You are on page 1of 91

Compiled By Umar Dalha Funtua.

🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
🏼🏼🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko yar'duniya?*‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍

*Dukkan yabo da godiya ya tabbata GA Allah S.W.A daya Kara dawo dani a lokacin da
banyi tsammanin Kara dawowa ba kasancewar banida isashen lokacin kaina tun rubuta
littafi na na karshe N@g@ TA K@IN@ Wanda akalla yanzu kusan shekara daya koma
fiyeda haka, Gani na Kara dawo muku da Takaitaccen labarin da baida yawa Wanda
cikin 70% yafaru da gske ina fatan zai amsu a makaranta kamar yanda kuke amsar
littafina shima a karbe shi hannu biyu biyu*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah Amaryar gobe😍*

Damko gashin kanta yayi yayinda ya Kara gwara shida bangon bayin a karo na biyu
cikin wahalalliyar murya take ihu hawaye masu zafi nabin fuskarta, kazamar banza
yar'iska ragowan Gayu Dan ubanki maina gaya miki kafun inbar gidan nan? Juyo da
fuskarta yayi yayinda ya daga habarta matse bakinta yayi cikin masifa ya hankado ta
wajen bayin saida ta buga kanta da kujerar dressing mirror take kan nata ya shiga
zubda jini, kasa jurewa tayi jin azaban take har cikin kwakwalwarta hakan yasa ta
Saki ihu tareda tsugunnawa tana murza hannayanta biyu Alamar hakuri, 'Dan girman
Allah AK kayi hakuri na tuba nabi Allah nakuma bika mijina ka yafe mun, takowa yayi
har inda take yayinda take matsawa baya saboda gudun azabar dazai Kara manna mata,
damko gashin kanta yakara yi tareda janta a kasa har bakin gadon dake dakin ya
zauna yana ware kafafuwan shi duka biyu, fuskarta datayi jaga jaga da jini da
majina yakara dagowa hadeda kai fuskar shi saitin bakinta cikin magana kamar rada
"fadi Laifin ki da bakinki ina jinki, hannu yasa yana dangwalo jinin dake bakinta,
" yinwa nakeji, 'tafadi dukda sanin yasan da hakan saboda kulle kitchen dinda
yakeyi idan ya shirya mata babban azaba.
shiyasa gakuma zazzabin Dana kwana dashi tun shekarun jiya rabona da
Abinci....'shiiiiii ya katse ta yana lumshe ido tareda jefa mata banzan kallo cikin
kyama, shiyasa kika samu damar kwanciya harda bcci bayan baki gama wanke mun
motocina Dana Saki ba?? Shegiya mayya duk uban abincin Danake kawowa gidan nan
bakida aikin yi saici kamar jaka, ooh jakar cema na tuna, yafadi yana jijjiga
kanshi, jakar titi, jakar maza, u fat for front u fat for back Bakida wani amfani
rashin Asali baiyi ba wlh saidai kici kiyi katon kashi kita cika mun Masai da wari
koh? Dama abunda yasa kika Aure ni kenan, nikuma baiwa na Auro banga mata anan ba,
ya nuna ta da yatsa harda dungure kanta Toh dole ki rage shegiyar kibar nan bazan
Gina ma wani kato jikin kiba Danni kozaki kwana kina yawo tsirara baki burgeni so
dole kifara rage tsoka Hahahaa yayi dariyar da bata wuce kalma Uku ba, "kinyi karya
wlh tunda kika hanani farincikin rayuwata a haka zamuyita Rayuwa a gidan nan babu
Wanda zai samu abunda yakeso nida ke sai karyan ustazanci Allah a baki fir'auna a
zuciya, yafadi tareda tureta kasa, mayya mai nacin maza mai fuskoki dayawa ugly pig
kawai, barin dakin yayi tanajin fitar motarsa daga gidan hakan yasa ta zube a kasan
tels din dakin hawaye masu dumi nabin kumatun ta, 'Ashe laifi ne a duniyar mu yin
biyyar Aure? Laifi ne tsarkake zuciya tareda Soyyah mai tsafta? Yazama laifi tona
asirin zuciyarta?
Cike da nadamar rayuwar Tata ta Mike tana Jan kafarta dayayi mata tsami bayi ta
shiga ta sakarma kanta ruwan zafi hadede gasa jikin nata kodata fito man zafi ta
nema ta malka ma jikinta bata daddara ba takara bin lafiyar gado a karona biyu
dukda tasan kotayi aikin daya sata ko batayi ba saiya samu dalilinda zai Kara
jibgarta anjima garata kwanta saiya jibgeta da tushe.

Azabar yinwa neya tashe ta misalin biyar da Rabi na yamma gashi ko sallar
la'asar batayi ba dakyar ta rarrafa tayi salla cikin zullumi tareda Addu'ar Allah
yasa ya bude mata kitchen din jinta takeyi kamar zata mutu saboda azabar yinwa jiri
na dibanta ta dakyar take iya bude idonta daya kumbura fuskar nan tayi suntum
tareda dafa bango ta karasa kitchen tunkafun ta karasa ta ganshi a bude wani dadine
ya ziyarce ta lokaci daya ta tattaro ragowar karfin jikinta kai tsaye fridge ta
nufa tasan bazata rasa abunda zata faraci ba

Ur comment is needed saboda samun kuzarin typing.

Mr's Sadik Rumah💅🏻


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah, my sister yar'amana Amaryar gobe😍ina yinki kanwata


irin totally dinnan😎*

Tana budewa tayi ido biyu da ragowar biredi bata damuda sanyin shiba ta barka ledan
lodawa takeyi hannu baka hannu kwarya hartana shakewa wurin fanfo ta nufa dukda
akwai ruwa burjik a cikin fridge din budewa tayi tareda kafa kanta kamar
mahaukaciya ta dinga kwankwadar ruwan Rabi nabin jikinta tana kara tura buredin
dukta jika jikinta, saida tafara dawowa natsuwar ta sannan ta dauko Karamar tukunya
ta dora ruwan shayi saboda tana bukatar Abu mai dumi a cikin nata, kamar ance ta
kalli gefen dirowan kitchen din tayi ido biyu da manya manyan ledoji har guda Uku
da farar takarda a kansu, sauri sauri ta karasa wurin
*sakwara da miyar Egusi, ferfesun kaji Dana kan Sa, dankali a soya da kwai,
fresh coconut juice da Fruth salad kunun gyada na shinkafa is needed at 8pm.* wani
murdawa cikinta yayi kafun kace kwabo ta yarda takardan bayi ta nufa tadunga
kwarara amai saida ta amayo duk abunda ta loda tasan dadewa datayi ba abinci shiya
jawo mata aman gashi kuma batayi cin hankali ba, cikin hanzari tagama ta gyara
wurin kitchen ta nufa tana salati da kwallar tausayin kanta Dora hannuwanta duka
tayi akai tareda tarin danasanin komawa bccin datayi, dabata komaba da yanzu taci
karfin aikin tunda karfe biyu yabar gidan, da gudu tafito da kansa Wanda yayi
kankara dauraye shi tayi dayake ta wanke tsaf sanda aka kawo prejar pot ta dauko
nanda nan ta markada kayan miyan dazatai amfani dashi harda na kajin hada komai
tayi tana neman agaji wurin Allah tasan yau kashe tane kawai AK bazaiyi ba, sauke
ruwan shayin data Dora tayi batashi take ba yanzu yayinda ta Dora kansa din akan
gas jawo ledojin daya kawo tayi ta fito da kaji guda biyu GA dukkan Alama Abokan
shi zasuzo cin abincin gidan tasan idan Dan tashi ne bayacin girkin ta sai wani
ikon Allah, gyara kajin tayi ta hada komai da komai ta Dora, kallan lokaci tayi
taga shida harta gota nan takara rikicewa tunowa datayi har sakwara zatayi ga firan
dankali

♀ ‍♀ 🙆🏻‍😭
Ga kunun gyada dukda sunada soyyar markadadden gyada a fridge tana
tanada saboda irin hakan, but aikin yamata yawa koda yake dama jakar shi ce kamar
yanda yake cewa, haka taita aikin sauri sauri har tana konewa damai a hannu wurin
soya dankali saboda rawan jiki bata damuda azabar dazata Shaba akan tijarar dazai
mata a gaban Abokan aikin nashi, dukda ba bakon Abu bane suma a wurinsu duk Wanda
mijinta ke kawowa gidan yana sane da cewa batada bambanci da banza, daza'a iya
shiga kwakwalwar kanshi a shiga tunanin shi sauron🐝 dake yawo a gidan yafita
muhimmanci Kota banza zai hanashi bcci da kuka, kallon lokaci tayi taga takwas
saura kwata ko magrib batayi ba salati ta saka Dan sai a lokacin zata daka sakwara
dukda tagama komai miyar neya rage ta karasa da coconut juice din, tana cikin
dakawa taji dawowar shi gidan tareda hayaniyar mutane Alamar bashi kadai bane kamar
yanda tayi zargi.
Cikin mintunan da basu wuce biyar ba taji taku Alamar za'a shigo kitchen din
yayinda take kulla sakwaran a Leda dukta hada zufan gajiya, 'kallon kitchen din
yakeyi a wulakance yayinda zuciyar shi ke Kara suya ji yakeyi kamar ya fusge
tabaryar dake gefenta ya sata a turmin yaita kirbata Kila zai huce takaicin data
sakashi
Naa...naaaa kusan gamaawa bari infara jera abincin a Dinning, tafadi cikin
rawan jiki baiko ji karshen maganar Tata ba banda ta raina shi tun yaushe yabar
gidannan? Lallai rainin nata gaba gaba yakeyi shikenan bai isa da gidan shiba? Mai
Aisha take nufi Dashi? Laifin shine data fara ganin gadon bccin shi shekara Uku da
Auren su amma har'yau bata bin umarnin shi? Komawa yayi tafkeken parlon nasu inda
yabar bakin nasa su shida, Abincin data gama tafara jerawa akan dining table dinsu
yayinda takoma kitchen domin jiran miyar Egusin yakarasa.

*More comments more typing😏*

*Mr's Sadik Rumah*💅🏻


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼

🤷🏻‍🤷🏻‍🤷
♀‍♀‍♀ *Ustaziya
🏻‍ ko yar'duniya?‍♀‍♀‍♀ *

*Written by Anty Mamie*

Masha Allah tun a page din farko naji dadin comments dinku shiyasa nayi page biyu
yau nima domin faranta muku, ina yinku yan Group Dina *Anty Mamie's Novel Groups*
irin sosai dinnan🤩

*Dedicated to sister Husnah.*

Mama na shirya zan tafi haddan, tafadi tareda daukar jakar makarantar ta, "toh Auta
har'zaa tafi ooh Allah dai yaimiki Albarka diyar nan wannan San karatun nan naki
har mamaki yake bani halima saikace Al'huda huda maza maza a tafi kada a makara
aita kwararo hadda, tafadi tana miko mata Naira dari a dunkule, Amsa tayi hade da
godiya tana gafda fita gidan taci karo da babanta ya shigo, " baban mu saina dawo,
toh uwata Allah yabada Sa'a saikin dawo idan kin dawo saiki kulle kofar gidan da
kwado kinji koh? Nasan kafun nan munyi bcci Yafadi tareda miko mata takardar Naira
dari shima, toh 'Baba ta Amsa cikeda murna harda sunkuyar da kanta kasa.
Misalin karfe bakwai na Dare ta fito daga gidan Budurwa ce yar'shekara sha'bakwai
cikin katotan hijab dinta dayake sharan titi tasha Safar kafa da hannu baka iya
ganin komai nata sai farin kwayar idonta, tafiya take kamar mai tsoran taka kasa
kallo daya zakai mata kaga tarin natsuwa da kamun kai, yarinya abun kwatance a
cikin dukkan unguwan nasu duk Wata uwa da zatai ma diyarta fada tohfa da halin
halima ake kwatance kowa ya shaida halima wurin natsuwa halima ce burin kowace uwa
a unguwan dattawa da iyayen unguwan kowa nama dan'shi Sha'awar Auran halima saboda
yanda gidan nasu yake gidan malamai babanta ne limamin masallacin unguwan yayinda
Mamarta takeda tarin ilimin Addini shiyasa yan gidan nasu suke cikeda natsuwa.
Tafiyar minti goma ne daga gidan nasu zuwa wurin haddar kodata karasa
sainaga harta wuce makarantar tasu ta tsallake babban titin dake gaban makarantar
duk a tunanina ko biro zata siya😕sainaga ta bude bayan Wata shegiyar farar
rangerover 2016 ta kame a ciki saikace ta tsohon ta, batare da bata lokaci ba aka
cilla motar akan titi cikin kwarewa koda na leka motukin motar macece mai tukin,
Yammata biyu ne a gaban motar cikin Wata shegiyar shiga kamar wadanda suka zo daga
America a cikin Daren saika rantse da Allah musulunci baije musu ba idan kayi
la'akari da kayan dake jikin nasu, 'leemah kin bata mana time fa, inji Wanda ke
tukin motar, 'sorry meena abun ne saida siyasa kinsan iyayen namu sai a hankali
Ummi nake Dan lallabawa saboda hawan jinin ta danta dagus banda matsala yaci
lokacin shi, tafadi tana zame hijab dinta tareda Jan tsaki, bari in cire wannan
buhun dukya dumama mun jikina mtseww, vest ce Mara hannu iya Mara tareda guntun
wando a jikinta, "yah club din zamu wuce direct koh? Wacce take gefen Direver ta
tambaya, noo nooooo feenah r u kidding me? Take a luk at me please saina watsa ruwa
sai zufa nakeyi and I need to change my clothe.

Unguwa ne na masu hannu da shuni motar ta dumfara horn naga tayi a wani katotan
gida madaidaici, bude gate din gidan wani buzun mai'gadi yayi, wuri ta naima tareda
ajiye motar suka furfuto cikin takun kasaita leema kuwa tuni ta nunke hijab dinta
ta Danna cikin jakar islamiyar da babu komai ciki sai kayan maye da kayan kwalliya,
a mota tabar jakar sanin tanada duk abunda take bukata cikin gidan, wow cikin gidan
yafi wajen gidan haduwa nesa ba kusa ba saidai wani abun mamaki gidan babu kowa sai
Yammata Uku da suka shigo yanzu, cikin gaggawa ta fada hadaddan bayi tareda sakar
ma kanta ruwa tanayi tana waka fitowa tayi zigidir haihuwar uwarta dukda towel
dinda ke bayi I'lla Dan karami data rike a hannun nata tana goge jikinta tana wakan
"cilindion mai taken Am Alive" kawarta meena ceta buga mata duwawu nan suka hau
wasan banza babu kunya a haka harta gama shiryawa nan take ta rikice daga diyar
musulmai takoma leemah sak, Yar'malam taki halin Malam, kawayan nata suka furta
cikin shewa suna jinjina mata ganin yanda take karairaya a gaban madubi, "da karatu
gwanda rawan disko tabasu amsa tareda Juyowa tana girgiza kirjinta Wanda babu
abunda ba'a gani ko bra batasa ba.

More comments more typing.

*Mr's sadik Rumah*💅🏻


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah*

Koda suka isa club din suna shigowa aka fara bude musu hanya anga dakin hutu sun
shigo Wanda hakan ne taken nasu, wani baki dogon saurayin dake zaune kallo daya
zakai mai kasan babban yaro ne kusan minti talatin da shigowar shi wurin barasa
yake sha batareda kula kowa a wurin ba da alamar jiran zuwansu yakeyi ganin ya Mike
lokaci daya ya dumfare inda suke batareda bata lokaci ba cikin kwarewa ya ruko
kugun leemah tsaf ta lafe a kirjin nashi tana shafawa da hannun hagu basu ko damuda
yawan mutanan dake wurin ba, saitin kunnanta yakai bakinsa tareda furta mata
*Ustaziya koh Yar'duniya*?
Lumshe ido tayi cike da duniyanci ta chapko lips dinshi na kasa ta shiga tsotsa
harda Dan cizon shi Sannan takai bakinta saitin kunnan shi yanda zaiji abunda
zatace *Duniya gidan kashe ahu tun kuruci bai wucemu ba* tureshi tayi tana juya
kugu ta nufa wurin da aka killace saboda shan hayaki tahau busawa cikin kwarewa da
wayewa ta hanci ta baki kamar yanda sauran frnds din nata keyi su a ganinsu kananan
chicks neke rawa a club sudai kawai suji sun hau saman gajimare sujisu a duniyar
sama yauwa shine magana Alhaji.

Hayaniya ke tashi a parlon Abokanan keta zuba fira AK kuwa sai kumbura yakeyi ganin
har 8:30 babu miya ba Alamar Sa dukda komai da komai na wurin kowa nacin abunda
yake Sha'awa sunata zuba santi,bakinta rike da sallama shigowa tayi da kular miyar
cikin natsuwa kanta da katon mayafi ta yafa, Amsa sallamar dukansu sukayi banda oga
gaishe su tayi cikin sakin fuska suka amsa yayinda take Allah Allah ta ajiye tabar
wurin "madam sannu da kokari wannan girki haka shiyasa AK kewani kiba yayi fresh
abunshi gskia Abokina kayi sa'ar mace zan turo madam dita a Kara hora mun ita gurin
girki inji Abokin shi Musa Wanda dama yasaba zolayar ta, murmushin dabai wuce
bakinta ba tayi ganin yanda gogan yakara hade Ranshi kamar hadari saika rantse baya
wurin, hannun shi rikeda da kofin mug dinda yakeshan kunun gyada sai girgizawa
yakeyi kamar baisan da halittar ta a wurin ba dayake kusa dashi take tsaye ta juya
kenan zata bar wurin ya Saki kofin cikin rashin Sa'a tayi saurin matsar da kafarta
aiko ya tarwatse a kasa yayinda takaici yakara cika shi domin a kafarta yaso ya
tarwatse duk Wanda ke wurin sunga abunda yafaru kowa yayi shiru yana kallon shi ba
halin magana yahau ruwan masifa, barin wurin tayi cikin hanzari ta dauko tsintsiya
ta kwashe tareda goge wurin kamar yana jira tabar wurin yabita kitchen din ta zauna
kenan tanacin abincin ta akan kujerar kitchen din, a kanta ya tsaya yana Kare mata
kallo, " miyar Egusi dinda ke gabanta ya dauka yana jujjuyawa a hannun shi aikuwa
yafara juye mata a jikinta a Hankali harya gama Tass, ferfesun kan Sa ya dauka
Wanda tadan zuba zata sha, batareda bata lokaci ba ya daga shi harda murmushin
mugunta jin yanada zafi sosai a kanta yafara zubawa da gudu ta tashi daga zaunen ta
matsa gefe jin azabar da kanta ke mata rokon shi ta shigayi yayi hakuri karya Kara
tozartata ta gwammace yaimata su kadai a gidan, "wannan ne kike kira miyar Egusi?
Eye? Dan mugunta saikace kashin jariri? Babu abunda kika iya sai jawo hankalin yan
iskan kwartayan ki nothing baki iya komai ba sai tarin iskanci da munafunci mai
fuska biyu bakar munafuka, Please! please!! Am sorry I did my best, " oooh this is
what u called ur best swt wiffy? Kureta yayi a jikin bangon miyar dake jikinta ya
lakuto yayinda ya murza mata akan ciwon dayaji mata a baki kafun ya fita, well make
sure kin cinye komai kin kuma gyara wurin nan cox niba kazami bane kamarki bazan
dauki Albazaranci ba, yafadi yana cusa mata katon sakwaran daya yanzo a hannun
shi, 'hannu ya wanke a fanfo sannan ya wuce parlor kamar Wanda akaima bushara da
gidan Aljannah, saikace bashi ke cika yana batsewa ba nan ya zage sukaita fira da
frnds dinshi daya cikasu da mamaki bakaramin Abu kesa AK dariya ba sai washe hakora
yakeyi harda zuba sakwara da Egusi tunda yaga tanaci a kitchen kanshin ya dame shi
sai hadiye miyau yakeyi nan ya zage ya kwasa girki yana buga santi da shewa, Aisha
kuwa bakinta ta toshe hawaye nabin kumatun ta maiyasa take kuka? Abunda muguntar
shi yagama bin jininta ta rigada tasaba Duk abunda yake mata bata taba jin tsanar
shiba ko kadan takaicin ta kenan, "shegiya zuciyata maiyasa zakimun haka??
Laifin maina miki kike gasani tareda horo mai tsanani? Duk cikin azabar dazaki gana
min maiyasa zaki samun soyyar maso wani? Soyyar abunda baida makiyi bayan ni?

*Mr's sadik Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?*‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah*

Maiyasa? Bakimun Adalci ba duk kece kika jamin maiyasa kika zabi Sani cikin rayuwar
kunci? Maiyasa kika zaban min bauta fiyeda yancin kaina? Kuka takeyi tana cusa
sakwaran dayasa mata a baki jijiyoyi dukya fito rado rado a goshin ta, tabbas babu
abunda batayi ba domin yakice AK a zuciyarta kodan ta kwato ma kanta yanci ya
zatayi? Cikin soyyar shi ta girma a cikinta take Rayuwa tun bata mallaki hankalin
taba kuma shine sanadin komai shine mugun daya cusa mata soyyar shi cikin mugunta,
shiya sata tafara sanshi cikin ruwan sanyi Abun dake Kara mata takaici bafa shi
bane Autan maza but why?? Why him? Da mutum Nada yancin ganin zuciyar shi babu
abunda zai hanata hukunta Tata zuciyar a karo da dama, inama zata iya damko
zuciyarta data nakada mata duka Kota samu sanyin takaicin data sata, tarasa dalilin
maiyasa zaiga Laifin ta maiyasa? Maiyasa shi kadai ke tuno mata da ciwon datake
burnewa a zuciyarta? Wai har yaushe? Har yaushe zai manta abunda yafaru? Nanda
shekara biyu? Ko biyar? Kokuma goma? Kosai bayan yazama Ajalin ta? kirjinta take
bugawa saitin zuciyarta hakan yasa ta zauna sosai tanacin sauran abincin nata koba
komai ya kamata ta rayu domin AK tasan bazata taba daina sanshi ba but tasan Allah
bazai barshi ba tanaso taga sakayyar azabar dayake gana mata tanaso taga yana kukan
jini, but ta yaya? Dazata iya ramuwar gayya da tanada yanda zatayi ta cusa mishi
Santa kona Wata Daya ne tabbas babu abunda zai hanata daukan fansa, kila nauyin da
takeji a kirjin ta ya ragu tanaso ta koyama kanta kinsa tanaso tayi fito na fito da
zuciyarta ta shirya damarar kwatan yancin kanta tun kafun ya kashe ta da kanta,
idan banda bakar talauci da tuni ta bar gidanshi koda gari babu suger ne takoma
gaban ummin ta saidai kuma wani nauyin zata daura musu ganin da ita suka dogara
koba komai idan zaiyi tafiya yanadan barin mata kudi masu tsoka shi take aika ma
iyayan ta suna Kara chefane kai koma ta koma Mayyar bazata barta cikin kwanciyar
hankali ba"zuciyarta" Dan itace weakness dinta but komai lokaci ne tana kuma
Addu'ar sauki wurin Allah. Tanajin bakin nashi sunbar gidan da alamar yaje rakasu
ta Mike da hanzari ta nufa dinning din as expected kuwa taga Envelop jiki na rawa
ta dauka kamar yanda take tsammani kudi ne shake a cikin Wanda a rubuce yake duk
Randa Tai musu girki haka saisun bar mata gudin kuma AK baitaba hanata ba dukda
tasan baida abunda zaiyi dasu, har so takeyi suzo saboda kudin ba karamin taimaka
mata da iyayan ta yakeyi ba haka ta tattara komai a gurguje ta gyara ko'ina gudun
kada mugun ta yadawo ya sameta, kamar yanda take cemasa Farin muguna,
Daki ta shiga ta garkame mukulli dukda a banza Wata rana idan ya daka mata tsawa
da kanta take bude mai ya jibga na jibga, wanka tayi tareda gasa jikinta tayi
salloli da doguwar Addu'a tabi lafiyar gado dukda taso tashi takai ma Allah kukanta
cikin dare amma gaba daya jikinta tsami yakeyi wurin 11 yashigo gidan baibi ta
kanta ba ya shiga dakin shida AC yagama jikawa yahau lallausan gadon shi nan danan
bcci yayi awon gaba dashi.
Ajiyar zuciya ta Saki jin rufe kofar shi Addu'a tayi ta shafa nan bcci yayi awon
gaba da ita ko motsi batayi saikace gawa

Sai wurin karfe uku na Dare unguwan tayi tsit bakajin motsin komai saboda Dare daya
tsala Ustaziya aka ajiye a Wata bakar mota tasha tint baki sidik bakin Saurayin ta
datake jida shi mai suna mahuta shiya dawo da ita dukda tanada su dayawa but ajin
mahuta daban ne shiyasa duk Wanda ya Santa a harkan yake mata kirari da suna *Ajin
hutu* ita kuma ta amsa *Sai hutu* cikin zumbulelan hijab dinta Saurayin ya maidata
bayan sun raba Daren nasu cikin kazantacciyar hanya kudi ya cika mata taf a Jakarta
Wanda bata wani Abun Arziki sai gyaran jiki da magungunan mata mahaukata masu
shegen tsada da kudin halal ne tabbas data ajiye kadarori masu tarin yawa dukda
account dinta shake yake da kudi Dan bata Karamar harka, amma dayake abun sai a
hankali a banza suke karewa, saitin kunnan shi takai bakin ta tareda cizon shi
kadan a kunnan tana lasa, *"ka goge mun hadda ta tayau mahuta* mai kakeso incema su
malam idan suka Sani tilawa? Kice musu ajin hutu kikaje, yafadi yana Kara jawota,
ture shi tayi sanin idan ta biye mishi wasan zai Kara chanza salo, rufe kofar motar
tayi tareda lekowa ta window motar ta furta, *sai hutu* gida ta shiga ta Danna musu
sakata a hankali inda Allah kadai ke tsare iyayan nata daga barayi da masu yankan
kai Dan wani zubin gafda asuba ake direta kuma basa taba Sanin tadawo bata dawo ba
sudai sunsan tatafi hadda, wuce dakin iyayen tayi sai zuba munshari sukeyi hankali
kwance dakinta ta shiga tana Dan rangaji Dan bata gama matsewa ba, karamin bayin ta
dake dakin ta shiga ta watsa ruwa ita kanta tasan tashi takeyi saboda tsaro,
tafito tabi lafiyar gado babu sallah bare salati dama sallar ta ganin ido takeyi
tafi ganewa ta jerosu lokaci daya direct kamar na kwana biyu haka.

*More comments more pages*

Mr's Rumah ce💅🏻


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?*‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍

*Written by Anty Mamie*

*Ina matukar jin dadin comments dinku na Sani nishadi tareda karamun karfin Typing
ashe haka AK keda bakin jini😂 Dan Allah ayi mishi A hankali babu ruwana idan kuka
hadu da fushin Aisha. Anty Mamie's Novel Group 1and 2 ina yinku sosai sosai😍
godiya mai tarin yawa fans Dina Wanda na Sani dama Wanda ban Sani ba ana tare.😍
👌🏻*

*Dedicated to Sister husnah*

Washe gari yakama ranar Wednesday hakan yasa halima ta tashi dakyar wurin 6:30
domin shirin zuwa makarantar Boko a lokacin SS3 take suna shirin jarabawar karshe
kuma tana gama secondary school tabbas Aure babansu zai mata kassncewar basa karatu
mai zurfi na Boko.

A' gurguje🤨
*Wacece halima?*

Isma'el Wanda akafi Sani da Malam liman shine mahaifin halima tareda Ma'haifiyarta
Raliya wacce suke kira Mama, dukkan su yan Asalin kauyan Rano ne dake jahar kano
Auren zumunci ne tsakanin iyayan nasu Wanda a tarihin gidan nasu tun kaka da
kakanni masana Addini ne gaba da baya Allah yabasu ilimin Addini sosai abun saiya
Zama kamar gado hakan yasa suke Auratayya tsakanin su, Malam liman na zaune a
unguwan sabon gari cikin garin Kaduna ne tareda iyalan shi cikin rufin asirin Allah
dukda bawata sana'a yakeyi ba I'lla iyaka duk juma'a manyan masu kudi dayan kasuwa
suna daukar karatun Dare a wurinshi anan babban masallacin unguwan nasu bayan
sallar isha'e kuma yana samun Alheri sosai daga wurin nasu sannan shine limamin
unguwan duk Wata matsala inta taso a sabon gari tohfa shawarar Malam liman ake
dauka kaf unguwan ana ganin mutuncin shi fiyeda kima, Allah ya azurta shida yara
hudu rak a duniya maza biyu mata biyu, Aliyu shine Babba Wanda Dan kasuwa ne yana
Aure da iyalan shi a Kano kuma yana taimaka ma iyayan nashi sosai da sosai, sai
tasi'u shine na biyu Wanda yake zaune a Kano tareda Dan'uwan nashi yana taimaka
mishi a kasuwancin nashi, sai Rumaisa'u itace ta Uku tana Aure anan garin Kaduna
yaron ta daya rak malamin islamiyyar su ta aura, sai Auta halima wacce burin
iyayanta kaf yakare a kanta yayinda suke mata soyyar da batada adadi kasancewar tun
tashin ta takeda kwakwalwa sosai Ga natsuwa batada Abokin fada ko kadan ga hakuri
kamar damo uwa uba sunan mahaifiyar Malam liman gareta kaf unguwan babu yarinya
Abun kwatance irin halima hakan yasa dayawa ma basusan ainihin sunan taba saidai
*USTAZIYA* saboda natsuwa da kamun kanta Wani abun Al'ajabi kaf unguwan babu wacce
za'a nuna ace wai kawar halima ce batada kawa ko daya a unguwan saidai Abokan
karatun ta a makaranta, idan akwai matsala daya a rayuwar gidan nasu toh bai wuce
yanda basa lura da rayuwar halima ba dukda ita kadai ce a gabansu suna ganin tunda
Allah yabata natsuwa har kwatance akeyi da ita tohfa basuda sauran tarbiyyar dazasu
bata shiyasa duk abunda tayi daidai ne babu maice mata komai tun tana shekara goma
a duniya ta sauke Alkur'ani mai girma yayinda tasha lashe manyan gasa tareda
kyaututtuka masu yawan gske a fannin Addini dukda haka tana zuwa makarantar domin
Karo karatu akan manya manyan littatafan Addini amma saida Dare kasancewar da rana
batada lokaci saboda makarantar Boko daganan kuma zata tsaya lesion, tun halima
Nada shekara sha'uku ta rikice tafara harka da kawayen banza yan karya data hadu
dasu a makarantar boko dukda babu abunda take Sha'awa kamar rayuwar yanci da wayewa
amma ganin gidan data fito shiyasa bata fito da kudirin nata a fili ba tanaso tasan
duniya duniya ma tasanta, halima Nada shekara sha'hudu a duniya tafara kananan
shaye shaye harda zuwa club makarantar ma ta rage zuwa sai jefi jefi Kota fito
saidai ta biya gidan kawayan nata yan'club suyita shaye shaye tareda baccin asara,
Mahuta shine saurayin daya kara budema halima ido sosai, sun hadu a sanadiyyar
yawan ganinta dayakeyi a club nan danan yakasa danne maitarsa a fili ganin yasamu
swt 14 yaita bibiyarta ganin bata Dade a harkar ba yakara samun kuzarin bude mata
ido yanaso ya Raine ta tahada komai dayake bukata shine Wanda yafara kawarma da
halima budurcin ta tun tana shekara sha hudu a duniya inda bata damu ba ganin ya
mallaka mata duk wani jin dadin Rayuwa har gida yabata itada kawayen ta Wanda yake
a GRA madaidaicin gida ne inda shida Abokan shi ke zuwa suna holewar su a gidan
kawayan nata dayake korarru ne a gidan iyayan nasu, feenah da meenah, shiyasa suka
tare a gidan din'din'din yayinda leema kuwa bcci kawai ke dawoda ita gidan iyayan
ta, dukda haka babu Wanda ya farga da kazantar da takeyi harta iyayan nata saboda
komai da taku takeyin sa.

Mahuta Dan gata ne gaba da baya irin sangartattun yaran yan siyasa Wanda babu kwaba
babu tsangwama kusan duk abunda yakeyi wurin babanshi ya gada barewa bazatai gudu
danta yayi rarrafe ba baban shi babban mazinaci ne hakan yasa shima ya haifi magaji
a zina babu abunda basu mallaka maiba najin dadin Rayuwa dukda baban nashi yana
samun labarin ta'asar da yaronsa keyi jefi jefi amma bai damu ba ganin hakan shine
wayewa, mahuta bakaramin manemin mata bane kuma Dan kwaya domin baya kananan shaye
shaye har cocaine sha yakeyi.

*Mr's Sadik Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Yah Allah ka zaunar mana da kasarmu lfy👏🏻kaduna people how market?🤣ya gajiyar
zaman gida? Wannan doka mun gaji da ita😭 ya Allah ka dauwamar mana da kwanciyar
hankali a kasar mu👏🏻.*
*Dedicated to sister Husnah*

ko lekawa dakin su meenah da suketa ramokon bcci batayi ba dayan dakin tasa makulli
tabude ta shiga kassncewar two bedroom flat ne sai katotan parlor a tsakiya tareda
toilet Uku, kowane daki da toilet sai daya a parlon ko'ina tsaf tsaf gwanin ban
Sha'awa yasha furniture's ba laifi gidan baida wani hayaniya, dakinda yake
mallakinta ta shiga saboda babu mai shigar mata nan take sauke mahuta da sauran
samarin ta yayinda dayan dakin kuma mallakin su meenah ne.
Cire kayan jikinta tayi batabar komai ba saidan pant da bra ta bararraje tafara
sharara munshari.

Kiran sallar asuba neya farkar da Zainab duk nauyin bccin da takeyi tohfa ana fara
kiran farko cikin ikon Allah saita tashi, nan ta Mike tayi salla tana zaune a wurin
tana lazumi har gari yafara haske sannan tashiga bayi tayi wanka, kwalin plaster
dinda ke garkame akan madubin dakin ta bude tareda daukan guda biyu, ta manna daya
a goshin ta daya sace amma yabar karamin ciwo, daya kuma a gefen bakinta ta manna,
blue material Mara nauyi ta dauko wacce akai mata simple dinkin doguwar Riga ba
hayaniya simple make-up tayi tareda feshe jikinta da turare nan tafito Ras abunta
dinkin ya amshe ta sosai dukda Zainab masha Allah kamar yanda AK yace she fat for
back she fat for front tohfa haka yake a cike take taf tareda taimakon shafaffen
cikinta dake tona asirin kyawun halittarta ya kwanta ya lafe kamar ba hanji a
ciki, irin dogayan matan nanan ne amma ba fara bace bakuma baka sidik ba black
beauty ce skin dinta mai tsada tanada kyau mai tsayawa a rai hmmmm *'nasan zakuso
kuji wacece Zainab ku cigaba da kasancewa da Yar mutan katsinawa*

Saida ta kyara ko'ina na cikin gidan dukda girman gidan amma yauda gobe tasaba bata
wani ganin wahalar hakan kasancewar tun Dare ta wanke kwanukan da akai Amfani dasu
tareda goge kitchen din, hakan yasa turaren wuta kawai tasa ko'ina yadau kamshi
masha Allah, ragowar ferfesun jiya ta dumama tareda Juyewa a cooler sai sandwich
datayi tareda dafa ruwan tea Wanda Yaji kayan kamshi kan dinning ta jera komai da
komai cikin rawan jiki tafito makeken harabar gidan nasu wurin jerun motocin AK ta
nufa guda Uku masu kyau, 'dattijon mai gadin gidan nasu ne ya matso wurinta tana
hango shi ta gaishe shi nan ya Amsa mata cikeda fara'a da mamakin ranarda zata
daina wankema AK motoci kusan shekara Uku Abu yakici yaki cinyewa ba karamin
tausaya mata yakeyi ba hakan yasa har Addu'a yake mata Allah yakawo mata karshe
wahala wurin uban gidan nashi, a iya sanin shi baitaba jin AK ya dagama wani murya
ba kokuma ya zagi wani sai matarshi hakan yasa yake cikeda zumudin San jin tarihin
rayuwar su dukansu idan da Hali, sanin babu halin shiyasa ya hakura yaja kafarshi
tareda komawa bakin aikinsa, 'motocin ta shiga wankewa sauri sauri gudun fitowar
shi, hakan yasa tagama dawuri ta wanke su duka tas tareda gogesu ciki da waje a
gajiye take lis ko wankin motocin wani katon aiki ne sanin ko kura yagani cikin
motar tohfa ta shiga Uku, tana gamawa ta dauki abun gyaran flowers ta nufi flowers
dinda ke zagaye da gidan nasu, dukda ada akwai masu aikin gyaran flowers din harda
mai wanke mai motan tun farkon Auran suya sallame su duka a cewarsa kudinsa ya huta
an kawo mishi jakar mai Aiki, cike da sabo da kwarewa tashiga gyarawa tagama komai
nan ta hau sharar tsakar gidan nasu dakyar ta gama saboda girman gidan, shiganta
cikin gidan yayi daidai da fitowar shi daga dakin shi sanye da dakakken suite milk
color yasha necktie black da zanan milk ya tsuke fuskar nan a murtuke dukda haka
yayi matukar yin kyau gawani bakin gashi daya zagaye fuskar nashi hakan yakara fito
da madarar kyan shi, dogon Namiji ne fari tas Tubarkallah masha Allah, shagala tayi
da kallon Sa kaunarsa na Kara ruruwa a ruhinta ji take kamar tayi tsalle ta
makalkale shi, ganin batada niyyar daina kallon nashi yasa shi watsa mata Wata
shegiyar harara a cewarshi kada ta shafa mai bad luck da sanyin safiya, russunawa
tayi tana gaishe shi, 'ina kwana ka tashi lafiya? Kamar kullum wuceta yayi kamar
tana magana da dutse kallon dining yayi yaga ta jera abinci kotakan abincin baibi
ba, dama baci yakeyi ba sai ranarda tayi matukar Sa'a idan kuma batayi ba wani
sabon tashin hankali ne, duk Randa tayi gigin mai tayin abinci kuwa a jikinta yake
Juyewa duk zafin shi.
Tanajin fitar shi gidan a gurguje tashiga daki Kara gyara jikinta tayi tareda
chanza kaya duk sun takura ta, ta matse cikin kananan kaya gajeran wando jins blue
da farar vest, masha Allah ita kanta tasan Allah ya kawata surar ta, shiyasa ta
dinga fuskantar matsaloli ada saboda hakan kan dining ta nufa nanta kwasa girkin ta
yayinda ta koshi daki ta koma ta zumbula dogon hijab sauran abincin ta juye awani
cooler Wanda yake mallakin mai gadi ne, mika mai tayi tadawo tareda kunna TV takamo
Arewa24 kwantawa tayi akan doguwar kujera tanata kallo har wurin 11 taji tsamin
jikinta ya dame ta baya mata dadi ko kadan, tashar ta chanza aikuwa ta kama Wata
tashar wakan turawa sai karkada jiki sukeyi, nan danan ta Mike wai itama zata gwada
kozata danji karfi karfi a jikin nata idanta jijjiga jinin jikin ta dukda maganin
datasha a banza, rawan ta shigayi tana botsarewa sai bankare bankare takeyi tana
juya cikin ta kamar yanda taga sunayi , tayi Akalla kusan minti 10 cikin nishadin
data dade batayi ba ganin takoma saikace yarinya yar shekara sha Tara, karan Abu
taji hakan yasa ta waigo da sauri abun mamaki AK tagani tsaye kamar gunki ya
sankare yana Kare mata kallo ko kyaftawa bayayi baki a bude aikuwa a 360 tabar
wurin tareda garkama makulli a dakin nata, wayarshi daya Saki ya kalla a kasa domin
tunda tafara rawan ya shigo da niyyar Amsa waya haryasa a kunne yanaji ana mai
magana cikin wayar amma yakasa tabuka komai............yanzu abun Aisha harya kaiga
haka? Tuno wani littafin sanin sirrin mata daya taba karantawa idan bai manta ba
malamin cewa yayi duk macen datake yawan mika ko bankarewa toh tana cikin tsananin
bukatar Namiji, *Innalillahi wa inna ilaihir raji'un* ya furta cikin sanyin jiki.

*Shin wakesan yasan labarin ma'auratan nan masu ban Al'ajabi?* duk maiso ya daga
💁🏻‍
hannu

♀ ‍♀

*Mrs Sadik Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah*

Bakaramin San halima mahuta keyi ba inda ya kudira a Ranshi idan lokacin auren shi
yayi zai iya Rayuwa da ita dukda yakai munzulin auren amma a cewarshi bayaso ya
tsufa abunda ya lura Aure na saurin tsufar da mutum tun bare idan yafara Tara yara
gara nanda kamar shekara 45 ya daure yayi, suko iyayan shi ko'a kwalar rigar su Dan
suma American style sukeyi basa takura ma yaro a cewar su rayuwar shice yanada
yancin yin komai, duk cikin bebs dinshi bai hada leemah da kowa ba a cewarshi
saboda tana nishadantar dashi yanda ya kamata, kullum jinta yakeyi zamzam ko kadan
bata sakaci da maganin mata hakan yasa yake mata duk abunda takeso gudun kada ta
naima a waje abunda baisani ba Yammata irin halima basuda Alkawarin rike saurayi
daya tunda zata iyama iyayanta basaja shi awa? yanda cikin takun ta take kula Gayu
sosai tareda basu kanta jinta takeyi bazata taba Rayuwa da namiji guda daya a
rayuwar taba saboda karfin Sha'awar da takeda shi hakan yasa kullum saita samu mai
debe mata kewa inda take abunta cikin kwarewa tareda taimakon maganin Hana daukar
ciki, tunda tataba yin ciki kusan sau biyu dakyar tasha inda a lokacin Mamarta keta
zuzuta yanda tayi haske dakara cika aiko nan ta sanarda mahuta sukaje asibiti aka
burge shi bakaramin wahala tasha ba hakan yasa aka daure mata bakin mahaifa, dayake
Allah ba'a mai wayau saiga wani Alamar cikin a jikinta a lokacin su meenah ne suka
farga cikeda tashin hankali suka koma Asibiti Ashe mahaifar budewa tayi ba karamin
wahala tasha ba inda har jinya saida tayi a gida amma ankasa ganewa mama tadage da
dafa mata huntu da ararrabi a cewarsu shawara ce taimata mugun kamu hakan yasa duk
Wata saitaje an duba lafiyarta a Asibiti saboda ba kowani maganin planning ke
amsarta ba shiyasa yakara cika ta dam dam harta fara losing shape ba tareda ta
farga ba.
Halima tana cikin jerin mata masu matsaikacin tsawo itaba gajera ba bakuma doguwa
ba, tanada haske farace amma ba Sol dinnan ba dirin jikinta ma babu laifi saidai
batada cikar kirji sannan basuyi Kanana sosai ba, yar madaidaiciya yayinda hancin
ta Dan daidai yadan bude kadan baiyi tsini sosai ba saidan karamin bakin ta tareda
ido masu Dan girma, baza'a kirata mummuna ba tanada kyau mai sanyi, tareda zubin
halitta mai kyau saidai kan nan nata ne toh masha Allah kamar kwallon goriba😕a
takaice dai irin gashin sister Husnah gareta🤣🤭 amma tareda taimakon karin gashi
wanda dorawa kawai takeyi akai bata yarda aimata kitson shi saboda tsaro shima tana
gama abunda zatayi take tunbuke shi saidai kan nata dukda bawani gashi a tsaftace
yake zaka ganshi Ras da kitso maiban Sha'awa kwarjinin ta shike Sa manyan Gayu ke
mutukar kaunarta duk kankantar ka indai zaka zube mata kudi toh babu abunda zai
hanata budema kafa a takaice dai *The definition of halima is fake*

*Cigaban labari*

Shiryawa tayi cikin kayan makarantar nata doguwar Riga wacce tadan haura kugun ta
da dogon wandon har kasa sky blue sai hijab dinta iya guiwa fari tas takalmin gida
tasa flat a cewarta tunda karatun WAEC sukeyi ba'a takura musu daka ganta kaga
student fuskarta babu kwalliya I'lla pawder da man baki Mara kala dukda haka tayi
kyau ba laifi, wurin 7:30 tafito dauke da Karamar jaka Wanda katon littafi guda
dayane a ciki shima dandai daukan nashi yazama dole ne, iyayan ta tasamu zaune a
matsaikacin parlor dinsu Wanda babu komai a ciki sai ledar tsakar daki a gefe daya
kuma katon dirowa ne shake da littattafai kala kala na Addini ko'ina tsaf gwanin
ban Sha'awa suna zaune akan tabarma da Alama Karin safe sukeyi, dukawa tayi ta
gaishe da iyayan nata cikin faraa suka Amsa mata, 'uwata ya karatu? Yakuma haddar
taki? Duk inda kike da matsala wurin rashin fahimta ki gayamun sai inkara doraki
akai, inji Malam liman, Toh Abba insha Allah bama Wata Matsala, "toh toh yayi haka
akeso aita dagewa shi ilimi da kike gani kogi ne sai gaba zakiga amfanin shi maza
zauna ki karya ki hanzarta kada ki makara ya fadi yayinda da kanshi ya tsiyaya mata
koko cikin kofin dake hannun shi da Alama ko gama sha baiyi ba tura mata yayi
gabanta harda ledan kosan daya siyo musu na Kari, mamanta ce ta turo mata wani
kwanon Samira ta ajiye gabanta, dumamen tuwon dawa ne miyar kubewa danya sai tururi
yakeyi, 'maza ki hada da wannan saboda kiji nauyi nauyi tunda keda dawowa sai shida
na yamma, 'a'a mama kosan maya isheni tafadi tana shan koko cikin natsuwa, dari
biyu babanta ya mika mata dari Na abun hawa dari kuma kozata siya wani Abu darana
saboda yinwa gashi zata tsaya lesson din WAEC, 'baba kabarshi Wanda kabani jiya da
daddare ma yananan tafadi , a'a uwata hada duka aikin chanchanci komai gurina babu
abunda bazan iya miki ba dakyar ta Amsa Naira dari wacce tace kudin mota zatayi
dashi, 'mikewa tayi cikin natsuwa tabar gidan a'daidaita ta nema drop ta dauka basu
zame ko'ina ba sai gidansu na isa kaita Wanda yake a U/rimi GRA rabonta dawata
shegiyar Boko harta manta a cewarta babu abunda kudi bazai siyan mata ba kuma tana
dasu, hakan yasa harta biya ansamu Wanda zaimata komai da komai da sunanta batareda
ciwon kai ba. tana isa mai'gadin su dayake zaune kofar gidan sanin cewa daidai
lokacin take zuwa, gaishe ta yahau yi Kota kanshi batabi ba 'kada abar kowa ya
shigo batareda ambaka izinin yin hakan Ba, tafadi yayinda tashiga cikin gidan,
batajin zata iya tarban baki da safe saita huta domin bccine sosai a idon nata.

*Mrs Sadik Rumah💅🏻*


🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
🏼🏼🏼
*Ustaziya ko Yar'duniya?*
‍♀‍♀ ‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍

*Written by Anty Mamie*

*Gskia sai jiya na tabbatar da masoyan littafin nan Nada yawa fiyeda tsammani na
wayata har daukewa takeyi saboda ruwan comments da Addu'a a gareni nayi matukar
farinciki tareda mamakin yanda kuka karbe shida hannu biyu biyu, bazan daina fadi
ba comments dinku nasani matukar nishadi tareda karfin typing, Godiya mai tarin
yawa Ga makaranta😍😍*
Sorry nayi mistake a last page inda zansa Sunan Aisha nasa Zainab, Afuwan typing
error ne.

*Dedicated to sister Husnah*

*Shin wacece Aisha? Wanene kuma AK?*

Ya'u shine Mahaifin Aisha tareda mahaifiyarta Ramata Asalin yan cirani ne daga
Damagaram dake jahar Nijar, inda suka shigo Nigeria lokacin da yaransu biyu, namiji
da yar'karamar yarinya mace wacce mahaifiyarta Ramata ke rike da ita a hannu, a
lokacin bazata wuce shekara biyu a duniya ba, namijin suna kiransa da garbati,
yayinda macen suke cemata shatu, Sanye suke da bakaken kayan buzaye yayinda sukasha
nadi a kansu daka gansu kaga bakin haure, daga Ya'u har Ramata irin dogayen
buzayen nanne sosai wankan tarwada kyawawa Tubarkallah, yayinda cikin ikon Allah
suka sauka garin Kaduna a unguwan shanu kai tsaye gidan mai unguwa sukayi inda
suka gayamai kudirin suna San fara sana'a yanda zasu tallafa rayuwar su, cikin ikon
Allah mai unguwn yabasu daki daya Wanda ke zauran cikin gidajan shina unguwan
aiko ba karamin murna suka dinga yiba tareda godiya da Addu'a a gareshi, dakin
karami ne baida girma sai window kwaya daya rak, inda Allah ya taimake su zauran
nada dan fadi hakan yasa Ramata keyin sanwa a lungun zauran, yayinda suka hada bayi
da mutanan dake cikin gidan dukda gidan bawani Babba bane dakuna Uku ne a cikin
gidan sai bayi guda daya da kitchen dinda kowa ke Amfani dashi, batareda bata
lokaci ba Ya'u ya kafa Karamar teburin shayi a gaba da gidan nasu nan danan yafara
Tara customer's bakaramin ciniki yakeyi ba darana kuma saiya kasa rake duk anan
wurin yayinda Garbati ke tayashi Zama a lokacin yanada shekara goma a duniya akwai
tazarar shekara takwas tsakanin shida Aisha, Ramata kuwa baa barta a baya ba,
wankau tafara a cikin gida, itama babu laifi tana samu hakan yasa tace barita gwada
shiga cikin gidajan masu kudin unguwan kila zata Dace su dauketa wani aikin, cikin
ikon Allah nan saman layin su sosai inda gidaje masu kyau suke nanta tunkara duk
gidan data shiga bata dacewa harta fara gajiya ga zafin rana Ga Aisha dake bayanta
sai kuka take tsalawa, ganin sauran wani gida daya Wanda yafi duk Wanda take zuwa
tsaruwa tana shirin komawa gida hakanan tace bari ta gwada sa'ar ta, tun daga
kofar gidan mai gadin gidan ya dakatar da ita, 'hajiya lafiya? Yana Kare mata kallo
sama da kasa, kafun takaiga bashi Amsa sukaji karan horn din mota Alamar masu gidan
ne suka dawo, matsawa tayi gefe tareda rusunawa, koda suka shigo hajiyar gidan ce
dayara guda biyu tareda ita, babban shekaransa goma sha biyar mai suna Abdulkareem
yayinda dayan bazai wuce sha'daya ba, shikuma Abdulhakeem kallo daya zakai musu
kaga kallar kamarsu da mamar tasu wacce take fara kar, 'a'a lafiya? Wacece wanchan?
Hajiyar ta tambaya tareda nuna Ramata daketa zuba zufa cikin tsakiyar rana, Kafun
mai gadin yabata Amsa ta karaso tareda Kara dukawa gaban hajiyar tana gaishe ta,
'amsawa tayi cikin sakin fuska, 'hajiya Dan girman Allah ki taimakeni kibani aikin
yi, ta furta cikin rawar murya, achan kasan layinku gidanmu yake Mijina ne mai
saida shayi da rake a kasan layi, 'shigo mu shiga ciki hajiyar ta furta ganin yanda
Aisha keta tsala kuka kamar zata suma, samarin kuwa tuni sukayi cikin gida hannun
su rikeda Leda da Alamar siyya sukayi da mamar tasu.

