You are on page 1of 71

[10/16, 8:01 PM] +234 816 616 9254: *_ALHINI_*

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*

1to2 ```Page```

kuka take kamar zata cire ranta, idanunta sun kad'a sunyi jawur saboda tsananin
kuka, fuskarta tayi face-face da hawaye, zaune take cikin d'akin kan tabarmar kaba,
jikinta wata atamface Riga da zani, simple da ganin atamfar kasan tad'an kwana biyu
saboda farin data d'an yi Alamar kod'ewa, sai wani madai-daicin hijabi data sanya,
shima dai dagani kasan ba sabo bane, amma kuma wankakke ne, duk kayan jikinta basu
tare da datti.

"Haba laraba kiyi ha'kuri ki daina kukan nan, sabi'u dai yariga ya mutu kuma kinsan
kukannan naki baze dawo dashiba, Addu'a kawai yanzu yake bu'kata daga gareki, ta
dafa kafad'arta kiyi hakuri dan Allah ki daina kukan nan.

Sai lokacin Balaraba ta kalli wacce keta faman rarrashinta tace "Haba indo dole
inyi kuka, kukan nan danike shi kad'ai ze ragemin rad'adi da ba'kin cikin danake
tartare dashi, (tacigaba da kukanta,)

Indo tana matu'kar tausayama halin da 'kawarta take ciki, itama wasu guntayen
hawaye ta zubar sannnan ta'kara matsaowa kusa da 'kawarta ta dafa kafadarta da
hannu guda,
gudan hannun kuma tana goge mata hawayen dake kwarara daga idonta, tace
"Tabbass nasan rabuwa da masoyi akwai ciwo, baranta kuma rabuwa ta har abada,
Amma dole kiyi ha'kuri ki d'auki wannan a matsayin jarabawa ce daga ubangiji.

Laraba ta fashe da wani sabon kuka, tace indo bazaki ta6a gane halin ba'kin cikin
danake cikiba, ki duba kiga irin soyayyar da muka shimfid'a nida Iro acikin
'kauyennan muna burge Kowa, amma lokaci guda ana saura sati d'aya bikinmu yaje
wanki rafi yafad'a ruwa sai dai gawarsa aka fiddo, tafashe da wani sabon kuka, indo
ma kukan take, amma hakan be hanata rarrashin 'kawar tata ba.

Cikin sheshshekar kuka tacigaba da cewa "yanzu kuma :yau an wayi gari sabi'u shima
ya mutu kamar yanda Iro ya mutu, wannan wane irin iftila'i ne yafad'amin.

Assalamu Alaikum, inna ce tashigo da sallama, indo ta amsa mata sannan tashigo
d'akin, ta cire ijabinta ta rataye kan 'kyauren d'akin sannan takai dubanta ga
Balaraba wacce taketa faman kuka indo kuma na rarrashinta wacce itama kallo d'aya
zakayimata Kazan kukan tayi.

Indo takai dubanta ga inna dake shirin zama kan kujera tace "lnna har kun dawo?
"Har na dawo indo ay anriga anrufoshi sai dai muyi mashi addu'ar samun rahamar
ubangiji, sabi'u kam yayi mutuwar ban mamaki, duk da ba mamaki cikin lamarin
ubangiji, amma mutane da dama sunce lafiya lao ya kwanta, kawai aka wayi gari ya
mutu, wasu siraran hawaye suka zubo daga idon inna dan tana tausayama tilon yarta,
wacce tayi rashin masoyi a karo na biyu.

Laraba ta fashe da wani irin kuka, ta taso daga inda take tafad'a jikin inna tana
kuka, "shikenan inna yanzu narasa sabi'u wayyo nashiga ukku, sabi'u miyasa kamin
haka saida kabari na sha'ku dakai sannan zaka tafi ka barni,
innalillahi,wa'inna,ilaihirraji'un, ta fad'a kawai sai ji sukayi tayi shiru ba
Alamar numfashi tattare da ita, duka jikinta ya saki
Nan inna tashiga wani irin rud'ani tana girgizata tana kiran sunanta, "fatima.....
Fatima innnalillahi nashiga ukku,
Indo dake tsaye hankalinta duk ya tashi tarasa inda zata sa kanta da gudu
tafita daga gidan tana neman taimako.

"Dan Allah Hashim ka taima mani kada ta mutu, wanda takira da hashim yace "wacece
zata mutu, bata bashi amsaba tacigaba da kuka tana cewa ka taimakeni, mutuwa
zatayi, dan Allah, da gudu takoma cikin gidan.

Har yanzu laraba na rungume jikin inna ba Alamar numfashi tattare da ita, inna kuma
sai kuka take tana kiran sunanta.

Da gudu hashimu yanufi gidan me gari ya aro baro,


Kofar gida ya ajiye baron, sannan yashigo gidan da taimakon, indo da lnna aka dora
Laraba kan baron, Hashim ne ke tura baron da gudu.

Lnna da indo suna biye dashi hankalinsu tashe suka nufi 'karamar asibitin dake
'kauyen.

