujera bai ce mata komai ba, kuka take sosai tana
kallonsa, Jin yyi shiru ya ki cewa komai cikin rawar murya tace "Domin Allah kada
ka biye ta halina Abban Imaan, in ci darajan 'ya yan da na haifa a gidan nan, in ci
darajansu don Allah...." Kuka take sosai tana kallonsa, Sai a sannan Daddy ya
kalleta amma ya kasa cewa komai, mikewa yayi kawai ya nufi kofa walking slowly ya
fita parlon, Umma ta fashe da matsanancin kuka, ta mike ita ma tana kallon kofar
dakin Ammi ta nufi dakin ta bude ta shiga, Ammi dake xaune gefen gado ta kasa daina
hawaye ta daga kai tana kallonta, Umma ta karasa cikin dakin ta xauna gefen gado
tana share hawayen idonta wasu na kuma xubowa, cikin rawar murya tace "Don Allah
Hajiya Aisha kiyi ma Abban Imaan magana ya sa Baki a lamarin nan, ya rufa min asiri
kada Ahmad ya sake ni, wllh duk sharrin shaidan ne, ko domin albarkacin auren da
aka hada na Imaan da Mujaheed kada a bi ta halina" Ammi dai bata iya ta ce mata
komai ba tana share hawayen idonta. Daddy na fita daga part dinsa parlon Abba ya
wuce, ya buda kofar a hankali ya gan yayan nasa xaune parlon, Mujaheed na duke kasa
gefensa ya rike kansa, Abba Kuma ya jingina kansa da kujera yana kallon saman
parlon, Xaunawa Daddy yayi yana kallon Abba, bayan few seconds cikin sanyi yace "I
am sorry about what happened barrister, amma ba a yanke hukunci cikin fushi, this
is very wrong, beside hukuncin is too strict, diyata ta cuta ba wata 6are ba, we
have the right to forgive, domin ko wani dan Adam ajizi ne, no one is above
mistake, kuskure ta riga tayi sai da Allah ya tsare na gaba ya kuma shiryeta, da
sauki tunda a gida ne hakan ya kasance ba a waje ba, we have to solve our problem
with outsiders intruding, wannan magana bai kai ka yanke hukuncin da ka yanke ba
Barrister, I am really not happy about this, ko ba komai ya kamata Hajiya Rukayya
ta ci albarkacin 'ya yanta a gidan nan, don haka na xo neman alfarman ka mayar da
ita, duk sharrin shaidan ne ba wani abu ba, Ni na yafe mata, Imaan ma nasan baxata
rike ta a xuciya ba tunda uwarta ce, haka ma mahaifiyar Imaan, daga karshe kuma
Allah ya shirye mu gaba daya ya raba mu da son xuci'an da xai kai mu ga dana sani
mara amfani, Hajiya Rukayya deserve to be pardon albarkacin yaranta...." Abba yayi
murmushin karfin hali yace "Babu aure tsakaninmu kuma, babu sauran igiyana a kanta
don haka before dusk ta bar gidan nan...." Shiru Daddy yyi yana kallonsa ya kasa
cewa komai, Babu wanda yace komai a parlon har bayan kusan minti biyar, Mujaheed ya
mike a hankali ya nufi kofa ya fita parlon, Daddy ya girgixa kai very sad yace "Am
not happy at this Barrister, a ta dalilin diyata fa ka sake matar ka?? Why? Wannan
wani irin xumunci ne namu? Komi Rukayya xata yi gidan nan baxa ta ci albarkacin
yaranta ba, don ta cuci Imaan daga karshe ba Mujaheed bane ya auri Imaan din? Plss
do something about this Barrister..." Abba ya girgixa kai yace "Ka dai san kwanaki
na ta6a mata saki daya, yanxu kuma nayi mata biyu so that's the end tsakanina da
ita, taje idan ni na cuceta a iya xaman mu na kusan shekara 35 Allah ya saka mata,
idan kuma ita ta cuce ni na yafe mata albarkacin xuri'ar dake tsakanin mu" Daddy ya
kasa cewa komai duk jikinsa yyi sanyi. Inna ce ta bude kofar parlon ta shigo tace
"Toh Ahmadu ko ni xan fita in samo babban mota a kwashe kayan matar nan a gidan nan
ne, kada fa dare yayi a xo ana guje gujen fitar da kaya hakan ba shi da kyau
gaskiya" Abba dai kallonta yake bai ce komai ba, Daddy kam ko kallonta bai yi ba,
Inna tace "Toh kun yi shiru kuna kallona" Mikewa Daddy yyi ya nufi kofa ya fice
daga parlon, inna ta bi sa da wani shegen kallo bayan ya fita tace "Gantalalle
kawai, da kyar idan ba hakuri ya xo baka ba da yake ba hankali ya ishesa ba, tunda
uwata ta haifeni ban ta6a ganin mutumi irin Bukari ba, Yar taka kwaya daya tak a
dinga bin ta da irin wannan cuta haka amma sbda karfin hali ka dinga nuna komai ba
komai bane sbda baka tsoron Allah, tun fa yana karami haka yake wllh, duk cutar da
xa a masa sai yace ya yafe sbda tsiya, gashi hakan ya bi sa har girmansa, wnn ai
bala'i ne da dabiyar tsiya, Ina kuwa xan yafe ma wanda ya cuce ni, ai Allah ma bai
ce haka ba, idan ban bi a sannu ba ma ai sai Allah yyi fushi da ni...." Abba dai
bai ce komai ba, inna ta ja tsaki tace "Wlh yau da ace ba Imaan matar nan ta cuta
ba to ni me iya yafe mata ne, kuma ince Ahmadu ma ya yafe mata, Amma imaan ce fa??
Takwara ta ce fa? Ita daya gare d'a na Bukar fa? Yanxu ko don irin xuciyar Bukar
Rukayya ya kamata ta cuci yar sa kwaya daya da Allah ya basa? Me yayi mata da xafi
haka, banda ma kyautatawa da tsaya mata da yake yi a lamarinta?? idan ma tana jin
haushin Aisha ne Imaan baxata ci albarkacin ubanta Bukar mutumin kirki ba..." Kuka
inna ta fashe da har da shessheka tace "Ni Mujaheed ne ma abun tausayi, sam yaron
bai yi dacen mahaifiya ba, gashi yaron kirki da yasan ya kamata ga tarbiya kaca
kaca, ko ya xai dau wannan xancen oho, Ni dai Allah ya isa tsakanina da Rukayya
bakin cikin xuwa makka duk shekara da ta min, shari'a ta da ita sai gaban ubangiji
don wllh wllh ban yafe ba, uban wa gareni dama da xai kai ni makkan duk shekara
banda Sadeeq din....." Daga haka ta fita parlon tana share idonta. Ammi na xaune
dakin Imaan tun bayan fitar Umma, Banda hawaye babu abinda Imaan ke yi har da
shessheka, Ammi dai tayi tagumi ta ma rasa abun cewa, cikin rawar murya Imaan tace
"Ammi ko don saboda Yaya ai bai kamata Abba yayi haka ba, I don't know how he will
take this, why will all this happen because of me?" Ammi dai tayi shiru bata ce
komai ba, Imaan na son gaya ma Ammi abinda ya faru ranan Thursday a zaria da ya sa
suka dawo gida amma ta kasa gaya mata sbda alkawarin da tayi baxata fada ba a gida,
da ta tuna ita
ce dalilin mutuwar auren Umma sai ta ji wasu sabbin hawayen sun xubo mata, Ammi ta
girgixa kai a hankali tace "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un...." mikewa tayi ta
fita dakin a sanyaye, duk da tasan babu sauran aure tsakanin Umma da Abba ta fita
xuwa parlon Abba. Karfe biyar saura kamar yanda Abba yace babban motar da xai
kwashe kayan Umma tass ya shigo gidan, Umma na can dakinta tare da Rahma da Ummi da
Maimoon dake taya ta kuka kamar ransu xai fita, Seeyama ma na xaune dakin ta kasa
cewa komai sai hawaye, Aunty dai na tsaye jikin mirror tayi tagumi ba uhm ba uhm
uhm.... Har parlor Mujaheed ya samu Abbansa ya duka nan kasa cikin sanyin murya
yace "Abba dama nace don Allah a bar kayan yanxu ko daga baya sai ni in kwashe"
shiru Abba yyi yana kallonsa, can Abba ya gyada kai a hankali yace "Toh ba damuwa,
do you have any idea of where she will be going now?" Mujaheed ya sunkuyar da kansa
yace "Xan kai ta Zaria yanxu" Abba yace "Ur home?" Mujaheed ya gyada masa kai, Abba
yace "Ina xaka ajiye Imaan?" A hankali Mujaheed yace "Nan kaduna" Bayan few seconds
Abba yace "I am sorry Mujaheed, I also Neva saw this coming but I think this is the
best, ga can abubuwan da kace min sun faru a gidan ka wanda har ya janyo ka saki
matarka bbu sauran aure tsakanin ku, sannan ga wannan, sure i was frustrated, but
na shanye abubuwan da mahaifiyar ka take min shekara da shekaru, Ina barin ta tana
cin albarkacin ku, but today's own is beyond me, I think this is best, Allah kuma
yasa hakan ya fi alkhairi, Ina me baka hakuri coz I know this is sad, sannan abinda
yasa nace ta tafi yau saboda wannan mata ta Bulasawa, kaga ko da xata dawo bata
ganta ba komai xai xo da sauki, mu kuma sai mu basu hakuri, sai kaga albarkacin mu
ta hakura..." Mujaheed bai iya yace komai ba hawaye ya kawo idonsa, Abba ya mike ya
shiga daki ya dauko kudi ya mika masa yace "You give her this, sae ta rike a hannu,
Allah ya maka albarka" mikewa Mujaheed yyi kansa a kasa yace "Toh ngd Abba" daga
haka ya fita parlon.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

96.....

Bayan sati daya da komawar Umma Zaria Abba ya kira Mujaheed parlonsa da yamma,
Mujaheed ya xauna kasa yana kallonsa yace "Ga ni Abba" Abba yace "Na ji shiru baka
ce xa ku koma gida da matar ka ba, what's happening?" Murmushi Mujaheed yyi yace
"Abba Inna ce" Abba yace "Me Innar tayi?" Mujaheed yace "She said I am not leaving
with her" Abba yace "Ko saboda me?" Wani murmushin Mujaheed yyi bai dai ce komai
ba, Abba ya gyada kai yace "Tashi ka tafi" mikewa yayi ya fita parlon. Inna ce
tsaye parlonta inda take shiga ba nan take fita ba tana kallon Imaan, Imaan dai na
kwance idonta a kan Tv bata yarda ta kalleta ba, Inna tace "Yau naga abinda ya
isheni yarinya mara kirki kawai, to a kan me xaki debar ma mutumi dambuna kuma d'an
walakanci ya bar min shi a walakance bai ci ba? waye kuma Mujaheed Allah na tuba
mutumin da na yi wahala da shi, meye nasa ne ban sani ba, 'ya yana suna wahala dani
ku kuma ku dinga cinye min" ita dai Imaan bata tanka ta ba, Inna tace "Yau naga
jarababbiya wai ni xata nuna ma son miji, Yar figigiya dake kin san dadin miji, ba
kunya ba tsoron Allah ki satar min nama ki kai masa shi kuma ya ki ci, anya Imaan
kina son gamawa da duniya lafiya kuwa?" Shigowar Abba yasa Inna tayi shiru, Imaan
ta mike xaune tana masa sannu da xuwa, Abba ya amsa yana kallon Inna ya xauna ya
gaisheta, Inna ta shimfida tabarma fuska daure ta xauna tace "Lafiya lau Ahmadu ya
aiki" yace "Alhmdllh" Imaan ta gaida Abba sannan ta mike ta wuce daki Inna ta bi ta
da harara sannan tayi kwafa, shi dai Abba kallonta yake bai ce komai ba, Inna tace
"Daxu ma Bukar ya kirani muka gaisa nace Allah yayi masa albarka, ya rabasa da
sharrin mutum da aljan, ya shiga ko ina a sa'a ya fita a sa'a" Abba ya gyada kai
yace "Hakan na da kyau ai" mikewa Inna tayi tace "Bari in d'an yi shara in dawo
Ahmadu" Abba yace "Magrib ai ya kusa Inna, dama kuma magana na xo xa mu yi" Inna ta
koma ta xauna tace "To lafiya dai ko?" Abba yace "A'a lafiya lau, kawai naga ya
dace Mujaheed ya dau matarsa su tafi ko, tun da Alhmdllh ynxu bbu wata matsala...."
Inna ta katse sa tana mitsi mitsi da ido tana girgixa kai tace "Ae ba Mujaheed ya
halitto min ita ba balle in basa ita su tafi, waye kuma Mujaheed?? ku dai wllh ku
dinga tsoron Allah komin rintsi, Ahmadu duk matan ka biyu da ka aura ka gaya min
warce aka ta6a baka bbu lefe? Shi ma Bukar ya gaya min ko bbu lefe ya auri Aisha,
sai Imaan ce xa a kai gidan Mujaheed ba lefe sbda ance maku gantalalla ce? Mutane
dai bbu tsoron Allah ko digo a xuciyarsu, tirr wlh" Murmushi Abba yyi yace "Inna ai
ba yace baxai yi bane, xai mata in sha Allah, wannan ai dole ne" inna tace "Toh
yayi mu gani tukun, gwalagwalai hudu na kirga a lefen da Bulasawa yyi mata wllh
tllh, duk atamfofin kuma babu na kasa da dubu hamsin, ga leshi duk 'yan dubu dari
dari, to me yafi haka ma'ana?? kaiiii Ahmadu ku ji tsoron Allah, wllh Imaan ba
banxa take ba, a kan lefen nan ma ni sai in soke auren nan gaba daya in ga ta tsiya
don uwa ta bata ce min je ki kya gani ba, haka kawai ya cutar min jika ya kai ta ya
barota bbu kayan aure jikata ta walakanta, to Allah ya tsine ma wanda yace auren
xumunci ne ko ba ayi lefe ba bbu komai, don da alama an rada maku hakan ne shi yasa
ku ke shashantarwa, to wllh bari ku ji, sai na ga akwati guda dai dai har sha biyu
sannan Imaan xata bar gidan nan, idan ba haka ba gwara inyi ta kallon abata, ba
ruwana ni yar gaskiya ce..." daga haka ta mike ta fita daga parlon tana cewa "A dai
dinga tsoron Allah komin rintsi, ance maka don kai ka haifi Mujaheed sai in ki gaya
maka gaskiya, haka kawai mutumi ka lallabo ka xo min nan don ka min dadin baki a
cuci Jikata, Albarka uwata ta dinga sa min kafin ta rasu wllh..." Murmushi kawai
Abba yake, can ya mike yana girgixa kai ya fita parlon. Karfe tara na dare Mujaheed
ya shigo parlon Inna da sallama ya ganta xaune saman darduma tana xuba gyangyadi ga
carbi a hannunta, tsayawa yyi yana kallonta, can yyi murmushi ya nufi kofar dakin
walking without making any sound, yana bude kofar dakin Inna ta bude ido daya a
hankali tana kallonsa har ya shiga dakin, yana shiga Imaan na fitowa daga bathroom
daure da towel, xaro ido tayi ganinsa, lkci daya ta nufi gefen gado da sauri ta
xauna tana kallonsa kamar xata yi kuka tace "Yaya shine xaka shigo bbu sallama,
gashi ban sa kaya ba, kuma idan inna ta gan ka fa? Don Allah ka fita plsss" Juyawa
yayi xai rufe kofar dakin ya ga Inna tsaye kyam bakin kofar tana kallonsa, duk da
yanda ya so dakewa kada yyi dariya sai da yayi dariyan yana sunkuyar da kai, ta
cakumosa fuska a murtuke tace "Dakina yyi maka kama da otal Mujaheed? Yaushe ka
lalace haka bani da labari, bbu kunya balle tsoron Allah ka afka ma yar yarinya
daki daga ita sai tawul ta fito wanka? Me hakan ke nufi fisabilillahi? Meye manufar
shigo mata tana tsirara?" Ya wara ido yace "Toh xa ki hanani shigowa gun matata ne
Inna?" Inna tace "Toh wllh ka gaggauta neman tubar ubangiji, ta ina ta xama matar
ka baka fita hakkinta na aure ba Mujaheed? ga sadakin ka can a cikin dirowa sai in
dauko maka in baka tsiyar ka yanxun nan kar ka kawo min nansans, Ina ce da shi kake
takama?" Ya shafa kansa yana murmushi yace "Toh ai Aunty ta fara hada mata lefen
sai ki bani matata mu tafi koh?" Inna tace "Wacece kuma Aunty? To wllh ka rufa ma
kanka asiri ka amso kudadden ka ka samu yar gayu ka bata ta hada ma jikata lefe,
kwata kwata ban yarda da siyayyan Aisha da Amina ba, duk yaushe suka waye? sai kaga
kayan da suka hada ma Yusuf duk rubabbu ba kyau, Kamar daga kauye" dariya kawai
Mujaheed ke yi yana kallonta tace "Atoh ni ba ruwana" tana rike da shi ta juya xata
fita dakin yace "Toh sakeni mana Inna" Bata sauraresa ba har suka fita dakin ya
juya yana kallon Imaan da tayi masa gwalo, wani murmushi yyi yana gyada kai Inna ta
kulle kofarta sannan ta sakesa, ta xauna tace "Kudin akwatuna nawa ka bata?" Yace
"Idan ta gama hadawa xa ki gani ai" tace "Ni da xa a ji ta nawa ma a siya mata sakk
irin na Bulasawa har kayan ciki" Mujaheed bai tanka ta ba, bayan kusan minti goma
Imaan ta fito sanye da hijab har kasa sai xuba kamshi take, kallonta kawai Mujaheed
yake har ta xauna, Inna tace "In xuba maki abincin ne ko ko?" Gyada mata kai Imaan
tayi, Inna ta mike tace "Ina xan bari ki lalace a shiyana Bukar yyi tunanin bana
baki abinci ne ya kullace ni" daga haka ta shiga kitchen, Mujaheed ya bi ta da ido
sannan ya mike, imaan na ganin haka xata tashi yyi saurin rikota, kamar xata yi
kuka murya can kasa tace "Yaya ka bari kaga Inna xata fito ynxu fa.. " xaunar da
ita yyi kusa da shi ya jawota jikinsa ya daura forehead dinsa kan nata yana kallon
lips dinta murya can kasa yace "Ke kika ce mata sai na maki lefe koh??" Xaro ido
tayi tana son komawa baya yaki saketa, rufe fuskarta tayi jikinsa hankali tace "A'a
wllh, ita ce dai ta fadi haka...." Rungumeta Mujaheed yyi yana son dago kanta taki
yarda, Inna na fitowa kitchen rike da plate din abinci tayi kasake baki bude tana
kallonsu, sai kuma ta saki salati, da sauri Imaan ta fara turasa tanq xaro ido amma
ya ki saketa, Inna ta ajiye abincin hannunta a kasa tace "Mujaheed iskancin naka a
parlor na xae kare yau kuma? Haka kawai mutumi ka shiga ka matse min yarinya ba
tsoron Allah??" Bata jira cewarsa ba ta tafi da sauri ta bude kofar parlon tace
"Taho ka fita kada Ahmadu ya fitar min da kai yanxun nan, wannan wani irin iskanci
ne da lalata, mutumi ka shigo xaka lalata yar mutane a parlona, meye ma'anar hakan
ma dai tukun?" Imaan dai tuni ta janye daga jikinsa kamar xata yi kuka, a fusace
inna tace "Ke kuma jarababbiyar yarinya kin wani sakar masa jiki kin makalkalesa
shashasha kawai jarababbiya, to wllh kai ki xai yi ya baro ki don ma kiji in gaya
maki, waye kuma bai san iskancin namiji, ohhh ni patuu yau naga iskanci gun yara, a
parlon nawa kuma babu tsoron Allah xaka makalkaleta Mujaheed, Toh wllh bari Ahmadu
ya shigo ba dani xa ayi wnn iskancin ba dama kada Mujaheed ya sake xuwa min nan
wllh ni ba gantalalliya bace kuma ni ba yar iska bace" Imaan ta mike tana turo baki
ta wuce daki, Inna na kallon mujaheed a fusace tace "Baxa ka xo ka fita ba ko sai
na tafi na kira ubanka, banda baka da tsoron Allah imaan din ma nawa take gaba daya
fisabilillahi da xaka matse ta haka kan kujera Mujaheed? Ni wllh ban taba ganin
haka ba tunda uwata ta haifeni, to me xaka mata?" Mujaheed ya mike yace "Da kin yi
ki shiru kiga abinda xan mata ai" daga haka ya bi ta gefenta xai fita dakin ta kai
masa dundu a baya tace "Toh Allah ya isa wllh, ka je kai da Allah, wanda bai yi
iskanci ba ma a rayuwar ya ya kare balle yyi iskanci" murmushi yyi bai kuma tsayawa
sauraranta ba yyi wucewarsa. Washegari da safe Imaan ta tafi gaida Amminta daga
part din Inna bayan inna ta jaddada mata ko minti biyar kada tayi a can don ita
tsoron kowa take a gidan bata yadda da kowa ba, A bedroom Imaan ta samu Ammi xaune,
ta duka kasa jikin gado tana kallonta a hankali tace "Ammi Ina kwana" Ammi tace
"Lafiya lau, kin tashi lafiya?" Imaan tace "Alhmdllh, daxu da kika xo ina wanka"
Ammi tace "Ohk, kinyi breakfast?" Kai Imaan ta gyada mata, Ammi ta yi shiru sannan
tace "Me Mujaheed din yace maki kan komawar ku?" Imaan ta sunkuyar da kanta tace
"Inna ce tace A'a" Ammi tace "Ba Aunty ta fara hada maku kayan ba" Imaan dai bata
ce komai ba, Ammi tace "Idan ma xa ki daina biye ma Inna ke daina biye mata ki bi
mijinki ku tafi, Daddy ma yayi magana jiya" Kai kawai Imaan ta gyada mata, Ammi
tace "Ki tafi kitchen ki debi abinci, idan kuma shayi xa ki hada sai ki hada, ko in
soya maki kwai?" Imaan tace "Ammi nayi breakfast fa" Ammi tace "Toh shikenan" Shiru
ne ya biyo baya, Ammi tace "Kina ji na?" Daga kai Imaan tayi ta kalleta tace "Ina
ji Ammi" Ammi tace "Bana son ki saka duk abubuwan da suka faru a ranki, no matter
what you've got to respect ur mother in law, in ma tana son ki in ma bata son ki,
duk wani abu na kyautata da kika san ya kamata ki dinga mata albarkacin d'an ta da
kike aure yanxu, kaninnsa ma gaba daya ko suna sonki, ko basa
son ki kiyi masu abinda ya kamata, babu ruwan ki da abinda suka maki a baya duk
wannan ya wuce, kuma nasan baki riko, lkci lkci sai ki ce ma Mujaheed din ya kai ki
ki gaisheta a can Zaria, just that you have to be very prayerful, never get tired
of praying domin addu'a shine makamin mumini, mijin ki kuma kiyi masa biyayya yanda
ya kamata, nasan ba sai na tsaya maki wani bayani a kan aure ba you are educated
Imaan, kin san komai, sai dai kawai kamar yanda kike yi a nan gida haka nake son ki
ci gaba da kasancewa cikin kamshi da tsafta, sannan ki dinga kama jiki don wani
lkcn na sanki da shegen son jiki, ko yaya ne ki dinga aikin da baxai takura ki ba,
kin dai ga yanda nake barin gida na a ko da yaushe very neat, try to keep ur home
clean kuma ya kasance cikin kamshi ko da yaushe, duk da nasan ki da kokarin gyaran
daki da wankin bandaki, but put in more effort daughter, Allah ubangiji ya
albarkaci auren ki, ya baku xaman lafiya me dorewa, da hakurin xama da juna....
Kasa cewa komai Imaan tayi kanta a kasa hawaye na sauka idonta, Bude kofar dakin
aka yi Ammi ta kalli direction din ta ga Inna tsaye bakin kofar, Ammi ta sauka
saman gadon tace "Sannu Inna" Inna tace "Sannu, me kike kitsa mata tun daxu bata
dawo ba Aisha??" Murmushi Ammi tayi tace "Kawai nasiha nake mata Inna" inna tace
"Ai kullum cikin yi mata nake" tana fadin haka ta kalli Imaan tace "Tashi mu tafi,
nasiha kuma wanne ne ban maki ba tun da kika dawo wajena idan ba gulmar uwarki bane
ya tashi" Imaan ta kalli Ammi a sanyaye, da fillanci Ammi tace mata ta tashi ta
tafi, inna ta saki baki tana kallonta, mikewa Imaan tayi ta nufi kofa, Inna tace
"Ba ruwana da munafurci wllh" daga haka ta bi bayan Imaan suka fita, bayan sun fita
apartment din Inna na kallon Imaan tace "Me ta ce maki wai?" Imaan ta turo baki
tace "Toh Ina ruwanki?" Da yamma Inna ta dinga bin Imaan da kallo ganin yanda ta
shirya cikin riga da skirt har da shafa powder, Jin shiru bata fito ba bayan ta
shiga daki Inna ta mike ta bi bayanta a hankali ta leka cikin dakin, a duke ta
sameta jikin gado waya kare kunnenta, Inna ta buda baki a sanyaye tana kallonta, Da
sauri Imaan ta katse wayar hannunta ta ajiye tace "Daddy ne fa nake kira" Inna ta
karasa ta dau wayarta tana kallo kamar xata yi kuka tace "In dai Mujaheed kika kira
da wayata ke da Allah, ba ruwana" Imaan ta mike ta fice daga dakin tace "Ai dai ba
ke kika saka katin ba Daddy ne ya saka maki naga" Maimoon ce ta shigo parlon tana
kallon Imaan tace "Abba na kiran ki Imaan" Inna tace "Ya dawo ne?" Maimoon tace
"Ehh ya dawo yanxu" Inna tace "Toh su kuma gantalallun nan da suka tafi raka katuwa
Rukayya basu dawo bane?" Maimoon tace "Ehh kila xa su yi sati daya a can" Inna na
tafe hannu tace "Toh maza maza su dawo don rukayya Bata da tarbiyar da xata yi ma
yaran nan kada ta kai min jikoki ta barosu in shiga uku...." Imaan ta dau Hijab
dinta ta saka ta bi bayan Maimoon suka fita parlon, Abba na xaune parlor hannunsa
rike da remote Imaan ta shiga parlon ta xauna kasa ta sunkuyar da kanta tace "Ina
yini Abba?" Abba yace "Lafiya lau Mamana" Imaan tace "Ya aiki?" Yace "Alhmdllh"
Bude kofar aka yi Mujaheed ya shigo da sallama, suna hada ido Imaan ta sunkuyar da
kanta tana wasa da fingers dinta, Mujaheed ya xauna kasa a hankali yace "Barka da
dawowa Abba" Abba yace "Yauwa, ya aiki?" Yace "Alhmdllh" Abba yace "Maa sha Allah,
kana ji na Muhd?" Mujaheed ya kallesa yace "Ina ji Abba" Abba yace "Ka dau matar ka
ku wuce gida yanxu, Allah ya ba ku xaman lafiya... na yarda xaka rike Imaan yanda
ya kamata don nasan tarbiyar da nayi maka, so I need not to say much, Kai dai kayi
kokari ka rike min ita da amana, sai kuma ayi ta hakuri, daga nan yanxu ku tafi ku
yi ma Hajiya Aisha sallama da Amina sai ku wuce ba sai kun je gun inna ba" Mujaheed
ya kalli Imaan da ta rufe fuskarta ta fara hawaye, ya d'an yi murmushi cikin sanyin
murya yace "Toh nagode Abba, Allah ya kara girma" Abba yace "Ameen, Allah maku
albarka, ya baku xaman lafiya" Mujaheed ya amsa da Ameen ya mike a sanyaye yana
kallon Imaan da ta ki motsi, Murmushi Abba yyi yace "To tashi ku je Mamana" imaan
ta mike da kyar tana share hawayen dake sakko mata da hijab ta bi bayan Mujaheed da
ya nufi kofa suka fita parlon.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

97.....