A babban parlon dake kasan gidan sukai masauki kassncewar gidan gidan sama ne,
parlon ya tsaru sosai, a gefen kujera Ramata ta zauna yayinda hajiyar tayi tayi ta
zauna kan kujera taki, Wata dattijuwa ceta shigo parlon rikeda farantin ruwan sanyi
da lemu tanama hajiya sannu da zuwa, amsawa tayi tareda mika ma Ramata ruwan aikuwa
ta Amsa ta sha sosai tareda kwanto Aisha tabata tasha nan tayi shiru tana Ajiyar
zuciya da Alama zafi neya dameta dama.

Basu bar gidan ba saida hajiya taimata Albishir din bata aikin wanke wanke da
gyaran kitchen da tsakar gida, tunda sunada mai musu girki sannan ba abincin kowa
suke ciba, cikin Ikon Allah tafara zuwa tareda samun Alheri mai tarin yawa inda
kusan anan take saman musu abincin da sukeci a gida, kassncewar idan abinci ya
kwana basa ci, nan hajiya taba Ramata izinin dauka tunda dama Almajirai ake dunduma
ma, dukda ranar juma'a ana girki na musamman da yamma Almajirai na layi amsar
sadakan abinci mai rai da lafiya, nanfa duniya tadawo masu ya'u da Ramata harma da
yaransu sabuwa sunyi fes sunyi kyau sosai sun murmure Aisha kuwa sai wayo takeyi
tayi bulbul da ita gwanin ban Sha'awa takawa takeyi ko'ina.

*Mr's Sadik Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah*

11

Tunda Aisha tazama cikakkiyar budurwa a lokacin tanada ilimin Addini Daidai
gwargwado, Boko kuma tana SS1 Makarantar gwamnati, nanfa samari suka yo mata chara,
yawancin marasa jin unguwan ne duk Wanda yasan unguwan shanu yasan ba laifi akwai
marasa ji saidai Allah ya shirya kawai, hakan yasa bata kula kowa ganin duk babu na
kwarai koma akwai babu hurumin shi a gefen zuciyarta, nanfa suka Kara samata ido
wasu harda zagi idan tafito, tana diyar mai shayi da rake amma tana girman kai,
wasu suce rufa mata Asiri zasuyi danta samu ana Santa diyar Dan kwaya, hakan yasa
tasa katon audiga tareda toshe kunnan ta, Ramata kuwa Kullum cikin hannunka mai
sanda take mata yayinda yayanta garbati abun yafi damun shi fiyeda kowa amma ya
zaiyi? Wasu yan'iskan ma cewa sukeyi darajar shi takeci mai akai da diyar mashayi
dan cha-cha?
Ya'u kuwa ko'a kwalar rigarsa hidimarsa yakeyi.
Cikin masu takura mata akwai wani Saurayin dake zaune a cikin gidan su Wanda yake
dan'sara suka ne yayi suna a unguwar wurin rashin ji, duk inda ka ambaci *Virus*
tohfa harta yaro yasan da zaman shi a unguwar, maguwar Sha'awar Aisha yakeyi tunda
ya kyalla ido yaga surarta, hakan yasa yaita mata tayin soyyar Sa babu yanda baiyi
ba ko darajar magana baya samu dukda yana aiko mata da kananan kyauta kozata kula
shi saidai ta kori Dan sakon tareda sakon, Wata rana da yamma tadawo daga islamiyya
Virus na zaune a kofar gida ganinta yasa yatare karamin kofar shiga cikin gidan,
tsayawa tayi dataga bayida niyyar matsa mata kallan shi tayi, 'zan wuce, 'kallon ta
yakeyi sama da kasa tareda lashe baki kamar tsohon maye, 'ki wuce mana, tareda Dan
bude mata hanya kadan, rabawa tayi ta gefen shi cikin natsuwa ta manne da bango
gudun kada jikinsu yataba juna Virus kuwa dayake bahaka yaso ba yaso yadan ji dumin
ta koda Dan gogarshi ne tayi hakan yasa kafun takarasa wucewa taji PA's ya bugan
mata gefen duwawu har yana Danna hannun shi, wooooooooo kafun yarufe baki aiko
Yaji saukan Mari a gefen fuskarshi, karamai wani tayi tana huci Ranta yayi mugun
baci ta kudiri aniyar duk abunda zai faru saidai yafaru tagaji da rainin wayaun su,
hannun ta aka kama daga baya, 'zoki wuce, inji Ramata wacce tafito duba sanwar data
Dora a zaure, babu musu tabi bayanta sukabar Virus na hucin ganin babu namijin
daya isa yayi mishi haka amma yau saboda ya latsa duwawun mace yasamu mari biyu
abun takaici kuma a gaban yaransa dake zaune a gefe, aikuwa masu dariya damai
kirari nayi masu bashi hakuri nayi nan yakara kulewa tareda Alkawarin daukar fansa.

Kuka takeyi da takaicin rayuwar data tsinci kanta a ciki bakowa yakara jamusu
abun gori ba I'lla baban su daya kasance mutumin kwarai babu Wanda zai watsa musu
shara, nan tayi mai isarta yayinda Ramata batabi ta kanta ba itama dazata samu mai
lallashin nata so takeyi, Aisha kukan fili takeyi itako tadade tanayin na zuci,
batada yancin shiga cikin mata sa'an ninta iyaye koda kuwa sha'ani ne na cikin
unguwan inko taje an dinga ya'da mata habaici kenan saikace itace keyin cha-cha ko
shaye
🤷🏻‍

♀ shayen‍♀ gidansu AK ne kawai basu chanza mata ba.

Bayan an kwana biyu, zaune suke a'dan tsukukun dakin su cikeda jimamin rashin
dawowar ya'u gida kusan kwana biyu kenan babu shi babu labari, shiba wayaba bare a
kira duk inda akesa ran ganinshi bayanan hakan yasa suka dangana tareda zubama
sarautan Allah ido, garbati ne ke zaune gefen mamar tasu da Aisha yana cin tuwon
masara miyar kuka Auta kuwa tana gefe daya tazuba uban tagumi sai tausar su yakeyi
akan baban nasu zai bayyana gobe da sassafe zai Kara dubashi ko za'a Dace, dakyar
ya lallaba sukaci tuwon suma tareda musu sallama zuwa makwancin shi a lokacin yabar
dakin su ganin rashin dacewar hakan shiyasa yakoma dakin abokinshi dake unguwan
yana kwana, sallama yayi musu yayinda yawuce a lokacin sunada matsalar wuta gashi
lokacin zafi ne babu halin kulle kofa dukda sunsan akwai hatsari barin kofar a bude
tohya zasuyi? Gashi kofar gidan nasu dan kwano ne akeja ake kullewa.

Wurin sha'dayan Dare dukansu sukayi bcci ga azabar sauro da zafi hakan yasa
Ramata ke daure da zani a kirji Auta ma haka, Aisha kuwa vest ce sai underwear a
cewarsu zafi bazai kashe suba.

Kafarta yake shafawa a hankali, nan yafara kokarin tube mata Riga,cikin
bcci taji ana shirin cire mata kaya gashi ana shafa mata jikin ta, aikuwa kwanciya
yayi sosai a jikinta jin nauyin shi yasata sakin ihun da Ramata ta farka, nanta
dinga zuba ihu daduk karfin ta aikuwa kafun kace kwabo muryarta ta karade ko'ina,
magana yafara cikin maye, meeeeyeee......ha.ka, Raaaa.. a'a
Mikewa tayi ganin ana shirin keta ma diyarta haddi akan idonta Kwanan samiran
dake gefenta ta kwada masa akai, sannan ta tuna da tuchlight dinda ke gefen katifar
su, ihu Ramata keyi akan akawo musu dauki kwarto ya shigo aikuwa tana kunna
tuchlight din idonta ya sauka akan Ya'u dake shirin cirema Aisha underware harya
fara yaga mata vest din jikinta, bin bango tayi tana salati tareda dafe kirji
tuchlight din hannun ta yafadi kasa hakan yayi daidai da karasowar virus da ihunsu
ya tashi kowa na gida, ihu yasaka jama'a uba kecin diyarsa shiyasa aka hanamu
dandane ashe cikin zafin nama ta tattaro duka karfin jikin ta tahau buga mai duk
wani Abu dake kusa da ita, virus kuwa ihu kawai yakeyi yana shela a unguwa ya gansu
turmi da tabarya, diyata? Duk karuwan gari sai diyata? Wlh kashe ka zanyi Ya'u
Allah ya la'ance ka Allah ya hanaka farinciki Aisha sumewa tayi ganin ubanta neya
yaga mata suturar jikinta yayinda Auta bilki tayi mutuwar tsaye numfashi na sama da
kasa.........

*Mrs Sadik Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah*

*Woooo page biyu harda Read more har biyu🤩dukda haka some one must complain😨😰
lemmi c*😏

10

Alhaji muktar babban Dan kasuwa ne kuma ma'aikacin gwamnati inda yake aiki a NGO
yayinda yake zaune a unguwan shanu, tareda matarsa hajiya Bilkisu wacce sukai Auran
saurayi da budurwa cikeda soyya, Alhaji muktar Dan Asalin jahar katsina ne matar
shi kuma yar Yola ce bafulatana kyakyawar mace sun hadu dalilin wani zuwa Yola
dayayi cikin ikon Allah har sukai Auran soyya tareda Arzikin yara biyu duka maza,
Abdulkareem shine Babba Wanda akafi Sani da AK, sai Abdulhakeem tun akansu haihuwa
ta tsaya musu chak dukda a duniya babu abunda suke Sha'awa kamar Tara yara masu
yawa Wanda burin hajiya Bilkisu wacce suke kira da Mamie bai wuce ta ganta da diya
mace ba, hakan yasa kullum Addu'ar ta kenan samun mace,
Alhaji muktar mutum ne mai tausayin talaka hakama matar tasa, ba karamin
kyautata ma talakawan unguwan yakeyi ba hakan yasa a karo da dama yaso barin
unguwan talakawa na hanashi ganin yanda suke karuwa dashi matuka dukda yanada
gidaje masu dumbun yawa a garin kullum arzikinsa karuwa yakeyi saboda yanda yake
wanke dukiyar shi inda yaso yakoma GRA cikin manyan gidajan shi nachan ya koma da
iyalan shi amma yan'unguwa sunyi kememe sun hanashi, babu yanda basuyi dashi ba
akan yashiga harkar siyasa yaki, a cewarshi bata burge shi.
zuwan su Ramata gidan yasa hajiyar sakewa da Aisha a cewarta yarinyar na burge ta
gata kyakyawa gata yar'duma Duma bakaramin gashi Aisha keda shiba inda tayi gadon
shi wurin dangin uwa harna uba, kyawawàn halin Ramata neyasa Mamie takara janta a
jiki itada diyarta domin tasha gwadata ta hanyoyi da dama kuma cikin ikon Allah
bata kamata dawani laifi, soyyar da Mamie kema Aisha yasa AK shiga lamarin ta indai
yana gidan tohfa tana hannun shi har fita kofar gida yakeyi da ita yanai mata wasa
kassncewar kullum zaka ganta fesfes an tubke mata gashi gwanin ban Sha'awa, hakan
yasa Ramata na zuwa Mamie ke amsarta taita mata wasa itama, shakuwa sosai ke
tsakanin AK da Aisha, inda a yanzu a'kalla takai shekara hudu a duniya wayau da
surutu kuwa ba'a magana komai Yaya AK, hakan yasa Mamie ke tsokanar AK Take
cemishi Angon Aisha, na Aisha wasa wasa shima yafara kiranta da matarshi, inda babu
Wanda yayi zargin wani Abu, shakuwar AK da Aisha ba'a magana inda hajiya har kaya
siyan mata takeyi hakan yasa Alhaji ma yafara sake mata ganin iyalin Sa na kaunar
yarinya shima ta shiga Ranshi, nan Ramata tasa Aisha awata islamiyya anan unguwan
tana zuwa safe da yamma, A'nanan har babanta yasata awata makarantar gwamnati
tafara zuwa Boko cikin lokaci kadan takara wayau sosai, a kwana a tashi saiga wani
cikin ya kuma bullowa a jikin Ramata nan taita rainon abunta har Allah ya sauke ta
lfy ta haifi diya mace inda a wannan karan hajiya Bilkisu akaima takwara a cewarsu
basuda kamarsu a kaf unguwan bayan mai unguwa, bazasu manta Alkairin su a garesu
ba, sunji dadin karan da akai musu nan suka Kara rike juna da Amana.

Abunda masu karatu basu Sani ba shine ya'u Nada wani mugun hali tun a kasarsu
nijar babban mashayi ne kuma dan'chacha ko bayan daya Auri Ramata babu abunda
yafasa a halinshi talaucin daya mamaye sune yasa ya ajiye shaye shayen a gefe ganin
baida kudin dazai siya tareda ma Ramata Alkawarin dainawa yayi gaba daya tunda yara
sun fara girma baiso yabar musu abun kunya, ganin yanda kudi ke shigo mishi yanzu
gakuma matarshi kusan ta dauke mai hidimar ci Dasha na gida hakan yasa yadawo da
tsohon halin shi, tun yanayi a boye har Ramata ta farga hankalinta ba karamin tashi
yayi ba, inda zata tasa shi a gaba taita masa magiya tana rokon Sa tana kuka, haka
zaikara mata Alkawarin daina wa, Wata rana idan ya bugu tana magana zai lakada mata
duka a daki tanaji tana gani zai jibge ta haka zata hadiye kukanta a cewarta bataso
kukanta ya tona asirin uban yaranta, haka yaran zasu makure a bango suna kuka
ganin yanda ake jibgar mamarsu, washe gari haka zaizo ya tsugunna yana bata hakuri
da nadama, amma hakan bazata chanza zani ba. babu yanda batayi dashi akan su nema
hayan gida kusa dasu koda wani daki dayan ne tunda garbati ma yafara Zama saurayi,
dakin yamusu kadan ga Aisha tafara girma rai biyar dakin bazai dauke suba amma
kememe ya shafa ma idon shi toka dukda yanada kudin yin hakan a yanzu ganin biyan
kudin hayan dakin da zai kama kamar barnan kudi ne gara yasha kudin shi yayi tatil
haka zai shigo yana rangaji tareda zage zage tun yan unguwa basu farga ba har aka
fara ganewa inda sanaar shayin ma yadaina garbati keyi yanzu shi saidai ya kwanta a
gida idan Ramata tatafi aikatau yaita baccin Asara, wasa wasa abun nashi yai
tsanani inda akaita kaima mai unguwa karar shi, hakan yasa ya kirashi yai masa
nasiha sosai, hakuri yaita badawa, inda har cewa yakeyi asiri akai masa daga
kasarsu a cewarshi wai sun sami labarin rufin asirin shine, Jama'a saidai suce
Allah shi kyauta, Daya daina na kwana biyu zai dawo ruwa tsundum harma yafi Nada.

Shakuwar AK da Aisha ba'a magana, inda AK bai hadata da komai ba hidima yake mata
baji ba gani a lokacin ya mallaki hankalin kanshi yazama kyakyawan saurayi sosai,
babu abunda yafi kauna kamar ka danganta shida Aisha tun bare idan kace mai mijin
Aisha hmmm har kowa yagane hakan ita kanta Aisha dadin hakan takeji komai Yaya AK
bakinta baitaba rabuwa da sunan shi, a lokacin yafara shirye shiryen barin kasar
zuwa Egypt yin jami'ar shi dukda baiso hakan ba a cewarsa wazai kula maida Aishar
Sa, dakyar iyayan suka lallaba shiya tafi, inda Aisha ta rikice lokacin tafara Zama
budurwa itama har abinci saida ta daina ci dukta rame nanfa iyayan suka fara tsoran
shakuwar dake tsakanin su. A kwana a tashi babu wuya komai na tafiya daidai banda
halin ya'u dake Kara birkicewa dukya rikice yakara tsufa abun na damun iyalan Sa
tun bare Aisha da a makaranta har gori ake mata haka zatai ta kuka tun bata saba ba
harta saba mai unguwan yaso korarsu a karo da dama tuno Laifin wani baya taba
shafar wani saboda darajar matarshi da yaran shi Wanda suka samu shaida mai kyau a
unguwan shiyasa ake daga mai kafa, inda Aisha tazama Silent kasancewar batada
kawaye a cewar su babu Wanda zaiyi harka da diyar mashayi, nan kewar yayanta yakara
cikata saidai ta kwanta a daki taita kukan kewar AK Wanda a lokacin tagama yarda
shine farin cikin ta, tagama yarda idan bada shita rayu ba toh rayuwar Tata batada
wani Amfani, tagama yarda sanshi takeyi soyya Mara iyaka inda Ramata tun tana biye
mata suna labarin harta fara tausaya ma diyar Tata ganin dala da gwauron dutsen
data dauko ma kanta ko'a duniyar mafarki AK ba sa'an ta bane hakan yasa Ramata
tadage dayimata Addu'a Allah ya yaye mata larurar data Dora ma kanta.
Ta fannin mamie kuwa komai na tafiya daidai duk sanda zasuyi waya da AK baida
abun tambaya sai Aisha, tun bata damuwa abun yafara damun ta nan ta taka mai birki
bataso zargin da takeyi yazama gaske, ganin yanda Ranta baisan hakan yasashi daina
tambayar badan Ranshi naso ba, Mamie babu abunda suka Fasa yima Ramata da yaranta
dukda sanin halin ya'u saidai mommy taita bata hakuri da tattausan kalamai.

A kwana a tashi lokaci na ta tafiya tun Aisha nasa ran dawowar AK harta dangana
saidai soyyar shi nanan daram a Ranta tareda Alkawarin bazata taba mai kishiya a
Ranta ba, yayinda ta bangaran shi kuwa iyayanshi kekai mishi ziyara a cewar su
gara ya zauna wuri daya saiya gama komai da komai tas na karatun shi domin yana
hada Degree gara ya karasa gaba daya zasu dinga zuwa tareda kanin shi Abdulhakeem
Wanda a yanzu shima yake shirin komawa chan karatu.

A lokacin ne makerin budurwa yagama kawata halittar Aisha fiyeda tunanin mai tunani
tahada duk abunda ake bukata a wurin mace, Allah ya wadata tada zaunannan baya
'duwawu' ga tudu kamar ka Dora Kofi ya zauna daram🤭 ga hips masha Allah ga kirjin
nan ya cika yayi dam Tubarkallah, da taimakon shafaffen cikinta shape din halittar
ta yakara baiyana, ko hijab tasaka idan tana tafiya komai na jikinta saiya dinga
kadawa, kiban jikinta a wuri biyu yake hakan ba karamin tsokale ma samarin unguwan
ido yakeyi ba uwa uba Allah ya zuba mata natsuwa ta musamman kullum cikin dogon
hijab zaka ganta hakan yasa yan iskan samari saka fara samata ido, inda Ramata ta
farga Kullum cikin yimata Addu'a da nasiha takeyi hakan yasa take Kara suturta
kanta kokadan bata shigan banza.

*Bakar rana........coming soon*

*Mr's Sadik Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah*

13

Bayan shekara Uku da faruwan hakan ne cikin Ikon Allah da Al'ajabi tayi wani
Saurayi daga sama wai yazo kuma ba wasa ya kawo shiba Aure yazoyi bayasan bata
lokaci, sunan shi Musa yanada mata daya da yara Uku baida Wata Sana'a I'lla iyaka
shago dayake dashi yana saida kayan masarufi harga Allah baimata ba amma hausawa
sunce da babu gara ba dadi hakan yasa batareda dogon nazari ba ta amince a lokacin
tanada shekara ashirin a duniya nan Ramata taita farinciki baki yaki rufuwa kashi
sittin na damuwarta ya yaye domin tagama sama Ranta Aisha bazata taba samun mijin
Aure ba kila Aure kuma sai a lahira idan anayi saboda bakin fentin da Ya'u ya goga
musu ita kanta Aisha bata taba tunanin samun mijin Aure ba koma zata samu batasa
ran anan kusa zata samu ba harga Allah tacire Auran AK a Ranta tasan kozata mutu
tadawo ita dashi har abada saidai babu na biyun shi zatai Aure bana soyya ba.

Mamie ce ke kaiwa da kawowa bakinta yaki rufuwa yayinda da kanta take shigo da
farantan abincin da suka gaji da haduwa domin tarban dan'lelen ta, farin saurayi
sosai kakkarfa mai kwantaccan bakin gashi dake daukar ido yayinda gefen bakin shi
bakin gashin ke zagaye da karamin bakin nashi Wanda Ake kirada *Quarter mullion*
hancin shi siriri masha Allah idon shi basu cika girma ba yan daidai sannan basuyi
fari kar ba duk inda ake naiman Handsome indai kaga Saurayin nan tohfa an Dace,
fara'a ne kwance a fuskar shi Rabon shida Nigeria harya manta he feel Alive gashi
cikin gidansu yayinda ya matsu yaci abinci akwai tarin tambayoyin da yake shirin
yima mamin nasa, zaune suke gaba daya harda Dadyn su anata cin abinci tareda basu
labarin nasarorin daya samu a tafiyar dayayi yasha Addu'a babu adadi wurin iyayan
nashi cike daso da kauna nan Dadyn su yai mishi Albishir din fara Aiki a ma'aikatar
su NGO tareda mukami mai girma saboda darajar kwalinshi saidai muce masha Allah,
gakuma kasuwancin shida yakeyi Abubuwa sunmai yawa yana naiman mataimaki tunda
tsufa yafara kamashi ba kamar daba, duk AK ne zai amshe su a'haka firar nasu na
ranar ya Kare batareda yasamu damar yima Mamie tambayar da yakeso ba.

Washe gari Allah Allah yakeyi a hadu cin abinci cike yakeda da zumudin dahar
mamakin kanshi yake, wanka yayi cikin kananan kaya misalin karfe Tara ya sauko
breakfast lokacin Daddy ya Dade da tafiya office, tsakurar abincin yayi sama sama
yayinda yake Jan Mamie da fira har akazo inda yakeso, 'wai Mamie ina mai muku wanke
wanke ne Ramata Kota daina zuwa dawuri ne Yanzu? Aisha fa nasan tazama budurwa
yanzu, 'hmmmm bari kawai son abun ne saidai muce Allah shi kyauta rabona da Ramata
kusan shekara Uku kenan baiwar Allah oooh Duniya, tafadi cikin jimami, nanta bashi
labarin Abunda yafaru bakaramin tashin hankali ya shiga ba sai zufa yakeyi of all
people why Aisha? Eye Mamie Anya ba sharri akayi musu ba kinsan fa mutane? AK kabar
mutum kawai Allah kadai yasan abunda yafaru nidai bazance yar'iska bace kamar yanda
ake fadi a unguwa saboda ban gani da idona ba, inadai musu aike jefi jefi saboda
samun lada, Allah yasa ta Auru shine kawai wlh na tabbata babu mai Auran yarinyar
nan, why mum? Meye Laifin ta? How sure are u bazata auru ba? Yafadi tareda mikewa a
fusace yabar wurin, ikon Allah konice Ya'u kokuma nice yan'unguwa dasuke kiranta
yar iska? Ihu fa kakemun AK, ita kadai take maganar ta AK kuwa ya Dade da barin
gidan cikin tashin hankalin da baisan dalili ba.

Saida yayi kwana biyu babu inda yaje sai tarin wasiwasi da yakeyi taya ma za'a
cemai Aisha yar'iska ce? Dukda ya Dade bai ganta ba amma ya tabbata ko cikin duhu
zai iya gane ta, why? Toh kodai gskia ne kamar yanda aka Kara bashi labarin abun a
unguwa dukda masu bada labarin suma sun Kara gishiri da Maggi a ciki.

Ramata keba Aisha labarin dawowar AK yi tayi kamar bataji taba saboda rashin abun
cewa zuciyarta kuwa idan banda bugu babu abunda takeyi inda har Ramata ta farga da
hakan taja bakinta ta tsuke,
Hijab ne kamar koda Yaushe katoto a jikin ta bayan sallar Isha'e Ramata ceta aiketa
bayan Layin su kai kayan wankin da taima wasu gida kusan kwana biyu kenan basu aiko
sun Amsa ba gashi ya cika mata daki gashi suna bukatar kudi basuda ko abunda zasuyi
Karin safen gobe, bilkisu ta aika Aisha tace zata bataso ana aikan bilki sannan
tafisan fitan Dare yanzu babu maisa mata ido kamar rana dukda Yanzu anfara sakar
mata Mara ba kamar daba dadan dama dama, ta bayan layinsu tabi inda tunda Vairus
yaga fitowarta da inda ta dosa Yaji kamar anmai bushara da Aljannah yayinda takai
sakon tareda amso kudin wankin Naira dari Uku da hamsin, siririyar hanya yar karama
ce ba'a cika wucewa ba kasancewar ba'a gama ginin gidajan dake wurin ba koda rana
hanyar shiru zaka jita bare da Dare dukda haka mutane nabin ta sosai saboda
shortcuts ne mai sauki indai zaka zagaya bayan Layin kana bulla ka huta dogon
tafiya, touch light ne hannun ta tana tafiya sauri sauri Addu'a dauke a bakinta
bata San maiyasa ba gabanta ke matukar faduwa sosai, ji tayi an buga mata wani Abu
akai yayinda aka toshe mata hanci da farin kyalle nan tafara ganin jiri, daukar ta
sukayi har cikin wani gini da ba'a karasa ba dukda tana ganin duk abunda yake
faruwa amma takasa komai jikinta ya mutu ko hannu bata iya dagawa, 'mai naaaay..yi
muku? K..uyi hakuri Dan darajar Allah kada ku tona mun Asiri tana fadi idonta na
lumshewa, "matsiyaciya asirin ki ya Dade da bankarewa ai kinada wani asirin da za'a
iya rufewa ne inji virus daya kwashe tada kyawawàn Mari har guda Biyu ya jefata
kasa a cewarshi ya Rama Marin datai masa shekaru Uku da suka wuce, kuji tsoran
Allah da ranar hisabi ku kashe ni kawai kiyi hakuri kada ku zalumci rayuwata da
Addinina, kafarsa yasa yaita hambarin ta a ciki, ko kiyimun shiru kokuma ina gama
farkaki in farke cikin ki, yafadi da karkausan murya

Sha'awar zagaye unguwar nasu yakeyi dukda bawani chanji da aka samu amma ya tsinci
kanshi yana Sha'awar zagayawa koba komai ya motsa kafa tunda yadawo yana zaune a
gida gashi baida Abokai a layin iyakar Sa kofar gida nanzai samu mutane biyu suyita
firar duniya, yagaji da zama wuri daya tafiya yakeyi jefi jefi yana danne danne a
waya iska mai dadi yana hura shi cike yakeda nishadi ya kwasa a kalla minti
shabiyar yana shiga lungu lungu batareda wani tsoro ba, a hankali yake jin nishi
tun baya jiyo abunda ake cewa harya fara jin hayaniyar samari suna ihu da shewa nan
kuma Yaji siririyar muryar mace, ana wyyoo Allah wash kaina zai fashe, dukda
zuciyarshi nabashi shawarar komawa amma idon shi nasan ganin Abunda Akema nishi da
shewa, cikin dakiya ya tunkari wurin yayinda yake haskawa da wayarsa, samari ne su
Uku kowa na rige rigen tube kaya yayinda Ga mace kwance a kasa idonta na lumshewa,
barin abunda sukeyi sukayi kowanne da gajeran wando Aisha kuwa tuni sun cire mata
katon hijab dinta sanye takeda Riga da Skart kanta da dankwali, wani irin sarawa
kanta keyi kamar zai fashe, 'mai kuka bani? Kaina bana gani sosai ta furta tana
shirin mikewa dakyar a karo da dama, Malam lafiya? Suka furta babu Alamar wasa
cikeda takaicin tsaidasu daga garar da suka kosa su kwasa, baibi takansu ba harya
juya zai tafi saikuma yadawo Kara kunna hasken wayarsa yayi tareda rissinawa daidai
fuskar macen bakaramin tashin hankali ya shiga ba jikin shi har rawa yakeyi nan
danan yafara hada zufa gashin jikin shi a Mike cikin tashin hankali, kulle fuskarta
takeyi Dan yagama kashe mata ido da hasken wayarsa bata gani, Dan girman Allah ku
Taimake ni zasu kashe ni a taimaka, aaaa.....isha ya furta tareda mikewa da sauri
har yana dafa bango, muryarsa dataji ne tadan Mike zaune cikin maye dakyar dukda
bata gane komai Amma taga gefen fuskar shi, Yaya, kaine? Yaya ka tafi dani daganan
yaya bana gani sosai kaina zai cire.. Virus kuwa ikon Allah suke gani sai a lokacin
suka gane AK cikin takaici ya kalleta, yaya? Ina yayan yayan ubanwa? Kin sanni ne?
In taimake ki? Uban waya kawo kinan? Kwartayan da suka fito dake lokacin nan su
maidaki Dan ubanki ni kikaba Goran gayyatar Dana gayyato miki su nan? Zare mata ido
yakeyi kwalla na zuba a idon shida yagama rinewa, harya juya zai tafi ya waigo
tareda kallon su virus, kuyi hakuri da katse ku danayi ku cigaba da abunda kukeyi,
juyawa yayi baiko waigo ba, Innalillahi wa inna ilaihir raji'un, AK kada ka tafi ka
rufamin Asiri AK! AK!! Zasu keta mun haddi AK!!! Aaaaaaaaaaa

*Mrs Sadik Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*


*Dedicated to sister Husnah.*

12

Kafun kace kwabo mutane sun yanyame zauran gidan, nan aka damki ya'u dukanshi
sukeyi Kota ina matasan unguwan, suna cewa duk iskancin su bazasu taba naiman jinin
suba karshan iskanci yakare uba ya nema yarsa ya'u tuni yadan dawo hankalin Sa
saboda bugun daya kesha jini ta hanci ta baki babu kyan gani kanshi a fashe duk
jikin shi ciwo, 'wlh na dauka Ramata ce, Allah na tuba shegiya, shegiyyaaa giya
giya Allah ya tsine miki yar iska ta kassarani Allah ka dauki raina Dan girman
Allah ku kashe ni banda Amfani nadauka Mamarta ce taya zan naima abunda na Haifa?
Bantaba zina ba ya za'ai infara akan diyar cikina? Allah ka shiga tsakanina da giya
kaimana hisabi Kin gama dani kinji dadi giyaaaaaaaa, Babu Wanda ya saurare shi,
Ramata kuwa kirjinta ta dafe nanta sulale kasa sharaf, matan makota ne suka
suturta ma Aisha jiki dukda ba'a tsirara take ba nan aka Kara rikicewa a tunanin su
mutuwa Aishar tayi danko motsi batayi, ruwa aka shiga watsa musu yayinda Ramata
taja Ajiyar zuciya mai karfi Aisha kuwa ko Alamar motsi batayi ba, Auta bilki kuwa
tana manne da bango kamar mutum mutumi itama ruwan sanyin aka shiga yayyafa mata
domin batada banbanci da wacce ta suma, ana haka ne Garbati ya karaso a rikice
dagashi sai gajeran wando saboda rudewa, dakyar aka iya bambare ya'u daga hannun
matasa, nan Abokanan garbati suka shiga lallaba su, kememe sukace sai sun kashe shi
mutumin da akace an ganshi turmi da tabarya shida diyar cikin Sa ina maganar
sassauci? Karku raina mana hankali mana malam, cikin dabara Abokanan garbati sukaja
hankalin su da sunan bada hakuri yayinda Garbati yaja ya'u batareda sun Ankara ba
saboda garin yayi duf kowa da tuchlight yake rike, ya'u kuwa babu abunda yakeyi sai
tsine ma giya da cha-cha tareda yima kanshi Allah wadaran sai a lokacin yasan illar
shaye shaye wato duk abunda musulunci zai Hana toh bakaramin Rahama bane a garemu
muddun zaka kusance shi kuwa sai Allah ya nunama kyakyawan jarabawa akan haka,
Allah ya tsine miki giya, kabarsu su kashe ni, 'suna barin wurin Virus ya karaso da
abokansa yan Sara suka harda fetur da taya wai zasu kona ya'u bakaramin takaicin
rashin samun Sa sukayi ba, yayinda wasu sukace a fito musu da Aisha, nan virus yace
su kyale ta batada laifi, Laifin baban ne dayake mata mugunta hartaki yin Aure Ashe
shike kwasar romon tunda budurwa ce su barta kawai, a zuciyar shi kuwa wani kudiri
ne na daban akan hakan dayayi tunda yaga Aisha da underwear yasa ma Ranshi koda
gawarta cefa saiya dandana.

Watsewa akayi babu Wanda yabi takan Ramata da yaranta kowa ya koma gida ana ruruta
abunda ya faru dama Wanda bai faru ba kowada kalar labarin Sa akan lamarin, dakyar
bilki ta tattaro jarumtar ta yayinda ta dibo ruwa a Roba da tsumma taita shafama
Ramata da Aisha a jiki saboda rashin mafitan abun yi shiyasa tace bari ta gwada
kila a Dace, Saida gari yafara wayewa Ramata ta farfado nan akai jugum jugum Aisha
kuwa babu ko Alama, saida tayi yini daya Sannan aka samu kanta, babu mai iya magana
cikin su kamar kurame yayinda zaman gida yagama Auran dukansu babu mai iya leka
waje, unguwa kuwa anyi gulma harta takashi🤭 a'haka Rayuwa ta kasance musu babu
labarin ya'u babu kuma Wanda yadamu yasani cikinsu bare ya tambaya ko maganar basu
Kara tadowa ba, hidimar gidan garbati ne ya dauka gaba daya harta gidansu AK Ramata
ta daina zuwa inda Mamie ta tako takanas tazo musu jaje rareda Alkairi mai yawa
inda Alhaji muktar ma yabada kudi masu yawa akan abasu.

Aisha kuwa saida aka dade sannan tafara fita hijab dogo har kasa take sawa kamar da
nan za'ai ta mata habaici da gori a unguwan, nan aka Sa mata suna *Ustaziya ko
Yar'duniya* yayinda ta dauki kaddarar tada hannu biyu bata taba tankawa ba
makaranta daina zuwa tayi Boko da islamiyya akan dole inda ko Kare baya naiman ta
samari kuwa ko'yan iskan ma sun daina zuwa a cewarsu ita kakarsu ce a bariki dakyar
da sidin goshi mai unguwa yabarsu sukara Zama tareda kashedi mai girma idan
makamancin hakan yakara faruwa za'a hukunta su tareda koransu gaba daya, sanarwa
yabada duk Wanda yaga ya'u a unguwar azo a gaya mai baice kowa ya dauki hukunci a
hannu ba.

Mr's Sadik rumah💅🏻


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Masu cewa idan wani Abu yasamu Aisha saisun kwanta asibiti kusha kurumin ku domin
a iya chemist kawai zaku tsaya.😂*

*Dan Allah ku dinga mun uziri idan banyi posting dawuri ba, kullum banayin kasa da
page biyu har Uku inayi, kunsan halin yauda kullum ba koda yaushe mutum keda lokaci
ba Ga hidimar gida damai gida, a dinga mana uziri.*

*Dedicated to sister Husnah*

14

Kai meye haku kukeyi? Inji virus yayinda yaga sauran yaranshi na zura wando, baibi
takan suba ya dumfare ta babu komai a jikin shi, hankade shi daya daga cikin su
yayi, oga Ashe baka gane ba, wani shegen ne zai ganmu a haka yace mu cigaba? Eye?
Tarko nefa kagane mana eyeh haba baba, kasan yanda yarinyar nan suke da gidan su
yaron nan AK harfa hawaye nagani a idonshi, Na Ukun ma ya amasa, 'Alkur'an nima na
ankare kai, kwalawa zai kwaso mana yayinda yagama Tara mana jama'a kawai eh yanee,
dakyar suka iya lallaba shi tareda janye virus da takaici ya kusa kashe shi badan
yaso ba amma tabbas AK tarko ya hada musu, nifa yasin yasin tsaf dazata Aure ni zan
yarda yarinyar akwai maiko yasin yafadi yana zura wandon shi, kaga Karamar kasa da
Arzikin man fetur yasin kirarin irin matan nan kenan, Allah yabamu kudi muci babbar
Giwa, Suna Allah ya isa suka watse a wurin yayinda suka dauki dari Uku da hamsin
dinda tayar a kasa a cewarsu ko sigari Sa sha su rage zafi.
Aisha kuwa wani bcci mai karfi yayi awon gaba da ita, inda su Ramata ganin
shirun bana karewa bane tace bari tabi sahu taga ko lafiya, gidan wankin tayi inda
suka shaida mata Aisha tabar gidan tuni harta Amsa kudin wankin, cikin mugun tashin
hankali taita duba lungu lungu sako sako babu ko tsoro, "hmmm wani Abun sai mama"
cikin ikon Allah hartazo inda Aishar take yashe a kasa bcci takeyi harda munshari
dalilin abunda ta shaka, salati tasaki babu halin ihu yanzun nan Sai akara fassara
su da gagarumar sharri, kan Aisha ta Dora akan cinyarta tana kuka mai fitarda
karamin sauti, jikin ta tashiga dubawa saida ta duba komai tsaf sannan tasaki
Ajiyar zuciya, barin wurin tayi gudu gudu tareda amso pure water awani shago mai
sanyi aiko ta dinga bulbula mata dakyar Aisha ta iya bude ido cikin maye a'haka ta
tallabo ta suka Mike tana layi Kamata sosai Ramata tayi a jikinta a haka sukayi har
gida cikin ikon Allah layin babu kowa babu Wanda ya farga, ba'a samu kan Aisha ba
sai washe gari inda taita sujadar godema Allah da bata wulakanta ba, babu abun
takaici GA diya mace irin zubarda budurci a titi koda Ramata tasamu labarin abunda
yafaru saidai bata gaya musu zuwan AK wurin ba, mikewa tayi tareda rantsuwar za'ayi
ta takare rashin gata ba hauka bane saidai subar unguwan, dakyar Aisha da Bilkisu
suka lallashe ta ko garbati bai sani ba ganin ba karamin tashin hankali za'a kwasa
ba, tunda Allah na Tareda mai gskia bawa bazai taba gujema jarabawar shiba idan
sunbar nan suje ina? Inda zasu wayasan gobe? Wayasan abunda zai faru??
Ta hakura tareda sharadin babu inda Aishar zata Kara zuwa Abu daya zai fitar da ita
daga gidan nan shine Aure insha Allah gashi kuma yana matsowa.

Musa yazo batareda boye boye yayinda Ramata ta turashi wurin mai unguwa a cewarta
shine mai bada Auran Aisha, baiko nuna damuwa da hakan ba yayinda yace bai damuda
sanin komai game dasu ba sun tsaida magana akan zai mata kayan fitar biki ne kawai
banda lefe a cewarshi tunda ba kayan daki zata zoda shiba zaisa abunda baza'a rasa
ba a dakin amma kada su cika buri, Basu damuda hakan ba sudai burin su ace Aisha na
dakin mijinta dukda yace tareda iyalin Sa zai hadata, ita kanta Aishar bata damuba
ganinta babu abunda zaikara sata farinciki a duniyar ta tun dataga AK dukda bawani
ganinshi tayi ba gaba daya takasa sukuni ko kadan bataga Laifin shiba I'lla haushin
kanta dataji daya risketa a haka shine takaicin ta, wani maganadisun soyyar shice
ke fusgarta zuwa Gare shi a karo da dama tasha yunkurin kodai ta bishi gida taimai
bayani ne? Sanin Ramata bazata taba barin ta fita ba hakan yasa ta rame sosai
kullum tana cikin kwalla da tunanin kada yaimata fassara Allah yasa baya fushi da
ita 'inda a barayin AK kuwa baida damuwa harkokin shi kawai yakeyi ya tattara ta
gefe guda ya watsar komai suna Aisha ya tsana a halin yanzu.

Angama komai na Auran Aisha Ramata da garbati sun danyi bajinta ba laifi inda
Ramata tasiya zanin gado guda biyu masu saukin kudi tareda risho da kula biyu masu
kyau da samiru su cups da jugs da plates harda ledan tsakar daki, da kujeran
tsugune, kaya dai ba laifi na fitar kunyar uwa a cewarsu basa mika ta haka gaya ba
saikace daga sama ta diru, ya'u kuwa shiru kakeji kamar an aiki bawa garinsu.

*Mrs Sadik Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Anty Mamie's Novel Group🎀1🎀2 tareda Ustaziya fans group ina mika gaisuwa ta, ana
Tare.🤝🏻*

*Dedicated to sister Husnah*

15
Mai unguwa yayi farinciki sosai tun bare yanda aka Dora shi akan komai hakan yasa
aka yanke ma Musa sadaki dubu talatin bayan an kwana biyu suka kawo kayan Sa rana
nan akasa sati biyu masu zuwa tunda babu wani shirin da za'ai, kati aka buga mai
saukin kudi akaita rabawa duk Wanda yagani saiya tofa Albarkacin bakinsa wasu na
tayata murna wasu na mamakin Wanda Ze aureta a cewarsu munafuntar shi akayi wasu na
ko sadaka basa so kowadai da abunda yake fadi, Ramata ta kaima mamie kati mai yawa
da alewa nata Dana Alhaji aikuwa ba karamin murna mamie tayi ba baki yaki rufuwa
nan taita Kara kwantar mada Ramata hankali tareda Alkawarin suma zasu bada
gudunmawa mai yawa a Auran ita da Alhajin, ana haka AK ya shigo gidan daga wurin
business dinshi yadawo tunda yayi sallama yaga Ramata dauke kai yayi harda juyawa,
Kiranshi mamie tayi badan yaso hakan ba fuska a daure yaje, 'baka gane Ramata ba
mamar Aisha wacce ka tambaya kwanaki? 'Ina wuni ban gane taba yafadi yana shirin
juyawa, 'katin Auran Aisha aka kawo Aishar ka zoka gani nanda sati biyu.......
Aishar babanta dai yafadi yayinda yadawo ba kunya yasa hannu ya dauki katin, kallon
shi sukeyi daga Mamie har Ramata dataji wani iri a Ranta, 'Allah sarki bawan Allah,
Virus zata Aura koh? Koda yake banga Alama ba su kansu maza yan iska suna neman ma
yaransu uwa tagari lallai wannan ya dauko kaikayi ina fatan dai sunje Asibiti anyi
gwajin kanjamau dukda maganin shi kyauta ne, 'AK wani irin iskanci ne wannan? Inji
Mamie ko kadan bataji dadin Abunda yayi ba, mai nayi Mamie daga fadin gaskiya?
Konayi karya ne? Yafadi yana ware hannuwa, Aisha fa nace wacce ka raina kafun
tafiyar ka.....au Karuwa zaki cemun zanfi ganewa wannan Yar'iskan? Tsawa Yaji an
daka mai ta bayanshi Alhaji muktar neya dawo, subhanallah Abdulkareem musulmi kake
kira da munanan suna haka? Mai akai maka daga dawowa kasar? Ashe bakada hankali ban
Sani ba? Mikewa Ramata tayi ido cikeda kwalla dakyar ta iya Jan kafarta batako bi
takan Mamie dake bata hakuri ba tabar wurin cikin kunar zuci tareda tunanin Laifin
da sukai ma duniya Tai musu daurin talala, AK kuwa daki ya shiga yayinda wani sabon
tsanar Aisha ya shige shi ji yake kaf duniya baida na biyun ta a makiyi a dalilinta
Mamie da Daddy kemai ihu a dalilin mai fuska biyu Yar'duniya yafadi 'gaban madubin
dake manne a dakin ya tsaya yana kallon kanshi kamar zai hango Aishar a ciki.

Ramata kuwa babu Wanda taba labarin Abunda yafaru tabarma zuciyarta a ganinta fadin
shi baida wani Amfani.

*Rana bata karya*

*Kai kubani kidan Amarya da Ango a sama kowa ya shirya kwaso shoki gobe nefaaaa👯🏼‍
♀💃🏽*

Sorry for d short page am occupied yau shiyasa.

*Mrs Sadik Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah*


16

Daddy ne zaune a parlor shida AK misalin karfe Tara da Rabi na Dare bayan sungama
fira, Dadyn ya gyara Zama Alamar akwai magana a bakin shi yayinda ya kalla AK din,
'Abdulkareem , ya kirashi tareda kallon shi, 'naam dady ya Amsa hankalin shi gaba
daya nakan baban nashi sanin daddy baya kiran sunan shi saida kwakwaran dalili,
'shawara ce nakeso inbaka inda hali, idan yama toh saidai muce Alhmdlh domin zanfi
kowa jin dadin hakan, 'ina jinka dady yafadi tareda gyara zaman shi sosai hankalin
shi akan daddyn, 'gyaran murya Alhaji muktar yayi sannan yafara magana, 'akwai
yarinyar aminina business partner Dina duk Wanda ya sanni toh yasan Alhaji dan'juma
mutumin kirki ne kuma mai Amana hakan yasa tuntuni na Dade dama Sha'awar baban
diyarsa saboda yarda da tarbiyyan gidan danayi idan Allah ya kaimu kaje ka dubata
idan tamaka harna masa magana akan zakazo kuga juna domin Kara dankon zumunci da
kasuwancin namu kuma harma yafini farinciki da hakan.......'Daddy, AK ya katse shi
daga maganar da yakeyi, 'ina jinka
Inji Alhaji muktar dukda baiji dadin katse shin dayayi yana magana, 'Kaimun gafara
Daddy wlh tallahi batayi mun ba bana Santa Dan Allah a hadata dawani, yafadi kai
tsaye bako kunya dajin nauyin mahaifin nashi 'kasan tane? Alhaji muktar yafadi
cikin mamakin AK, kaje ko ganinta kayi mana, 'ban Santa ba daddy basai na ganta ba
amma bata yimun ba koda naje zan Amince ne bada San zuciyata ba,
'Toh!
Toh!!
Toh!!!
Hakan yayi kyau, inji Alhaji muktar cikin rashin jin dadin Abunda AK yaimai, kanada
wacce kakeso ne? Saika kawota da gaggawa niba mutumin banza bane ace shekaru nata
jamaka sa'annin ka sai haihuwa suke tunda kadawo muke maka maganar Aure mai kake
cemana? Lokaci kake jira koh? Toh mun gaji da Zama cikin lokacin ka, wacece wacce
kakeso??
'Cikin rikicewa ganin yanda Alhaji muktar yadau maganar da zafi ba kamar yanda
yayi tsammani ba sai zufa yake hadawa a zaune.....'dakai nakeyi fa inane gidansu
suwaye iyayanta cikin satin nan nakeso aje gidan nasu, 'damaaaa damaa Wata ce bamu
gama daidaitawa ba tukunna, yafadi cikin rawar murya, 'mttsssew Abdulkareem tashi
kabani guri, naga Alama nazama Abokin wasanka ance kakawo mata kaki anbaka mata a
gidan mutunci kace bakaso shin auren ne bakaso koko isa dakai ne bamuyi ba? Zakasha
mamaki jeka jeka shikenan, mikewa yayi jikin shi a sanyaye yabar wurin dukya rasa
maike damun shi wai ina matan suke ne? Ance akwaisu a gari sosai shi yar yanzu bai
gansu bafa ya akeso yayi??