Zee Elkaseem
Mmn khady
[10/16, 8:02 PM] +234 816 616 9254: *_ALHINI_*

```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*

3to4```Page```

Sannu Laraba sannnu kinji, kallo kawai take bin mutanen dake gurin dashi, idanunta
suka ciko da hawaye, Inna tasa gefen mayafinta tana goge mata.

Sai da musalin 'karfe biyar na yamma aka sallamesu daga asibiti, bayan 'karin ruwan
da aka sanya mata ya 'Kare,
Indo kuwa duk abinnan tana tare dasu sai gab da magrib inna ta umarceta data koma
gida kada anemeta,
haka ta wuce tana me tausayama halin da 'kawarta ta tsinci kanta.

Hashim kuwa tinda akaje asibitin yaketa hidima da Laraba dan kusan duk kud'in da
aka kashe shine yabiya, yana mutu'kar tausaya ma Laraba,

Shima sai lokacin yabar gidan yanama Laraba fatan samun lafiya, inna kuwa godiya
kawai take mashi dan ya taimakesu ba kad'anba, dan in baccin shi da batasan inda
zata samu kud'in da zata biya na magani da 'karin ruwan da akayima Laraba ba.

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

*_BAYAN SATI BIYU_*


Zaune take kan guntuwar tabarmar da aka shimfid'a kan shararren gidansu na 'kasa,
ta tasa kwanon abinci gabanta, ita bata ciba kuma bata maida ta rufe ba, ta zubama
abincin ido tana kallo, wasu zafafan hawaye suka zubo daga idonta, tasa hannu ta
goge.

"Yanzu Laraba bazaki cire damuwarnan daga cikin ranki ba, kiyi ha'kuri ki d'auki
kaddara, kin riga kinsan dukkan me rai mamacine, muma nan mutuwa jiranta muke ko
yau ko gobe ko jibi koma yanzu,
Dan Allah kisama ranki ruwan sanyi.

Wasu siraran hawaye suka zubo daga idanunta tace na ha'kura inna.... Na
ha'kura..... Ki tayani da addu'a Allah yayemin damuwar dake tattare dani.

Inna ta tausayama Laraba har cikin ranta, tace "Allah yaye maki Laraba, Allah sa
maki 'ha'kuri da dangana.

Tace Ameen tare da share hawayen dasuka zubo daga idanunta.

Da 'kyar inna ta rarrasheta taci abincin, Wanda taci be wuce loma hud'uba, dan ma
lnna ta matsa mata ta d'ora da fura rabin cup, sannan taji d'an 'karfi-'karfi.

Da sallama ya shigo gidan, ya dur'kusa har 'kasa ya gaida inna, cikin far'a ta Amsa
"Hashim kaine sannu da zuwa, ta d'auko wata guntuwar tabarma ta shimfid'a mashi ya
zauna, tunda ya shigo idanunshi na 'kan Laraba wacce duk tabi ta rame ta fita
hayyacinta,

Saida ta lura da yanda yake kallonta sannan tace mashi "ina wuni, ya amsa da
"Lafiya lao Laraba ya jikin naki?
"Da sauki, "Allah 'kara sauki, tace "Ameen.

Sannan ta tashi tanufi randa ta ebi ruwa cikin wani madai-daicin bokiti tashiga
kewaye dan tawatsama jikinta taji sanyi.

Tunda ta tashi yake binta da kallo, cikin zuciyarshi yana cewa


_"Na dad'e ina son Laraba dan dai wasu sun rigani ne yasa na ha'kura, amma yanzu
bazanyi sake da wannan damar ta wuceniba, 'kila dama rabonace shiyasa Allah ya
kashe lro da Sabi'u_.

Inna ce ta katse mashi tunani "Hashim ya mutanen gidan naku?, yayi saurin dawowa
daga dogon tunanin dayake yace "suna lafiya sunce agaisheku, daga gurin aike nake
nace bari in biyo inga jikin Laraba, inna taji dad'i har cikin ranta yanda Hashim
ke nuna kulawa ga 'yarta, tace "jiki Alhmdlh, yace "Allah 'kara sau'ki tace Ameen.

Nan dai suka 'dan ta6a fira kafin yayi mata sallama, ya ajiye wata ba'kar leda yace
"ga wannan aba Laraba, inna tace "a'a Hashim hada hidima kuma, yace "ba kome inna
Allah sauwa'ke nina wuce, tace to Angode Allah bada lada, yace Ameen.

Bayan fitarsa ne, Indo tashigo, lokacin Laraba tagama wanka tana shafa mai, inna na
Nuna mata abinda Hashim ya kawo mata, balangu ne lafiyayye hanta tafi yawa aciki,
sai 'kananan robar yourghut guda ukku,.

Bayan inna tafita waje, Indo ta kalli Laraba tace, "gsky Laraba Hashim yanada wata
manufa acikin ransa dangane dake, dan ni nasan ba a banza yake maki wannan hidimar
ba,
Laraba ta kalleta cike da nuna rashin sanin inda maganarta ta dosa, tace "Ban
ganeba wace manufa kuma? Indo tayi murmushi tace "gani nake kamar 'Hashim sonki
yake.. .
Wani mummuman Fad'uwar gaba Laraba taji, dan yanzu ko kad'an bataso taji an anbaci
kalmar wani na sonta.

Tace Dan Allah indo mubar wannan maganar Hashim ba sona yakeba, inajin kawai dai
yana tausayi na ne, amma babu wata soyayya dayakemin, murmushi kawai indo tayi, dan
bata so suna kace-nace da 'kawar tata.

Ranar dai indo ta d'ebema Laraba kewa dan fira suka sha sosai, har fita sukayi suka
d'an zaga gari,

Tinda suka fita mutane ketayima Laraba ta'axiyya, indo ce ke amsawa dan bata son
abinda ze daga hankalin 'kawar ta.

Sai bayan la'asar indo taraka Laraba har 'kofar gidansu saida taga shigewarta
sannan itama ta wuce gidansu.

Zee Elkaseem
Mmn khady
[10/16, 8:10 PM] +234 816 616 9254: [20/08 12:47 pm] 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

5⃣to6⃣```Page```

🖊Kwanaki sun ja lokaci na tafiya, yau an wayi gari sabi,u nada wata ukku da sati
biyu da rasuwa,
Alhmdulillahi Laraba ta saki jikinta, ba kamar da ba, kuma jikinta ya goge yayi
sumut,

6angaren Hashim kuwa kullum soyayyar Laraba 'kara ha66aka take acikin zuciyarsa,
har yakai da yakasa sukuni, hakan yasa ya yanke shawarar zuwa gidan yayarsa, ya
fad'a mata halin dayake ciki, kuma ya ro'keta taje gidansu Laraba ta gabatar dashi
amatsayin me neman Laraba da Aure.

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
Laraba ce tafito cikin shirinta, atamfa ce jikinta d'inkin doguwar riga, kalar
ruwan 'kasa duk da atamfar ba sabuwa bace amma ta masifar yimata kyau, abinka ga
farar mace, kowane kaya tasa kyau yakeyimata, wani 'karamin hijab ta sanya shima
'kalar ruwan 'kasa tayi kyau abinta, duk da ta taso 'kauye bazaka kalleta ka kirata
'yar 'kauyeba, saboda bata irin shigar nan da 'yan 'kauye keyi na zani daban riga
daban, ita tanasa kayanta complete, sannan kuma bata fiye sa gyale ba, yawanci
kullum zaka ganta da hijab d'inta, gata da nutsuwa da kamun kai, shiyasa duk
mutanen 'kauyen take burgesu.
Kitchen ta iske mahaifiyarta tana faman girka masu abincin rana, tace "Inna zan
d'an fita,
Inna ta kalleta tace "ina kuma zaki Laraba,?
"Inna inaso zanje gidansu indo ne naji kwana biyu ban gantaba,
To shikenan Laraba kije Allah kiyaye hanya, tace "Ameen, sannan ta fice daga
gidan.

Inna kuwa har cikin ranta taji dad'in yanda d'iyarta ta saki jiki, dan rabon datace
zata fita tun da rasuwar masoyinta sabi'u.

Cikin nutsuwa take tafiyarta, kanta sadde dan batason yawan kallon da mutane suke
mata.

Dai-dai santar dazata sadata da gidan su indo ne taji kamar ana kiranta, waigowa
tayi dan ganin me kiranta,

Cikin nutsuwa ya iso inda take fuskarsa d'auke da murmushi, yace "Laraba kina
lafiya, tace "Lafiya lao Haruna,
ya'kara fad'ad'a murmushinsa yace "Laraba ashe kina ganuwa, itama mumushin tayi
tace wace ni ince bani ganuwa,
yace ay naga tun rasuwar sabi'u rabon da inganki sai yau tace kaidai bari Haruna,
wallhi fitar ce yanzu kwata-kwata tayimin wahala yauma dan naga kwana biyu banga
mutumniyarba shiyasa nace bari inzo inga ko lafiya, Haruna yayi murmushi yace
"gaskiya ne 'kara da kika fito, nikau wallahi 'kawancenku yana birgeni keda lndo,
duk 'kauyennan ba Wanda besanku tare ba.

Murmushi kawai tayi tace "Haruna kenan, yace "Allah kuwa, duk 'kauyennan kuna burge
mutane da dama kuma gashi kunsha bam-bam da 'yan matan 'kauyen, gurin nutsuwa da
kamun kai.

Tace "to mungode da wannan yabo damuka samu daga gareku, ni zan wuce kaga rana na
'karayi baniso in wuce azahar ban koma gida ba,
Yace "to Amma idan bazaki damuba inaso zamuyi wata magana dake, tace "ina
sauraronka Amma Allah sa bazata d'auki lokaci ba.

Yace "inshaAllahu bazata d'auki lokaciba duk da bansan yanda zaki ji ba indan
kikaji maganar dazan fad'a,
bejira tafad'i wani abuba ya'kara gyara tsayuwarsa yace "watako Laraba a gaskiya
na dad'e ina Sonki cikin zuciyata, ganin sabi'u yarigani ne kuma gashi har
maganarsa takai ga iyaye yasa na ha'kura ban bayyana kainaba, amma yanzu tunda ta
Allah ta kasance shine nace bari nazo da 'ko'kon barata ko Allah zesa a ki 'kar6eni
in maye gurbin sabi'u a cikin zuciyarki.

Tunda ya furta kalmar so, Laraba taji gabanta yayi wani mummunan fad'uwa, da kyar
ta tattaro nutsuwarta, batare da ta kallesa ba tace "naji duka bayaninka amma inso
kabani likaci inyi shawara.

Yace "nabaki kwana biyu ko wace shawara kika Yanke zanji, tace "Allah kaimu yace
"Ameen.

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Da sallama tashiga gidansu lndo, innar indo ta iske tsakar gida tana wanke-wanke,
ta dur'kusa har 'kasa ta gaisheta, "inna ina wuni, cikin fara'a ta amsa "lafiya lao
Laraba yau kece a gidan namu, tayi murmushi tace "nice inna, indo nanan kuwa?
"Tananan da yanzu ma take cemin zata gidanku, ki isa mana.

Cike da murna indo ta tarbeta, 'kawata sannu da zuwa, wlh shirinnan da kika ga
inayi gidanku zani, Laraba tace "sai kuma gani nazo, lndo tayi dariya tace "ay naji
dad'in zuwanki, dama jiya Hashim yazo gidannan yabani sa'ko gurinki, Laraba cikin
halin rashin damuwa da maganar da lndo zata fad'a mata tace sa'ko kuma, lndo tace
kwarai ko, dan abinda na dad'e ina gaya maki ne ya tabbata, Hashim dai yace inmi'ka
'ko'kon bararsa gareki, yace wlh ba wasa yakeba sonki yake, kuma baza'a d'auki
lokaciba yakeso ayi aurenku.

Laraba tayi murmushi tace "yanzu ma kan hanya Haruna yatsareni da surutu waishi a
dole yana sona, lndo tayi murmushi tace "inkon Allah, to yanzu yazamuyi kenan?
Laraba tace "yafa zamuyi addu'a zamuyi Allah za6amin abinda yafi Alkhairi, indo
tace hakane Allah shige mana gaba, Laraba ta amsa da "Ameen.

Ranar gidansu indo Laraba ta wuni, sai bayan la'asar takoma gida.

Zaune ta iske innarta cikin inuwar bedi tana hutawa, d'aki tawuce tacire hijabinta
sannan tadawo ta zauna kusa da innar, tace inna sannu da hutawa, tace "yauwa har
kin dawo, tace nadawo innna.

Inna ta kallata tace bayan tafiyarki, saratu yayar Hashim tazo gidannan, wai Hashim
ya turota yana sonki idan anbashi dama kuma kin amice Aurenki zeyi, cike da kunya
Laraba ta sadda kanta 'kasa ta gayama inna yanda sukayi da lndo, sannan kuma ta
gayamata shima Haruna yana sonta, inna tace "to dukansu dai basuda makusa amma ni
aganina Hashim kamar zefi, kuma idan kikayi la'akari da hidimar daya dad'e