Gun Aunty suka fara wucewa a bedroom dinta, Mujaheed ya xauna gefenta yace "Aunty
xa mu wuce" Aunty tayi murmushi tace "Toh maa sha Allah, Allah ya bada xaman lafiya
ya kawo kazantar daki" murmushi Mujaheed yyi ya mike Imaan dai na durkushe kasa,
Aunty ta nuna mata gefenta tace "Dawo nan daughter" Mikewa Imaan tayi tana share
hawayen idonta ta dawo kusa da Aunty ta xauna, Aunty ta kalli Mujaheed tace "Toh
sai ka bamu waje koh?" Juyawa yayi ya fita dakin yana murmushi. Nasiha me ratsa
jiki game da xamantakewar aure Aunty ta dinga yi mata tana bata shawarwarin da xa
su amfaneta, Imaan dai ta rufe fuskarta jikin Aunty hawaye na sauka idonta, Aunty
ta dago kanta daga karshe tana kallon kwayar idonta tana murmushi tace "Allah ya
albarkaci auren ki my daughter, ya kawo mana 'yan biyu da wuri" Imaan ta sauke
idonta kasa hawaye na xuba idonta, Aunty ta mike ta dagota tace "Toh mu je yana
jiran ki a waje" tana rike da hannunta suka fita dakin, Maimoon dake parlor ta mike
ta rungume Imaan a hankali tace "Soon idan Maryam ta dawo xa mu je mu gan ki kin ji
sis?" Imaan ta gyada mata kai hawaye wasu na bin wasu a idonta, Aunty na rike da
ita suka nufi kofar fita tace "An kai maki duk kayan ki can gidan, a ko da yaushe
ki xamo cikin kamshi duk da nasan ki ba baya ba, sannan ki xama mai tattala komai
naki da na mijin ki, kin ji?" Kai kawai Imaan ke gyada mata, ganin Mujaheed tsaye
jikin flower Aunty tace "Toh ga daughter na amana Muhd, though bani da fargaba
nasan xaka rike min ita yanda ya kamata, sai kuma ayi ta hakuri, Allah ya baku
xaman lafiya" ya sauke kansa kasa yace "In sha Allah Aunty, nagode" Aunty tace "Xa
ku je kuyi ma Ammi sallama koh?" Yace "Ehh" Aunty tace "Ohk to sai kun fito"
Mujaheed na gaba imaan na biye da shi har suka isa part din su, shi ya fara shiga
parlon da sallama sannan ta bi bayansa walking slowly, juyawa yyi ya kama hannunta
ganin ta makale bakin kofa ta warce da sauri, jin an bude kofa ya nufi kujera, Ammi
ta fito daga bedroom dinta tana kallonsu, ya xauna kansa a kasa yace "Ina yini
Ammi?" Tace "Lafiya qlau Mujaheed, ya aiki" yace "Aiki Alhmdllh" Imaan dai na tsaye
bata bude fuskarta ba har lkcn, murya can kasa Mujaheed yace "Dama xa mu wuce ne
yanxu Ammi" Ammi tace "Toh Allah ya kiyaye hanya" A hankali yace "Ameen mun gode"
kallon Imaan da taki bude fuskarta tana shessheka yyi ya sauke kansa sannan ya mike
yace "To mun tafi" Ammi tace "Allah ya sanya alkhairi, ya bada xaman lafiya...."
Imaan ta nufi Ammi hawaye na sauka idonta, Ammi tayi murmushi tace "Ji
shashanci...." Rungumeta Imaan tayi ta fashe da kuka, Ammi bata iya ta ce komai ba,
Mujaheed ya juya a hankali ya fita daga parlon, Ammi ta dago kanta tana kallonta,
lkci daya jikinta yyi sanyi tace "Ki xama me biyayya ga mijinki kinji Imaan, Allah
ya albarkaci auren ku, ya baku xuri'a dayyaba, nasan baxa ki bani kunya ba" Kuka
kawai Imaan take bata iya ta amsa mata ba, Ammi tayi karfin halin kin barin tayi
hawayen ita ma ta kama hannun Imaan har bakin kofa tace "Allah ya tsare" daga haka
ta sake ta Imaan ta fita daga parlon still crying, Parking space ta tadda Mujaheed
tsaye ya rungume hannayensa ya kafeta da ido, kin karasawa gun sa tayi ta tsaya, ya
bude mota sannan ya nufeta ya kamo hannunta ya bude front seat ta shiga ya rufe
motar, ya xaga ya shiga maxaunin driver yyi horn mai gadi ya bude masa gate ya fita
gidan da motar, yana hawa saman titi ya kamo hannunta a hankali cikin sanyin murya
yace "Ki daina kukan nan haka plss, tare da yayan ki fa kike" Kamar ya kara
tunxurata yin kukan hakan yasa yayi shiru, har ya tsaya gun masu siyar da fruits ya
siya ya dawo motar Imaan bata bude fuskarta ba, ya ci gaba da driving dinsa, bayan
kusan minti goma ta xame hannunta a hankali daga fuskarta tana kallon titin
gabanta, da sauri ta kallesa tana goge idonta tace "Ina kuma xa mu je yaya?" Ya
kalleta murya can kasa yace "Zaria xa mu je" kallonsa ta dinga yi ko kiftawa babu,
ya kamo hannunta cikin sanyin murya yace "Xa mu je mu gaida Umma" Imaan dai tayi
shiru bata ce komai ba, and the rest of the journey was very silent har suka isa
garin Zaria, horn yyi bakin gate, sabon Mai gadi da ya sa a gidan ya fito ya bude
gate din ya shiga da motar yayi parking, imaan dai gabanta sai faduwa yake sosai,
ya kashe motar ya sauka ita ma ta bude side dinta a hankali ta sauka tana bin gidan
da kallo, Rahama ce ta fito daga cikin parlor ganinsa ta nufesa da sauri cike da
murnan ganinsa tace "Sannu da xuwa Yaya.... Mujaheed yace "Yauwa sannu" tunda
Rahama ta kalli Imaan bata sake kallonta ba ta amshi ledan hannun yayan nata ta
wuce ciki, Rufe motar yyi yana kallon Imaan yace "Mu je" ta sunkuyar da kai bata ce
komai ba ya kama hannunta suka nufi entrance din parlon, ko ba a fada masa ba he
notice duk a tsorace Imaan take, though shi ma dai karfin hali kawai yake don bai
nuna ba har suka shiga parlon, xaunar da ita saman kujera yyi sannan shi ma ya
xauna, sosai xuciyar imaan ke bugawa, yana kallonta murya can kasa yace "Relax plss
imaan..." Tayi masa murmushin karfin hali tana karanto addu'a a xuciyarta, Ummi ta
leko daga kitchen ta fito tana murmushi tace "Welcome Yaya" yace "Thank you, Umma
fa?" Ummi tace "She's upstairs" Bata rufe baki ba sai ga Umma, Imaan ta daga kai
suna hada ido ta sunkuyar da kanta da sauri, Umma ta karasa shigowa cikin parlon ta
xauna, Imaan ta xamo kasa ba tare da ta yadda sun hada ido da ita ba murya can kasa
tace "Ina yini Umma" Umma bata kalleta ba tace "Lafiya lau, Alhmdllh" Mujaheed yyi
kasa da kai yace "Ina yini Umma" Umma tace "Lafiya lau ya gida" yace "Alhmdllh"
tace "Ya aiki fa" yace "Alhmdllh Umma" Umma tace "To madallah" kallon Ummi tayi
tace "Kin gama girkin ne?" Ummi ta nufi kitchen tace "A'a na kusa dai" Mujaheed na
kallon Umman tasa yace "Aunty Mariya ta koma ne?" Umma tace "Aa taje kasuwa xata
dawo" Mujaheed yace "Ohk..." Ummi ta dawo rike da tray mai dauke da table water
daya da goran coke daya da cup ta ajiye kusa da Mujaheed, kallonta kawai Mujaheed
yake har ta mike xata wuce Umma tace "Ruwan daya ya rage a gidan?" Ummi bata ce
komai ba ta xumburo baki ta koma kitchen sai ga ta ta dawo da wani table water guda
daya ta ajiye kan tray kusa da Mujaheed ta wuce, Umma tace "Ya su Maimoon fa?"
Mujaheed yace "Suna lafiya" Umma tace "Daxu Yusuf ya xo, bai jima da wucewa ba ma,
shekaranjiya ma ya xo" Mujaheed ya mike yace "Ohk, ban yi la'asar ba Umma, xan je
in yi sllh" sosai gaban Imaan ya fadi jin xai fita ya barta ita kadai, ta dinga
kallonsa bata dai ce komai ba, Umma tace "Toh ka tafi masallaci, ita baxa tayi
sllhn ba?" Mujaheed ya kalli Imaan yace "Kin yi sllh ai?" Girgixa kai tayi da sauri
duk da tayi a gida, Umma tace "Toh ta tafi sama" mikewa Imaan tayi ta nufi stairs
xuciyarta na bugawa, Mujaheed ya bi ta da ido sannan ya kalli Umma dake kallonsa
yace "Sai na dawo Umma" Umma tace "Toh sai ka dawo" daga haka ya fita parlon. Imaan
ta bude daya daga dakunan ta shiga, sosai gabanta ya fadi ganin jakunkunan Umma a
dakin wato dai dakin Umma ta shiga, tana shawaran xata fita daga dakin aka bude
kofa sai ga Umma ta shigo, kasa kwakkwaran motsi tayi inda take tsaye, kallo daya
Umma tayi mata ta dau wayarta dake gaban mirror ta fita dakin, Imaan ta sauke wani
ajiyar xuciya har lkcn gabanta bai bar faduwa ba, darduman da ta gani shimfide kasa
a dakin ta nufa ta xauna a kai tana ci gaba da karanto addu'o'i a ranta, ta fi
minti goma xaune dakin aka bude kofa, kanwar Umma Hajiya Mariya ta shigo dakin, da
fara'a take kallon Imaan tace "Ashe amarya ce a gidan yau, sannun ku da xuwa" Imaan
ta kirkiri murmushi tace "Ina yini Mama" Hajiya Mariya tace "Lafiya lau Imaan, ya
ku ka baro mutan gidan?" Imaan tace "Alhmdllh" Hajiya Mariya tace "Toh madallah,
Allah ubangiji ya sanya albarka a auren nan, ya bada xuri'a dayyaba" Imaan ta
sunkuyar da kai bata ce komai ba, Hajiya Mariya ta ajiye handbag din hannunta ta
fita dakin. Imaan na ta xaune dakin har shidda saura na yamma, Rahma ta bude kofar
dakin tana kallonta tace "Ance ki sakko ki ci abinci" daga haka ta juya ta wuce, a
hankali Imaan ta mike ta dauke pray mat din ta linke ta ajiye sannan ta nufi kofa
ta fita walking slowly har ta isa downstairs, Mujaheed na xaune parlon da Umma dake
dibar masa abinci a plate, Hajiya Mariya ma na xaune parlon tana answering din
call, Imaan ta karaso parlon kanta a kasa ta xauna a kasa jikin kujera, kallonta
kawai Mujaheed yake, Umma ta ajiye masa abinci kusa da shi, ta dau wani plate din
ta xuba wani ta kalli Imaan, kafin tace komai Mujaheed na kallonta yace "Ga abincin
ki" mikewa Imaan tayi ta nufi Umma ta duka ta dau abincin a hankali tace "Nagode"
sannan ta koma ta xauna duk da ba yunwa ta ke ji ba, hira kawai Mujaheed ke yi da
kanwar mum dinsa, Imaan sai juya abincin gabanta take, Hajiya Mariya tace "Toh ko
xa ki wuce dinning ki ci abincin Imaan?" Imaan tayi murmushi tana kallon direction
din dinning din, Hajiya Mariya tace "Tashi ki je can ki xauna kin ji" mikewa Imaan
tayi ta dau abincin da ke cike da nama ta wuce dinning ta xauna, tana ta xaune can
bayan ta d'an ci abincin da xata ci, Hira kawai Mujaheed yake da Hajiya Mariya amma
gaba daya hankalinsa na kan Ummar sa da tayi shiru bata cewa komai, can kuma ta
mike ta wuce sama ya bi ta da kallo, jin ana kiran Magrib ya mike yace "Xan je
masallaci in dawo mum" Hajiya Mariya tace "Toh sai ka dawo" ya kalli imaan sannan
ya nufi kofa ya fita, Hajiya Mariya ta mike ta dau plates dake parlon ta kai
kitchen ta fito tana kallon Imaan daga inda take xaune tace "Tashi kema kiyi sllh
Imaan" Imaan tace "Toh" daga haka ta mike, sbda dadewan da tayi xaune a dinning din
sai taji kafarta ya d'an rike mata, haka dai ta daure ta wuce sama, wani dakin
daban ta bude ta shiga bandaki tayi alwala, ta fito ta xauna bakin gado, ta kusa
minti biyar a xaune aka bude kofar dakin Ummi na tsaye bakin kofa tace "Ance ga
darduma can kije kiyi sllh" Mikewa Imaan tayi ta fita dakin tana tafiya a hankali
saboda kafarta, dakin Umma ta bude
ta shiga da sallama murya can kasa, taga darduman a shimfide ba kowa dakin, ta hau
saman darduman ta tada sllhn, tana ta azkar bayan ta idar da sllh Hajiya Mariya ta
shigo dakin tace "Imaan ke Mujaheed ke jira xa ku wuce" A hankali Imaan tace "Toh"
sannan ta mike ta dauke darduman ta linke ta ajiye, Hajiya Mariya tace "Sai ayi ta
hakuri, Allah ya ba ku xaman lafiya" imaan bata iya tace mata komai ganin yanda
take tafiya Hajiya Mariya tace "Me ya samu kafar kuma" kamar xata yi kuka tace
"Ciwo yake son ya min" Hajiya Mariya tace
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

"Ayya sannu, kun xo da drugs din ki ne?" Imaan ta girgixa mata kai, kama hannunta
Hajiya Mariya tayi suka fita dakin, tun da suka sakko mujaheed ke kallonsu haka ma
Umma, Hajiya Mariya tace "Wai ciwon kafa take Mujaheed, sai kun fita xaka siya mata
magani ko akwai a gida?" Yana kallon Imaan yace "Xa mu siya idan mun fita" Daga
haka ya mike ya nufeta yace "Yaushe ya fara maki ciwon?" imaan tace "Daxu" yace
"Allah ya sauwake" Komawa gun Umma yayi ya durkusa yace "Xa mu koma kaduna umma, in
sha Allah xan xo jibi" Umma tace "Toh Allah ubangiji ya kiyaye hanya ya tsare,
Allah ya maka albarka" yace "Ameen Umma ngd" har bakin mota suka rakasu gaba daya,
Hajiya Mariya na rike da hannun Imaan dake dingishi ta bude mata front seat ta
shiga Imaan ta ce ma Umma sai da safe, Umma tace "Allah ya tashe mu lafiya" Hajiya
Mariya ta rufe motar, Umma na kallon Mujaheed tace "Ko a kawo maku aboniki ne?"
Yace "Toh Umma" juyawa tayi ta koma cikin gida sai ga ta ta dawo da kwalban man
xafin gaba daya ta mika masa ya amsa yace "Mun gode sai da safe" daga haka ya shiga
front seat Mai gadi ya bude masa gate ya ja motar sisters dinsa na masa Allah ya
kiyaye hanya, sai da ya kusa barin layin yyi parking yana kallon Imaan yace "Sosai
kafar ke maki ciwo?" Ta girgixa masa kai tace "Yana dai yi min ciwo" ya dau man
xafin ya bude yace "Bari in shafa maki kafin mu kai kaduna in siya maki wanda kike
shafawa" Bata ce komai ba ta daga hijab din jikinta da skirt tana yatsine fuska ta
juya tana facing dinsa ta daga masa kafar, ya debi man xafin yana shafa mata a legs
dinta tana masa kukan shagwaba tana rike hannunsa wai xafi, murmushi kawai yake
yana kallonta shi dai bai ce mata komai ba har ya gama shafa mata ta sauke kafarta
kasa yace "Sorry wife" ta make kafada tace "Ko dai lil sis" kallonta yyi yace
"Koh?" Tace "Ehh" ya gyada mata kai yana murmushi yace "Gaskiya ne, come closer in
shafa maki sauran na hannuna a jikin ki" Bai jira cewarta ba ya jawota ya saka
hannunsa a hijab dinta ya daga rigar jikinta ya shiga shafa mata both hands dinsa a
warm tummy dinta gently in a circular motion, ta xaro ido tana son komawa baya ya
ki barin tayi hakan yana kallon fuskarta to see her reaction, da farko kasa cewa
komai tayi, can kuma ta rike duk hannunsa kamar xata yi kuka tace "Wllh bana son
irin haka yaya, don Allah stop it" Bai saurareta ba har sai da ya kyaleta don kansa
yana murmushi, ta turo baki xuciyarta na bugawa har lkcn tana jin kamar hannunsa na
jikinta, driving din ya ci gaba da yi yana satan kallonta yana murmushi. Har suka
shiga garin kaduna Imaan bacci take tun bayan da suka baro Zaria, yayi parking a
wani babban pharmacy yana kallonta ganin yanda take bacci hankali kwance don ya
gyara mata kujeran motar, bai tasheta ba ya sauka motar ya rufe sannan ya shiga
pharmacy din, duk drugs dinta ya siya mata da na shafawa sannan ya biya kudin ya
fito, ya sameta tana bacci har lkcn, rufe motar da yyi bayan ya shiga ne ya tada
ta, ta dinga bin inda suke da kallo, yana murmushi yace "Kin gama baccin ki na
daren yau kuma yarinya, sae kuma gobe...." Ta gyara xamanta tace "Where are we
now?" Yace "Kaduna" daga haka ya tada motar suka bar haraban pharmacy din... Gun
masu gashin kaji yayi parking yana kallonta yace "Do you care for some?" Tace "Meye
shi?" Yar dariya yyi yace "Kazan kika manta yau?" ta make kafada tace "Ni dai a
koshe nake" yace "A'a kin taba ganin inda amarya ta kwana bata ci kaza ba?" imaan
ta wani hade rai tace "Ni ba Amarya bace" yace "Xa ki san ke amarya ce yau" daga
haka ya sauka motar ta bi sa da kallo, guda daya ya siya sannan ya hada da chill
fresh milk da suke siyarwa a wajen, yana dawowa cikin mota ya mika mata, ta ki amsa
ta wani daure fuska, ya ajiye yana murmushi bai ce mata komai ba ya tada motar, har
suka isa gida fuskarta a daure yake, Mai gadi ya bude masa gate bayan yyi horn ya
shiga gidan yyi parking, ya juya yana kallonta, hawaye ya gani makale idonta, sauka
yyi motar ya xaga ta side dinta ya bude motar ya kama hannunta ta fito daga motar
hawayen dake idonta ya sauko kasa, jawota yyi jikinsa a hankali yace "Yayah ne fa
Imaan"

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

98......

Imaan dai bata ce masa komai ba ta sauke kanta kasa a hankali, yana murmushi ya ja
dogon hancinta ta turo baki ta dauke kai, ledan dake cikin motar ya dauko ya kulle
motar sannan ya kama hannunta suka nufi entrance din gidan, da makulli ya bude
kofar ya shiga tana biye da shi a baya, banda kamshi na turaren wuta me dadi bbu
abinda ke tashi a parlon dake dauke da new furnitures kamar ba a ta6a rayuwa ciki
ba, komai na parlon sabo ne, yana rike da hannunta suka isa tsakar parlon ya ajiye
ledan hannunsa ganin taki yarda ta daga kanta, ya kai bakinsa kunnenta yace "Baxa
ki kalli gidan ki ba kanwata" Ita dai bata ce masa komai ba, yana facing dinta ya
dago kanta a hankali yace "Imaan" shiru tayi tana kallonsa, ya sa finger dinsa ya
share hawayen idonta yana murmushi ya kama hannunta suka wuce upstairs, bedroom
dinta ya bude mata yana kallonta yace "Ur room" kallon dakin ta dinga tana tsaye
bakin kofa, ya shigar da ita ciki ta lumshe ido ta bude jin daddadan kamshin dake
tashi dakin, I don't want to talk about how expensive foreign furnitures da Daddy
ya xuba ma tillon yar tasa, kudi ne ba na wasa ba ya kashe a dakin Imaan, ko yar
governor sai haka, lol, ganin ta kasa cewa komai Mujaheed ya juya ya fita dakin,
Imaan ta dinga bin babban bedroom din da kallo wasu sabbin hawaye suka kawo idonta
amma na farin cikin abinda mahaifinta yayi mata, a sanyaye ta nufi kofar da ta gani
cikin dakin ta bude a hankali taga bandaki ne babba, ta sauke kanta kasa ta juya ta
fito daki, hijab din jikinta ta cire ta linke ta ajiye ta bude press taga gogaggun
kayanta me yawa da sleeping dresses har inner wears, rufe gun kayan tayi ta koma
bandaki ta dauro alwala ta fito ta dau sabon darduma dake linke kan stool din
mirror, babu kalan turaren da babu gaban mirror din, sai lotions dinta da take
shafawa da hair cream, ta shimfida darduman hannunta sannan ta tada sllhn Isha, ta
jima xaune kan darduma bayan ta idar da sllh tana addu'a daga karshe ta mike har
xata cire kayan jikinta sai kuma ta kalli kofar dakin, turo baki tayi ta tafi ta sa
makulli ta dawo ta cire kayan ta linke ta ajiye ta shiga bathroom, babu abinda babu
na bukata a cikin bathroom din tun daga sponge, soap da take amfani da, shower gel,
toothpaste, toothbrush, hatta washing machine sai da Daddy ya siya mata aka sa a
bathroom, ta hada ruwan xafi a bucket da ta gani tayi wanka, ta wanke bakinta da
Listerine sannan ta dau brand new towel da ta gani a bandakin ta daura alwala ta
dauro ta fito. Bata wani dau lkci xaune gaban mirror tana shafe shafen turare ba ta
mike ta fiddo kayan baccinta a press ta saka, ta dau hijab tasa ta hau saman gado
ta shige cikin duvet ta rufe idonta, Har bacci ya fara daukanta taji ana knocking,
ta mike xaune ta wani hade rai tace "Waye wannan?" Mujaheed yace "Waye koh? to bude
ki amshi drugs din ki..." Tace "I am not feeling pain anywhere" murmushi yayi yace
"I know... but you need to take them" Kamar xata yi kuka tace "Wllh Yaya bana jin
ciwo, kuma ni bacci nake ji, gobe xan sha" ya hade rai yace "Imaan open this door
now" ta marairaice ttace "Yaya wllh am feeling okay" yace "Idan kika bari na bude
kofar da kai na xan baki mamaki" tace "Wayyoo Yaya ba sai in sha gobe ba nace" yace
"Ohk jira in samo makulli in dawo yanxu, Allah da gaske sai nayi shock din ki" xaro
ido tayi tana kallon kofar, jin shiru ta mike gabanta na faduwa, murya can kasa
tace "Yaya?" Taji shiru bai amsa ba, kara kiransa tayi ta ji bai amsa ba ta nufi
kofar a hankali ta murda makullin dake jiki ta bude kofar, cafkota yyi ta fasa ihu
a tsorace tace "Wayyo Yaya wllh ka ban tsoro" yace "Da me yasa kika rufe kofar?" Ta
marairaice tace "Saboda Ina jin bacci" yana rike da ita suka xauna gefen gado yana
kallonta yace "But Ain't you hungry?" Kai ta gyada masa gabanta na faduwa tana
kallonsa, ya d'an yi murmushi yace "Toh amma sai ki ci kazan ki ko kadan ne, bari
in dauko" da har xata ce A'a sai kuma ta kalli kofa, da sauri tace "Toh..."
kallonta ya dinga yi kafin ya mike yana wani murmushi ya isa kofar ya cire makullin
jiki ya fita dakin, ta xaro ido tana bin sa da kallo kamar xata fashe da kuka, ba a
dau lkci ba ya dawo da plate dauke kaza sai fresh milk with cup, ya ajiye su saman
lallausan carpet dake dakin ya xauna yana kallonta yace "Ko in xo in dauko ki?" A
hankali tace "Yaya wllh na koshi da gaske" yace "Ehh just tsoka daya xa ki ci sai
ki sha madaran" shiru tayi tana kallonsa kamar xata yi kuka, duk da dariyar da take
basa ya hade rai yace "Baxa ki sakko ba" xamowa kasa tayi a hankali ta xauna tana
facing dinsa ya dau tsoka daya ya kai bakinta ta sa hannu xata amsa, ya mata wani
kallo ya ki bata, haka nan ta bude bakin ya sa mata naman ta kauda kai tana taunawa
da kyar kamar warce ke taunar magani, shi dai kallonta kawai yake, tana girgixa
tace "Allah Yaya baya rai na yau, kamar fa xan yi amai nake ji" Yana murmushi yace
"Toh cinye na bakin ki sai ki sha madaran shkkn" da kyar ta hadiye na bakinta ya
bata fresh milk din ta sha shi ma kadan tana yatsine fuska, ya ajiye su gefe ya
mike ya dau darduma ya shimfida yana kallonta yace "je ki wanke bakin ki Let pray"
mikewa tayi ta hau saman gado ta kwanta xata rufa da duvet tace "Ni dai nayi sllh
tun daxu, good night" Yace "Ai ban ce baki yi ba, come down my frnd kiyi abinda
nace maki" ta xaro ido tace "Yaya har shafa'i wllh nayi, kawai wutr ne dai banyi ba
tunda xan yi sllh cikin dare, wllh bacci nake ji yaya" Ya nufi gadon ta mike da
sauri tana komawa baya, yce "Sakko ki rufa ma kanki asiri kiyi wutr dinki don ba
yin sllhn nan na cikin dare xa ki yi ba yau" ta hade rai tace"Saboda me?" Bai bata
amsa ba ganin xai cafkota da sauri ta sakko kasa daga kan gadon, ya dau hijab dinta
ya mika mata ta amsa tana kallonsa hawaye cike idonta ta tafi bandaki ta wanke
bakinta ta fito. Tun da suka idar da sllh ya juya yake kallonta ta ki yarda ta
kallesa, yyi murmushi ya matsa dab da ita, a hankali ya kai hannunsa saman goshinta
praying for the best in their married life, sun jima a haka daga bisani ya mike
yace "Saura drugs din ki" ta bi sa da kallo har ya fita dakin ta tashi ta koma kan
gado ta kwanta tayi lamo, yana dawowa rike da ledan drugs din da glass cup dauke da
ruwa ya kashe wutan dakin, ta mike xaune a hankali tace "Yaya me yasa ka kashe??"
Kunna kananun wuta mara haske sosai yyi ya iso saman gadon ya xauna gefe ya ballar
mata gaba daya Magungunan ya mika mata da glass cup din ruwan, ta amsa ta kai baki
ta shanye, ya karbi cup din ya ajiye kasa, ya bude tube din da take shafawa a kafa
yace "Saura wannan" make kafada tayi tace "Ni dai wanda ka shafa min a mota ma yyi,
ai kafar ya daina min ciwo" ya daure fuska yace "Take off that hijab in shafa maki
in tafi in kwanta i am feeling sleepy" ta kallesa tace "Tafiya xaka yi ka kwanta?"
Yace "Ehh, or did you have anything for me" girgixa masa kai tayi ta cire Hijab
din, da sauri kuma ta rufe jikinta tace "Ni dai ka kashe wutan kawai idan xaka fita
sai ka kunna min mara hasken" yyi murmushi yace "Yau kuma ni ake boye ma kafar?"
Bai jira cewarta ba ya kashe switch din dake jikin bango kusa da gado ya dawo kusa
da ita, ta daga rigar jikinta xuwa gwiwa, ya bude tube din ya fara shafa mata
lotion din a legs dinta xuwa toes tana kwance, ya fi minti goma yana shafa mata ya
kai fuskarsa nata jin tayi shiru, murya can kasa yace "Bayan fa?" Ta bude ido tace
"Har da shi?" Yace "Ehh" mikewa xaune tayi ta sauke rigan kasa tayi kwanta saman
pillow, ya debi lotion din ya fara shafa mata tun daga shoulders dinta har xuwa
waist, ta wani turo baki kamar yana ganinta tace "Ni dai Yaya da karfi xaka shafa
min bana son kana min a hankali" ya kai bakinsa kunnenta yace "Why?" Ta dauke kai
tace "A'a ni bana so dama ai bance yana min ciwo ba..." Yana murmushi murya can
kasa yace "Ohk bari in daina yi a hankalin" ta xaro ido tace "Toh ai kuma ni bance
ka karya min bayana ba, ka yi a hankalin" Bata kuma cewa komai ba idonta a rufe,
Lkci daya ta juyo jin gaba daya shafa magani a baya na neman canxa salo tana
kokarin mayar da rigarta sama tace "Yaya kawai ka kunna wutan I am now feeling
better ya isa haka ka tafi ka kwanta" kamo hannunta yayi ya kwanta gefenta ya rufe
bakinta kamar me rada yace "ohk bari in shafa maki sauran a tummy din ki kamar
daxu..." Bai bata chance din cewa komai ba ya fara shafa mata hannunsa a ciki,
turasa ta dinga yi jikinta na 6ari tana cewa "Ni wllh bana so yaya ka bari" lkci
daya ta ji Yaya fa kamar ba shi ba, ta fara kokarin mikewa tana kokuwa da shi, ta
dade bata yi rikicewan da tayi a lkcn ba ganin ba sarki sai Allah ta galla masa
cizo da karfi amma ko gezau, hakan yasa ta dinga kiransa iya voice dinta, shi kuma
ya rufe bakin, tsoro yasa numfashinta ya dinga daga nan kuma bata kuma sanin komai
ba. Ray din rana da ya sauka kan fuskarta ya sa ta bude ido a hankali ta sauke kan
Ac dake dakin, kalle kallen dakin ta shiga yi as if trying to recall something, dai
dai nan aka bude kofar dakin suka yi ido hudu da Mujaheed lkci daya ya sauke idonsa
kasa ya kullo kofar, ta mike xaune da kyar, ta dafe kanta tace "Yaya Ina jin
xaxxabi, my head is aching" Ya iso kusa da ita ya xauna gefenta still ya ki
kallonta yace "Kiyi sllh sai kiyi breakfast in baki magani" ta xaro ido ta kalli
agogo taga karfe takwas ya kusa a hankali tace "Sllh kuma Yaya, me yasa baka
tasheni da asuba ba..." Komawa tayi ta kwanta saman pillow tace "and my body is
weak, xaxxabi nake ji" Ya mike ya shiga bathroom ta bi sa da kallo kanta na sara
mata, kara kallon agogo tayi ta mike xaune tana son tashi amma taji kamar idan ta
tashi xata fadi ga ciwo da bayanta ke mata, fitowa yayi bathroom din yace "Ga warm
water a kettle kije kiyi alwala" Yana fadin haka ya iso gabanta ya kama hannunta
trying not to look at her in the eyes, sosai yaji jikinta yyi dumi, Imaan dai sai
kallonsa take, Lkci daya ta xame hannunta ta fasa ihu tana komawa baya tana
kallonsa, rikota yyi cikin sanyin murya yace "Stay still Imaan" girgixa masa kai ta
dinga yi jikinta
na bari tace "Wayyo Allah na, don Allah ka sakeni yaya...." ya saketa yace "Toh
alwala xa ki yi ai" ta rufe fuskarta da pillow tana kuka sosai tana kiran inna,
juyawa yyi ya fita dakin ya kulle mata kofar. Ba karamin wahala imaan ta ba
Mujaheed ba ranan, though yasan dole xata daga masa hankali amma bai yi tunanin xai
kai haka ba, sai a lkcn yasan raki yafi yawa a ciwon da take yi a gida, bai ta6a
ganin mai raki irin Imaan ba, duk ta sa shi ma ya dinga jin kamar xaxxabi sai
rufesa, duk abinda yasan xai mata ta samu relieve na ciwon baya da take ta ce masa
yyi.. amma Imaan taki bari ya huta da rakinta, damuwarsa abincin da ta ki ci tun
safe, gashi duk ta ishesa da kuka ita ya maida ta gida, a haka dai ya yini yana
fama kamar Nanny har washegari, nan ma kuma ta daura daga inda ta tsaya jiya,
though da Xaxxabi sosai ta tashi ranan, sure yasan she is in pain but ko kadan bata
da juriya, karfe sha biyu ya fita pharmacy ya siyo ruwan drip da xai kara mata,
bayan ya saka mata ruwan shine ta samu tayi ta bacci har kusan yamma. Yana xaune
parlor ya jinginar da kansa da kujera har bacci ya soma daukansa a haka aka danna
bell, bude ido yyi ya mike ya isa kofar ya bude, Maimoon ce tsaye da basket da ke
dauke da abinci tana murmushi tace "Ina yini Yaya?" Ya shafa kansa yace "Lafiya
lau, how are you?" Tace "I am fine, Inna ce tace in kawo ma Imaan abinci amma fa
wai ban da kai, tace bata baka ba ko ka ci" tana magana tana dariya, ya d'an yi
murmushi yace "Toh shiga ki ajiye mata" Yana fadin haka ya bata hanya ta shiga
parlor ta ajiye abincin tace "Tana Ina?" Yace "She's sleeping upstairs" tace "Inna
ta ban sako in gaya mata fa" yace "Bacci take yi..." Maimoon na murmushi tace "Toh
shkkn sai da safe" yace "Jira in dauko maki transport" tace "A'a driver ne ya kawo
ni" yace "Toh ki gaida Aunty and everyone" tace "In sha Allah" daga haka ta fita
parlon ya kulle kofa, Yana son xuwa sama amma yana tsoron tashin hankalin Imaan, ya
fi minti sha biyar xaune daga karshe ya mike ya wuce sama, a hankali ya bude kofar
dakin, ya ganta xaune ta jingina da gado hawaye na sakkowa idonta... Ya sauke
idonsa ya kulle kofar ya karasa kusa da ita, ta hade kanta da gwiwa tana shessheka,
har ransa ya dinga jin tausayinta, cikin sanyin murya yace "I am sorry Imaan, na fa
ce ki yi hakuru..." Ta fashe da kuka tace "Ni bana so, kuma wllh sai na fada ka da
Inna" murmushi yyi ya dago kanta ya jawota jikinsa tana kuka sosai, yace "Toh na ji
ki gaya ma Inna in har xa ki hakura" ita dai bata ce komai tana shessheka.
*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