Alhaji muktar neke shirin zuwa Office dukda baicika zuwa ranan juma'a ba ko zaije
baya zuwa dawuri amma tun safiyar ranar ya tashi ya shirya dawuri Mamie ceta shigo
dakin cikeda mamaki, Daddyn su Abdul badai fita zakayi ba? 'Kaji mai idonki yagani
idan ba fita zanyi ba mainene amfanin babbar rigar Dana Sa? Bafa nasan tambayar
rainin wayau, 'Allah yabaka hakuri gani nayi yau juma'a ai sai bayan an sauko
masallaci kake Fita gashi yaune daurin Auren diyar Ramata na dauka zakaje, 'auu
kinga ko shaf na manta wlh Wasu baki mukeda su zasu zo daga Lagos zamuyi meeting
dasu tuntuni Nike jiran kiransu saboda yau zasu toso da sassafe, karan kiran
wayar shine ya tsaida shi yayinda ya dauki wayar dake kan kago cikin hanzari ya
juya harshan turanci, yayi minti Uku a wayar ya katse cikin takaici sai masifa
yake, 'ina amfanin rashin cika Alkawari kun tsaida mutane Dan iskanci kuce kun daga
sai ranan Monday? Kaji fa, akin banza, 'ya akayi kuma mai gidana wake tabo munkai
yaune inji Mamie datake shirin samai hula akan shi, 'maida ai nama Fasa fitan anyi
canceling meeting din sai Monday insha Allah, yafadi tareda cire babban rigar shi,
Anjima naje wurin daurin Auran ko lada na samu.
Misalin karfe daya babban masallacin unguwan ya cika makil babu masaka tsinke
yayinda aka idar da sallar juma'a ana shirin daurin Aura saidai mai? Babu ango babu
Alamar shi babu waliyan Ango nanfa akaita kananan surutu, a gefe daya ya'u ke zaune
jikinshi manne Dana mai unguwa kassncewar tunda bikin ya matso yaita tura garbati
wurin mai anguwa naiman Alfarman halartar daurin Auran diyarshi tareda Alkawarin
ana daurawa baza'a Kara ganin shiba, dakyar da sudin goshi mai unguwa ya lallashi
matasan unguwan akan subashi damar shigowa yau daya rak koba komai Auran diyarsa
ake, yasha fararan kaya harda babban Riga sai washe baki yakeyi cikeda farinciki
saikace shine angon, tunda akaga babu wani dangin ango bare angon aiko ya'u yaita
hada zufa harda cire hular kanshi yana fifita dukya jike babban Riga, 'Musa ne ya
shigo masallacin cikin hadin gambiza sanye da wandon farin shadda tasha guga sai
Wata bakar kodaddiyar T-shirt baza ido yakeyi sai zage zage yakeyi aikuwa charaf
idon shiya sauka kan ya'u daya kara makure jikin mai'anguwa, 'munafukin Allah
ta'ala wato ni zaka Aurama diyarka daka gama kwakule ta saida ka tande ta tsaf zaka
kawo mun tallar Auran ta? Macucu mazinaci tir duk iskancin ka ace sai kayi da diyar
cikinka? Billahillazi ko balarabiya ce sai andawo da kudina tundaga kan taro zuwa
sisi na bazaiyi ciwon kaiba yafadi yayinda yake nade kafar wandon shi kafun a
Ankara harya shako wuyan babbar rigar ya'u ya hadashi da bango yakai masa naushi a
baki, 'banda rainin hankali karuwar zaka aura mun duk mazan unguwan nan sungama
saninta akace, mutane ke bashi hakuri yaki sakin ya'u a cewarsa sai an maido mai da
komai saikace Wanda ya kashe kudin Arziki babu yanda baayi dashi ba kememe yaki
sakin wuyan ya'u daya Kara makurewa, ya'u kuwa kunyar duniya tagama rufe shi ji
yakeyi kamar kasa ta bude ya shiga kokuma Allah ya dauki Ranshi a lokacin wannan
abun kunyar damai yayi kama? Dawani ido zai Kara kallan iyalin Sa a karo na biyu
yakara tarwatse musu Rayuwa a dalilin gyaran dayake tunanin yayi, 'Alhaji muktar
neya Mike yayinda ya tunkari wurin rike hannun Musa dake wuyan ya'u yayi, bawan
Allah kaima Allah ka sake shi, wannan ai tozarci ne, fisabilillah saboda masifa ya
fadar Ma yarinya ko'ince jarabawa saikuma taki auruwa? Haba jama'a ku tayani ganin
lamarin nan idan ba'a Aurarda da ita ba karuwa barnar zatayi kadauki hakan akan
zakayi sadakatul jari'a hakan ya kamata aima irinsu bawai Asa musu karan tsana ba
da tsinuwar dake Kara dulmiyar da doran kasa bawai a dinga gudun suba Allah kadai
yasan yawan ladan dazaka Sa.......''dakata dalla Malam gafara kafun in hadaku duka
in tumurmusa rainin wayau kana nufin in Aure ta dukda ubanta ke cinta komai kake
nufi? Toh billahillazi babu Dan iskan daya isa ya cuceni da dadin baki waikai zakai
mun wa'azin bogi uban waya hanaka yin sadakatul jari'ar kai? Komu matsiyata akeso
mu dinga yinta muna Auran yara karuwai idan kanaso ka burge ba haka zakayi ba saika
Mike kawai a daura dakai ko mai gadin gidan ka ka Kara masa yakarasa ragowar ubanta
dawata wa'azin ka Mara ma'ana sannu limamin madina kabar ganin ana kaunarka kanaso
ka Kara siyan soyyar mutane da dadin baki, dalla kauce bani wuri ba maganan matsayi
akeyi anan ba, 'Alhaji muktar Ranshi yayi mutukar baci ganin yanda Musa ya kwance
mai zani a tsakiyar kasuwa duk girman shida daraja shida mutane keyi, abun takaici
wasu burgesu Musa yayi yayinda dayawa ke dariya da ganin wautan Alhajin, cikin
sanyin jiki yaje yaja hannun liman tareda makwabtan dake jikin gidan shi mutum biyu
gefe suka koma cikin minti kadan liman yafara magana a lasifika,toh jama'a Alhmdlh
ina cikeda farinciki tareda Kara ma Allah godiya akan lamarin daya faru yanzu wani
baya taba Auran matar wani, duk a gyara Zama Dan Allah a kimtsa za'a daura
Aure....'da uban wa? Inji musa, badai dani ba? Babu Wanda yabashi Amsa I'lla iyaka
sadakin shida aka mika mishi dubu talatin chif, nan yaita washe baki yayinda ya
zauna bako kunya harda lankwashe kafa cikin yan kallo shima yanaso ya kashe
kwarkwatar idonsa, ya'u kuwa da garbati sakin baki da hanci sukayi, nanda nan
jama'ar wurin suka shaida Auran *Abdulkareem muktar tareda Aisha Ya'u* akan
sadaki Naira dubu hamsin nan take Alhaji muktar ya kirgo su tsaf makwabtan shi sune
waliyan Ango sumai unguwa kuma waliyan Amarya duk Wanda ke cikin masallacin ba
karamin mamaki yayi ba, ya'u kuwa hawaye kebin idon shi wani nabin wani yatashi
jiki na rawa har inda Alhaji muktar yake zaune zubewa yayi hade da rike kafafun shi
duka biyun sai bude baki yakeyi amma yakasa magana sai hawaye kawai, damke kafan
Alhajin yayi sosai sai nishi da numfashi yakeyi idon shiya kafe a sama, dif ya zube
a wurin zuciyar shi ta buga lokaci daya baiko motsa ba nan akayi kanshi ana salati,
'Vairus kuwa baiso haka ba domin kadan yake jira yace a daura Auran dashi dama
Addu'ar shi daya Aisha tayi kwantai yaga samu yaga rashi.

*Mr's Sadik Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
🏼🏼🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Yah Rabbi duk inda na zaga duk inda na leka kowa Ustaziya harna rasa bakin Magana,
waya kona amsata babu iyaka messages kuwa na mutane har wayata na daukewa, shin ta
ina zan fara muku? Gskia mutum Rahama ne, nagode da Addu'ar ku a gareni masoya,
Ustaziya fans group kuna Sani nishadi Mara iyaka comments dinku na jiya naci
dariya, godiya gaduk masoyan Ustaziya makwaftan Aisha ina gaisuwa da kawayan ta
tace ace muku adaina kushe mata Angon ta hakanan take san abunta.🙏🏼😍*

*Dedicated to sister Husnah Amarya*

17

Kan Ya'u akayi ina rai yayi halinsa tuni nan aka dauki kabbara Allah sarki ya'u
ashe yanada rabon ganin Auran diyarsa Allah ya dauki Ransa a wurin daurin Auran
yar'sa, jama'a nata jimamin lamarin tun bare jarumtar da Alhaji muktar yayi, liman
yabada sanarwa da la'asar za'ai mai salla akai shi makwancin shi nan danan wani
yaro ya ruga gida batareda bata lokaci ba Amarya taci kwalliyar ta babu laifi tayi
kyau tasha lallan gargajiya inda babu wasu yan biki masu yawa sai makwaftar da
gulma ce yakawo su harda masu kawo mata gudunmawar maganin mata na Ni'emah maganin
matsi kuwa ankawo mata shi babu iyaka wasu saboda cin fuska kawai zasuzo suna mata
bayanin yanda zatayi matsi bilki ceke tanka musu yayinda Ramata ta kwabar musu kada
kowa ya tanka sunaso ayi rigima ne kuma yau ranar farinciki ne, shinkafa jaluf
akayi mai kyau sai faten tsaki, Amarya kuwa kawayan ta basu wuce mutum biyu ba suma
Abokanan karatunta ne suka samu labari dukda bata gayyaci kowa ba suko sunzo,
'Aisha ta Auri AK Dan gidan Alhaji muntari Naira, abunda yaron keta shela kenan
harya isa gidan, Kai zonan mai naji kana cewa bafa masan iskanci, inji Wata
makwafciyar suda ta damki hannun yaron tana shirin ingiza keyarsa waje, Wlh wlh
yanzu aka daura Auran Aisha da AK wannan baturan daya dawo kwanaki, yasin idan nayi
karya Allah tsinan, 'mikewa Aisha tayi bako kunyar Amare tareda jawo hannun yaron
cikin daki, 'ummah kinji fa abunda yake cewa, tafadi tana washe baki nan kallo
yakoma kanta, koda karya yakeyi yagama faranta mata ayau tunda ya danganta AK a
matsayin mijin Auren ta, nan mata akaita surutu ana karyata zancen, 'yo duk matan
garinga hauka yayi dazai Auri diyar unguwan nan, haba Malam banda ma haka GA yara
masu komai a unguwa kai dalla wuce kada in zabga maka Mari, inji wasu matan da abun
yafara kaisu bango, 'yauwaaa sannan babanku Ya'u mai shayi yafadi ana tunanin kamar
Maya rasu, 'salati aka dauka gaba daya nan kowa yagama yarda ya'u ya rasu, Ramata
kuwa tunda aka fara maganar kallon kowa dai'dai takeyi tarasa abun cewa koda aka
fadi Rasuwar ya'u ko motsi takasa yi nan aka dinga bata baki, ana haka Garbati ya
shigo tareda rokon jama'a akan subar musu dakin yanasan ganawa da Mahaifiyar Sa,
'zaure suka koma wasu kuma na zaune kofar gida a cewarsu sai sunga abunda zai ture
nadin buzu, 'kallon Aisha yayi yayinda ya kalla bilki, 'ki harhada duk wani abunda
Musa yakawo na Aure harda kayan fitan bikin dayayi ta cire wannan na jikinta a hada
da sauran a kawomun, sannan mama........babanku ya rasu koh Garba? Ta katse shi
tana kallon cikin idonsa, Allah ya gafarta masa mukuma Allah yabamu juriya da
tawakkalin rashin nasa, 'jikin shi yayi sanyi yayinda tunda abun yafaru sai lokacin
Yaji hawaye nabin kumatun Sa na tausayin mamar tasu da kannan shi, Wata irin mace
ce ita mai dakewar zuci? Bata taba bayyana sirrin Ranta, hannunta yakamo zaiyi
magana, 'tashe kuje a suturta shi akai shi gidan shina gaskiya, kukuma ku share
hawayen ku Addu'a zamu cigaba dayi, 'mikewa yayi zai fita saiya waigo tareda kallon
Aisha wacce ta hade kanta da guiwa tana kuka kasa kasa, 'An Daura Auranki da
Abdulkareem Dan gidan Alhaji muktar akan sadaki dubu hamsin, dukda tana cikin
tashin hankali saida ta dago ta kalli yayan nata idonta taf hawaye, murmushin ke
neman subce mata nanta maida kanta akan cinyar ta samun kanta tayi da mika
tawassali tareda godiya ga Allah Ashe AK Santa yakeyi?
Ashe ba ita kadai take dakon soyyar shiba?
ashe zata Kara tsintar farinciki a Rayuwar ta lokacin data cire ran samun murmushi
a duniyarta sai gashe bayan lokaci mai tsawo ta manta daduk kuncin ta dukda Rasuwar
mahaifin ta nanan daram a gefen zuciyarta amma murnar Mallakar AK ya shafe duk wani
kunci a tattare da ita, mikewa tayi kamar mahaukaciya tareda girgiza bilki datake
gabzan kuka, 'Auta Auta kinji mai yaya yake cewa? Auta Dan Allah ki mareni Auta ki
jijjiga ni dukda nasan ba mafarki nakeyi ba inaso in tabbata bani kadai naji Abunda
yake cewa ba, cewa fa yayi nazama matan Aure kuma AK na Aura, yaya AK na,
Auta Ashe AK zan Aura? Ashe sona yakeyi? Ashe shine ya Hana Musa Aurena yayinda
kaddara taso ta shiga tsakanina dashi, Ummah, tafadi tareda rarrafawa tana rike
kafan Ramata dake binta da kallo itada bilki gani sukeyi tadan samu matsala akanta
ubanta fa akace ya rasu yanzu amma tana murnan Mallakar namiji ko kunyar idonsu
bataji, 'ummah kice wani Abu mana, kinji, kinji umman mu, Kuka tafara yi mai sauti
inda kadan yarage Ramata tayi kanta da bugu ganin ta zube a wurin tana kuka mai
taba zuciya taji tausayin diyar nata yagama mamaye ta datasan matsayin ta a wurin
AK din datafi haka yin kukan babu Wanda ya lallashi wani cikin su Ramata kuwa babu
koda digon hawaye a idonta.

Ankai ya'u gidanshi na gaskiya saidai muce Allah ya gafarta mashi idan tamu tazo
Allah yasa mu cika da imani, yayinda Garbati yace baza'ai zaman makoki ba sanin
babu abunda za'ai a wurin sai gulman mamacin hakan yasa kowa ya watse badan rai
yaso ba, 'Mamie ceke tsaye a parlor sai zufa takeyi dankwali rike a hannun ta tunda
abun yafaru yan'gulma suka gaya mata komai tareda cikama wandon su iska gudun kada
Alhaji muktar yadawo ya samesu a gidan, bakaramin tashin hankali ta shiga ba inda
har kukan bakin ciki saida tayi ta kudiri aniyar saidai tarasa Auranta akan Auran
Aisha amma Sam danta bazai taba Auran Yar'duniya ba, shigowar Alhaji muktar neya
Kara tunzura ta da hanzari ta tarbe shi bakin kofan falo inda taita ruwan Masifa
tana zagin Ramata akan asiri sukayi banda aikin Asiri ina AK ina Auran Aisha? Ance
kwarya tabi kwarya ko cikin kwaryar bakowace kwarya bace tadace da dangatan danta
ba, Aikin banza aikin hofi wlh saiya Saki karuwan nan bazan Zama abun nunawa a gari
ba yarinyar da ubanta ke neman ta, 'kallon ta Daddy yayi tunda tafara haukan ta
baice mata komai ba kanshi na Sara mishi babu abunda yake bukata sai bcci a lokacin
dukda ana neman karfe biyar na yamma, wucewa zaiyi ta tare mishi hanya akan saitaji
dalilin tozarcin daya jamusu, 'cikeda takaici ya kalle ta sama da kasa, 'wai bilki
baki San mahaifin yarinyar nan ya rasu bane yau? Karona farko tun Auran su dataga
yamata irin kallon nan, 'toh sai me? Nice na kashe shi? Ina ruwana dawata Rasuwar
shi? Allah na tuba ai gara daya rasu koba komai an rage mugun iri a doran kasa, bai
dameni ba wlh yau yau sai an sakar musu da diyarsu, 'hankade ta yayi saida tafadi
akan kujera bayasan biye mata bare yadauki mummunan hukunci cikin fushi, yanufa
dakin sa yayinda yarage kayan jikin Sa, wai maiyasa mata wani zubin sukeda Karamar
kwakwalwa ne? Idan tanada magana dashi aiba haka ya kamata ta tunkare shiba yaushe
bilkin ta chanza Halinta ne? Shi za'a kawoma iskanci a cikin gidanshi aiko zaiyi
maganin ta daga ita har yaron nata Aure kuma zaiga ubanda ya isa ya raba shi muddin
yana raye.
Gogan kuwa yana chan yana harkokin Sa a cikin gari gaba daya gidan nasu baya mishi
dadi yanzu ya gwammace yabata lokacin Sa wurin business dinshi hakanan yau ya
tsince kanshi da Muguwar faduwar gaba harsaida ya gayama wani Abokin shi inda
yabashi shawarar yaita Addu'a kila Alkairi ne zai Same shi, hankalin shi gaba daya
ya karkata kan gida hakan yasa shida saura ya doshi unguwan nasu tunda matasa suka
hango motar shi nan akaita ihu ana daga masa hannu, Ango Angooo Angoooo kawai
kakeji suna fada suna shewa, mamaki yayi toh dawa sukeyi? ango? Kodai sunyi
tsammanin wanine bashi ba? Dariya yayi harda Jan tsaki yakara murza zaman hularshi
a kanshi, 'oooh mutane da rigima sukeyi kaji wai Ango nida ko budurwa bantaba yiba
naiman rigima kawai yawancin suma ban sansu ba, 'yafadi shi kadai, yana isa kofar
gida tunda yayi horn kafun mai'gadi ya bude mai tuni wasu sun biyo motarshi a baya
inda akan dole ya bude musu glass din motar cikeda mamaki, 'Ango kasha kamshi Dan
Alaji yaushe za'a hada mana walimar maza tunda Auran yaxo bawai an shirya bane,
'walimar maza? Ya tambaya cikin mamaki, 'au eh mana wacce akeyi bayan an daura Aure
mana, koda yake jeka huta muna nan munanan muna Sa ido Dan Allah kada a manta damu
Dan Alaji, wooooo sai Ustaziya yasin Allah barku tare, 'dayaga abun yazama hauka
Jan motarshi ciki yayi cikeda Al'ajabin samarin unguwar tasu, haka yafito ya rufe
motar jikin shi dukyayi sanyi, mai'gadi kuwa sai kirari yake masa tareda Addu'ar
Allah ya sanya Alkairi, 'wucewa yayi baiko bi takanshi ba inda yana shiga parlor ya
tadda Mamie ta buga tagumi da hannu biyu biyu cikin yini guda harta Dan fada saboda
tashin hankali, 'subhanallah Mamie lfy? Ya tambaya yayinda ya zauna kusada ita,
kallon shi takeyi idonta ya rine yayi jajir, 'AK kasan abunda babanku yaimana? Kaji
labarin tozarcin dayayi mana? Toh an daura maka Aure yau bayan sallar juma'a kasani
idan baka Sani ba kabude kunne kajida kyau kazama mai mata mai iyali, tafadi tareda
gyara zamanta harda buga cinyarta, 'dariya yayi har saida fararan hakoran shi suka
bayyana, haba Mamie wlh kema kin iya tsokana Auran lfy saikace yaro, 'riko hannun
shi tayi tareda kafa mishi ido babu Alamar wasa take kallon shi nan jikin shi yayi
sanyi ganin yanayin nata, 'Abdulkareem nataba maka irin wasan nan? Wlh yau aka
daura Auran kada Aisha diyar mai shayi, Mikewa yayi zumbur hadeda goge kunnansa
harda Dan bugawa a tunanin shi baiji dakyau bane, 'eye? Yafadi yayinda yayi jifa da
hular kanshi Mai kikace? Mikewa Mamie tayi hadeda maimaita mai abunda tace, 'chab
haba wasa yakeyi duk matan duniya?jada baya baya yakeyi, Idan hukuntani yakeyi
saboda naki Auran diyar Aminin Sa toh yanzu na yarda, Mamie Yammata nawa nema a
gidan? Sun kai hudu? Wlh idan dukansu yakeso in aura na yarda akan abunda kike
danganta nida shi, wlh ina sansu, ko Auran kauye ne aimun na Amince, kowacece na
yarda Mamie ina Dadyn? Yafadi yana waige waige waiko zaiga Dadyn a wurinda suke,
*Ina Dadyn?* yafadi cikin razanannan ihu har saida jijiyoyi suka furfuto akansa
idonshi kamar zasu fado kasa sai zaro su yakeyi sunyi jazur, 'shi maiyasa bai
aurota ata biyu ba? Maiyasa baiyi sadakatul jari'ar da itaba bayan yataba Aure?
Tunda yataba Aure maiyasa dasai yakara da bazawara why me??
Why?
Why?
Auran fari infara da bazawaran titi?
Haba!
Haba!!.
Bazawara duk mazan gari sun Santa fa, Ustaziyaar banza? Kirarinta fa kenan, wai
Ustaziya saboda yanda takeda fuska biyu, Ustaziya koko yar'duniya? yafadi yana
yarfa hannunsa duka biyun saikace zai Mari mamin, saidai shi Dadyn ya aureta wlh
sakinta zanyi Dan bata auru ba sai zaro mata ido yakeyi itako baki da hanci tasaki
tana kallon ikon Allah yayinda take girgiza kanta cikin bacin randa bata taba
tsintar kanta a cikin saba, ji takeyi kamar ta rufe shida duka, Dan ubanka AK ni
zakaima bakin ciki? da tsufa na kake mun fatan kishiya? Yaron nan bakada mutunci
kishiya kakemun fata da tsufana diyar cikina yarinyar Dana raina da hannuna? Lallai
ko kishin mamarka bakayi kakemun fatan babanku yakara Aure? Tafadi da Alamar
maganar ba karamin zafi taimata ba.
*Mrs Sadik Rumah💅🏻*
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Yah Rabbi duk inda na zaga duk inda na leka kowa Ustaziya harna rasa bakin Magana,
waya kona amsata babu iyaka messages kuwa na mutane har wayata na daukewa, shin ta
ina zan fara muku? Gskia mutum Rahama ne, nagode da Addu'ar ku a gareni masoya,
Ustaziya fans group kuna Sani nishadi Mara iyaka comments dinku na jiya naci
dariya, godiya gaduk masoyan Ustaziya makwaftan Aisha ina gaisuwa da kawayan ta
tace ace muku adaina kushe mata Angon ta hakanan take san abunta.🙏🏼😍*

*Dedicated to sister Husnah Amarya*

17

Kan Ya'u akayi ina rai yayi halinsa tuni nan aka dauki kabbara Allah sarki ya'u
ashe yanada rabon ganin Auran diyarsa Allah ya dauki Ransa a wurin daurin Auran
yar'sa, jama'a nata jimamin lamarin tun bare jarumtar da Alhaji muktar yayi, liman
yabada sanarwa da la'asar za'ai mai salla akai shi makwancin shi nan danan wani
yaro ya ruga gida batareda bata lokaci ba Amarya taci kwalliyar ta babu laifi tayi
kyau tasha lallan gargajiya inda babu wasu yan biki masu yawa sai makwaftar da
gulma ce yakawo su harda masu kawo mata gudunmawar maganin mata na Ni'emah maganin
matsi kuwa ankawo mata shi babu iyaka wasu saboda cin fuska kawai zasuzo suna mata
bayanin yanda zatayi matsi bilki ceke tanka musu yayinda Ramata ta kwabar musu kada
kowa ya tanka sunaso ayi rigima ne kuma yau ranar farinciki ne, shinkafa jaluf
akayi mai kyau sai faten tsaki, Amarya kuwa kawayan ta basu wuce mutum biyu ba suma
Abokanan karatunta ne suka samu labari dukda bata gayyaci kowa ba suko sunzo,
'Aisha ta Auri AK Dan gidan Alhaji muntari Naira, abunda yaron keta shela kenan
harya isa gidan, Kai zonan mai naji kana cewa bafa masan iskanci, inji Wata
makwafciyar suda ta damki hannun yaron tana shirin ingiza keyarsa waje, Wlh wlh
yanzu aka daura Auran Aisha da AK wannan baturan daya dawo kwanaki, yasin idan nayi
karya Allah tsinan, 'mikewa Aisha tayi bako kunyar Amare tareda jawo hannun yaron
cikin daki, 'ummah kinji fa abunda yake cewa, tafadi tana washe baki nan kallo
yakoma kanta, koda karya yakeyi yagama faranta mata ayau tunda ya danganta AK a
matsayin mijin Auren ta, nan mata akaita surutu ana karyata zancen, 'yo duk matan
garinga hauka yayi dazai Auri diyar unguwan nan, haba Malam banda ma haka GA yara
masu komai a unguwa kai dalla wuce kada in zabga maka Mari, inji wasu matan da abun
yafara kaisu bango, 'yauwaaa sannan babanku Ya'u mai shayi yafadi ana tunanin kamar
Maya rasu, 'salati aka dauka gaba daya nan kowa yagama yarda ya'u ya rasu, Ramata
kuwa tunda aka fara maganar kallon kowa dai'dai takeyi tarasa abun cewa koda aka
fadi Rasuwar ya'u ko motsi takasa yi nan aka dinga bata baki, ana haka Garbati ya
shigo tareda rokon jama'a akan subar musu dakin yanasan ganawa da Mahaifiyar Sa,
'zaure suka koma wasu kuma na zaune kofar gida a cewarsu sai sunga abunda zai ture
nadin buzu, 'kallon Aisha yayi yayinda ya kalla bilki, 'ki harhada duk wani abunda
Musa yakawo na Aure harda kayan fitan bikin dayayi ta cire wannan na jikinta a hada
da sauran a kawomun, sannan mama........babanku ya rasu koh Garba? Ta katse shi
tana kallon cikin idonsa, Allah ya gafarta masa mukuma Allah yabamu juriya da
tawakkalin rashin nasa, 'jikin shi yayi sanyi yayinda tunda abun yafaru sai lokacin
Yaji hawaye nabin kumatun Sa na tausayin mamar tasu da kannan shi, Wata irin mace
ce ita mai dakewar zuci? Bata taba bayyana sirrin Ranta, hannunta yakamo zaiyi
magana, 'tashe kuje a suturta shi akai shi gidan shina gaskiya, kukuma ku share
hawayen ku Addu'a zamu cigaba dayi, 'mikewa yayi zai fita saiya waigo tareda kallon
Aisha wacce ta hade kanta da guiwa tana kuka kasa kasa, 'An Daura Auranki da
Abdulkareem Dan gidan Alhaji muktar akan sadaki dubu hamsin, dukda tana cikin
tashin hankali saida ta dago ta kalli yayan nata idonta taf hawaye, murmushin ke
neman subce mata nanta maida kanta akan cinyar ta samun kanta tayi da mika
tawassali tareda godiya ga Allah Ashe AK Santa yakeyi?
Ashe ba ita kadai take dakon soyyar shiba?
ashe zata Kara tsintar farinciki a Rayuwar ta lokacin data cire ran samun murmushi
a duniyarta sai gashe bayan lokaci mai tsawo ta manta daduk kuncin ta dukda Rasuwar
mahaifin ta nanan daram a gefen zuciyarta amma murnar Mallakar AK ya shafe duk wani
kunci a tattare da ita, mikewa tayi kamar mahaukaciya tareda girgiza bilki datake
gabzan kuka, 'Auta Auta kinji mai yaya yake cewa? Auta Dan Allah ki mareni Auta ki
jijjiga ni dukda nasan ba mafarki nakeyi ba inaso in tabbata bani kadai naji Abunda
yake cewa ba, cewa fa yayi nazama matan Aure kuma AK na Aura, yaya AK na,
Auta Ashe AK zan Aura? Ashe sona yakeyi? Ashe shine ya Hana Musa Aurena yayinda
kaddara taso ta shiga tsakanina dashi, Ummah, tafadi tareda rarrafawa tana rike
kafan Ramata dake binta da kallo itada bilki gani sukeyi tadan samu matsala akanta
ubanta fa akace ya rasu yanzu amma tana murnan Mallakar namiji ko kunyar idonsu
bataji, 'ummah kice wani Abu mana, kinji, kinji umman mu, Kuka tafara yi mai sauti
inda kadan yarage Ramata tayi kanta da bugu ganin ta zube a wurin tana kuka mai
taba zuciya taji tausayin diyar nata yagama mamaye ta datasan matsayin ta a wurin
AK din datafi haka yin kukan babu Wanda ya lallashi wani cikin su Ramata kuwa babu
koda digon hawaye a idonta.

Ankai ya'u gidanshi na gaskiya saidai muce Allah ya gafarta mashi idan tamu tazo
Allah yasa mu cika da imani, yayinda Garbati yace baza'ai zaman makoki ba sanin
babu abunda za'ai a wurin sai gulman mamacin hakan yasa kowa ya watse badan rai
yaso ba, 'Mamie ceke tsaye a parlor sai zufa takeyi dankwali rike a hannun ta tunda
abun yafaru yan'gulma suka gaya mata komai tareda cikama wandon su iska gudun kada
Alhaji muktar yadawo ya samesu a gidan, bakaramin tashin hankali ta shiga ba inda
har kukan bakin ciki saida tayi ta kudiri aniyar saidai tarasa Auranta akan Auran
Aisha amma Sam danta bazai taba Auran Yar'duniya ba, shigowar Alhaji muktar neya
Kara tunzura ta da hanzari ta tarbe shi bakin kofan falo inda taita ruwan Masifa
tana zagin Ramata akan asiri sukayi banda aikin Asiri ina AK ina Auran Aisha? Ance
kwarya tabi kwarya ko cikin kwaryar bakowace kwarya bace tadace da dangatan danta
ba, Aikin banza aikin hofi wlh saiya Saki karuwan nan bazan Zama abun nunawa a gari
ba yarinyar da ubanta ke neman ta, 'kallon ta Daddy yayi tunda tafara haukan ta
baice mata komai ba kanshi na Sara mishi babu abunda yake bukata sai bcci a lokacin
dukda ana neman karfe biyar na yamma, wucewa zaiyi ta tare mishi hanya akan saitaji
dalilin tozarcin daya jamusu, 'cikeda takaici ya kalle ta sama da kasa, 'wai bilki
baki San mahaifin yarinyar nan ya rasu bane yau? Karona farko tun Auran su dataga
yamata irin kallon nan, 'toh sai me? Nice na kashe shi? Ina ruwana dawata Rasuwar
shi? Allah na tuba ai gara daya rasu koba komai an rage mugun iri a doran kasa, bai
dameni ba wlh yau yau sai an sakar musu da diyarsu, 'hankade ta yayi saida tafadi
akan kujera bayasan biye mata bare yadauki mummunan hukunci cikin fushi, yanufa
dakin sa yayinda yarage kayan jikin Sa, wai maiyasa mata wani zubin sukeda Karamar
kwakwalwa ne? Idan tanada magana dashi aiba haka ya kamata ta tunkare shiba yaushe
bilkin ta chanza Halinta ne? Shi za'a kawoma iskanci a cikin gidanshi aiko zaiyi
maganin ta daga ita har yaron nata Aure kuma zaiga ubanda ya isa ya raba shi muddin
yana raye.

Gogan kuwa yana chan yana harkokin Sa a cikin gari gaba daya gidan nasu baya mishi
dadi yanzu ya gwammace yabata lokacin Sa wurin business dinshi hakanan yau ya
tsince kanshi da Muguwar faduwar gaba harsaida ya gayama wani Abokin shi inda
yabashi shawarar yaita Addu'a kila Alkairi ne zai Same shi, hankalin shi gaba daya
ya karkata kan gida hakan yasa shida saura ya doshi unguwan nasu tunda matasa suka
hango motar shi nan akaita ihu ana daga masa hannu, Ango Angooo Angoooo kawai
kakeji suna fada suna shewa, mamaki yayi toh dawa sukeyi? ango? Kodai sunyi
tsammanin wanine bashi ba? Dariya yayi harda Jan tsaki yakara murza zaman hularshi
a kanshi, 'oooh mutane da rigima sukeyi kaji wai Ango nida ko budurwa bantaba yiba
naiman rigima kawai yawancin suma ban sansu ba, 'yafadi shi kadai, yana isa kofar
gida tunda yayi horn kafun mai'gadi ya bude mai tuni wasu sun biyo motarshi a baya
inda akan dole ya bude musu glass din motar cikeda mamaki, 'Ango kasha kamshi Dan
Alaji yaushe za'a hada mana walimar maza tunda Auran yaxo bawai an shirya bane,
'walimar maza? Ya tambaya cikin mamaki, 'au eh mana wacce akeyi bayan an daura Aure
mana, koda yake jeka huta muna nan munanan muna Sa ido Dan Allah kada a manta damu
Dan Alaji, wooooo sai Ustaziya yasin Allah barku tare, 'dayaga abun yazama hauka
Jan motarshi ciki yayi cikeda Al'ajabin samarin unguwar tasu, haka yafito ya rufe
motar jikin shi dukyayi sanyi, mai'gadi kuwa sai kirari yake masa tareda Addu'ar
Allah ya sanya Alkairi, 'wucewa yayi baiko bi takanshi ba inda yana shiga parlor ya
tadda Mamie ta buga tagumi da hannu biyu biyu cikin yini guda harta Dan fada saboda
tashin hankali, 'subhanallah Mamie lfy? Ya tambaya yayinda ya zauna kusada ita,
kallon shi takeyi idonta ya rine yayi jajir, 'AK kasan abunda babanku yaimana? Kaji
labarin tozarcin dayayi mana? Toh an daura maka Aure yau bayan sallar juma'a kasani
idan baka Sani ba kabude kunne kajida kyau kazama mai mata mai iyali, tafadi tareda
gyara zamanta harda buga cinyarta, 'dariya yayi har saida fararan hakoran shi suka
bayyana, haba Mamie wlh kema kin iya tsokana Auran lfy saikace yaro, 'riko hannun
shi tayi tareda kafa mishi ido babu Alamar wasa take kallon shi nan jikin shi yayi
sanyi ganin yanayin nata, 'Abdulkareem nataba maka irin wasan nan? Wlh yau aka
daura Auran kada Aisha diyar mai shayi, Mikewa yayi zumbur hadeda goge kunnansa
harda Dan bugawa a tunanin shi baiji dakyau bane, 'eye? Yafadi yayinda yayi jifa da
hular kanshi Mai kikace? Mikewa Mamie tayi hadeda maimaita mai abunda tace, 'chab
haba wasa yakeyi duk matan duniya?jada baya baya yakeyi, Idan hukuntani yakeyi
saboda naki Auran diyar Aminin Sa toh yanzu na yarda, Mamie Yammata nawa nema a
gidan? Sun kai hudu? Wlh idan dukansu yakeso in aura na yarda akan abunda kike
danganta nida shi, wlh ina sansu, ko Auran kauye ne aimun na Amince, kowacece na
yarda Mamie ina Dadyn? Yafadi yana waige waige waiko zaiga Dadyn a wurinda suke,
*Ina Dadyn?* yafadi cikin razanannan ihu har saida jijiyoyi suka furfuto akansa
idonshi kamar zasu fado kasa sai zaro su yakeyi sunyi jazur, 'shi maiyasa bai
aurota ata biyu ba? Maiyasa baiyi sadakatul jari'ar da itaba bayan yataba Aure?
Tunda yataba Aure maiyasa dasai yakara da bazawara why me??
Why?
Why?
Auran fari infara da bazawaran titi?
Haba!
Haba!!.
Bazawara duk mazan gari sun Santa fa, Ustaziyaar banza? Kirarinta fa kenan, wai
Ustaziya saboda yanda takeda fuska biyu, Ustaziya koko yar'duniya? yafadi yana
yarfa hannunsa duka biyun saikace zai Mari mamin, saidai shi Dadyn ya aureta wlh
sakinta zanyi Dan bata auru ba sai zaro mata ido yakeyi itako baki da hanci tasaki
tana kallon ikon Allah yayinda take girgiza kanta cikin bacin randa bata taba
tsintar kanta a cikin saba, ji takeyi kamar ta rufe shida duka, Dan ubanka AK ni
zakaima bakin ciki? da tsufa na kake mun fatan kishiya? Yaron nan bakada mutunci
kishiya kakemun fata da tsufana diyar cikina yarinyar Dana raina da hannuna? Lallai
ko kishin mamarka bakayi kakemun fatan babanku yakara Aure? Tafadi da Alamar
maganar ba karamin zafi taimata ba.

*Mrs Sadik Rumah💅🏻*


🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
🏼🏼🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Ina kuke yan hannun dama na🤝🏻godiya Mara iyaka sister futu marubuciyar Ramlat,
tareda Asiyar Bachaka marubuciyar Danasani keya, leemat muna jiran sabon
novel.Nagode sosai da kaunar ku a gareni.*

*Dedicated to sister Husnah*

18

Babu abunda zai hanani sakinta yanzun nan kuwa, juyawa yayi yayinda sukayi ido Biyu
da Alhaji muktar Wanda hayaniyar su yafito dashi daga daki duk abunda suka tattauna
akan kunnan shi, AK na shirin Gilmawa Yaji daddy na fadin, 'bazan hanaka sakinta ba
kamar yanda ban naimi shawarar Aura maka ita wurin kowa ba haka bazan tilasta maka
Zama da ita ba tunda ka nuna ban isa dakai ba shikenan nikuma zan nuna isata a inda
na isa, kallon Mamie yayi ita mai zugakan tareda Aisha zasuyi zawarcin kasan da
sanin datse igiyoyin Auran Aisha daidai yakeda mutuwar Auran Bilkisu mamarka, a
razane Mamie ta kalla daddy yayinda takarasa wurinsa, wai wace bilkin kake magana
Alhaji? Ban gane ba badai ni Bilkisu ba? menene hadin Aurena Dana AK? Jama'a aimun
Adalici mana Lallai Alhaji kamar bakai ba nice fa bilkin ka yar'fulanin ka shakara
kusan Arba'in muna tare ko daga mun murya baka taba yibafa, tafadi jikinta na rawa
yayinda hawaye daya nabin daya a idonta....'yauwa sannan kana sakin Aishar ni zanyi
sadakatul jari'ar da ita insha Allah bazaku maidani karamin mutumin banza ba
dattijon banza Wanda bai isada gidanshi ba kunji na rantse muku, AK kuwa mutuwar
tsaye yayi cikeda takaicin Daddy Anya daddy ne kuwa? Idan shine kuma maiya same
daddy a'yau? Daddy na shirin barin wurin mamie ta fada a kirjin shi tareda sakin
kuka mai cin rai, Ashe zaka iya Rayuwa batare dani ba? Ashe akwai Ranarda ko'a
mafarki Zaka iya dangantani da kishiya? Wlh ban zuga AK ba harga Allah mijina babu
abunda yarinyar nan ta taba mun Allah yabasu zaman lfy tunda abun yazama haka wlh
kowa ya gyara Auran shi bazan bari Aurena ya mutu ba saboda na wani, 'dariya taso
taba daddy dakyar ya iya gimtse dariyar Sa, 'haba mamie wlh an cutar dani kada
kimun haka, inji AK dayake tunkaran iyayan nashi, 'wlh Abdulkareem kowa yaje ya
gyara Auran shi bazan koma gida yin zawarci da tsufa naba bayan haka inasan tsohon
mijina ban hadashi da komai ba a duniya dukda ina sanku banda kamarku amma sanku
bai isa ya kashe mun Aure naba tareda rugujemun soyyar shekara Arba'en danayi ba,
Kara Rungume ta Daddy yayi a jikin Sa cikeda kaunar matar tashi, Yauwa yanzu ne
bilkin shi tadawo bilki amma da dukta rikice an birkita mishi mata, Sakinta yayi
yayinda ya tunkari dakinsa, 'Dadyn su Abdul na tuba Dan Allah kayi hakuri mai
gidana, tafadi harda daga muryar ta, baiko waiwayo ba bayaso ya nuna mata ya sauko
dawuri saiya Dan Kara gasata nan gaba bazata Kara jayayya da hukuncin saba, 'AK
barin wurin yayi yayinda ya shiga dakinsa da hanzari ko ganin Gabansa baiyi sosai
cikin minti Uku yafito da karamar jakar kaya a hannun Sa, 'Yau saika haifi da'mai
bakin ciki? Inji Mamie tana kallon AK na saukowa daga steps, 'ina Zaka? Muddun ka
dauki hukunci akan Yarinyar nan bazan taba yafe maka ba Abdulkareem kaji na gayama
wlh Aure da ita kasama ranka kamar kafara ne mutu ka raba kaida ita muddun ina
numfashi idan ba haka ba kuwa bazan yafe maka ba, Aure baifi Aure ba, 'tuni AK
yabar gidan cikin motarsa kamar zai tashi sama kanshi kuwa kamar zai fashe tuni
zazzabi da ciwon kai mai zafi ya rufe shi dakyar ya iya karasawa 17th hotel tareda
kama daki na kwana uku, cikin rawan sanyi ya zube akan gadon dakin kuka ya fashe da
karfi kamar mace yana dukan gadon a hankali, 'why Aisha? Why cikin mata maiyasa
saike? Maiyasa kika koya mun muguwar tsanarki? Maiyasa? Dukda na guji rayuwarki
maiyasa kika sake shiga duniyata tareda zaban Rayuwa dani? Kin cutar dani Aisha wlh
bazan yafe miki ba bani kadai zan rayu da bakin ciki ba dukanmu mun rasa abunda
mukeso daga rana tayau dukanmu zamu rayu cikin kunci wlh zan dandana Miki kunci
kwatankwacin Wanda kika Sani a ciki, maiyasa zanga Aibun ki? 'Yah Rabbi ka sassauta
min Aisha a cikin zuciyata, ka rage mun ita ta dameni, kuka yakeyi yana rawan sanyi
jikin shi kuwa kamar garwashin wuta saboda zafin zazzabi.

Mamie kuwa wanka ta dauka tareda tsara girki mai matukar dadi cikin gaggawa ada ta
kudiri niyyar babu Wanda zaici abincin Dare a gidan saboda Auran AK harsai an mata
abunda takeso shiyasa tun kafun daddy ya farga batayi girki ranar ba ta shiga cikin
hanzari tayi, Abdulhakeem kuwa yana makaranta achan Egypt gidan babu kowa sai masu
aiki da Mijinta hakan yasa ta tunkari dakin shi domin Kara lallashin Sa sai kamshi
take zubawa mai tsayawa arai.

Washe gari kuwa karfe goman safe ta shirya cikin shiga ta Alfarma yayinda itada
masu aikinta dake dauke da manya manyan kuloli shake da Abincin sadaka Wanda tun
daran jiya tasasu dafawa da asuban farin yau, Abinci ne mai rai da lafiya haka aka
daddauki kulolin da kwalayan lemuna da ruwan gora katon katon kai tsaye gidan
Rasuwa suka nufa hakan datayi ba karamin Kara soyyar ta yayi a zuciyar Alhaji
muktar nanda nan tausayin matarshi ya shige shi ganin yanda take matukar tsoran
rabuwa dashi, 'Cikeda mamaki Ramata ta tarbe su hannu biyu biyu a kasan Ranta kuwa
taji dadi sosai sai a lokacin hankalinta yadan kwanta kwana tayi da tunanin yanda
Rayuwar marainiyar yar'ta zai kasance a gidan Alhaji muktar tareda kallan da Mamie
zatai musu, samun kanta tayi da washe baki hadeda godema Allah a fili, mikewa Aisha
tayi tana gaishe da mamie har kasa ta tsuguna cikeda kunya zata bar dakin Mamie ta
rike hannun ta tareda zaunar da ita kusa da inda take, 'gaisuwa Tai musu na rashin
da sukayi sosai itada ja'maar gidan ta sannan tace musu Alhaji muktar yace akara
musu gaisuwa mika ma Ramata Envelope tayi cikeda kudi a cewarta Alhaji muktar
neyace abata, kememe Ramata taki Amsa da ada ne Amsa zatayi amma yanzu bataso suga
kwadayin su tunda anzama sirikai kada ace sun siyarda yar'su, dakyar da sudin goshi
aka samu Ramata ta Amsa harsaida mutane sukasa baki a cewarsu ta Amsa a matsayin
sadaka ba'a maida kyauta, nan yan'unguwa akaita shigowa kwasar abinci mai raida
lafiya tunda sukaga shigan kayatattun kulolin Abinci da Hajiya bilki nan akaita
shigowa har babu wurin Zama kamar an bada sanarwan jama'a, Mamie tayi minti
ashirin a gidan yayinda ta Mike zata tafi, riko hannun Aisha tayi tace ta biyo ta
zasuyi magana, kiran Ramatan tayi har waje suka shiga bayan motan ta saboda jama'a
dake wucewa, 'Aisha kokuma ince diyata tunda yanzu anzama daya, Dan Allah ki gani
kiki gani, duk abunda zai shiga tsakanin kida AK kiyi hakuri kada ki biye mishi ki
daure kuba Mara da' kunya Yanzu kowa jira yake aga yanda zakuyi kada ki biye mishi
duk abunda zai miki kiyi hakuri kodan saboda ni kinji diyata? Harda rikema Aisha
Hannu wacce kunyar duniya tagama rufeta, duk abunda ke damunki ki gayamun ki
daukeni a matsayin uwa keda AK mutu ka raba insha Allah nanta roki Ramata Alfarman
Kara tausasa Aishar inda sukaita godiyar jin dadin Abunda hajiya Bilkisu tayi nan
duka bakin cikin Ramata ya yaye koba komai Aisha tayi dacen surukai ta fannin AK
mai sauki ne dama ganin yanda AK din ya tsani Aishar da furicin dayayi a gabanta
babu ko kunyar ta a matsayin Mahaifiyar Aishar shike hanata sukuni.

Aishi kuwa dukta kosa ayi sadakan bakwai akaita gidan mijinta masoyinta ji takeyi
kamar ace ta tashi ta naimo shi ta bishi, gawata azabar soyyar shida ta Mike mata
kullum cikin murmushi zaka ganta batada damuwa ko kadan Yanzu ko bcci takeyi sunan
AK take kira mafarkin AK babu Wanda batayi harsai Ramata ta girgiza ta ko bilki,
abun yafara damun Ramata inda cikin takaici tafara tankama Aisha, Kidai yi a
hankali wlh ba baki nai miki ba muddin kika nunamai soyyar nan zaki sha bakar
wahala ace ayi mace ba kunya wannan wace irin Rayuwa ce kika daukan ma kanki dakon
soyyar wahala? 'Ummah wlh yayi AK na sona kila fiyeda yanda nake sanshi, 'haka ya
gaya miki? Yaushe kika ganshi? Koko sako ya aiko miki na soyyar taki? Kidai yi a
hankali banasan hauka da rashin kamun kai, 'Idan Ramata tayi furucin nan Haushi
Aishar keji sosai, hakan yasa tafara lallaba Auta bilki akan ta leka mata kofar
gidansu AK ko zatagan shi tanaso taga ko yana lfy kwana biyu tarasa sukuni tanasan
sanin lafiyar mijinta? Kai tsaye bilki tace mata bazata jeba aiko nan taita dukan
bikin cikin takaici, 'wlh Anty kozaki kashe nine babu inda zanje ni wlh haushi yake
bani ma ace ko gaisuwa yakasa zuwa yayi mana sirikin shiya rasu haba Dan Allah, 'ke
mai kika Sani? Gaisuwa banda Wanda mamarshi taxo tayi a madadin shi? Harfa masu
Aikin gidan su sunzo mana gaisuwa da tarin Alheri mai yawa, 'Ramata dake girki a
zaure tashi tayi cikeda takaicin Aishar shiga dakin tayi mafici ta dauka ta buga ma
Aishar, sannu dadi miji saikije gidan nasu ki bishi, fitar min a daki Mara kunya
Kifa kiyaye ni Aisha wlh ranki zai baci akan yaron nan, turo baki Aishar tayi tana
gunguni, mutum da mijinsa sai a hanashi jin yanda yake? Gskia baai mata Adalci gara
tayi tayi tabar musu gidansu.

Alhaji muktar neya sauko daga dakin shi misalin karfe sha'biyu na rana yana shirin
fita, kwalama Mamie dake kitchen tareda yan aiki suna girki kira yayi, 'amsawa tayi
hadeda shigowa parlon nasu Zama kusa dashi tayi, Dadyn su Abdul harka shirya Ashe,
'Eh zan Dan fita nisa zanyi sai yamma zan dawo insha Allah, Allah ya dawo dakai lfy
mai'gidana Angona ni kadai ta furta cikin murmushi, mikewa yayi sannan ya kalleta,
'danki bai dawo daga gudun hijirar dayayi bane? 'Uhm bari kawai lamarin AK sai a
hankali wlh haryau babu labarin shi mamaki yake bani sati daya babu shi Anya Alhaji
ko za'a bada cigiyar sane? Duka wayoyinsa a kashe office ma yadaina zuwa, 'bawata
cigiyar katon Saurayin dazan bada yanda ya dauki kafa yabar gida toh zai dawo da
kafarsa, idan yadawo kice ya gaggauta barin mun gidana nima, Ga mukullin gida na
Wanda ke Malali GRA ba'a Dade da kammalawa ba ki bashi ya tarkata yanasa yanasa
chan zasu zauna kafun in kai masa matarshi insha Allah.

*Mr's Saddiq Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Alhmdlh nadawo nagode da Addu'ar ku masoya, Gskia banyi niyyan posting yauba but
Alkawarin danayi shiyasa kuka jini masu kirana suji lfy ina godiya sosai😍, Zaku
cigaba dajina insha Allah daga yanzu*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah*

19

Ak kwance yake akan gadon dakin hotel dinda yakama a yanzu gadon baida banbanci
Dana asibi saboda tun daga ranar daya sauka a dakin ciwo yaita yi kamar bazai kai
labari ba family doctor dinsu yakira nan aka Dora mai ruwa babu yanda likitan baiyi
akan zaifi samun kulawa a Asibiti Sam yaki yarda yayinda yaima doctor din kashedi
mai tsauri akan bayasan iyayanshi Susan inda yake harsai sun neme shi, kimanin
kwana Tara kenan yana kwance a dakin dukya fige ya rame sai uban farin daya Kara
likitan ne atare dashi yayinda yagama zarkada masa Allurar karshe daya gama Amsa a
ranan kashedi yaimasa akan yarage tunani domin yana gafda kamuwa da ciwon zuciya
banda hawan jinin dayake dashi a halin yanzu, godiya yaima doctor din nan yafara
hada yanasa yanasa a cewarsa ko mutuwa zaiyi gara ya mutu a gaban iyayan shi ba'a
dakin hotel ba dukda bawai ya yafe musu cutarshi da sukayi bane😡aa zaidai koma ne
kila a yanzu sunyi nadama sun kuma San zafin rashin Sa a kusa dasu, misalin karfe
Tara na Dare ya shigo falon nasu yayinda yake tafiya kamar Wanda kwai ya fashe ma
aciki hannun shi rikeda jakar gudun hijirar Sa, Daddy da Mamie na zaune a parlor
suna kallo cikin nishadi kallo daya zakai musu ka tabbata basuda damuwa, sallamar
sane yadawo dasu nan Mamie ta Mike da sauri ta tarbe shi tana salatin ganin yanda
ya rame shiko gogan Kara murtuke fuska yayi adole fa anmai laifi, wani irin ciwo
kayi haka ka ganka kuwa? daddy kuwa kallo daya yaimasa ya kauda idonshi ya cigaba
da kallon shi, 'Ciwo kayi ne AK ka ganka kuwa? Kanaso ka halaka kanka akan abunda
bai taka Kara ya karye bako? Tafadi rikeda hannun shi har bakin kujerun parlorn
kememe yaki Zama a kujerar, 'yanaga kadawo dawuri? Koko sauran kayan ka kazo kwasa?
Aida bakaxo ba saika yi waya idan yaso maba bireba yakawo maka sauran kayan inji
Alhaji muktar yayinda ko kallon AK baiyi ba, shiko wani takaici yakara turnuke shi
ganin iyayan shi sun daina sanshi da tausayin shi duk akan wata shegiyar Aisha,
'dukda haka bata baci ba zan yarda kayi kwanan karshe a cikin gidana, naba mamarka
makullin daya daga cikin gidajena kaje chan ka zauna insha Allah nakusan kawo maka
iyalin ka, 'nifa banda kudin dazan iya zuba kaya a cikin gidan, inji AK
Cikeda mamaki Mamie ta kalle shi wai AK ne baida kudi, 'Karka damu ai ninaga
zan iya nasa muku duk wani abunda zaku bukata a matsayina na Uban Amarya uban Ango
kuda akaima Auran gata? Lefenka ma ake hadawa bana bukatar ko kwandalar ka, ahtoh
daddy yafadi yayinda AK ya wuce daki kai tsaye cikin takaici.

AK ya tare a dankareran gidan su Wanda ya hadu ya hadu ya hadu harya gaji da


haduwa, gidan ba gidan sama bane four bedroom ne manya manya sai katotan parlor
Guda daya a tsakiyar dakunan yayinda kowane daki yanada bayi harda parlor kowani
daki saida a zuba furniture's hadaddu parlor kuwa Royal kujeru ne har set biyu sky
blue da Orange, sai barayin dinnin dinda aka kewaye shida transparent glass komai
na wurin white ne gskia dady ba karamin kudi ya zuba a gidan ba, hmmmm sai Wanda
yagani bari inyi shiru kada ace zan zuba karya🤭.