yanayimaki idan kika gujeshi yanzu kamar munyi butulci ne.

Laraba tace "inna nidai duk Wanda kika za6amin shine za6ina, fatana kawai kitayani
addu'a Allah za6amin abinda yafi Alkhairi.
Inna tace "Ameen.

🖊Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:10 PM] +234 816 616 9254: [20/08 6:36 pm] 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

7⃣to8⃣```Page```

🖊 Soyayya me 'karfi ta 'kulle tsakanin Laraba da Hashim duk 'kauyen mutane sun gama
sanin Hashim ne ze Auri Laraba.

Haruna kuwa hakuri Laraba tabashi akan soyayyar daya nema daga gareta, bata za6e
Shiba,
A ranshi yaji ba dad'i amma sai ya nuna bedamuba, yayi mata fatan Alkhairi.
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Inna na zaune gidin bedi tana tsintar wake wanda zasuyi sanwar rana, tajiyo
sallamar mal Lawal, Wanda ya kasance 'kanine ga mahaifin Laraba, da fara'a inna ta
amsa sallamar "a'a mal Lawal ne sannu da zuwa, jiki na 'kyarma taje ta d'auko
tabarma ta shimfid'a mashi.

Mal Lawal mutum ne d'an bala'i bayada mutunci ko kad'an shiyasa lnna ke binsa
ahankali dan tasan duk garin Laraba batada mahaifin daya wuceshi,
Yayinda shikuma yake amfani da wannan damar yanayimasu yanda yaga dama.

Laraba ma masifar tsoronsa takeyi, hakan yasa tanajin shigowarsa gabanta yayi
mummunan fad'uwa dan tasan akwai abinda yakawo shi,
Zuwa tayi har gabansa ta dur'kusa ta gaisheshi, cike da gadara da nuna isa ya
amsa, sannan ta mi'ke taje ta d'auki tukunyar 'kasar data kasance ta ebar ruwansu,
ta yafo gyalenta tazo gaban inna tace "inna zanje d'ibar ruwa, inna ta kalleta,
tariga tasan dalilinta na son tafita, saboda haka bata hanataba, tace to Allah bada
sa'a tace "Ameen sannan tafice.

Kamar jiran fitarta yakeyi, ya maida hankalinsa ga inna yafara magana cikin bala'i
da d'aga murya,

"Hinde dama gurinki nazo, watako banida daraja a idonku dan baku d'aukeni bakin
komeba keda d'iyarki, shine har yarinyar nan tana soyayya da wani ba'a sanar daniba
dan an d'aukeni mahaukaci Wanda besan abinda yakeyiba.
Tunda yafara masifarsa lnna bata d'aga kai ta kalleshiba, saida yagama,
sannan tace "Allah baka ha'kuri, dama wallahi yau nayi niyyar inzo dakaina har gida
ingaya maka.

Ya tari numfashinta cikin masifa, yace "sai kuma gani nazo, to duk da bakison
sanyani cikin Al'amarinki baki isa ki rabani da Laraba ba, saboda Laraba batada
Uban da ya wuceni duk fad'in 'kauyennan.

"To duk da baki tura shi Hashimun gurinaba yaje ya sameni munyi magana, kuma yatura
magabatanshi mun tsaida maganar aurenshi da Laraba nan da sati ukku idan Allah ya
kaimu.

Inna tace "Allah kaimu Allah sa muna raye, ta tashi tashige d'aki tana matsar
kwalla, kusan duk randa mal Lawal yazo gidan sai inna ta zubar da hawaye.

Nan yagama zamanshi yanata zazzaga masifa marar dalili, ta inda yake shiga ba tanan
yake fitaba, lnna kuwa tana d'aki tana jinshi har yagaji ya'karama rigarsa iska.

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Zaune suke kan wani dutse 'kafafunsu na cikin ruwa, da Alama sunajin dad'in yanayin
gurin, Hashim ya kalli Laraba yace "Am Laraba na manta ban sanar dakeba, jiya
baffanki yasameni yace intura magabata na, yanzu haka kafin infito nabaro su baba
bala sun tafi,
Wata irin kunya takamata tasa hannu tarufe fuskarta, tace "kace munkusa zama miji
da mata, Hashim yayi dariya yace "Allah dai yacika mana burinmu, wlh Laraba dan
bakisan yanda nake sonkiba, ina maki 'kaunar da duk cikin masoyanki babu wanda
yata6a yimaki makamanciyarta,
Wani lokaci nakan zauna inta tainani, inga kamar baffanki baze bani keba, sai
inji gabana yayi wani mummunan fad'i.

Laraba ta kalleshi cike da tausayawa, dan ko ita tagama yadda da son da Hashim yake
mata bana wasa bane tace "ka kwantar da hankalinka masoyina indai muna raye
inshaAllahu bakada wata mata bayan ni.

Cike da jin dad'in kalamanta Hashim yace "Allah sa tace "Ameen.

Haka ta Ebi ruwan Hashim d'in ya d'aukar mata suka kama hanyar gida suna tafiya
suna tad'i cike dajin dad'i.

Saida suka kawo gab da gidansu Laraba sannan yami'ka mata tukunyar ya tsaya nan
saida yaga shigarta sannan ya wuce.

Da sllama tashiga gidan, inna tayi saurin 'kar6ar ruwan dake kanta, tace "Laraba
kindawo,

Kallo d'aya tayima innar tata tasan tana cikin 6acin rai, tasan arina _(wai ansaci
zanin mahaukaciya)_ muddin ldan baffa Lawal yazo gidan to dole sai inna ta zubar da
hawaye.

Bata ko tambayi inna dalilin 6acin ranta ba, tashiga rarraahinta tana bata ha'kuri.

Inna ta kalleta cike da tausayawa tace "Laraba 'kanin mahaifinki yazo, ko ban
fad'aba kin riga kinsan halinsa, yace ya sanya bikinki da Hashim nan da sati ukku,
ina ro'konki da dan Allah kada ki d'aga hankalinki ki zamo me biyayya sai kiga an
zauna lafiya.

Laraba bataji komeba dangane da abinda mahaifiyarta ta fad'a mata sai cewa tayi
"inna kitayani Addu'a Allah za6a min abinda yafi zama Alkhairi a rayuwata, inna ta
share wasu guntayen hawaye tace, tashi kiyi wanka ga abincinki can gindin bushiya,
cikin langa, ba musu ta ebi ruwa cikin bokiti tafad'a kewaye, inna kuma tacigaba da
matsar kwallar tausayin yarta.

🖊Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:10 PM] +234 816 616 9254: [21/08 8:18 am] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

9⃣to🔟```Page```

🖊Ranaku suna wucewa lokaci na tafiya, yau saura kwana hud'u d'aurin Auren Laraba da
masoyinta Hashim
Hidima sosai 6angarorin guda biyu sukeyi, lnnar Laraba kuwa bata wani damu ba
game da abubuwan da ake bu'kata gurin biki, saboda dama tanada kome ta tanada, sai
d'an abinda ba'a rasaba,

6angaren Laraba kuwa yau sun fita gayya itada 'kawarta indo, sun gayyato 'kawayensu
da dama wad'anda mafi yawansu sunada aure, marassa auren basuda yawa, wasu ma harda
'ya'yansu.

A gajiye suka dawo, gidansu indo suka sauka, lnnar indo tayi masu sannu,
Sannnan suka wuce d'aki suka cire mayafansu suka fito suka d'aura alwala suka
gabatar da sallar la'asar sannan lndo ta d'auko masu abinci suka fara ci, dambun
masara ne yaji zogale, sai 'kamshin man gyad'a ke tashi,
Sun kammala indo ta d'ebo masu ruwa me sanyi a tulu suka sha, sannan suka cigaba da
tattauna yanda shirin bikin ze kasance, sun shirya taron 'kawayen amarya ana gobe
d'aurin Aure.

Sai gab da magrib suka fito indo zatayima Laraba rakiya ta tafi gida, suka gamu da
ilu saurayin lndo,

Laraba ce tafara gaidashi, ya amsa cike da fara'a,


Sannan lndo ta gaidashi cike da jin kunyarsa, ya amsa sannan ya maida dubansa ga
Laraba cikin tsokana yake magana "Amarya baki laifi,.... Laraba tayi saurin
tarbarsa "kada dai ka ida wannan magana dan ba yanda za'ayi mutum yakashe d'an masu
gida ace beyi laifi ba, kai ko kazar masu gida marya takashe sai tayi laifi
barantana d'a.

Suduka sukasa dariya, ilu yace yanzufa nan da kwana hud'u kinzama marya, tayi
dariya tace kai kuma nan da wata d'aya kazama ango, yace "inshaAllah ga kuma
amaryata, ya nuna indo ya wani kashe mata ido, cike da jin kunya indo taja hannun
Laraba tace zomuje dan Allah yamma na'karayi, haka suka wuce suka barshi cike daso
da 'kaunar indon sa.

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
Yau Yakama Alhamis, kuma daren d'aurin auren indo,
Yau ne kuma suke taro da 'kawayenta, sun taru gidan wata mata nan makwabciyarsu,
anata shewa, Kowa kagani cikin farin ciki, abin Alhamdulillah.
Indo ce tafito cikin shigar sabuwar atamfa riga da zani d'inkin yayimata kyau,
duk da simple ne d'inkin amma ya'kara fito da kyawunta,
Kafarta tasha 'kunshin Jan lalli, tayi kyau tafito amarya sak _(amma a
'kauyensu)_😜

Sun zauna Kowa na yaba kyawu irinna Laraba, wata daga cikin 'kawayensu me suna
hansai tace "gaskiya Laraba kinada kyau, inama ace yayana ne ze aureki ki ri'ka
haifo masa kyawawan 'ya'ya masu Kama dake.

Murmushi kawai Laraba tayi mata dan tasaba jin haka 'kawayenta da dama sunaso ta
auri yayyensu.

Hansai ta matso kusa da Laraba ta rad'a mata a kunne, wallahi yaya habu ya d'ad'e
yana sonki, abinda yasa be furta maki ba dan yaga lokacin bashida 'kud'i, tun bayan
rasuwar masoyinki na farko, yanzu kuma yadawo daga birni yayi kud'i, amma sai
yadawo da rashin sa'a ya iske saura sati d'aurin aurenki.

Wani mummunan fad'uwar gaba Laraba taji lokacin da hansai ta tuna mata da rasuwar
saurayinta, sai lokacin ta tuna da samari biyu nefa aka saka masu rana sai ana gab
da d'aura masu aure suka mutu.

Wasu zafafan hawaye suka zubo daga idonta tasa gefen mayafinta ta goge, cikin ranta
tace _(Ya Allah kada ka kashe Hashim Allah sa muna da rabon kasancewa inuwa d'aya
nida shi)_

Ganin Laraba na hawaye yasa hansai tayi shiru da maganar datake tace "dan Allah
kiyi ha'kuri idan maganata ta 6ata maki rai, bata jira jin abinda Laraba zatace ba
ta tashi ta koma cikin 'kawaye aka cigaba da labari, amma tana yawan satar kallon
Laraba dan ganin yanda lokaci d'aya hankalinta ya tashi.

Indo tafito da biskit da cingam wanda suka kulla cikin ba'kar leda tashiga
rarrabawa, saida ta tabbatar da Kowa ya samu sannan takoma kusa da Laraba ta zauna,
tin tana cikin rabon kaya ta lura da 'yanda 'kawar tata take cikin wani irin
yanayi.

Sai gab da magrib 'kawayen amarya Kowa ya watse, lokacin lndo da Laraba suka wuce
gidan su Laraba.

Gidan cike yake da 'yan'uwa da abokan arzi'ki, anata hidima, nan suka gaisheda
mutanen dake tsakar gidan sannan, suka wuce d'aki.

Suna shiga Laraba ta cire mayafinta ta zauna da6as kan tabarmar dake shimfid'e
tsakar d'akin jikinta ba 'karfi ko kad'an,
Indo ta kalleta tace "Laraba na lura dake tun d'azu baki cikin nutsuwarki, wai me
ke damunki?

Wasu zafafan hawaye suka zubo daga idanunta tace, "lndo jikina duk ya mutu,
hankalina yakai 'kololuwa gurin tashi, gani nake Hashim mutuwa zeyi kamar yanda,
lro da sabi'u suka mutu... ta fashe da wani irin kuka me ban tausayi.

Indo tace ki daina wannan tinanin acikin ranki, dan Allah ki daina kuka inshaAllah
Hashim baze mutuba, ay mutum baya mutuwa sai kwananshi sun 'kare, suma da suka mutu
dama Allah ya 'kaddaro hakan ne garesu.

Nan lndo tarin'ka rarrashinta, sai bayan isha'i sannan tabar gidan cike da tausayin
halin da 'kawarta take ciki.

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
```Rana bata 'karya sai dai uwar d'iya taji kunya```