*Albishirinku 'yan uwa*

Shin ko kun San zaku iya magance mafi yawan cututtukan da suka addabi al'umma yanzu
cikin sauki?
Sinadarin _Stemcell total care_ yayi fice wajen magance matsalolin diabetes, BP,
asthma, sickler, cancer, stroke, rashin haihuwa, fibroid, infection da duk wata
matsala da ta danganci lafiyar Al'umma.
Ba wannan kadai ba, akwai coffee na double root Wanda ke inganta duk wani abu da ya
shafi rayuwar aure ga maza da Mata, inganta qwayoyin haihuwa da dai sauransu.
Akwai sinadarin rage tumbi da dai sauransu.

*Domin neman qarin bayani ku tuntubi wannan lambar 07068136856*


Sai an gwada akan san na kwarai.

99.....

Mujaheed ya sauka kasa ya debar mata abincin da Maimoon ta kawo yana kallonta yace
"Come and eat plss" ta make kafada ba tare da ta kallesa ba tace "Ni baxan ci ba"
daukan abincin yyi ya dawo gefen gadon ya xauna yana kallonta cikin kwantar da
murya yace "Haba wife, ki ci ko kadan ne don Allah" matsawa tayi daga kusa da shi,
ya ajiye abincin yace "Toh me xa ki ci?" Ta goge idonta a hankali tace "Ni gida xan
tafi gun Ammina" ya d'an yi murmushi yace "Ita ma gaya mata xa kiyi?" Kallonsa tayi
da sauri, lkci daya suka dauke kai a tare, Imaan ta rufe fuskarta da pillow hawaye
ya kawo idonta, a hankali ya dawo kusa da ita ya dagota ya rungumeta ya lumshe ido
murya can kasa yace "Toh ki ci ko kadan ne gobe xan kai ki gida in sha Allah" Bai
jira cewarta ba ya dau abincin da spoon ya debi tuwon ya kai mata baki, ta girgixa
kai cikin sanyin murya tace "Ni bana son tuwo ba" cikin lallami yace "Toh me xa ki
ci?" Tace "Shinkafa..." ya ajiye abincin ya mike ya dau hijab dinta ya mika mata
yace "To sa mu je in siya maki" mikewa tayi a hankali ta amshi hijab din tasa ya
kama hannunta tana biye da shi walking very slowly, steps din nata yake kallo har
suka fito dakin yace "Ko in dauke ki, you can't walk?" Bai jira cewarta ba ya
dauketa kamr little baby, ta rikesa da sauri tace "Meye haka Yaya? Xan fadi plss"
sosai gabanta ya fadi memory din shekaranjiya na dawo mata jin ynda ya riketa, ta
ki yarda su hada ido, parking space ya ajiyeta yana murmushi yace "My weightless
wife..." Ta turo baki tace "Ni ka daina ce min wife dinka" ya wara idonsa yace "Toh
me ya rage? Ko sai mun sake abun shekaranjiya?" Tsabar yanda xuciyarta ya buga sai
da ta jingina da mota da sauri tana kallonsa, ya sauke kansa yana murmushi, lkci
daya ta fashe da kuka sosai, ya xaro ido yace "A'a toh yi hakuri wasa nake maki..."
Ta juya ta kife kanta da mota tana shessheka, ya juyo da ita ya bude front seat ya
shigar da ita ta xauna ya rufe motar sannan ya xaga maxaunin driver ya shiga, ya
dago kanta yace "It's a promise baxan sake ba Imaan, sai idan ke kika sameni har
daki..." Yana murmushi ya karasa fadin haka, Ita dai bata ce masa komai ba a ranta
kuwa cewa tayi ashe har abada kuwa in dai ita xata je dakinsa ta samesa, yace "Kuma
ni ma sai na maki shagwaba yanda nake so kafin na yadda" Tabe baki tayi ya kalleta
ta gefen ido don sarai yasan tunanin da take, ya wani murmushi yana gyada kai,
murya can kasa tace "Is that a promise?" Ya d'an bude ido yace "Suree" Bata ce
komai ba amma har ranta taji dadin promise din nan. tafiya yake amma gaba daya
tunaninsa na waje daban, the memory was just still fresh, that night be an
unforgettable one to him, bai san lkcn da yyi wani murmushi ba, ya kamo hannunta a
hankali ba tare da ya kalleta ba yace "Imaan" ita dai idonta na kan glass din mota
tana kallon waje ko kiftawa babu, nan ko tunani take me yasa ta kasa recalling gaba
daya abubuwan da suka faru shekaranjiya, tasan dai ta tashi cikin daren but ba
komai ta tuna ba, all she could remember was the pain, she was seriously in pain
all over daga baya kuma bata san ya aka yi ba, bata san lkcn da ta koma bacci ba,
jin bata amsa ba Mujaheed ya sake kiranta a hankali, da sauri ta juyo, suna hada
ido a tare suke sauke kai ya mayar da idonsa kan titi ita ma ta ci gaba da kallon
inda take kallo gabanta na faduwa, cikin sanyin murya yace "Allah ya maki
albarka..., I am proud of you" ita dai bata ce masa komai ba, har suka kawo wajen
cin abinci yayi parking yace "I will be back soon" Yana fita ta bi sa da kallo
gabanta na faduwa don har xuciyarta take tsoronsa ynxu, tsoro me tsanani, har dai
ya shiga cikin eatry din, ta jinginar da kai da kujera ita dai fa memory din da ta
kasa cirewa ranta was just the moment da ta dinga jin unbearable ail and after that
bata kuma sanin komai ba, Bayan kusan minti goma ya fito rike da take away daya a
hannunsa, ta sauke idonta daga kallonsa har ya shigo motar ya tada suka bar haraban
eatry din. Suna isa gida a parlon ya sa ta xauna ya bata abinci ta dau spoon tana
juyawa a hankali, shi kuma ya xauna saman kujera yana kallonta, Kamar ana tilastata
ta dinga cin abincin, daga karshe ta rufe ta tashi xata wuce sama yace "Imaan" Bata
juyo ba amma ta tsaya, yace "Baki ci da yawa ba" tace "Na koshi" daga haka ta wuce
sama ya bi ta da ido, murmushi yyi shi kadai ya mike ya dauke abincin ya kai
kitchen, Tun da imaan ta fito wanka bayan isha ta gansa a dakinta ta xama restless,
yace "Are you sure baki kara ruwan sanyi a ruwan ba?" Ta hade rai bata basa amsa
ba, dama da hijab dinta har kasa ta fito sbda sanyi da take ji ta tafi can karshen
gadon ta xauna ta takure waje daya, yace "Baxa ki sa kayan ba" shiru tayi masa ta
wani hade rai, ya mike yace "Toh shkkn na tafi" daga haka ya fita dakin yana sha
kansa, ta tashi da sauri ta sa kayan baccinta ta feshe jikinta da turare ta sa wani
hijab din ta hau saman gado ta kwanta ta rufe har kanta gabanta na faduwa, kafin
karfe goma har tayi bacci, a lkcn ya shigo dakin dakin rike da Magungunanta, ya
xauna gefen gadon ya cire duvet din a hankali ya kai hannu goshinta, a tsorace ta
farka ta mike xaune da sauri tana ja baya ta fashe da kuka tace "Don Allah yayi
hakuri yaya" yace "Magani xa ki sha Imaan" hannunta na rawa ta amshi maganin da
yake mike mata da ruwa ta sha, ya mike yace "To sai da safe" daga haka ya fita
dakin sai da taji ya shiga dakinsa ya rufe sannan taji hankalinta ya kwanta ta koma
a hankali ta kwanta tana sauke ajiyar xuciya. Da asuba bayan Mujaheed ya dawo
masallaci ya shigo tashinta ya ganta xaune saman darduma har ta idar da sllh ga
qur'ani gabanta tana karantawa cikin sanyin muryarta, yyi murmushi ya xauna gefen
gado yana kallonta ko kiftawan kirki bbu, sai da tayi rabin suran da take karantawa
sannan ta rufe qur'an din, amma bata yadda ta kallesa ba, murya can kasa yace "I
once told you kids dina baxa su samu flaws in recitation of Al-quran ba kin tuna?"
Sai a snn ta kallesa tayi shiru, yyi murmushi yana shafa kansa yace "Kin gane me
nake nufi yanxu?" Ita dai kallonsa kawai take and she looks so confuse, ya sakko
kusa kusa da ita yace "Fatan kin tashi lafiya sweet wife?" Ta sauke idonta bata ce
komai ba ta hade rai, mikewa yyi ya fita dakin ta bi sa da kallo. Can ta tashi ta
dauke Quran din da darduman ta ajiye su inda ya kamata sannan ta shiga bathroom ta
hada ruwan wanka yanda taga yana yi mata tayi, ta wanke baki ta fito, doguwar riga
kawai ta saka bayan ta shafa mai ta fesa turare ta kwanta. Misalin karfe takwas da
wani abu danna bell da aka yi downstairs ya farkar da ita, ta mike xaune jin
dannawa ake ta yi ba kakkautawa ta sauko daga saman gadon ta fita dakin dai dai
lkcn da shi ma ya fito parlonsa, ta sunkuyar da kai yace "Go and sleep I will
check" Bata ce masa komai ba ya fita ta bi bayansa, tsaye ta gansa yana lekan
balcony din through window, ganin ya ki matsawa daga jikin window din ta karasa
downstairs har ta iso bayansa dai dai lkcn da ya sake curtain din xai juyo suka
kusa cin karo jawota yyi jikinta, tayi lamo, murya can kasa tace "Waye?" Yace "I
think it's not necessary...." Sosai gabanta ya fadi jin abinda yace ta daga kai
tana kallonsa, ya ja ta xa su bar parlon. Ta fixge hannunta tace "Who is it plss?"
Shiru yayi yana kallonta kafin yace "Kishiyar ki" ta buda ido tana kallonsa gabanta
na faduwa, lkci daya ta juya ta wuce sama ya bi ta da kallo yana murmushi sannan ya
kara kallon kofar da aka fara bubbuga da karfi maimakon bell da ake dannawa, ya
koma gun kofar ya tsaya yace "Who is that?" Da karfi tace "Ubanka ne, nace ubanka
ne..." dariya yyi yace "Toh kya kara tsufa a inda kike tsaye kuwa, kawai da sassafe
mutane basu tashi ba ki taho masu gida, ke haka ake yi a garin ku?"

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

*Albishirinku 'yan uwa*

Shin ko kun San zaku iya magance mafi yawan cututtukan da suka addabi al'umma yanzu
cikin sauki?
Sinadarin _Stemcell total care_ yayi fice wajen magance matsalolin diabetes, BP,
asthma, sickler, cancer, stroke, rashin haihuwa, fibroid, infection da duk wata
matsala da ta danganci lafiyar Al'umma.
Ba wannan kadai ba, akwai coffee na double root Wanda ke inganta duk wani abu da ya
shafi rayuwar aure ga maza da Mata, inganta qwayoyin haihuwa da dai sauransu.
Akwai sinadarin rage tumbi da dai sauransu.

*Domin neman qarin bayani ku tuntubi wannan lambar 07068136856*


Sai an gwada akan san na kwarai.

100...

A fusace inna tace "Ni dai duk wanda ya walakanta ni kansa ya walakanta duniya da
lahira, don ba banxa nake ba, ta yaya xa a barni a gantale bakin shegen kofa daga
xuwa abun arxiki?" Mujaheed na murmushi ya bude kofar yace "Toh mu munce ki xo mana
da sassafe ne balle a bar ki a gantale" Bangajesa ta kusa yi ta shige parlon fuska
daure, ya bi ta da kallo yana dariya, ta cire Hijab din jikinta ta linke ta ajiye
tana kare ma parlon kallo tace "Idan ba dai ya xamar min dole in duba jikata ba
uwar me xai kawo ni gantalallen gidanka Mujaheed, me kake bani? wllh albarkacin
Imaan na xo gidan nan yau, don ubanta ya min abinda har in mutu baxan manta ba ya
rike ni da kyau, ka tafi ka kira min ita in ga jikata in kama hanya inyi
wucewata..." Ya dawo kusa da ita ya xauna yana murmushi yace "Oh ni ba jikan ki
bane?" Ta daga hannu sama da sauri tace "A'a ba ruwana da wannan xancen, uban me
dama na hada da kai?" Ya mike yace "Toh bari in kira maki ita, kina ganinta ki
tashi ki bar min gidana dama kar in sa mai gadi ya fitar da ke" Bai jira cewarta ba
ya wuce sama, xaune ya tadda Imaan gefen gado tana kallon door din dakin, ita kanta
bata san irin kwanciyar da hankalinta yyi ba jin muryar Inna, don gaba daya
tunaninta Safeenah ce kamar yanda yace mata, ya karasa dakin ya xauna gefenta ta
dauke kai, murmushi yayi ya juyo da fuskarta a hankali yace "Ki sakko ku gaisa da
kishiyar ki" Yana fadin haka ya mike ya kama hannunta suna isa kofar dakin yace "Ko
in dauke ki?" Ta hade rai tace "Saboda me?" Daukarta yyi kamar jiya, ta xaro ido ta
rikesa tace "Yaya bana so da gaske ka ajiye ni plss" bai saurareta ba har suka
sauka downstairs, Inna na ganinsu ta yo waje da ido ta mike da sauru tace "Nashiga
uku, me ya sameta Mujaheed??" Imaan na kokarin sauka tace "Don Allah Yaya ka ajiye
ni plss" ajiye ta yyi bayan sun shigo parlon yana kallon eye balls dinta, turo baki
tayi tana sauke rigarta da ya tattare, Inna ta koma ta xauna tayi tagumi, Imaan ta
karasa gunta tana murmushi ta xauna kusa da ita ta shige jikinta tace "Sannu da
xuwa Inna" Inna ta turata daga jikinta tace "A gaskiya Imaan ba ki yi halina ba ko
kadan, kwata kwata baki da jan aji, haka kawai mutumi bai maki lefe ba ki dinga
shigewa jikinsa salon ya cuce ki ya kai ki ya baro ki, meye amfanin daukan ki da
yayi ynxu?" Sosai ta ba Mujaheed da ya xauna yana kallonta dariya, Imaan dai bata
ce komai ba, Inna na nuna ta da yatsa tace "Wato duk abubuwan da nake gaya maki
baki ji ba kenan koh?" Imaan ta turo baki tace "Ni nace maki ban ji ba?" Inna ta
matsa daga kusa da ita tace "Ba ruwana wllh, idan ba ni din ba dama waye xai gaya
maki gaskiyar da xai maki amfani, Bukar da Ahmadu da matansu duk sun lalace babu
tsoron Allah, kuma a gaskiya ni dai ban karya ba na fito gida yunwa nake ji" Mikewa
Imaan tayi ta nufi kitchen tana tafiya a hankali, Inna tayi mitsi mitsi da ido tana
bin ta da kallo tace "Me ya sami kafar kuma?" Mujaheed ya mike ya isa kusa da ita
ya duka dai dai gabanta yace "Ke dai kin fiye sa ido, Ina ruwan ki da abinda ya
samu kafarta" sake baki tayi tana bin Imaan da kallo har ta shige kitchen, ya mike
yana murmushi ya bi bayanta xuwa kitchen din, tsaye ya ganta tana taran ruwa a
bowl, ya isa kusa da ita yace "Me xa ki yi?" Bata juyo ba tace "Tace bata yi
breakfast ba" Ya jawota jikinsa murya can kasa yace "Xa ki iya?" Tana shakan
kamshin sa tayi shiru, sai kuma ta gyada masa kai tace "Uhm" daga haka ta janye
jikinta ta debo Irish ta dau peeler ta fara peeling dinsu, ya duka yana kallonta,
shi ya taimaka mata ta gama soye soyen just to keep and eye on her to make sure is
fine, tana daura su kan tray ya rungumeta ta baya, sosai gabanta ya fadi, tana
kokarin barin wajen tace "Bana so Yaya" murya can kasa yace "Baki son me?" matsawa
tayi daga kusa da shi ta hade rai, ya dinga kallonta yana murmushi, shi ya dau
breakfast din ya fita parlor, xaune ya tadda Inna kana kujera tana ta xuba
gyangyadi, yyi dariya ya isa kusa da ita ya ajiye tray din hannunsa yace "Mutum
baxai tsaya gidan yyi bacci ba kawai ya xo gidan mutane da sassafe yayi ta
gyangyadi...." da sauri ta bude ido bai jira cewarta ba ya koma kitchen, tare da
Imaan da taki fitowa suka dawo parlon, gaba daya taki yarda ta kalli Inna, Inna dai
sai kallonsu take ta gefen ido tana bude Madara har suka wuce sama, sannan ta gyada
kai tace "Ikon Allah, da kyar idan 'yar nan ta Bukar ba jarababbiya bace" gefen
gado Mujaheed ya sa imaan ta xauna ya duka gabanta yana kallonta yace "Toh ke me xa
ki ci wife?" Ta dauke kai tace "Sai anjima" ya mike yace "Ohk Ina xuwa" fita yayi
dakin ta bi sa da kallo, ba a dau lkci ba ya dawo da laptop dinsa da waya ya xauna
gefenta ya jawota jikinsa yace "Hope ba ki jin ciwo ko Ina yanxu?" Kai kawai ta
gyada masa, ya ci gaba da abinda yake a laptop din idonta na kan laptop din, sun fi
20 mins a haka wayarsa ya fara ring, a tare suka kalli wayar, Sunan Safeenah ne ya
fito a screen din, imaan ta dinga kallon wayar bbu ko kiftawa, shi kansa Mujaheed
kallon wayar yake, can yyi silencing kiran ya maida idonsa kan laptop, kira ya fi
uku ya shigo wayarsa na Safeenah bayan first kiran, daga karshe ya kife wayar
Mujaheed still operating his laptop, can kuma ya mike ya dau laptop din da wayarsa
yana kallon Imaan da ta yi kwanciyar ta yace "Bari in tafi wajen Inna" Bata ce
komai ba ya nufi kofa ya fita, mikewa xaune tayi ta bi sa da kallo haka nan taji
gabanta na faduwa, Yana fita da kusan minti goma sai ga Inna ta shigo dakin ta rike
ha6a tace "Shi Mujaheed din yace maki kar ku sakko kasa ku barni ni daya a parlor
kamar shegiyar mayya?" Imaan tace "Ba ya sauka ba shi inna" cike da masifa Inna
tace "Ya sauka ina? Ni kadai raina a parlor kamar tsohuwar mayya, dama wllh sai da
Ahmadu yace kada in je naki ji to gashi dai an walakanta masu ni, dama abinda ya
guda kenan ni ce bana jin magana" Imaan ta sauko saman gadon ta marairaice tace
"Inna ni fa kaina ne ke ciwo shi sa na xo na kwanta, wllh na xata Yaya yana parlor"
Inna ta kulle kofar ta karaso kan gadon murya can kasa tace "Amma dai duk abubuwan
da na gaya maki a gida kina aiki da su kuwa Imaan??" Imaan tace "Na me kenan?" Inna
tace "A dakin nan Mujaheed ke kwana?" Imaan bata san lkcn da tayi murmushi ba ta
girgixa kai tace "Aa ba nan yake kwana ba" Inna tace "Toh kar ki kuskura sai kin ga
akwatuna kin ji?" Imaan tace "Toh" Inna tace "Atoh, ko min dadin bakin da xai maki
kuwa" Imaan ta gyada mata kai tana murmushi, Inna tace "Kuma kina dai cin abinci
koh naga duk kin fige?" Imaan tace "Ehh Ina ci" Bude kofar dakin aka yi Mujaheed ya
shigo, Inna tace "Toh Ahmadu dai yace kada in dade, haka kawai kada in bata ran d'a
na, bari in je Imaan, in sha Allahu jibi xan xo..." A hankali Imaan tace "Inna ki
bari da yamma mana" Inna tace "A'a haka kawai, wa gareni da xai gaya min gaskiya
banda Ahmadun, ga Bukar ya xama abinda ya xama" daga haka ta nufi kofa Imaan ta
mike ta ki yarda ta kalli Mujaheed dake kallonsu ta bi bayan Inna. Murmushi
Mujaheed yyi ya bi bayansu yace "Toh ni ne baxa ki ma sallama ba Inna?" Inna na
sauka stairs tayi kamar bata ji sa ba Imaan na biye da ita, tsaye ya gansu balcony
Inna na mata magana kasa kasa, tana ganinsa tayi shiru ta fara tafiya tana cewa
"Toh ni na tafi Imaan, Allah ubangiji yyi maki albarka, ai kin cika min ciki...."
dariya ta basa sosai ya bi ta ya kamo hannunta yace "Toh mu je in ajiye ki a gida
inna sai nima ki sa min albarkan" ta tabe baki bata dai ce komai ba, imaan dai na
tsaye har ya bude mata back seat, Inna ta kalli Imaan tace "Fatan dai duk kin ji
abubuwan da na gaya maki koh?" Imaan ta gyada mata kai a hankali, Mujaheed yace
"Dauko Hijab dinki mu je mu yi dropping dinta" yi tayi kamar bata ji sa ba ta juya
ta koma ciki, tana tsaye parlor har ta ji fitar motarsa a compound din, sai da taji
Mai gadi ya kulle gate sannan ta wuce sama ta shiga parlonsa da sauri, tun da suka
xo gidan ranan ne ta fara shiga parlon, duk iya dubanta bata ga wayarsa ba, hakan
yasa ta karasa cikin bedroom dinsa, daddadan kamshi ke tashi dakin nasa dake very
neat, ta nufi saman gado ganin wayarsa ta dauka ta bude, call logs ta shiga, sosai
gabanta ya fadi tana kallon kiran safeenah da yayi picking, ta shiga details don
duba minutes din kiran aka bude kofar dakin, da sauri ta juya xuciyarta na bugawa,
kallonta ya tsaya yi sannan ya mika mata hannu alamar ta basa wayar, sauke kanta
tayi kasa bata motsa daga inda take ba, ya karasa ya karbi wayar a hannunta sannan
ya juya ya fita, Bata san lkcn da ta durkusa kasan dakin ba ta hade kai da gwiwa
sai dai taji kukan ma ya ki xuwa, ta fi minti goma a haka sannan ta mike da kyar ta
fita dakin ta koma nata, xaunawa tayi gefen gado har sannan xuciyarta na bugawa.
Imaan na tsaye kitchen tana wanke abubuwan da ta 6ata wajen hada ma inna breakfast
ta ji shigowar motar mujaheed gidan, Bata fito kitchen din ba sai da ta gama
tsaftace ko ina sannan, xaune ta samesa parlor ya jinginar da kansa da kujera, ya
bi ta da kallo yace "Aunty na gaishe ki" tace "Ohkk" sannan ta wuce sama, tsaf ta
gyara dakinta ta canxa bedsheet ta kunna turaren wuta dama tun da tayi wanka ta
wanke bandakin sama sama, duk da yunwar da ta fara ji sosai bata yadda ta sauka
parlor ba tayi kwanciyarta tayi lamo gaba daya taji hankalinta ya ki kwanciya, Bude
kofar dakin aka yi ta rufe ido da sauri kamar mai bacci, ya kulle kofar ya karaso
kusa da ita ya xauna gefenta ya kai fuskarsa dai dai nata yace "Kin ma yi breakfast
din kuwa Imaan?" Tana kokarin juya masa baya har lkcn idonta a rufe tace "Uhm"
dagota yyi ta bude ido fuska daure tace "Bana son haka..." Bai bari ta rufe baki ba
ya hade bakinsa da nata, Turasa ta dinga yi amma ya ki sakinta, ya rungumeta sosai
yana kissing duk jikinta, ta fara girgixa masa kai kamar xata yi kuka tace "Yaya
stop plss" ko sauraranta bai yi ba yana bin ta a hankali kuma a nutse, sun dau lkci
me tsaho a haka ganin gaba daya ta sakar masa jiki ya bude lumsassun idonsa a
hankali yana kallonta, ita ma idonta a rufe
suke yyi murmushi ya ja hancinta a hankali yana shafa fuskarta yace "Imaan" turo
baki tayi ta juya masa baya ba tare da ta bude idon ba, ya mike xaune ya dagota ya
rungumeta murya can kasa yace "What are taking for breakfast?" Bata ce komai ba
kuma bata bude idon ba, ya mayar da ita ya kwanta yana murmushi ya mike ya fita
dakin, sai a sannan ta bude idonta a hankali. Har bacci ya fara dauketa Mujaheed ya
dawo dakin da take away din rice and stew ya ajiye abincin ya hau saman gadon ya
kai fuskarta yace "Imaan" Bude ido tayi da sauri suna hada ido ta kauda kai ta mike
xaune yace "Ga abinci ki ci, I am going to mosque now" ta gyada masa kai ya mike ya
fita, tana jin ya shiga dakinsa ta kalli agogo taga sha biyu ya wuce, mikewa tayi
ta wuce bathroom, ta hada ruwan xafi sosai tayi wanka sannan ta dauro alwala ta
fito, tana ta xaune kan darduma bayan ta idar da sllh, ga abincin da ya ajiye mata
bata ko bude ba, ya shigo dakin sanye da kananun kaya yana kallon ledan takeaway
din yace "But I told you to eat first Imaan" ta jawo abincin tace "Yanxu xan ci" ya
xauna gefen gado yana kallonta yace "Did you take ur bath?" Ta girgixa masa kai ba
tare da ta kallesa ba ta bude abincin ta fara ci, ya mike yace "idan kin gama you
come downstairs" ta gyada masa kai ya fita dakin, tana gama cin abincin ta mike ta
fita da take away din xuwa parlor, tv kadai ke aiki parlon ta karasa kitchen ta
ajiye ledan hannunta ta fito, wayarsa dake kan kujera ya fara ring ta karasa da
sauri tana kallon screen din ta ga Safeenah, still tayi ta kasa daina kallon phone
din, jin ya bude kofa upstairs ta tafi bayan kujera da sauri ta durkusa har ya
sakko parlon ya dau wayar yana duba screen din sannan ya daga ya kai kunne, daga
daya bangaren cikin sanyin murya Safeenah tace "I've been waiting kuma baka kira ba
Mujaheed" Mujaheed ya d'an kalli sama sannan yace "I said later not now Safeenah"
cikin rawar murya Safeenah tace "Don Allah ka kira Mujaheed I am waiting" yyi shiru
kamar baxai ce komai ba sai kuma yace "Ohk let chat" Safeenah tace "Nooo don kira
nake so" Yace "Alryt, I will call later when am outside" mikewa imaan tayi daga
inda take ta wuce sama ba tare da ta kallesa, bin ta yyi da kallo da mugun mamaki
har ta haura sama, ya katse wayar ya ajiye saman kujera. Imaan na shiga daki ta sa
makulli ta cire ta ajiye gaban mirror ta xauna gefen gado, wasu hawaye ne suka
dinga sakko mata ba tare da ta sani ba kawai jin saukansu tayi, lkci daya ta fashe
da kuka a hankali ta kife kanta da pillow tana jin xuciyarta na mata xafi, murda
kofar dakin taji yyi ta mike xaune da sauri tana goge idonta, yace "Imaan" tace
"Na'am" yace "Open the door" tace "I want to take my bath" shiru ya d'an yi sai
kuma a hankali yace "Ohk" komawa tayi ta kwanta, har dare bata fito daga dakin ba,
bayan ta idar da sllhn Isha ta shiga bathroom tayi wanka ta fito dare da towel, ta
gansa tsaye bakin kofar bathroom din, turo baki tayi xata koma ya rikota da sauri,
kamar xata yi kuka ta duka tace "Wayyo Yaya ban sa kaya ba stop it" ya dagota yace
"Why did you close the door?" Ta marairaice tace "Saboda Ina son in yi bacci, gashi
har na tashi" kallonta ya dinga yi, ta turo baki xata juya ya fixge towel din
jikinta, rungumesa tayi da sauri tana xaro ido tace "Nashiga uku Yaya" ya lumshe
ido laying her down on the bed. Karfe dayan dare Imaan ta farka ta daga kanta a
hankali tana kallon Mujaheed, xame jikinta tayi daga nasa ta sauka saman gadon ta
dau hijab dinta ta saka ta nufi kofa a hnki ta bude tana kallonsa ganin bai motsa
ba ta fita, parlonsa ta nufa ta bude kofar ta shiga ta kunna wuta tana kalle kallen
inda xata ga wayarsa, ta karasa cikin daki ta ga wayar kan gado ta dauka, missed
calls din Safeenah ta gani har hudu da text message, ko bude text din bata yi ba
tayi dialing number ta ta kai kunne, ringing daya kawai yyi Safeenah ta daga...