Mamie ce ta aika gidansu Aisha aka amso measurements din kayan ta da size din
takalmi da undis nan aka hada mata lefen ta mai rai da lafiya akwati set daya
yayinda aka dinka kayan ciki sosai bayan an kwana biyu Mamie da kanta tazo da
direba inda ta dauki Aishar basu zame ko'ina ba sai babban boutique English wears
taita jidan ma Aishar a cewarta so takeyi ta rikita AK tanaso taga yazo ya durkusa
yana musu godiya akan aura mishi Aishar da akayi kunya ta cika Aishar inda take ji
kamar ta nutse a kasa, kaya ne naban mamaki masu daukar hankali ko kunya Mamie
bataji ba nanta dinga gayama Aishar kissar mallake miji cikin dabara saikace ba
sirikarka ba, itako Aishar jinta takeyi a sama duniyar ta fes, tun daga ranar
Kullum da safe zatazo ta dauke ta takaita wurin gyaran jiki na amare, hmmmm Allah
sarki Naira, cikin kwanaki Uku kachal Aisha tayi masifar kyau naban mamaki tayi
fresh color dinta yakara fitowa gashin nan ba'a magana yayinda akaita dura mata
maganin mata a zuciyar Mamie kuwa sotake AK yayi har kukan Agwagwa Ranan 1st 9yt😉
oooh su Mamie iyayan Zamani, ranar karshe Kunshi akakai Aisha akai mata baki daja,
hmmmmmm Kara gyara mata kanta akayi inda Mamie ta hadata da turaruka masu matukar
kyau da motsa Sha'awa, sai wurin la'asar suka dawo nan take shaida ma Ramata akan
daddy zaizo karfe Tara na Dare shi da kanshi zaikai Amarya dakin ta ba'a bukatar
yan rakiya idan yaso bayan an kwana biyu sai aje aga daki, Hmmmm zo kuga bakin
Aisha har saida yakusa yagewa saboda murnar zata kwana da masoyin ta ayau, tunda
yamma Ramata ta hada mata ruwan wanka na turare kala kala, nanfa Aisha abun naima
yasamu taita durzan fatan jikin ta a cewarta ayau zata fara hada jiki da Rabin
Ranta muradin ta AK, shiru kakeji kamar an aiki bawa garinsu yayinda Ramata take
shirin binta bayin sugani ko wani wabu yafaru ne ko nakuda takeyi ai ya isa ace ta
haihu Yanzu inji Ramata, haba har ana shirin shin sallar Isha'e, Aisha kuwa badan
taso ba ta fito kassncewar ruwan yakare kuma fatar jikinta yafara zafi durza yasha
bana kadan ba, 'harara Ramata tabita dashi, aina zaci bcci kikayi a bayin, Kota
kansu batabi ba tafara kwalliya mai daukar hankali tana rera wakar soyya cikin
nishadi.

"So bai karewaaaa


"So bai chanzawa aaa
"Wanda nake kauna "da'eman fa bazai "chanza baa gani gaka, harda rufe fuska a dole
tanaba kanta kunya, bilki kuwa daga uhmm sai uhm uhm, suna ganin ikon Allah, turare
taita sawa kala kala saida bilki ta kwace kwalbar a hannun ta, nan tasaka wani
dankareran red lase dinda yagaji da haduwa cikin kayan lefenta Mamie ta bata dazu
tace shi zatasa idan za'a kaita, lefenta tuni ankai mata gidanta ko ganin shi
basuyi ba a cewar Mamie Sa gani achan gidan, wow bilki ke cewa ita kanta yayar Tata
tamata ba kadan ba ko makiyin ki wlh Anty Aisha idan yaganki saiyace shegiya amma
fa tayi kyau, mayafin kayan tasa Wanda keda digo digon baki tareda flat shoes tasha
dankunne ta sarka da zobe harda agogo da warwaro sak Amaryar masu kudi sunan da
bilki tasa mata kenan a lokacin, 'Ramata da garbati sai santin ta sukeyi saikace ba
ita ba lallai kudi sunyi, nan sukaita mata nasiha da fada mai shiga zuciyar mai
sauraro inda Ramata keta kukan rabuwa da murnar Aurarda Aisha, itako Aishar batama
San sunayi ba dukta kosa daddy yazo inda Rabin fadan dasuke mata ke shiga kunnan ta
ya fita ta dayan kunnan jefi jefi tana Satan kallon agogo wurin karfe Tara saura,
maiya tsaida Daddy? Itafa takosa akaita taga mijinta, 'toh Kidai rike maraicin ki
kinsan wacece ke basai na tuna miki ba mu talakawa ne lis bamuda gata saina Allah,
ke ai ko ba,ai miki fada ba ya isa kima kanki ganin irin Rayuwar da mukeyi har a
unguwan nan, hakuri Aisha, Hakuri bazan daina maimaita miki ba, kiyi hakuri,
girgiza kai kawai takeyi cikin mayafi sai a lokacin ne ta matso jaririn kwallar
rabuwa da yan'uwanta bilki kuwa kuka takeyi kamar zata suma saika rantse itace
Amaryar dukta kankame Aisha, aikowa akayi daddy yazo daukar ta, inda dakyar garbati
ya sashi shigowa suka gaisa sama sama da Ramata daketa zuba godiya da kuka, rike
hannun ta bilki tayi inda ta bude mata bayan motan ta zauna yayinda daddy ke zaune
gaban mota shida driver dinshi, Inda akace bilki zata kawo mata kayan da akai mata
anan zuwa jibi insha Allah,motar na tashi ta tsinci kanta da muguwar faduwar gaba
tareda fargaban yanda daren nasu nayau zai kasance itafa tsoro takeji Allah yasa AK
ya bita a hankali saboda tataba ji Wata yar'islamiyyar su tana bada labarin 1st 9yt
dinta idan tace har saida ta suma, hmmmm nan takara rikicewa tana Addu'ar Allah
yasa mijinta yabita a hankali.

Bakaramin rikitata gidan nata yayi ba ko'a duniyar mafarki bata taba gani da zuwa
irin gidan nan Wanda harya gaji da haduwa ba bare kuma ace nata ne, ooh Allah kenan
Dare daya yakanyi Bature, da Addu'a ta shiga gidan kamar yanda Ramata ta umarce ta,
wani sanyi AC neya ratsa su yayinda gogan ke kwance nashe nashe yana shan madarar
shanu mai kyau cikin kwanciyar hankali yake kallon American movie dinshi sanye da
kananan kayan shan iska su matukar yimai kyau, mikewa yayi tareda gaishe da daddy
cikin fa'raa da murna kamar bashi ba, shi kanshi daddy yayi mutukar mamakin sauyin
AK, kodai ya dangana ne? Inji daddy, idan ma bai dangana ba dole zaiyi kuwa, a
zuciyar shi yake fadi yayinda AK da Aisha ke zaune a kasa daddy nakan kujera,
nasiha yayi musu mai shiga jiki tun bare AK yaita tausasa shi har saidaga karshe
yatashi ya Mike tareda kallon Aisha, 'zan aiko miki da waya na tambayi mamarku tace
bakida waya zansa miki number na a ciki, zan dinga jin yanayin zaman naku ko kallon
banza yaimiki Wanda zuciyar ki bata amince dashi ba kiyi gaggawan sanar dani, Allah
yaimiki Albarka yabaku zu'ri'a dayyiba, kaikuma ina jiranka ka aiko min da gawarta
domin yanzu mun Riga Munsa kafar wando daya ni dakai, 'subhanallah daddy Dan Allah
kayi hakuri nayi nadamar abunda naimuku kaida Mamie insha Allah babu Wanda zaiji
kanmu katayani ba Mamie hakuri idan an kwana biyu zamuzo sai in Kara bata hakurin,
cikin jin dadi Dady yace, 'a'a kuyi zaman ku kada kaje ko'ina ku huta Sannan kuzo,
fita daddy yayi yayinda AK yatafi mai rakiya, tunda suka fita takara gyara mayafin
kanta a cewarta angon ta ne zai yaye mata kamar yanda akeyi a Al'adance, shiko AK
tun shigowar ta parlon turaren ta yagama susuta shi wani irin turare ne wannan? Kai
waya bata? Gskia kamshin shi yamasa jiki a mace ya shiga parlon.

*Mrs Sadik Rumah💅🏻*


🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
🏼🏼🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah*

20

Tanajin motsin shigowar Sa takara natsuwa dakin shiya wuce kai tsaye Kota kanta
baibi ba, inda shiru shiru babu ango babu labarin Ango kafarta harta fara tsamin
gajiyar Zama gawata yinwa datake ji rabonta da abinci tun rana saboda zumudi batama
wani ci sosai ba a cewarta yau zataci kazar amarci, har karfe sha'daya darabi shiru
tana zaune a wuri daya inda sai a lokacin hankalinta yakara tashi toh kodai ya
manta an kawo mishi Amaryar sane? Gashi taga yakara mata wani masifar kyau dukda ta
cikin mayafi ta kalle shi, shiko gogan yana kwance nashe nashe akan gado sai
chatting yakeyi a Facebook tareda frnds dinshi hankali kwance inda kamshin turaran
ta daya shaka duk yabi ya hanashi sukuni, tsaki yaja a karo ba adadi tareda mikewa,
gskia dole in nema matar mutunci in Aura mutum shi kadai kullum Ga Sha'awa hakurina
yafara karewa shekara talatin da biyu ba wasa ba, ya furta parlon ya wuce ta inda
ya dinga bin wutan gidan yana kashe wa haryazo kanna parlon, kashe kayan kallo yayi
harya kashe wutan parlon ta Mike ganin baisan da halittar taba, 'Yaya AK, tafadi
cikin hanzari ta Mike,Yaya..tasamu kanta dajin nauyin shi inda lokaci daya ya tsaya
yana Kare mata kallo hadeda kunna wutan parlon, 'ya akayi? Menene? Jarabarki ta
motsa ne?? Ooooh ba haka kikai tsammani bako? Kin saba jin namiji kwance akan
cinyarki wace irin Amarya ce wannan? Banda iskanci harkin fara nema na uwar mai zan
miki Wanda ba'a taba miki ba? Look bari in kankara miki warning na farko yafadi
yana nunata da yatsa, nidai ba mazinaci bane asalima ko yatsar Wata macen ban taba
rikewa ba ma'ana ni tsarkakekke ne tas Alhmdlh, sannan ni bantaba cin diyar Wata
ba, duk Randa kika Kara mun magana kiyi kuka da kanki kada kisake kiyima kanki wani
kallo na daban a cikin gidan nan, kisama ranki kinzo a lokacin bayi, rayuwar bauta
zakiyi idan nace miki yar'aiki toh kinsamu promotion, noooo noooo ke baiwace black
monkey kawai wawiya mazinaciya mai fuska biyu simi simi kamar mutuniyar Arziki
idonshi harya fara rinewa yayinda Aisha kafarta Sam takasa daukarta hawaye daya
nabin dayan jikinta na wani irin rawa yayinda zufa yagama wanke ta dukda sanyin AC,
takowa yayi har gabanta murmushi kwance akan fuskar shi wuyanta ya shako hadeda
dago kanta yana mata kallon kiyayyah, congratulations na tayaki murnar samun namiji
Irina Wanda babu kamarsa amma kamar yanda zaki fara ganin babu kamana a mugunta,
congratulations daga rana tayau kunyi bankwana da farinciki a duniyar ki, ina
tayaki murnar sabuwar rayuwar bauta, kakari tafara cikeda azaba nan yayi wurgi da
ita kan glass cup dinda yagama shan fresh milk bakaramin bugewa tayi a kanta ba,
juyawa yayi sannan yakara dawowa, 'Akwai mai gadi na dattijon Aziki ina neman
Alfarman kada ki bata tsohon mutane domin mijin marigayiya ne ance kefa jarabar
taki har tsofaffi baki bari ba, kiyimun Alfarma iskancin ki ya tsaya a waje banda
yan aikina wlh wlh zan iya kashe ki har lahira Randa na kamaki dawani a gidan nan,
sannan inada masu bama flowers ruwa damai wanke mun mota, congratulations a dalilin
ki kinsa sun rasa aikin su bazan barki da gattin samari masu jini a Jika a cikin
gida ba kamar naba kura Ajiyar nama ne, 'kanshi yadaga Alamar yana tunani chan
yadawo ya tsuguna yadago fuskarta da hawaye yagama wankewa, 'bazan taba baki damar
kizama karuwar gida ba kada kazantar zunibin kiya halakamu baki daya, idan jarabar
kita motsa kinsan inda zaki GA kwartayan ki, Wuceta yayi hadeda rufe bedroom dinshi
harda Sa mukulli a cewarshi kada taimasa fyade tunda ankawo ta cikin maza babu
abunda bazata iya ba.

Anan ta kwanta kanta dukya kulle tarasa abun yi inda sai wurin biyun Dare ta Mike
taci kuka harta gode Allah taita shiga sauran dakunan harta gane dakin ta saboda
ganin hadaddun akwatunan lefen ta, komai na dakin dark purple ne yayi matukar kyau
amma Sam bai burge taba Yanzu dama ba Auran soyya tayi ba? Mai AK ke nufi?? Dukda
taji matukar takaicin abunda yaimata amma soyyar shi nanan daram dam a zuciyar ta.

Tun daga ranar tafara aikin bauta a gidan, AK ya kori matasa masu gyara gidan a
cewarsa ankawo kura cikin garkin nama kudin sallama yabasu sosai nan aikin gidan
yadawo kanta mace da wankin mota harda gyaran flowers idan tatashi tun asuba bata
Kara komawa bcci, idanko tayi lattin wanke mai mota ranar hmmm bakaramin duka zata
Shaba, idan yadawo ya taddata tana bcci kuwa ruwan sanyi mai kankara zai dinga
watsa mata tijara iri iri babu Wanda bata gani ba nan tasa mai suna *farin mugu na*
ta tsani AK amma a iya bakin ta, kullum muguwar kaunarshi ke samun masauki a Ranta
duk yanda tayi kokarin fito na fito da zuciyarta abun yaci tura, Babu Wanda yasan
halinda take ciki sai bilki itama ranan tazo gidan ta taradda Aisha da AK a
kitchen inda yayi fatali da indomie Wanda shine yasata dafa mai a cewarsa kanme
zata dafa mai haka babu kifin gwangwani shiba matsiyaci bane shida kudin shi aita
masa mugunta akan abincin dayake siyowa, batada aikin yi saidai taci ta cika Masai
da kashi mai wari sai uban kiba datake narkawa a kugu,ana haka bilki ta shigo indai
Ranta yai mugun baci har saida ta tanka mai, 'karya kakeyi ka kiramu da matsiyata
tunda munada wadatar zuci sannan kashin ma ni'ema ce mutum yace shi baya kashi mana
sai uban takama da iyayin Gayu kamar kaidin baka kashi...... Rufe mata baki Aisha
tayi inda bilki ta dinga ruwan masifa, AK kuwa baibi ta kanta ba a cewarsa ita ba
sa'ar yinsa bace wacce tasata ita zata girbe mata abunda tasata ta shuka mai,
Aikuwa bilki taita masifa ta wanke Aisha Tass inda Aisha taita bata hakuri akan
kada a gayama Ramata da garbati dakyar bilki ta yanda saboda rashin lafiyar da
Ramatan keyi akai akai tun bayan Rasuwar babansu kullum yau ciwo gobe lafiya.

Haka AK da Aisha ke Rayuwa har ayau shekara Uku da Auransa, dawowa gida yayi da
yamma misalin karfe biyar kamshin girkin Aisha dukya cika gidan tun a tsakar gida
yabude kofofin hancin shi tareda shakar kamshin abincin daya gama Kara masa yinwar
Sa dukda bayacin girkin nata sai idan taimasa shida Abokanan Sa Wanda saita jera
abinci kala biyar duk ita kadai a cewarsa kada ta kuskura taba wani yaimasa girki
tunda ya taba taradda bilki tana tayata ranan tasha azaba wai ana jagwalgwala masa
abincin daya kashe kudi akai, dukda baci yakeyi ba saida ya gasa ta, 'Shigowa
parlon yayi daidai da daukewar farin cikin daya dawo gidan dashi dalilin wakan da
take rerawa mai matukar dadin gaske cikin muryarta mai sanyi da zaki yaji tana
cewa.

'AK ne Raayina
"AK sona yakeyi yana bala'en jidani,.
" na rubuta sunan AK akasa ruwa aka goge wlh kosun goge basu goge sanshi a zuciya
ba.......ido biyun da sukayi baki sake batasan sanda ta tsuguna tana bashi hakuri
harga Allah batasan yadawo ba cikin mamakin Sa ya juya yatafi a ranar baimata komai
ba, a cewar Sa hukuncin Laifin ta zai iya kashe ta saboda hakoran bakinta ya kamata
ya banbare a cewarsa kada yafara kisa akanta shiyasa ya kyale ta saboda bata taba
bata masa rai irin na ranar ba wai AK Santa yakeyi yana ba'laen jida ita kalmar
Nance tafi komai kona masa rai inda Yaji Aishar tagama cutar dashi.
*Cigaban labari*

Leemah ce zaune gaban Malam liman yana shaida mata wani matashi anan bayan unguwar
su yazo ya same shi akan yana Santa da Aure inda Malam liman yace bazai ma diyarsa
dole ba amma yaje ya nemi soyyar ta yabashi izini, sanar mata yayi akan zatayi bako
daga yau zai dinga zuwa da yamma saboda bayasan tadin Dare su daidaita idan yamata
toh idan baimata ba kada ta cuci kanta babu mai mata dole, Amincewa tayi lokaci
daya tun bataga bakon nata ba ta amince zata iya Auran shi saboda wani kudiri Wanda
ita kadai tasan abunda ke ran nata.

*Mrs Saddiq Rumah 💅🏻*


[11/7, 11:43 PM] ANTY JM D ILYA: 🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
🏼🏼🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?*‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah*

21

Da yamma misalin karfe biyar na yammacin ranar talata wani karamin yaro neya shigo
gidan Malam liman inda yake shaidawa ana sallama da halima inji Ahmed, kassncewar
tasan da Zuwan bakon nata bata wani bata lokaci ba ta zurkuma zumbulelan hijab
dinta sky blue Wanda ke Jan har kasa, fuskarta da kwalliya ba laifi, sanarda mama
tayi zuwan bakon nata inda ta fita ta same shi jikin Wata katuwar bishiyar dake
kofar gidan nasu, ba laifi yana da kyau daidai misali saidai zata fishi tsawo da
haske domin baki ne maidan jiki, hakan bai dami halima ba koda kuwa mummuna ne
futuk ba matsala bane a wurinta, zaune yake akan Mashin dinshi Roba Roba yayi
wankan manyan kaya sai zuba kamshi yakeyi, nan taimishi sallama hadeda gaishe shi,
batareda bata lokaci ba ya shaida mata kudirin Sa a akanta domin a shirye yake
yagama komai, Ahmad ya kasance cikin soyyar ta tunda dadewa sanin dokar gidansu
yarinya saita gama secondary ake mata Aure shiyasa yaita shirin shi a hankali
kassncewar yanzu tana gafda gamawa yabashi karfin gwaiwar tunkararta da Maganar
inda bawani kwana kwana ta Amince nan take, ba karamin dadi hakan yaimasa ba, cikin
lokaci kadan suka fara soyya mai tsafta daban Sha'awa a kwana a tashi har iyaye
suka shiga Maganar, kawayanta su meenah kuwa babu irin surutun da basuyi mata ba ko
kadan bata Dace da Ahmad ba ai gara ta Auri daya daga cikin Alhazawan da suke
holewa tare idan ma Auran takeso, mutum ya tashi a talauci ya koma talauci kai
kenan Kullum babu wani cigaba, nanta warware musu kudirin ta gameda Auran nashi
aiko abun yamusu dadi nan suka hau mata kirari, 'hoooo dakin hutu yar'gidan malamai
muna yinki ilimin nan naki ba'a dakin hutu kawai ya tsaya ba eyehh kanki fa Naja
kina wutaaaa diyar Malam, muma munbi ki munbi sahu irin naki zamuyi Alkur'an.
Ansa bikin halima nanda Wata Uku masu zuwa, inda Ahmad mutum ne mai matukar
ibada kullum cikin rokar Albarkan dake cikin Auran da zaiyi yakeyi baida aiki sai
sadaka da istahara kullum akan Allah ya kauda fitina tareda basu kyakyawan zu'ria
bakaramin San halima yakeyi ba itama ba laifi tana Dan jinshi sama sama koba komai
yana bata kulawa na musamman Ga kyauta akai akai, hankalin mahuta ba karamin tashi
yayi ba sanda yasamu labarin Auran halimar inda dakyar ta lallashe shi akan cewa
Aure ne na lokaci kadan bawai Zama zataje tayi ba babu yanda batayi ba akan ya
fahimce ta ina Sam ya kasa kishi ya rufe masa ido, nan yadan Saki Ranshi kadan
ganin kulawar da take bashi yamafi Nada tana matukar sakin mishi jiki tareda
Alkawarin ko bayan Auran babu abunda zai Chanza.

Mahuta ne kwance a dakin shi inda kishi ya turnuke shi bayajin zai iya barin wani
ya lasar mishi zumar dashi kadai yafara lasa kuma yake kan lasa, inaaa bazai taba
barin wani ya huta da kayan hutun shiba, wayar shiya dauko a gefen shi batareda
bata lokaci ba ya shiga messages dinshi number Ahmed dayasa a nemo masa yaketa
kallo nan ya yanke shawarar abunda zaiyi.

Ahmad ne zaune a cikin Abokanan shi suna fira shigowar messages yaji awayarsa nan
ya dauko wayar tareda dubawa salati ya Saki kanshi har sarawa yakeyi.

*Ina tayaka murnar Auranda zakayi, Abun takaici a matsayin kana kimtsatse baka dace
da mace irin halima ba, halima tamu ce ta irinmu ce masu gidan hutu, wlh wlh wlh
Nina fara cin halima tun tana shekara sha Hudu tazama katifa ta kullum saina hau
ruwan cikin ta inda sau biyu tana zubar da cikina.*

Tambayar da Abokanan shi ke masa neya sakashi tattaro natsuwar Sa, Lafiya maiya
faru haka?
'Ba komai ba komai ina zuwa bari intafi gida sai munyi waya, Kassncewar a Mike yake
tun sanda yaga sakon hakan yasashi tafiya gida kai tsaye ranar ko wurin halima bai
jeba sai sake sake yakeyi daga karshe ya tattara komai ya watsar a cewarsa mace mai
natsuwa irin halima dole tasamu masoya dayawa masu Sha'awar Mallakar ta, ya ajiye
hakan akan wani kesan rabasu domin ya mallake ta.

Halima kuwa sai rawan kai akeyi tanata yad'awa zatayi Aure sai banke banke take
bankawa babu Wanda Ahmad ya gayama abunda ke faruwa.

*Mrs Saddiq Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼 11:43 PM] ANTY JM D ILYA: 🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
[11/7,
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Ina farin cikin gayyatar ku bikin kanwata wacce nake jida ita chan cikin zuciyata
Husnah Wanda za'ayi a cikin satin nan insha Allah a garin Kano, muna bukatar
Addu'ar ku akan Allah yabasu zaman lfy mai dorewa tareda zuri'a dayyiba🙏🏼* Zaku
iya jina a cikin satin nan amma banyi Alkawari ba sai yanda ta kasance idan nasamu
lokaci toh Ga page har biyu namuku yau.
*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husna Amaryar gobe mai farin jini😍💃🏽*

22

Wasa wasa fa Karamar magana tazama Babba mahuta baida aikinda ya wuce turama Ahmad
texts din yanda yake holewa da halima tareda shaida masa akan ya bincika gaskiyar
maganar, tun abun bai damun Ahmad har ya shaida ma Abokanan Sa inda nan suka
kwantar masa da hankali akan kishi ke damun mahuta mace kamar halima mai ilimi da
natsuwa diyar malamai jikan malamai sharrin mutane ne kawai, nan ya yanke shawara
akan zai gwada halimar inda idan suna waya jefi jefi zai dinga sako maganar batsa
Wanda ada baya mata hakan kwata kwata, abun mamaki sai yaga bata damu da hakan ba
ko kadan bata taba nuna masa rashin dacewar hakan ba, saima nunawa datayi tafisan
irin firar akan kowace fira dayake mata, nan zaita gaya mata yanda zai mata idan
sunyi Aure, haka zatai ta biye mishi babu kunya hankalin Ahmad yayi mutukar tashi
ko a mafarki bai taba tunanin zata biye mai ba, nan yakara bullo mata dawani salo
idan yazo tadi kafun yatafi saiya San yanda zaiyi ko hannun ta ya rike nan ma bata
Hana shiba😳, ana haka Wata rana mahuta ya turo masa dawani text dinda yakara
birkita shi inda yake cemasa.

*Gskia ango Amaryar ka tabude dayawa nayi mamakin budewar ta dukda kasancewar
nikadai ke shiga ramin nata, waiii zurkumi, wlh wlh jiya na durje ta tun safe muke
Abu daya har yamma, hahahaa koda yake kafi kowa sanin bata gida jiya da yamma har
zuwa Dare muna tare ka kirata da la'asar ina jin sanda take gaya ma kada kazo bata
gida inda a wurina take yin haddar da aka turata a gidansu, na goge mata tsaf
tareda dasa mata karatuna a kanta. Idan namata karya kada Allah yasa inga Annabi,
Nina fara cin halima*

Bakaramin tashin hankali ya shiga ba ganin furucin da akai na karshe, wanene zai
iyama kanshi wannan fatan? Wani riba mahuta zai samu idan yaimata karya GA manya
manyan rantsuwar dayakeyi Anya babu Alamar gskia a lamarin nan kuwa?? Harda cewa
kada Allah yasa yaga Annabi hmmm Da zazzabi ya kwana ranar nan ya yanke shawarar
hakura da halima dukda ya dage dakaima Allah kukan Sa Ga sadaka dayake yi akai akai
cikin lokaci kadan tafara sire masa, dukda haka ya kudiri aniyar kureta.

Ahmad da halima ne a waya inda yake kashe tada maganganun batsa hankalinta ba
karamin tashi yayi ba Sha'awar shi takeyi sosai takosa taji yanda zumar shi yake,
ganin yasamu yanda yakeso a wurinta hankalinta yayi sama, 'matata wlh ina tsananin
bukatar ki har nakejin bazan iya jura sai an kawoki gidan muba lokacin yamun yawa
bby ki taimake ni kidan fara Ragemun zafi kafun a kawoki mana, 'bakaramin murna
tayi ba nanta amince mishi inda sukayi da ita akan zasu hadu zata bishi har gidansu
cikin shigar tana hijab da nukab, nan yace mata gobe zaizo su Kara tsara yanda
haduwar nasu zai kasance aikuwa washe gari batareda bata lokaci ba yakara tado mata
da maganar, 'yanzu taya zaki shiga gidan mu kinsan fa layin akwai mutane dukda
dakina yana ta waje ya za'ai?
'Ai kawai barin dakinka zakayi a bude bayan sallar la'asar saika fita nikuma
zansha hijab da nukab harda safa kafa da hannu sai in shiga bayan yan mintuna sai
in kiraka a waya, mace ke fara shiga dakin namiji saboda gudun zargi, 'cikin
matukar razana jikin shi har rawa yakeyi da amsar data bashi inda yakara tambayar
ta, 'toh wurin fita fa?? 'Namiji ke fara fita daga baya sai macen ta fito.
Hmmmmmm, ba komai hakan zaai sai mun hadu goben.

Washe gari leemah ta shirya batasha wahalar barin gida ba kamar kullum ta kira
Ahmad Wanda yagama tsorata akan lamarin nata, 'gani a kofar gidanku ya kenan?
Gaskiya kiyi hakuri mu hakura tsoro nakeji mubari ma chanza wurin haduwa gida babu
tsaro, yana fadi ya kashe wayarshi aiko bakaramin bata mata rai yayi ba tariga
tagama banke banken maganin mata haka takira wani Saurayin ta ya rage mata zafi a
gidansu na Isa kaita.

Mahuta Ahmed ya kira sau babu adadi inda cikin Sa'a ya dauki wayar Wanda ada baya
dauka, nan yaima Ahmed bayanin komai bai boye masa ba, godema Allah Ahmad yaitayi
ya tsallake rijiya dabaya inda yace shida halima har abada.

Ranar da daddare suna waya da halima bai nuna mana komai ba, cikin dabara tasako
zancen, 'Kasan menene?
A'a saikin fadi yabata Amsa, wlh Wata kawata ce wani Saurayin ta yaimata ciki abun
mamaki ankusa bikin ta, 'tohfa yafadi shikuma Wanda zata Aura yasani? Yabata Amsa
cikin jimami, 'hmmmm mu muka bata shawara akan ta gaya mishi idan zai iya Auranta a
haka aikuwa yace ba matsala shi ita yakeso ba jikinta ba amma a zubar da cikin,
aikuwa ana zubarwa ya Aure ta kuma xo kaga yanda yake Santa baitaba goranta mata
ba.
'Gskia ya matukar burgeni lallai ya cika namijin gaske haka akeso ba karamin
lada zai samu ba, 'Allah masoyi na? Ta Tambaye shi cikin zumudi, 'wlh kuwa, 'kai
zaka iya mun haka?? 'Kwarai mai zai Hana? Tsakanina da Allah nake sanki a ba jikin
kiba zan iya mana babu abunda zai hanani Auranki, ",ka tabbata tafadi har tana
yar'dariyar murna, 'kwarai kuwa kina shakka ne??
" hmmmmm a'a nasan kana matukar sona, "eh wlh babu abunda bazan iya miki ba
insha Allah.
"Aikuwa nimafa an taba, 'aka taba mai😳? Ya bata Amsa.
'Wlh wani yataba mun fyade munje bikin kawar mu wurin dinner ya yaudare ni har
yaimun ciki😭😭

'Ciki? Amma wasa kikeyi koh? Cikin tashin hankali ya furta hakan, 'wlh wlh da
gaske nakema.
'Karki damu nariga nasan komai ai tun kafun ince zan Aure ki nasan koke wacece
amma ke nakeso, nan yafara gaya mata wasu daga cikin sirrin ta Wanda mahuta ya gaya
masa, nan taita mamaki bata iya karyata shiba aiko nanta bude baki taita bashi
labarin Abubuwan dabai Sani ba cikin ikon Allah kamar wacce aka matsa ma baki, inda
taimasa karya akan sau goma kawai muhuta yasanta a mace, 'kanshi kasa daukar
zancen yayi nan yace mata zai kwanta yanajin bcci duk yanda yaso ya nuna mata babu
komai kasawa yayi kashe wayar shi yayi tareda tausayin Rayuwar mu ayau, shin wacece
macen Auran? Haka Zamani ya Zama? Da Addini suke fakewa suna ta'asa a doran kasa?
Halima tagama rikita shi nan danan tausayin Malam liman ya rufe shi dattijon
Arziki.

*A' gurguje.*

Shiru kwana biyu babu Ahamad ba dalilin shi Kota kirashi baya dagawa inda dakyar
tasamu ya Amsa wayarta nanta fashe mishi da kuka akan yadaina naimanta, 'maganar
gskia bazan taba Auran mazinaciya bari muyi gwari gwari niba Dan iska bane babu
wani boye boye kin bani mamaki bazan Auri mai fuska biyu ba kije ki aura mazinaci
daidai ke Allah ya shirya ki yasa kigane ni kaina ba wayo na ko karfi na bane ya
kubutar dani daga auranki illah Addu'ar da nakeyi da wacce iyaye kemun sai Ince
Alhmdlh, 'babu irin magiya da Rokon dabata masa ba Sam yaki yarda ya shafama idonsa
toka, 'Dan girman Allah ko Auran Dare daya muyi ko baka taba niba ka rufamin Asiri
ka aureni koda baka sona, ko bakai mun komai ba, 'saboda me? Ya tambaye cikeda
mamaki, "saboda in goge bakin fentin Dana kwasa zan biyaka konawa ne insha Allah ko
Auran kwana daya ko biyu ne na yarda, 'kai tsaye ya gaya mata bazai iyaba.

" halima taci kuka badan tana San Ahmad ba saidan Auran shi rufin asirin tane
mutane zasu shaida tataba Aure daga baya saita aura mijin da takeso mai kudin gaske
inda zata huta ta kece Raini koya jita a bude ba matsala tunda yasan bazawara ya
Aura, ko banda wannan ma kasuwar zaurawa tafi budewa manyan mutane sunfi San harka
da bazawara sannan Abu na Uku dayasa takeso tayi Aure saboda ta tabbata Malam liman
sai yamata Aure kwanan nan amma idan tazama bazawara zai sakar mata mara ta tsula
tsiya a cewarsu tayi Aure tafito batayi dacen gidan miji ba jama'ar gari babu Wanda
zai zarge tada wani Abu.

*Note:- labarin rayuwar halima Wanda nake badawa a yanzu wlh wlh yafaru da
gaske babu abunda na rage bare in Kara*

*Mrs Saddiq Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Godiya ta musamman Ga masoyan littafin nan Wanda na Sani dama Wanda ban Sani ba,
da bazarku nake taka rawa masoyana na Facebook dukda ban sanku ba ina gaisuwa.🙏🏼*

*Dedicated to sister Husnah*

23

Babu yanda halima batayi ba Sam Ahmad bayako sauraran ta daga karshe ya tura iyayan
shi amso kayan Auran da akakai gidan su, ba karamin tashin hankali iyayan su suka
shiga ba babu irin tambayar da baayi masa akan dalilin yin hakan ba Sam yaki fadi a
cewarsa zai rufa mata Asiri, nanfa iyayan shi suka hau fushi dashi harta kai saida
kanin Malam liman ya tarke shi duk yanda yaso ya gujema abun ya gagara kowa shi ake
bama laifi itako banda kukan munafunci babu abunda takeyi inda ta dage akan bata
masa komai ba, dayaga ba sarki sai Allah hakanan ya warware ma kanin babanta duk
abunda ke faruwa inda abun ya daure masa kai sosai koda aka gayama iyayan ta Sam
kin yarda sukayi a cewarsu za'a bata Ma diyarsu suna dama ba Santa yakeyi ba yaxo
ne ya tozarta su Mamarta rantsuwa tayi saitayi shari'a da Ahmad babu yanda Malam
liman baiyi ba akan abar maganar ina ta shafa ma idonta toka saida takai Kara
police station inda aka tasa keyar Ahmad nan aka fara sabon case Wanda koda halima
taji yana maida jawabin abunda yafaru kallon shi taita yi batace komai ba dakyar
kanan Malam liman ya roka aka rufe case din a cewarsa koda anje kotu tozarci zai
Zama a wurin diyarsu ko itace da gskia za'a bata Mata suna ne inda Ahmad kuma yace
sai anyi sha'riar da gaskiyar Sa, dakyar aka rufe maganar kowani sashi na zagin
dayan sashin inda iyayan halima keta lallashin ta Malam liman harda mata rubutun
dangana ganin yanda tasa abun a Ranta basusan kawai basaja take masu ba, mahuta
kuwa yafi kowa farinciki da hakan inda yakara riketa gamgam.
Wasan bera da mage aka shiga yi Aisha da AK tunda ya ganta tana rawa take gujema
duk hanyar dazai hadata dashi
Tun rananda AK yaga Aisha cikin karamin 3quater da farar vest fa hankalin maza ya
tashi, hmmm jiya ba yauba koba komai shekaru sunja duk yanda yaso yakice abun a
Ranshi hakan ya faskara inda ko rufe idonshi yayi toh surar jikin Aisha kawai yake
gani tana juya kugu tana rawa kamar zata karye Anya akwai mace mai irin zubin
halittar Aisha kuwa? Idan ya tuno da shafaffan cikin ta da kirjin ta haka zaita
juye juye akan gado tun yana daurewa har saida yayi jinya ciwon ciki mai matukar
azaba ya turnike shi dakyar yasha saida yayi sati biyu tareda taimakon maganin da
aka Dora shi akai inda likitan shi yabashi shawara akan yakusa halaka kanshi
bakomai ke damun Shiva sai muguwar Sha'awa bakaramin takaicin likitan Yaji ba inda
ya karyata hakan mai zaisa Yaji sha'awa? Toh Sha'awar wama zaiji? Cikeda mamaki
likitan ke kallon shi, 'yallabai amma kanada iyali koh? Ya Tambaye shi, shiru ma
Amsa ne yatashi ya cikama rigarsa iska.

Wasa wasa fa AK ya shiga tsaka mai wuya yarasa natsuwa inda kullum haushin Aisha
yakeji a ganin shi mugunta ceta sata yin irin shigan nan a parlon banda mugunta
menene amfanin bedroom dinta? Kai anya ma Aisha bata ciko? Kaiiii gskia tana ciko
irin wannan hips haka kamar an zana, 'nazari ya shiga yi, idan kuwa tana ciko saina
ci ubanta akan mai zata dinga mun ciko a gida? Hankalin wa takeso taja? Mikewa yayi
tareda nufan dakinta kafarshi yasa ya hankade kofar tana kwance tayi rufda ciki
akan gadon ta cikin Riga da Skart na Atamfa ta dame ta tsam Rabin kirjinta a waje,
baisan sanda ya lashe bakinsa ba, keee, ya daka mata tsawa inda ta Mike jikinta na
rawa, oya zonan, yafadi tareda juyawa ya koma parlor Zama yayi kan kujera kafa daya
nakan daya sai girgima kafa yakeyi fuska a hade, 'tsugunnawa tayi Dan nesa dashi
kanta na kallon kasa, 'wayace ki tsuguna?
Kayi hakuri ta furta tareda mikewa, 'saina daga murya? Yafadi yana banka mata
muguwar harara, 'matsowa tayi kadan kusa dashi inda ya shagala wurin kallon hips
dinta burinshi daya yataba Yaji yanda zai mishi a hannu yanaso ya cire zargin
dayake yi yanaso yasan tana ciko ko batayi, idonshi tabi da kallo ko kyaftawa
bayayi Wata irin kunya takama ta ganin inda yake kallo, charaf suka hada ido nan
taji kamar ta nutse a kasa inda yakara hade ransa kamar hadari kamshin ta yana Kara
rikita shi, 'uhmm yayi gyaran murya, 'menene a kasan kujeran nan? Kallon kujeran ta
shiga yi, 'bakida baki?
Tsugunnawa tayi Sosai nan kirjinta ya bayyana sosai AK har tura kanshi yakeyi yana
Kara leke ya gwale ido a kidime take dubawa batama San yana kallon taba, 'yaya wlh
banga komai ba kayi hakuri, eyeah? Yafadi yana Kara kallon kirjin ta, duba duba
dakyau, duk yanda taso ta hango wani Abu takasa tana dago da kanta karaff sukai
karo dakan AK daya Kara tsawo dalilin kallon ta, Dan Allah kayi hakuri, ta furta
hartana murza hannun ta tasan bakaramin azaba zata shaba, 'inda dakyar ya iya saita
kanshi tareda gyara murya har yana share zufa, 'waige waige yafara shi bama takan
karon da sukayi yake ba cikin Sa'a yayi ido biyu dawani karamin tsinke, uban menene
wannan??
'Saida ta kalla sosai tagane tsinke ne, 'Au wlh wurin shara ya makale.....mtsew
kazamar banza common malama bace Munda gani, yafadi yana mamakin abunda ya hanashi
mangare ta kamar yanda ya saba, mtsewee yaja tsaki, 'zonan tadawo yayinda yakasa
dauke idonshi a jikin ta, uban wa yaimiki dinkin nan?baki a bude take kallon shi
tana mamaki karo daya na rauwarsu daya taba tanka ma lamarin ta, 'Dan Allah kayi
hakuri bari in chanza tafadi tareda saurin juyawa, 'mtseww mutum yawani guma manyan
kaya a gida ko zafi baiji, mtsew please wuce kibani wuri ni mummuna dawani kugun ki
a wurin, 'da hanzari tabar wurin inda ya shiga dakin shi hannu rike da Mara yana
dingishi cikin shiya rike, 'misalin karfe takwas na Dare ya nufi kan dinning table
kamar kullum abinci a jere gwanin ban Sha'awa sai hadiye miyau yakeyi yanaso yaci
bayasan ta raina shi, 'Ina kike?? Yafadi chan kasan makoshi, shi kanshi yasan
bazata jiba, Karo na biyu yadan Kara daga murya kadan, 'Black slave where d fuck r
u before I lose my temper, a yanzu haushin kanshi yakeji yanda yakejin wani Abu a
zuciyar shi tana hanashi dukan ta kamar Yanda yasaba, 'jiki na rawa tafito sanye da
bakar doguwar Riga ta yane kanta da karamin mayafin rigar mamakin ganin zaici
abinci yau takeyi, tsaki yaja tareda dauke kanshi bakaramin haushi tabashi ba ko
ubanwa yace ta chanza kaya oho ko zafi bataji aiko AC gidan nan zan cire mutum sai
Albazaranci, 'mtsew Dan mugunta omo ma sai ansa mutum yayi asara, yafadi dukda taji
abunda yace amma takasa gane inda ya dosa, 'Ina kunun aya na? Ya tambaya dukda
baisata yin kunun ayan ba cikin ikon Allah tayi nata nasha haka kurum taji tana
marmarin sha, jiki na rawa ta shiga kitchen inda ta dauko katon glass jug cikeda
kunun aya mai kauri yasha madara da kwakwa da madarar pick tareda dorawa akan
faranti da glass cup mai kyau, ajiyewa tayi a gabanshi, 'gashi ta furta jiki na
rawa ta juya tareda barin wurin, Toh maiyasa yanzu yake yawan San kallon ta? Girman
hips dinta ke baka mamaki Yaji wani sashi na zuciyarsa na bashi Amsa, yesssss yesss
shiyasa dakuma boobs dinta danake tunanin ciko take musu, oooh mata kenan komai sai
anyi cuwa cuwa, mtsew mai zaisa in damu dawani kazamin jikinta? Bari kawai in cire
zargin danake yi yafadi kai tsaye ya Mike bedroom dinshi ya shiga tareda jawo
bedside drowa dinshi magungunan da aka bashi na ciwon cikin shi ya nemo inda ya
dauko wani magani Kanana Kanana na bcci sanda yaima doctor din complain baya iya
koda bcci saboda zafin ciwo shine doctor din ya bashi maganin da sharadin kwaya
daya zai dinga sha kassncewar maganin Nada karfi sosai, komawa parlor yayi inda ya
tsiyaya kunun ayan a Kofi fari tar gwanin Sha'awa nanya balle maganin har guda Uku
ya watsa a ciki ya jujjuya murmushin mugunta yayi saida ya tabbata maganin ya narke
kassncewar maganin baida daci salam yake baza'a taba gane ansa Abu a ciki ba, Aisha
na zaune tana tunanin kallon da AK ke mata, toh kodai baida lafiya ne? Ta tambayi
kanta a karo babu adadi dukda kwana biyu bata cika ganin shiba tama dauka yayi
tafiya ne kassncewar ya rage tsangwaman ta........kiranta yayi da sunanda yasa mata
inda a tsorace ta Mike tana gafda fita dakin tayi Addu'a, Yah Allah ka kareni daga
wulakanci da tozarcin farin mugu na, shawafa tayi ta nufe shi kai tsaye Addu'a
dauke a bakinta, 'jijjiga kofun dake hannun shi yayi, 'menene wannan? Ya tambaya
baiko kalle taba, 'kunun aya ne, 'ya akai naga yayi fari sosai? Uban mai kika saka
mishi naji yana Dan daci daci, 'cikin mamaki ta kalle shi, daci kuma? Wlh bansa
komai ba daga kwakwa sai madarar pick..... Oooh toh nazama makaryaci kenan koh?
Mika mata kofun dake hannun shi yayi inda ya kafeta da ido, Amsa tayi tana kallon
shi saboda batasan mai hakan ke nufin ba, saida sukayi minti biyu a haka dayaga
batada niyyar sha ya waigo tareda watsa mata mugun kallo, dalla malama ki kwankwade
kila barbade kika fara min saboda insoki waya Sani ban yarda dake ba maza shanye
kibani kofin, Wlh wlh yaya AK ko gishiri ban taba sama ba a abinci da sunan ka
soni, mtsew munafuka banasan surutun da ba'a tambaye kiba, 'kafa kai tayi ta shanye
tsaf tareda ajiye kofin a gaban shi tana goge guntun kwalla, "saida safe ya furta
baiko kalle taba, sanin abunda yake nufi wato ta bace masa daga gani shiyasa taja
kafarta takoma dakinta cikeda sake sake, cikin yan mintuna taji wani azababben bcci
ya tunkare ta yayinda taita zuba hamma babu adadi, kasancewar bata Dade dayin
wanka ba rigar bcci ta dauko yar Karama ko guiwa bata kaiba mai santsi shara shara
red color gaban rigar net ne maiban Sha'awa a yanke ta feshe jikinta da turaren
data saba shafawa nanta fada gadon ta dakyar ta iya jawo bargon ta ko wutan dakin
bata kashe ba baki bude idonta ya rufe ko Addu'a takasa nan magani yafara aiki bcci
takeyi batako San inda kanta yake ba, AK kuwa misalin karfe shadaya sanye da Riga
da wando na bcci sky blue mai taushi sai kaiwa da kawowa yakeyi tsakanin dakinshi
da kofar dakin Aisha inda yaita yunkurin shiga yakasa bayaso ya shiga bccin ta
baiyi nauyi ba shahada yayi ya tura kofar dakin a hankali inda ya hangeta ta
bararraje baki bude sai bcci take zubawa, kofar ya kulle a hankali ya shiga dakin
cikin san'dah saikace tsohon kwarto

*Mrs Saddiq Rumah💅🏻*


🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
🏼🏼🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah.*

24

Tafiya yakeyi sada'f sada'f inda ya tsaya chak cikeda wasi wasin abunda yake shirin
yi a karo ba adadi yayi yunkurin komawa inaa zuciyarsa takasa barin shi, 'toh ai
daddy na yabada kudin sadakin bazakici banza ba koba komai dukiyar daddy tawa ce
kuma matata ce bawai laifi nayi ba kawai inaso in cire shakku ne, zuciyarsa ke Kara
basa shawarar tunkarar ta tareda mishi surutai akan hakan kai tsaye ya doshe ta
batareda bata lokaci ba ya yaye bargon data rufa dashi bakin shi yayi saurin
toshewa kadan yarage bai Saki ihu ba ganin zubin Halittar da Allah yaima Aisha ba
karamin rikita shi hakan yayi ba kwance take fuskarta na kallan sama kafa a ware
santala santalan cinyoyinta na waje, haba dole dole ma yarinyar nan shaidanun maza
su dinga wawar ta kotaki kotaso ya dauki akalla minti biyar yana Kure mata kallo
hannun shiya saka kan rigar bccin data gama bayyana surar jikinta inda yasamu
kanshi yana shafata sama sama runtse idonshi yayi inda taiwani juyi ta mirgina
jikinshi sosai kanta na wurin kugun shi yanajin numfashin ta a jikin nashi baisan
sanda yasaki Ajiyar zuciya mai karfi ba numfashin shi nafita sauri sauri, hannu
yakai yana shafa kugun ta dayake janshi zuwa gareta kamar Mayan karfe, yauwa koba
komai ya cire zargin dayake yi maiya rage? Yanaso yatashi yatafi wani Abu na
jawoshi zuwa gareta dukya gigice ya Dimauce zame rigarta yayi tasama nan halittar
kirjin ta suka bayyana Tubarkallah hmmm AK yagama firgita hannun Sa yadora duka
biyun akai, subhanallah ya furta a razane wani shocking Yaji yana bin dukkan jikin
shi da sauri ya Mike har yana faduwa, Innalillahi wa inna ilaihir raji'un yaita
furtawa da gudu gudu yabar dakin ta kamar Wanda yayi gamon Aljani jiki na rawa dama
haka kirjin mace keda ban Sha'awa tabbas idan yakara mata kallo na biyu babu
abunda zai hanashi damkar ta Kota bala'e kitchen ya shiga ruwan sanyi ya dauko Roba
daya yakafa kai yadinga sha saida yarage Dan kadan sannan ya watsa a saman kanshi
dukda haka jikin shi zafi rau gawata jarabar Sha'awar da baitaba tunanin yanada ita
ba, toh kodai likitan shi gskia yafadi dayace masa Sha'awa ke neman masa illah? Toh
badai Sha'awar Aisha bace koh? Noooooo girkiza kanshi ya shiga yi hango yakin da
hakan ke nufi a gare shi nan yakarasa bayin shi ko kaya bai cire ba tsakiyar shower
dinda ke bayin ya tsaya tareda sakarma kanshi ruwan sanyi cikeda takaicin tozarcin
dayake shirin jama kanshi, ranar ko barawon bcci baiyi nasarar sace AK ba yanda
yaga Dare haka yaga rana inda ya yanke shawarar Samo ma kanshi mafita tun kafun
yafara hauka, Aisha kuwa bcci tayi bana wasa ba inda ko sallar asuba bata samu
daman tashi ba ko motsi batayi saikace gawa dakyar ta iya bude idonta da sukai
mata nauyi jikinta ya mutu sosai salati tasaki ganin karfe Tara na safe tana hamma
da mika jinta takeyi zata Kara maimaita bccin datayi domin bai isheta ba, bayi ta
shiga tana tangadin bcci Alwala ta daura nan danan tayi sallar asuba tana mai neman
yafiyar Ubangi tareda mamakin bccin nata, kodata idar bayi ta shiga domin yin wanka
a cewarta kila takara watsakewa tana shiga AK ya tura kofar dakin nata Wanda tunda
gari ya waye yake lekota jefi jefi tana bcci, da cikin kwanakin baya ne ruwan sanyi
zai watsa mata ya daka mata tsawa saiya samu kanshi dajin tausayin maganin daya
bata har guda Uku masu karfi yananan tsaye inda sauri sauri ta watsa ruwan so
takeyi taje tayi aikin data saba kafun farin mugun ya lallasa ta daure takeda farin
towel a kirji tafito yayinda karamin towel ke hannun ta tana goge gashin kanta data
wanke a bayin dogayan santala santalan cinyoyinta sai daukan ido sukeyi gwanin ban
Sha'awa hamma ta fito tanayi tareda mikan kasala, bakaramin tsoro taji ba ganin
mutum tsaye a gefe yana Kare mata kallo bako kyafta ido, ihu tasaki tana shirin
komawa bayi....Aaisha ya kira sunanta chan kasan makoshin Sa muryar shiko fita
batayi sosai, chak ta tsaya karona farko tunda tayi wayau bata tabajin ya kira
sunanta ba, kasa Juyowa tayi cikeda kunyar ganinta dayayi a haka, zo zauna muyi
magana mai muhimmanci, jiki sanyaye ya zauna a gefen gadon ta inda itama takoma
gefe a takure tana Addu'ar sauyin datake gani harga Allah tsoran shi yakara saka
mata batasan sauyin nan bata saba dashi ba tafi sabawa da muguntar shi fiyeda
komai, 'banasan karya tsakanin kida Allah yaushe rabon kida namiji? Ya Tambaye ta
babu wasa a tareda shi yakasa dauke idonshi a kirjinta dakeda danshin ruwa, 'kamar
ya yaushe rabonta da namiji? Maiya hadata da namiji? Mai maganarsa take nufi? Katse
mata tunaninta yayi, look ba wasa nazo yiba kada ki bata mun lokaci ba tunani na
Saki ba, kina Sha'awar namiji ne? 'Subhanallah yaya AK wallahi bana Sha'awar
kowama tafadi murya na rawa, 'wlh wlh karya kike munafuka, daga muryar shi yayi a
wannan Karon, In banda ke munafuka ce uban mai zaisa ki dinga mika kina bankarewa
kusan Wata Daya kenan nake kamaki kina bankare bankare da mika kinaso kiyi seducing
dinane? Dafa kirjin ta tayi yayinda ta zaro manyan idanun ta, 'nooo wlh a'a bana
Sha'awa jikina ke tsami shiyasa nake mika ni wlh yaya kayi hakuri, girgiza kai ta
shiga yi tana Kwalla a ganinta sharri kawai yakeso yai mata yasamu dalilin
jibgarta, 'masana halittar mace sun tabbatar da duk macen da take yawan mika da
bankara tana bukatar da namiji idan ni nayi miki Karya suma karya sukayi kenan?
Mikewa tsaye yayi, Look banasan dogon surutu ki shirya nanda minti goma ki sameni a
mota ban yarda dake ba, fita yayi daga dakin inda tafara tausayin kanta sauri sauri
ta shirya cikin doguwar rigar atamfar tareda simple kwalliya madaidaicin hijab ta
saka ta fesa turare sama sama flat shoe tasaka tana tunanin inda zasu kodai gida
zai
🙆🏻‍

♀ maida ta yace tana Sha'awar mazan waje? Ooooh ni shatu naga ta kaina‍♀ tawa
ta sameni ya Allah ka fitar dani daga sharrin farin mugu Allah ka taimaki baiwarka
wlh nagaji nagaji da Auran nan Anya zan iya kuwa? Hakurina yafara karewa gskia
nagaji da sharri, tafadi tana girgiza kanta da Asalin gskiar ta Auran AK yafara
cutar da ita, a bakar motar shi ta same shi cikin shigan manyan kaya farin yadi
mai shara shara yayi masifar kyau kanshi da bakin hula dukda bakaramin kyau yaimata
ba amma samun kanta tayi takasa kallon shi kamar yanda ta saba, idonta ta kauda
gefe, gaban motar ta bude korona farko dazasu fita tare karo na farko data shiga
motar shida niyyan fita wani waje dukda tana shiga idan tana wanke mai amma wannan
shigar ta babanta da sauran, dukda taji dadi amma tsoron abunda zai faru ya shafe
jin dadin nata, baba mai gadi Baki yaki rufuwa ganin Abunda bai taba gani ba nanda
nan yaita zuba musu Addu'a yana kirari yana wasa su sun burge shi ba kadan ba, get
din ya wangale yana musu fatan dawowa lfy inda ko kallon Arziki bai samu ba yau a
wurin maigidan nasa, tafiya sukayi maidan nisa tsit kakeji babu Wanda yakara kallon
wani saida yayi tafiyar minti shabiyar sannan ya tsaya a wani dankareran asibiti
inda kai tsaye ya daga wayarsa da Alama dawani likitan yake magana, Aisha kuwa
cikeda damuwa take maiya kawosu Asibiti? Gaban tane ya fadi rass kodai Ramata ce ba
lafiya? Innalillahi yah rabbi kasa ba haka bane tafadi a fili tunawa datayi Ramata
kwana biyun nan cikin ciwo take Wanda take zuwa dubota a gida jefi jefi tareda kai
musu kudin hidimar magani, kallon ta yayi ganin batada Niyyar fitowa, 'malama zan
rufe motata ba gadi kikazo yiba inada abunyi, 'fitowa tayi jiki a sanyaye inda tabi
bayanshi kai tsaye wani office suka dosa inda ya kwankwasa kofar wani katon likita
baki ya fito yana washe hakora, 'mika ma AK hannu yayi suka gaisa inda yaimasa nunu
da kujerar dake fuskantar Sa Aisha kuma ta zauna cikin kujerun dake katon office
din duk a takure take, 'yauwaa yalla'bai itace mai aikin gidan mu wacce na baka
labarin muna zargin tana biye biye, kokuma ince ni nasan tana biye biye shine nazo
a gwada komai na jikinta a tabbata tsaftar jinin ta, kallon AK likitan yayi dukda
baiji dadin cin fuskar da AK yaima mai aikin nasu ba akan idonta, 'ba matsala bare
inkira a diba jininta yama wadatar nan za'a tantance komai, Mikewa Aisha tayi
jikinta har rawa yakeyi tana girgiza kanta hawaye daya nabin daya mai take shirin
ji? Badai itace yar'aikin ba?, 'nooo Doctor har kashin ta inaso a gwada, kashi da
futsari idan da halima ku turata a Engine gaba daya nasan bazaku rasa ba aita
aunata akan idona gskia inasan lafiyar jikina, 'dariya likitan yayi ganin AK daduk
gskiar shi yake maganar, waya yadaga yakira Wata nurse nanda nan ta shigo inda
likitan yadanyi kananan rubuce rubuce a takarda, Aisha kuwa tana tsaye tanaso taga
ikon Allah, 'kutafi da ita lab a diba jininta gani nan zan biyoku, likitan
yace......'nooo nurse hada kashin ta a gwada, dariya nurse din tayi yayinda ta rike
hannun Aisha, zo muje madam, wani irin tsawa ta dakama nurse din, 'kada ki kuskura
hannun kiya tabani, a tsorace AK ya kalle ta tunda suka shigo baibi takanta ba
ganin tana mike a tsaye cikin mamakin Wanda taima ihu yake kallonta lallai Ashe
itama batada kunya jinjina kai yakeyi tareda mikewa, 'meye haka? 'Look I have no
time to West malama ki bita kafun raina ya baci, wani kallon banzan da batasan ta
iyashi ba taimishi sama da kasa taja dogon tsaki tareda shirin fita office din,
look Aisha, yafadi cikin hanzari ya damko hannun ta kamar yanda ya saba, karfin ta
tasa gaba daya ta hankade shida hannu biyu saida yadafe table din kusa dashi kadan
yarage yafadi dukda haka ya buge gefen hannun shi, 'wlh wlh muddun ka tabani ayau
zakayi danasani Wanda harka mutu bazaka Kara kamarsa ba, mtsewee tafadi tareda fita
BAMMM ta banko kofar office din yayinda ta bangaje nurse dinda ke kusa da ita,
Kamar Wanda aka dasa haka ya sankare saida doctor dinya girgiza shi kusan sau biyu
sannan ya maida kallon shi wurin doctor din, mukullin motan shida ke kan table din
yaja baibi takan kowa ba yafita kamar zai tashi sama.