'Daruruwan mutane sun taru 'kofar gidansu Laraba domin halartar d'aurin Aurenta.

Yayinda itakuma a ranar ta tashi sukuku, jikinta ba 'karfi ko kad'an, matar 'kanin
babanta ce mal Lawal ta matsa mata tayi wanka ta shirya cikin wata koriyar atamfa,
riga da zani sannan tayi mayafi da kalar zanin atamfar,

A 'kofar gida kuma yan'daurin aure sungama taruwa dangin ango kawai ake jira a
d'aura aure, amma shuru basu ba labarinsu,

Mal Lawal yagama 'kulewa shiru kawai yayi, jira yake dangin angon suzo sai ya sauke
masu ta cikinsa snnan a d'aura auren.

Bayan kamar minti talatin mal Lawal yanata cika yana batsewa, sai ya hango ml bala
tare da wasu mutane guda biyu suna tinkaro su.

Cike da bala'i mal Lawal ya mi'ke dan ya saukema mal bala ta cikinsa, sai mal bala
yafad'a mashi wata magana wacce ni kaina bansan meya fad'a ba, sai ji nayi ya rafka
uban salati, nan mutane suka taso suna tambayarsa "meya faru?.

Cikin gida kuwa mata sunata tsegumin an'ki d'aura aure an shanyasu, jira suke a
d'aura atafi da amarya gidan mal Lawal daga can za'a d'auketa akaita gidan miji.
Baba salame ce wata makwabciyarsu tashigo gidan hankali tashe, bako sallama, da
sauri mutane sukayo kanta ana tambayarta "meya faru? Sai ta fashe da wani irin
kuka, wata magana tafad'a masu bansan me tafad'aba saboda cikin muryar kuka tayi
maganar sai jinayi suduka sun d'auki salati.

*To fah 🤔 nifa ansani aduhu😱 miye ake fad'a wanda yake tada hankalin mutane 😭🙆🏻*

_ku biyo zee mmn khady dan jin cigaban labari_

_08166169254_

🖊Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:10 PM] +234 816 616 9254: [21/08 12:15 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

1⃣1⃣to1⃣2⃣

🖊 zaune take d'aki tasha lulli6in zanin atamfa, wani mummunan fad'uwar gaba taji,
kawai sai jitayi hawaye suna gangarowa daga idonta, suna diga bisa jikinta.