So sorry for the late update pls.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

*Albishirinku 'yan uwa*

Shin ko kun San zaku iya magance mafi yawan cututtukan da suka addabi al'umma yanzu
cikin sauki?
Sinadarin _Stemcell total care_ yayi fice wajen magance matsalolin diabetes, BP,
asthma, sickler, cancer, stroke, rashin haihuwa, fibroid, infection da duk wata
matsala da ta danganci lafiyar Al'umma.
Ba wannan kadai ba, akwai coffee na double root Wanda ke inganta duk wani abu da ya
shafi rayuwar aure ga maza da Mata, inganta qwayoyin haihuwa da dai sauransu.
Akwai sinadarin rage tumbi da dai sauransu.

*Domin neman qarin bayani ku tuntubi wannan lambar 07068136856*


Sai an gwada akan san na kwarai.

101.....

Cikin rauni Safeenah tace "Haba Mujaheed, why don't you want to listen to me? Why
ain't you picking my call bayan kuma kace xaka kira baka kira ba, you don't know
why I am....." Imaan dake sauraronta ta katse tace "Ke dakata... What business do
you have with my husband again?" Shiru Safeenah tayi jin muryarta, a mugun fusace
tace "Uban me yasa xa ki daga wayata, ke na kira da xa ki daga min wayar mijina?"
Imaan tayi wani dariya tace "Ehh lallai yanxu na sake confirming cewar ke babbar
mahaukaciya ce, kuma kinyi mugun nisa a hauka, shi Mujaheed din ne mijin ki??"
Dariya Imaan ta kara yi sannan tace "Toh bari ki ji in gaya maki, ko a mafarki da
kyar ki ga Mujaheed a matsayin mijin ki, Mujaheed yyi maki nisa sosai, sai dai ki
ajiye a tarihi kin ta6a auren Mujaheed, and let me drop u this last warning, keep
from my husband Safeenah kike ko wa?? Wllh ki fita hanyar mijina, even by mistake
kada ki sake kiransa don bashi da wani alaka da gantalalla mai tunanin dabbobi irin
ki, tun ban nuna maki wacece ni ba maza maza ki goge number mijina daga shegen
wayar, wahalalliya kawai mara xuciya, dama can mijin aro kika aura sai a ci gaba da
zawarci kuma...." Safeenah bata yadda hawayen da ke sakko mata ya hanata fashewa da
dariya ba tace "Ai kuwa ni ke da alaka da mujaheed fiye da kowa... don kuwa a yanxu
haka ina dauke da cikin d'an sa ko yar sa, kin gane abinda nake nufi or you need
more elaboration?" Imaan da taji wani diff ta bude ido sosai jin abinda tace, shock
da taji bai hanata cewa "Ki nemo uban cikinbki amma ba mijina ba, karya kike wllh
banxa kawai jahila, ke da Mujaheed bari in sake gaya maki wllh sai dai hange, shi
ma daga nesa nesa, Allah ubangiji ya raba sa hada xuri'a da watsatsun tambadaddun
family irin naku, duk sharrin ku da kulle kullen ku kuma a kan ku xai kare, xan ga
kuma ta inda xa ki sake kiran mijina jaka kawai mahaukaciya" daga haka Imaan ta
katse kiran ta danna mata block ta kunna data ta hau WhatsApp can ma ta danna mata
block sannan ta goge lambarta gaba daya a wayar tana huci, xata ajiye wayar ta ji
muryar Mujaheed a bayanta yace "Toh sannu! give me my phone" ta bude ido sosai sai
dai bata juyo ba, yace "I said give me my phone Imaan" lkci daya ta juyo fuska a
murtuke tana kallonsa tace "Baxan bayar ba, or do you have any business with the
useless lady da xata dinga kiran ka a waya kana biye mata, har ta cancanci ka sake
daga kiranta bayan abinda tayi ma mahaifiyar ka?? Ko har ka mance ne? Or is it
because you didn't watch the scene? To ba ruwana wllh baxan yadda ba, kuma xan gaya
ka da Abba...." karasawa yyi xai dau wayarsa ta dauke a fusace ta fice daga dakin
kamar xata tashi sama ya bi ta da kallo, Imaan na komawa dakinta ta ji wani
takaicin da bata san lkcn da ta fashe da kuka ba, ta rufe fuskarta da pillow, Lkci
daya tayi tsit ta daure fuska jin budewar kofa, muryarsa taji yace "But did you
know u just shouted at me Imaan?" Banxa tayi masa bata dago ba, ya karasa kan gadon
yace "Imaan" tashi tayi a fusace xata bar wajen ya fixgota, ta fara buge hannunsa
tace "Ni ka kyaleni, leave me alone" ya matse ta jikinsa yace "Listen to me now,
bana son kina min magana haka, you don't know why I answered her call and I don't
think you have the right to call her, sure Safeenah raised her hands on my mum amma
na tabbatar wannan kuskure ne kin kuma san irin xuciya ta Imaan, i don't keep
anybody in mind..." Katse sa imaan tayi tace "Ehh nasan kalan xuciyar ka amma ban
san kalan yanda ka ba ma addinin ka muhimmanci ba, ban san irin fahimtar da ka ma
addinin ka ba, ban san ko kasan illar tarayyar ka da mahaukaciyar ba tunda dama ita
nasan jahila ce ba sani tayi ba" yyi gripping dinta da karfi yace "Ke xaki koyar da
ni addini na? Do you have to? Are you thinking kin fini sanin addini ne? Safeenah
is carrying my child so I have to listen to her no matter what, it's my
responsibility or ain't you aware of that religious lady?" kasa cewa komai Imaan
tayi tana kallonsa ko kiftawa babu, ya saketa yana kallon wani direction din, can
ya juyo ya jawota xata kwace kanta ya kankameta giving her a romantic kiss all over
her neck, wasu hawaye suka dinga sakko mata tana son kwacewa amma ba rikon wasa yyi
mata ba, murya can kasa yace "I have to listen to her for the Kamar daxu hot
romance ya shiga mata amma wannan karan she didn't even respond, bata kuma sake
jiki ba, har lkcn kuma hawaye take har da shessheka, hakan yasa ya kyaleta yyi
kwanciyarsa ya juya mata baya, tun bayan aurenta da Mujaheed yau shine karo na biyu
da Sadeeq ya fado mata, tasan Sadeeq baxai ta6a mata haka ba, he will never, dama
kuma Mujaheed ai bai ce yana sonta ba kawai aura masa ita aka yi, dole ya nuna mata
muhimmanci Safeenah gareta, tunanin hakan yasa ta fashe da kuka sosai shi dai bai
ce mata komai ba. Daren ranan gaba daya Imaan ta kasa bacci, karfe biyu saura ta
mike ta shiga bandaki ta dauro alwala ta fito ta fara sllh, sai uku saura taji
bacci ya fara damunta tayi kwanciyarta nan saman darduman, haka yasa Mujaheed ya
mike ya kashe Ac dake aiki a dakin ya koma yyi kwanciyarsa, daga nan kuma bacci ya
dauketa. Da asuba bude kofar dakin da yyi ya farkar da ita, tana ji ya koma dakinsa
bayan wani lkci ya fito ya wuce masallaci. ko da ya dawo sllh ya tadda ta tana yi,
ya xauna gefen gado har ta idar, ta mike ta dauka qur'ani ta koma kan darduman ta
xauna, duk yana bin ta da kallo ta gefen ido, ta fara karatun ta, bayan wani lkci
ya mike ya fice daga dakin. Sai da gari ya fara washewa Imaan ta mike ta ajiye
qur'ani ta dauke darduma ta fita dakin a hankali, bude kofar parlonsa tayi making
sure bata yi making sound ba ta karasa kofar dakinsa da bai rufe ba gaba daya ta
tsaya, waya ta ji yana yi calmly, sosai gabanta ya fadi tana sauraren abinda yake
cewa, "What did you mean Safeenah, sure i will take care of you, I will take care
of my child u are carrying, after that ba wani abu kuma..." Abinda Imaan taji ya
fada kenan, da mamaki ta ji yace "Auren kisan wuta kuma?? Did you even know what
you are saying?" Imaan taji gabanta yyi mugun faduwa taji ta ma kasa tsayuwa bakin
kofar, mikewa mujaheed yyi yana kallon kofar jin motsi da sauri ta matsa ta jingina
da bango, ya karaso bakin kofar ya bude suka yi ido hudu ta wani daure fuska, yace
"We will talk later" daga haka ya katse wayar yana kallonta yace "Why do you derive
joy intruding in my affairs imaan? gari ya waye common ki bude baki ki gaida mijin
ki baki iya ba amma kin iya kishi da saka masa ido, do you have any problem? Meye
amfanin kishin naki?" Kallonsa kawai Imaan take bbu ko kiftawa, yace "Bana son kina
saka min ido a abinda nake yi, and I don't think it's necessary ki dinga shigo min
nan da safe ba gaisheni kika xo yi ba..." juyawa imaan tayi ta nufi kofa ta fice
daga parlon ta wuce dakinta, ita kanta tayi mugun mamakin yanda ta dake xuciyarta,
ta cire kayan jikinta ta tafi bathroom kawai ta wanke baki ta hada ruwan wanka tayi
ta daura towel ta wanke bandakin ta fito, sai bayan da ta gama shiryawa ta feshe
jikinta da turare sannan ta gyara dakinta ta kunna turaren wuta. Tana goge goge a
parlor Mujaheed ya sakko cikin shiri sai xuba kamshi yake, yana kallonta yace "What
will you take for breakfast Imaan?" Ba tare da ta kallesa ba tace "I will sort that
out" kofa ya nufa ta bi sa da kallon gefen ido har ya fita gidan ta ji fitar
motarsa gaba daya. Sai a sannan wasu hawaye suka dinga sakko mata ta dinga jin wani
xafi a ranta, tayi kukanta mai isarta ta gama goge gogen da take ta wuce sama ta
kwanta, har sha daya bata fito daki ba balle ta nemi abinda xata ci gaba daya taji
yunwar ma bata ji. Da rana tana kitchen ta na dafa indomie ta ji shigowar motarsa
gidan, tana ji ya shigo parlor sannan ya karaso kitchen jin kamshin dahuwar da take
yi, yana tsaye bakin kofar yana kallonta daga sama har kasa don skirt ne karami
jikinta sai riga yace "Kin yi breakfast din?" Tace "Nayi" yace "Ohk ga lunch na
kawo maki and you are cooking, amarya bata girki ai" Bata ce komai ba ya juya ya
fita, har ta fito daga kitchen yana xaune parlor, ta wuce sama rike da plate din
abincinta, kasa cin indomie din ta yi ta sha five alive da ta debo kadan ta tura
abincin gefe tana jin wani xafi da xuciyarta ke yi mata, bayan wani lkci ta mike ta
fitar da plate din har lkcn yana parlor xaune ya bi ta da kallo ta shiga kitchen ta
fito ta koma sama, bata kuma sake fitowa ba har Magrib. Bayan Isha tana tsaye gaban
press sanye da hijab har kasa xata fito da kayan bacci da xata sa Mujaheed ya shigo
dakin, ko kallon direction dinsa bata yi ba ta ci gaba da ciro sleeping dress
dinta, ya kulle kofa ya karaso ya ajiye ledan hannunsa yace "Ga abinci" shiru bata
ce masa komai ba ya isa bayanta ya jawota jikinsa murya can kasa yace "Ni kike
sharewa ko??" Bai jira cewarta ba ya fara daga hijab dinta to gain access to her
body, a fusace tace "Stop it Yaya" juyo da ita yyi ya fara kissing dinta gently
yana daga hijab din, ta fara turasa amma ya ki sakinta, sun dau lkci sosai a haka
amma gaba daya ta ki sakar masa jiki sai kukan take masa tana son kwace kanta, ya
saketa daga karshe ya mike ya xauna gefen gado da idanuwansa da suka sauya kala,
sauka take son yi daga saman gadon ya fixgota yace "You are only good at show
casing unnecessary kishi, to warce kike kishi a kanta 6ata ta6a hana ni hakkina ba,
ko da kuwa sau goma ne a rana.. I know what I am saying" Imaan tace "Sai kaje ta
baka yanxu ai" daga haka ta nufi kofa ya bi ta da kallo har ta fice daga dakin,
sannan ya gyada kai. Washegari gaba daya Mujaheed bai shigo dakinta ba yanda ya
saba da safe, ita dai ta gama duk abinda take, ta fita xuwa kitchen ta hada shayi
ta dawo parlor ta xauna, sakkowa yyi downstairs kasancewar ranan Friday ne sanye
yake cikin milk shadda da yyi masa kyau sosai, tun da ta kallesa sau daya ta dauke
kai, ya shigo parlon ya dau makullin motarsa yana kallonta don har snn kayan bacci
ne jikinta yace "Sai yanxu kika tashi kenan?" Ba tare da ta kallesa ba tace "Ehh"
yace
"Ohk, xan je gida sai na dawo after Juma'at prayer" tace "Nima xan je gida" yace
"A'a ki jira next week xan kai ki" ta wani hade rai ta kallesa, yyi murmushi yana
shafa kansa ya dawo kusa da ita ya xauna yana kallon fresh legs dinta don kayan
iyakar sa kneels yace "In sha Allah next week xa ki je ae" Bata ce komai ba ya
amshi shayin hannunta ya jawota jikinsa ta fixge ta matsa daga wajen ta dau cup din
shayin ta, mikewa yyi ya nufi kofa ta bi sa da kallo, lkci daya ya juyo tayi saurin
dauke kanta, yace "What will you be taking for lunch?" Ba tare da ta kallesa ba
yace "I will sort that out" dawowa parlon yyi ya ajiye makullin hannunsa da waya ya
koma sama, ta bi sa da kallo gefen ido, sai da taji budewar kofar parlonsa sannan
ta mike da sauri ta dau wayarsa ta ga ya sa lock, kallon wayar ta dinga yi da
mamaki kafin ta kashe ta ajiye ta koma da sauri ta xauna, ya sauko downstairs rike
da Atm card dinsa ya dau waya da makulli ya nufi kofa yace "Sai na dawo" Bata ce
komai ba har ya fita, ta ajiye shayin hannunta don gaba daya ji tayi ya fita ranta,
imagining ta dinga yi wai gun Safeenah xai je, lkci daya taji hawaye ya kawo idonta
ta jinginar da kanta da kujera tana jin xafi a xuciyarta. Sai kusan la'asar
Mujaheed ya dawo gidan, sai bayan kusan minti talatin ya shiga dakinta ya ganta
kwance idonta rufe ya karasa kusa da ita ya xauna yana shafa fuskarta a hankali
yace "Lil sis" kin bude ido tayi yyi murmushi don yasan ba bacci take ba, ya kai
lips dinsa nata ta bude ido da sauri ta dauke kai, shafa cikinta yyi yace "Ga
abinci Inna ta bada a a kawo maki downstairs" ta mike xaune ta koma can karshen
gado on a serious note tace "Bana son kana ta6a ni Yaya, I don't like it" shiru yyi
yana kallonta, can yace "Kar na ta6a ki sbda me?" A takaice tace "Saboda bana so"
yace "Ohk" daga haka ya nufi kofa yace "Farida ta kira daxu tana gaishe ki" daga
haka ya fita ta bi sa da harara, sai kuma ta 6ata fuska xata yi kuka. Haka nan suka
ci gaba da rayuwa gidan da gaske kuma ya daina ta6a ta iyaka ya siyo mata abinci da
drinks ya ajiye mata, wani lkcn ya hada da gasasshen kaza wani lkcn kuma fruits, a
ko da yaushe tana daki ita kadai, shi kuma yawanci yana parlonsa, duk dare dai xai
shigo to make sure ta sha drugs dinta sannan ya wuce dakinsa yyi kwanciyarsa. A
haka har yayi resuming aiki ranan Monday, karfe takwas saura ya shigo daki ya ganta
kwance tana bacci sbda dadewa da tayi tana azkar bayan sllhn asuba, ya isa gabanta
yana kallon skin dinta dake wani sheki, ya durkusa kusa da ita, ya fi minti biyu
yana kallonta kafin a hankali yace "Imaan" Bude ido tayi, sai kuma ta mike xaune ta
koma baya, ya mike yace "Xan wuce aiki, akwai kayan shayi downstairs with bread, I
don't know ko xa ki ci egg ki soya yanxu kafin in tafi" ta girgixa kai tace "Baxan
ci ba" yace "Ohk..." Daya wayarsa ya mika mata yace "If you need anything you call
me, but don't call anybody with the phone" tace "Ni dai xan kira Ammi na" juyawa
yyi ya fita dakin ya kulle mata kofa. Sai kusan karfe hudu da rabi ya dawo gidan
yana haurawa sama ya bude dakinta daga kai tayi ta kallesa daga xaunen da tayi
gaban mirror tana tsefe kitson kanta, yace "Kin ci abinci kuwa?" Ta ci gaba da
abinda take tace "Na ci" yace "Me kika ci?" Tace "Ni dai na ci" yace "Gobe xa a
kawo maki house maid sai ki dinga monitoring dinta tana girki" ta kallesa tace "A'a
bana so, xan iya" yace "Ai ba ni na fada ba, daddy ne ya fada" daga haka ya fita
dakin nata. Ta gama tsefe gashinta ta dau abubuwan wanke gashi ta shiga bandaki ta
wanke gashin nata sannan ta fito ta busar. Kwanciya tayi saman gado maganganun da
Ammi tayi mata daxu ya dinga dawo mata, ji tayi kamar ta fashe da kuka tunawa da
tayi Ammi fa ce mata tayi bbu ruwanta dole yana da hakkin kula da Safeenah da cikin
da tace tana da shi, ita ko kadan bata yadda Safeenah na da ciki ba ta rasa dalili,
gashi duk hanyar da xata san ko suna waya ynxu bbu don tun ranan bata sake shiga
dakinsa ba. Bayan isha Mujaheed na dawowa masallaci ya shigo bedroom dinta da ledan
abinci, kamar ko da yaushe a dai dai wannan lkcn yau ma ta fito wanka ne, da sauri
ta koma bathroom, ya ajiye mata ledan abincin ya fita dakin, ta gama shirin
kwanciyarta har ta kwanta sai kuma ta mike ta dau ledan ta fita da shi, xaune ta
gansa parlor ya bi ta da kallo ganin kitchen xata shiga yace "Kin ci abincin?" Tace
"Am not hungry" mikewa yyi ya bi bayanta, ta ajiye ledan xata juyo suka kusa cin
karo, komawa baya tayi da sauri ya dau ledan da plate sai cup ya kamo hannunta yace
"You must eat, baxa ki kwanta haka ba" da mamaki tace "Ka ta6a ce min I must eat a
gidan nan?" Bai tanka ta ba ya xaunar da ita ya debar mata abincin ya ajiye mata
sannan ya xuba mata drink din ya ajiye yace "ki cinye yanxun nan Ina kallon ki" da
mamaki take kallonsa, can tace "Ni dai nace maka na koshi" yace "I am not joking
imaan, ki ci abincin nan ko kuma ki sha drink" shiru tayi tana kallonsa, can ta
turo baki ta dau spoon ta fara cin abincin yana kallonta ko kiftawa bbu, da kyar
take hadiyewa daga karshe ta ajiye cokalin ta mike tace "Ni dai na koshi" rikota
yyi yace "Drink din fa?" ta xaro ido tace "Ni bana shan drink da daddare" ya hade
rai yace "Take it now Imaan" dariya ya bata ganin how serious he is tace "Ni ka
ta6a ganin na sha drink da daddare haka?" Yace "Ehh ki sha ko kadan ne" kamar xata
yi kuka tace "Ni Yaya fa baxan iya Sha ba" ya dauka cup din ya kai five alive din
bakinta yace "Bude bakin my friend" karba tayi a hannunsa kamar xata yi kuka ta kai
bakinta ta fara sha, ya dinga kallonta har tayi rabi sannan ya saketa ya mike yyi
wucewarsa sama ta bi sa da kallo ta ajiye sauran drink din.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

*Albishirinku 'yan uwa*

Shin ko kun San zaku iya magance mafi yawan cututtukan da suka addabi al'umma yanzu
cikin sauki?
Sinadarin _Stemcell total care_ yayi fice wajen magance matsalolin diabetes, BP,
asthma, sickler, cancer, stroke, rashin haihuwa, fibroid, infection da duk wata
matsala da ta danganci lafiyar Al'umma.
Ba wannan kadai ba, akwai coffee na double root Wanda ke inganta duk wani abu da ya
shafi rayuwar aure ga maza da Mata, inganta qwayoyin haihuwa da dai sauransu.
Akwai sinadarin rage tumbi da dai sauransu.

*Domin neman qarin bayani ku tuntubi wannan lambar 07068136856*


Sai an gwada akan san na kwarai.

102....