*"Zaiyi wuya kujini gobe da jibi shiyasa nai muku mai yawa, but idan nasamu sarari
zaku iya jina."*

*Mrs Saddiq Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Godiya Mara iyaka Ga duk Wanda ya halarci bikin sister na dama Wanda bai samu
halarta ba mun gode da Addu'ar ku tareda soyyar ku a garemu🙏🏼Allah ubangiji ya
zaunar damu a gidajan mu lfy wadanda basu samu sun shiga ba Allah yaimusu zabin
Alkairi.🙏🏼*

*Dedicated to sister Husnah*

25
Tafiya yakeyi sauri sauri sai faman waige waige yakeyi waiko zai ganta amma ina
babu Aisha babu Alamar ta Ranshi ya baci sosai yanda ta yarfa shi lallai Ashe
itama haka take Ashe? Fuska ne bata samu ba tabbas Aisha batada kunya nan gaba
kadan ya rage sufara dambatawa ganin yanda ta naimi kaishi kasa dazu, tsaki yaja
yana jijjiga hannun shida ke faman mai zugi tareda dosar motar shi yana jinjina
lamarin kai tsaye gida ya wuce yasan zai taradda ita so yakeyi suyi wacce zasuyi
a'yau toh karya yaimata? Shifa baiga abun fushi ba a maganar Sa tsakani da Allah
yayi laifi daya kaita Asibiti domin Duba lafiyar ta? A'a ikon Allah shifa yanasan
kanshi yasan maizai faru gaba yanda kullum take bankare bankare kila ta kawo mai
hari shiyasa yaima kanshi gata tun yanzu kada ta shafa mai masifa, shi kadai yaita
surutun shi harya isa gida baba mai gadi na bude masa gate ya sauke Window
motarshi, Aisha ta dawo? 'Yalla'bai bata dawo ba tunda kuka fita tare, cikeda
mamaki yakarasa parking din motarshi toh ina taje mishi da igiyar Auransa har guda
Uku? Shifa bazai dauki iskanci ba da izinin ubanwa ta fita? Kasa sukuni yayi sai
kaiwa da kawowa yakeyi, wayarsa ya dauka tareda shiga contact dinshi, 'mtsew Ashe
ma banda number ta, oooh God tohko Mara kunyar kanwar ta zan kira inji ko tana
gida? Yah rabbi banida number kowa nata why? Saboda irin haka yakamata insamu
number wani nata, wayarsa ya dauka tareda kiran mamien Sa, suna gaisawa ta tambayi
Aisha, Au Ashe bata karaso ba tun dazu tacemun zatazo muku wuni zata fara biyawa
gidansu daganan zatazo nan wurinki, Au Allah sarki aiko bata karaso ba inajin
saidan anjima zatazo, 'yauwa Mamie please a tura wani gidan nasu a gaya mata tagama
duk abunda zatayi dawuri zanzo in dauketa karfe biyar na yamma insha Allah, 'a'a
harsai an tura wani kabari idan tazo din basai a gaya mata ba, a'a Mamie adai tura,
ikon Allah toh kai ka kirata a waya mana, 'nakira Mamie wayar bata shiga inaga
matsalar network ne,
Toh ba matsala zan aika yanzu, idan kazo inaso muyi magana ka sosamun inda kemun
kaikayi Allah yasa ba abunda nake zargi kukeyi ba haba shiru shiru muma munaso muga
yan dagwas gwas a gaban mu kodai planning kukeyi? Hmmmm bari kawai Mamie idan nazo
mayi maganan nima abun na damuna, toh Allah Shi kyauta saikazo, a'haka sukai
sallama, kaji tsofaffin nan su Sam basuda damuwa sun hadani da bala'e suta jikoki
sukeyi ma duk nasan abunda zan muku bazaku kashe niba, yace a fili yana tunanin
hukuncin da zaima Aisha.

Kodata fito bata zame ko'ina ba inda kai tsaye bakin titi ta nufa cikin Sa'a
tasamu keke napep empty Allah yasa tanada chanji a jikinta gidansu ta wuce kai
tsaye inda tana shiga dakin nasu ta fashe da kuka nan hankalin Ramata da bilki yayi
mugun tashi inda sukaita lallashin ta babu yanda basuyi akan ta gaya musu dalilin
kukan nata Sam taki, nan Ramata a karona farko tace mata idan taga da cuta a
zamanta da AK ta tattara ta dawo gida tabata goyan baya ganin Aishar bata taba yin
hakan ba tunda tayi Aure kullum nuna musu take tanajin dadin zamada mijinta shiyasa
ganinta yau ya tada hankalin Ramata bataso ta shiga hakkin yar'ta mai hakurin gske,
cemusu tayi zata shiga makwabta nan Ramata ta fita tabarsu da bilki tayi hakan ne
waiko kila zata gayama bilki matsalar ta tasan bilki zata bata shawara mai kyau
tunda ita takasa gaya mata ba mamaki ta gayama yar'uwarta, aiko bilki tasata a gaba
saida ta gaya mata wasu Abubuwa nan bilki taita masifa tana zagin AK, kuka take
taya yar'uwarta sosai inda tabata shawara akan bata yarda ta rabuda AK ba harsai ta
gasa masa aya a tafin hannun Sa a cewarta idan ta barshi yanzu yaci bulus duk
wahalar daya gana mata yatafi a banza, haba Anty wlh kina bani haushi bubeki Dan
Allah mace har mace ni kaina zubin halittar ki burge ni takeyi wlh kowace mace
saita kyasa ki bare namij, haba inada irin surar nan taki Malam mai akai da maza?
Nan bilki ta cire kunya taita kintsa ma Aisha hanyar daukan fansa wuni sukayi cur
tana tsara mata yanda zatayi Aishar kuma ta dauki darasin sosai kuma taji dadin
hakan a cewarta itama mutum ce kuma tanada zuciya ta kudiri sai AK yazo ya tsuguna
ya bata hakuri sannan yabata takardar ta tagaji, ana haka ne mai aikin Mamie Wata
yar'budurwa taxo tareda basu sakon AK tana fita Aisha ta kalli bilki, sis kinji
koh? Wlh baisan nan zanzo ba kinga daya daga cikin sharrin nasa koh, dariya bilki
tasaki tana salati harda tafa hannu, oooh Allah ni Bilkisu namiji da makirci Lallai
mijin nan naki saike wlh wuri yasamu nuna mishi zakiyi kin fishi iyawa keda kike
mace har za'a gayama makirci? Nan bilki takara zugata tareda Dora mata sababbin
karatun da suka zauna sosai a kanta inda Aishar taita dariyar mugunta harta kosa ta
koma gida tareda Alkawarin ta daina bari hannun shi yana sauka a jikinta ita ba
jaka bace takuma daina aikin bauta.

Misalin karfe hudu bayan la'asar Bilki ta Rakata har gidan Mamie inda suka
tadda ta a kitchen nan suka hau tayata aiki cikin sakewar fuska ta tarbe su harda
rungumar Aisha sam Mamie ta watsar da komai inda ta rike Aisha da hannu biyu biyu
ganin hidimar da Aisha take musu muddun zataso saita kawo musu girke girke masu
mutukar dadi ta dauke su tamkar sune suka haife ta hakan yasa suke matukar kaunar
ta, wurin shida saura suka gama taya Mamie aiki inda nan bilki taja Aisha bedroom
din Mamie a cewarsu bayi zasu shiga, kwalliya taima Aishar mai kyau sai zuba kamshi
takeyi nan suka fito bilki tanama Mamie dake zaune a parlor sallama ya shigo cikin
shigar kananan kaya hannun shi rikeda katuwar Leda da Alama siyya yaima iyayan
nashi, mintsinin Aisha bilki tayi tana mata nunu da ido Wanda Aishar ta fahimce
abunda take nufi darasin da sukayi yau takeso yafara aiki tun yanzu, 'mai sona,
Aisha ta furta hadeda kashe masa ido daya Wanda chak ya tsaya kamar Wanda akaima
umarni kodai kunnan shi ke jiyo mishi gaibu? inda takarasa wurinshi cikin natsuwa
tareda amsar ledar hannun shi, 'sannu da zuwa Ur Excellency, ta furta cikin
yalwatatciyar murmushi harda dan riko hannun shi inda ya bita zagwai zagwai kamar
rakumi tagama kashe shida mamaki, Anya Aisha Nada hankali kuwa? Meye haka kuma?
Mamie kuwa sun gama burgeta kana ganinsu kaga masoyan da suka jike a soyya hakan
yasa taita zuba murmushi tareda Kara godema Allah daya Kara hade kansu, oooh namiji
munafuki ji yanda ya bita saikace bashi bane yayi gudun hijira ranar da aka daura
musu Aure,oooh yaran yanzu saisu, Mamie take zancen zuci inda takosa daddy yadawo
taimasa Albishir, Bilki kuwa Dan dukawa tayi ta gaishe da AK, ina wuni yaya, kallon
ta yayi ganin ko kallon Arziki bata masa tun daga Randa ta same shi yana dukan
Aisha ko sallama batayi idan tazo gidan, bata jira amsar shiba nanta waiga ta kalli
Aisha, oooh sister saboda yaya AK yazo shiyasa aka Fasa rakani bakomai Mamie kinga
tun yanzu anfara min hannunka mai sanda koh idan naji haushi nima inyi Aure, 'da
gskiar su takwara ta kema kiyi Aure ki kyale mun yara na banasan Sa ido, yauwa
Mamie gaya mata, inji Aisha tafadi tana tunkarar dinning dinda suka gama jera
abinci akai, 'bari ma kigani mijina zan sama abinci nasan baici komai ba tunda yau
ban wuni a gida ba shikuma ba abincin waje yake ciba, 'aiko dai ya gado daddyn kune
daughter shima haka yakeyi baicin abincin kowa inba nawa ba, Wucewa bilki tayi
renta yayi fari fes ganin tunda AK ya shigo da sallama yana zaune kamar Wanda aka
dasa shiko gogan sai bin kowa dai'dai yakeyi da ido yana ganin Dan karamin dramar
da ake tsarawa a parlon nasu, shirya abincin tayi a gabansa inda shima ya kalleta,
wato dashi zata buga game kenan ohk let's c who will succeed, yafadi murmushi a
fuskarsa, 'Amma kinsan bani kadai nake cin abinci bako? Mamie kinga saboda gulmar
ganinki yau takicin abinci dani ya fadi da iyakar gaskiyar Sa yayinda ya Mike harda
rikoma Aisha Hannu zaunarda ita yayi a kasan carpet din shima ya sauka, bari in
dauko extra spoon tafadi tana shirin mikewa, 'nooo honey bunch ban yarda ba yanda
mukeyi a gida zamuyi da spoon daya zamuci, yafadi yana mata kallon let's keep
playing the game, 'ooooh ni Bilkisu naga abunda yafara fin karfina haka soyyar ta
maidaku? Babu ko kunya AK kuyi abunku lokacin kune nima bari in lalubo tsohon
mijina inji inda yake tafadi tareda dosar dakinta dauko waya ta kira daddy a
cewarta itama tanada mijin kuma ta iya soyyar, tana wucewa ya dauko full spoon
dinda ya cika tafda shinkafa da miya bakin Aisha ya dosa murmushin mugunta kwance a
fuskarsa saida yazo saitin bakinta ya Saki spoon din nan abincin ya zube a jikinta
harda chokalin, Oooops am sooo sorry darling wiffy yafadi yanasa hannu da niyyar
kakkabe mata da gayyah yake dukanta inda cikin ikon Allah gaba daya ta naimi tsoran
AK a Ranta ta rasa, Worry not hubby karka damu Anything for you my luv, tafadi
tareda shafa gefen bakinsa, 'Anya Aisha ba gamo tayi ba😫wasa wasa fa yaga kamar ba
Aishar saba har cikin idonshi take kallo yanzu batako kyaftawa a'a kodai a Asibiti
tayi gamo da Aljanar rashin kunya ne? Idan zai tuna da safe har kuka saida taimasa
tana durkushe a gabansa, Mamie ceta katse su inda take shaida musu daddy nakan
hanya, 'yauwa dama magana nakeso inyi daxu dukanku, tattara kwanukan dake wurin
Aisha tayi Wanda itace ta cinye kusan abincin dake ciki, saida ta gyara gun sannan
tadawo ta zauna tareda fuskantar Mamie, banaso ku fassara maganata nasan komai nufi
ne daga Allah babu mai badawa kuma mai hanawa sai shi, tafadi ko kadan Aisha banaso
ki fassara magana ta dawata fuka sanin kanki ne bakida banbanci da diyarda na Haifa
a cikina harga Allah ina jinki sosai a Raina, abun na damuna Aisha nakosa inga
jikokina nida daddyn ku a karo da dama munso muyi muku Maganar amma bamusan ta inda
zamu fara ba idan wani Abu ne na daban sai a nema taimako idan likita zaku gani
gara asan abunyi amma Abu shekara Uku shiru kodai kun tsaya sisi ne? Tafadi tareda
kafe Aishar da ido, yauwa Mamie AK ya furta Ranshi fal farincikin yanda zai gumama
Aisha, Wlh Mamie maganarki haka take, ya furta tareda mikewa ya koma kujeran Mamie,
kwalla ne suka fara ambaliya a fuskar Aisha dake Duke a kasa ganin yanda AK ya Mike
tasan wani bomb din zai Dana mata, "have confidence wani sashi na zuciyarta kece
mata, dnt let him see ur weaknesses again u r far more beyond that Aisha.
, subhanallah Daughter maiya faru kuka kuma? Idan maganata yamiki zafi kiyi hakuri
daughter......ko kadan Mamie kin Sosa mun abunda ke damuna wlh babu yanda zanyi ne
Allah ne shaida ta shike bani maganin Hana daukar ciki a cewarsa bayaso jikina ya
baci ina haihuwa zan Zama mama kuma bai shirya Zama baba ba Wanda shine da naki
amincewa munsamu sabani akan hakan yafita harkata haka nan na Amince amma wlh raina
baiso ba amincewata shine sanadiyyan shiryawan da mukayi yanzu tareda Soyyah da
farinciki a gidanmu.....Ashe kai mutumin banza ne Abdulkareem? Innalillahi mai nake
shirin ji ni bilki? Whatttttttt sukaji an furta da karfi yayinda kallon su yakoma
kan Daddy da shigowar shi yayi daidai da bayanin da Aishar keyi, mikewa AK yayi
jikinshi na digarda zufa kallon Aishar yayi charaf suka hada ido nanta kashe mishi
ido daya harda gwalo fuskarta taf da ruwan hawaye.

*Mrs Saddiq Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah*

26

Daddy wlh ba haka bane, Daddy.....'Bani kaima ba Abdulkareem kanka ka cuta bakowa
ba Kekuma Allah ya saka miki cutar dake dayake yi, wlh kaji na rantse nakusa
sallama ka cikin yarana AK, daddy yafadi da iyakar gskiar Sa, akan yarinyar nan zan
dauki mummunan hukunci fiyeda tunanin ka mutum banza kawai Wanda baisan ciwon kansa
ba, wucewa dakinsa daddy yayi cikeda takaici, "Ai Alhaji kai naka kadan ne
Abdulkareem muddin ka Kara musgunama yarinyar nan ban yafe maka ba, kekuma daga
yau sai yau idan yakara baki magani kikasha kema ban yafe miki ba menene Amfanin
iyaye? Kema Aisha Ashe wawiya ce ina miki kallon mai hankali maiyasa tuntuni baki
sanar damu ba? Idan ya lalata miki mahaifa wa keda asara? Ke kikeda asara shi
namiji ne zai iya nemo Wata ta Haifa masa kefa? Yagama da rayuwar ki idan maganin
yakeso shi maiyasa bai Shaba? Yi shiru share hawayen ki kikuma kwantar da
hankalinki insha Allah zan dinga zuwa gidan naku akai akai inga yanda zaman naku
yake muddun naga sabani daga gareka zakasha mamaki na kuwa, 'rungume Aisha Mamie
tayi tana Kara lallashin ta tareda goge mata hawaye, 'maza ku wuce kubar mana gida,
Mamie tafadi tana banka mishi harara, diyata zamu karasa magana a waya saida safe,
shigewa daki Mamie tayi bata Kara waiwayowa ba, hijab dinta ta dauko tareda
sakawa inda yake binta dawani mugun kallo yama rasa mai zai Mata ko kadan taki bari
su hada ido dukda tasan kallon ta yakeyi, saida ta shirya tsaf ta wuce ta gefen shi
kamar batasan da mutum a gurin ba kai tsaye tabar gidan domin neman Abun hawa a
cewarta tunda ba tare sukazo ba bataga dalilin da zaisa su koma tare ba ta tabbata
bazai taba daukar ta a motarsa ba, tana tsaye baki titi tana neman Abun hawa ya
wuce ta gabanta da gudu kamar zai tashi sama harda badeta da kura, nan jama'a
akaita magana akan irinsu masu banke yaran mutane saikace sunfi kowa uziri, mtsew
aikin banza koka tsaya ba shiga motarka zanyi ba, kodata koma gida kai tsaye
dakinta ta shiga tareda yin sallar magrib bata nema komai ba kasancewar cikinta a
cike yake hakan yasa ta dauki wanka tareda tsara kwalliya mai burgewa yar Karamar
matsatsiyar rigarda bai gama rufe mata cinya tasaka maroon color mai santi yanada
siririyar hannu Rabin kirjinta a waje ita kanta saida taji kunyar kanta amma tariga
ta kudiri daga rana irinta yau zaman Yar'duniya zata dinga yi a cikin gidannan gara
tazama yar'duniyar da yake mata fatan Zama kullum gashin kanta ta Kara gyarawa
tareda tufke shida ribom din kayan tayi matukar kyau ita kanta tasan tayi kyau ba
karya, turaruka masu sanyin kamshi ta fesa a kowace ga'ba na jikinta inda daga
karshe ta shafe jikinta dawata fitinanniyar humran matan Aure Wanda wani zuwa
datayi Mamie tabata harda mata bayanin amfanin shi wato ba'a sashi sai an shirya🤪
🙊, parlor ta koma tana tafiya tana yauki kamar karkashi inda ta jona bornar na
turaran wuta nan kamshi ya mamaye kowani lungu na gidan ta kunna TV tareda kure
volum tashar waka ta kama bakinta na taunar cingum strawberry na Orbit ji kake
karararassss rasss Ras cikin kwarewa kallo daya zakai mata kasan Aisha ta rikide
tadawo Yar'duniya a hankali ta Mike tsaye tana taka rawa cikin kwarewa da nishadi
bata damuda volum dinda ta kure ba dama haka takeso tanaso a yau basai gobe ba ta
kararma farin mugu da ruwan kanshi itama ta cike katin zaman cikakkiyar bakar
muguwa daga rana tayau, 'kwance yake rufda ciki abun duniya dukya dameshi akan
Bakar yarinyar nan iyayan shi ke neman yimai baki, idan baiyi wasa fa tabbas Dan
hakkin daya raina zai kwakule masa ido bawai tsolewa ba, sauti yafara ji sama sama
tun yanaji kadan kadan harya fara jin abun yawuce hankali saikace club an kure
volume ga tashin speaker's ta ko'ina tsaki yaja tabbatar da cewa a cikin gidan shi
karan ke fitowa, belt din wandon shi ya zaro sanye da farar singlate da blue dogon
wando a jikinsa, bude kofar dakin yayi mai zai gani? Wata ce sanye da Killer
dressing kallo daya zakai mata kasan babbar mace ce babu Raini duk inda ake neman
classy beb takai, baki bude yake gwale ido ganin yanda take rawar cikin kwarewa
tana kasa da sama sai bankarewa takeyi kamar kifin tarwa'dah, tunda ya shigo Taga
shigowar shi hakan yasa takara bada himma cikin ikon Allah ko kadan neman kunyarta
tayi ta rasa cike takeda nishadi, yayinda AK ya karaso sosai dafda
ita......AAAAA'EEEEEESHAAAA Ya fadi cikin rawar murya inda dakyar ya motsa hannun
Wanda ke rikeda belt da niyyar zuba mata amma belt din yakasa sauka jikinta ganin
yanda Tai masifar tafiya da tunanin shi ga jarababben kamshin ta Wanda ke kashe
mishi jiki, wai dama haka matarshi keda kyau? Amma yau tadawo mishi yar duniya
zalla, kafun ya Ankara ta fada jikinsa inda cikin salon rawarta mai motsa Sha'awar
duk wani namiji mai jini a jiki kuma mai cikakkiyar lfy tafara shafa jikinshi da
mazaunan ta tana sama da kasa, mai zan gani ni Mamie??😳 AK nagani ya Saki belt
dinshi a kasa jiki na rawa gashin jikinsa dukya gama mikewa.........dinshi ta Mike
kem kamar zata Fasa wandon shi🙊 saitin kunnan shi takoma inda tafara taunar cingum
dinta Kararassssass rass harshe ta fito dashi kumatun shi take lasa a hankali harta
kai gefen kunnan shi murya chan kasa kasa cikin kasala tace, "how did u lyk the new
me? Congratulations daga yau zaka fara Rayuwa da tantiriyar yar'duniya Original mai
kwalin karatun duniyanci ta kowani fanni na Dade da zuwa bautar kasa ai hakan yasa
har Award gwamnatin tarayyah tabani a fanin duniyanci yanzu nafara daukar hanyar
Zama international Yar'duniya tareda taimako da hadin kanka, kanshi ta juyo saitin
fuskarta numfashin su na haduwa idonshi sun kankance sunyi jajir, 'my love tace
mishi tareda sakin makirin murmushi, sakinsa tayi batayi taku biyu ba taji ya
finciko ta ba tareda bata lokaci ba ya hada bakinsu wuri daya kamar mayunwacin zaki
ture shi takeyi hade hannuwan ta yayi duka biyun da hannun shi daya inda yasa dayan
hannun da karfi ya janye rigar jikinta wacce yafara barkawa, azaba ya ishe Aisha
jin lips dinta takeyi kamar ana cire su ta tabbata Yaji mata ciwo, kasan carpet ya
kwantar da ita tareda danneta da kafafun shi farar singlate dinshi yahau zamewa,
'bake yar'duniya ba abunda kika Dade kinaso zan baki harda kaima iyayena karata
karki damu bazan baki maganin Hana daukan ciki yauba, ranarki ce kin sameni a
bonanza game koh? Let's c Wanda zaiyi nasara tsakanin mu, ihu takeyi iya karfin ta
inda take dukanshi da hannuwa duka biyun ko kadan ta tsani AK bazata taba bashi
budurcin taba ALKAWARI ne ta gwammace ta rabama Gayu a titi, budurcin datasha
gwagwarmaya ta dalilin karewa budurcin da jama'ar gari dashi kansa ke zaginta akan
tagama zubarwa akan mai zata bashi Dare daya? Daga sama nooo bai chanchanci samun
Wannan budurcin ba insha Allah inda akasan darajar shi anan zata bada..........
wani gigitaccen Kara tasaka jin yakara keta rigarta daga sama har kasa inda komai
na jikinta ya bayyana gashi dama ko bra batasa ba falon nan nasu tar da hasken
lantarki kafun ta Ankara taji bakin shi akan kirjinta nan ya shiga sarrafata yana
sude ta tas kamar yasamu swt inda tuni ya Dade da hadiye cingum din bakinta ta
yagama lulawa duniyar sama.

*Ooopppss

♀ kuyi hakuri salon labarin ne yazo da hakan babu yanda na iya🙈🏃🏻‍‍♀.*

*Mrs sadeeq Rumah*💅🏻


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Masu neman littafi daga farko ta private kuyi hakuri bazan iya turama kowa ba,
amfanin groups Dina kenan wasu suna group din but saisun biyoni private bayan
kullum cikin turowa akeyi a group din babu fashi koka tambaya ko baka tambaya ba
sai an turo Ustaziya fans🧕🏼 1and 2 ina godiya🏼😍😍i luv ur comments and
encouragements especially ur Du'a a gareni Anty Mamie's Novel Groups kuma ina
yunku😍😍😍❤wlh inajin dadin comments dinku ko banyi niyyar typing ba sai nayi.*

*Dedicated to sister Husnah.*

27

Ba karamin yamutsa ta yakeyi ba inda taci kuka harta gode Allah babu yanda batayi
kokari tureshi ba inaa hakan ya faskara lokaci mai tsawo ya dauka yana Abu daya,
kokarin shigarta yakeyi karfi da Yaji inda ruwan kanshi yagama kwancewa yama rasa
yanda zaiyi yarasa ta inda zai fara, ganin ta'asar da yake shirin mata daduk gskiar
Sa yasa tafara neman ma kanta mafita ko kashe ta zaiyi bazata bashi kanta ba
dabara ceta zo mata nanda nan tafara biye masa tana maida martanin duk abunda yake
mata saida yagama sakin jiki sosai harya Mike daga kanta tareda jin dadin duk
abunda take masa asan Ranshi sukoma bedroom dinshi inda Aisha takara lulawa dashi
sabuwar Rayuwa, ganin yanda jikinshi yasaki numfashi sama sama yakeyi da karfin
gaske ta Mike tareda hankade shi daga jikinta remote din TV Wanda ke kusa da ita ta
dauka da iya karfin ta ta kwala masa akai, jiki a mace yake shirin rarumo ta inda
taja baya da gudu tana Ajiyar zuciya Kare kirjinta tashiga yi ba halin daukan
yagaggiyar rigarta, 'inaaa Dan samari yanzu Aisha tawuce ma tunanin ka kaga wannan
jikin da kake gani wlh wlh haramiyar ka sai gani sai kallo sai hadiye miyau ka
dauki Abunda yafaru ayau a matsayin Alakoro ne nabaka bawai danka chanchanta ba,
Ashe kaima ba daga baya ba kaima dan'iskan kanka ne mugu har kakeda bakin kiran
wani Dan iska? Daidai nake dakai wlh duk abunda zai faru a gidannan yadade bai faru
ba duk Randa kakara gigin yimun fyade saina maka mugun I'lla, garani kwartaye na
kaimusu kaina nakeyi kaifa? Kirikiri kake shirin mun fyade da tun farko kayi biyyah
Dana Dan lasa maka koda kadan ne Malam ka sauke girman kai bawai ka nema da karfi
ba, da gudu ta shiga dakinta tareda Danna key ganin yanda ya zaburo da karfin gske
ya tinkaro ta inda yaita buga kofar kamar zai ballata Aisha kuwa kirjinta kamar
zai fadi kasa bakaramin kokari tayi ba wurin mishi tsiwa nan tsoronsa ya darzu a
zuciyarta jin kalaman da yakeyi, 'ki tsaya mana Dana nuna miki banbanci na da
sauran kwartayan ki Karamar Mara kunya karyan cika baki kikeyi, buga kofar yakeyi
sosai, bazaki bude ba? Malama dalla ki bude kofar tunda ba taki bace nayi miki
Alkawarin muddin na shigo dakin nan saina yagalgala ki yanda ko likitoci bazasu
samu nasaran hadaki ba, tanajin furucin dayayi tayi maza ta daura towel tareda
zumbula katon hijab har kasa bayinta ta shiga takara Danna key jiki na rawa tana
kuka, 'na shiga Uku na Wlh idan wani Abu ya sameni bilki sainaci ubanki kin ballo
mun ruwan dayafi karfi na ni Aisha Naga ta kaina, Daki yakoma yafara lalubo mukulan
gidan aiko cikin nasara yaci karo dasu nan yadawo yafara gwadawa daya bayan daya
amma inaa ba nasara kasancewar tabar mukuli a ciki bata zare ba, ihu yakeyi kamar
mayunwacin zaki inda Aisha tagama kule shi gawata jarabar data dame shi shiba
manemin mata ba dayau babu abunda zai hanashi kwana da Yammata biyu amma yana
mutukar kyamar zina insha Allah da matar sunnah zai fara sanin mace, 'Allah ya isa
muguwa wlh ki rubuta ki ajiye zamu hadu kuma duk Randa muka hadu zakisan wanene AK,
wucewa yayi tareda maida kayan jikinsa inda ya tsuguna a wurinda abun yafaru kwalla
Yaji yana diga a kumatun shi, Yah Allah kada ka jarabceni da sha'awar yarinyar nan
wlh zai nakasa ni zaimun illah wyyooo marana, dama akwai ranarda zanyi Sha'awar
Aisha haka? Sha'awar kuma mahaukaciya? kwanciya yayi a wurin hannun shi kan
cikinshi inda abunda yafaru yaita dawo mishi one by one, Bakar muguwa muguwa muguwa
kin gama dani, dama haka ma'aurata keji? Hmmmm a haka ma dukya rikice inaga ya biya
bukatarsa? Kila saiya suma, wani sashi na zuciyarsa ke bashi Amsa, kaga yarinya sai
laushin jikin tsiya wlh wlh Aure zanyi Danni ba dotse bane bazan shiga halaka ba
duk inda zan nemo mata insha Allah cikin satin nan zan Auri natsatsiyar mace kamila
budurwa dal a Leda swt 18 insha Allah saina kunsa miki bakin ciki fiyeda Wanda kika
Sani a ciki karyar iskanci kikeyi saina Rama abunda kikai mun yau saikin kawo mun
kanki da kanki I promise you saikin nemeni akan in taba jikinki saboda bakar
Sha'awar dazamu dinga cusa miki nida Swt 18 kuma bazaki Kara fita gidannan ba daga
yau sai yau, da karfi yake fada da Alama dai AK ya zare a daran yau, mikewa yayi
hannu akan Mara dakyar ya karasa kitchen inda yahada ruwan Lipton baki wuluk da
lemun tsami mai yawa, daki yakoma yana ma Aisha Allah ya'isa yana sha wato saida
tasamu nasarar seducing dinshi hankalinta ya kwanta baisan waya koya mata mugunta
ba yarinya yau kawai dukta birkice ta chanza daga safe zuwan Dare tazama muguwa,
jinshi yakeyi kamar zai mutu saboda ciwon Mara, 'batace idan ka roketa zata baka
ba? Why not tadan baka koda nayau ne karage zafi kodan kadan basai da yawaba, 'what
ni? In roketa? Allah shi kyauta in roki Yar'duniyar nan jikinta Allah ya kiyaye
nida nake shirin Auran Yar'shila in bude abuna inkuma mata irin rainon da nakeso,
Shi kadai yaketa zancen shi kamar Mara hankali yanda yaga rana haka yaga Dare Aisha
ma hakane a wurinta inda bakinta saida ya kumbura gasa jikinta tayi a bayin tareda
godema Allah daya kubutar da ita a hannun farin mugu tabbas babu abunda zai Hana
bai mata illah ba, ko'a haka ya barta tasha azaba jikinta Radadin azaba kawai yake
musamman kirjinta dayasha matsa.

Washe gari baba mai gadi yasamu tareda mashi warning kada ya kuskura yabar Aisha
takara fita gidan nan daga rana tayau, idan ba haka ba kuwa a bakin aikinsa, kai
koni nace kabarta ta fita kada kabari, yafadi tareda wucewa Asibiti yakeso yaje
akara hadamai magani Susan yanda zasuyi dashi, wlh Aure nidake yanzu muka fara mutu
ka raba, 'ya furta yayinda ya shiga motarsa yanata ruwan masifa, 'anya maigida
lafiya lau yake kuwa? Inji baba mai gadi ganin yanda AK ke magana da masifa shi
kadai dukda jiya yanadan jiyo ihu ihu a cikin gidan nasu, Ooooh Allah ka daidaita
tsakanin ma'auratan nan gida saikace barikin sojoji kulum cikin tashin hankali.

Aisha najin fitarshi misalin takwas din safe tafito sauri sauri gudu gudu ta shiga
kitchen kayan shayi ta kwasa sosai da cornflakes tareda Golden moon duk wani abun
da zata bukata na kwana biyu ta diba, inda ta maida komai dakinta, batada matsalar
ruwan zafi kassncewar tanada shi a toilet, sauri sauri ta dafa indomie tareda soya
kwai guda biyu inda tashiga dakinta tana dariyar diramar abunda ya faru jiya, Ooooh
ran maza ya baci dole inyi Yaji a dakina sai an kwana biyu, tafadi tareda dariyar
mugunta.

*A gurguje.*

AK yana daya daga cikin malaman da Malam liman kema karatu bayan sallar Isha'e na
kowace ranar daran juma'a inda yawanci manya manyan masu kudi ne da Yan'kasuwa masu
bukatar karo ilimi hakan yasa jefi jefi yanama Malam liman Alheri yakai mishi har
gida inda wani zubin kayan Abinci yake cikawa tafda motarshi yasa yara suyita
shigarwa ciki, ba AK kawai ba yawancin daliban Malam liman haka suke masa Alheri
tunda karatun da yake musu bana kudi bane hakan kesasu jin dadi suma suke kyautata
mishi matuka, 'Ranar juma'a bayan an sauko masallaci kamar yanda Ak yasaba jefi
jefi, makullin motarshi yaba yaron office dinshi tareda bashi kudi masu yawa akan
yasiyo mishi duk wani abunda ake bukata na abinci yakawo mishi, cikin minti talatin
yadawo da uban kaya shake a cikin booth din mota inda AK dake sanye da coffie brown
shaddar gezner tasha aiki sai kyalli yakeyi yayinda ya murza hula masha Allah daka
ganshi kaga kyakyawan matashin da kudi suka zauna daram da duwawun su burin kowace
mace, kai tsaye ya tunkari unguwar sabon garin Kaduna yana tafiya tareda jin tafsir
a motarshi harya isa kofar gidan sanannan malamin, inda batareda bata lokaci ba
yasamu yara suka fara shigada kayan ciki inda ya raba musu dari biyu biyu nan danan
yara suka cika wurin har rige rigen dauka akeyi, Sanye takeda bakin hijab dogo har
kasa kamar koda yaushe fuskarta da kwalliya Mara hayaniya inda Tafito domin zuwa
shagon dake kusada su mama ta aiketa, charaf suka hada idanu, Alhamdullah mashe
Allah da wannan kyakyawar halittar leemah ta furta a zuciyarta inda tagaza dauke
idonta a kanshi ba karamin rikita ta kyaunshi yayi ba, Ga uwa uba kallo daya zakai
masa kasan farare sun zauna daram da duwawun su, kallon ta yakeyi ganin yanda take
tafiya natsuwar ta tamishi inda sallamar Malam liman ne ya katse musu kallon kallon
da sukeyi.

*Mrs Sadieeq Rumah*💅🏻


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?*‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍

*Written by Anty Mamie*

Naga kurafe kurafen ku harda masu biyoni private akan kada AK ya Auri leemah
littafin zai baci, wasu kuma suce sunfiso ya Aureta, ku cigaba da bina kuga karshan
littafin please, tun kafun infara rubutawa nagama tsara littafina, godiya nakeyi😍
Washe
🤦🏻‍

♀ ‍♀ groups dinda na bude saboda littafin nan sunada yawa masoya kullum
bulbulowa sukeyi ta inda bana zato wayata daukewa take😢 masoya kunada dadi wlh😍
Dan Allah duk Maison shiga group ku hada kanku ku bude sannan kusani🤣zan zauna
daram in dinga muku posting insha Allah. Please a dinga mun uziri.🙏🏼

*Dedicated to sister Husnah*

28

Iya rikicewa leemah ta rude akan surar AK idan yagama tafiya da tunanin ta sauri
sauri takeyi ta amso sakon da aka aiketa tanaso ta Kara gilmawa ta gabanshi tabbas
ba'a taba namijin daya wuce da dukkan tunaninta lokaci daya kamar hot guy dinnan
Everything about him, his looks, dressing, kamshin turaran shi tasha hurda da manya
hadaddun guys but this very one he is very special, 'gaisawa sukayi da Malam inda
yaita zubama AK Addu'a nan suka Dan fara fira sama sama inda AK ya nuna Alamar
tafiya zaiyi sunanan tsaye aka gama shigarda komai inda yayi daidai da dawowar
leemah cikin tafiyarta ta natsuwa wacce takeyi ta musamman tazo gilmawa inda har
saida Malam ya lurada kallonta da AK yakeyi inda Malam ya kauda kai tareda gyaran
murya, leemah kuwa bata kalle shiba saida tazo gafda su tadaga idanun ta Wanda
tagama narkar dasu cikin salo taimasa wani kallo guda daya kwakwara mai wuyar
fassara, dauke kanta tayi tareda shiga cikin gida inda AK ya Saki Ajiyar zuciya,
'gskia rabonda yaga mace mai tarin kamala kamar yarinyar nan ya manta, abun Sha'awa
gata very Yong and cute, yasan Aisha tafita kyau nesa ba kusa ba, but wannan tafi
Aisha Kuruciya, haske Da uwa uba natsuwa da kamun kai, gyaran murya Malam yayi a
karona biyu ganin AK ya Lula duniyar tunani, 'cikin kame kame yayinda kunya tadan
kama shi ganin kallon da Malam ke masa, yanaso yaima Malam maganan ta amma yanajin
kunya matuka ganin tsananin kamarda takeyi da Malam din ya tabbata diyarsa ce,
sallama yaima Malam inda kai tsaye ya doshi gida cikeda tunani harga Allah tunda ya
taso a duniya baya Sha'awar Auran mata biyu, aso samu mace daya rak ta isheshi
rayuwar duniya tohya zaiyi? Aisha tariga tagama dashi koba komai shiba dutse bane
bayaso yafada halaka shekara talatin da biyar ba wasa ba dole ce zatasa yayi Aure
saboda Martaban da Asalin gidan dakuma yarda dayayi da tarbiyyan Malam liman, wasa
wasa cikin kwana biyu AK ya kammala dukkan binciken da zaiyi gameda halayyan halima
wacce shaidar data samu da yabo a unguwan nasu saida yabashi mamaki inda yakara jin
San abun sosai a Ranshi, kai tsaye ya tunkari Malam liman da maganar batareda bata
lokaci ba yace ya yarje masa ya nemeta, hmmmm ina leemah zata shiga a sabuwar
duniyar ta saboda farincikin burin rayuwarta zai tabbata Auran mijinda ta Dade tana
mafarki saidai kashe ba a lokacin nan taso su hadu ba taso ya hadu da ita a
matsayin bazawara wacce tayi Aure ta fito saboda gudun zargi harga Allah irin mijin
nan taci burin Rayuwa dashi har abada tareda yaransu bataso tabada kofar dazai
mata kallo na daban, but ya zatayi? Gskia bazata wuce damar taba zata iya hakura da
komai banda zazzafan handsome Saurayin nan insha Allah zata nema mafita dole asan
abun yi tasan tabbas tunda tanada Anty zakwai bazataji kunya ba "Wata shahararriyar
mai maganin mata ce tun daga mai'duguri take mata hadi na musamman" Kudi zata baza
mata a like ta tsaf akan AK babu abunda bazata iyayi ba kuwa itada shi kuma mutu ka
raba insha Allah.

'Soyya sukeyi Mara hayaniya Sam AK bai saba da hakan ba kasancewar baitaba yin wani
I love you I need u dawata ba hakan yasa yake ganin abun wani iri kamar shirme har
kunya ma yakeji inda leemah takebin duk wani hanyar dazata jawo hankalin shi akanta
kira 24/7 text kuwa ba'a magana har mamakin iya soyyar ta yakeyi, koda Ya tunkari
su Mamie da Daddy da maganar saida akakai ruwa rana dakyar da sudin goshi daddy ya
Amince amma da sharadin babu hannun su a ciki tunda ya dage sai yayi Auran suna
ganin hakan kamar cima Aisha fuska zaiyi daga maganar haihuwa saiya zo musu da
batun Karin Aure, saida akakai ruwa rana sannan suka amince inda ya tabbatar musu
bazai taba tozarta Aisha ba, babu abunda zai Chanza a Auran
Dazai Kara nan hankalin Mamie yadan kwanta, Ankai kudin gaisuwa tareda kayan Sa
rana inda ba'a ja bikin ba Wata Daya akasa a cewar AK yanaso ayi da wuri harga
Allah Sha'awa na neman yimasa illah inda duk abunda akeyi Aisha batasan wainar da
ake toyawa ba.

Kawayan leemah su meenah kuwa koda suka samu labari suka kuma kyalla ido sukaga AK
nanfa hankali ya tashi ganin yanda Leemah tayi musu fintinkau a bariki dukda sun
rigata shiga Amma tafisu cin riba uwa uba zata Auri babbar harka, tsananin barikin
su saida iyayan su suka koresu a gida inda suke zaune darajarta sukeci kasancewar
gidan na mahuta, gashi kuma akan idonsu zata Auri handsome young milonia sukuma
fa? Sukare a duniya? Inaaaa nanfa hassada mai zafi ya darsu a zuciyar su inda ta
rokesu bataso mahuta yasan da Auran da zatayi suka Amsa mata akan ana Tare bazasu
gaya masa ba.

Amarya fa sai lakuce lakuce da banke banke da like like takeyi kullum cikin hayakin
HQ take saikace yar'bori maganin mata kuwa sha take kamar hauka daga karshe saida
yasata zawo saboda shan haukan da takeyi Anty zakwai kuwa ta kuke ta dage tun daga
Maiduguri tazo hada leemah inda tai mata masauki a dakinta na isa kaita, kudi sosai
tasamu wurin mahuta inda ya sakin mata Aljihu ganin ta chanza test da harta fara
sire mishi ta bude dayawa amma yanzu dayaji sabon sinadari nan ya ware Aljihu, Wata
kawarta ce Deejah bariki tabata shawara akan zata Rakata asibiti a dinke ta tsaf
kamar kwarya yanda ko AK na aiki da Aljanu bazai taba gane ta bude ba, nan kuwa
leemah tayi matukar farinciki San AK take kamar hauka nan takara sakinma mahuta
jiki ya kwashi gara aikuwa tasamu yanda takeso kudi yabata sosai ba tareda bata
lokaci ba suka nufi asibi inda saida aka kankare fatar wurin aka goge, subhanallah
Karamar tiyata akai mata a wurin *"hattara mata wani sabon bala'e daya shigo kenan
yanzu mace saitaje Asibiti Yammata harda matan Aure akan a dinki su tsaf ko kunya
babu ku wage jiki da sunan gyara haka za'ai ta dinke ku saikace buhun masara kai
jama'a waiduk kan da'namiji😕 hmm Wata kotayi a banza wlh kozai chanza miki na
lokaci kadan ne zaki Kara budewa ke kenan kin dinga zuwa ana miki dinki kenan?
Saikace wacce ta haihu? Shi namijin maiya dinke kokuma mai yakeyi domin samun
gamsuwar ki? Wlh wani ko magani bazai taba Shaba domin burgeki amma duk kudinki
yagama
🤦🏻‍

♀ karewa akan maganin mata‍♀ karshe su nakasa miki mahaifa GA cancer datai
yawa a mata yanzu, subhanallah wata ma yanzu tana samun ciki yana shiga Wata tara
zataje asibiti ta kwanta aimata operation tun bata fara nakuda ba wai ita tayi
dabara bataso ta bude ita uwar sisi da gayu maisan gamsar da namijin da bazakiyi
bajinta ba ko tsoran lafiyar ta batayi, Allah yasa mu dace🙏*

Rabonda Aisha tasa AK a ido an kwana biyu tun tana boyema ganin shi harta daina
kwata kwata baya Zama a gida inda kayan abincin su yayi kasa sosai tanaso taimasa
magana batasan ta yanda zata fara ba, dukda shike duba komai zaiba yaron aikin shi
kudi ya siyo duk abunda ake bukata saidai taga an jera mata su a kitchen, tana
zaune sanye da Pakistan Riga da wando, wandon pencil rigar ma batada wani tsawo
pink mai kyau tasha ado sai zuba kamshi takeyi kanta daure da karamin rober band,
shigowa parlon yayi yana waya da leemah cikin nishadi dukda daga wurinta yake amma
ka'eda ne yana barin gunta zata kira shi suyita waya harya kai gida yauma hakan ne,
burki yadan ja cikin mamakin ganin Aisha zaune a parlor tana kallo harga Allah
rabonda yasata a ido ya manta dukda yaga tadan rame amma kuma takara kyau, 'matar
so just a minute I will call you, kashe wayar yayi 'A'a su Ustazai ne Ashe kunyi
wuyar gani, yafadi cekeda zolaya inda saida tayi mamakin shi wai yau itace yake
zolaya, tunda Allah yasa mun hadu yau wlh Sam nama manta dake a gidan, cut the
story short, yauwa next week insha Allah za'a kawo mun matar so, Amarya kuma
uwargida ta swt 18 Asalin Ustaziya diyar mutunci diyar malamai da kamala kimtsatiya
kamila, hafiza, malama bawai a suna ba nooo, uwa uba uwa ga yarana insha Allah,
farincikin AK ina fatan zaki bita sau da kafa saboda gudun shiga matsala a wurina?
Biyya dole ce gara ki kwantar da hankalinki zaki karu da ita yauda gobe na tabbata
zata saki a hanya kema kidanyi hankali, yafadi yana dariyar keta, kallon shi tayi
daga sama har kasa dariya ciki ciki, 'heeeyeeeeah Allah tafadi yayinda ta tafa
hannu duka biyun, sannu namiji, Sannu Ango kasha kamshi lallai ka cika namiji
Gwarzo ai abunda ya kamata kayi tuntuni kenan Allah yakawo matar so, Allah yakara
kauna tsakanin kada matar so, Allah kuma yakara Soyyah, mikewa tayi yayinda takara
kallon shi shekeke, daga kai har matarka bakwa gabana gara tun kafun ta karaso kaja
mata kunne ka ajiye rikakkiyar Yar'duniya billahillazi ta shiga gonata nan zaku
Kara tantance banbancin diyar malamai da diyar mai'shayi yar duniya ubanta zataci
ni baka gabana daga kai har ita, akwai lokacin da nake jira yanayi zan cikama
rigata iska inbar muku gidan Soyyah kukara soyewa, Allah ya sanya Alkairi ango mai
jiran gado, daki ta nufa tana tafiya tana juya mazauni harda yar Karamar waka,

'Ga ango Na Amarya,


"Inaaa Ango Na Amarya,
" Kai sai ango Na Amarya.

yayinda yabita da kallo baki bude samun kanshi yayi dajin takaicin maganar
datayi saiyaji Auran yadan sire mishi ko kadan ba haka yaso tayi ba aiya dauka
shake shi zatayi tana rokon shi kada yaimata kishiya ta tuba inda zai shuka mata
Rashin mutunci sosai Lallai kodan kishin da mata keyi Aisha bata masa kishiya fa
yace zaimata muguwar yarinya maiya mata a Rayuwa Wanda takasa nuna jinjirin kishi
akan Sa? Wace irin kiyayya ce haka? Ada idan zai tuna ai tana matukar sansa dama so
na chanzawa? Ikon Allah, Kodan kukan da mata keyi baiga Alamar tanada niyyar yiba.