Hayaniya tajiyo a tsakar gidan, a tunaninta an d'aura auren ne amma koda ta 'kara
saurarawa sai taji sa6anin haka *_Dukkan me rai mamacine, Allah ji'kan hashim_*

Wata uwar 'kara ta saki tare da fashewa da wani irin kuka, wanda yajawo hankalin
mutane zuwa gareta,

Lokaci guda tanemi numfashinta ta rasa, ta fad'i 'kasa sumammiya, nan fa aka shiga
tsananin tashin hankali, inna tayi saurin tallafota tana kuka, tana kiran sunanta,
da sauri aka d'ebo ruwa aka yayyafa mata sannan numfashinta ya dawo, amma duk da
haka batasan inda kanta yakeba.

A ranar dai anga tashin hankali, mutanen dasuka taru d'aurin Auren Hashim sune
sukayi jana'izarsa,

Bayan an kaishi makwancinsa aka dawo aka cigaba da zaman makoki, mutane kowa na
Al'ajabin yanda mutuwar Hashim ta kasance, dan kuwa ranar saida abokaninsa duka
suka taru, yashiga wanka bayan yafito ya shirya cikin farar shaddarsa, har sun fito
zasu tafi, yace masu kanshi na ciwo zeje chemist ya siyo magani.

Har wani cikin abokanin yace bari yaje ya siyo mashi, amma sai yace ya barshi kawai
zeje da kanshi, haka yatafi yabar abokaninsa suna jiran dawowarsa su wuce gurin
d'aurin auren,

Sun kai kimanin minti arba'in suna jiransa amma shiru,saboda haka suka Yanke
shaawarar binsa.

Innalillahi'wa,inna,ilaihirraji'un suka furta, lokacin da suka hango Hashim kwace


cikin ciyayi, ga jini duk ya 6ata farar shaddar dake jikinsa, amma ba Alamar rauni
jikin sa.

"To ta ina ya samu wannna jinin? Tambayar dasuka rika yima Kansu kenan wacce basuda
amsarta.

Nan suka d'aukeshi suka nufi gida hankali tashe,


Kafin kace miye labari yagama baje gari, abunka da 'karamin gari duk inda kanufa
maganar akeyi, dan wasu har sun fara yima abun wata mummunar fassara,

*_°Bayan sati biyu_*°

6angaren Laraba kuwa tun rasuwar Hashim batasan inda kanta yakeba sai yau tadawo
hayyacinta, abin mamaki batayi maganr mutuwar Hashim ba, kawai tacigaba da
hidimominta,

Wanka tayi ta shirya cikin, sabuwar atamfarta d'aya daga cikin wacce aka kawomata
na lefen aurenta, da aka maida gidansu Hashim suka 'ki kar6a,

Kwalliya tayi sosai, tayi gwanin kyau abunka ga 'kya'kyawa duk yanda tayi kwalliya
yimata kyau take, duk da tana tashin 'kauye, gyale ta dauko ta rataya kafad'arta
tazo gaban inna tace inna zanje gidansu lndo, inna ta d'ago idanunta ta kalleta
cike da damuwa, da mamakin yanda halayyar Laraba ta canja bayan rasuwar Hashim,
tace "haka zaki fita Laraba yakamata ki sanya hijab d'inki, ta turo baki tace ni
gaskiya inna bazansa hijab ba kamar wata me takaba, lnna ta girgiza kai cike da
takaici da kuma mamakin abinda ke damun 'yarta wanda har zatayimata magana tace ba
hakaba, wanda da ba halinta bane.

Koda taga Inna batada niyyar mata magana kawai sai tasa kai tafice, tace "saina
dawo, cike da takaici inna ta matse kwallan dasuka taru idonta tace "Allah maidoki
lafiya.

Tafiya take hankalinta kwance abinta, ga gyalenta rataye a kafad'a gashi ta wani
kashe d'aurin d'an kwali,
Kan hanya kuwa duk wanda yagamu da ita cikin wannan yanayin sai yayi mamaki, kafin
kice me mutane sun fara tsorata da Al'amarinta.

A zaure ta iske indo da saurayita ilu suna zance, Wanda yau yarage saura sati d'aya
bikinsu, dama suna cikin tattaunawa ne akan maganar Larabar ne, inda ilu ke
garagad'in indo a kan ta rabu da laraba indai har tanason su shirya, sai gata
tashigo, ta kalli ilu cikin sakin fuska tace ango kasha 'kamshi,...

Wani irin fad'uwar gaba ilu yaji lokacin daya jad'a ido da Laraba , saboda haka
jiki na kyarma yayima lndo sallama yabar gidan.

Cike da mamaki lndo ta kalli Laraba, tace "kawata yau kece da wannan shigar abinda
ban ta6a gani kinyi ba,
Laraba tayi dariya tace "lndo kenan yo kuma kullum haka zanta yawo da hijabi kamar
me takaba, ay nan gaba ma ko gyalen barin sawa zanyi.

Cike da mamaki indo tace "to Allah ya 'kyauta, sannan suka wuce cikin gidan.
Innar indo na zaune tana shan iska taji shihowarsu,
Laraba ta gaisheta, wani mummunan fad'uwar gaba taji da ganin Laraba, dan taji
rad'e-rad'in da akeyi agari, *aiko dole tasan yanda zatayi taraba 'yarta da Laraba
tun kafin suma ta kashesu.

Indo ce ta lura da yanda mahaifiyarta tashiga dogon tunani tace "inna Laraba na
gaisheki ko bakijiba ne? Firgigit tadawo daga dogon tinanin datake ta washe baki
tana ya'ke tace lafiya lao.

🖊Zee Elkaseem
Mmn khady💋
[10/16, 8:10 PM] +234 816 616 9254: [21/08 4:53 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