Tun da Imaan ta koma daki ta kwanta ta ji ta very restless, gaba daya ta rasa
takamaiman abinda ke damunta, ta dinga juye juye kan gado, can ta mike xaune, a
hankali ta xamo kasa daga kan gadon ta durkusa ta kife kanta da gadon, ta fi minti
ashirin a haka aka bude kofar dakin Mujaheed ya shigo rike da goran ruwa da drugs
dinta, kallo daya yyi mata ya dauke kai ya karaso kusa da ita yace "Yau kuma haka
xa ki kwanta" k'in cewa komai tayi kuma bata dago ba ya dagota ya juyo da ita yana
kallonta ganin hawaye idonta da damuwa yace "Subhanallah me ya faru?" Bata ce komai
ba ya kwantar da ita saman gadon yace "Ko kafarki ke ciwo?" ita dai bata ce komai
ba ya mike ya dauko man shafanta na kafa ya kashe wutan dakin ya bar mara haske ya
fara shafa mata, lumshe ido tayi, hakan yasa yyi murmushi yana kallonta, Bayan wani
lkci ya kai bakinsa fuskarta yace "Bayan ma yana maki ciwo?" Bata bude masa ido ba
ta gyada masa kai, juyar da ita yyi ya sauke wear dinta kasa ya fara shafa mata
lotion din a bayanta, ya jima yana massaging back dinta gently sannan ya juyo ta
yana kallonta yace "Yayi sauki koh?" Ta bude idonta a hankali tana kallonsa, ya
sakar mata murmushi ya ja dogon hancinta yace "Sleep tight dear, sai da safe" xai
mike kawai ya ji ta jawosa sai kuma ta fashe da kuka, ya wara ido yace "what
happened?" Ta mike xaune ta rungumesa tana shessheka, ya lumshe idonsa murya can
kasa yace "Ki gaya min menene?" Shiru bata ce komai ba yana jin yanda take sauke
numfashi a hankali, kamshin gashinta duk ya cika sa, ya janyeta jikinsa yace "Xan
kwanta, I have work tomorrow" kin sake sa tayi tana kara shigewa jikinsa, and that
really turned him on duk da yanda ya so ya share even for sometimes, lkci daya ya
fara bi da ita gently kuma romantically, ko kadan bai yi mamakin martanin da ta
dinga mayar masa ba, ta basa hadin kai 100% ba raki ba komai, daga karshe ma shi ya
rikice mata, and that nyt will forever remain in his memory... Can karfe biyu Imaan
ta farka ta dalilin kanta da ke ciwo sosai, ta janye daga kusa da shi a hankali ta
mike xaune tana kallonsa tana rufe kanta da duvet, lkci daya ta ji kunya ba na wasa
ba ya rufeta, maganganunsa suka dinga dawo mata da daddaya da daddaya, kallonsa
kawai take ko kiftawa bbu, kawai gani tayi ya jawota ya kankameta ya kai bakinsa
kunnenta yace "Why are you staring at me wife" rufe idonta tayi da sauri ta boye
fuska jikinsa kamar yana ganinta, yyi murmushi yana shafa gashinta, a haka bacci ya
kara dauketa. Tun da Mujaheed ya dawo masallaci yake bacci a bedroom dinsa, Imaan
ta fito kitchen bayan ta juye ruwan xafi flask, tana kallon agogo ganin bakwai ya
wuce ta wuce sama, ta fi minti biyar tsaye bakin kofar parlonsa sannan ta bude a
hankali ta shiga ta wuce bedroom dinsa, bata gansa dakin ba amma jin saukan ruwa ta
gane yana wanka, ta nufi gaban madubi ganin envelope ta bude envelope din ta leka
ciki sannan ta ciro takardan, warwarewa tayi tana duba content din, Takardar scan
ne dauke da sunan Safeenah, sosai gaban Imaan ya fadi ta dinga kallon takardan dai
dai nan Mujaheed ya fito bathroom, ta madubi ta kallesa ta sunkuyar da kai da
sauri, ya karasa bayanta ya tsaya ya kwanto ta jikinsa a hankali yace "Wife..."
Bata dago kanta ba ya juyo da ita yana kallonta yace "Ko xa ki rakani office yau?"
Ta girgixa kai kawai, ya dau takardan ta linke ya mayar cikin envelope din yace
"Toh fito min da kayan da xan sa" Shiru tayi bata ce komai ba ya dago kanta yace
"Kin ji?" Tace "Ai ban san gun kayan ba" nuna mata yyi ta tafi gun press din ta
bude, a gabanta ya saka kayan bai bari ta fita ba kamar yanda tayi niyya, yana saka
safa kafarsa yace "Kin ga yau kin sa na makara" Ta d'an turo baki tace "Ni kuma?"
Yyi mata slight kiss a lips yana rike da hannunta yace "Ehh mana lil sis..."
Sunkuyar da kanta tayi ya mike ya dagota yace "What are you taking for breakfast?"
Tace "Anjima xan dafa indomie" yace "Ohk, mu je ki rakani gun mota xan dawo in sha
Allah da karfe 12 in ga wife dita sai in koma karfe daya..." tace "Breakfast fa?"
Yace "Xan yi a office dear" ta turo baki tace "Na fa dafa maka ruwan xafi kuma
akwai bread" ya wara ido yace "Da gaske?" Ta gyada masa kai yace "Toh mu je inyi
breakfast din" suna isa dinning tace "Or should I fry you egg?" Yace "Xa ki iya?"
Tace "Uhm" a tare suka tafi kitchen din yana tsaye bayanta ta gama soya eggs din ta
kashe gas, ya juyo da ita ya daura forehead dinsa kan nata a hankali yace "Plss ki
dinga min haka Imaan, wllh I want to be with you till eternity, baki San yanda nake
ji dake ba ko kanwata? Ki daina bani wahala haka, one day you will know what I
mean" Ko kadan abinda ya fada bai burge Imaan ba, Wai he just want to be with her,
shi dai kawai so yake ya kasance da ita and nothing more, ta sauke idonta da ya
kawo hawaye ya rungumeta ta tayi lamo jikinsa tana jin kamshinsa, lumshe ido yyi
yana jin wani irin sonta da sha'awarta na daban, wanda dai dai da second daya bai
ta6a jin sha'awar Safeenah ba sai in ita ta kawo kanta, tare suka yi breakfast din
duk da bata wani ci da yawa ba ta rakasa har bakin mota kamar yanda ya bukata
sannan ta koma ciki bayan ta kulle gidan, dakinta ta wuce ta kwanta lkci daya
baccin da bai isheta ba ya dauketa. Karfe sha daya ta farka, babu 6ata lkci tayi
wanka ta shirya cikin doguwar riga na material, ta feshe jikinta da turare tana
gyara gadonta taji an bude kofar dakin, a tsorace ta dago ganinsa ta turo baki ta
xauna kamar xata yi kuka tace "Yaya ka bani tsoro" ya karaso cikin dakin yana
murmushi ya cire necktie dinsa ya nufeta yace "Tsoro kuma sai kace ba takwarar Inna
ba baby?" Turo baki tayi ya xauna kusa da ita yyi mata side hug yana murmushi yana
kallonta murya can kasa yace "Kin yi kyau sosai wife, did you know I have been
thinking about yesterday throughout yau a office" Bata yarda ta kallesa ba kuma
bata ce komai ba, ya kai bakinsa kunnenta yace "Gaya min wa ya koya maki in masa
kyauta" boye fuskarta tayi shoulder dinsa cike da shagwaba tace "Ni bana so fa
Yaya" kwantar da ita yyi saman gadon ya kwanta shi ma yace "Ae kuwa xa ki so ynxun
nan" sai kusan karfe uku Mujaheed ya bar gidan ya koma office Imaan na bacci bayan
ya ajiye mata lunch a daki. Kiran la'asar ya farkar da ita ta bude ido a hnkli ta
kalli gefenta ta mike xaune ganin bata gansa ba, farin takardan da ta gani gefen
pillow ta dauka ta warware taga rubutunsa kamar haka "God bless you dear, sai na
dawo anjima, I care..." Turo baki tayi ta ajiye takardan tana jin bayanta na d'an
mata ciwo ta sauka daga kan gadon ta wuce bathroom. Da Mujaheed ya tashi dawowa
around 5 na yamma da waya irin wanda Sadeeq ya ta6a siya ma Maryam ya shigo gidan,
tana kitchen ta gama blending kayan miya ta ji shigowarsa gidan, leka parlor tayi
suka yi ido hudu ya buda mata hannu yana murmushi, ta make masa kafada ta, a
hankali yace "Toh shikenan" daga haka ya wuce sama ta bi sa da ido, ta gama fiddo
nama a deep freezer sannan ta fito ta wuce sama, a hankali ta bude kofar parlonsa
yanda baxai ji ba ta shiga ta karasa bedroom dinsa don a bude kofar yake, button
din rigarsa ta samesa yana cirewa ta karasa dakin ta kwanta bayansa ta lumshe ido
murya can kasa tace "Wlcm" ya juya da ita drawing her closer to him, girkin da bata
karasa a lkcn ba kenan ta biye ma Mujaheed. Tana xaune saman darduma tana kallonsa
bayan sun idar da sllhn Magrib, ya mike yace "Let go out and get something to eat"
Tace "Ae yanxu xan yi girkin" yace "Noo I don't want to stress you anymore, mu tafi
mu siya a eatry" Bata ce komai ba ya kama hannunta ta mike ya dauke darduman ya
ajiye, ledan da ya shigo da shi daxu ya dauko mata ya kama hannunta ya mika mata
yana kallonta, ta dinga kallon ledan sannan ta bude, lkci daya ta wara ido ta
rungumesa gam tace "Waow nagode Yayana, thank you very much" ya lumshe ido yace
"You are welcm sweet" ta turo baki ta 6ata rai tace "Ni dai ka daina ce min sweet
bana so" yace "Ohh daxu da na gaya maki kin xata wasa nake ba sweet xan dinga kiran
ki ba" ta make kafada tace "Ni bana so" ya dauketa Kamar yar baby yace "Toh sai
ince maki Zuma" dariya tayi ta rikesa gam tace "Ni dai bana so" yyi kissing
hancinta ya ajiyeta yace "Toh mu je idan mun dawo sai ki bude wayar" daga haka ya
dau makullin motarsa ya kamata suka fita dakin. Lafiyayyen abinci ya siya masu da
gasasshen kaji, suna dawowa wayarsa dake ajiye kusa da shi a mota ya fara ring, a
tare suka kalli screen din, a hankali Imaan ta dauke kai ganin sunan Safeenah a
screen din. Bayan few seconds yyi Picking call din ya sa handsfree ya ajiye yayi
sallama, maimakon ta amsa murya can kasa tace "Dr wllh kaza nake son ci, tun safe
nake ta amai bani da appetite na komai, yanxu kuma naji ina son cin kaza pls idan
ban takura ka ba" Mujaheed yace "Ohk" tace "Kazar gida nake so fa kuma a lafta min
yaji plss" yace "Alryt" tace "Sai ka hado min da Hollandia milk with shawarma kila
in ci" yace "Naji" daga haka ya katse wayar. Ya kalli Imaan dake kallon window yace
"Sweet let get her what she want before going home" shiru tayi masa bata ce komai
ba, ya kamo hannunta a hnkli, sae a sannan tace "Ohk" duk sai da Mujaheed ya siya
ma Safeenah abubuwan da ta lissafa masa sannan ya tafi gidansu, yana isa kofar gida
ya kira wayarta, bayan ta daga yace "I am outside ki turo a amsar maki kayan" ya
ajiye wayar yana kallon Imaan da ta jinginar da kanta da kujera, Bude gate aka yi
sai ga Safeenah ta fito daga gidan sanye da hijab har kasa, kallonta imaan ta dinga
yi ta jikin glass sbda hasken fitulu ne ta ko Ina a kofar gidan nasu, ba karamin
ramewa tayi ba sai idanuwa, Mujaheed na ganin ta fito ya bude motar xai fita ita
kuma ta bude side din Imaan suka yi ido hudu, da sauri Safeenah ta juya coz bata
ta6a tunanin tare suke ba, Imaan kuma ta dauke kai, Mujaheed ya xaga ya mika mata
ledan hannunsa yace "How are you feeling?" Ta amsa ta gaishe sa a hankali, yace
"Allah ya kara lafiya, sai da safe" daga haka ya xaga ya bude front seat ya shiga
ya ja motar ta bi sa da kallo. Gaba
daya daren ranan Mujaheed bai gane kan Imaan ba, abincin ma ta ki ci, ta ki yarda
kuma ya ta6a ta, a haka ya kyaleta yyi kwanciyarsa amma ya kasa bacci, can cikin
dare bayan tayi bacci ya jawota jikinsa ya rungume, a haka ya samu yyi bacci. Sai
da ta dau kusan sati taki sake masa taki yarda ya ta6a ta, duk ya daga hankalinsa
ba kadan ba don just for two days da suka yi tare ta basa hadin kai ya ji baxai
ta6a iya nisantarta ba, mamakin irin kishinta yake it's just too much, bai san ana
kishi haka ba don ko lkcn da Safeenah take kishi da Imaan tun bata ma san xai
aureta ba da ya fara aika mata sakkoni shkkn sai kuma wani lkcn, haka nan bai gaji
ba ya dinga lallabata don Imaan na da baiwar da ba ko wace mace ke da shi ba, she's
totally different from a lot... Tana linke hijab bayan ta idar da la'asar ya shigo
dakin, dawowarsa aiki kenan, ta dauke kai ta ajiye darduman, kamota yyi cikin
lallami ya marairaice mata yace "Haba imaan, why are you doing this to me?" Ta hade
rai tace "Me na yi?" Ya xaunar da ita gefen gado ya xauna yace "Don Allah kiyi
hakuri, me yasa xa ki dinga kishi da Safeenah that's not my wife, she's not my wife
any longer, kuma babu aure tsakanina da ita, it's just my responsibility to take
care of her and her baby har ta haihu, so kike Allah yayi fushi da ni sweet?" Imaan
ta fashe da kuka tace "Toh dole sai ka dinga xuwa wajenta, tayi ta gilla ma karya
xata ci wannan xata ci wancan duk don kaje ta dinga ganin ka" Sosai ta basa dariya
ya rungumeta sosai yace "Toh daga yanxu baxan sake xuwa in je ta gan ni ba I
promise you, if she need anything xan bada a kai mata in sha Allah, idan kuma ta
haihu sai mu amso babyn mu, shkkn bbu kuma abinda ya hada ni da ita" cikin rawar
murya tace "Ba wani nan ai ba tare muke fita kullum ba balle in san ko ka je ko
baka je ba, kuma ni nasan cikin karya...." Rufe bakinta yyi da nasa ya lumshe ido,
nan ya shiga lallashin lil sis din tasa yanda ya kamata. Kiran sllhn Magrib yasa
Mujaheed ya bude ido a hankali yana kallon Imaan da ta makalkalesa, murmushi yyi
yana shafa kanta ya kai bakinsa kunnenta murya can kasa yace "It's time for prayer,
sweet...." A hankali ta bude idanuwanta tana kallonsa ta turo baki tace "Stop
calling me sweet" ya lumshe ido yace "Billah ke sweet dita ce" Ranan Saturday da
safe har Mujaheed ya gama abinda yake a laptop imaan bacci take duk da ko azkar
bata yi ba after subhi prayer ta koma baccin, ya kalli agogo ganin karfe goma saura
ya mike ya wuce dakinta, xaunawa yyi gefenta ya kai hannu fuskarta ta bude ido tana
kallonsa yace "Ni da kika hana bacci ban yi baccin safe har war haka ba sai ke
koh?" Ta turo baki ta mirgina ta mike xaune tana mitsika ido, yyi murmushi yace "Xa
mu fita yau fa, and I told you yesterday" a hankali tace "Toh" ya mike ya fita
dakin, cikin riga da skirt na atamfa super imaan ta shirya ta shafa powder fuskarta
sannan ta dau gogaggen hijab dinta har kasa color din supern jikinta ta saka ta
feshe jikinta da turare tana yamutse fuska ta fita, shayi kawai ta sha bata ci
bread ba, Mujaheed da ya shirya cikin kananun kaya shi ma ya mike ya dau makullin
motarsa ya kama hannunta yace "Toh mu je" Sai da suka hau saman titi ya kalleta
yace "Zaria xa mu fara xuwa sai mu tafi can gida ko?" A hankali tace "Toh" ko da
wasa bai yarda imaan ta lura da takardan scan din Safeenah da ya kai mota tun tuni
ya ajiye inda baxa ta gani ba, har suka kama hanyar Zaria bacci imaan take, ganin
yanda ta takure gu daya ya kashe ac din motar, suna isa gidan yyi parking a hankali
ya ja hancinta cikin cool voice dinsa yace "Sweet...." bude lumsassun idonta tayi
ta kallesa, ya dinga kallonta sannan yyi murmushi yace "Mun kawo..." ta fara kalle
kalle, ya sauka motar ba tare da ya dau envelope din ba ya xagayo ya bude mata side
dinta, sosai sisters dinsa dake gidan har lkcn basu koma kaduna ba suka ji dadin
ganinsa, babu wanda ya wani considering din Imaan sai Seeyama da ta xo gidan ranan
ita ma, Imaan ta xauna saman kujera ta sunkuyar da kanta bayan sun gaisa da
Seeyama, daga sama Umma ta sauka ta shigo parlon tana kallon Mujaheed tace "Sannu
da xuwa" yace "Yauwa sannu umma" Imaan ta sauko kasa a hankali tace "Ina yini Umma"
umma ta kalleta tace "Lafiya lau ya gida?" Imaan bata dago ba still tace "Alhmdllh"
Umma ta kalli Mujaheed dake gaisheta shi ma ta amsa ta xauna tana tambayarsa ya
aiki, yace "Alhmdllh Umma, ya gida fa" tace "Lafiya lau, sannun ku da xuwa" Seeyama
ce ta mike ta wuce kitchen ta dauko masu ruwa da lemo, ita kam har yau shiru ko
6ari bata yi ba, kana ganinta kasan tana tare da damuwa sosai don duk ta rame, ta
fito kitchen ta ajiye ma Mujaheed lemo da ruwan, sannan ta kai ma Imaan nata, Imaan
ta kalleta tace "Nagode" Seeyama tayi murmushi ta tafi ta xauna. Mikewa Umma tayi
ta wuce sama Mujaheed ya bi ta da kallo, Ummi na kallon Seeyama tace "Aunty Seeyama
mu je mu gama girkin toh" mikewa Seeyama tayi ta bi bayanta xuwa kitchen, Rahma ma
ta tafi ta ci gaba da wanke wanken da take, sae a sannan ya mike ya tafi kitchen
don cin uban kannin nasa. Bacci imaan ta dinga ji amma ta ki kwanciya, ta dai
jinginar da kanta da kujera ta lumshe ido, bayan kusan minti biyar ta bude ido da
sauri jin abu na taso mata ta dalilin aroma dake fitowa daga kitchen, mikewa tayi
ta rufe bakinta ta rasa inda xata, Seeyama da fitowarta kenan tare da Mujaheed tace
"Subhanallah me ya faru" kofa Imaan ta nufa xata fita compound kafin ta isa kofar
aman ya taho mata, lkci daya ta xube wajen ta dinga kwarara amai, Seeyama ta isa
kusa da ita da sauri ta durkusa ta riketa tace "Sannu Imaan, baki da lafiya ne??
Sannu" Mujaheed ya kasa karasawa ya tsaya yana kallonta ganin umma dake sakkowa
downstairs ita ma tana kallon imaan, Umma ta karasa gun su tace "Subhanallah, Me ya
faru Seeyama?" Cike da damuwa Seeyama tace "Amai take yi" Umma na kallon Imaan tace
"Sannu" Kasa cewa komai Imaan tayi wani aman na taso mata, Umma ta dagota sai ga
shi ta fara kwararo wani aman, hakan yasa Mujaheed ya taho wajensu, Seeyama ta tafi
debo ruwa da sauri, Umma dai sannu kawai take mata, sai da aman ya tsaya mata
sannan Umma ta nufi sama da ita Mujaheed ya bi su da kallo.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

*Albishirinku 'yan uwa*

Shin ko kun San zaku iya magance mafi yawan cututtukan da suka addabi al'umma yanzu
cikin sauki?
Sinadarin _Stemcell total care_ yayi fice wajen magance matsalolin diabetes, BP,
asthma, sickler, cancer, stroke, rashin haihuwa, fibroid, infection da duk wata
matsala da ta danganci lafiyar Al'umma.
Ba wannan kadai ba, akwai coffee na double root Wanda ke inganta duk wani abu da ya
shafi rayuwar aure ga maza da Mata, inganta qwayoyin haihuwa da dai sauransu.
Akwai sinadarin rage tumbi da dai sauransu.

*Domin neman qarin bayani ku tuntubi wannan lambar 07068136856*


Sai an gwada akan san na kwarai.

Where are those ladies with kwaikwaido hair??😆

To maxa ku garxayo Khaleesat ta sama maku wani oil da ku da cute babies din ku mai
shegen kyau da xai mayarshe ku indian's, it's tested and trusted sisters sai kun
xo.... Thanks

103....

Mujaheed na xaune gefen Imaan dake bacci a dakin Umma Seeyama ta shigo dakin da
abinci ta ajiye masa tace "Yaya ga abinci Umma tace a kawo maka nan" Yace "Ohk
thanks" ajiye abincin tayi tana kallon Imaan tace "Ya jikin nata?" Yace "Alhmdllh,
ya Mai gidan ki?" Tace "Yana lafiya qlau" yace "That's good" juyawa tayi ta fita
dakin, Mujaheed ya juya ya kalli Imaan dake bacci ya kai hannunsa forehead dinta a
hankali yaji bbu xafi jikinta, ya dauke hannunsa sannan ya bude daya daga warmer
din abincin da Seeyama ta kawo, stew ne dake ta xuba kamshi, Imaan ta bude ido ta
mike da sauri tana rufe hancinta da kyar tace "Yaya meye shi?" Murmushi yyi ya rufe
miyar ya kalleta yace "Sweet dita ce" Bata tanka sa ba ta koma can karshen gado ta
kwanta a hankali har sannan bata bude hancinta ba, a haka bacci ya kara dauketa ya
mike ya xaga kusa da ita ya duka a hankali ya janye hijab din daga fuskarta yana
kallonta ko kiftawa babu, murmushi yyi ya kai lips dinsa cheek dinta sannan ya mike
ya rage ac din dakin ya fita ya kullo mata kofar. Umma na parlor tare da Seeyama
dake cin abinci mujaheed ya shigo, Umma ta kallesa tace "Ya jikin nata?" Yace "Da
sauki bacci take" Umma tace "Toh Allah ya sauwake, har ka ci abincin ne?" Yace
"Idan nayi sllh xan ci Umma" ta kalli agogo tace "Ohk it's almost time" yace "Eh
lkci ya kusa" daga haka ya fita daga parlon ya tafi gun motarsa ya bude ya fiddo
envelope da ya taho da shi ya kulle motar ya koma ciki. Yana ta xaune parlor idonsa
a kan tv ya rasa ta yanda xai ba Umma takardan har dai daga karshe ya mike ya isa
kusa da ita ya mika mata ta amsa tana kallonsa tace "Meye wannan din" komawa yyi ya
xauna yace "Na Safeenah ne Umma" kallonsa Umma ta dinga yi babu ko kiftawa lkci
daya ta daure fuska tace "Me xan yi da shi? Kuma amfanin me xai min?" Mujaheed ya
sauke idonsa kasa yace "Ta kirani last week take sanar min she is pregnant, so
shine na tafi na amshi takardan scan din wajensu...." Umma ta dakatar da shi da
sauri tace "Karya take, nace karya take, Allah ubangiji kuma yyi maka tsari samun
zuri'a da wannan yarinyar, idan ma cikin ne Allah ya san yanda xai yi da shi balle
karya take..." Lkci daya hawaye ya kawo idon Umma, Mujaheed dai ya kasa cewa komai
duk jikinsa yayi sanyi, Umma na goge idonta tace "A asibitin ku aka mata scan din?"
Ya girgixa mata kai, Umma tace "Toh sai su je asbitin ayi scan din kafin a
tabbatar, in sha Allahu bata da wani cikin ka, in Allah ya yarda, domin wata
manufarta daban ta kintsa wannan karyar, kuma tana son amfani da hakan ne don kawai
ta ja ra'ayin ka gareta, Mujaheed ko hanyar gidansu ban baka izini ka bi ba balle
kaje gidansu, babu abinda ya hada ka da yarinyar nan, dama can ta dalilina ka santa
kuma a ta dalilina ka bar ta in har ka ba ma yarinyar nan da iyayenta listening
ears ban yafe maka ba Mujaheed, ko bayan raina bbu kai babu su in sha Allah babu
xuri'a tsakanin ka da ita, yanxu akwai abinda nace kayi shine ka sanar mata kuje
can asibitin da kake aiki xa a mata scan, kuma albarkacin annabi da al-qurani idan
ma cikin ne Allah yasan yanda xai yi da shi, in sha Allahu baxa ta haifa maka d'a
ba, Allah ya mana tsari da xuri'a irin tasu...." Mujaheed dai kansa na kasa bai ce
komai ba amma duk jikin sa yayi sanyi sosai, Umma ta mike tana goge hawayen idonta
da ya ki tsayawa ta wuce sama. Har yamma Imaan bacci take a dakin Umma, Seeyama ta
sakko downstairs tayi shirin tafiya tana kallon Mujaheed dake ta xaune parlor tace
"To Yaya ni xan wuce, Allah ya ba Imaan lafiya, naga har yanxu bata tashi ba balle
mu yi sallama" Mujaheed yace "Toh Ameen, da ta tashi sai mu tafi gaba daya coz we
are also going back to kaduna today" Seeyama tace "Ayya ba komai, Allah dai ya bata
lafiya Yaya" yace "Ameen, Allah ya tsare hanya" tace "Ameen" dubu biyar ya ciro
aljihunsa ya mika mata yace "Kiyi transport da wannan" amsa tayi tana murmushi tace
"Toh ngd Yaya Allah ya kara budi" su Ummi ne suka rakata xuwa bakin titi. Mujaheed
ya mike ya wuce dakin da Umma ke xaune, ya xauna saman carpet dake dakin yana
kallonta a hankali yace "Umma ba sai kin 6ata ran ki a kan wannan magana ba in sha
Allah xan yi yanda kika ce, sai taje can ayi scanning din, amma Umma kar ki manta
it's my responsibility to take care of her and the child..." A fusace umma tace
"Wani child din Mujaheed? Nace maka babu wani ciki, in sha Allahu baxa mu ga ciki
ba, idan ma da cikin Allah ubangiji ya san yanda xai yi da shi, wllh Safeenah
baxata haifo d'an ka ba in sha Allahu, idan Allah ya yarda kana tare da warce xata
haifa maka xuri'arka amma ba Safeenah ba, ko ba komai nasan asali da irin 'ya yan
ka" Mujaheed ya sauke kansa kasa shi dai bai ce komai ba amma har ransa ya ji dadin
furucin umma, Umma tace "Kana wani min maganan responsibility, responsibility din
me?? Ba sai da ciki ake daukan responsibility ba, to wllh idan kana son ganin bacin
raina kada ka fita harkan iyalan gidan Hajiya Mansura, duk Ni ce sillar komai kuma
ina rokan ka gafaran xamantowa ta silla, ba a mayar da hannun agogo baya amma da
banyi abubuwan da nayi a baya ba, Allah ya nuna min ishara ta hanyoyi da ban ta6a
xata ba, nan gaba idan Allah ya yarda ko ina k'in abu xan k'i sa saisa saisa,
sannan baxan fito fili in nuna kiyayata ba xan bar ma Allah komai, I have learnt a
great lesson, kuma na kara tabbatar da mutum ko waye shi bai isa ya ja da ubangiji
ba yayi kadan ne, sannan ina mai kara gargadinka ka rike addu'a don hakan shine
makamin mumini, ka dage da ibada especiallly at night, never get weak of praying
Mujaheed, Allah ubangiji yayi maka albarka, ya baku xuri'ar masu albarka" a hankali
Mujaheed yace "Ameen Umma nagode" sannan ya mike yana kallonta yace "Let me check
ko ta tashi coz we are leaving for kaduna today" Umma tace "Bata ci abinci ba, idan
baxata iya ci ba akwai gruel da muka yi jiya sai Ummi ta dama mata ko xata iya sha"
yace "Toh Umma" daga haka ya fita dakin, bedroom din Umma ya shiga ya tadda imaan
kwance still sleeping, ya karasa ya xauna gefenta ya daga rigarta yana shafa
cikinta a hankali, Bude lumsassun idonta tayi tana kallonsa, Kamar xata yi kuka
tace "Yaya na gaji" yace "Kin gaji da baccin koh?" Bata ce komai ba ya dagota ta
kwanta jikinsa tana maida numfashi a hankali, unlike daxu, yanxu kam jikinta ya
fara xafi, murya can kasa yace "Ina ke maki ciwo sweet?" Bata ce komai ba hakan
yasa ya dago kanta yana kallonta yace "Tell me how you are feeling" buda masa hannu
tayi alamar bata sani ba ta kara kwanciya jikinsa, yace "Toh xa ki ci shinkafar
yanxu? Sai in sa maki miyar kadan" da sauri ta girgixa kai tace "Aa bana so, amai
nake ji" yyi shiru sannan yace "Ko xa ki sha kunu kadan" Bata ce komai ba ya dago
kanta ta gyada masa kai, ya kwantar da ita ya mike ya fita dakin, yana tsaye kofar
kitchen Ummi ta gama dama kunun cikin cup daya ya sa ta saka sugar kadan sannan ya
dauka ya fita kitchen din ya koma daki ya ajiye don ya huce, kallonta ya dinga yi
don har ta koma bacci, Banda sheki bbu abinda jikinta yake, tayi haske kuma sosai,
bayan ya tabbatar kunun ya huce ya tada ta gently, ganin she looks so weak ya
jinginar da ita da gado yace "Sorry sweet, ga kunun ki sha kadan sai mu wuce gida
koh?" Karban cup din tayi a hannunsa ta kai bakinta a hankali, ko qtr bata yi ba
xata ajiye yace "Noo baki sha komai ba" tace "Allah na koshi Yaya" yace "A'a sai
kin kai rabi" Kamar xata yi kuka tace "Wllh cikina ya cika" dauka yayi ya daure
fuska ya kai bakinta, da kyar ta dinga sha tana hadiyewa daga karshe ta cire
bakinta da sauri, ya wani hade rai yace "Sai fa kin kara" toshe baki tayi tana
kallonsa, ya jawota da sauri yana patting bayanta a nutse yace "Stay calm baxa ki
yi ba..." Girgixa masa kai ta dinga yi xata sauka saman gadon jiri ya debeta ya
rikota kafin ta kai kasa nan tayi masa wanka da aman kunun da ta sha, sai da ta
fito da shi tass, ya dinga kallonta cike da tausayin ta, Umma ta shigo dakin jin
yunkurin aman nata tace "Ko dai xa ku je asibiti Mujaheed?" Yace "A'a Umma ai gida
xa mu wuce yanxu" Yana fadin haka ya mike ya daga ta suka wuce bathroom, Umma ta
yaye xanin gadon da ya baci da amai ta dau cup din kunun ta fita. Biyar na yamma
Mujaheed ya sami Umma a can dakin da take yace "Umma xa mu wuce gida" tace "Baxa ku
kwana ba Mujaheed tunda bata da lafiya?" Yace "A'a umma Ina son mu je can gida ne
ta sha magani..." Umma tace "Toh Shikenan, Allah ubangiji ya bata da sauki, Allah
ya sauwake" yace "Ameen" Hijab din Ummi Imaan ta sa sbda nata da tayi amai an
wanke, Mujaheed na rike da hannunta suka fita parlon, kana ganinta kasan she's very
weak, ya bude mata front seat ta shiga, Umma tace "Toh Allah ya sauwake Allah ya
tsare hanya" Da kyar Imaan ta amsa mata da "Ameen" Mujaheed yayi ma Umma sallama
suka bar gidan, Mujaheed na kallon Imaan da ta lumshe ido yana driving a hankali
yace "Sweet nace ma Farida idan mun shigo Zaria xa ku gaisa, mu je sai ta fito ku
gaisa sannan ku wuce" Imaan ta gyada masa kai kawai don ko magana bata so, yana isa
kofar gidan Farida ya kirata, kin fitowa tayi da farko wai sai sun shigo yace mata
sauri suke kuma Imaan din bata jin dadi, hakan yasa ta fito ta bude side din da
Imaan take xaune, Imaan ta gyara xama tana murmushi tace "Aunty Farida Ina yini"
Farida ta rike ha6a tace "Sannu imaan, ashe dai da gaske baki da lafiya" Imaan tayi
murmushi kawai, Farida tace "Toh Allah ya baki lafiya, Allah ya sauwake kin ji" a
hankali Imaan tace "Ameen Aunty" sai a sannan Farida suka gaisa da Mujaheed, nan
tayi masu Allah ya kiyaye tace xata je gidansu in sha Allah idan ta shigo kd, a
haka suka rabu Mujaheed yyi reverse ya bar anguwar. Har suka isa kaduna imaan bacci
take, yana parking a parking space ya bude motar ya fito ya xaga ya bude side
dinta, Bai bari ta sauka motar ba ya dauketa suka wuce gidan, a bedroom dinsa ya
kwantar da ita ta rikesa murya can kasa tace "Yaya sanyi nake ji" ya ja duvet ya
rufa mata sannan ya kashe Ac din dakin, duk yanda ya dinga lallabata daren ranan ta
sha shayi kin sha tayi wai
xata yi amai, a haka ta ci gaba da baccinta, karfe goma saura ya shigo ya ganta
xaune kan darduma tana sllh, yyi murmushi ya xauna gefen gado yana kallonta, tana
idarwa ta kwanta nan kan darduman, ya mike ya dagota ya kwantar kan gado yace
"Allah ya karba sweet, but fa sai kin sha shayi xa ki ci gaba da baccin ki" Daren
ranan Imaan bata yi wani bacci ba don da xaxxabi sosai ta kwana, Mujaheed ya dinga
tattalinta yanda ita ma bata yi bacci ba haka shi ma bai yi ba. Washegari lahadi ya
fita ya harhado mata drugs da yasan xa su mata amfani bayan yak'i da yyi da ita ta
d'an sha shayin ya bata drugs ta sha, sannan ya shiga bandaki ya hada mata ruwan
wanka, duk yanda ta dinga nonnoke masa haka nan ta hakura tayi wankan amma a
kunyace yana bandakin. Karfe sha biyu saura ya shiga dakin ya ganta tana bacci
sosai, dukawa yyi kusa da ita ya lumshe ido manna mata kiss a lips dinta sannan ya
rufeta da bargo gaba daya jikinta ya mike ya sauke curtain ya fita dakin, makullin
motarsa ya dauka ya fita gidan, driving yake har ya isa dai dai saman layin su
Safeenah, parking yyi ya dau wayarsa ya kirata, tana dagawa yace "Ban gan ki wajen
ba" mota ce tayi park gefen nasa sai ga ta ta fito a ciki, bude front seat tayi ta
shiga ya ja motar suka bar wajen, har suka isa asibiti bai kalleta ba, ita ko gaba
daya mood dinta kamar warce aka ma mutuwa. Yayi parking ya sauka motar ya rufe ita
ma ta fito a hankali tana kallonsa, ganin har ya nufi entrance din hospital din ta
bi bayansa kamar me counting steps dinta har suka shiga ciki, xaunawa tayi a
reception don har ya wuce office dinsa, gaisawa tayi da few nurses da ta sani a
wajen, wata nurse tace "Kwana biyu baki biyo Dr ba Madam" Safeenah tayi murmushin
karfin hali tace "Ae kuwa" tana ta xaune very restless har wata nurse ta kira ta
suka wuce sama.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