Tana shiga daki ta kulle da makulli toshe bakinta tayi nan bakin kofa ta zube
tareda fashewa da kuka mai kona zuciya.

*Mrs Saddiq Rumah 💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Gobe bazan samu daman typing ba saboda wani babban uzirin dake gabana.*
*Dedicated to sister Husnah.*

29

Tayi kuka tayi tayi harta gode Allah, harga Allah taji ciwo kishiya da ciwo koba
komai ita macece sannan cikin soyyar AK ta rayu dukda batajin shi kamar da amma
wani zazzafan kishin shine ya kamata ganin zai fara sanin Wata mace kafun ita dukda
ta cire rai akanshi amma samun kanta tayi cikin matukar kishin hakan cikin Daren ta
kira bilki tareda gaya mata abunda ke faruwa inda taita kwantar mata da hankali
yayinda ta shaida mata zatazo idan gari ya waye, da ciwon kai mai zafi tareda
zazzabi ta kwana inda duk yanda taso ta raya daran da Rokon Allah hakan ya faskara
jikinta ba abunda yakeyi sai rawa inda kirjinta kamar zai fashe a'haka daran nata
ya kasance gogan kuwa dakinshi ya shiga jikin shi yayi sanyi leemah ceta kirashi a
waya yayinda ya kasa dauka kashe wayar yayi gaba daya ya cillar da ita gefe kwata
kwata bayajin dadin jikinsa, shirye shirye nata wakana AK yakara dagewa wurin
gyaran gidanshi dukda babu abunda gidan ke bukata amma saida ya chanza furniture's
din gidan kaf banda na dakin Aisha harta kitchen bai bari ba kasancewar kitchen din
kwaya daya tak shiyasa Aisha taci darajar gyaran dazaiyi yanzu ne zaiyi Aure kudi
yake kashewa bana wasa ba, babu yanda Malam liman baiyi ba Sam AK yace baya bukatar
ko Allura kobai Auri leemah ba shimai iya mata kayan daki ne darajar Malam din a
wurinsa, hmmm gida fa ba'a magana komai ya dauka har barayin mai'gadi saida aka
gyara lefe yake hadawa bana wasa ba akwati dai'dai har dozin tareda manya manyan
jakar fata guda biyu yakama goma sha'hudu kenan wani abun da gayya yakeyi saboda ya
kular da Aisha amma Kota kanshi batabi aikuwa ya kulu ganin Mamie da Daddy ko
Allura basu bashi ba shiyasa yace zaima kanshi abunda ba'a tunani, fadin haduwar da
lefen daya hada yayi hmmmm bata baki ne babu ne kawai babu a ciki ango nata rawar
kai Aisha kuwa da taimakon bilki ta kwantar da hankalinta yayinda Mamie ke Kara
tausasa ta, a wannan karan ma Mamie tadau aniyar gyara Aisha a cewarta bataso abar
diyarta a baya inda Aisha har tausayin Mamie takeji ganin Wanda akeyi domin shi
baima San anayi ba sai Asarar kudi ake amma hakanan takeshe koba komai zatai fresh
maganin mata ne natural na itatuwa ba masu illah ba.

Amarya leemah ce zaune a gaban likita sai kuka takeyi kamar Ranta zai fita jin
bayanin dayai mata, lallai ba karamin sakaci da ganganci ta tafka ba tafi kowa
sanin maganin planing bai cika karban taba hakan yasa take taka'tsantsan every
month tana zuwa ana duba ta, gafda zata haduda AK ya kamata taje medical check up
amma taki haduwa da AK ya Kara mantar mata da tunanin ta, su meenah ke Kara
lallashin ta, 'please beb this is not the end of ur life remember, za'a samu mafita
insha Allah ki kwantar da hankalinki please......what mafita? taya? Kinji mai
doctor yace kuwa? Am two months pregnant fa yake gayamun can u imagine why ooooh
why sai yanzu bikina sauran kwana Uku ya zanyi ni diyar Malam, doctor please do
something duk maganin zubar da cikin daka bani yakiyi sai bakar wahala da
galabaita nakeyi iyayena duk tunanin jimamin barin gida ke Sani jinya kwana biyu ni
kadai nasan azabar da nake sha how can I be so stupid, tafadi tareda rushewa da
kuka harda majina, Wyyooo future husband Dina wyyooo mijina wyyyooo burina wyyyooo
Naira mafarki na, GOD ka rufamun Asiri taya zanfara tunkarar Gidan miji da cikin
wani mahuta ka cuceni maiyasa na baka kaina,ooooh bariki Alalen gero gashi yauta
kwabe dani 'look hajiya please ku natsu munsha gaya miki jininki Nada mutukar karfi
yadace ki dinga zuwa ana duba ki jefi jefi and kinga yanzu Babu abunda bamuyi ba
akan cikin nan ya zube yaki uwa uba kinje anmiki dinki Wanda babu yanda zamu Sa
karfen dazai markade cikin a cikinki sai mun kwance dinkin da akai miki idan kin
yarda fine.....noooo bikina saura kwana Uku idan aka budeni maizan kaima mijina
kenan? Taya za'a Kara budeni bayan har yanzu ban gama hadewa ba har yanzu ina kan
jinya ne Taya zan fara mishi bayani? Look hajiya shawara ya rage naki idan kun
tsaida magana daya zaku iya dawowa namu aiki ne.
Ficewa doctor yayi yabasu wuri ganin suna bata mishi lokaci wurin awa daya ana
magana daya, dakyar meenah suka tasa keyarta suka koma gidansu domin samun mafita
leemah kuwa sai yanzu tafara ganin illar bariki Ga miji har miji amma tama kanta
makeken bakin fenti a Rayuwa inda meenah kuwa sunfi kowa matukar murnar faruwar
hakan, mahuta suka nema a waya tareda yimishi bayanin komai da komai har Auran da
zatayi harda cikin shi datake so ta zubar takasa, Ranshi yayi mugun baci inda babu
macen datai mishi yaudara irin nata, he can't believe Aure zatayi nanda kwana Uku
and take kawo masa kanta ko kunya take cewa tana sanshi for all the hidimar da yake
mata menene baya mata? Mai Wanda zata Aura ya fishi dashi? Mai zai bata Wanda shi
bai taba bata ba? zai nuna mata ita Karamar yar'bariki ce kuma zaiga shegen likitan
dazai cire mata cikin shi za'ayi karamin yaki akan cikin nan ko duniya zata tashi
bazai yarda ta cire ba, bawai Dan yanaso ba nooo fansa zai dauka da cikin nata
wazaiji kunya idan duniya tasani a tsakanin shida ita?
'Leemah kuwa tuni ta sallami Anty zakwai a cewarta yanzu bata zaki takeyi ba
mafita take nema inda mama taita ko'dah kyau dinda leemah takara tayi haske sosai
skin dinta sai kyalli yakeyi duk a tunanin ta gyaran Amaran datace tana zuwa
kawarta na mata shiya maida ta haka, wani Asibitin suka chanza idan suka samu wani
doctor ya amince zai burge cikin amma koda za'a bude ta Dan kadan ne nanma
hankalinta bai kwanta ba idan an bude ta tayi yaya da 1st 9yt? Hakura tayi yayinda
tace idan sun gama shan Amarcin su zatazo a cire cikin Kota halin yaya gudun
tonuwar asirin ta kada ta haifi katon bakwaini.

Ankai lefe saidai muce masha Allah Allah yaba Amarya da Ango zaman lfy da kwanciya
hankali har saida Malam liman yayi fada akan uban lefen da aka kawo inda dakyar ya
Amsa a cewarsa ba siyarda diyarsa zaiyi ba yayinda akai ma masu kai lefen tarba ta
musamman tareda sha'tara na arziki, Mamie kuwa ba yabo
Ba fallasa itama ta yaba inda da kanta taima Aisha kayan fitan biki masu zafi kala
goma duka an dinka su AK kuwa dubu hamsin ya ajiye ma Aisha cikin Wata farar
takarda wacce yayi rubutu a ciki ya ajiye kan kujera a cewarsa yabata ne sadaka
tasa ma auransu Albarka tunda satin farinciki zasu shiga bayasan hayaniya da kowa
itama tasamu nasa kati, da taki daukar kudin yayinda ta kira bilki a Waya ta shaida
mata, bilki ce tasata dauka karfi da Yaji a cewarta raba mugu da makami ibada, inda
Aishar tace bazata ci ko sisin saba aikuwa bilki taxo ta Amsa kudin yayinda tayi
kasuwa fitunannun kayan bcci da shegun kananan kaya ta siyo mata fadin haduwar su
bata baki ne a cewarta sune bomb na farko da yayar Tata zata Dana ma ango Da Amarya
a cikin gidansu saita saka Aisha ta ruguje musu tunani da natsuwar su kaf saita
sasu sun rasa kwanciyar hankalin su insha Allah muddin tana raye karyan iskanci AK
yakeyi waya gaya mishi ana Jada mace? Macen ma cikakkiya irin Aisha mai kayan aiki
komai Yaji masha Allah.

*Mrs Saddiq Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Fan's Dina farinciki na, murmushi na hakika ina ganin zallar Soyyah kuma yau naga
ninkin shi a wurinku Allah yasa ku cigaba da kasancewa dani ko'bayan na gama novel,
banaso kusoni Dan novel Dina, A'a please kusoni a Mamie dina.*😍naso inbaku kyautar
page
🤦🏻‍

♀ dinnan saidai kashe‍♀ novel dinnan gaba daya sadaukarwa ne Ga kanwata
*Husnah*😍 dukda haka kusani ina yinku wlh.😍💞
*Written by Anty Mamie.*

*Dedicated to sister Husnah.*

30

Amarya ansha lalle tareda gyaran kai babu laifi


Shirye shiryen biki ba kama kafan yaro ta kowani barayi shiri akeyi inda Ranar
juma'a dinbun jama'a suka shaida daurin Auran Abdulkareem muktar tareda Amaryar Sa
Halima daurin Auran daya samu halartar manya manyan malamai da kusoshin gwamnati
har'yan kasuwa ba'a barsu a baya ba, tun a wurin daurin Auran akaita rabon manya
manyan ledoji masu dauke da hadaddun Abincin da Ango yabada kwangilar ayi, Duk inda
AK ya gilma wasa shi akeyi sanye yakeda manyan kaya farare tas Riga da wando da
malum malum yasha aiki da golden zare hmm iya haduwa ya hadu sai murmushin yake
yakeyi shi kanshi baisan maiyasa tunda aka daura Auran gabanshi ke faduwa ba, gidan
Amarya
👯🏼‍

♀ kuwa hausawa sukace Abu namu maganin a kwabe mu‍♀ Walima gangariya Akayi
wa'azi kuwa ba'a magana inda manya manyan malamai mata sukaita fadakarwa gameda
zaman Aure Amarya kuwa tana zaune a gefe cikin kawayan ta jefi jefi tasha katon
hijab yayinda su meenah keta kaiwa da kawowa sune kirjin biki, shigowar text
message taji wayarta duk a zatonta Angon tane Wanda taita kira a karo ba adadi amma
yaki dauka dukta shiga damuwa.

Number mahuta ne nanda nan ta bude

*Congratulations Amaryar shagali, gskia kin iya zabe wato ko'a cikin mazan Auren
saida kika zaba kika darje naga ango ba karya yayi ya cika namiji harna mishi
Addu'ar zaman lfy yayinda muka gaisa a wurin daurin Auran naku, da Alama anjima zan
kai mishi ziyara na musamman tareda labari mai dadi harda gudunmawar Auran naku zan
hada in bashi, hmmmm kina nufin da cikina zakije gidan wani ya turmushe ki? A
wannan Karon kinyi karya wlh wlh San cikina nakeyi idan har wani Abu yasamu cikina
zaki tabbatar dani tantiri ne kallon ki kawai nakeyi inga karyan duniyancin ki
nabaki nanda Minti Goma sha biyar idan baki sameni a dakina ba, hmmm ki saurari jin
labari mai kayatarwa tareda girgiza jama'a A gidan TV anjima da daddare sannan
kada ki manta ki ajiye Redio a kusa domin sauraran program din Inda ranka zakiji
labarin Diyar malamai budurwa mai Aure da cikin shege, hahahaa.*

Hijab din jikinta ta shiga girgizawa rufa dukya rufeta, innalillahi na shiga Uku ni
halima yayinda ta Mike tsaye, Kallo ne ya koma kan Amaryar da Akema wa'azi a cikin
mutane, 'lfy? Maiya faru? Nan kallo ya koma kanta Ashe a fili tayi maganar, Antyn
tace tajata gefe inda take tambayar ta dalili, cewa tayi babu komai Wata kawarta ce
aka turo mata text akan ta rasu, toh'ai Addu'a ya kamata kiyi duk kin tada mana da
hankali, wucewa Antyn tayi inda ta shaida ma masu tambayan dalilin salatin Amarya,
Meena ne suka jata lungu inda tana kuka take shaida musu Abunda yafaru wani
munafukin ya gayama mahuta tanada cikin shi kuma yaki fita, wani munafukin ne ya
gaya mishi Auran ta?,Dan girman Allah ku nema mun haryar fita Kota Katanga ne wlh
mahuta zai iyayin fiyeda haka wyyooo ni kaina taya zan fara? Ya zanyi? Kuka takeyi
inda taita kiran mahuta yaki daukan wayar text taita mishi babu reply inda daga
karshe ta Amsa wayar meena ta kirashi aiko ya dauka, "yanzu ni zaka tozarta cikin
sha'shakar kuka take magana hannu daya akan kirjin ta, duk soyyar Dana gwada maka?
Kada ka manta fa kaika fara Sani na,....eh kuma kika yaudareni kika Auri wanina ba
munafuka Karamar yar'bariki, 'kasan har duniya ta tashi bazan taba ba wani namiji
irin zumar Dana baka ba ya kamata inci koda darajar wannan ne a gunka, 'lashe bakin
shi yashiga yi tuno irin Roman daya kwasa dukda Yanzu bayajin irinshi a tareda ita,
murmushi yayi tuno gskia ta fadi, 'dakyar da sudin goshi suka bashi hakuri itada su
meenah tareda Alkawarin nanda kwana biyu zatazo gareshi, 'idan ma bakizo ba wlh wlh
zaki ganni a gidan naki, kina nufin zaki bashi kanki cikina fa? 'Nooo Babu abunda
zai shiga tsakanin mu nama Alkawari saboda inada ciwon da bai gama warkewa ba,
'Shegiya leemah, shikenan saimun hadu sai nazo yafadi tareda kashe waya yana
dariyar mugunta.

Misalin karfe Tara na Dare yan'daukan Amarya sukazo inda Abokan AK sukaita kwasar
su Amarya tasha fada ba laifi sai kuka takeyi za'a rabu dasu Malam dakyar aka
banbare ta daga jikin su malam inda aka kaita gidanta daya gaji da haduwa, nan su
meenah suka Kara kulewa harda kwallar takaicin daular da leemah ta shigo babu Wanda
baiyi santin gidan ba Addu'a kuwa sunsha shi, an damkar Amanar Amarya a hannun
uwargida Aisha wacce bata gayyaci kowa ba sai kanwarta bilki datai ta kwantar mata
da hankali inda da hannu biyu biyu ta Amsa bilki na tayata sai washe baki sukeyi
nan akaita yabon Aisha ba karamin rudewa Leemah dasu meenah harda dangin amarya
sukayi ba ganin surar Aisha Cikakkiyar buzuwa komai Yaji mai diri kyakyawa black
beauty, sanye take dawani danyan leshi kalar ruwan kwai da mint green bilki tamata
kwalliya na Musamman irinnan amare kannan yasha daurin gwggwaro anbude gashinta ta
tsakiya ga kananan kitso an yarfa mata gashin nan masha Allah kunshi hannu da kafa
Jan lalle a tafin kafa sai zuba kamshi takeyi nesa ba kusa ba tafi Amarya kyau nan
aka fara kananan gulma wasu na cewa idan banda jarabar namiji Yanada mace irin
wannan Auran mai zai Kara kuma? Leemah hankalin ta yagama tashi inda su meenah keta
dariyar mugunta a zuciya a fili kuwa lallashin ta sukeyi a cewarsu da baya Santa da
bazai aurota ba ai yasan da matar tashi, kowa ya watse Leemah ta tasa keyar su
meenah akan babu mai kwana mata a gida dole taji dumin jikin mijinta yau, badan
sunso ba suka tafi suna mata Allah ya isa ta hanasu Dana gadon da za'ai bidiri
akai.

Sai karfe goma da Rabi Ango ya shigo indai kai tsaye dakin Amarya ya nufa hannun
shi dauke da manyan ledoji kasancewar ya Hana kowa rako shi inda akaita mishi
tsiya, kwance ya tadda ta tsakiyar gado kaiba dankwali baiji dadin ganinta haka ba
shida yake tunanin zai ganta da lullube ya yaye da kanshi, sallah ya umarceta suyi
kai tsaye ta shaida masa batada tsarki yadanji takaici yaso yasan zakin mace ayau
nan sukayi Addu'a sosai ya ciyarda ita taci ba laifi, gassar kaza ce sai yogot
inda kai tsaye ta shiga wanka jiki na rawa ganin irin kyau dinda AK yakara mata nan
wani mugun kwadayi ya motsa mata amma ya zatayi? Nan gani nan hange, shigar kayan
bcci tayi kallo daya yaimata ya kauda kai ganin ko kadan bata kaima rabin tunanin
shiba yanda kasan Agwagwa haka surar jikinta yadawo ba shape ba komai ga cikinta
yadan tura kadan kamar karamin tunbi, samun kanshi yayi dajin haushin ganinta a
hakan ko kadan bata burge shiba tunowa da surar jikin Aisha hakan yasa shi mikewa
tareda Jan karamin tsaki yabar dakin, Jiki a sanyaye takoma gefen gado hadeda buga
uban tagumi,mai hakan ke nufi? Daga kallo daya a first 9yt saikuma tsaki? Tayi
tunanin zai tashi ya rungume tane ya rikice kamar yanda sauran samarin ta keyi,
dakin shi ya shiga inda yayi wankan tareda chanza kaya zuciyarsa na azalzala masa
yanaso yayi tozali da Aisha yanaso yaga halinda take ciki kodai tana kukan kishi
ne? Murmushi yasamu kanshi dayi sanye da kayan bcci ya doshi dakin ta inda a karo
da dama yake tunanin shiga, bude kofa tayi da niyyar zuwa kitchen zata ajiye
Kofunan da akai Amfani dasu sanye take cikin hadaddiyar rigar bcci tayi matukar
kyau, Jada baya tayi wyyoo Allah, harga Allah taji tsoran ganin mutum tsaye a bakin
kofa, gefensa ta ratsa zata wuce inda zuciyarta ke suya ganin shida kayan bcci,
'tare hanya yayi, nanma takara yunkurin wucewa yakara tarewa, 'Malam wai lfy?
Tafadi cikin harara, 'nazo kisama Aurena Albarka ne yafadi murmushi a fuskarsa
samun kanshi yayi da farincikin ganinta tun bare yau tamishi kyau fiyeda koyaushe,
jikinta kawai yake kallo ji yakeyi kamar ya ganta kwance a kirjin shi ....'Allah
sanya Alkairi, tafadi yayinda ta wuceshi, tsayawa yayi anan harta fito daga kitchen
din takara wuceshi inda ta buga kofarta tareda Danna key, Dakin leemah ya shiga da
gudu inda har'saida taji tsoro ganin yanda ya shigo kamar maibin wani Abu, ledar
kajin daya shigo ya dauka dama kaji Uku ya siyoma leemah sauran biyun ya dauka
hadeda juice dinda suka rage, 'lfy kuwa ango Na ina kuma zaka? Baibi ta kanta ba
dakin Aisha yakoma inda yahau buga kofar da karfi, tsaki taja yayinda takara Jan
bargon ta hawaye daya nabin daya azababben kishi ke damunta, ganin baida niyyar
dainawa harya fara kiran sunanta hakan yasata mikewa a hatsile, Malam wai lfy?
Tafadi yayinda ta bude kofar Konaci ban biya bane? Hannu daya rike a kugunta tana
girgiza jiki cikin masifa ji take kamar ta kifa masa Mari, 'Aisha kuka kikeyi?
Kukan kishi na? Ji idonki laaaa wlh na kamaki hawaye ne, goge idonta tayi bataso
yaga kukanta ba harga Allah ta manta kuka takeyi da bata bude kofar ba, 'mtsww lfy
nace bccin ma baza'a barni inyi ba? Ina kabar matar so tazo taja mijinta, AK harda
buga dariya abun yamai suger yau Aisha na kukan kishi,yarinya da tuntuni Abunda
kikayi kenan kila Dana Dan huce, Anyway kazarki na kawo miki, mika mata ledar
hannun shi yakeyi, wace kazar? Wacce na Aikeka ka kawo mun? Toh na yafe ka hada
duka kaba matarso, BAMMM ta buga kofar tareda maida key, Juyowa yayi harda shewa
yana dariya ya wuce leemah da tunda yafara buga ma Aisha kofa tafito ganin ikon
Allah, cikeda takaicin daukar kazar Amarcinta take inda ta daure bata mishi magana
ba a Ranta ta kudiri niyyar saita nunama Aisha ita Karamar yar'bariki ce saita gasa
mata aya a hannu, Daki ta koma inda ta taradda AK ya kwanta wannan karan dariya
yakeyi, ikon Allah, tace cikin Al'ajabi mai kuma ya sameka? Ashe haka Akeji idan
ana kishin mutum? Kamar ya? Ta tambayeshi, ban gane ba?
Mu kwanta kawai Amarya bazaki gane ba, rufe ido yayi yafara sarrafata inda Yaji
kirjin ta bawani labari Ashe ciko ne gashi sun zube sunsha matsan hannun gardawa
kala kala Ranshi sai mamaki yakeyi har wani Dan kyama Yaji itako ta dage bako
kunya wai a dole itama tanaso tarage zafi, haka nan yafara kiyasta surar jikin
Aisha harga Allah bayajin komai gameda Amaryar tasa, da taimakon tunanin uwargida
yake neman amsar budurcin Amarya inda cikin murya kasa kasa take Kara tuna mai
batada Tsarki tana fashin sallah, ba haka yaso ba yaso ya rage azabar dayakeji kila
idan ya dandana ta zai daina haukar Sha'awar Aisha, kila leemah zata mantar dashi
surar Aisha.

*Mrs Saddiq Rumah💅🏻*


🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
🏼🏼🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie.*

*Dan Allah masu mun mgn ta private kuyi hakuri kada kuga bana Amsa ku, kunmin yawan
dazan Amsa lokaci daya zan Amsa kowa a hankali aimun uziri please.🙏🏼*

*Dedicated to sister Husnah.*


31

Aisha kuwa kuka tasha harga Allah idan tace soyyar AK bata cutar da ita tayi karya
wannan wace irin jaraba ce? Shin ita haka rayuwarta zata Kare? Har yaushe zataji
dadi? yah Allah ka rangwanta mun yah Rabbi ka taimake ni idan wani laifi naimaka
kake jarabbtata da soyyar Wanda baisan inayi ba Allah ka yafemun, durkushe take a
kasa hannunta na sama tana rokon Allah tana kuka, dukda haushin AK da takeji amma
soyyar shi tananan daram a gefen zuciyarta daurewa kawai takeyi domin kwatar
yan'cin ta, 'Ango kuwa hankalin maza fa yagama tashi bai taba tunanin zai samu 1st
9yt dinshi a haka ba a tunanin shi ganin macenda yakeso kuma ya Aura zai samu
sassauci a zuciyarsa, haka yaita juye juye akan gado dukya kosa gari ya waye Amarya
kuwa barci take kwasa harda karamin minshari na gajiya inda yakeji kamar yabar
dakin ya tsani minshari yanda yaga Dare haka yaga safe Amarya ce kawai tasha bcci a
daran.

Washe gari da sassafe ta tashi dukda bccin dake idonta amma takasa komawa saboda
tariga tasaba da tashin wuri, wanka tayi inda tahau gyaran gida ko kadan batasan
kazanta macece mai matukar tsafta kanta kedan mata ciwo gashi idonta yadan kumbura
kadan na kukanda tasha, parlor ta gyara ta shiga kitchen Abinci maikyau ta hada
musu Karin safe itada baba mai'gadi dankali da kwai ne sai ruwan shayi parlor
tadawo cikin shigar kananan kaya Wanda a yanzu tagama sabawa dasasu dogon wandon
jins ne sai yar Karamar Riga yamata kyau sosai kanta babu dankwali ta baza gashinta
dayasha kitso, zaune take kafa daya kan daya tana kallon tashar Arewa24 inda AK ya
fito daga dakinshi da Alama wanka yayi sanye da kananan kayan shan iska hamma ya
fito yanayi yinwa yakeji sosai ba kadan ba, kallon Aisha yayi Kota kanshi batabi ba
Kara daure fuska tayi, madam babu gaisuwa? Wlh yarinyar nan kin karo wulakanci fa
koda yake banida lokacin ki yanzu kinci Albarkacin Amaryata, ko kallan tsiya bai
samu ba a'daidai lokacin Amarya ta fito sanye da Atamfa Riga da Skart anci dauri
tasha kwalliya ba laifi sai kamshi takeyi, hannu ya mika mata yayinda yajata zuwa
jikinshi inda ya sakin mata karamin kiss a baki harda rungumar ta idonshi kan
Aisha, wow Matar so kinyi kyau kin ganki kuwa waiiii kece wacce ake cema ko a cikin
Wata Zahra ta dabance toh koh a cikin mata keta daban ce matar so, Kara lafewa tayi
a jikinshi saboda yagama burge ta harga Allah tana shakkar surar da kwarjinin Aisha
amma hakan dayayi mata yakara nuna mata ita din yakeso bawai jiki ba, 'Ustaziya ina
breakfast dinmu a kawo mana nan, kamar yana magana da dutse kallonta kawai takeyi,
Anty ina kwana? Leemah ta furta cikin kirsa Ranta fari fes ganin yanda ake jiji da
ita, Kota kansu Aisha batabi ba, Lallai kin fara wuce tunanina Aisha Amma bashi
kikaci, zauna anan Amarya bari inje in dauko mana, 'no Angon bari in dauko, wucewa
leemah tayi sai karairaya takeyi a lokacin Aisha ta Mike domin kai plates dinda
tayi Amfani dasu kitchen inda AK ke binta da kallo har saida yaci tuntube da kujera
ba karamin bugewa yayi a kafarshi ba akan idon leemah akai komai nan taji mugun
bakin kishi hadeda tsine ma Aisha ko ita Aishar tana mata kyau bare kuma mijin su
lallai saita dage kada garin kallon ruwa kwado yaimata kafa, wannan ita ake cema
karuwar gida, Cikin takaici leemah ta shiga kitchen ta dafa musu indomie tareda
kazarsu ta jiya nanta kawo musu sukaci suka koshi Aisha kuwa tunda ta koma daki
bata karabin ta kansu ba.

Bayan an kwana biyu.

Aishar ce misalin karfe biyar na yamma sanye da mini skirt baki guntu sosai ya
kamata dakyar take iya tafiya tareda rigarshi wacce ake kulle ta da igiya batada
hannu shafeffen cikinta a bude milk color, dakyar bilki ta shawo kanta sannan ta
Amince zatasa kayan ita kanta sun bata kunya, tayi kyau ba kadan ba ribom ta daure
kitson ta dashi saboda so takeyi tayi karkabe karkabe a parlor kassncewar yanzu
lokacin kura ne sau biyu take shara da goge gogen parlon ko kadan batasan datti GA
gidan nasu kura yamusu yawa, Leemah zaune akan kujera tanata ciye ciyen snacks
Wanda tunda tazo gidan sune cimarta fita sukeyi da AK su siyo yayinda AK yace ta
huta ba yanzu zata fara girki ba sai anyi sati biyu ko Wata Daya sai sunci Amarcin
suda tsinke, Aisha ce dauke da kayan goge goge nanta fara goge duk wani abunda ke
parlon kassncewar basa magana da leemah kota mata bata Amsa ta a cewarta bada ita
zatayi ba Wanda ya ajiyeta shine daidai da ita, 'tsaki leemah taja cikin takaici ta
wuce tana zage zage, haba ace anyi mace sai shegen karuwanci banza karuwar gida
kawai, mtseww daki ta shiga inda tahau chanza kaya itama dukda Aisha tajita amma
tayi banza da ita a cewarta bazatayi fada da wacce ko kanwarta bilki ta girma ba,
fitowa tayi sanye da pencil wando dawata Riga shara shara ana ganin komai na
jikinta rigar daidai kugu itama ta tufke gashin kanta Wanda ya kamu dakyar saikace
bindin kaza ta lafta turare har yana hawa kai, AK ne ya shigo daidai lokacin da
Aisha tadan duka kadan tana goge center table dinda ke tsakiyar parlon bayanta na
kallon kofar shigowa, 'Assalamu Alai.....kum, yafadi tareda Jan numfashi idonshi
nakan abunda baya taba gajiya da kallo yayinda lokaci daya yafara tafiya a hankali
sai kallon bayan Aisha data rusuna yakeyi hips dinnan kamar an dasa su, 'sannu da
zuwa leemah tafadi tana kwarkwasa dukda Yaji muryarta amma yakasa dauke idonshi
akan Aisha, 'Hannun shi taja jin takaicin Abunda yake kallo Wanda ko kallo daya
baimata ba, janshi takeyi amma sai waige waige yakeyi, 'wannan duwawun fa? Whatt??
Mai kace? Tafadi tana hucin haushi, sai a lokacin ya kalli Amaryar tashi, cewa nayi
wannan duwawun fa? Mtseww ai dole ka tambayi duwawu tunda ka ajiye karuwar cikin
gida, tafadi tareda hararar Aisha dasai a lokacin Aishar ta lurada Abunda yafaru
inda dariya takusa kufce mata amma ta kanne, 'sorry matar so ina nufin wannan
kwalliyar fa gskia kinmun kyau dole inbada tukuicin yauda daddare nasan yanzu
kingama ai, gyara maganarsa yayi ganin tabargazar dayayi cikin borin kunya ya
rungume leemah inda sai a lokacin tadan Saki Ranta, karka damu Angona yau zan
shayar dakai mamaki insha Allah, 'Zama yayi matarso taje kawo mishi abunda zaici
Aisha kuwa da gayya taita girgiza girgizan jiki inda harwani mika takeyi,
wasssshhhhh tareda bankarewa tana lashe lips dinta salati leemah tasaki ganin yanda
AK ke zillo dukda yana zaune akan kujera sai gyare gyaren Zama yakeyi kafun kace
kwabo, hankalin maza yatashi🤣🤣........🙈🙊Aisha na lura da hakan tasaki shewa
harda guntun dariya dama abunda takeso kenan bukata ya biya a cikin ruwan sanyi
zata gasasu shida matarso din tashi.

*Mrs Saddiq Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

Masu San shiga group Dina kuyi hakuri nabude groups yafi a kirga akan novel dinnan
wlh kozan bude group 20 ne saiya cika kamar yanda kuke cewa and bazan iya kulada su
gaba daya ba, zaku samu novel Dina a'kowani group insha Allah nasan duk inda fans
Dina suke novel Dina nanan. Afuwan🙏🏼ana tare🤝🏻
*Dedicated to sister Husnah*

32

Dakinta ta nufa kai tsaye inda leemah taita tsine mata da zage zage shikuwa gogan
lallabawa yayi tareda shigewa daki cikin kunya da takaicin muguntar Aisha, dama
haka take yaushe Aisha tazama Mara kunya haka?

Text neya shigo wayarsa bayan sallar magrib bakuwar number ce.

*Hausawa sukace abun rabo ne Auran mace da ciki, Congratulations ina tayaka murnar
rainon cikin wani tareda Auran wacce aka Riga aka gama sudewa, a fuska dai gaka mai
ilimi Allah yasa yanda fuskarka ta nuna haka brain dinka ke Aiki, duk kwaskwarimar
tsohuwar mota dole a'gane tsohuwa ce, Angon Leemah dakin hutu, hahahaa Ustaziya
diyar Malam.*
*Karka damu da sanin ko wanene ni zan kawo maka kaina da kaina domin amsar
abunda yake nawane Wanda ke Rayuwa a gidanka.*

Tunda aka turo masa da text dinnan yake cikin tashin hankali tareda nazarin duk
wani harafin da aka rubuta a text din kanshi gaba daya ya kulle, hakanan yabar Abun
a Ranshi tareda Alkawarin dole ya warware ma zuciyarsa zargin data fara zuwa anjima
insha Allah.

*A'gurguje.*

Misalin karfe goman Dare Amarya anci wanka da kwalliya har'an gaji like nan manne
chan hayaki da turare kuwa ba'a magana banda maganin dataita Kara bankama kanta
overdose saiwani rawankai akeyi ta barayin AK kuwa shima ba'a barshi a baya ba a
matse yake inda yayi shirin shi cikin kayan bcci wannan karan shiya gayyaceta dakin
shi inda misalin karfe sha'daya na Dare yakashe komai na gidan baibi ko takan Aisha
ba tun haduwar da sukayi da rana daki ya shiga tareda kashe musu wutan dakin inda
ya kunna musu na bcci Mara haske sosai, jawota yayi jikinshi ya shiga sarrafata duk
yanda leemah taso daurewa kasawa tayi a matse take matuka hakan yasa takasa boye
zalamar ta yayinda ta Amsa gaba daya ragamar wasan take gudanarwa sarrafashi takeyi
cikin kwarewa sai nishi take Wanda yake nuna Alamar ta shirya inda kirjin AK keta
bugawa nan yafara zargin wani Abu tareda tsoran text dinda akai masa daxu dukda
yanajin dadin yanayin data saka shi amma ta tsorata shi harga Allah yanada Sani
akan ilimin halittar mace tun daga ranarda yakama Aisha dasu Virus yashiga binciken
ilimin sanin dabi'un mace da yanda rayuwarta yake kullum cikin research yakeyi biye
mata yakeyi inda har akazo Gangara leemah fa ido ya rufe sha'awa takeji ba kadan
ba, yana shiga yaji wajen a'dan tsuke ciki kuwa zuruf ya wuce babu gargada babu
signal bare wani kwana bawani shamaki direct ya zarce, waje a'tsuke amma dukda haka
jikewar datayi yakara Sa wurin sakewa ciki zuwa direct ya zarce babu jijiyar datai
gardamar hanashi wucewa, salati yafara yi inda yacedai bari yakara gwadawa kodai ba
daidai yasa ba dukda baisan mace a zahiri ba amma Wawa aiba mahaukaci bane shakara
talatin da biyar yawuce a raina masa hankali yanada ilimin yine kawai baiyi ba,
Kara turawa yayi Yaji fa tabbas a bude cikin yake leemah kuwa Kara Rungumeshi
takeyi sai ihu takeyi tanaso ya cigaba da aiki tagama rudewa da zumarsa, kan'uban
chan, kutumelesi menene haka? Maizan gani zuruf na wuce fa Kodai ba halima bace?
Mikewa yake shirin yi inda tasa mishi kuka, 'wyyyooo zan mutu dadi please I need
you Angona kanada dadi, fadi take gaba daya bata cikin hankalin ta, 'idan baku
manta ba leemah dakyar take iya kwana daya batareda namiji ba Wanda rabonta da
Namiji yanzu tunda akai mata dinki shiyasa takai makura,
Naushi yakaima bakinta yayinda ya shiga marinta, Shegiya macuciya Allah ya isa
tsakanina dake yar'karama dake shine kikai irin budewar nan kamar wacce tayi
haihuwa biyar kin matse waje kina tunanin ni jahili ne bakisan ba'a taba ma Allah
chuwa chuwa ba yariga ya bambanta bazawara da budurwa wlh saina kashe ki a darannan
tunda kikai mun Asarar jikina duk yanda nake ma matata tattalin kaina kin gama
ruguje mun jikina daya hadu danaki shegiya taxi motar kowa, dukanta yakeyi inda
yake maida kayan jikinsa, hakuri take bashi, wlh babu Wanda nasani saikai wyyyoo
Allah na shiga Uku na Wlh ni budurwa ce kada kamun sharri na shiga Uku jama'a ku
taimaka zai kasheni dukanta yakeyi kamar yasamu katon gardi, Allah ya isa kin
cuceni kin gama dani Ashe shekaru ba shine dacewar mace ba da bazawara na Aura
nasan bazawara ce amma in siya sabuwar mota dal a kwali ina budewa inganta da
mataccen engine, kuka yakeyi inda leemah tayi shame shame a bakin kofa tuni ta Dade
da sumewa sakamakon naushin daya dinga mata a ciki fuskar nan jini da majina dukta
chabe ta bugu iya bugawa, shari'a nidake har a lahira sai an mana kwankwasa kofar
dakin su akeyi Wanda kusan minti biyar da suka wuce ake buga kofar tasu bakowa bane
sai Aisha kukan leemah da magiya ya hanata bcci daga farko tadauka sabon iskanci ne
saidataji muryar AK da kukan leemah da kalaman da yakeyi ga karan duka Wanda yagama
karade gidan da alamar karamin yaki akeyi a dakin, kuka yakeyi sosai mai fitarda
sauti, yah Allah ban kasance mazinaci ba na kasance bawanka mai matukar kyamar zina
yah rabbi Laifin mai naimaka daka hadani da mazinaciya? Wacce alamu ya nuna duk
mazan gari sun gama saninta?
'Yaya AK Dan girman Allah kabude kofar, tafadi da muryar kuka bakaramin tausayi
yabata ba, mikewa yayi tareda bude kofar batareda bata lokaci ba ya rungume ta tsam
a kirjin shi har suna shirin faduwa kasa sakin mata nauyin shi yayi gaba daya
jikinshi ya mutu, Aisha, ta cuceni Aisha ya zanyi na Auri mazinaciya 'Aisha nasan
babu Wanda kika tsana sama dani a duniya, kiyimun Alfarma yau daya ki lallashe ni
ki dauki hakan da zakiyi kamar taimakon Addini, Aisha zuciyata zata fashe Aisha
kiji tausayina ki gayamun kalamai masu dadi na lallashi Aishaaaaa, rufemai baki
tayi da hannunta inda suka zube kasa kanshi na kwance akan cinyar ta tana shafa
gashin kanshi a hankali sai zufa yakeyi hawaye daya nabin daya, kyamar zinar
danakeyi sai Allah ya hadani da kototuwar Yar'duniya a tunanina Ustaziya na Aura,
kanshi takeso ta janye jikinta a hankali, riketa yakarayi dukya chukuikuye ta
please dnt live me Eesha karki barni please Eesha am sorry My Eesha harda hakkin ki
wlh zan rayu dake har karshan rayuwa ta gara ke nasan Ga yanda na Aureki ina tareda
dake please eesha kaina zai fashe zafi kaina Aisha....Kara rungumar ta yakeyi 'yaya
AK ruwan sanyi zan dibo maka......'nooo noooo karki tashi nafi bukatarki fiyeda
ruwan sanyi, sun kwashi minti shabiyar a haka kafarta dukta sage kassncewar bata
zauna da kyauba, leken fuskar shi tayi taga idonshi a lumshe kamar mai bcci har
yanzu hawaye nabin idon nashi, ta tsani AK amma duk wani mai'imani idan ya ganshi a
haka saiya tausaya masa, Kara tashi zatayi a karona biyu, ina zaki?
'Zan rufe mata jikinta ne naga barinta a haka bai Dace ba, mikewa yayi tunowa
dayayi leemah na kwance yashe a kasa' kada ki kuskura kije kusa da ita jikinda
iskar duniya tagama busarda shi wani sutura ya rage mata a gidannan? Bafa ta
numfashi yaya AK kada wani Abu ya sameta....wlh zanso haka kinga na kashe banza,
wayarsa ya dauko cikin daran ya kira doctor dinshi tareda shaida masa yanasan
ganinsa da asuban fari Akwai Emergency a gidanshi yanaso idanda Hali yazo da masu
tayashi aiki harma da kayan aikin Kwajin kanjamau yakeso Aimasa.

Kulle dakin nasa yayi bayaso yakara kallon leemah inda Aisha takama hannun shi
tajashi har dakinta sai layi yakeyi dakyar tasamu yayi wankan tsarki inda ya zube a
kasan dakin jikinshi na rawar sanyi zazzabi mai zafi ya rufe shi bargo ta jawo
mishi kasa tareda rufeshi ruf, hannunta ya rike Alamar bayaso ta barshi sunanan a
haka har akayi asuba inda sukai sallah a daddafe saida gari yafara washewa da
dabara Aisha tabar dakin wurin leemah taje inda har yanzu take yashe numfashi sama
sama dakyar take iya bude idonta daya kumbura Halittar jikinta dukya chanza saboda
bugun datasha ba karamin tausaya mata tayi ba koba komai itama macece yar'uwarta
suturta mata jikinta tayi cikin doguwar bakar Riga inda takejin ana kwankwasa musu
kofar nasu ko bata duba ba tasan doctor ne.

*Mrs Saddiq Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Ummu minal marubuciyar nafi karfin shi inamai baki shawarar toshe kunne ki maida
komai ba komai ba tattarasu zakiyi gefe daya gaba daya kiyi musu sallar gawa ki
share surutun banzan su ki cigaba da typing dama ai bawanine yasaki ba kuma ba
Wanda akaima dole saiya karanta muna jiran next post dinki please🙏🏼ana tare.*🤝🏻

*Dedicated to sister Husnah*

33

Daki takoma tareda saka katon hijab tare suka fitoda AK kai tsaye kan kujera ya
nufa inda Aisha tabude ma doctor kofa cikeda gaisuwa gaba daya suka karasa parlon
yayinda suka zauna, 'doctor sonake ka diba jinina aje a auna sannan ka diba jinin
Yar'iskan chan, yafadi tareda nuna dakin leemah shima a auna inasan inga results
da gaggawa please, batareda bata lokaci ba likita yayi abunda aka umarceshi inda
Aisha ta nuna mishi dakinda leemah ke ciki kememe taki yarda a diba jininta babu
yanda doctor baiyi ba, cikeda takaici AK yashiga dakin nan yaita ball da ita kamar
yasamu kwallo yanayi yana zaginta dakyar Doctor ya kwaci leemah a hannun Sa inda
Aisha na gefe daya tareda kallon fadan dayafi karfin ta, daga ummm sai uhmuhm
kawai take cewa hakura leemah tayi ganin AK zai halakata daga daran jiya zuwa yau
tunda take a duniya bata taba ganin Wanda akaima dukan mutuwa irin wannan ba gashi
yau anmata kuka takeyi tana jamasa Allah ya'isa kasa kasa inda sai ihu takeyi ya
kala mata sharri ya cire mata budurci Ga azabar budurcin daya cire mata Ga zafin
ciwo damai zataji ga bugu ya akai yasan ba budurwa bace indai shima ba danawa
yakeyi ba, a fusace yakara dosar dakin inda Aisha ta tareshi Abun yafara bata
dariya ma, 'Ubanwa ya cire miki budurcin? Lallai yarinyar nan ki kalla tsabar idona
ki raina mun hankali zanyi maganinki karyar rashin mutuncin kikeyi, Jan kafarta
takeyi tareda dauko hijab da sauri da sauri ta wuce ta gefen Aisha sotake tabar
gidan tun kafun doctor yadawo ta tabbata kashe ta kawai zaiyi idan yasan tana dauke
da ciki, AK na ankare da ita wani wawan Mari ya Kara zabga mata Wanda yayi
sanadiyyar toshe kunnanta saida taga taurari na yawo a sama dif kakeji tayi shame
shame a kasan parlon kukanma yaki fitowa sai nishi takeyi Tareda danasanin Kaddarar
dataja mata Auran AK bata tabajin labarin mugu irinshi ba baida imani ko kadan,
Zaune suke zuru zuru kamar masu zaman makoki leemah na yashe a kasa, kitchen Aisha
ta nufa ganin Dramar da akeyi da matarso a gidan nasu bamai karewa bane Hadaddan
shayi ta hada tareda katon burodi da soyyan kwai, parlon takoma harda kunna TV tana
karyawa tana kallo dukda ana neman karfe bakwai na safe ne ko karabin takansu
batayi ba indata hade Ranta sama da kasa AK kuwa sai Satan kallon ta yakeyi ganin
yanda take saka lomar burodi batareda wani damuwa ba ko alamar tayi babu dukda Kota
mishi baci zaiyi ba, zaune suke a wurin Doctor yadawo tareda mikama AK sakamakon
gwajin, hannu ya mikama AK tareda fadin, *Congratulations sir your wife is Three
month pregnant.*
'Kallan shi AK keyi yakasa fahimtar abunda yake nufi inda doctor ya maida
hannunshi daya gajida mikawa, What? Yimun magana da Hausa yanda zan fahimce abunda
kake cewa likita, 'yalla'bai ina nufin Matarka Nada shigan cikin Wata Uku a
takaice, 'wyyooooo ni halima wlh fyade akaimun.......'wait wait wai ciki? Ai kowa
Nada ciki AK ya furta yana zare ido cikin tashin hankali, "yes sir kowa Nada ciki
but nata na mutum ne Mai rai, Bby na Rayuwa a ciki harna tsawon Wata uk...... Kam
bala'e what a ina? A gidana? Matata? Amarya? Innalillahi wa inna ilaihir raji'un,
ya dinga maimaitawa babu Adadi Aisha kuwa kashe TV tayi tausayin shi dukya mamaye
ta bakaramin firgita maganar taimata ba bata taba tunanin leemah zatayi haka ba,
rarrafawa leemah tayi har wurin kafar AK dake zaune a kasa yayi zaman yan'bori rike
kafarshi tayi da hannu biyu biyu, Kaimun Rai ka rufamin Asiri kamar yanda Allah ya
rufama Wlh fyade akaimun mijina na tuba nabi Allah kuma nabika kallonta yakeyi
cikeda kyama yama rasa mai zaiyi ya zaiyi? Taya zaifara? Dagayin First 9yt sai ace
Amarya Nada cikin Wata Uku, tana nufin da cikin wani tazo gidanshi kenan kuma tasan
da cikin ta Aureshi, hawaye daya nabin daya ya kalla doctor, 'yah kanjamau fa?
Akwai ko babu? 'Alhmdlh babu wani ciwo tareda ku dukanku likita yafadi cikeda
Al'ajabin abunda yake gani, shigowar mai'gadi neya katse musu shirun inda yake
shaidawa wani yazo neman hajiya Amarya damai gidan a cewarsa yanada Ajiyar mutum
sukutum a gidan, mahuta neya danno kanshi sanye da kananan kaya bakake wando da
Riga fuskarshi daukeda murmushi inda yake shafa sajen dake fuskarshi, Halima gidan
hutu dakin hutu diyar malamai mai tarin ilimin hutu a daki, ooops forgive my
manners please, Assalamu Alaikum banyi sallama ba kasancewar ina cikeda murnar
ganin unborn bby Dina dake kwance a dakin hutu, Mutuwar zaune limah
tayi........mmmaaaa...huta tafadi cikin rawar murya, mai kakeyi a gidannan? Ya
zakaimun haka? Waya kawoka waya nunama gidana? 'Sorry baby Sanin inda kike bamai
wahala bane kawayanki suka kawoni yanzu haka nabarsu a mota Sunce ma in gaishe ki
su meenah nake nufi, 'Malam uban waye kai? Maiya shigo dakai har cikin gidana
wurin iyalina da izinin wa kato dakai? Calm down Yalla'bai Kwantar da hankalinka
zanma bayanin kaina ai, sunana mahuta Saurayin halima uban babyn dake kwance cikin
mahaifarta nazo ne inga lafiyar bby na jiya nakwana da zullumin cikina Allah yasa
kuna ciyar dashi sosai,.......... karfin da baisan yanada shiba ya tattaro tareda
kaima mahuta mugun naushi a baki nanda nan jini ya balle duka yake kai mishi tareda
Alkawarin kashe shi da hannun shi, kwarto kwarto har gidana wlh dukanku mai rabani
daku sai Allah babu yanda Mai'gadi da doctor basuyi ba ina sunkasa raba AK a jikin
mahuta Wanda akaima jini da majina a fuska sai zare ido yakeyi dukya galabaita
baitaba tunanin zai riske haka ba saida AK ya cire mishi hakori daya dakyar yasha
inda yakwasa a 360 babu koh waige lallai AK baida hankali yayi dana'sanin zuwa
gidannan Kan leemah ya dosa wacce tayi hanyar waje tana dingisa Kafa dakyar da
sunan guduwa kiran mahuta takeyi ya taimaka ya rike mata hannu su gudu tare tabbas
AK babu abunda zai Hana bai kashe su ba, ganin AK ya dosota kamar zaki tuni ta taka
kafa tareda kwasa ana Kare har waje yabisu tuni mahuta yaja mota leemah kuwa ta
kule tanata tikar gudu babu ko takalmi bare mayafi ko waige batayi, nishi yakeyi
sama sama tareda kokawa da numfashin Sa kafun a Ankara tuni ya zube a kasa ihu
Aisha tasaki hadeda kiran sunanshi tana kuka da taimakon likita suka sashi a motar
likitan Aisha da Ak na baya kanshi akan cinyarta sai girgizashi takeyi, kada ka
tafi idan katafi basuda asara ni sukaima asara ya zanyi Yaya AK kafi kowa sanin
kaine farincikina Dan Allah ka kasance dani wlh bazan gujeka ba koda zaka dinga
dukana kada ka mutu, kwantar da hankalinki madam bazai mutuba insha Allah inji
Doctor daketa zuba gudu a titi, Kai tsaye dakin Emergency akayi dashi Dakyar aka
Hana Aisha shiga wacce tagaji dacin kuka harta gaji.