1⃣3⃣to1⃣4⃣

```Bayan kwana sha ukku```

Yau ake taron 'kawaye na lndo, gobe kuma d'aurin aurenta, 'kawayenta ne cike ma'kil
da gida anata shewa, Kowa kagani cikin farin ciki, hansai ta kalli lndo tace "waini
indo ina Laraba naga tunda nazo ban gantaba, lndo tayi murmushi tace "tun d'azu
muna tare ta koma gidane ta shirya, amma nasan tana gab da dawowa, hansai tace
Allah sarki, sai ta tashi ta goya d'anta tace "to amarya ni zan wuce sai kuma gobe
idan Allah ya kaimu, lndo tace "kai hansai tun yanzu bazaki bari Laraba ta dawo
tabaki biskit d'in ba? Hansai tayi dariya tace a'a ba kome wlh ay zan dawo gobe,
kafin tarufe Baki suka jiyo sallamar Laraba, aiko ko kallon inda take Hansai
batayiba tasa kai tafice daga gidan,
Can sai wasu gun-gun 'kawayensu suka taso suma sun kai su goma suka ce "muma dai
mun wuce, cike da mamaki lndo ta kallesu "tun yanzu baku bari ajima, tare suka
had'a baki suka ce "a'a akwai inda zamu ne, suka sa kai suka fice,

in takaita maku labari shigowar Laraba gidan saida yasa duk mutanen dake gidan
suka tafi.
Indo tasan dalilin tafiyarsu, har ga Allah bataji dad'iba amma ba yanda zatayi, ta
dad'e da sanin mummunan zaton da mutanen 'kauyen keyima Laraba, wasu guntayen
hawaye suka zubo daga idonta tasa hannu ta goge batare da Laraba ta kula da halin
datake ciki ba.

Ranar dai haka suka gama yinin, abin ba dad'i.


Laraba kanta ta fahimci yanda mutanen garin ke gudunta, a zuciyarta tace
_"me nayima mutane suke guduna_ *_Innalillahiwainnailaihirraji'un_*
Tafad'a tare da goge wasu zafafan hawaye.

Washe gari aka d'aura auren lndo da ilu, da dare aka kai amarya,
Ranar Laraba taga tashin hankali, dan 'kiri-'kiri mutane suke nuna tsana da
tsangwama da 'kyama gami da tsoro agareta.

Hakan yasata barin gidan bikin batare da ta shirya ba, lndo ta tausayama 'kawarta,
cike da tausayi take mata addu'a Allah ka yayemata abinda ke faruwa da ita.
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
Kiyi ha'kuri kinji Laraba, inshaAllah kome ze wuce, kiri'ka addu'a kinji Allah yaye
maki matsalar dake tattare dake, wasu zafafan hawaye suka zubo daga idanunta tasa
hannu ta goge "yanzu shikenan inna babu ni babu maganar Aure duk namijin dayace ze
aureni da lokaci ya gabato sai a wayi gari ya mutu, gashi nazama abin tsoro cikin
mutane duk inda naje sai afara barin gurin, ta'kara fashewa da wani sabon kuka.

Inna har cikin ranata take tausayama d'iyarta, itama hawayen take, tace "kiyi
ha'kuri Laraba ki d'auki wannan matsayin kaddara, inshaAllah wata rana kome ze zama
labari.

Nan lnna tayita rarrashinta tana kwantar mata da hankali,


Harta samu tayi shiru tace "tashi ki d'au tukunya ki d'ebo ruwa kiyi wanka, ba musu
ta tashi ta dauki 'yar 'karamar tukunya tanufi rafi, bako gyale jikinta barantana
hijab wanda har ta manta yanda ake sanyashi, inna tayi fad'an harta gaji ta
'kyaleta

Haruna ta hango zaune cikin gonarshi shida wani abokinshi suna cin gyad'a me 6awo,
suna fira, abokin nashi ne yafara hangota ta doso inda suke, cikin dabara ya tashi
yacema Haruna "ina zuwa bari in d'an zagaya can wlh jiya naci wata tafasa tad'an
6atamin ciki.

Haruna yace "Allah sauwa'ke, ya mi'ka mashi ruwa, ya amsa yawuce, yayi nesa kad'an
ya hango Laraba ta iso inda Haruna yake zaune tanayimashi magana, a fili yace
"Allah nagodema da Laraba bata riskeni gurin can ba, da sauri ya 'kara gaba yayi
cikin gari yana tinanin yanda abokinshi ze rabu da Laraba *Mayya* la'kanin da
mutanen 'kauyen suka fara kiranta dashi kenan dan su acewarsu mayya ce shiyasa duk
wanda yace yana sonta take cinye kurwarshi ya mutu.

Da fara'a take magana "Haruna dama ina nemanka, cike da tsoro ya kalleta, duk
illahirin jikinsa kyarma yake amma bakinsa yakasa furta kome,

Bata kula da halin dayake cikiba tacigaba da magana, "waini Haruna ya maganar
soyayyarmu, tunda Allah besa anyi da Hashim ba mizai hana ka dawo a d'aura mana
aure.
Sai lokacin yasamu yayi magana cike da tsoro bakinsa na 'kyarma yace "Laraba dan
Allah kiyi ha'kuri ni wallahi tuni nafasa yin Aure, bazanyi Aureba kwata-kwata.....

Cike da mamaki Laraba ta 'kara matsowa inda yake tace bazakayi aureba fa kace
Haruna, nice fa Laraba ka manta irin soyayyar da kace kanayi mani, a da,

Yace "a da ba amma yanzu na daina soyayya kiyi ha'kuri, Laraba ta'kara matsowa kusa
dashi yana matsawa "Haruna nice Laraba baka ganeni ba ne?

Cike da tsoro yace "na...na..ganeki mana, haba sai lokacin yasamu ya ranta a na
kare 🏃🏻
Mamakine tare da takaici da ba'kin ciki suka rufe Laraba ta dur'kusa nan tana kuka.
_Allah sarki laraba na tausaya maki_

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:10 PM] +234 816 616 9254: [22/08 7:26 am] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

1⃣5⃣to1⃣6⃣

🖊Zaune suke sun buga uban tagumi, Laraba na zubar da hawaye itama lnna hawayen take
zubarwa dan taji yanda ake maganar Laraba a 'kauyen mutane suna kiranta *mayya*
tasa hannu ta goge hawayen dake idonta, abinda yafaru da ita jiyane yashiga dawo
mata a kwalwa,

shikenan yanzu abin Laraba har inna yake shafa, dan jiya akayi bikin wani d'an
Aminiyarta, wacce a da matar taso ace d'anta Laraba ya aura amma Allah be nufaba,
lnnar Laraba batada aminiya wacce ta wuceta, amma har aka fara biki ba'a
gayyacetaba, saboda haka tace bari taje tayi mata Allah sanya Alkhairi,

Haka ta shirya ta nufi gidan, tana isa zauren gida, magan-ganun dataji anayi
gidanne yasa hantar cikinta juyawa,

Muryar mata taji daban-daban suna magana "wah ay Laraba ta fiddo maitar ta fili,
yanzu fa mutum ukku ta kashe 'kauyennan kinsan kuwa maitarta takai inda takai, can
wata mata ta kar6e zancen "ay ance gado tayi gurin mahaifiyarta, dan ance ita ta
kashe mahaifin Larabar, muryar wata matar taji tana cewa "to mudai uwar biki Allah
sa baki gayyato mamu suba, dan nasan bakida Aminiya kamarta, can sai tajiyo muryar
amiyar tata tana cewa "a da ba, amma banda yanzu dan ban gaji da rayuwaba inaso
inga auren auta ta har inga jikokina, suduka sukasa shewa "heyyyyyy, wata tsagerar
mata takama hanci ta rangad'a guda "ayyuririiii,.........

Innar Laraba najin haka wasu zafafan hawaye suka zubo daga idonta, zuciyarta
tayimata nauyi, kanta yayi wata irin Sarawa, take ciwon kai me tsanani ya saukar
mata jitake kamar kanta ze rabe, haka ta dafe kanta tanufi gida cike da takaici da
ba'kin cikin magan-ganun data ji, dan gidan bikin da bata shiga ba kenan,

Kan hanya ma duk wanda tayima magana sai taga ya matsa da Alamar tsoro tattare
dashi baze ko amsa maganar ba,
Wasu kau dasun hangota suke rugawa, abin ya matu'kar d'aure mata kai.
°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Yanzu kai habu larabar kake so, kana ganin yanda mutane ke gudunta, amma kai karasa
wacce zaka za6a sai ita, kuma kariga ka gama sanin *mayya* ce,
habu ya kalli abokinsa cike da takicin kalmar mayya daya furta ga Laraba yace "eh
ni ina sonta koda zata ri'ka yankan naman jikina tana ci d'anye 'karewar maita zan
aureta, abokin nashi yace to "Allah raka taki gona, nidai kaga tafiyata, kuma
muddin kasani idan kana tare da Laraba to abotarmu ta 'Kare, habu yayi wani guntun
murmushi mai d'auke da takaici yace, Allah had'a kowa da rabonsa, rabuwar habu
kenan da abokinsa.

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Zaune suke sunyi tagumi duniya tayi masu zafi itada innarta, dan fitama wahala take