*Albishirinku 'yan uwa*

Shin ko kun San zaku iya magance mafi yawan cututtukan da suka addabi al'umma yanzu
cikin sauki?
Sinadarin _Stemcell total care_ yayi fice wajen magance matsalolin diabetes, BP,
asthma, sickler, cancer, stroke, rashin haihuwa, fibroid, infection da duk wata
matsala da ta danganci lafiyar Al'umma.
Ba wannan kadai ba, akwai coffee na double root Wanda ke inganta duk wani abu da ya
shafi rayuwar aure ga maza da Mata, inganta qwayoyin haihuwa da dai sauransu.
Akwai sinadarin rage tumbi da dai sauransu.

*Domin neman qarin bayani ku tuntubi wannan lambar 07068136856*


Sai an gwada akan san na kwarai.

104.....

Mujaheed ya dinga kallon takardan da nurse ta kawo masa office some hours later, a
hankali ya linke takardan ya ajiye ya jinginar da kansa da kujera, Imaan ce ta fado
masa ya mike da sauri yayi clearing din table din gabansa ya sauke curtain ya dau
wayarsa da makullin mota da takardan scan din sannan ya fita ya kulle office din,
Yana tsaye reception nurse ta tafi ta tado Safeenah da har ta fara bacci a wani
ward, yana ganin ta fito ya fara tafiya, har ya isa gun mota ya bude ya shiga yana
jiranta, tare da nurse dake rike da hannunta suka iso gun motar nurse ta bude mata
front seat ta shiga ta ajiye ledan Magunguna, mujaheed yyi mata godiya sannan ya ja
motar ya bar hospital din, sai da suka yi nisa ya d'an kalleta yaga bacci take, har
suka isa gidansu bata bude ido ba, shi ma kuma babu abinda ya ce, yana gama parking
ba tare da ya kalleta ba yace "Safeenah" bude ido tayi da sauri, ya dau ledan
maganin ya mika mata yace "Allah ya sauwake" amsa tayi ta bude kofar motar ta sauke
kafafuwanta waje amma bata fita ba murya can kasa tace "Is there any difference
between the first scan and this?" Yana kallon waje yace "No Allah ya raba lafiya,
Allah ya sauwake" tace "Ameeen" shiru tayi kamar yanda shi ma yyi shiru yana jiran
ta sauka ya wuce, tace "kayan shayin sun kare" yace "Ohk" sauka tayi daga motar ta
rufe ido sbda jirin da take ji ta dafe motar da sauri, ya kalleta yace "Careful"
Bata ce komai ba ta fara tafiya a hankali, tana isa gate dinsu kamar warce aka
hankade sai gani yayi ta tafi luuu, fitowa yayi da sauri daga motar, masu gadi dake
wajen ma duk suka taso, Suhaila da tayi parking dai dai lkcn kuma ita ma taga
abinda ya faru ta fito motarta da sauri ta nufi yar uwartata tana kwala kiran
sunanta, amma tuni Safeenah tayi collapsing a nan kasa, dukawa Mujaheed yyi kusa da
ita ya dagota yana jijjigata, daya daga mai gadin ya bude masa gate ya dauketa ya
shiga gidan da ita, Suhaila ta bi bayansa tana salati hankali tashe, sosai hankalin
yan uwanta ya tashi bayan ya shigar da ita parlor, babu dai wanda ya bi ta kansa
kamar yanda shi ma bai ko kallesu ba, har sai da Safeenah ta farfado bayan kusan
minti sha biyar, juye juye ta dinga yi tana rike da cikinta tana hawaye uwarta na
rike da hannunta tana mata sannu, Mujaheed ya ji tausayinta sosai... Hospital suka
kara komawa da Suhaila da Hajiya Baturiya, suna shiga reception din hospital din
jini ya 6alle ma Safeenah, nan da nan aka shigar da ita emergency ward, kasa shiga
emergency ward din Mujaheed yyi ya wuce office dinsa. Yana ta xaune office amma
hankalinsa ya kasu biyu sbda imaan dake gida, har wani colleague dinsa Dr Yusuf ya
shigo yana kallonsa ya ja kujera ya xauna, bayan few seconds yace "I am sorry Dr,
she had miscarriage" Shiru Mujaheed yyi yana kallonsa, lkci daya jikinsa yayi
sanyi, Dr Yusuf ya mike ya fita office din, tashi Mujaheed yyi ya fita office din
shi ma, ward din da Safeenah ke kwance Mujaheed ya nufa tun daga bakin kofa ya ji
Hajiya Baturiya na cewa "Wllh wllh shi xubar da cikin, wato dama tun da yace ta
shirya xa su asibiti yau naji ban yadda da shi ba, shi yasan abinda yayi cikin ya
xube..." Suhaila ta katse ta tace "Aikin banxa to sai me?? Allah na tuba dama me xa
ayi da iri irin na uwarsa matsafiya, Ni wllh ba ku ji murnan da nayi ba da cikin ya
xube, naji dadi har raina da Allah ya rabata da wannan tsinannen cikin, kawai
karshe ayi ma yar uwata wankin ciki a karasa rabata da tsiyarsu.." ita dai Safeenah
na kwance sai hawaye take, Hajiya marafa dai sai girgixa kafa take, juyawa Mujaheed
yyi ya fasa shiga ward din. Sai kusan Magrib Mujaheed ya koma gida ranan ya tadda
imaan na barci har lkcn, tausayinta ya ji sosai ya xauna gefenta yana kallonta
sannan ya fita xuwa dakinsa yyi wanka ya fita masallaci yin Magrib. Bayan sati biyu
da xubewar cikin Safeenah ranan Saturday da sassafe yana parlor yana operating
laptop, gaba daya laulayin Imaan ya damesa don wahala take sosai, duk ta rame gashi
ba abinda take iya ci, kuma bai sanar ma kowa a gida ba har lkcn banda umma da ta
sani, kusan kullum kuma xata kira ta ji jikinta, wani lkcn tace masa ya bata, danna
kararrawar da aka yi tare da bubbuga kofa yasa ya daga kai ya kalli kofar amma bai
tashi ba, Jin irin bugun da ake ma kofar yyi murmushi ya mike ya isa gun window ya
daga labule a hankali yana lekan waje, Maimoon kadai ya hango tsaye hannunta rike
da warmer ta xumburo baki tana kallon Hajiya Inna dake faman buga kofa da duk
karfinta, Inna ta ja tsaki ta tafi can inda ta hango wani dutse babba ta dauko ta
dawo Maimoon ta buda ido sosai tace "Kar fa kije ki gurje ma mutane kofarsu inna,
daga buga kofa sau daya baki jira ki ga....." Katse ta Inna tayi tace "Kada in
gurje ma mutane kofa? Waye mutanen? Mujaheed ko Imaan? yaran da aka haifa kan idona
nayi wahala da su tun durowarsu duniya xa ki ce kada in gurje masu kofar banxa
kawai, banda shegantaka ga shegen takalmansa Ina gani bakin kofa su bar ni tsaye
kamar mara makabuli duk sanyin safiya ya kare min?? Uban me suke yi a ciki toh har
yanxu basu tashi ba, ni ba a ta6a min irin haka ba duk gidajen da nake xuwa da safe
gaskiya" murmushi Mujaheed yyi yana shafa kai, nan Inna ta fara bubbuga kofar da
dutsen hannunta da gaba daya strength dinta, ya koma gun kofar ya bude yace "Idan
kika lalata min kofa sai kin biyani don baxan yadda ba Hajiya" shigewa parlon tayi
har tana neman bangajesa bata ko kallesa ba fuska daure, Maimoon na murmushi tace
"Ina kwana Yaya" yace "lafiya lau daga Ina ku ke?" Dariya tayi tace "Gida mana
yaya" ganin Inna ta nufi sama ya bi ta da kallo yace "Ikon Allah, Ina kuma xa ki
Hajiya?" Bata tanka sa ba har tayi wucewarta sama, shafa kansa yayi a hankali ya
kalli Maimoon yace "Abba yasan kun xo?" Maimoon ta girgixa kai tace "A'a ba wanda
ta gaya ma" hanya ya bata ta shigo parlon sannan ya wuce sama, direct parlon
Mujaheed Inna ta shige sannan ta wuce daki, kallon Imaan dake kwance a lullube tayi
tace "Meye kuma haka cikin xafin nan??" Karasawa kan gadon tayi ta fixge bargon
tana kallonta, Imaan ta bude ido a hankali, mikewa tayi ganin Inna, Inna ta saki
baki tace "Na shiga uku me ya same ki haka?" Imaan ta bata fuska ta jingina da gado
tana kallonta, Inna tace "Naga abinda ya isheni, Wace cuta ce wannan ta kama ki ni
patu duk kika kare?" Mujaheed dake tsaye bakin kofa yace "Xaxxabi take" Inna ta
kallesa da sauri tace "Xaxxabi?? Na cixon sauro ko me?" Yace "Ehh shi" Inna ta xaro
ido tace "Garin ya xa ku ba sauro izinin shigowa wannan santalelen gida haka, Ina
sauro ya ga wajen xama gidan nan fisabilillahi, toh gaskiya da sake, Kwata kwata
Mujaheed baka da kula, haka kawai ka bari sauron mayata su shigo gida har su cutar
min jika, tunda Imaan take bata ta6a xaxxabin cixon sauro ba a gidan ubanta, to ina
Bukar xai yarda da haka dama tunda yasan ciwanta, wato ga yarinya an baka a banxa
shine xa ka yarda ka ba sauro daman ya cuceta, to ba ruwana wllh, dama ni nasan
baxa ka iya rike min jika ba..." Daga haka ta fice dakin ya bi ta da kallo yana
murmushi, sannan ya isa gun imaan da ta koma ta kwanta, ya xauna gefenta ya kai
fuskarsa nata murya can kasa yace "Kin daina jin sanyin yanxu mu shafa cream?"
Marairaice masa tayi bata ce komai ba, ya jawota jikinsa a hankali yace "Wai da
gaske sauro ne ya cije ki?" Shiru tayi tana kwance jikinsa, ya shafa kanta yana
murmushi. Inna na komawa parlor dama wayarta ta ciro daga cikin jaka ta mika ma
Maimoon tace "Maxa kira min Ahmadu" Maimoon tace "Me ya faru?" A fusace Inna tace
"Don Allah ki kira min shi babu abinda ya shafeki da mai ya faru, yarinya duk naga
ta rame sai hanci da idanuwa ina xan yadda wai cixon sauro" Maimoon ta amshi wayar
ta kira Abba ta mika ma inna bayan ya fara ring, ko sallaman Abba inna bata amsa ba
tace "Ahmadu to fa ga Imaan rai a hannun Allah, na xo gidan na ganta a dunkule
cikin katon bargo duk ta kare tass sai k'ashi, wai cixon sauro, anya Ahmadu akwai
abun kirki a auren nan, da kyar fa take tashi take kwantawa, kada fa ku manta ita
kadai ke gare Bukar, Kar mu cucesa, wani irin cixon sauro ne yarinya xata rame ta
xabge ta fita hayyacinta haka, to ni dai wllh ba ruwana xan daukota mu taho gida, a
kan me Mujaheed xai amince sauro su shigo gidansa har su cutar min jika" kuka ta
fashe da ta mika ma Maimoon wayar tace "Kashe min wayata mu je ki hada min kayanta
a akwati sai dai duk xagin da Ahmadu xai min ya min, shi xai yarda a rike yar sa
yanda mujaheed ya rike imaan" daga haka ta wuce sama. Mujaheed yyi picking call din
Abba da ya shigo wayarsa ya kai kunne tare da yin sallama, Abba ya amsa yace
"Mujaheed me ya sami Mamana?" Mujaheed yyi kasa da kai yace "Abba bata da lafiya
ne" Abba yace "Me ya sameta?" Ya d'an yi shiru sai kuma yace "Rashin lafiya ne"
Abba yace "Tun yaushe?" Mujaheed yace "Kusan two weeks yanxu" Abba yace "Ciwonta ne
ya tashi?" Mujaheed yace "A'a" Abba ya d'an yi shiru, sai kuma yace "Toh Allah ya
bata lafiya, kuna xuwa asibiti ne" Mujaheed yace "A'a ina dubata a gida" Abba yace
"Innar tana nan har yanxu?" Mujaheed yace "Ehh" Abba yace "Toh ka bari su taho tare
gida tunda ta bukaci hakan, hakan ne kwanciyar hankalinmu gaba daya" yace "Toh
Abba" daga haka Abba yayi masa sallama ya katse wayar. Inna ta gama hada kayan
Imaan da kanta cikin jaka a bedroom dinta tana mita, Maimoon dai na tsaye tana
kallonta, Inna ta xuge zip din ta mika ma Maimoon wayarta tace "Kira min Aisha"
Maimoon ta amshi wayar ta kira Ammi, Ammi na dagawa Inna tace "Toh Aisha ga dai
imaan nan na xo na sameta ba kanta, tunda nake ban ta6a ganin ta rame irin yanda na
xo na sameta ba, Ni ba ruwana ki Kira mijin ki yanxu xan taho da jikata gida don
baxan kirasa ya bata min rai ba yayi min rashin kunya, wllh babu mahalukin da ya
isa hanani fitar da Imaan daga gidan Mujaheed yau, don idan ta mutu ni kadai nayi
asara ba wani ba" daga haka ta mika ma Maimoon wayar tace "kashe min kayana"
Maimoon na murmushi ta kashe wayar. Kafin Inna ta gama hade haden kayanta ta fito,
har Mujaheed ya saka ma
Imaan hijab yana rike da hannunta ya tafi parking space, front seat ya bude mata
ta shiga ya rufe sannan ya koma cikin gidan. Bai ko bi ta kan Inna ba ya kira
Maimoon yace ta xo su wuce sannan ya koma gun motar. Har suka isa gida Inna mita
take cikin mota wai taya sauro xai shiga gida mai lafiya haka ya illata mata jika
haka, bbu wanda ya tanka ta a motar, imaan dai baccin ta kawai take, daga karshe
mujaheed ya kure karatun Qur'anin dake tashi a motar. Parking yyi Inna ta bude
motar ta fice tana kallon Maimoon tace "Sakko ki bude mata ta fito" Maimoon ta fito
ta bude side din Imaan, ganin tana bacci Inna tace "Kin ga jaraba koh? Wannan
sauron lafiya ne kuwa ni patuu" Murmushi Maimoon tayi tana tashin Imaan, Imaan ta
bude ido sannan ta fito motar tana rike da Maimoon sbda juya mata da kanta ke yi,
Inna tace "Toh Allah dai ya isa" daga haka ta kama hannunta ta wuce sashinta da ita
fuskarta babu walwala, Mujaheed ya bi su da kallo yana murmushi, Maimoon ma ta bi
bayansu. Saman kujera Imaan ta kwanta ta juya baya, Inna dake ta kallonta tace
"Bari in xubo maki abinci ki ci mu wuce asibiti, ba sai na jira kowa ya ban kudi
ba, lafiyar ki ta fiye min komai dama tuwo nayi tun asuba kafin in baro gida" daga
haka ta wuce kitchen ta xubo tuwa da miyar kubewar da tayi ta dawo parlor ta ajiye
kusa da Imaan tace "Sakko ki ci, kin ji takwara" Imaan ta bude ido da sauri tace
"Ni fa baxan ci komai ba ki tafi da shi" Inna tace "Baxa ki ci komai ba kuma, ni fa
bana son wahala, yanxun nan xuciya ta debeni sai in tattaraki ki koma gidan
Mujaheed din ki mutu" Imaan ta ki juyowa tace "Inna ni ki tambayesa na ci abinci
fa" Inna ta xauna tayi tagumi tace "Ai ni na shiga uku" Aunty ce ta shigo parlon da
sallama ta gaida Inna tana kallon Imaan tace "Wai imaan bata ji dadi ba" Inna tace
Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

"Wllh, wai xaxxabin cixon sauro Amina, yaushe rabon da ayi wannan ciwon
fisabilillahi, tun tale tale fa, toh yanxu xamanin nan wa ke yarda sauro ya shigar
masa gida ma balle ya cucesa?" Aunty ta dago Imaan tana kallonta da damuwa tace
"Sannu Imaan" Imaan bata iya tace komai ba, Inna tace "Cewa nayi ga abinci ta ci in
kai ta asibiti da kaina ta ki ci" Aunty ta dago abincin tace "Ki ci ko kadan ne
imaan" tunda Imaan ta ji aroma din miyan, ta dauke kai tana matsawa daga kusa da
Aunty, Aunty ta lura da hakan ta mayar da abincin ta ajiye, Inna ta kuma daukowa
tace "Ji min mata, ki bata abinci kin mayar kin ajiye, abu dai baxa ayi sbda Allah
ba" Imaan na hada ido da abincin for the second time ta mike da sauri tana rike da
cikinta tayi hanyar dakin Inna, Aunty ta bi ta da kallo, inna ta saki baki tace
"Meye haka kuma?" Jin kakarin amanta Inna ta kalli Aunty tace "Meye ma'anar hakan
Amina?" Murmushi kawai Aunty tayi bata ce komai ba ta mike ta bi bayan imaan, Inna
dai na xaune rike da abinci baki har lkcn a bude, can ta ajiye plate din ta wuce
daki ganin yanda Imaan tayi mata amai a tsakar bandaki ta xauna gefen gado tayi
tagumi, Aunty ta cire mata hijab ta ajiye a bucket, ta taimaka mata ta wanke
bakinta sannan suka fito bandakin tana mata sannu, Inna tace "Toh aman meye wannan
aka kirba min a bandaki duk karni haka? Bandakin da na wanke da hypo biyu daxu, ah
gaskiya wannan rashin Imani ne, tana jin amai kuma baxata tafi can tsakar gida ba
sai ta juye min shi a bandaki na, sannan ke kuma Amina kin dau hijabi dumu dumu da
amai ki sa min a bokitin wanka na, haba jama'ah, wannan rashin kirkin har ina"
Aunty dai bata tanka ba ta kwantar da Imaan dake maida numfashi tana mata sannu,
Inna tace "Toh wllh Amina ki san yanda xaki yi da bandaki na ban dauko ta don ta
cuce ni ba gaskiya, xuciya daya na daukota ganin halin da take ciki, meye kuma xata
kaxance min bandaki da amai???" Daga haka inna ta fice daga dakin, Aunty ta koma
bandakin don ta gyara mata, ta fito parlor daukan omo Inna dake xaune parlorn ta bi
ta da kallo tace "Dama malaria na saka amai Amina?" Murmushi Aunty tayi tace "Gashi
kin gani kuwa Inna" Inna tace "Toh Allah ubangiji ya mana tsari da shi, amma
gaskiya mujaheed da kyar idan xan iya yafe masa wllh" Aunty ta fita tana dariya
kasa kasa. Karfe goma saura Mujaheed ya shigo parlon Inna, har lkcn Imaan na daki
tayi bacci, Inna kuma na bandaki tana wankewa bayan wanda Aunty tayi, ya shigo
dakin ya nufi kan gadon ya xauna kusa da ita yana kallonta a hankali yace "Imaan"
Imaan ta bude ido tana kallonsa yace "Sannu" ta gyada masa kai kawai, xaunar da ita
yayi yace "Toh me kike son ci?" Ta girgixa masa kai, da damuwa yace "Noo dole xa ki
ji da abinda kike son ci a ranki what is that?" Shiru tayi tana kallonsa, can tace
"Ni dai danwake nake so yau" Yace "Ohk toh, bari in gaya ma Aunty ta maki" kwantar
da ita yayi ya mike ya fita dakin, ya tafi can part din su gun Aunty, Aunty dake
bedroom dinta tace "Ae kuwa babu flour wllh, sai dai kaje ka samu Ammi nasan baxata
rasa ba sai tayi mata" yyi maza yace "A'a ni baxan iya xuwa ba Aunty ko xaki aika
Maimoon" Aunty ta tabe baki tace "Toh xan kirata a waya" murmushi yyi ya mike yace
"Toh ngd aunty" daga haka ya fita dakin, aunty ta kira Ammi, Ammi na dagawa bayan
sun gaisa Aunty tace "Kina da flour don Allah" Ammi tace "Ehh baxa a rasa ba" Aunty
tace "Toh Imaan xa ki yi ma danwake shi take son ci wai" Ammi tace "Toh bari in
duba" daga haka ta katse wayar. Cikin kankanin lkci Ammi ta gama danwaken da farko
Maimoon tayi niyyar kira ta kai danwaken amma sbda yanda take son ganin condition
din 'yar tata, tayi deciding ta kai da kanta kawai, Inna na xaune Parlor ta sa
tuwonta a gaba tana ci, Ta dinga bin Ammi da kallo har Ammi ta xauna ta gaisheta,
Inna ta amsa tace "Yar ki kika xo dubawa kenan, ai har na kullaceki nayi xaton baxa
ki xo ba don kece ta farko da na fara kira" Ammi tayi murmushi ta ajiye abincin
hannunta tace "Ga danwake nan na kawo" Inna tace "Toh gata can, malaria ne ya kusa
mata illa Ahmadu yace ba sai na kai ta asibiti ba an riga an kai ta" Ammi tace "Toh
Allah ya sauwake" Inna tace "Ameen, mijin ya dai cuce ta jeki ki ganta" mikewa Ammi
tayi ta wuce dakin, karasawa tayi kan gadon tana kallon imaan ta cire blanket din
jikinta, Imaan ta bude ido, da sauri ta mike ganinta tace "Ammi" sai kuma ta
rungumeta, Ammi tayi murmushi lkci daya jikinta yyi sanyi ganin yanda ta rame,
Imaan tace "Ammi Ina yini" dago kanta Ammi tayi tace "Ya jikin?" Imaan tace "Da
sauki" Ammi tace "Mu je parlor ki ci danwaken na kawo maki" Ta marairaice tace
"Ammi ina son inje can bangarenmu mu" Ammi tace "A'a kiyi xaman ki a nan" Inna ce
ta shigo dakin tace "Toh ta fito ta ci danwaken tun daxu babu abinda ta saka a
baki" Ammi ta mike tana kallon Imaan tace "Sakko mu je ki ci" A plate Ammi ta xuba
mata danwaken, Imaan dai sai kallon abincin take, ta dau fork da Ammi ta sa mata ta
dau daya a hankali ta kai baki, Ammi ta koma saman kujera ta xauna, Inna dai sai
kallon Imaan take tace "Toh ni dai ko wancan mayyar da ya saka ce ta kama jikata ba
a sani ba...." Ko rufe baki Inna bata yi ba Imaan ta mike tayi hanyar daki da gudu
tana yunkurin amai, Inna ta mike da mamaki tace "Yau naga tsiya, naga jaraba, meye
kuma amai amai kamar me ciki? Aman meye kuma wannan take yi?" Mikewa Ammi tayi ta
bi bayanta, Inna tayi shiru kamar me naxari, can ta bi bayansu ta shiga dakin da
sauri tana xare ido tana kallon Ammi da ta dago Imaan tana mata sannu, tace "Mun
shiga uku, Astagafirullah Aisha ko dai ciki ne da Imaan din?" Ammi dai bata kalleta
ba kuma bata ce komai ba, Inna dai sai xaxxare ido take tana kallon Imaan dake
sauke numfashi Ammi ta karasa shiga bandaki da ita. Inna ta saki salati tana tafe
hannu dai dai shigowar Aunty dakin, Inna tace "Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un,
ta cuce kanta wllh, kanta ta cuta ba ni patuu ba" da mamaki Aunty tace "Me ya faru
Inna?" Hawaye cike idon Inna tace "Yanxu sbda rashin tsoron Allah Amina sai da
yarinyar nan ta amince da wannan mutumi har ya kai ta ya baro babu kayan aure,
cikin d'an mutum ne da ita fa Amina, wllh tllh danyen ciki ne shataf da ita, ni
naga yarinya tayi wani haske kamar danyen nama, sai kirji da suka cicciko, to sai
kuma ga amai naga ta kirba daxu a bandaki daga tayi ido hudu da tuwo, yanxu kuma
daga uwar ta kawo mata danwake da mai da yaji ta kai loma biyu baki sai amai shaaaa
duk karni, kaiiii Amina lallai sai dai a kyale yaran yanxu, amma ba a ta6a kunyata
ni irin yanda Imaan ta kunyata ni ba yau" Aunty dai sai kokarin danne Dariyarta
take tace "Haba Inna, yarinya da mijinta kuma...." A fusace Inna tace "Ke dalla
rufe min baki, Mujaheed ne har xa a kira miji, dama jira kawai yake yyi mata ciki
ashe ni ban sani ba, ita kuma jarababbiya kawai, oh oh toh ba ruwana ya xo ya
tattara ta ya mayar da ita gidansu su je can su karata da aman su ba da ni ba xa
ayi wannan gagarumin kazantar ko 'yar cikina Hadiza lkcn da take da cikin d'an ta
na farko ban amince ta xauna da ni ba sbda amai da yawu balle wa ennan kareren, duk
kawai a bata min gida da k'arnin aman ciki, Aa wllh duk inda yake ya xo ya dauketa
ko kuma uwarta ta maida ta bangarensu suje can su karata wllh wllh ba ruwana, ba
dani ba, duka duka yaushe aka yi auren har ta yadda da shi ciki ya shiga idan ba
fitina ba" Aunty ta fita dakin tana girgixa kai tana murmushi, Ammi dai ta gama
gyara mata jikinta a bandaki ta fito da ita dakin tana rike da hannunta Inna ta
basu hanya da sauri fuska daure, Ammi ta fita dakin, ta dau cooler din danwaken
suka bar parlon ta wuce part dinta da yar ta.