"Baki na bude ni Mamie ganin yanda Aisha ta bankeni harsai Dana kai kasa a
kokarina nabinsu Asibiti domin dauko muku rihoto inaji ina gani aka badeni da kura
suka barni tsaye nida baba mai'gadi, kokarin shiga gidan nakeyi tsawa mai'gadi ya
dakamun, 'toh uwar gulma masu gidan basanan mai zaki musu a gida kuma?Sakata yasa
yabarni cikeda takaici na watsar da Alkalamina nayi cikin fushi 'muma mijinnan

munada
🏃🏻‍🏃🏻‍
♀‍♀ shi bare a karya mishi ni a banza😡‍da
♀‍♀gudu nayi wurin My Rumah‍♀‍♀ naga
kowa nashi yasani.

*Mrs Saddiq Rumah 💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to sister Husnah*

34

Bakaramin artabu akasha wurin daidaituwar numfashin nasa inda saida aka kwasa
mintuna mai yawa sannan Aka samu nasarar numfashin Sa Kiran su Mamie Aisha tayi
tana kuka ta shaida musu suna asibiti batareda bata lokaci ba Mamie da Daddy harda
Abdulhakeem suka rankayo Auta bilki ma ba'a barta a baya ba Ramata kuwa cewa tayi
zatazo da yamma duba jikin nashi, aikin lallashi bilki ta shigayi inda Aisha ke
makale jikin Mamie yayinda take musu bayanin iya abunda tasani salati suka dauka
gaba daya daddy na girgiza kanshi cikin takaici, maganin shi kenan ai duk Wanda
baijin Maganar iyayanshi taya yake tunanin ganin mai kyau a rayuwar Sa yara ana
nuna muku gabas kuna yamma tafi kyau Wanda baiyi sharar masallaci ba wlh harta
tasha zaiyi ina amfanin irin wannan? "Haba Alhaji haba Alhaji kadaina yin furucin
nan shin bawa na wuce kaddarar sane? Mudauki haka akan shine jarabawarsa Saimu
rakashi da Addu'a tareda nasarar cinyewa, tausasa daddy Mamie keyi ganin yanda Abun
yaimasa ciwo sosai ita kanta Mamie tausayin dan'nata neya gama rufeta doctor neya
katse musu jimamin da sukeyi yana share zufa da farin hankacif cikeda gaisuwa yake
sanarda daddy akan zaiyi mgn dashi a Office inda hali, binshi daddy yayi nan likita
yafara bayani, " duk mai imani yakamata ya tausayama AK halinda yake ciki Wanda
komai yafaru akan idona saidai muce Alhmdlh Allah ya takaita munyi iyakar kokarinmu
wurin dawoda numfashinsa dake kokawa sanadiyyar bakin cikin dayake ciki Wanda
zuciyarsa tafara kumbura da taimakon ubangiji tunda bayin mu bane Alhmdlh komai
yana shirin dawowa daidai Dan Allah Alhaji arage bata masa rai kassncewar Sa mai
zurfin cikin gaske shiyasa Ciwon yayi saurin tasiri a gareshi yanada damuwa tattare
dashi ku taimaka mana dashi kanshi wurin kwantar masa da hankali tareda dauwamar da
murmushi a gareshi, godiya daddy yayi cikeda tausayin AK.

Tunda mahuta ya figi mota bai zame ko'ina ba sai gidan iyayanshi inda tun'da
mai'gadi ya bude mishi kofa ya watsama su meenah kallon banza wadanda suke cikeda
gulmar sanjin abunda yafaru amma ganinshi a halin nan yasasu tsuke bakinsu dukda ba
hakan sukaso ba amma ko banza sun huce haushi tunda sunsan bakaramin bomb Aka tadar
a gidanba tabbas yakuma tashida dakin hutu.......uwar mai kukemun a mota kananan
yan'iska ko bina gidan iyayena zakuyin? Jiki na rawa ganin yana shirin huce haushi
akansu suka shafama kansu lfy inda Meenah ta leko da kanta ta windon motar, "dan
Allah kabamu na mota wlh bamu fitoda jaka ba.......idan banci ubanda ya haifeku ba
shege nake, kokarin bude motarshi yakeyi a kufule tuni suka kama gabansu ganin yana
shirin musu tijara da sanyin safiya suna tafiya suna tikar dariyar murna harda
hawayan farinciki inda basuda burin daya wuce na ganin leemah tareda sanin halinda
take ciki.

Mahuta na layi kanshi kamar zai fashe mommy sane da daddy suna karyawa a dinning
section ihu momnyn Sa tasaki ganin shalele na shirin faduwa fuska jini da majina da
gudu suka tashi har'rige rigen rikeshi sukeyi itada daddyn Sa inda babanshi yaita
kunduma manya manyan Ashar tareda rantsuwar daukan fansa akan duk Wanda keda hannu
akan abunda akaima dan'sa likitoci yashiga kira saikace Wanda yarasa kafafu inda
yakira commissioner of police tareda lauyoyi manya guda biyu a cewarsa suzo akwai
katon tashin hankali a gidansa yanaso yayi shari'a dawasu daga yau har'igiya tayi
rara, 'batareda wani kunya ba mahuta ya gayama iyayanshi duk abunda yafaru cikin
sha'gwaba nan mommy takara kulewa, 'matsiyata suba abun farinciki bane ace Dan lele
kamarka yama diyarsu ciki ita mijin nata ai abun yayi murna ne jininka na Rayuwa a
gidanshi akan dan'karamin abunnan ne zasu nakasaka harda cire hakori saikace Wanda
yaima Yammata dubu ciki muba matsiyata bane idan bamasan cikin sai a burge idan
munaso kuma dandai rai daya jal sai'a dauko masu aiki suyita kulada babyn mukayima
wasu banza bare namu tsiyar rashin wayewa kenan ina ranar dakikanci? wlh wlh bazan
yarda ba harta iyayan yarinyar sai munyi sha'ria dasu akanka aka farama mata ciki?
Koko dole kayi mata har'tayi cikin?......'Mamie mijinta fa Babba ne daga gani shima
Dan babban gida ne ina ganin kawai abar case dinnan abari ta haifo mun bby na kawai
dukda ban shirya Zama tsoho ba but zanyi hakan a matsayin daukar fansa inbata sunan
iyayanta diyar manyan malamai cefa.....'kaci gidanku, daddy yaimasa dakuwa, kana
nufin sun bugi banza kenan?

Leemah kuwa kamar mahaukaciya tadawo duk inda ta gilma sai kallonta akeyi wasu
najin kyamar ta wasu na tausaya mata chan gabada unguwar sosai ta tsaya a cewarta
kada AK ya biyota dakyar tasamu napep dinda ya dauketa yayinda ya kaita gidanta na
Isa kaita, fitowa tayi tashiga buga gate din mai'gadin gidan ya bude saida tabashi
tsoro..........haaaajjiiya.....kece kuwa? Kodai bake bace? Subhanallah hatsari
kikayi abun babu kyan gani wlh, 'banasan surutu karamin munafuki sallami mai
a'daidaita kakuma kulle mun gidana......'isowar su meenah neya katse mata maganar
ta yayinda suka fito suna salatin ganin ta a haka cikin munafunci ransu yayi fari
kar' kamar audiga, "ubanwa yayi miki haka kinga fuskarki kuwa saikace zombie,
meenah tafadi tana shirin shafa fuskar leemah, kul kada ki kuskura munafukin
hannunki ya sauka a jikina Algunguma butulu maciya Amana wadanda basusan mutunci da
Arziki ba matsiyata....'haba dakin hutu mai yayi zafi haka yanzu dai dan Allah bani
kudi mu sallami mai abun hawannan, kudinda ubanku yabani ajiya? Tafadi tareda bude
idonta dayayi suntum dakyar take iya ganinsu, Kallan mai'gadin sukayi, sallame su
Dan Allah sai binmu sukeyi da ido, yana shirin basu kudi leemah ta buga masa tsawa,
su kakema aiki koni? Wlh muddin kabiya kudinnan kamar ka yanki takardar barin
aikinka a gidannan ne, oooh hajiya kuyima Allah kuyi hakuri har mutane sunfara
kallan ku, 'kuma kada kabar kowace yar'iska shigan mun gida tunda gidan bana uban
mutum bane, zuciya taja meenah jin Abunda leemah kecewa, ke gidan na uban naki ne
mai dattin hula?
'Dukda bana ubana bane amma da sunana aka siyeshi sannan nikeda mallakin shi Baku
ba, dama ance tsintacciyar mage bata mage.....aiko
nan suka damko leemah suka hau jibgarta dama a kule suke da ita kafun kace kwabo
jama'a ancika akansu layi ya kaure da tikar dambe dakyar aka kwaci leemah a hannun
su wacce da ana suma hamsin tabbas da tayishi a yau, yan unguwar ne suka raba
dakyar masu napep kuwa cewa sukayi sunyafe kudin domin rabonda suga damben mata
Wanda ya kayatar dasu irin wannan tun yarinta, nan yan'unguwa aka shiga zaginsu
meenah kassncewar ansan gidan karuwai ne gidan amma ganin manyan masu kudi sun
daure musu gindi kowa yakasa magana ganin yau dama tasamu hakan yasa akai musu chaa
akai ana tsine musu harda masu dukansu tareda jama mai'gadi kunne duk wacce yabari
tashiga gidan saisun gona gidan da mutanan gidan sungaji da zunubin da ake cika
musu unguwa dashi, kuka su meenah sukeyi inda suke roko abarsu sushiga koda wayarsu
ne su dauka gasuda uban kudi a gidan Ga motoci dankara dankara, kememe aka rakasu
da duka sukabar layin kaya duk'ya yage kamar mahaukata takaicin su babu mai waya
bare su kira Alhazawan samarin su, kuka sukeyi tareda tsine ma leemah a cewarsu ta
shafama rayuwarsu bakin fenti ina suka dosa? Suba dangin iya barena Abba a garin
kaduna dama barikice takawo Alkawarin zuwa gidansu leemah sukayi domin warwarema
iyayanta halinda take ciki.
'Leemah kuwa tana kwance da alamar wani suman tayi wani makwafcin sune ya
tausaya mata inda shida matasa guda biyu suka dauketa zuwa asibiti cikin gaggawa
aka amshe ta babu kyan gani yayinda aka gyara mata cikinta da azaba yasashi komawa
gefen mahaifa amma bai zube ba, azaba iya azaba tasha inda ta gwammace dama mutuwa
tayi nan wadanda suka kawota sukayi wucewarsu.

Sai'chanda yamma AK ya farka inda yayi ramuwar sallolin da ake binshi ba laifi
jikin nashi yayi kyau Sannan yaga gata wurin dangi kowa jidashi yakeyi tareda
kwantar masa da hankali Aisha kuwa tana gefe daya tarasa sukuni babu ko kunya AK ke
kallanta tareda tarin nadamar Abubuwan dayayi mata abaya cikeda Alkawarin neman
gafararta ya yarda zaiyi Rayuwa da ita a'haka ya Amince yanzu baya bukatar swt 18
kokuma budurci matarshi yake bukata da soyyar ta duk runtse saiya lallaba abarsa,
'mikewa yayi gaban daddy dasu Ramata daki yacika yayi makil inda babu kunya kai
tsaye ya dosa Aisha wacce ke zaune kusada Mamie cikin mamaki yasaki kuka tareda
Dora kanshi akan cinyar Aisha nan kallo yakoma kanshi ganin katon Allah na rasgar
kuka A'gaban matarshi, 'Mamie na cuceta na cuce kaina hakika Aisha bazata yafemun
ba shiyasa nake naiman Alfarmar neman yafitarta a gabanku daddy Dan Allah kasa baki
tanajin kunyar ka na cutarda matata wlh banida abunda nakeso samada Aisha wlh Mamie
kinfi kowa sanin yanda nayi rainon soyyar Aisha tun kafun inbar kasarnan da soyyar
ta natashi nakuma rayu Mamie duk abunda nayi soyyar ta ce sila, Santa ne sanadi da
bakin kishin ta ku rokamun matata please Mamie har'dukan Aisha inayi......rufe masa
baki tayi tana girgiza masa kai, bataso yayi bakinjini a idon yan'uwanta ga
mahaifiyarta a wurin ga wanta garbati bawai hakan na nufin ta yafe masa bane a'a ko
kadan saiyaji kwatankwacin azabar da tasha dukda ko'a haka tabarshi tasan ya gasu
burinta taga wannan ranan, rananda AK zai tsuguna akan kafarsa yana kuka tareda
neman gafararta, zata iya shiryawa dashi sukuma bazasu taba daina mishi kallon ba
har'abada darajarshi bazata dawo a idonshi ba, kuka takeyi kamar Ranta zai fita,
'bawani uziri yaya AK bakada uziri baka sona kada kawani fake da soyya ta,
Rungumeta yayi tsam a jikinsa tareda Kara fashewa da kuka.....'my Eesha bakisan
sirrin dake zuciyata ba kinsan yanda nakeji duk Randa nasaki kuka
kuwa........'gyaran murya Alhaji muktar yayi tareda kallansu, 'yanzu dai bare
mufita mubar muku Asibitin tunda ka nuna matarka kakeso tayi jinyarka ana mana
korada Hali babu ko kunya kuke rungume rungume a gabanmu harda kukan soyya, 'hajiya
tashi mu wuce saiya gaya mata sirrin zuciyar tasa baza'ai rashin kunyar nan a
gabana ba idan kuma zaki tsaya kallan dramar soyya toh Nina tafi saimun hadu a
gida, fita Daddy yayi Ramata tabi bayanshi da garbati cikeda kunya Aisha tayi tayi
AK ya saketa rantsewa yayi akan bazai saketa ba sai Mamie tabata hakuri harda
rikema Mamie gefen zani inda Aisha keta kukan abun kunyar da AK kemata gaban
surukai saikace yara. Mamie kuwa murmushi takeyi ganin sababbin Romeo and Juliet a
gabanta.

Mrs Sadik Rumah 💅🏻


🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
🏼🏼🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie.*

*Dedicated to Sister husnah*

35

Mikewa takesan yi Amma ya'hanata wai saitace ta yafe mishi inda Mamie cikeda dariya
take tayashi ba Aisha hakuri dukda batasan abunda ke tsakanin suba amma ya zatayi?
Ya hanata koda motsi ne cewa tayi ta hakura ganin idon Mamie gakuma kunyar yanda ya
kankameta koba komai Mamie bata chanchanci musu a wurinta ba hakan yasa Mamie
mikewa tareda janye mayafinta yayinda taimusu fada sama sama wucewa tayi sanin
daddy na jiranta a waje inda Aisha tafito Rakata nan Mamie ta dinga janta a jiki
tareda nuna mata akan takula da Mijinta wannan wata sabuwar damace Allah yabata
idan laifi yaimata duk mace mai aji basaita gayama mijinta yamata laifiba zai gane
Laifin Sa cikin hikima da dabara ake komai a'haka sukayi sallama inda tabi daddy
Wanda yaketa mamakin karfin Hali da rashin kunyar AK saikace ba shine yagama ihun
bayasan Aisha oooh yaran yanzu basuda kunya yaro anama gata kakasa ganewa kadan ma
kagani, inji dady yafadi yana murmushi. AK kuwa sabuwar sha'gwaba yake xubama Aisha
kamar yaron goye ita abunma kunya yake bata gaba daya bata sakan masa fuska inda
yakicin Abinci wai itace zata bashi a baki sai shege mata yakeyi ita kuwa cikin
rashin sabo sai janyewa takeyi bataso tabashi fuska harga Allah tana matukar kaunar
mijinta amma bata shirya Amsar'sa a yanzu ba saiya gane kuransa tukunna nan gaba
yasan darajarda takeda shi.

Commissioner of police ne zaune gaban sanata inda Yaketa bashi hakuri tareda
Alkawarin daukan mataki cikin gaggawa nan sanata ya Saki bakin Aljihu saboda komai
yatafi daidai zai iya yafe komai banda cima iyalinsa fuska, mahuta kuwa azaba
yakesha kanshi kamar ya fashe likita ya duba lafiyarsa tareda Dora shi akan
magunguna bayi yashiga yadade yana gasa jikinsa bakaramin bugu yaci a hannun AK ba
nan yashafa maganin zafi duka jikin nasa inda yaci abincin da mommy ta tasashi a
gaba shayi kawai yasha saboda bakin nashi dake mishi azaba magani yasha nan yaita
bccin wahala.

Kai tsaye su meenah gidansu leemah sukaje inda Mama ta tarbesu hannu biyu biyu
Cikeda mamakin ganin yanayin su babu Alamar mutunci kaya a yage kamar an kwato su
daga bakin kura yayinda yayyan leemah maza wadanda ke Kano sunanan da iyalansu
tun biki basu koma ba gida yacika gwanin ban Sha'awa Malam liman nanan shima cikin
daki take shirin jansu su kimtsa jikinsu amma suka nuna bashine ya kawosu ba,nan
kowa yafara tambayan lafiya kallo daya zakai musu kasan basa cikin natsuwa, izinin
Zama Malam liman yabasu ba musu suka zauna aka basu ruwan sanyi sukasha saida Malam
ya tursasa musu cin abinci nan sukaci kadan badan sunso hakan ba dukda suna tareda
uban yinwa amma kwarjini Malam din yake musu basa iya Musa mishi, bayanin Abunda ya
kawosu suka farayi tiryan tiryan inda kafun meenah tarufe bakinta taji saukan
murfin kwanon'sha Wanda mama ta buga mata tana huci, ooooh bakin ciki kukema diyata
ganin tayi Aure a gidan Arziki cikeda kwanciyr hankali shine saboda fitsara kuka
wanke kafafunku ba kunya kukema diyata Dana dage wurin bata tarbiyya kazafi wlh mai
rabani daku sai Allah, sirikanta mata ke riketa inda duk abunda ta rarumo take
jifansu Meenah dashi Malam liman kuwa tunda suka fara magana baice komai ba har
zuwa yanzo inda ya tsawatarma mama dakyar ta natsu tana kuka tareda Allah ya isan
sharrin da akaima diyarta, kallon su meenah yayi inda yabasu umarnin su cigaba da
bayani meenah kuwa duk a tsorace take baki na zuban jini cikeda azaba take shirin
barin gidan inda yayyin leemah suka dakatar da ita, feenah ce takarasa bayanin tana
kuka ganin tashin hankali da suka jefa kansu daga wayewar garin yau, ana hakane
Motocin yan'sanda suka dinga Dira a kofar gidan saikace sansanin yaki inda batareda
bata lokaci ba akayi musu sallama damai gidan wasu rikeda bindigogi cikin sanyin
jiki Malam liman da yayyin leemah suka fita waje inda kai tsaye aka tasa keyar su a
cewarsu saisun fitoda yar'su da sirikinsu dasuka boye sakamakon sunje gidan AK
mai'gadi ya shaida musu bakowa a gidan shiyasa sukazo nan a tunanin su Malam dinne
yaboye AK da leemah, Salati Malam yadinga nanatawa tareda kiran sunan Allah
yayinda jiri ke dibarsa nan unguwa ta cika makil inda matasa da dattawan unguwan
sukace indai suna raye bazasu bari aci mutuncin Malam ba hayayyakoma yan'sandan
sukayi ganin ba sarki sai Allah haka yasa suka hakura Malam yashiga daya daga cikin
motar matasan unguwan da suka shirya binsu domin ganin yanda zata kasance cikeda
tashin hankali mama take inda kukan da takeyi tuni ya tsaya tama rasa abunda zatayi
taji dadi a Ranta.

Rikici akayi sosai a station sunan Allah kawai Malam ke kira jin Laifin da ake
zargin AK dashi wato na cirema yaron sanata Wanda Saurayin leemah ne a sakamakon
yaje duba Ajiyar cikinsa dake jikinta, dariya ma maganar tabama jama'ar wurin Abu
saikace wasan yara taya mace da Auranta kuma ace tanada cikin wani? inda kassncewar
babu kwakwaran shaida akan abunda ake zargin suda shi hakan yasa sanata yace a
sakesu kai tsaye kotu za'akai karar saiyaji dalilin da zaisa a cirema danshi
hakori, isarsu gida yayi daidai da kiran wayar Mama da aketayi inda dakyar ta iya
amsawa Asibitin da leemah takene suka tasata gaba akan saita bada number wani nata
an kira babu yanda batayi ba sukace indai zata biya kudin Asibitin ba matsala zata
iya tafiya ganin batada kosisi kuma batada Wanda zata kira yabata gashi tabar
wayarta a gidan AK tun daran 1st 9yt bareta kira samarinta hakan yasa badan taso ba
tabada number Mamarta nan aka kira mama aka shaida mata tazo asibi ana nemanta
cikin gaggawa tazoda kudin biyan AAsibiti cikin gaggawa itada sirikanta mata biyu
suka shirya zuwa Asibitin shigowarsu malam yasa aka rankaya gaba daya inda kai
tsaye aka nuna musu dakinda leemah ke ciki nan cikeda tashin hankali da tarin
tambayoyi mama ke kallon leemah da halittar ta tagama chanzawa duk Wanda ya Santa
ada bazai iya ganeta ba wasu dayawa musawa sukayi akan ba ita bace mama kuwa kallon
ta takeyi batako kyafta ido sanadiyyan bayanin da likita yaimusu akan cikinda ke
jikin leemah harna Wata Uku.

*Mr's Saddiq Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Alhamdullah Allah ya dawo dani kamar yanda naimuku Alkawari, gobe nasoyin posting
amma messages dinku da yawan kiranda nake samu dole kujini yau saboda kada a kashe
mun batir din waya, lol😜 masoyana Naga sakonin fatan Alkairi da Addu'a godiya
nakeyi Allah ya barmu tare.*
*Dedicated to sister Husnah*

36

Kuka leemah keyi ganin yanda mamanta ke kallon ta babu ko kyafta ido, tun tana
shirin jin saukan duka har'abun yafara bata tsoro, saida mama ta dauki minti biyar
tana kallon ta inda akaita 'kallon kallo a dakin sautin kukan leemah kawai ke tashi
sannan ta bude bakinta dayake mata nauyi, 'menene Laifin mu a matsayin muna
iyayanki? Ilimi koko gatan da muka baki? Ciki kikayi kodai mafarki nakeyi? Diyata?
Ni? Jinita dayin cikin Shege......Dan Allah mama kiyi hakuri kaddara
ce,.....kaddara? Wace irin kaddara ce wannan data sauko tsakiyar gidan malamai?
Durkushewa tayi kasa tareda ware duka muryarta tana kuka tana bugun kirjinta tareda
Rokan Allah ya dauki Ranta akan ganin bakin ranan nan diyar cikinta hafiza wacce
suka ginata akan ilimi da tarbiyya ita keda cikin Wata Uku ko sati daya batayi ba
dayin Aure, kuka mama keyi inda Malam liman ke manne jikin bango sai kallon matar
tasa yakeyi da diyarsa kamar TV babban dansa ne da jama'ar da sukazo tare ke shirin
tabashi da niyyan lallashi yayinda ya dakatar dasu da hannun da Alamar su barshi
kawai duk Wanda ke wurin saiya tausayama Malam da hawaye daya kebin daya a fuskarsa
karona farko a tarihin rayuwar malamin da suka ganshi a yanayin nan wurin Mama
yakarasa tareda tsugunnawa ya Tallabota jikinsa yayinda suka Mike domin shirin
barin dakin suna gafda fita akaga idon mama ya kafe sama kumfa na fita ta bakinta
jikinta na rawa kamar an jona mata wutan lantarki wani ihu leemah tasaka yayinda ta
nufi wurin Maman tana kuka tana girgiza ta tuni likitoci suka dauketa da gaggawa
inda babban wansu ya rufe leemah da duka tako'ina yana kuka harda majina yana mata
Allah ya isa, kallon su Malam liman keyi yana durkushe kafun a Ankara shima ya zube
bakinshi dauke da salati nan asibiti aka rikice da surutai yaran Malam liman ne
duka Ukun suka taruma leemah da duka ta ko'ina Alkawari sukai saisun kashe ta tunda
tayi sanadiyyan kashe musu iyaye bazasu barta ba, dakyar aka kwata leemah a hannun
su wacce ko motsi batayi jini sai ambaliya yakeyi ta kasanta Asibiti ya cika makil
kowa na ganin abun Al'ajabi kassncewar Malam liman sananne hakan yasa harda
yan'jaridu da TV stations anata kokawan daukan labarai, cikin hanzari aka karayin
gaba da leemah inda saida tarasa hakora Uku biyu a saman baki daya a kasa ta gefe
duk yanda akaso ankasa daidaita numfashnta inda ake shirin sakata a coma.

AK kuwa gaba daya chanzawa yayi yayinda abun yafara ba Aisha tsoro ganin dama AK ya
iya magana haka, kwana daya yayi a Asibitin dakyar Wanda daran jiya yadamu Aisha da
roko da magiya akan tayafe mishi ganin duk abunda yake mata bai hanata jinyar shiba
dukda babu yanda baiyi da ita akan ta kwanta akan gado ba amma kememe taki inda ta
raya daran nata wurin Rokan Allah akan ya daidaita rayuwarta ko'itama zata samu jin
dadi tun AK na kallonta Yayinda take burge shi har bcci yayi awon gaba dashi, washe
gari Dagewa yayi akan bazaici abinci ba wai hannun shina ciwo a cewarsa mahuta ya
bugan masa hannu sosai yanama tunanin har'yayi targade hannun yayi tsami inda Aisha
baki bude take mamakin yanda Yaya AK ya kware a karya idan bata mance ba baima ba
mahuta damar dukansa ba amma ji yanda yake gilma karya babu ko kunya, kiri kiri
yakicin Abinci dukda yanajin yinwa a cewarsa indai Eesha bata bashi a baki ba tohfa
saidai ya mutu da yinwa ko jiyama haka yayi inda madara kawai yasha Aisha kuwa ta
murzama idonta toka dukda Tausayin shida takeji bataso yasamu weakness dinta, ana
cikin haka ne kaninshi Abdulhakeem ya shigo inda AK yahade rai tareda kunkuni, "wai
nayau ma kawai baza'a bar mutum ya sake da iyalinsa ba? Mtseww, Zama Hakeem yayi
tareda murmushi, Daddy ne yace inzo in kwana dakai a Asibiti Anty ta koma gida
itama ta huta.......ka kwana dawa? Badai niba? Wace Antyn? Badai my Eesha ba?
Yafadi fuska a hade kamar zai mangare Hakeem, Allah ya kyauta in kwana da katon
kato a daki daya bayan inada matata wacce zata kula dani, my Eesha ko bakyaso ki
samu ladan jinyar mijinki ne? Ya fadi murmushi akan fuskarsa, mikewa Aisha tayi
yayinda tajawo hijab dinta tareda shirin tafiya dukda tanaso ta kasance da Mijinta,
kallon Hakeem tayi, 'yauwa ka bashi Abinci a baki yace bazai iya Amfani da hannunsa
ba Nina tafi saida safe, 'wait Wait Hakeem ya furta cikeda dariya yana tafa hannu
tareda nuna AK da yatsa, Badai Bros kike nufi zanba abinci a baki ba tsofai tsofai
dashi? Nooooo it can't be possible kuna wasa ne wlh bazanba wani kato abinci a baki
ba look ki ciyarda mijinki, 'nine katon? AK ya Tambaya sounding so serious fuska a
harde, " am sorry bro but u and ur wife are very funny, 'Nina tafi Aisha ta furta
tana shirin bude kofa inda AK yayi wani mugun tsalle daya tareda damko ta saikace
bashi ke jinya ba, rungume ta yayi sosai da hannuwa duka biyu ta baya har'saida
tasaki yar'kara sai kokarin kwace jikinta takeyi ina yaki barinta ihu tafarayi kasa
kasa tana bubbuga kafarta cikin shagwaba, Kallon Hakeem yayi Wanda yasaki baki da
hanci yana kallo da mamakin salon yayan nashi, toh magulmata sai abamu wuri koh
jeka waje ka nemo mun lemun bawo mai zaki, 'Allah ya Baku hakuri ni ina zan iya
kallon abun kunyar nan? Dama fita zanyi ko'bakace ba yafadi yayinda ya Mike, but
Bros wannan uban lemun fa? Yafadi tareda nuna tarin lemun zakin dake jibge a gefe
daya, 'look Malam basu nakeso ba kana bata mana lokaci, ko kunya baiji ba ya juyo
da Aisha tana fuskantar Sa fuska sharkaf hawaye inda yake kokarin zame mata hijab
ita kuma ta kunkume taki bari, Kofa Hakeem ya kulle tareda mamakin dama haka
yayanshi yake baida kunya?
"Kuka Aisha keyi maidan sauti tunowa da irin wulakancin da azabar da AK yake
gana mata a ganinta rainin hankali ne kwana daya rak yadawo wai yana Santa yana
Santa kodai yana Sha'awar ta? Kuka takeyi sosai.....'nooo my Eeasha please please
not again banaso in Zama sanadiyyar zubowar hawayanki insha Allah daga yau
har'abada please my wife karki horani ki tausaya mun.......'daka rasa swt 18 dinka
koh? Daka rasa matar so? Ni banza yar'tasha Mara tarbiyya kazar kowa yar'duniya
wacce batada gata wacce tagama rabarda duk wani mutincinta a titi wacce batada
Amfani a gidanka face taci takuma cika maka Masai da kashi mai wari a gida....."
Nooo Eeasha please please karkice haka ki fahimce AK dinki nasan naso kaina dayawa
na cutar dake Wanda bazaki iya yafemunba wlh kiyimun duk hukuncin daya Dace I
deserve please wife but ki kasance tareda ni karki gujeni wlh dakin San wanene ni
da kinsan halinda nashiga a kanki da kinsan mahaukacin Soyyar da nake miki saikin
tausaya mun.....'oh yes, tafadi tana shirin kwace jikinta daga nashi amma yaki
sakinta, Soyyar da babu komai sai azaba da bauta? Soyyar tozarci da duka? Soyyar
bauta? Mara yan'ci? Ko zamanin jahiliyyah bantaba jin labarin irin soyyar nanba,
'girgiza mata kai AK keyi kamar zaiyi kuka kwalla tafara cika masa ido cikeda
nadama tareda tsanar kanshi akan abunda ya aikata, Aisha kuwa kuka takeyi tuno da
azabar daya gana mata eye? Gayamun gayamun haka ake soyya a duniyar ka? Inko haka
soyyar ka take tun wuri kaje ka nema wacce zakayi irinshi da ita badaini ba not
again nagama wlh nagama kokuma idan matar so tadawo....rufe bakinta yayi danashi
jin zuciyarshi tana shirin fashewa tumomai da abunda leemah tayi Wanda bazai iya
sauraran taba tun ana na hankali tana kokarin kwacewa dakai masa bugu ina dorata
yayi akan gadon Asibitin inda yayi Mata rumfa da jikinsa sunkai minti goma a haka
har'karfin Aisha yakare inda ya sake bakinta yafara lashe hawayan dayayi Alkawarin
bazasu Kara zuba a sanadiyyar saba saidai tayi hawayan dadi insha Allah, runtse ido
Aisha tayi jikinta na rawa tana wasiwasi Anya ba mafarki nakeyi ba? Yaya AK kecewa
yana Santa? Ashe dama zataga ranan nan a zahiri ba'a mafarki ba? 'Likita dake
tsaye a kansu Wanda baiyi minti daya da shigowa ba shine yayi gyaran murya tareda
kauda kansa gefe yana murmushi duba jikin AK yazoyi inda yake shirin aiko masa
dawasu maganin, 'Ranka shi Dade da Alamar sallama kawai kake bukata Dan naga jiki
yayi kyau Alhmdlh da Allah bai kawoni ba kila da'a dakin nan za'a sama mana
tsarabar dan'baba, Hakeem neya shigo jin maganar da doctor keyi aikuwa ya tuntsure
da dariya inda AK ke zaune a gefe sai kame kame yakeyi tareda gyarama Aisha
dankwalinta daya cire mata, fusge dan'kwalin tayi ta cusa kanta ciki cikeda kunya
shikuwa sai hade rai yakeyi a dole bayasan Raini, "bari in rubuta muku takardar
sallama mu ai haka mukeso Lallai uwargida Maganinki yafi asibiti tasiri wannan aiki
haka hmmm, likita yafadi cikin barkwanci tareda barin dakin aikuwa mikewa AK yayi
yafara hada kaya, 'Bros ya haka? Ina kuma zaka? Inji Hakeem dayake faman dariya,
'ban saniba koba a gabanka aka sallame niba look bansan munafunci uban maiya dawo
dakai bayan na sallame ka? zo kayi gida Malam, yafadi har yana hankade Hakeem waje
harda Danna sakata a dakin inda Hakeem keta sheka dariya, wooooo soyyah masu gari
dole inba su Mamie da Daddy labarin nan hahahaa love on point Gskia nima dady ne
zai nemo mun matarda zan Aura naga alaman baya zabin banza, 'Allah ya isa indai
akayi gulmata Dana matata, Ak yafadi da karfi sounding so serious Aisha kuwa Yanzu
abun yadaina bata mamaki sai tsoro.

*Mrs Saddiq Rumah💅*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Afuwan jiya nayi mistake a wurin page number, 36 zansa nasa 37 yanzu zan cigaba da
38 kawai gudun rikicewa.*

38

Dole hakeem sukabi yakaisu gida yayinda ko takardar sallama bai jira ankawo ba suna
isa gida mai'gadi ya bude gate tareda gaishe shida jiki yanaso ya gaya musu zuwan
yan'sanda neman AK amma ganin rashin dacewar hakan Ga Wanda yadawo daga Asibiti
yasashi tsuke bakin shi inda Aisha ta kira bilki batareda bata lokaci ba tazo
yayinda suka Kara kimtsa gidan tas ko'ina sai kamshi yakeyi Mamie ceta kira Aisha
tareda shaida mata kada tayi girki za'a kawo musu daga gida tahuta na kwana biyu
hakan yasa suka koma daki itada bilki inda take bata labarin sabon salon AK dariya
bilki ta dinga yi inda ko kadan bataji tausayin Shiba saima cewa datayi kadan
yagani, "idan ankawo abincin ki daure kibashi a baki kada ki sakar masa fuska, a
haka suka tsaida maganar, aikuwa ana kawo abincin AK ya shigo dakin da sallama
"hmmm maza kenan ji yanda yayi ladabi cikin kwana biyu" yayinda yayi wanka ya
chanza cikin farin jallabiya kallan bilki yayi yana murmushi, " kanwar mu sannu da
zuwa yasu mama? 'Lafiya kalau suke sunce a gaida ka, tafadi dukda ada ta tsani AK
amma koba komai zaici darajar Auran yayarta da yakeyi kuma tsakanin miji da mata
sai Allah, my Eeasha am hungry please Dan Allah Kibani Abinci Eesha yafadi a dole
so yakeyi Aisha taji tausayin shi, 'Bata Musa masa ba suka fito gaba daya harda
bilki inda jalof rice ce tasha hadi sai kamshi takeyi ga hadaddan Pepe chicken
awani kula hakan yasa Aisha ta zuba abincin yayinda ya zauna akan dining bilki na
tsakiyar parlor tana kallo kusada kujerar shi Aisha ta zauna yayinda ganin baida
niyyar ci yasa ta juyo da kujerarta sosai tana fuskantar sa tafara ciyar dashi
batareda tabari sun hada ido ba inda yakecin abincin cikin natsuwa so yakeyi ta
dinga sakewa dashi amma taya? Taya zai fara? Maiya kamata yayi domin gyara kuskuran
daya tafka? Yah rabbi ka kawomun mafita a gidana, ya furta a zuciyar Sa inda saida
yaci ya koshi sannan ta diba nata awani plate din tareda dauka tabar wurin parlor
takoma inda bilki take nan suka zauna sunaci suna fira harga Allah baiso ta tashi
ba dukda baida abunda zaice mata amma yanaso taita Zama kodan ya dinga kallon ta,
waito taya ake lallashin mace ne? Ooh gskia lamarin mata sai a hankali dukda kukan
dayayi mata a gabansu daddy Yanzu maiya rage? Oooh GOD wazai gayamai abunda zaima
matarsa ta huce? Ba ance mata nasan goyo ba toh kodai tsugunawa zaiyi yace tahau
bayansa yaita zagayawa da ita? Nooo nooo Goya wannan katuwar saita karyani ai,
murmushi yayi tunowa dayayi da jikin Aishar, ita kuwa Aisha Rashin sabo yasata
barin wurin ganin yanda ya kafeta da ido bazata iyacin abinci a gabanshi ba hakan
yasa ta tashi.
A' Asibiti kuwa Ansamu Malam liman da mama sun farfado amma an rikesu a cewar
likitoci sai sunyi kwana biyu saboda tabbatar da lafiyar su Wanda Malam din bai
damu ba ko kadan baisan dawani ido zai kalla jama'a ba, taya zaifara? Taya? Tabbas
yasan hakan na cikin jarabawar shi dukda ganganci da sakaci irin nashi dasai yanzu
yake ganin gudunmawar da suka bada wurin bata tarbiyyan diyarsu nan yaita kuka yana
neman gafarar ubangiji Wanda ya jarabceshi ya nuna masa duk tarin ilimin shi ba
shine zai Hana Allah jarabtar bawansa ta inda bai zato ba, nan ya kudiri Aniyar
idan komai ya daidaita zai karbi halima da hannu biyu baya cikin iyayan dake gudun
kuskuran su zai Amsa kuskuransa da hannu biyu tareda kulada cikin jikinta har Allah
ya sauke ta lfy koda kuwa jama'ar gari zasu koreshi akan yana rainon cikin shege
duk zaginda za'ai mishi zai toshe kunnan Sa barna ce anriga an tafka hannun ka baya
rubewa ka yanke, inda labari yagama bin gari duk inda ka waiga maganar diyar Malam
akeyi karya da Gskia haka mutane keta ruruta lamarin har kasashan ya'da labarai
saida akasa domin yazama iznah ga iyaye Wanda wasu da biyu sukeyin hakan domin
tozarta malamin masu zagi da takaicin leemah nayi, masu ganin ganganci da Laifin su
Malam nayi, harda masu Allah Kara, nidai nace kanku akeji.

Ta fannin mahuta kuwa Lauyoyin Dadyn shine suka bashi shawarar janye karar da yake
shirin makawa kotu ganin duk yanda ake daukan lamarin tohfa ya wuce nan, Ranka shi
Dade wannan ba maganar kudi akeyi ko matsayi ba duk abunda akace akwai idon mutane
a ciki gaba daya Al'ummah sun karkata akan case dinnan kasancewar ta diyar babban
Malami a ganina fa barin sha'riar nan itace hanya mafi sauki kada Allura ta tono
garma babu abunda mutane ke jira illah iyaka Susan Wanda yaima halima ciki ya kake
ganin za'ai idan muka fito da kanmu tareda tona kanmu har a'kasan Dan gidan babban
dan'siyasan da yayi suna shine ya banka ma diyar babban Malami ciki ya kake ganin
makomar siyasar ka? Goge zufa daddy yayi dukda baiso hakan ba amma Yaji dadin
Sha'awar nan Allah yaso shi dayayi tabargaza garin neman gira arasa ido hakanan
yanaji yana gani aka rufe case din Inda sukayi luf sukayi shiru suna kallon yanda
Abun zai kasance.

Mahuta kuwa tuni aka saka mishi hakorin Roba a wawulan bakin shi inda ya kudiri
aniyar nanda wani lokaci zaibar kasar domin haduwa da manya manyan likitoci asan
yanda za'ai dashi bazai yiwu babban guy kamarshi ba Dan kudi yakarasa Kuruciya babu
hakori a bakinsa ba, yawa ne indai kudi na aiki tohfa komai yazo da sauki tuni
yakoma kan network inda ya hada duka kawayan leemah meenah da feenah ya ajiyesu
gida na musamman babu ko kunya aka dasa daga inda aka tsaya a cewarsa Gari dayawa
maye bazai taba cin kansa Sa Ga mata jaga jaga wasu ma koda kudinka saida rabon ka,
sukuwa ko kishin kansu basayi tunda rufin asiri suke nema kuma mahuta ya sake musu
kudi wani Kishin namijin bariki zasuyi Wanda baida tabbas?

AK ne zaune a parlor sai safa da marwa yakeyi misalin karfe goma na Dare Wanda tuni
Aisha tadade da Danna ma dakinta sakata, sai sake sake yakeyi yarasa abunyi, dakin
limah yashiga nan yafara jido akwatinan lefenta daya hada mata kaf saida ya hadasu
akwati dozin da manyan jaka guda biyu, dukda ta dinka wasu bai damu ba, akwatin
dankunne yabude tareda Addu'ar Allah yasa gold dinda yasa mata a lefe yananan,
aikuwa yana dubawa saiga dankunne da sarka da zoben gold nan yaita kinkimar kayan
yana jerasu tsakiyar parlon dakyar ya karasa dukya gaji, kai tsaye dakin Aisha ya
nufa yaita buga mata kofa sanin bazai taba dainawa ba harsai ta fito yasata bude
kofar fuska a hade sanye da Riga da wando masu taushi blue color sunyi kyau sosai
sai kamshi takeyi tana yamutsa fuska, "yadai? Bcci nakeyi lafiya ka tasoni cikin
daran nan? My Aeesha magana zamuyi ki sameni a parlor, yafadi tareda Kare mata
kallo yakoma parlon, kai tsaye ta bishi kanta babu Dan kwali tsayawa tayi trus tana
mamakin uban hadaddun sababbin akwatin da suka cika parlon nasu kallonta yayi, "
zauna mana sarautar mata, yayinda yake nuna mata kusada shi, kan hannun kujera
tadan zauna nesa dashi yayinda ta kalle shi tareda kauda ido, ehm ina jinka tafadi
Alamar kosawa, "Aiishaa, yafadi in a husky voice, duk kayanda ke nan wurin ki kwasa
na mallaka miki idan akwai abunda bai miki ba kibada idan akwai abunda kike bukata
ki gayamun, kallon kayan tashiga yi daya bayan daya cikin Al'ajabi da mamakin jin
furucin shi cikin tsohon daran nan wannan kyautar dukta mecece? Shin maiya kamata
tayi? Ta Amsa kokuwa? Mai zatayi da uban kaya haka?, "ya mai karatu kuba Aisha
shawara shin ta Amsa kyautar da AK yaimata kokuwa??

Gogan kuwa Rokan Allah yakeyi yabashi Hanyarda zai lallashi Eeashar Sa, " Shin
wazai ba AK shawarar yanda zai lallashi uwargida?.

Ina jiran comments dinku domin samarma ma'auratan mafita ku taimaka ma AK da


kalaman
👯🏼‍

♀ Soyyah kunsan fa sai a hankali ta fannin Soyyah a play class yake‍♀
💃🏽
Eh:- "Kodai yace yake mintin zuciyata na tuba ki yafemun idan bake ba sai lahira
🤣😜

*Mr's Saddiq Rumah*💅🏻


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Dedicated to Sister Husnah.*

39

My Eeasha kinyi shiru, yafadi tareda karasowa inda take ya tsuguna da guiwoyinsa
duka biyun hannun ta yarike yayinda ya kafeta da ido Aisha kuwa banda bugu babu
abunda zuciyarta keyi, "kana tunanin kayan nan zasu siyeni ne? Mai zanyi da
kayanka? Au wato saboda babu matarso kwalliya bata biya kudin sabulu ba shiyasa ni
banza ka dauko kayan dabada sunana akayi ba kakawo munko? Bana bukatar su maisu
zata dawo ta dauki abunta 'hawayan da take kokarin boyewa suke zubowa, " Aaaisha ki
bude kunnanki dakyau kiji abunda zan furta miki sannan sai kiyimun duk hukuncin
daya Dace dani na Amince na yarda ban chanchanci yafiyarki ba, kayan banza bayan
dakai da kaya duk Mallakar wuya ne, da kayan dani kaina duka naki ne a karkashin ki
muke saikuma yanda kikayi damu Allah yasani Aisha zan gaya miki sirrin da babu
Wanda yasani saike da zakiji a yanzu Wanda duk abunda zan furta miki shine ainihin
gskiar magana, "mikewa yayi daga tsugunnan dayayi tareda Zama kusada ita harda Kara
juyo da ita suna fuskantar junan su hannun su rikeda juna, gyaran murya yayi Alamar
duk abunda zai fadi yanada muhimmanci "tun kafun ki mallaki hankalin kanki Aisha
tun ana mun wasa ana kiranki da sunan matata harga Allah tun a lokacin banida
burinda ya wuce in tattalaki Inkuma kulada ke har'zuwa lokacin da zaki Zama matata
hakan yasa naita rainonki cikeda zallar Soyyah banasan kukanki Aisha, tafiyata
karatu kasar waje ba'a San raina bane kassncewar banaso ki saba da kowa banasan
abunda zai taba mun ke babu yanda banyi ba akan inyi kara2 a kasarnan Daddy yaki
hakan yasa badan naso ba natafi na barki amma dukda haka tunaninki bai taba barin
zuciyata ba koda na sakan daya ne, Duk sanda zanyi waya da mamie saina tambayeta ke
hakan yasa harta fara zargin wani Abu my Eesha shiyasa aka hanani dawowa hutu 9ja
ko'sau daya a ganinsu dakyar aka samu naje dama gara ingama gaba daya, wlh wlh wlh
Aisha bantaba Soyyah ba ban sanshi ba kuma bansan ya yake ba sai akanki, Akanki
Aisha nasan soyya bantaba jin Wata diya mace ta burgeni ba saike My Eeasha ke kadai
ce a idona ina tareda makauniyar soyyar ki, Aisha wacce hawaye daya Kebin daya
cikeda tausayin AK tama rasa mai takeji kukan dadi takeyi kona bakin ciki? Tabbas
ta tuna shakuwarsu shiya darsar mata da soyyar Sa a zuciyarta tun bata mallaki
hankalin kanta ba, tabbas shiya koya mata sansa, "murya na rawa dakyar ta iya
furta...butt kasan kana sona maiyasa kake tozarta ni? Kamana Adalci kenan? Why?
Maiyasa? Ka wahalardani kakuma gasa zuciyata ka horani horo mai tsanani "........
karkiga laifina sanki ne sanadi,kece sila, sanki shine sanadin duk abunda na
aikata Miki a baya my Eeasha kishin kine wlh wlh am not longer my self I can't
control my Eeasha, nadawo kasarnan cikeda tarin nasara da zumudin ganinki domin
bayyana miki sirrin ruhi na Just Imagine kiyimun Adalci my Eeasha, nasamu labarin
kina bin maza har aka gayamun babanki ma naimanki yakeyi am sorry to say, wlh ban
yarda ba kuma na kudira a raina koda hakan ne nasan ba Laifin ki bane kila
tsautsayi ne yafada a kanki dukda haka ana kwana biyu naji nishi a lungun da babu
kowa cikin tsohon Dare na kamaki da maza Uku Eeasha maza Uku oooh my GOD, yafadi
hawaye daya nabin daya kuka yakeyi wiwi hannun shi daya dafe da kanshi Alamar abun
har yanzu namasa ciwo saida suka dauki kusan minti biyar babu mai lallashin kowa
cikinsu, rinannun idonta tadago Wanda suka gama jikewa tareda tausayin mijin nata
ta kalleshi "Yaya AK wlh ba abunda kake tunani bane.......'shiiiii dnt say anything
please banasan in Kara tuna duk abunda ya shafi ranan Bakin rana Wanda bazai taba
gogewa a tarihin rayuwa taba, nasha wahala nayi takaici nayi kukan zuci nayi na
fili nayi ciwo, nayi ihu nayi Dana sanin dawowa kasarnan a dalilin bakin ranan
Aisha why? Inama ban gani ba har yanzu abun na idona, duk sanda zan dakeki ranar
nake gani a idona Radadin ranan ke dawomin sabo shiyasa nake hucewa a kanki Wanda
zafi nake Karama kaina duk Randa nasaki kuka wlh wlh bana iya rintsawa ke kukan
fili kikeyi amma Nina zuci nakeyi I love you sooo much Eassha wlh a kanki zan iya
kashe duk Wanda yakara gigin tunkararki please ki killace mun kanki abunda ya wuce
a baya yariga ya wuce ke nakeso ba vaginity ba kece sanadin Auran halima danayi
Sha'awar ki ke neman halakani kece sanadin halinda na fada, I don't want vagine
Aisha, yafadi yana hawaye, tsugunnawa yayi guiwoyinsa biyu tareda rike mata hannuwa
Duka biyun, "My wife, ya furta in a husky voice, I want you and just you alone,
Aisha Ke naso kekuma nakeso, kezan cigaba daso har'abada insha Allah namiki
ALKAWARI Eeashaa zan wanke duka Laifin Dana miki kikara bani dama a karona biyu a
rayuwarki domin in gyara kuskuran Dana tafka kada kibari inkara maraicin ki please
my wife help me, my Wife am helpless please U r the only one idan kika kini ina
zanje inji sanyi a raina? Wlh ina matukar kaunarki Believe me, ki kalleni Aisha,
yafadi tareda tallabo fuskarta wacce tagama jikewa da hawayan farinciki da tausayin
mijinta, Zokiji, kanta ya Dora daidai saitin zuciyarsa aiko nan taji heartbeat
dinshi na bugu da sauri da sauri, mikewa tayi cikin tsoro cikin rawar murya
tafurta, Mijina..ka yafemun Wlh ina matukar kaunarka kafi kowa sanin a cikin soyyar
ka nake Rayuwa, siihhhuuu, yafadi tareda Dora yatsar hannun Sa akan bakinta Alamar
yasan komai basai tayi magana ba, nan suka rungume juna kowanne na bada labarin
irin soyyar da wahalar dayasha akan Dan uwansa, Tallabota jikinsa yayi nan suka
nufi dakinta tareda Zama tsakiyar gadonta labari yaki karewa babu abunda kakeji a
wurin ma'auratan sai fira da shewa AK na makale da matarsa gwanin ban Sha'awa har
kusan asuba ana Abu daya, "Tsakanin miji da mata sai Allah nidai jamusu kofa nayi
ganin yanda naketa doka hamma da gyanyadi" Asuba tagari Eeshar AK.