masu kullum suna gida basuda aiki sai tinani sai kuka,
Rabon kau da wani mutum yashigo gidansu har sun manta,
Itako Laraba da gidan lndo kad'ai take zuwa taji d'an dad'i-dad'i shima yanzu
yaushe rabon dataje, tun ranar dataje ilu yayimata wula'kanci yace kada ta 'kara
zuwar mashi gida idan kuma bata dainaba hukuma zata rabashi da ita,

Suna cikin wannan yanayin sukaji an bankad'o kyauren gidan kad'an yarage a
karyashi, mal Lawal ne yafara magana cikin bala'i da masifa, watau kin koyama d'iya
maita tana kashe mutanen gari, to wallahi ba maitaba ko uban maita ke gareki dole
Laraba ta fito da miji inyimata aure, dan bazan yarda tana yawo agari ana zagina a
matsayin mahaifinta na gaza aurar da itaba.

Tunda yafara magana basu cemashi 'kala ba, saida yagama bala'i sannan ya kalli
Laraba yace "waye kuma yanzu kike so wanda tsautsayi ke shirin afka mawa,

Cikin kuka da bakin ciki tace "dama Haruna ne tin kafin rasuwar Hashim yake sona,
mal Lawal yace "to bari yanzu inje in samu Haruna idan da gaske yake ya turo
iyayenshi dan bazaki 'kara sati biyu a gidannan ba, sadaki kawai ze kawo a d'aura
aure, haka yafita gidan yanata bal-balin bala'i, inna dai bata cemashi ci kanka ba
illah kuka datakeyi.

Haruna Zaune shida abokinsa suna fira, mal Lawal ya iso gurinsu, suka gaidashi ya
amsa, sannan yace Haruna gurinka nazo kan maganar Laraba, wani irin fad'uwar gaba
Haruna yaji,
jin an ambaci sunan Laraba, mal Lawal be jira abinda Haruna ze fad'aba yaci gaba
da magana, "tace kaine wanda ta tsaida shine nace ka turo magabatanka bamu bukatar
kome daga gareka sadaki kawai zaka kawo nan da sati d'aya a d'aura maku aure.

Haruna Wanda tinda mal Lawal yafara maganar jikinsa ke rawa kamar mazari yace "a'a
ni maganar soyayayya bata ta6a had'ani da Laraba ba, kuma bani sonta, inaji ba dai
ni harunan take nufiba

A fusace mal Lawal yabar gurin da niyyar yaje gida yaci mutuncin Laraba da
mahaifiyarta.

Tinda mal Lawal yabar gurin jikin Haruna ke 'kyarma, ya kalli abokinshi yace kanafa
jin wannan mutumin, abokin nashi yayi dariya yace "watako yarinyar nan tasaka a
zuciyarta tagama kwad'aituwa da kai walh saika tashi tsaye,
Kazo muje gidan kakata 'yar me ganye tana bada maganin mayu, Malam abaka kasha kayi
wanka.

Ba musu Haruna yace mutafi,


Sun isa gidan 'yar me ganye anba Haruna maganin daze ri'ka ji'kawa yana wanka dashi
sannan aka bashi tazargade yari'ka haya'ki, matar tace indai yana amfani da wannan
badai maye ba, ko sarkin mayu sai dai yaganshi ya 'kyale.

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:10 PM] +234 816 616 9254: [22/08 6:41 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

1⃣7⃣to1⃣8⃣

🖊 "lna 'yar iskar yarinyar nan take, dan ubanki kinsan babu soyayya tsakaninki da
Haruna kika turani gurinshi, naje naji kunya, to bari kiji in gaya maki tunda dai
kinzamar ma mutane bala'i kin zamar masu 'karfen 'kafa to zan aurar dake ga duk
wanda naga dama,sannan ya juya gurin inna wacce tunda yafara fad'anshi ta kauda
kanta gefe tana zubar da hawayen takaici, shin wai dame zasuji da tsana da
tsangwama da tsoro da 'kazafin da 'yan garin kemasu koda masifa da bala'in mal
Lawal.

Yaci gaba da magana, cikin d'aga murya "Kara Ku yanke shawara tun kafin nan da
kwana biyu idan kuma ba hakaba zan yanke duk hukuncin da naga dama, yasa kai yafice
yanata kumfar baki.

Yana Fita Laraba ta taso tafad'a jikin innarta ta fashe da wani irin kuka me ban
tausayi, itama lnnar kuka take amma duk da haka rarrashin 'yar tata takeyi.

*```Bayan kwana Hud'u```*

Inna ce ke rarrashin 'yarta wacce duk yinin yau kuka take, ko ruwa takasa sama
cikinta saboda tsananin damuwa, tariga tagama sanin sunan da ake kiranta dashi a
'kauyen na *Mayya*
"Kiyi ha'kuri Laraba duk tsanani yana tare da sau'ki, in Allah ya yarda duk
masu gudunki sai sun dawo suna binki, kedai kiri'ka addu'a Allah yayi maki maganin
matsakarki.

Suna cikin wannan ne sukaji an bankad'o 'kyauren gidan, suduka suka maida
hankalinsu ga 'kofar ganin 'kyauren sukayi 'kasa ya karye, kasancewar dama na
langa-langa ne bayada wani 'kwari.

Mal Lawal ne yabi ta kan 'kyauren yashigo gidan a sukwane,


Laraba na jikin inna ta 'kan-'kameta duk tsoro yakamata gani take yau baffa Lawal
dukan ta zeyi.
Kudi ya watso jikinta yace "ga sadaki nan na d'aura aurenki da habu, yayan hansai,
idan kin cika ke mayyace yau kada ya kwana da rai, tinda sauran kafin a d'aura kike
kashesu, to wannan karan an d'aura kuma 'kurwarsa kur kuci kanku, *Mayu*.

Wani irin kuka Laraba ta 'kara fashewa dashi, ta 'kara shigewa jikin innarta Wanda
shi kad'aine yanzu take ra6a taji sanyi tace.

"Shikenan inna bamuda Kowa bamuda Wanda zamu ra6a muji dad'i, abin takaici da
ba'kin ciki wai hada baffa Lawal ake kirana *Mayya* to waye ma baze kirani da
*mayya* ba tinda 'kanin mahaifina ma yakirani haka.

Bayan magrib mal Lawal da kansa yazo ya tafi da Laraba tana kuka tana kome ya
kaita gidan miji, basu iske kowa gidan ba amma duk wani Abu na Al'ada na tarbar
amarya an kawo an aje masu,

Haka baffa lawal ya ajeta yabar gidan, tunda Allah ya halicceta bata ta6a ganin
irin wannan auren da akayimata ba, gashi dai ankawota gidan miji amma ba kowa sai
ita kad'ai cikin gida kamar *Mayya* _(sunan da mutanen 'kauyen ke kiranta dashi)_

Ta fad'a kan soson katifar da aka kawota dashi wanda ko zanin kirki bayadashi, ta
fashe da wani irin kuka, baiwar Allah Laraba tana cikin tashin hankali, duk tabi ta
rame, ta kod'e idanun nan nata sunyi zuru-zuru, hancin ya 'kara tsawo sai wani uban
'kashin wuya daya fito yayi mata 'kwaro-'kwaro.

A 6angaren habu kuwa yariga yasan an kawo amarya, yaje gun 'yan uwanshi yaro'kesu
akan suje gidan ayi d'an shagalin bikin da akeyi bayan an kawo Amarya amma sukace
"ina ay basu gaji da rayuwaba tukun, waye ze kai kanshi ga halaka.

Indo kuwa taso zuwa bikin 'kawarta kuma aminiyarta, amma ilu ya bad'e ido toka yace
bazataba, 'karshe data isheshi da magiya sai cewa yayi idan ta'kara maganar zuwa
bikin Laraba to bakin aurenta, hakan yasa ta ha'kura badan ranta yaso ba.

Bayan habu yagama fama da 'yan uwanshi akan suje gidanshi sun'ki sai yatafi gidan
'kanwarsa hansai, da sallama yashiga gidan, ta amsa sannan ta gaisheshi ya amsa,
nan yake tambayarta

"Hansai ya ban ganki gurin bikin ba, lafiya kuwa? Hansai ta yamutsa fuska tace
lafiya lau, kaina ne yake d'an yimani ciwo, cike da tausayi yace eyyah Allah
sauwa'ke tace Ameen.

Yace Amma naga kamar kin d'anji sauki, kozaki daure ki le'ka gidan kai amaryar,
Cikin firgici Hansai ta kalli yayanta tace "wah ni Yaya habu, idan ka ganni lahira
kaini akayi, wallahi bazani gidan *mayya* ba.

Cikin 6acin rai habu ya d'auke hansai da mari yace "idan bazakiba ki zauna, amma
kada ki kuma kiran matata da *Mayya* yasa kai yafice ranshi a 6ace.

Me zai faru yana fita daga gidan Laraba yagani tanayimashi murmushi, ta 'karso
gurinshi tace masoyina nagaji da jira ne gida ni 'kad'ai shine na biyoka...

cike Da mamaki yace "ya akayi kikasan ina nan, murmushi kawai tayi Mashi ta kama
hannunshi suka nufi gida.

🖊Zee Elkaseem
Mmn Khady 💋
[10/16, 8:10 PM] +234 816 616 9254: [23/08 5:48 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

1⃣9⃣to2⃣0⃣

🖊 Tafiya suke Laraba na ri'ke da hannun angonta Habu, sai da sukayi nisa da gari