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

*Albishirinku 'yan uwa*

Shin ko kun San zaku iya magance mafi yawan cututtukan da suka addabi al'umma yanzu
cikin sauki?
Sinadarin _Stemcell total care_ yayi fice wajen magance matsalolin diabetes, BP,
asthma, sickler, cancer, stroke, rashin haihuwa, fibroid, infection da duk wata
matsala da ta danganci lafiyar Al'umma.
Ba wannan kadai ba, akwai coffee na double root Wanda ke inganta duk wani abu da ya
shafi rayuwar aure ga maza da Mata, inganta qwayoyin haihuwa da dai sauransu.
Akwai sinadarin rage tumbi da dai sauransu.

*Domin neman qarin bayani ku tuntubi wannan lambar 07068136856*


Sai an gwada akan san na kwarai.
105.....

Da daddare Ammi na tsaye dinning tana debar ma Imaan kunun da ta dama mata a flask
aka bude kofar parlor, rufe flask din tayi tana kallon kofar Abba ya shigo da
sallama, amsa sallamar tayi har suka karaso cikin parlon Mujaheed na biye da shi a
baya, Abba ya xauna saman kujera yace "Sannu da gida Hajiya" Ammi ta karaso parlon
tana murmushi tace "Ina yini Alhaji" Abba yace "Lafiya lau, ya mai jikin ta kara
ji?" Ammi tace "Da sauki, Alhmdllh" Abba yace "Toh Allah ya bata lafiya" Ammi tace
"Ameen" shi dai Mujaheed kansa na kasa bai kalli Ammi ba yace "Ina yini Ammi" tace
"Lafiya lau, ya aiki?" Yace "Alhmdllh, ya mai jiki" Ammi tace "Da sauki tana ciki"
Abba ya mike yace "Bacci take ne?" Ammi tace "A'a ina jin idonta biyu" Bedroom din
Imaan Abba ya nufa Mujaheed ya mike ba tare da ya yarda ya kalli Ammi ba ya bi
bayansa, idonta rufe suka sameta dakin ta rufe duk jikinta da bargo, Abba ya tsaya
yana kallonta yace "Ta koma baccin kenan" Shi dai Mujaheed na tsaye sai kallonta
yake bai ce komai ba, Abba ya girgixa kai yace "Allah ya bata lafiya, I will check
on her tomorrow" daga haka ya juya ya nufi kofa, Mujaheed ya bi sa da kallo har ya
fita sannan ya isa kusa da ita ya xauna ya sauke blanket din jikinta ya kai hannu
forehead dinta yace "Imaan" Bude ido tayi tana kallonsa, ya sakar mata lallausan
murmushi ta kamo hannunsa cikin sanyin murya tace "Yaya" ya dagota ta xauna yace
"Kanwata" shiru tayi tana kallonsa, yace "Are you feeling pain anywhere?" Ta
jingina da gado tace "Ina jin xaxxabi da tashin xuciya, kuma my leg is aching me
now" yace "Toh xan taho maki da magani yanxu, but me kike son ci kanwata?" A
hankali ta girgixa masa kai tace "Amai xan yi" da damuwa yace "No baxa kiyi ba
sweet, tell me what u want to eat let me get it now" ta d'an yi shiru kamar me
naxari, can tace "Beans" ya wara manyan idanuwansa yace "Ke da ba ki cin beans
baby?" Turo baki tayi tace "Ni dai xan ci yau" murmushi yayi yana shafa cikinta a
hankali yace "Babynmu beans yake so kenan?" Kallonsa ta tsaya yi, ya ja hancinta
yace "Ko ba haka ba?" Ta 6ata fuska tace "Wani babyn?" Ya kashe mata ido yace "Na
mu mana sweet" turo baki tayi kamar xata yi kuka, ya ja hancinta yana murmushi yace
"Salon ki haifo min baby me turo baki koh?" Rufe fuskarta tayi da pillow, ya mike
yana murmushi yace "Xan dawo anjima kadan" Ita dai bata ce komai ba ya nufi kofa ta
dago kanta a hankali ta bi sa da kallo har ya fita, Ammi na tsaye dinning rike da
cup din kunu tana jiransa ya fito, Bai iya yace mata komai ba duk da ya so ce mata
xai dawo anjima, har dai ya nufi kofa ya fita ya kulle kofar sannan Ammi ta nufi
dakin. Abba na fita part din Inna ya nufa, ya shiga parlon da sallama jin ta a
kitchen ya xauna, sai ga ta ta fito tace "Ahmadu ne" yace "Ni ne, Ina yini Inna"
tace "Lafiya lau, aiki nake a kitchen, baka ji bayana ba wllh kamar xai balle in
huta" D'an murmushi yayi yace "Me kike girkawa kuma da daren nan Inna, ba an kawo
maki abinci ba?" tace "Me nake girkawa kuma? Wannan yarinya me laulayi nake ma
faten tsaki, wai daxu daga nace tana jin amai da sai ta min magana in kai ta waje
tayi a can sbda kar mu xama kazamai tunda a daki bandakin yake, kada kazanta ya
ra6e mu, na dai mata magana ta fahimta Ahmadu, shkkn in gaya maka sai matar nan
Aisha ta kullace ni ta taho ta dauketa ta tafi ba kunya ba tsoron Allah, suka bar
ni tsaye baki sake ina kallonsu, ni abun ma mamaki ya bani wllh, baka ji ba duk
jikina yyi sanyi qlau, nace to meye kuma daga magana dai mata ta figi hannun
yarinya ta wuce, to kaga agwai?? To ka ji tsoronsa, ni dai nayi shiru ban ce mata
komai ba, to ni dai bana bi ta mata bafillatana in ki kyautata ma jikata ba, daxu
na kira ta Rasulu ta aiko min jikarta da tsakin masara ko garin acca in yi mata
fate mai kyau da lafiya, shine nake yi tun daxh..." Abba yace "Ai kam kin kyauta
Allah ya bada lada" Inna tace "Ameen, amma da don ta Aisha ce wllh baxan yi ba don
bata da kirki Sam, ni dai ba ruwana inyi magana Bukar ya kullace ni, ita kuma Imaan
kaga ikon Allah daga auren sai ga rabo ko Ahmadu, ni dai nayi murna nayi murna, na
gode Allah, na gode Allah, na kuma yi addu'ar Allah ya raba lafiya, in sha Allahu
sae ta cika parlon ubanta da jikoki, tass sai ta haife kanninta muna nan da ku...
Da kyar kuma idan ba mace xata haifa ba don ita ce aka ce ko da bala'i sai ta je
gidan ubanta, Kai Alhmdllh, uwarta fa sai da tayi shekara kusan sha biyar ta
haifeta ita kuwa dubi daga shiga sai ga rabo" Abba dai sai murmushi yake, can yace
"Toh Allah ya raba lafiya" Inna tace "Toh Ameen, Allah ya bata da sauki naga kamar
irin mugun laulayin nan take irin dai wanda uwarta tayi, ni tsorona ma kada ta xama
k'ashi da rai dama gata ba lafiyayya ba" Abba ya mike yace "Toh bari in je Inna sai
ki ci gaba da abinda kike" Inna tace "Toh Allah maka albarka, amma gudun kada a
tada rigima gwara kawai in ci girma in bar Aisha da halinta sai ta karata da 'yar
ta ni kuma kullum sai in yi ta sintirin xuwa dubata koh Ahmadu?" Abba yace "A'a in
sha Allahu xata dawo wajen naki, xan je ynxu..." Da sauri Inna ta katse sa tace
"Lalala kar ka fara Ahmadu, a bar ta a can kawai ta xauna, ni kadai nasan irin
halin Aisha, bar mata yar ta kawai su karata, gani take baxan iya kula da ita ba,
bar su a can kawai ni babba ce baxan kulata muyi tashin hankali ba" Murmushi kawai
Abba yyi ya fita, Inna tayi wucewarta kitchen murya can kasa tace "kawai kawai ina
ganin irin aman da take kirbawa, ta ina xan fara ni ba kamfanin hypo da omo ba, ni
ba boyi boyi ba, A'a wllh uwarta na da rai ai" Inna na gama faten ta juye a cooler
ta fito kai ma Imaan, dai dai balcony suka hadu da Mujaheed da warmer a hannunsa da
leda, tana ganinsa ta hade rai, ya kalleta yana murmushi... Yace "Kishiyar ki kika
ma girki kenan" Wucewa ciki tayi tace "Ni dai ba ruwana, in sha Allahu a kanka
ciwon da jikata take xai kare, kuma sai Allah ya saka mata, lefe kuma ni dai ko na
mutu ban yafe ba ehe" bin bayanta yyi yana dariya yace "Sai dai ciwon ya kare a
kanki" Mikewa Ammi tayi bayan Inna ta shigo dakin, Inna dai bata kalleta ba ta nufi
Imaan dake kwance tace "Sannu takwara, ga faten tsaki me tsafta na maki, xai gyara
maki baki, ta shi in xuba maki ki ci" Tana fadin haka ta fita xuwa kitchen dauko
plate da spoon, mujaheed dai na xaune parlor, ta dauko plate din ta koma dakin ta
bude ta dibar mata faten da ya ji kayan hadi da ganye mai yawa ta nufi Imaan tace
"Tashi xaune" Imaan ta mike xaune tana kallon plate din da kyar tace "Meye wannan?"
Inna tace "Fate ne mana...." Imaan ta amshi plate din tana rike numfashinta sai
kuma ta ajiye ta dauke kai, inna ta bude baki tace "A'a ni fa ba wahalalliya bace,
kuma ba asararriya bace, cefanen dari biyar kenan kike gani wllh, babu abinda xai
maki sai ma gyara maki ciki da baki da xai yi" ita dai Ammi na tsaye, Imaan ta juya
a hankali ta dau spoon din ta debi abincin ta kai baki, Inna ta xauna gefen gado
tace "Dama banda ke wa xan ma haka? Ko Hadiza wllh bata samu haka ba, baki ji
maganata ba an dai cuce ki kawai" juyawa Ammi tayi ta fita dakin, Imaan ta dinga
cin abincin a hankali sbda tsamin yyi mata dadi a baki, sai da ta ci kusan rabin
plate din sannan ta ajiye, Inna tace "Ya aka yi?" Ta girgixa kai tace "Na koshi"
Inna tace "Toh sai ki ci sauran anjima" tana fadin haka ta mike tace "Gashi har kin
d'an marmaro, amma a bar ki haka ba kula kila tun safe babu abinda Aisha ta baki
kika ci, ni dai na tafi idan na gama sllh ko cikin dare ne xan shigo in duba ki"
daga haka ta fita, Mujaheed ya bi ta da kallo bayan ta shigo parlor yace "Toh ni
nawa abincin fa" Inna ta nufi kofa tace "Wanda uwarka Amina ta dafa kenan" yyi
murmushi yace "Ehh shi" bata tanka sa ba ta fita, ya mike ya dau warmer da ledan
drugs da ya siya ya wuce dakin, imaan da ta kife kanta da pillow ta dago tana
kallonsa, ganin yanda ta 6ata fuska ya karasa cikin dakin yace "What happened?"
Kamar xata yi kuka tace "Amai" ajiye abin hannunsa yayi ya xauna kusa da ita yace
"Sorry dear, baxa ki yi ba" bubbuga bayanta ya dinga yi a hankali, tayi lamo
jikinsa ta rufe ido, Bayan wani lkci ya dago kanta yace "Are you okay now?" Ta
gyada masa kai, yace "Toh in xuba maki waken?" da sauri ta girgixa masa kai tace
"Na koshi" yace "Toh ga magani ki sha" kamar xata yi kuka tace "Aa idan na sha
yanxu xan yi amai" yace "Toh anjima Ammi xata baki ki sha, xan je in yi sllh yanxu"
kwantar da ita yayi ya manna mata kiss a forehead yace "Allah maki albarka sweet"
lumshe idonta tayi, ya ja mata blanket ya mike yace "I will come in the morning in
sha Allah" gyada masa kai tayi ya juya ya fita dakin. Haka Imaan ta ci gaba da xama
part dinsu tana laulayi gun Amminta dake bata kulawa yanda ya kamata, har wanka
Ammi na taimaka mata idan jikin ya matsa mata sosai, throughout kuma Ammi na dakin
to make sure she is fine, komai tace tana so Ammi na kokarin ganin ta yi mata,
Aunty ma a rana ta kan shigo kusan sau hudu dubata, ita ma once in a while tana
girki irin na gargajiya ta kawo mata, dama ana idar da sllhn asuba Inna ke rafka
masu uban sallama a bakin kofa da cup din kunun ta a hannu, baxa kuma ta bar part
din ba sai in Imaan ta kirba amai kamar yanda take cewa, to ko second daya bata
karawa xata yi gaba tana yamutse fuska, Duk irin yanda Mujaheed ke son ganin wife
dinsa a ko da yaushe kasa shiga yake sbda Ammi, nauyi da kunyarta yake ba kadan ba,
kwata kwata bai iya shiga, haka nan xai wuce gun aiki da safe da tunanin wife din
tasa, a gun aikin ma gaba daya rabin hankalinsa na gun Imaan, gashi yyi ta kiran
wayarta bata dagawa sbda ko da yaushe silent wayar yake bata son ringing din, sai
dai kuma babu abinda ya rage su da, don every week sai ya siya kayan shayi, duk da
Ammi ta gaya ma Maimoon dake kawowa tace masa ba fa wani sha Imaan ke yi ba, hakan
bai sa ya fasa siya ba, Magungunan ta ma duk ya san lkcn da xai kare ya siya ya
bada a kai mata, once in a while idan Abba xai shiga da daddare shine xai bi sa su
shiga tare, duk Friday Yusuf kan shigo dubata
shi ma, ya kan dade dakin yana mata hira duk sai dai tayi murmushi tana kwance, a
haka har cikinta yayi wata uku, laulayin ya d'an mata sauko tayi wani kyau na
musamman ta kara haske, gaba daya Mujaheed ya kagu Abba yace ya wuce da matarsa
gida amma shiru Abba dai bai ce komai ba, yau Saturday da yamma kamar ko da yaushe
Inna na bakin tap dinta tana gurje gurjenta taji footstep, daga kai tayi, tayi
mitsi mitsi da ido tana kallon mai tahowa, lkci daya ta dauke kai ta ci gaba da
abinda take....

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

*Albishirinku 'yan uwa*

Shin ko kun San zaku iya magance mafi yawan cututtukan da suka addabi al'umma yanzu
cikin sauki?
Sinadarin _Stemcell total care_ yayi fice wajen magance matsalolin diabetes, BP,
asthma, sickler, cancer, stroke, rashin haihuwa, fibroid, infection da duk wata
matsala da ta danganci lafiyar Al'umma.
Ba wannan kadai ba, akwai coffee na double root Wanda ke inganta duk wani abu da ya
shafi rayuwar aure ga maza da Mata, inganta qwayoyin haihuwa da dai sauransu.
Akwai sinadarin rage tumbi da dai sauransu.

*Domin neman qarin bayani ku tuntubi wannan lambar 07068136856*


Sai an gwada akan san na kwarai.

106.....
Har Umma ta iso kusa da Inna Inna bata dago ba ta wani tsuke fuska tana ci gaba da
abinda take, Umma tace "Sannu Inna" Inna tace "Sannu" Umma ta d'an risina tace "Ina
yini Inna" Inna tace "Lafiya lau..." Umma tace "Ya gida ya aiki" Inna tace "Lafiya
lau" Umma tace "To madallah, sannu da aiki" Inna tace "Toh ga dai kofar a bude..."
Umma ta kalli kofar parlon Inna ta nufi parlon ta shiga ciki ta xauna, sai da Inna
ta shafe minti sha biyar bakin tap din sannan ta mike murya can kasa tace "Uwar me
ta xo min toh? Ni dai ba ruwana, bari ma dai...." Part din su Imaan ta nufa ta
tadda Ammi xaune parlor, tana kallon Ammi bayan ta kulle kofa tace "Kina ji na
Aisha?" Ammi ta mike tace "Ina ji Inna, sannu da xuwa" Inna tace "Bacci imaan
take?" Ammi tace "Ehh yanxu ta kwanta" Inna tace "Toh ko da wannan mata Rukayya
xata shigo nan kada ki kuskura ki yarda ta yi ido hudu da Imaan, a gaskiya idan
kika yarda ta ga yarinyar nan wani abu ya sami jikata bayan tafiyarta to xan rufe
ido in mance kina auren d'a na in dau mummunan mataki, babu wanda bai san Rukayya
axxaluma bace, to banda wani sharrin mai xaman kansa ya kawota uban me xata shigo
mana gida tayi kuma? Ni dai ba ruwana ki tafi ki makala ma kofar dakin jikata
makulli iyaka idan Allah yasa ta shigo nan ku tsaya iya nan parlor kuyi tadin ku ta
kara gaba, idan tace maki imaan fa kice ai tana can bangarena tun safe, don gaskiya
idan wani abu ya sami jikata da cikin dake cikinta har Bukar sai abun ya shafa ba
ke kadai ba, kai gwara ma abu ya same Imaan a kan wannan ciki na jikinta don ma ki
ji" daga haka ta fice daga parlon, Ammi ta girgixa kai ta koma ta xauna, Inna na
komawa part dinta ta shiga parlor tana kallon Umma dake xaune tana kallo, tace
"Daxu wani almajiri na da muka dade tare tun ina gidan mijina ya xo na kawo masa
swan water da ya rage a fridge, abinci kuma ba a kawo min na dare ba tukun" Umma
tace "A'a ba komai dama na xo duba Imaan da jiki ne..." Da sauri Inna tace "Wace
imaan din kuma? Ai Imaan ta warke garas tana ma ciki tana bacci bata son damuwa,
A'a wllh ta warke tun yaushe ma, ai dama laulayi ne ba wani abu ba, dama baki yi
asaran kudin motar ki ba duk da ban san daga inda kike ba amma jikata kam Alhmdllh
tana ma ciki tana bacci abun ta" Umma tace "Toh shkkn Allah ya kara lafiya ni xan
koma" Inna tace "Toh mun gode, Allah yayi albarka" Umma ta mike tace "Ameen
nagode..." Inna tace "Har xa ki tafi?" Umma tace "Ehh xan koma" Inna tace "Toh
yanxu wajen yayar taki mai shinkafa da wake a kasuwar tasha kike ko kuma wajen
Hadiza a kano" Umma tace "A'a ina Zaria" Inna tace "Ayyoo, kuna da yan uwa a Zaria
kenan?" Umma tace "Ehh" Inna tace "Toh madallah, sai dai kiyi kokari kiyi aure
shine mutuncin ki da rufin asirin ki tunda dai kin ki xaman gidanmu, Allah ya hada
ki da na gari dai" Umma tayi murmushi tace "Toh nagode" Inna tace "Toh kamar ina da
canji bari in baki kudin mota" Umma tace "A'a ki bar shi Inna nagode" Inna ta bude
jakarta ta fiddo hamsin biyu ta mika mata tace "Gashi nan kya yi kudin mota Allah
ya kiyaye" Umma ta amsa tace "Toh Allah amfana" Inna tace "Ameen" leda dauke da can
malt shidda ta ajiye ma Inna tace "Gashi ba yawa" Inna tace "Ke da kike fama da
kanki kuma kya siyo mantina ki kawo min, Toh Allah yayi albarka" Umma tace "Ameen"
Inna tace "Imaan din na ciki tana bacci da sai ince ki shiga ki ganta, amma bacci
take" Umma tace "A'a ba komai, a gaisheta idan ta tashi" Inna tace "Toh xata ji"
daga haka Umma ta fita parlon, Inna ta ta6e baki tana fito da malt din da daddaya
da daddaya. Umma na isa part din su Imaan tayi sallama bakin kofa, Ammi dake parlon
har sannan ta amsa sallaman, Umma ta shiga parlon, Ammi tayi mata sannu da xuwa,
umma ta xauna tana amsawa, nan suka gaisa, Ammi ta tafi kitchen ta dau tray ta
daura mata ruwa da lemo sannan ta fito ta ajiye kusa da ita tana tambayarta ya
gida, Umma tace "Alhmdllh, Alhaji fa" Ammi ta xauna tace "Yana Abuja kuwa" Umma
tace "Toh Allah ya taimaka, ya Imaan da jiki" Ammi tace "Jiki Alhmdllh, tana ciki
ma" daga haka ta mike ta wuce dakin Imaan, Abinci Ammi ta sameta tana ci tana kallo
a tv dake dakin, Ammi ta bude warmer din abincin tace "Yanxu wani abincin kike kuma
ci Imaan?" Imaan ta marairaice tace "Na kasa baccin fa, yunwa kuma nake ji" Ammi ta
tabe baki tace "Sai ki shiga kitchen da kanki kiyi wanda xa ki ci anjima baxan iya
ba, ki fito ku gaisa da Hajiya Rukayya" Imaan ta xaro ido tace "Ta xo Ammi?" Juyawa
Ammi tayi ta fita daga dakin, Imaan ta ajiye plate din abincin da ta cika dam bayan
wanda ta ci ko awa daya ba ayi ba, ta rufe abincin, sannan ta sakko daga saman
gadon ta bude press dinta ta dau ironed hijab dinta har kasa ta saka ta fito
parlor, dukawa tayi har kasa bata yadda su hada ido da Umma ba tace "Ina yini
Umma?" umma tace "Lafiya lau Imaan, ya karfin jiki" Imaan tace "Na ji sauki" Umma
tace "Toh madallah, Allah ya kara lafiya" Imaan tace "Ameen, ya gida" Umma tace
"Lafiya lau" Umma na kallon Ammi tace "Tun daxu na shigo Ina bangaren Inna" Ammi
tace "Allah sarki, bari a xubo abinci" Umma ta mike tace "A'a Alhmdllh, xan shiga
mu gaisa da Amina sannan in wuce, dama nace dai bari in daure in fito yau in duba
jikinta" ledan hannunta ta ajiye kusa da Imaan, Ammi tace "Toh Allah ya amfana,
Allah ya saka da alkhairi" Umma tace "Ameen sai da safe, Allah ubangiji ya kara
mata lafiya" Godiya Imaan ta kara yi ma Umma, Ammi ta rakata waje, Imaan ta mike ta
koma dakinta. Haka rayuwa ya ci gaba da kasancewa Imaan ta ji sauki sosai, bata da
wani takamaiman aiki sai ci, komai ta samu ci take, da wanda bata ci a da, da wanda
take ci, ita dai ta ci, son jiki kuma ya karu kan nada, ko kadan bata son stressing
kanta, har wanka sai tace Ammi ta cuda mata bayanta, Dama da Hajiya Inna ta ji
footstep ta leka da sauri taga imaan ce ke xuwa boye duk wani abinta na ci take yi
karkashin gado da gudu ta dawo ta xauna a parlor ta fuske, bbu abinda Mujaheed ya
rage ta da shi na abubuwan ciye ciye da kayan makulashe, komai tace masa tana so ko
karfe sha biyun dare ne sai ya fita ya siyo mata don yawanci a gidan yake kwana,
wani lkcn kuma ya tafi gidansa, ganin irin kunyar Ammi da yake ji dake sa shi bai
iya shigowa yasa Imaan da taga lkcn dawowarsa ya kusa daga gun aiki take wucewa gun
Inna, duk Ammi na lura da ita amma bata ta6a ce mata komai ba, shi kam Mujaheed duk
ya xuba masu ido a gidan ganin bbu wanda ke da niyyar cewa ya dau matarsa ya tafi
ko suna nufin tana gida har sai ta haihu ne shi dai bai gane ba. Inna ce tsaye
parlor sai mita take tana masifa tana cewa "Ni dai ba ruwana a daina xuwa ana 6ata
min waje ana takurani, ke dai baxa ki iya xama bakin ki bai yi motsi ba ki wani
shigo min parlon da na sha wahala na tsaftace da shegen bak'in gyada kina ci kina
tara min 6awo a parlor salon parlona yyi wari, ita Aishar ce ta turo ki ki cuce ni
ko Mujaheed din? Don nasan Bukar baxai turoki ki xalunce ni ba" Imaan dai sai cin
gyadan ta take tana tara 6awon, Inna tace "Ni wannan wahala ya isheni wllh, wani da
maki ciki ni kuma da cutuwa da wahala da cikin, kullum ayi ta cutata ana matsa min
ana kazantar min da parlor, wlh na gaji, ni ba abinda na hada dake gaskiya balle
mijin ki, shi mujaheed din da yayi miki cikin ki tafi dakinsa mana ki ci gyadan
idan ba rashin tsoron Allah ba xaki yo min nan...." Mujaheed dake tsaye bakin kofa
xuwan sa kenan yana cire takalmansa yana murmushi ya shigo parlon, Inna ta kallesa
ta wani hade rai ta shige daki, imaan ta bi ta da kallo tana taunar gyadarta tana
tabe baki, Xaunawa Mujaheed yayi kusa da ita yace "Wa ya siya maki gyada?" Ta wara
masa ido tace "Xaka ci?" Yace "Aa na bar maki da babies dinmu ku ci ku koshi" Imaan
ta 6ata fuska tace "Ni dai sai ka ci..." sakkowa yyi ya xauna gefenta ya jawota
kusa da shi yace "Toh sai ki tauna ki sa min a baki" dariya tayi ta 6are daya ta
kai masa baki, ya make kafada yace "Chew it first" Tace "Aa ni dai" lumshe ido yyi
ya fara kissing lips dinta dai dai fitowar Inna daga daki.... Da sauri Imaan ta
kauda kanta, Inna tayi kamar bata gansu ba tana kakkabe kujerunta ba tare da ta
sake kallonsu ba tace "Ni dai a fita a bar min parlona ni ba yar iska bace, ni ba
gantalalliya bace, kawai jaraba yayi yawa a duniya dai ga shi nan, Banda haka meye
kuma xa a xauna min parlor ana tambada ba kunya ba tsoron Allah, ni dai ba ruwana,
ban ma ta6a ganin haka ba tunda uwata ta haifeni, meye kuma mutumi xaka xauna gun
yarinya kamar xaka shige jikinta tana fama da kanta, a gaskiya ban san me kake nufi
ba, ita kuma jarababbiya tayi mukus... Kai jama'ahhh naga abinda ya isheni ni
patuu" mikewa Mujaheed yyi bai son yayi dariya yace "Ke dai baxa ki daina sa ma
mutane ido ba a gidan nan" da sauri Inna ta kallesa tace "Maxa ku fitar min daga
parlor ba ruwana, maxa maxa ku fita, kuma wllh kada in sake ganin kafafuwan ku a
nan, bari kuma Ahmadu ya dawo, ni dai ba ruwana, tunda uwata ta haifeni ban taba
ganin iskanci haka ba, haka ranan ka shige daki ka latse yar mutane saman gadona,
wancan ranan kuma ka bi ta har bandaki ban san me ku ke yi ba, idan kuma kitchen ta
shiga shi ma ka bita ka datse kofa, to wannan wani irin fitina ne, to kai baka da
tsoron Allah ne? Ni dai ba ruwana wllh" Mujaheed na dariya yace "Idan kina sa min
ido da ni da matata sai idonki ya tsiyaye nima ba ruwana" d'aga Imaan yayi suka
fice daga parlon Inna ta bi su da kallo baki bude. Da daddare Abba ya shigo gaida
Inna, ko amsa gaisuwarsa bata yi ba tace "Ahmadu kana ji na??" Abba yace "Ina ji
Inna..." Inna tace "A gaskiya ka yi ma d'an ka Mujaheed magana ya dauke matarsa su
bar gidan nan, ko kuma in har xa su xauna gidan nan su daina shigo min ni ba
gantalalliya bace, don abubuwan da nake gani sun isheni haka, ni dai ba ruwana
baxan ce komai ba amma gaskiya ya dauketa tunda mun gama bauta da ita ta samu
lafiya sai ma wani tashen fitsara da take min, ko mi ta ci ta bar min shi kaca kaca
a parlor duk wari sai dai ni in dauke in share, shi kuma Mujaheed na yi masa uxuri
don tun ba yau yake min rashin
kunya ba dama can ya rainani, wllh ce min yyi idona xai tsiyaye, to idan idona ya
tsiyaye ina lafiya Ahmadu? Naka xai kalli tsabagen idonka ya maka wannan mugun
alkaba'i? To ba ruwana kowa yyi ta kansa wllh ba don kai da Bukar ba ni dai babu
abinda na hada da Imaan da mutumin nan Mujaheed" Abba dai bai ce komai ba kansa na
kasa. Daren ranan Abba ya kira Mujaheed parlonsa yace masa washegari dama ya
tabbatar ya dau matar sa su wuce gida tunda mahaifiyarsa suke renawa, sosai
Mujaheed ya ji dadin jin haka har ransa amma bai dago kansa dake kasa ba, Abba yace
"Sai ka ci gaba da kula da ita, coz abinda take bukata kenan yanxu, if possible a
samar mata yar dattijuwa immediately sbda house chores, if there is anything you
let me know" kasancewar Washegari lahadi ne da safe Mujaheed ya tafi part din Inna
don yasan da kyar Imaan bata can, Xaune ya sameta parlor tana shan shayi da bread
leda guda, Inna dake share bakin kofarta tace "Jiya na ajiye maka fura da nono
shiru shiru baka dawo ba kuma" yace "Ni da kika kora da matata kuma me xan yi da
furan ki" daga haka ya shiga parlon yana kallon Imaan dake kokarin boye bread din
da take ci da sauri, yyi dariya yace "I caught you..." Kamar xata yi kuka tace "Ni
fa ba duka xan cinye ba fa, nawa ne da na Inna" Inna tace "Karya take Mujaheed,
daga wajen uwarta ta taho da shi, ba ruwana tass xata cinye shi, Ni wllh kada ma ta
tsiyace min kai da wannan uban cin da take, ni gani nake ma ba na lafiya bane"
Mujaheed yace "Toh Ina ruwanki?" Tsayawa Inna tayi tana kallonsa daga bakin kofa.
Karfe sha biyu saura Imaan na saka Hijab dinta Ammi ta shigo dakin, tana kallonta
tace "Ba abinda xaki tafi da shi" Imaan tace "A'a Ammi" Ammi ta xauna gefen gado
tace "Toh na dai gaya maki ki rage ciye ciyen kayan xaki, sannan kuma ki daina
wannan shegen son jikin kina kwanciya Kamar ruwa, try and be doing little works, ko
da an kai maki mai aikin, sannan wanka kuma da kike yi da ruwan sanyi ki daina"
Imaan tayi murmushi tace "Toh Ammi ai na daina" Ammi tace "Toh Allah ya kiyaye
hanya" Imaan ta dau handbag dinta tace "Ameen, ai xan dinga xuwa fa bayan kwana
biyu ki dinga min irin dambun da kike min" Ammi ta ta6e baki ta mike ta fita dakin,
Imaan ta bi bayanta, gun mota ta tadda Mujaheed na jiranta, sai da ta shiga part
din Aunty tayi mata sallama tukun tana bobboye cikinta da hijab kamar yanda take yi
idan ta ga Aunty, duk gidan banda Aunty da Abba sai Yusuf babu wanda take boye ma
ciki, da farkon fitowar cikin tana d'an jin kunyan Amminta tayi ta saka hijab tana
takure kanta, amma daga karshe kuma kawai ta sake, amma Inna from day one take
tsirara ma a gabanta da cikin, Aunty na murmushi tace "Toh Allah ya kara lafiya
daughter, Allah ya kiyaye" Sabbin turaren humra da aka kawo ma Aunty ta debar mata
da yawa sannan ta rakota har parlor imaan tayi mata godiya ta fita. Suna hawa saman
titi Mujaheed ya kamo hannunta yace "Babu abinda xa a siya maki sweet?" Imaan ta
langwabar da kai tace "Ni Ice-cream nake so plss Yaya, Ammi bata bari na sha wanda
ka siya min shekaranjiya ba" Mujaheed yace "Toh amma karami xan siya maki sbda
kinga garin da sanyi, bana son kina shan ice-cream din nan" Tace "Toh na ji, sai ka
siya min har da pizza" ya shafa lap dinta ya kashe mata ido yace "Toh mum twins" ta
turo baki tace "Bana so" murmushi yayi bai ce komai ba har suka isa babban eatry
din Mujaheed yyi parking ya bude motar ya sauka, ita ma ta sauka a hankali, still
tayi tana kallon motar da ya shigo yayi parking gefen motarsu a haraban eatry
din...