Bayan kwana biyu aka sallami Malam liman da matarsa inda suka koma gida Leemah kuwa
har'zuwa lokacin bata farka ba saidai komai nata na tafiya daidai cikin jikinta ma
abun mamaki lafiyarsa Ras sai girman shi yakeyi dukda mamarshi batasan inda kanta
yakeba, gulma kuwa anyita babu iyaka a unguwan Wanda gaba daya Malam daina fita
yayi kwata kwata, shikuwa AK Sam yama manta da zancen Wata Leemah bare Auran su sai
soyewa yakeyi da matarsa Wanda kafun Aisha ta farka daga bcci tuni ya gyara gidan
tareda hada mata breakfast lafiyye bakaramin wahala yakeci ba saboda rashin sabo
haka zaiyi waja waja abincin ma bawani iyawa yayi ba wanima a waya yake nemo
recipes din yanda akeyi dukda baya dadi sosai amma Aisha bata taba nunamai ba, akan
dole ya dauki hutun Annual live a Office inda ya zake yanata nemo soyya a wurin
matarshi babu yanda Aisha batayi akan yadaina aikin gidan ba amma kememe yaki, dan
har wankin motanshi shi yakeyi haka zaita nishi idan yagama Aisha taita mishi
dariya yayinda wani sabon tausayinta da soyyar ta ke Kara rufe shi baba mai gadi
kuwa yana ganin love haka AK zai dinga watsama Aisha ruwan dayake dauraye mota
itama ta biye mishi kamar yara suyita dariya suna guje guje a tsakar gidan Saisun
jika ko'ina mai gadi kuwa baki bude yake kallon ikon Allah ganin abun bana karewa
bane gashi shi kunya ma suke bashi hakan yasa yaja yar'raidion shi tareda girgiza
kai, "Uhmm su Alhaji manya ashe kaima Dan soyya ne anaso ana kaiwa kasuwa ikon
Allah, dakinsa ya shiga inda shigarsa babu dadewa Yaji ana kwankwasa gate din
budewa yayi tun a bakin gate din bilki ke tafa hannu ganin yanda AK ya makure Aisha
a jikinsa yana watsa mata ruwa duksun jike sai dariya sukeyi basuma sanda zuwanta
ba, Ooooh su Anty Soyyah ake sha haka? Yaya AK dama ka iya dariya Ashe? Ikon Allah,
ko jinta basuyi ba sai dariya sukeyi gwanin Sha'awa duk Wanda yaga masoyan a
lokacin saisun burgeshi mai'gadi neya kalleta, " ai hajiya wadannan idan ba zuwa
kusada su kikai harki tabasu ba ina shaida miki kozaki kwana wurinnan basu sanin
zuwanki, ooh ni iro ina ganin wani Abu waishi Soyyah a cikin satin nan, da gskiar
yaran zamani dasuke Wata waka wai ita Soyyah dadi, "Wuceshi bilki tayi inda tana
zuwa gafdasu Aisha ta bangaje AK duk sunyi sharkaf bayan bilki ta boye tana ihu
aikuwa ya hada dukansu yana musu feshin ruwa sai ihu sukeyi matarshi yaja jikinshi
tareda janta ciki, " muje in tsaneki baby na kekuma gwauruwa saiki taho, yafadi
yana dariya bilki kuwa bakaramin burgeta sukayi ba dukda Aishar ceta kirata tace
mata tazo gidanta akwai suprice da zata gani, zuwanta kuma wannan abunda tagani
yawuce suprice hakan yasa jikinta na digar ruwa tashiga cikin gidan tana rawar
sanyi dakin Aisha tanufa bata ciki nanta chanza kayanta tasa na Aisha wacce
kakejinta shiru a barayin AK, saida suka kimtsa ruwan zafi ya tsarama matar tashi
sosai sannan tayi wanka inda saida ta fito yashiga yin nashi tsaf'ta lurada kallon
sha'awarda mijinta kemata tana saneda yanda feeling's ke hanashi bcci kwana biyu
yayinda yayi Alkawarin bazai taba nemanta ba harsai Randa ta Amince takuma shirya
amsarsa a matsayin mijinta hakan yasa tacema bilki tazota Kara hadata sotake su
Angwance sukuma sha soyya mai tsayawa arai tareda tarin tarihi a daran nasu nayau,
dakyar yabarta zuwa wurin bilki yayinda yace mata zaifita daganan zai musu takeaway
na abinci yau bazai samu daman yimusu girki ba a cewarsa ita Amarya ce yanzu tazama
yar'hutu, har dakin ya Rakata rikeda hannun ta inda ya damkama bilki Amanar matar
tasa saikace wani zai kwace masa, tsokanarsa bilki taitayi fita yayi tareda manna
ma hannun Aisha kiss, hakan yasa takara mikewa wai zata rakashi bakin
gate......"wlh Adda zanyi tafiyata nayi wurin awa guda ina jiranki a dakinnan nasan
daga zuwa rakiya Zama ki iya binshi oooh wannan Soyyah muma Allah yabamu namu,
"Ameen inji AK, kema idan kinji haushi kiyi Auran, yaya AK abun harda gori kuma?
Tafadi baki bude, " eh wlh ki daina sama matata ido my Eesha na yafe miki rakiyar
nan kada uwar sharrin nan tasaki a gaba idanna fita saina dawo bakuma zan Dade
ba,yafadi tareda kallon bilki, wato korada Hali ake mata ma, hmmmm lallai duniya
juyi juyi inji masu iya magana.

*Mr's Saddiq Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie.*

*Dedicated to sister Husna.*

40
Fira sukeyi sosai da bilki inda bakin bilki yaki rufuwa saboda tsabar murna, oooh
ikon Allah kenan wato mahakurci mawadaci Adda Allah ya dauwamar da farinciki a
rayuwar auranku, nan biki taita zuba musu addu'a yayinda suka nufi kitchen, dabinon
da Aisha ta jika tun daran jiya shita dauko a cikin wani jug Mai kyau ya jiku yayi
luguf, a blender tasa tareda yanka kankana Mai zaki bata cire kwallon taba ta
gauraya da dabinon tareda zuba madarar shanu Mai kyau akai, da isharshan kanunfari
nikasu tayi suka niku luguf batareda ta tace ba kasancewar yayi laushi nanta bude
madarar ruwa gwangwani biyu ta zuba akai tareda yarya'da Zuma, hmmmmm abun baa cewa
komai domin bakaramin dadi yayi ba, juyewa tayi a katon jug yayinda tasaka a fridge
danya dauki sanyi, "wata tukunyar takara daukowa sassaken baure ta wanke tareda
zuba masa ruwa, kanunfari tasa maidan yawa tareda mazar'kwaila sai rake data yanka
kanana kanana nanta Dora gaba daya akan wuta yana dahuwa a'hankali yayinda suke
fira da bilki harya dahu babu abunda ke tashi sai kamshi Mai dadi nan yayi duhu
sosai har danko danko yakeyi gashi yayi kauri, saida tabari yasha iska sannan ta
tace inda ta dauko Karamar robar ruwan zamzam ta bude tareda juyewa a ciki, fridge
shima ta saka, Yar'shilan kazarta ta dauko shima farfesun hadin ridi da nonan
rakumi tayi inda tana gamawa ta juye a plate suka koma parlor abunda ta yini ci
kenan yinin ranan hmmmm kafun yamma kuwa🤪baa magana abun sai Wanda yagani🙈har
tsoran yanda ta dinga naso takeyi inda bilki taimata hadin dilka taita gurje mata
ilahirin jikinta, gashin kanta ma baa barshi a baya ba, yini sukayi cur suna Abu
daya inda Aisha kejin kanta babu abunda wata amaryar zata nuna mata a'yau sai
wurin karfe shida ta shiga wanka yayinda ruwan wankan nata yasha hade haden
hadaddun turare masu sirrin kamshi harda hadin ruwan lalle a ciki, sabulun kanshi
hadi na musamman yasha lokaci ta dauka sosai inda ta dinga durza fatarta kamar zata
chanza brush kuwa saida takusa kararda macline din bayin, oooh su Aisha abun nema
yasamu🤣 tana gama wankan bilki ta miko mata kaskon turaran tsugunne wanda magic
chacole ne ta kunna kasancewar babu garwashi a gidan botikin fenti tasaka kaskon a
ciki inda bilki ta zuba mata garin turaren tsugune na mai'duguri Mai matukar kamshi
zama tayi akan bokitin inda akasa bargo aka rufe ta dumi na ratsa duk wani lungu na
jikinta tanayi tanashan hadin tsumin datayi saida takusa minti Ashirin akai sannan
ta Mike inda bilki tagama turara mata wasu hadaddun fitinannun kananan kaya tareda
rigar baccin dazatasa anjima harta pantis dinda zatasa saida aka turara mata da
kumasa shi kanshi pant din aka diga mishi turaran miski Mai matukar kamshi nanta
zauna ta tsara Kwalliya inda kowani lungu na jikinta da kalar turaran da aka shafa
mishi, bilk kuwa tana ihu harta hango yanda Ak zaiyi kukan Agwagwa🦆 Sai zuzuta
Kyau da Aisha tayi take, sanye takeda Purple slik short gown Mara hannu Mai
budadden kirji kadan ya saukan mata kugu kyawawan cinyoyinta sai kyalli sukeyi
gashin nan yasha gyara shima an kamashi da karamin ribom Mai kyau ya sauka ta baya
lips dinnan sai kyalli yakeyi ba janbaki tasa ba man baki tasa Mai matukar kyau
dadan ratsin pink pink a ciki, hmmmmm fadin haduwar da Eeshar Ak tayi baa magana,
sai wuraran karfe takwas saura na dare Ak ya shigo kasancewar Daddy yasashi wani
aiki shiyasa bai shigo da wuri ba Wanda dama hakan su Aisha sukeso yanda zasu
shirya a hankali, tun daga bakin gate yakejin wani masifar kamshi na tashi a cikin
gidan nashi hakan yasa sauri sauri yakarasa cikin gidan idan yana bude kofa Aisha
tafito daga daki cikin takunta na kasaita sai juya jikinta take a natse kugun nan
kam hmmm baa magana, ledar dake rike a hannun shiya sake Wanda takeaway ne yaimusu
da gasssar kaza, da hanzari ya rungume Matar tashi yana ihu, wowww African Beauty I
can't believe this Angle is my wife, dagata yayi yana jujjuya parlon da ita
batareda bata lokaci ba yahada bakinsu tare shan bakinta yakeyi cikin kwarewa da
zalama kamshinta dukya rikitashi yagama fita hayyacin shi, bilki ceta fito ganinsu
a haka kunya taji inda take musu sallama Aisha ce take kokarin kwatar jikinta
ganin zuwan bilkin gogan kuwa baimasan duniyar dayake ciki ba sai kankame matarsa
yake karayi, 'Dakyar ta kwata kanta a jikinshi, Hubby bilki nanan fa please ka
tsaya, oooh Eeasha wacece bilki kuma? Yafadi with his red eyes sai lumshesu yakeyi,
"Ni bilki zan wuce saida safe sabon Ango, " kallonta AK yayi shi wlh yama manta
wata bilki, oooh dama baki tafi ba Ashe, toh saida safe mai'gadi zai kaiki gida mun
gide....."aa Mai gadi kuma? Tafadi tana dariyar yanda ya rikice, "ooh Ina nufin
saida safe yafadi tareda Jan matarshi zasu shiga daki Aisha na turjewa duk kunyar
kanwarta takeji, " meye haka Eeasha mijin ki yadawo ko ruwa kya bani, "but Yaya
kabari muyi sallama da ita mana, look banasan musu tayi miki uziri mana yinwa
nakeji muje ki zuba mun abinci, but Kabar ledar a parlor ai....datse kofar bedroom
dinshi yayi batareda bata lokaci ba ya cigaba da abunda yakeyi Eeasha kinyi masifar
kyau am going insane kamshinki zai kasheni, abunda yake furtawa kenan biki kuwa
tafa hannu takeyi kunya dukta isheta tama kasa magana tsallake ledar da Ak ya zubar
tayi inda taja musu kofar parlon su tareda Alkawarin bazata kara kaiwa dare a gidan
yayar tataba daga yau bare taga abun kunya taga alamar Ak baisan wata kunya ba.

Dakyar Ak ya sararama Aisha yayinda ta zuba mishi abinci yadan tsakura sai hadin
dabinon data wuni sha ta zuba masa nan yaita zuba santi, a'daddafe dakyar yabari
karfe goma yayi inda ya watsa ruwa sama sama cikin kayan Bcci milk color riga da
wando Aisha kuwa tsoro yagama rufeta ganin haukan da Ak ketayi tun ba'aje ko'inaba
yagama rikicewa ita kanta a takure take tana bukatar mijinta hakan yasa takasa ko
motsin kirki inda ya shigo batareda bata lokaci ba ya rage hasken wutan dakin
yayinda ya kunna na Bcci, 'Hubby tun yanzu zamu kwanta? 11 fa muke Bcci, 'karki
damu yau dawuri zamu kwanta Bcci nakeji toh Bari inje in chanza kaya, tafadi jiki
na rawa harta kai bakin kofa tana shirin budewa, 'my Eeasha basaikin wani chanza
kaya ba please kizo, 'waigowa tayi cikeda fargaba, yanzu zan dawo Ina zuwa tana
fita ko tsakiyar parlon bata kaiba taji anyi sama da ita, Daukarta yayi batareda
Yaji nauyin taba, "naga saiwani jamin aji kikeyi kinaso ki manna mun hauka, yafadi
tareda direta a'tsakiyar Gado inda yaimata rumfa da faffadar kirjin shi ya shiga
aika mata da zafafan sakonnin da suka fara kwance mata da dukwani tunaninta a
duniyarta dukansu bakaramin fita hayyacinsu sukayi ba Ak kuwa tun ba'aje ko'ina ba
tunda yafara sarrafa jikin Aisha ya dinga ihu kadan kadan kusan awa daya suna buga
hot romance a lokacin da zaka tambayesu sunayan su tabbas bazasu Iya tunawa ba,
ganin abun bamai karewa bane yasa na lallaba tareda barin musu dakin da sai nishi
sukeyi duk kunya ma tagama cikani wlh🙈, parlor nakoma na zuba tagumi inaso Inga
abunda zai turema buzu nadi batareda bata lokaci ba naji Ak na salati Wanda saida
ya furgitani, "Innaa...lillahi, ya salam, Wyyooo Mamie na, Aisha Aiiiiishaaa meye
haka?
Meye haka Aisha? " ita kuwa kuka kawai takeyi harda magiya tun muryarta na fita
cikin tashin hankali harna daina jinta...........
"Zaki kasheni Aisha,
Ihu yakeyi sai kiran sunan Aisha yakeyi kamar Wanda zaa zarema rai😕nifa sunsani a
tsaka Mai wuya kamarya zata kashe shi? Damai zata kashe shi?🙁

*Mr's Saddiq Rumah💅🏻*


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie*

*Kuyi hakuri kwana biyu kun jini shiru, wlh Hidima namun yawa da weekend ne shiyasa
but karku damu askin yazo gaban goshi insha Allah.*
*Dedicated to sister Husna*

41

Ba karamin rikicewa Ak yayi ba inda ya dinga kiran sunan Allah sai misalin dayan
dare yasamu natsuwa inda ya kwanta gefe yana maida numfashin gajiya yama rasa
abunyi yarasa tunanin dazaiyi cikin kankanin lokaci zazzabi Mai zafin gaske ya rufe
shi inda yajawo Aisha jikinshi A ranshi kuwa zuba mata Addu'a kawai yakeyi yama
rasa bakin magana, rufesu yayi da bargo yanda yakejin kanshi ko wutan dakin bazai
Iya kunnawa ba saboda Mazarin da jikinshi keyi kafun lokaci kadan Bcci yayi gaba
dashi sai munshari yake bugawa yayinda ya kankame jikin Aisha yana sauke ajiyar
zuci tuni Bcci yayi gaba dashi kiran sallar Asuban farko yatashi sakamakon nishin
da Aisha ke fitarwa na wahala Wanda yakeji sama sama a kunnan shi da hanzari ya
Mike tareda kunna wutan dakin da gudu ya karasa wurinta ya shiga jijjigata, "na
shiga uku my Eeasha subhanallah, rungumeta yayi kam jikinsa dake rawa da zafi yana
kuka kamar karamin yaro sai hakuri yake bata, "bana cikin natsuwata har yanzu
nakasa tuno komai kaina ya kulle am a very bad parson Aisha ki yafema mijinki na
cuceki, kwance take a jikinshi sai lumshe idon wahala takeyi tana jin maganar nashi
sama sama, " I can't believe u r still a vargin wowww my Eeasha a vargin that's my
dreams coming true yah rabbi yah Allah Kaine Mai maida Impossible To be possible am
confused, sumbatu ya cigaba dayi yana kuka daka ganshi baya cikin natsuwar sa inda
lokaci daya ya jawo wayarsa dake bedside dukda haka kan Aisha na rungume a jikinshi
sai faman lailaya mata yakeyi yana hawaye likitan shi yakira cikin daran inda wayar
taita Kara tana katsewa har kusan sau biyar harya gama cire ran zaa amsa wayar
yafara tunanin kodai Mamie zai kira tazo ta dawo mishi da Eeashar sa daidai? Muryar
doc dince ta katse shi cikin magagin Bcci, "Doc wlh she is a vargin and I hurt her
soo badly ooh how can I be soo stupid nayi zargin innocent jewel Dina, oooh Allah
na shiga uku please ya zanyi idonta a lumshe yake tun dazu tana nishi help me
please my wife is in pain and becox of my stupidity why? How comes? She is a vargin
wlh wlh Nina fara saninta I can't believe what am seeing......." Carm down Sir
please ka kwantar da hankalinka sir kaimun bayani yanda zan gane and who is a
vargin? Tsawa Ak ya daka mishi kamar zai fasa wayar, "Who Else if not my wife u
stupid Moran malam just tell me abunda zanyi banasan gulma, " sorry sir, taimaka
mata zakayi ka gasa mata jikinta sannan ka kimtsa ta kakawo mana ita asibiti zanma
likitan mata bayani zaai mata duk abunda yadace, "shikenan abunda zanyi? Ya tambaya
murya na rawa
" yes sir shikenan kafun inzo anjima....dif ya katse wayar shi tareda jifa da ita
nan ya Mike cikin kwarin jiki ya shiga yin duk abunda likitan yasashi, yanayi
dukkansu suna kwallar azaba Aisha nayin hawayan radadin zafin datake ji shikuma
yanayin hawayan radadin zafin dayasata tareda Dana sanin duk abunda yaimata a baya
yafi kowa sanin matarshi shiya fara budeta koda cikin hauka yake yasan ayau shiya
amshe budurcin Aisha, nan yaita rasgar kuka harda majina yana rokonta gafara yana
mata wanka itako Aisha idonta a lumshe yake ta kanta takeyi, Cikin kankanin lokaci
ya kaita asibiti inda batareda wani bayani ba aka Amshe ta sanin zuwan nasu kai
tsaye Aka fara bata kulawar daya dace inda Ak ya karata yanda yaje mata batareda
sanin budurwa bace yadauka inrinsu leemah ne zuruf zai shige🤣, sai safa da marwa
yakeyi hannu duka biyu akai dagashi sai dogon wando da farar singlate duk Wanda
yazo wucewa saiya kalle shi ganin yanda yake rasgar kuka kamar tsohon bayairabe
inda wani likita yazo gilmawa harya wuce yadawo tareda dafa kafadar Ak ganin yanda
babban saurayi ke hawaye, sannu bawan Allah Dan Allah ka kwantar da hankalinka irin
wannan kuka saikace ba namiji ba? Da alama madam na labour ne Addu'a zakai mata ba
kuka ba Allah ya raba lafiya, "kallon mutumin yakeyi ji yakeyi kamar ya watsa masa
mari kozai huce takaici, shi kanshi likitan ganin irin kallon da Ak yake masa shiya
sa yawuce da sauri kada ya
huce a kanshi.
Aisha kuwa bakaramin wahala Tasha ba inda likitan dake dubata tayi masifa da fada
sai kumfar baki takeyi bakaramin haushin Ak takeji ba wannan ai rashin hankali ne
ko makaho ne bai kamata yasa miki karfi haka ba ko kinmai gardama ne? Ta tambayi
Aishar da batada niyyar bata amsa, dakin hutu aka kaita tareda Kara mata ledan
ruwa da alluran Bcci.

Kafun gari yawaye harya kirasu Mamie dasu bilki yan'uwa yaita kira Eeashar sana
Asibiti priceless Jewel batada lafiya batareda tunanin dalilin dazai gaya musu ba,
aikuwa nansu Mamie da brother Hakeem sukazo harda bilki wacce Hakeem yacema Mamie
su biya su dauko ta Ramata kuwa cewa tayi basai taxo ba Adduar ta ya wadatar
batareda bata lokaci ba Mamie ta tambayi abunda yasamu Aishar Ak kuwa da gaskiar
shi yake shirin yima Mamie dalla dalla inda bilki ta farga tayi saurin katse
shi,........" Wlh maleria ne yasata gaba jiya danaxo haka na barta jikin sai a
hankali Ashe jikin nata yayi tsanani bayan tafiyata, "Adduar samun sauki sukai mata
inda bilkin tayi hakan ne saboda surutun da mamakin da zaai shekara uku da Aure sai
a lokacin ma'auratan suka San junansu it will look somehow, "Ammah bro duk ciwon
sister neya rikitaka kazo asibiti babu ko riga? Sai a lokacin Ak ya kalla jikinshi
inda kunya tagama kamashi yiyinda Mamie ta kalleshi tana girgiza kanta, " Allah ya
shirya ka Ak dannaga alama kana gafda fara hauka, wucewa dakin da Aisha ke bccin
hutu tayi bilki kuwa sanin Abunda yafaru da yayar tata bakaramin tausaya mata tayi
ba inda suka koma gefe daya itada hakeem sai fira sukeyi kallo daya zakai musu ka
faminci zallar soyyah a idonsu, "hmmmm wata sabuwa da Alama jinin buzaye yagama
mallake
👯🏼‍

♀ gidan Alhaji Muktar‍♀

Mota Ak yakoma inda yakira PA dinshi tareda shaida masa yataho masa da sabuwar riga
yana asibiti yazo kuma zai Aikeshi wani wuri.

Takarda ya zaro da biro a jikin motarshi inda yafara rubutu kamar haka.

*Ni Abdulkareem Muktar na saki Munafuka makira muguwa Shegiya macucuya Kuma
Azzaluma Halima Mai fuska biyu, Saki uku nida ita har abada Kuma Allah ya isa
tagama dani Bankuma yafe ba.*

Nade takardar yayi inda abubuwa suka dinga dawo masa dai'dai cikin lokaci kadan
naga ya yaga takaddar tunowa dayayi da darajar malam liman a wurinsa nagartaccen
dattijo Wanda baida kwadayin duniya da abunda ke cikinta idan banda haka saiyayi
sha'ria da halima saboda tagama masa rami a rayuwa Amma ya dauki hakan a matsayin
jarabawa tareda hakkin Aisha,
Wata takaddar ya dauko inda yakara rubutu kamar haka.

*N Abdulkariem na datse dukkan igiyar Auren dake tsakanina da halima na saketa saki
uku a dalilin cin amanar Aurena datayi.*

Mikama PA dinshi yayi tareda bashi izinin kaiwa gidansu leemah inda saida Aisha
tayi kusan sati daya a asibiti gatan duniyar nan ta ganshi a wurin Ak makale mata
soyyah kuwa hmmm kamar ya kashe kanshi bakaramin soyyah suke sha'ba hakuri kuwa ta
sha'shi inda yaita mamakin yanda yasameta a vargin nanta warware masa komai Addua
sukaita ma ya'u inda ya kudiri aniyar duk Wanda yakara jin yakira matarshi da
makamancin sunan Ustaziya ko Yar'duniya kowaye kuwa saiyayi sha'ria dashi kuma zai
fito ya nunama duniya shikadai ne namijin dayasan ta sai inda karfin shi yakare
akan hakan, koda aka sallami Aisha Kyautar 1st 9yt dinta na musamman na jiranta
inda yasai musu dankareriyar motoci guda biyu hadaddu shida ita na Aisha fara tas a
cewarsa saboda rayuwar shida ta haska shiyasa yaimata kyautar farin mota, tashi
kuma milk color inda ya biya musu kujerar hajji itada family ta gaba daya su
garbati Mai rake za'a zama Alhaji a cewarsa it is the little he can do ganin baida
wata hanyar faranta mata zai cigaba da wanke mata bakincikin daya dasa mata da
karfin shi dakuma dukiyar shi koda zai zauna baida ko'sisi a duniya zai kararda
komai akan Priceless Jewel dinshi tattali na musamman yake bata kamar zai maidata
cikin shi.

Halima saida takusan kwasan wata daya sannan aka sallameta tayi baki tarame ta kode
saikace Mai ciwon kanja'mau inda tun kafun akai ko'ina tayi nadama matuka iyayanta
gaba daya basa bin ta kanta inda mamarta bata amsa koda gaisuwar ta ko kallon inda
take batayi malam liman kuwa kullum cikin wa'azi yake mata a cewarsa hannunka bazai
rube ba ka yanke dukda abun namasa ciwo Amma bazai bar sanrai yasa yayi aikin
jahilci ba, gaba daya aikin gidan ita keyi babu yanda malam bai lallashi mama akan
ta dinga sassauta mata ba hakan yasa Maman ta tattara halima da malam din dukansu
ta watsar a cewarta da tanada wurin zuwa babu abunda zaisa ta zauna gida daya da
halima taga Alamar malam dinne ke daure mata gindi Inda kullum halima na kunshe a
daki kamar daddawa duniya tamata zafi danma Allah ya taimake ta cikin baya bata
wahala ko kofar gida tayi Alkawarin bata Kara fita koda malam yabata takardar
sakinda Ak ya aiko mata ranan tawuni kuka kamar ranta zai fita ganin yanda tacuci
kanta da rayuwarta Allah yamata gata babu abunda tarasa San zuciya yasa tama Allah
butulci Ina ranar bariki? Duk ribar da mutum zai samu a bariki na lokaci kadan ne
yayinda zai karasa sauran Rayuwarsa cikeda nadama wacce batada amfani tanaji tana
gani tayi asarar nagartaccen miji har abada, mahuta kuwa bishasha kawai yake zubawa
inda neman mantan shiya ninku saikace Wanda akaima baki kowace kareda doki binta
yakeyi abun yazama mishi jaraba saidai muce Allah ya kyauta yakuma hanemu da aikin
danasani Mara amfani.

Aisha fa tama rasa bakin godiya saidai hawayen farinciki ganin yanda mijinta ke
rurutata takara godema Allah daya tsare mata budurcin ta tabbas duk macen datayi
asarar budurcinta a titi wlh wlh tayi asarar babban farinciki da kwanciyar hankali
a gidan auranta bawata daraja da zatayi matukar Mijin yagane duk sanda yake miki
babu inda auranku zekai koma Auran yayi tasiri wlh sai an samu zargi tareda wasi
wasi a zaman.

"Misalin karfe goma na dare Ana sati daya daidai da daran 1st 9yt dinsu bayan
tagama kimtsawa tadau wanka sai kamshi takeyi kamar koda yaushe wayarta ce tayi
Kara *King of hrt* shine sunanda yafito baro baro akan fuskar wayar tata batareda
bata lokaci ba ta amsa tana faman zuba mishi kirari tana wasa Mijin nata kamar
yanda ta saba, sanar mata yayi ta sameshi dakin shi Wanda anan ne akayi
sha'galin😜 batareda bata lokaci ba dama a shirye take tunda yamma ta hada hadaddan
hadi na musamman, danyan zogale ta gyara da madarar pick na ruwa ta markada tareda
zuba masa Zuma Mai kyau akai shita wuni sha dukda baida dadi a baki Amma biyan
bukata yafi dogon buri, Alkawari tayi koda duk kwanan duniya Ak zai dinga karata
Ana dinketa Bazata taba guje ma shinfidar shiba, duk halinda take ciki Alkawari
tayi bazata taba hanashi kanta ba zata juri komai saboda king of hrt, she is Ever
Ready, yes a shirye take da faranta mishi koda hakan na nufin Ajalin ta, tana bude
kofar dakin sanye da hadaddun kayan Bcci red cikin takun kasaita yayinda take
mamakin abunda ya boye Mijin nata tun dazu bai makale mataba kamar yanda yasaba,
batasan sanda tasaki ihun dadi ba tsalle tayi tareda rungume mijin nata tarasa
awace duniya zata sakashi ganin yanda.............😜
Saimun
👯🏼‍

♀ hadu a next page Wanda zai zama second to the last insha Allah‍♀
*Mr's Saddiq Rumah💅🏻*
🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie.*

*Dedicated to Sister Husna*

42

Aka kawata dakin da rose flowers masu ban sha'awa na masoya saman gadon yasha red
bedsheet masu matukar kyau an zuba flowers jajaye gwanin ban sha'awa yayinda aka
watsa multicolors balam balam Mai hrt shape ta'koina har zuwa kasan dakin Wanda
ke dauke da karamin table dauke da madaidaicin Hadaddan red cake da rubutun,
*"Happy One week Anvasary"* tareda hotonsu a jiki Wanda ya matsa mata suka dauka
sanda take jinya a asibiti dukda babu Kwalliya fuskarta hoton yayi kyau sosai kanta
nakan kafadar shi yayinda shikuma yake kallon fuskarta daya tallabo da dayan hannun
sa gefe daya kuma Kwalbar Hadaddan champagne ne tareda red glass cups dogaye guda
biyu, wani cool music ke tashi a hankali cikin wakan sanannan mawakin nan black
American "Akon a wakarshi Mai taken " Am so lonely " cikin sauti Mai natsuwa da
ratsa jiki "bin dakin tayi da kallo inda lokaci daya ya sunkuce ta tareda direta
tsakiyar gadon dayasha gyara sai dariya sukeyi yana mata chakulkuli saida suka
dauki minti biyar sannan ya dakata yayinda ta kalleshi cikeda mamaki, "king of hrt
wai yaushe kayi duk wadannan abun? And na menene? Bakinsu ya hada wuri daya yana
bata wani irin sako Mai wuyar fassara saida suka dawo hankalin su sannan ya rike
hannun ta har zuwa wurin cake din tareda mika mata yar'karamar wuka red, "
bismillah nakosa inci cake dinnan dear feed ur hubby please, "but cake din mainene?
Na Anvasary din sati daya da first 9yt dinmu ne idan zaki tuna tundaga ranan bamu
Kara kwana a dakin nan ba saidai inbiki dakinki saboda jinyar da kikeyi, "
tugunnawa yayi a gabanta kamar karamin yaro sanye yakeda wando 3quater fari tareda
red armless riga Mai daukeda rubutun, *Give me Another special place in ur hrt* a
gaban rigar Wanda rubutun ya kasance fari, "shiyasa a karona biyu nakara gayyatarki
dakina Wanda banaso ki dinga tunowa da komai sai ire iren abubuwannan just our
happy moments, Mr's Abdulkareem congratulations because am All urs sai yanda kikai
dani babu boka ba malam kin gama mallakeni yanzu dai ki ciyarda mijinki, yafadi
yana chuno mata baki, Cikin wata sabuwar duniyar farinciki ta Lula yayinda ta yanka
cake din Wanda ya kasance chocolate and red velvet cake sai hadiye miyau takeyi
tareda gutsoro madaidaici tana shirin dorawa akan karamin Tea plate ta hango wani
Jan Abu namata kyalli tacikin cake din, hannu tasa tareda turawa tsakiyar cake din
dauko Hadaddan karamin case ne Mai kamada gidan dan'kunne tana budewa tayi ido biyu
da kyawawan zobuna guda biyu sai kyalli sukeyi tareda daukar ido na mace Dana miji
cikeda mamaki ta maida kallon ta ga AK Wanda ya kashe mata ido daya yana zuba
murmushi, Rike hannunta na dama yayi tareda Amsar zoben ya zaro na macen Dan siriri
Mara hayaniya saika saka ido sosai a zoben zakaga Harafin A&A Wanda aka rubuta da
ruwan gold, yatsar hannunta na biyu ya rike inda ya kalleta with a serious look, "
My Eeasha I know I made a mistake a baya banyi Alkawarin bazan Kara bata miki raiba
Amma nayi miki Alkawarin hawayan idonki bazai Kara zuba ba a dalilina namiki
Alkawarin duk hawayan dazai fito idonki a gidana insha Allah zanyi iyakan kokarina
Inga ya kasance na farinciki sannan zanyi iyakan kokarina wurin faranta miki da
dukkan Abunda nake dashi, kasancewar bikin mu baayi wani shagalin da zamu dinga
tunowa dashi ba kasancewar abubuwan da suka faru ada cikin rashin Sani shiyasa na
hada miki yar'karamar dinner nidake a dakinmu Mai tarin tarihi da farinciki inaso
ki manta da abunda yafaru a baya ki rike ranar yau a zuciyarki wacce Ranar yaune
zai zama Ranar da zamu dinga Celebration akai, My wife, please kikara bani dama a
karona biyu insake taka rawa a rayuwar ki, zura mata zoben yayi a tsintsiyar hannun
ta Wanda ba karamin kyau yayi mata ba yayinda ya rike hannun tareda sumbatar shi, a
daran masoyan sun Kara lulawa sabuwar duniyar ma'aurata Mai tarin natuwa tareda
tsayawa a'rai saidai muce Asuba tagari Eeashar AK💃🏽.

*Bayan wata Shida.*

Leemah ce keta mutsu mutsu gwanin ban tausayi dukta bushe ta jeme tayi baki tarame
ga uban ciki, tun tana daurewa tana nishi da kuka kasa kasa harta galabaita ita
kadai a daki da Alama nakuda takeyi bakaramin wahala tasha ba taci kuka harta gode
Allah yayinda mama batasan Abunda ke faruwa ba kasancewar bata shiga harkarta gaba
daya, Addua takeyi Allah ya dauki ranta kozata huta da azabar da take ciki inda
takasa jurewa ta kwallama Maman kira cikin kukan azaba tana rokon yafiyar iyayan
nata tareda nadamar abunda ta aikata, cikin hanzari mamar ta karasa dakin saida ta
tausayama halinda taga diyar tata bakaramin azaba take sha'ba, wurin malam ta
garzaya tareda amso rubutun nakuda Wanda yadade a ajiye, dakyar tasamu halima yasha
kadan saboda tanasha tana dawoda rubutun ne ganin anata Abu daya har yanzu babu
Alamar haihuwa hakan yasa malam ya dauko shatan keke napep aka sakata a ciki
batasan inda kanta yakeba Allah ya taimaka unguwar babu mutane a lokacin babu Wanda
ya farga da abunda ke faruwa, cikin ikon Allah Ana gafda isa asibitin halima tasaki
wani uban ihu Wanda harta Mai napep din saida ya tsorata batareda bata lokaci ba
Ashe yaron ne yayi mugun karata inda jariri ya sumbulo kasa salati mama tasaki
ganin kashi jaga jaga a wurin da gudu likitoci suka karasa tareda gadon daukan Mara
lafiya duk mai imanin dake wurin saida ya zubar mata da hawaye sakamakon karantan
da jaririn yayi harya shafan mata wurin kashi,kai tsaye dakin tiyata akayi hanzarin
shiga da ita inda mama keta kukan tausayin diyar tata bata taba ganin Abu irin
wannan ba, katotuwar baby gal ta Haifa kyakyawan gaske Mai kamada ubanta sak kamar
mahuta yayi kaki saidai bbyn farace tas, anyi ankin cikeda nasara saidai Halima
tasamu larurar yoyan fitsari inda sai a hankali A hankali zata warke tareda
shawarwari masu kyau daga likitoci hakan yasa suke zaune a asibitin tana jinya inda
Malam yace tana samun sauki zataje Kano ta karasa jinyar gidan babban wanta saboda
gudun surutun jama'a wadanda basuda gadonka Amma sunada gadon maganarka, Allah
sarki halima bakaramin nadama tayi ba kullum batada aiki sai neman yafiyar iyayanta
da Ubangiji a cewarta sakamakon zinar datayi ne take girba tun ba'aje ko'ina ba.

Mahuta uban duniya shida yammatan shi su meenah da finah kuwa kowa shagalinsa
yakeyi suna holewa inda baa iyakar junansu kawai suka tsaya ba duk Wanda ya taya
saisun bashi yammatan biyu kuwa meenah da feenah likafa ta cigaba domin yanzu har
lesbianism sukeyi "Subhanallah" hakan yasa lokaci daya kuraje masu matukar wari da
uban kaikayi suka Addabe suda wari da kaikayi tun abun nayi kadan kadan harya fara
wuce hankali idan suka fara Susan jikinsu har saisun jima kansu ciwo ko'a gaban
waye kuwa idan yafara musu saisun Sosa hakan yasa abokan iskancin nasu suka fara
guduwa ganin yanda warin ke damunsu ga kurajan sun fara rashewa saboda uban Susan
da sukesha hakan yasa meenah da feenah zuwa asibiti domin ganin wani kwararan
likita ganin yanda ki Bcci sun daina samu saboda azabar susa su kansu warin jikinsu
damunsu yakeyi, gwajin farko aka shaida musu dukansu su biyun suna daukeda cutar
ciwon sanyi tareda hepatitis wacce tayi mugun tasiri a jikinsu bugu da Kari ga
Infection daya mamaye su, fadin irin tashin hankalin da suka shiga bata baki ne
atake akaba kowacce Gado inda suka fara Amsar kulawar da batada amfani sai uban
kudi da suke kashewa, ganin abun bana karewa bane yasa suka sanarda mahuta saboda
kudin hannunsu kaf yakare a magani da kudin asibiti inda batareda bata lokaci ba
yazo ganin halinda suke ciki yama fisu shiga tashin hankali baiyi kasa a guiwa ba a
lokacin yaje domin tantance jininsa cikeda tashin hankali da Adduar Allah ya
kubutar dashi, "hmm su mahuta kenan Ashe ka Iya Add'ua, ya manta da Ubangijin sa
na lokaci Mai tsawo ganin yana cikin tsanani shiyasa ya tuna Allah Wanda shi Allah
ba'a masa wayau da dabara gwajin farko aka sanar dashi ya kira iyayansa domin bazaa
Iya nuna masa sakamakon gwajin nashi ba saida wani babban jigon shi,babu yanda
baiyi ba Kiri Kiri likitan yace saiya kira wani na jikinsa Babba, ganin babu mafita
yasa yakira sanata da mommy inda cikeda tashin hankali suka karaso asibitin tareda
uban bodyguard sai jiniya ke tashi a asibitin saikace shugaban kasa ne yazo, ganin
result din kai tsaye sanata ya yanke jiki ya fadi Wanda hakan yayi sanadiyyar
shanyewar barin dama na jikinsa gaba daya mommy ma baa barta a baya ba saida ta
suma inda mahuta ke tsaye kamar mutum mutumi yakasa ko motsi sai hawayan dake bin
idonshi.

Awani madaidaicin gida na Hango Hajiya Ramata da Alhaji Garbati Wanda ake shirin
Auransa nanda wata biyu masu zuwa inda Ak yajashi jikinshi sosai tareda dorashi a
wani sashi na kasuwancin shi, Alhmdlh kuma Garbati ya shiga da kafar dama
kasancewar samai rikon gskia da amana inda AK ya siyan musu karamin gida Mai
matukar kyau tareda daki hudu da sunan Aisha anan gaban unguwansu kadan inda dakyar
suka koma saida Aishar tasa baki sannan dakyar Ramata ta yarda inda AK ya biyama
Mai'unguwa kujerar umara adalilin Adalcin sa uwa uba shine Wanda yafara masu
Eeashar sa sutura a garin Kaduna Wanda yabaka muhallin zama fiyeda shekaru masu
yawa bakaramin masoyin ka bane kuma uwa uba mutumin bai taba goranta maka ba, Murna
wurin mai'unguwa baa magana ganin shima yanzu za'a fara kiransa da Alhaji
mai'unguwa matsayi akan matsayi inda Aisha bataje hajji ba sakamakon yanayin da
take ciki a yanzu Mamie ce taje a madadin Aishar.
Aisha nagani zaune a kujerar parlor tareda katotan ciki a gabanta ta kumbura
hancin nan yayi double fuskarta ya ciko sosai kafanta nakan cinyar AK Wanda keta
tsokanarta yana kiranta da sabon sunanta " Orobo Maman iyabo"kukan sha'gwaba take
masa tareda Alkawarin zata gayama mamien ta

*Mr's Saddiq Rumah*💅🏻


🏼🏼🏼
🧕🏼 🧕🏼 🧕🏼
‍♀‍♀ *Ustaziya ko Yar'duniya?‍♀‍♀ 🤷🏻‍🤷🏻‍🤷 🏻‍
♀*

*Written by Anty Mamie.*

*His Smile😌OMG, paradise💞 Alhmdlh for having u in my life, u are a great


blessing from Allah SWA. I want you in my arm's, in my drmz, in Reality and in
fantasy, U have Always been supportive My dearest hubby may Allah protect,👏🏻
Bless,👏🏻 Guide👏🏻 and prolong ur life for us👏🏻MAI'NI.*

*Dedicated to sister Husna.*

43

*END*

Shirye shiryen bikin Auta bilki akeyi babu sassauci tareda Angonta Abdulhakeem inda
babu Wanda yakai Alhaji Muktar farinciki Mamie kuwa bakinta yaki rufuwa da murnar
samun Nagartttun sirikai mata daga gidan mutunci marasa San abun duniya inda Hajiya
Aisha tafi kowa murnar ganin yar'uwarta kuma kanwarta Kawarta sannan Aminiyar ta
wacce batada kamarta zata Aura kanin mijinta inda taita godema Allah hidima akeyi
bana wasa ba, Lefen leemah da Ak yayi Shiya kai aka chanza masa wasu daga cikin
kayan tareda Kara masa da sababbin yayi inda aka chanza duka setin Akwatin
kasancewar a wurin Abokin kasuwancin shi dama ya siya kayan ba'a wani sha wahalar
gyara Lefen ba, Kaninshi yaba gaba daya kayan a cewarsa shine gudunmawar sa na
bikin Hmm zokaga murna da gulma a unguwa masu kishi nayi masu bakin ciki nayi wasu
har'cewa sukeyi asiri su Ramata sukayi saboda mallake iyalan Gidan Alhaji Muktar
inda munafukai suka fara kananan maganganu irinsu Virus harda tunoda rayuwar Aisha
nabaya, Ak baiyi kasa a guiwa ba inda aka tasa keyar virus magarkama a dalilin
batancin sunan daya dade yanama su Aisha wasa wasa maganar saida taje kotu inda
dama burin Ak kenan yanaso ya wanke Matarshi da marigayi sirikinshi daga karshe da
wuya yayi wuya Virus ya warware duk kullin dayayi ma Aishar harda sharrin dayayi
akan yaga ya'u da diyarsa na zina harda niyyan fyaden da sukaso yima Aisha Allah
bai basu nasara ba, nan Ak ya bude Babban murya tareda shedama Duniya Matarshi
Tsarkakkiya ce shine namiji na farko kuma na karshe a rayuwar ta nan kotu ta wanke
Aisha tsaf daga zargin da ake mata, murna wurin Aisha kuwa baa magana Virus kuwa
Tara aka cishi tareda horo Mai tsanani na tsawon shekara uku a gidan yari saboda
samun shida laifuka masu yawa da akayi.

*A'gurguje*
*Bayan shekara Goma.*

Shekara hudu kenan da Rasuwar mahuta inda ciwo Mai karya garkuwan jiki yayi
Ajalinsa wato *HIV* Wanda yasha jinya Mai tsawo cikeda nadama tun kafun ya rasu ya
nema Alfarmar Amso mishi yarinyar sa a hannun leemah wacce Malam Babba ke rikewa
yayinda leemah ta auri wani magidanci Mai mata uku itace cikon ta hudu ba laifi
yanada rufin asiri suna zaune a garin Kano tareda yaronta daya wanda yaci sunan
malam liman, Bakaramin soyyah iyayan mahuta kema Zainab ba diyar mahuta, saboda
tausayi da soyyar da sukema mahuta ganin yanda suka hanashi tarbiyyah harda sakacin
sune yakara jefa shi a rayuwar dayayi nadama ce sukayi Mara amfani domin mahuta
tuni ya rigamu gidan gskia saidai muce Allah ya gafarta masa mukuma ya kyautata
karshan mu👏🏻.

"Yammata ne guda biyu kyawawa babbar fara tas wacce bata Gaza shekara Goma ba Mai
suna Husna, sai Mai bimata chocolate color hartafi Babban kyau, Mai suna Rahma suna
cemata "Ummita" sai karamin namiji Wanda shine karamin su Wanda bazai Gaza shekara
hudu ba inda sunan Alhaji Muktar yaci suke cemasa "Calipha" babu Abunda ya bari na
ubansa kama yakeyi sak da Ak babu abunda ya bambanta su, Hajiya Aisha wacce tagama
zama babbar mace ceta fito daki sanye da doguwar riga baka yayinda take turo Dan
karamin bakinta hayaniyar yaran dukta isheta inda kai tsaye kitchen ta dosa a
dalilin kaurin dataji, sanye yakeda Apron ya zake sai game yakeyi da yaran a wata
katotuwar wayar shi yana biye musu sunata ihu duksun makalkale shi yayinda yake
zaune a doguwar kujerar kitchen din basa kojin kaurin da dake tash kai tsaye ta
kashe gas din Wanda tafashen nama ya Dora zai musu abincin dare kasancewar Aishar
bata iyayin girki saboda uban laulayin daya tasata a gaba inda Ak keyi duk sanda
yake gida kokuma ya dibesu suje restaurant kokuma gidan Mamie kona "second Grandma"
wato Ramata kamar yanda yaran kece mata, kwata kwata bai yarda da abincin yan aiki
ba dukda sunada su"Haba Haba 1st love duk kuncika gida da ihu bakwa kojin kaurin
naman da yake konewa katasa yaranka kun hanani Bcci, Shiru sukayi mata kamar
basusan da ita a wurin ba, " dear magana fa nakeyi ko baku ganni bane? "Sorry wife
mun jiki muna zuwa please bari mudan gama wurin nan, " Husna, ta kira sunan babbar
diyarta, "Yes mommy ta amsa batareda ta kalli mamar tata ba sai ihu sukeyi da
daddyn su ganin basuda lokacin tane kamar yanda suka saba mata hakan yasa itama
taimusu abunda tasaba, kwace wayar tayi dadan gudu gudu ta fita tsakar gida inda
gaba daya suka biyota suna ihu harda Daddyn su, Please mommy please mommy ki bamu
wyyooo mommy za'a cinyemu, Ak neya fadi cikin muryar magiya kamar yanda yaran keyi,
Damkarta sukayi suna ihu A'daidai lokacinda Mai gadi ya wangale gate din gidan wata
bakar hadaddiyar mota tashigo nan yaran suka fara tsallen murnar ganin motan kai
tsaye suka rungume bilki wacce takeda yara biyu a lokacin duk maza Mai aikinta ce
tafara fitoda manya mantan kulolin shake da abinci kala kala Wanda bilki ta tsara
domin yin dinner a gidan yayyin nasu itada iyalan gidanta gaba daya dama sunayin
haka jefi jefi saboda karuwar zumuncin nasu kai tsaye suka rankaya katafaran parlon
dake gidan inda Ak ke tsokanar Eeashar sa, " Maman yan hudu taka a hankali, harara
ta wurga masa, 'dayan ma yana kare? Gskia daga wannan zan huta....wlh baki isa ba,
duk shekara saikin sullubo mun kyawawa masu kamada ke idan har Allah ya bamu saikin
haifo mun yara Ashirin insha Allah, "Yeeeeaaaaahhh mommy zata Haifa yara ashirin
inji Calipha Wanda keta faman tsallan murna A tunanin shi cikin jikin Mommyn nasa
ne dauke da yara Ashirin, dariya akai tamasa inda " Aisha taketa faman hade rai
sanin yanda Ak ke kaunar yara ita kuma tana bukatar hutu, 'Gskia ni wlh hutawa
zanyi Yara ishirin inyi Yaya dasu? "Wlh koki haifo mun kokuma in nemo Mai haifo
mun, yafadi cikeda zolaya " Aiko baka isa ba indai akan haihuwa zakai mun kishiya
duk bayan wata Tara na yarda zan dinga sulluboma yara......."kai Mommy kowa ya fadi
duka yaran dake wurin harda iyayan suka furta suna zare ido tareda rike habar su,
"ku kyale mun Eeasha ta da gskiar ki dole kiyi kishin mijinki First love nayi miki
Alkawari daga ke babu wata dake kadai zan rayu insha Allah, " Yeeeeeaaaah gskia
mommy kin Iya zaben miji am so jealous, "Inji Husna tafadi tana cuno baki tareda
Dora kafadarta akan na Ak wai tana kishin mamarta, "kanta Aisha ta ture inda ta
Dora nata a kafadar Ak harda rikeshi da duka hannuwa biyu, " Ki kyale mun 1st love
Dina kowa ya nemo nashi, Allah ya barmu tare mutu ka raba insha Allah. Dariya aka
hauyi Ana tafi ganin yanda soyyar su kullin kekara zama sabuwa fil duk sanda zaka
gansu tabbas zakaga soyyar na Kara haihuwa shiyasa gidan nasu yake cikeda farinciki
da kwanciyar hankali.

*Alhamdulillah
🏼🤷🏻‍

♀ anan nakawo karshan littafi na ‍
Ustaziya ko Yar'duniya ♀
kuskuran danayi Allah ka yafemun👏🏻 Allah yasa mu Amfana da darasin dake ciki
tareda watsar da abunda ke akasin hakan.👏🏻*

*Godiya ta musamman ga masoyan littafin nan ustaziya fans group 1 har zuwa group 8,
tareda Anty Mamie's novel 1&2 da kuma Zama na amana Facebook,Kai da duk wani groups
dinda nake ciki Wanda lissafo su zai Iya kararmin da Alkalamina dama wadanda bana
ciki Ina mika tarin godiya Mai yawa Allah ya hada fuskokinmu da Alkairin sa.*

*Ina gaisheda kowace marubuciya bazan Iya kiran suna ba kowa tawace Wanda nasani
dama Wanda bansani ba Ina yinku sosai Allah yakara mana hadin kai*.👏🏻

*Bazance ga Randa zaku kuma jina ba, zaku Iya jina a'koda yaushe zakuma ku Iya jina
shiru ya danganta, Amma karku manta Ana tare🤝🏻totally😍*.

*Matar Saddiq ce.*

You might also like