*Imaan isn't for free* it's 300 via

Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then u show ur evidence of payment via my WhatsApp number


07087865788

*Albishirinku 'yan uwa*

Shin ko kun San zaku iya magance mafi yawan cututtukan da suka addabi al'umma yanzu
cikin sauki?
Sinadarin _Stemcell total care_ yayi fice wajen magance matsalolin diabetes, BP,
asthma, sickler, cancer, stroke, rashin haihuwa, fibroid, infection da duk wata
matsala da ta danganci lafiyar Al'umma.
Ba wannan kadai ba, akwai coffee na double root Wanda ke inganta duk wani abu da ya
shafi rayuwar aure ga maza da Mata, inganta qwayoyin haihuwa da dai sauransu.
Akwai sinadarin rage tumbi da dai sauransu.

*Domin neman qarin bayani ku tuntubi wannan lambar 07068136856*


Sai an gwada akan san na kwarai.

107.....

Imaan ta dauke kai da sauri ta jingina da mota jin kafafuwanta sun kasa daukanta
xuciyarta na bugawa ganin wanda idonta yyi tozali da, tun da Mujaheed yyi ido hudu
da Sadeeq ya dauke kai ya rufe motarsa, Imaan ta bi sa da kallo don har ya kusa
entrance din eatry din, Xagayowa Mujaheed yyi yace "Mu je" Bata yadda ta kallesa ba
ta girgixa masa kai, yace "What?" Ta bude motar bata son ya ga hawayen idonta ta
shiga tace "I will wait here" mujaheed bai ce mata komai ba ya nufi cikin eatry
din. Hada idon da suka sake yi da Sadeeq cikin eatry din yasa Sadeeq ya d'an yi
murmushi ya karasa gun Mujaheed yana kallonsa ta glass din idonsa ya mika masa
hannu hade da masa sallama cikin cool voice dinsa, Mujaheed ya mika masa nasa
hannun yana mayar masa da murmushin, suka gaisa sannan Sadeeq ya koma inda yake
tsaye, packaging masa burger da ya siya aka yi ya bar eatry din Mujaheed ya bi sa
da ido, Yana isa gun motarsa suka kara ido hudu da Imaan da sauri ta dauke kanta
xuciyarta na bugawa, ya bude motarsa ya shiga ya tada ya bar haraban eatry din,
wasu hawaye ta dinga ji suna xubo mata bata san dalili ba, ta jinginar da kanta da
kujeran mota tana jin kamar ta fashe da kuka ko xata ji dadi a ranta. A haka
Mujaheed ya dawo ya sameta, tun da ya kalleta sau daya ya dauke kai ya tada motar
ya bar eatry din, har suka isa gida kuma bai ce mata komai ba yyi parking ya bude
motar ya dau ledan abubuwan da ya siya ya fita, ita dai bin sa kawai tayi da kallo
tana goge hawayen idonta, har ya tafi kuma ya dawo ya bude mata door din motar,
k'in fitowa tayi ya juya yyi wucewarsa, a hankali ta sakko daga motar ta rufe
sannan ta wuce ciki a sanyaye, kwanciya tayi kan kujera gaba daya ta rasa me ke
mata dadi, bayan kusan minti talatin Mujaheed ya sakko ya kunna Tv ya xauna parlon,
Juya masa baya Imaan tayi ta hade rai ya kalleta ta gefen ido ya ci gaba da
kallonsa, Har aka yi azahar Imaan taki yarda magana ya hada ta da Mujaheed, tana ta
kwance parlor ta juya baya kan kujera, sau biyu yana ce mata ta tashi ta dau Ice-
cream dinta xai yi melting tayi masa shiru, shi ma kuma bai sake ce mata komai ba,
jin ya fita masallaci ta mike a hankali ta wuce dakinta taga har ya canxa xanin
gado ya gyara dakin, bathroom ta wuce ta dauro alwala ta fito ta shimfida darduma,
tana idar da sllh ta sauka xuwa kitchen ta ciro manyan indomie biyu a kwali, ta
wanke tukunya ta kunna gas ta daura ruwa, tana gama dafa indomien ta juye a babban
plate ta fito, xaune ta ga Mujaheed a parlor ya bi ta da ido, ta hade rai ta wuce
sama, ta cinye indomien tass sannan ta kwanta nan da nan bacci ya dauketa. Har dare
Imaan bata sakko ba duk da yunwa da take ji sosai, tana fitowa wanka bayan Isha
taga ledan abinci ajiye a dakin, riga kawai ta xura bayan ta goge jiki ta xauna ta
bude ledan taga jollof ne har takeway biyu ko wanne da babban kaza a ciki sai drink
da bottle water. Sai da ta kusa cinye gaba daya sannan ta mike da kyar ta tafi
bathroom ta wanke bakinta ta fito ta feshe jikinta da turare ta kashe wuta ta
kwanta ta lumshe ido, Bayan kusan awa daya aka bude kofar dakin Mujaheed ya shigo,
tana ji taki juyowa balle ta bude ido, ya karaso kan gadon ya xauna gefenta murya
can kasa yace "Imaan" Shiru tayi bata ce komai ba ya hau saman gadon ya kwanta
gefenta yace "Tell me what ur problem is plss" a takaice tace "I don't have any
problem plss" dagota yayi, ta fashe masa da kuka, shiru yyi yana kallonta, bayan
few seconds a hankali yace "Baki son xaman mu tare har yanxu koh Imaan? To shkkn
har yanxu deal dinmu na nan, give me five kids that look like you, sae in sauwake
maki ki koma gun wanda kika gani daxu kike shareni, but let me tell u this, I won't
tolerate ki dinga min shiru sbda kin ga tsohon saurayin ki, after all ba ni na
hanasa auren ki ba ai, I was home on that very day aka kirani na xo gida aka gaya
min an aura min ke..." mikewa xaune imaan tayi lkci daya hawaye ya kawo idonta tace
"Ehh gaskiya ne baka sani ba aka aura maka ni, but don't forget kaddara ya hana
Sadeeq aurena nasan shi ma ba da son ransa ba, kuma ni nasan har in bar duniya
baxan ta6a samun masoyi na gaskiya irinsa ba, baxan samu me sona xuciya daya kamar
Sadeeq ba, nasan kuma da wuya moment din mu tare yayi fading a xuciyata da wuri, I
will never forget our...." Rikota Mujaheed yyi cikin tsawa yace "Baki da hankali ko
Imaan? Da auren nawa a kanki kike min wannan maganan, da auren nawa kike ce min
baxa ki manta da Sadeeq ba, are you out of ur senses??" Yana huci ya kare maganar,
ta fashe da kuka tace "Why will I forget someone that always say he loves me
innocently anytime, anywhere?? don me xan mance wanda baya shakkar furta min kalmar
so, he always tell me he loves me not he cares, I pray Allah forgive me amma ni
nasan da wuya in samu so irin wanda Sadeeq yayi min a rayuwa kuma..." shiru
Mujaheed yayi yana kallonta da idanuwansa da suka sauya launi, ta goge idonta ta
juya masa baya ta kwanta tana shessheka, Mujaheed ya jinginar da kansa da gado ya
lumshe ido, bayan wani lkci ya bude yana kallonta, dawowa yyi kusa da ita a hankali
ya kwanta ya jawota jikinsa murya can kasa yace "Imaan are you still pretending you
don't know I love you?" Jin tayi shiru ya lumshe ido cikin sanyin murya yace "Imaan
tun baki san kanki ba nake sonki... son da ni kaina ban san irinsa ba, I have loved
you from the beginning and I have always dreamt of living with you as my wife, the
mother of my kids till eternity, Imaan nasan kinsan Ina son ki, son da duk duniya
bayan iyayenki babu mai maki irin sa, baki min adalci ba idan kika ce min baki sani
ba don nasan kin sani you are only playing with my intelligence thinking babu aure
tsakaninmu kamar yanda kika sa ma kanki wannan tunanin, me yasa baki ta6a xama
kinyi naxarin me yasa duk cikin siblings dina nafi damuwa da lamarin ki ba, me yasa
baki yi tunanin dalilin da yasa na mayar dake favourite dina ba, nasan kin san
komai Imaan, shekaru biyu da suka gabata Umma ce ta xama barrier tsakaninmu kika ga
na daina kula ki amma ba wai a son raina ba, sai dai duk da haka kullum kina rai
na, kuma duk ranan da ban ganki ba I will be restless, are you thinking saboda Inna
nake tafiya part dinta in xauna a lkcn? Kina tunanin sbda ita nake xuwa bangarenta?
I am always there because of you Imaan, Ina xuwa ne don kawai in ganki in tabbatar
you are okay, I love you tun baki san kanki ba Imaan, wllh son da nake maki Ina ga
na Ammi kadai ne xai fi nawa, da na rasa ki Imaan da ban san halin da xan shiga ba
duk da a lkcn na ma cire rai da ke, ban ta6a xaton xaki xama tawa ba all of a
sudden, Daren da na fallasa maki sirrin xuciyata ta yanda nake tunanin xaki fahimta
sai kika mayar da ni mahaukaci, kika nuna sam baki gane abinda nake nufi ba baki
gane inda na dosa ba kuma ni nasan kin gane Imaan, it's just that you are soo good
at pretending tun kina 'yar karama, you are perfect in that...." Jin har sannan ta
ki cewa komai yasa mujaheed ya leka fuskarta a hankali, murmushi yaga tana yi, suna
hada ido cikin duhun tayi saurin rufe fuskarta cike da shagwaba tace "Ni bana soo
Yayaa" ya lumshe ido ya rungumeta sosai yace "Plss tell me meyasa dinga wasa da
hankalina kina pretending all those time?" Murya can kasa tace "Because you are
also pretending, kuma kana da girman kai, you too big to tell me kana so na" xaro
ido yayi yana kallonta bai san lkcn da yyi dariya ba yace "In gaya maki ina sonki
ki daina kulani Imaan? komai fa sai kice Yaya ne..." Ta shige jikinsa tace "Toh ni
ban ta6a ganin inda Yaya xai ce xai auri kanwarsa ba sai a kanka" Yana murmushi ya
shafa cikinta yace "Gashi kin gani kuwa, har da result..." turo baki tayi tace
"Kyaleni joor" ya lumshe ido yana shakan kamshin gashinta, a hankali tace "Toh yau
sai ka gaya min inda ka kai min wayar da Sadeeq ya siya min" Yana murmushi sosai
yace "Yana can gida, idan na koma xan kai ma Inna ta dinga waya da shi idan xata
iya" Ta dago kai tana kallonsa tace "Ai nasan kai ka dauke dama wllh" hade bakinsa
yyi da nata... a wannan daren kamar wancan daren da ya xuba mata pill a drink, duk
sai da Mujaheed ya fallasa ma Imaan gaba daya sirrin xuciyarsa da ta riga ta sani
tun ba yau ba take kakkaucewa, Ita ma kuma ta basa hadin kai dari bisa dari fiye da
xaton sa, a daren ita ma kuma ta bude baki tace "I know you are, and will always be
the best for me yayana, nima ina sonka, Ina kuma alfahari da kansancewar ka mijina"
5 years later.....
Imaan ce tsaye bedroom din Umma gaban mirror tana gyara Hijab dinta, Umma ta gama
saka ma wani little handsome dake tsaye gabanta yana mata surutu takalminsa, komai
nasa sak na Mujaheed kamar yyi kaki, babu abinda d'an yaron ya mance na uban nasa,
Umma dai sai kallonsa take tana murmushi don hatta muryarsa kamar Mujaheed dinta
yana karami, tana rike da hannunsa ta nufi kofa jin horn din mota a compound tace
"Kiyi sauri tunda ya fara horn Imaan" fesa turare Imaan tayi ta gyara fuskarta sama
sama ta bi bayan Umma da sauri, Mujaheed dake xaune mota rungume da little sister
din Musaddeeq ya fito motar yana kallon Imaan yace "I told you it's late already
kar mu yi missing flight..." Umma ta hararesa tace "Tunda barin kasar xa ku yi
ba.." murmushi kawai yayi ya shafa kansa, Mai aikin Umma ta iso wajen da jakan
Imaan da kids dinta ta saka a booth, ta koma ta dauko wani jakan ta saka a booth
tana kallon Imaan tace "Mum Ilham Allah ya kiyaye hanya" Imaan na murmushi tace
"Toh Aunty faiza sai mun sake dawowa" Umma na kallon Imaan tace "Inji baku mance
komai ba dai" Imaan tace "Idan ma mun manta Umma wani lkcn sai mu dauka idan mun
dawo" Umma ta dau Musaddeeq tana kallonsa kafin tace komai ua manna mata kiss a
goshinta yana murmushi yace "We are going to miss you granny" Dariya tayi tace "I
will miss you more sweetheart ka gayar da old woman da grandpa and grandma a gida
ka ji?" Gyada mata kai yayi ta sa shi back seat, ta amshi Ilham dake hannun
Mujaheed tace "Teemah will be staying with me" Mika ma imaan hannu yarinyar tayi da
sauri tana 6ata fuska xata yi kuka, imaan tayi dariya tace "Baxa ki xauna gun
granny ba..." Umma ta saka ta cikin mota tana dariya tace "Allah ya kiyaye hanya, a
gaida kowa da kowa a kaduna" Driver ne ya taho wucewa da su airport din, Mujaheed
ya shiga motar bayan ya kara yi ma mahaifiyarsa sallama Imaan ma tayi mata sallama
sannan suka bar gidan. Satin Imaan biyu kenan a kano wajen Umma da kids dinta, jiya
Mujaheed ya taho daga kaduna mayar da su gida, Shekaru uku da suka wuce Umma ta
koma kano da xama gaba daya, yanxu fita take Dubai duk bayan wani lkci, business
take sosai wanda cikin kankanin lkci ta fara tara abun duniya bbu abinda ta rasa,
Rahma kadai ce gabanta har lkcn bata yi aure ba tana karatu amma Ummi tayi aure da
Maimoon 2 years back. Cikin lkci kadan suka shigo garin kaduna a flight, duk inda
Mujaheed ya bi da little Ilham mai sunan Inna sai an tanka ta don kyakkyawa ce
sosai yarinyar gashi kwata kwata bata son mutane, Ammi kadai take makale ma don har
suka gama xama kano bata wani yadda da Umma, Suna fitowa daga cikin airport kamar
ance Imaan ta waiga ta ga Sadeeq yana jan trolley yana danna waya da alama saukansa
kenan kasar don ba waje daya suka fito ba, da sauri ta dauke kai don bai ganta ba,
Mujaheed dai na waya yana rungume da Ilham, Ita kuma Imaan tana tafe tana jan
trolley Musaddeeq na rike da hijab dinta a gefenta, tuntube yayi da trolley din
hannunta ya fadi wanda hakan ya ja hankalin mutane da yawa ciki har da Sadeeq, bai
yi kuka ba yaron Imaan ta sake jakan hannunta ta dago sa da sauri tana ce masa
sannu, Kallonsu Sadeeq ya dinga yi, bai san lkcn da yace "Imaan" juyawa tayi ta
kallesa da sauri, Mujaheed ma ya juya da sauri jin an kira sunanta, Sadeeq ya
nufeta yana murmushi yace "Waow is this ur son Imaan??" ta kirkiri murmushi ta
gyada masa kai, daukan Musaddeeq yayi ya rungumesa ya manna masa kiss a goshinsa
yace "He is soo cute, ya sunansa??" Tana murmushi tace "He is Abubakar Sadeeq"
Sadeeq ya kara rungumesa yace "Ohhh takwara na kenan, where is his dad?" sai a lkcn
ya ga Mujaheed dake kallonsu shi ma, Sadeeq ya nufesa still smiling ya basa hannu,
nan suka gaisa yana kallon Ilham ya ja Cheeks dinta yace "Waow little imaan kenan"
murmushi kawai Mujaheed yyi yana kallonsa, Sadeeq yace "It's been long, over five
years yanxu...." mujaheed yace "Sure, where are you coming from" Sadeeq yace "I am
coming from Uk now, ya Kaka?" Mujaheed yace "Tana lafiya lau" Sadeeq ya shafa kai
yace "Xan dai je in gaisheta in sha Allah Maryam ta bani sako in kawo mata, you
know we are not far from each other a can UK, driver ya xo daukan ku ne?" Mujaheed
yace "Not at all, xa mu hau taxi" Sadeeq yace "Driver ya taho min da mota yanxu,
muje sai mu yi dropping din ku" Har kofar gida Sadeeq ya ajiye su bayan ya siya ma
Musaddeeq bindiga na wasan yara a hanya, Ilham kuma ya siya mata babban doll, Imaan
na kallonsa tana murmushi tace "Baxa a hadani da Madam muyi xumunci ba?" Shafa kai
Sadeeq yyi yace "Madam... tukunna dai in sha Allah" Imaan ta xaro ido tana kallonsa
da mamaki, yace "Ko xa ki sama min madam din?" Dariya tayi ta sauka motar tace "Ni
kuma" Sadeeq yyi murmushi yana kallon Mujaheed yace "Ae gaskiya ne, ko in jira
little Imaan kawai?" dariya Mujaheed yyi yace "Lkci dai na ta wucewa Sadeeq, try
and settle down" Sadeeq yyi murmushi yace "In sha Allah, A gayar min da Kaka soon
xan shigo" A haka suka rabu da Sadeeq, Tun da suka shiga compound duk da Ammi dake
tsaye tana shanya Musaddeeq bai bi ta kanta ba ya nufi part din Inna da gudu yana
kwala mata kira yana cewa "Old womannn, old womannn, where are you" Ammi ta bi sa
da kallo tana murmushi, Imaan ta sauke Ilham ta nufi Ammi da gudu tana murmushi
dimples dinta na lotsawa Ammi ta dauketa ta rungumeta, Imaan ta karasa ta rungume
Amminta tayi mata kiss a goshi tana murmushi a hankali tace "Nayi missing dinki
Ammina" Inna da ta fito da duk kwanukan kitchen dinta da tukwane bakin pampo xata
wanke wai sun yi k'ura ta daga kai ganin Musaddeeq tace "Waye kuma wannan?" ya
kyalkyale da dariya ya saita mata bindiga har da kulle ido daya, xaro ido tayi tana
kallon bindigan da yayi kama da na gaske daga nisa, da gudu ta shige parlonta
jikinta na rawa tana cewa "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un, Mujaheed ya haifi
jaraba" Mujaheed da tahowansa kenan ya dinga dariya yana kallon son din nasa da ya
bi bayan Inna da gudu yana cewa "I missed you old woman...."

Documents By AIHAUSANOVELS

Always visit Aihausanovels.com.ng For downloading free hausa novels

Like our Facebook page Fb.me/aihausanovels

*Ina mai sake jaddada cewar littafin Imaan ba free bane na kudi ne* settle ur debt
it's just

it's 300 via


Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

07087865788

I want to draw the attention of those posting my books that are not free on
Facebook, ku ci gaba xa mu hadu gaban ubangiji in sha Allah...

_Toh Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah😃 a nan na kawo karshen littafina me


taken *Imaan* kurakuran da nayi a ciki Allah ubangiji ya yafe min, darussukan dake
ciki kuma Allah ubangiji ya sa mu amfana da shi_
Na sadaukar da littafin nan xuwa ga beloved brother na Yahya M Bello, Allah
ubangiji ya raya min kai little bro, ya albarkaci rayuwar ka ya sa ka xamo apple of
our parent eyes... Gaisuwa ta musamman xuwa ga mahaifiyata Hajiya Hajarah, she is
my first, my world, my role model, my everything Allah ya bar min ke Hajjaju Yaya,
Allah ya kara maki lafiya ya karo arxiki mai albarka, my siblings Ahmad, Maryam,
Fatima, Baby, Haiydar, Papi, Ilham, Fadil, sudais, Jamcy, Humairah, Aneesah,
Mujaheed, Big Ilham, Yusuf, small Baby, And my takwara Khaleesat, Allah ya
albarkace ku gaba daya, Ina son ku har raina, Small Mum Aunty Rukky thanks for the
encouragement from the beginning of this book till the end Allah bar min ke ya
daukaka ki, my Aunty Didi ur daughter jiddo is greeting with respect Allah ya
ubangiji ya jibanci lamarrukan ki, Hajiya Inna Allah ubangiji ya bar mana ke mu ga
me taka 'yan jikokin ki a duniya, Muna alfahari da kasancewar ki grandma dinmu.
Hajiya Sadiya Chamo😉 Hafsat Oum Ilham, Ummu Zainab, Anty Ay(Ummu Lailah) Hajiya
Asabe, Hajiya Fauziyya fiji, Mama Dutse, Khaleesat Haiydar na gaishe ku gaba daya
with respect, Allah ubangiji ya raya 'yan kannena ya albarkace su, All the members
na payment groups dina guda bakwai da nayi creating for the book Imaan, Ina
gaisheku Ina maku fatan alkhairi, Ina alfahari da ku for patronizing me, Allah ya
bar xumunci ya kara maku budi, members na murmushin novels da Seembieluv groups ina
godiya da kauna, and finally my fans... words Alone isn't enough to express my
feelings toward you guys, Ina son ku sani a ko da yaushe Ina maku fatan alkhairi,
Allah ubangiji ya sa mu gama da duniya lafiya Ameen.
Taku har ko da yaushe Khaleesat Haiydar (Hauwa Bello Jidda)
Na bar ku lafiya✍🏻

Tohm Ina masu neman cream da xai gyara masu jiki, su yi kyau suyi haske suyi ta
glowing 😉 da masu fama da sunburns, da strong palms... to maxa ku garxayo ga wani
product that is tested and trusted I am assuring you guys.... Xa ku iya tuntuben
wannan number in sha Allah. 08038103096.

108.....

You might also like