sun shiga gonaki, baka ganin kome sai duhun daji da kukan tsuntsaye,

kasancewar akwai 'yar tazara tsakanin gidan Hansai da gidan Laraba, sun shiga
cikin duhun ciyayi, Habu ya waigo ya kalli Laraba yace "Amma Laraba nayi mamakin
yanda kika san ina gidan Hansai, kodai wani ya gaya maki ina nan?

Shuru yaji tayi batada niyyar amsa mashi tambayar da yayi mata, hakan yasa ya juyo
ya kalleta, suna had'a ido da ita gabanshi yayi mummunan fad'uwa dan ganin ta yayi
ta d'ad'd'aure fuska yanda kasan tunda Allah ya halicceta bata ta6a dariya ba, ga
fuskar tata tayi duhu, ba alamar haske tattare da ita, kamar ba larabar da
yasaniba, kya'kyawar yarinya fara tas fatar ta kamar ka ta6a jini yafito, amma
lokaci guda ta sauya takoma ba'ka, ga fuskar ba Alamun fara'a tattare da ita.

Lokaci guda jikinsa yafara 'kyarma kamar mazari, yakasa matsawa daga inda yake, sai
da 'kyar yasamu ya iya daga baki yace La....la....Lara...ba, miya sa kika biyoni,
miyasa zaki tsoratar dani......

Kafin ya rufe bakinsa yaji ta gagga6e da wata irin mahaukaciyar dariya tace,

"Tambaya kake yanda akayi nasan inda kake, to ayni ba sai na tambaya ba, tunvdaga
ranar daka furta kalmar so gareni nake biye dakai, kuma kasani sai nazama
ajalinka..... Hhhhhhhhhhhhhhhhh, ta 'kara gagga6ewa da wata nahaukaciyar dariya
karo na biyu.

Habu kuwa banda 'kyarma ba abinda yake, yariga yagama sad'aukar da rayuwarsa, dan
yasan 'karshen rayuwarsa ne yazo, kwata-kwata kasa yin wata addu'a yayi dan
tsananin tsoro, sun kai kimanin minti ashirin tsaye gurin Laraba, tana tsoratar da
Habu.

Sai zuwa can Allah yabashi ikon furta kalmar *lnnalillahiwa,inna'ilaihirraji'un*


sannan yasamu 'kafar guduwa daga gurin,

Gudu yake iyakar 'karfinsa, domin yau ya tabbatar ma kanshi maganar da mutane ke
fad'a suna cewa Laraba *mayya* ce, a zuciyarshi yana cewa koma miye Nina jawoma
kaina, dama ance _(Wanda beji bari ba yaji hoho)_.😱

Lokaci guda yahad'a wani uban gumi, ga tsabar tsoro ga kuma uban gudun dayasha, da
kyar yashiga gida ya maida 'kyaure yarufe, yana maida numfashi.
'Daki yanufa yana nishi yana goge uwar zufar data rufeshi kamar wanda aka watsama
ruwa,

Mutuwar tsaye yayi dan wani babban tashin hankalin daya tarar a gidan, yasan dai
yabaro Laraba a daji, amma kuma yanzu gata ya tarar da ita kwance kan 'yar
katifarta tana kuka.

Jin alamun shigowar mutum yasa Laraba tashi daga kwancen datake, ta d'ago da manyan
idanunta wanda suka kad'a sukayi jawur saboda tsabar kukan data sha.

Cike da mamaki Habu ke kallonta, a zuciyarshi yace "to wai miye ke shirin faruwa
dani ne, kodai ba Laraba bace wacce nabaro a daji.

Ganin bashida niyyar ida 'karasowa cikin d'akin yasa Laraba tayi magana "Sannu da
zuwa, tafad'a cikin zazza'kar muryarta mai sanyin sauraro.

"Yauwa yafad'a zuciyarsa na dukan ukku-ukku, "bari inje in dawo nayi mantuwa a
gida, cike da tsoro Laraba tace "miye kuma ka manta, nifa wallahi tsoro nakeji ni
d'aya gida, a zuciyarsa yace _"Ai kece abin tsoron laraba, ke yakamata aji tsoro
bake zakiji tsoron wani abu ba_

"Tinanin me kakeyine, ta tambayeshi dan ganin ya tsaya a gun bayada niyyar tafiya,

Yayi saurin dai-daita nutsuwarsa yace "a'a zanje bari intafi bazan dad'eba zan
dawo, sannan yasa kai yafice, cike da tsoro yafita daga gidan, zuciyarshi cike da
tunani kala-kala.

Tafiya yake bekoyi nisa da gidan ba amma wani mugun abun tsoro daya gani shine
yakusa sanya numfashinshi ya d'auke, dan Laraba yagani gabanshi, ta kashe d'an
kwali ta ri'ke 'kugu tana jijjiga jiki, suna had'a ido ta gagga6e da wata
mahaukaciyar dariya, sannan kuma ta d'aure fuska kamar bata ta6a dariyaba.

Tace "Habu kana gan-ganci da rayuwarka, inaso kafin nan da safiya ka gaggauta
yankema kanka hukuncin daze fitar dakai.

🏃🏻Da gudu yayi baya yakama hanyar gidanshi, tashin hankali wanda ba'a samashi
rana 😳 Laraba ya iske a tsakar gida tafito daga kewaye hannuta ri'ke da buta.

Wata irin gigitattar 'kara yasaki nan take yafad'i 'kasa kanshi yabugu da wani
dutsi dake tsakar gidan, aiko kan yafashe jini yafara zuba.

_Innalillahiwa'inna,ilaihirraji'un_ Laraba tashiga furtawa, tanufi inda Habu yake


kwance tana jijjigashi tana kiran sunanshi amma ba alamar numfashi tattare dashi.

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:10 PM] +234 816 616 9254: [24/08 2:03 pm] Zee Elkaseem: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```
_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

2⃣1⃣to2⃣2⃣

🖊 "wayyo nashiga ukku dan Allah habu katashi kada ka mutu, idan kamutu nasan bazan
'kara shan ruwa garinnan ba, dan Allah ka taimakeni, Laraba ce ke fad'in haka cikin
muryar kuka,
Yayinda habu yake kwance har yanzu besan inda kanshi yakeba, ga kuma inda kanshi
yabugu har yanzu zubar da jini yake,
"Ya salam laraba tafad'a "Lallai rayuwata tana cikin had'ari ya Allah ka fitar
dani, wasu sabbin hawaye suka gangaro kan kumatunta.

Lokaci guda jikinta ya mutu li'kis kamar wacce akayima duka


Ta tashi da sauri tanufi d'aki ta dauko wani tsohon zani cikin zannuwanta ta yaga
ta d'aurema Habu kanshi inda jini ke zuba, cikin ikon Allah kuwa sai jinin ya
tsaya, amma har yanzu ba Alamar numfashi tattare dashi,

Sai lokacin dabarar ta yayyafa mashi ruwa ya fad'o mata a arai, da sauri tanufi
randa ta d'ebo ruwa me sanyi ta yayyafa mashi, a firgice ya tashi yana "cewa "dan
Allah kiyi ha'kuri Laraba kada ki kasheni, Laraba ni me 'kaunarki ne bekamata ki
sakamin da sharri ba.

Wata irin 'kara Laraba tayi, cikin wata gur6atacciyar magana take cewa, Habu bazan
ta6a raga makaba, babu ragi ba ragowa tsakanina dakai, nariga na gaya maka kafin
gari ya waye ka nemama kanka mafita,

Cike da tsoro da firgici habu ya kalli Laraba, yaga fuskarnan tata ba Alamar
sassuci, tabbass idan yaci gaba da zama da ita ze iya rasa rayuwarsa, hakan yasa ya
yanke shwarar rabuwa da ita.

"Laraba"yakira sunanta,
Jiki a sanyaye ta juyo ta kalleshi, yace "kije na sakeki *Saki ukku*
Daga yau babu ni babu ke,

"Hhhhhhhhhhhhhh, wata irin mahaukaciyar dariya sukaji ta gauraye gidan, har tsawon
minti biyar sannan dariyar ta lafa, wata irin murya sukaji wacce basu San daga inda
take fitowaba ana cewa,

"Yaro kayi ta barka, ashe kana son rayuwarka, aka sake bushewa da wata dariya,
sannan sukaji d'if kamar anyi ruwa an d'auke.

Wani matsanauncin tsoro Yakama Laraba dan jin wani sabon Al'amari, da gudu tanufi
habu wanda shima jikinsa mazari kawai yake saboda tsananin tsoro tafd'a jikinsa ta
'kan'kameshi.

Cike da tsoro habu ya finciketa daga jikinsa, yajata kiiiiii, ya turata waje yace
"kije nace nasakeki *Saki ukku* ya maida 'Kofa ya rufe.

Laraba ta shiga bugun 'kyauren gidan, tana cewa "Dan Allah habu ka taimakeni ka
barni in kwana gobe sai intafi, haka ta rin'ka magiya amma bataji Habu yayi
maganaba, hakan yasa ta kalli gabas ta kalli yamma kudu da arewa, ba Alamar haske,
garin yayi duhu dind'um bakajin kome sai kukan tsintsaye, take wani mugun tsoro ya
dira a zuciyarta.
[24/08 2:38 pm] Zee Elkaseem: Wani irin haske ta hango daga nesa yana nufo inda
take, tin tana kallonsa nesa da ita har yazo gab da ita,
Wani irin matsanancin tsoro ya'kara kamata,
Wata irin 'kara ta fasa sannan ta ranta a na kare🏃🏻

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Inna na kwance d'aki, kan guntuwar tabarmarta sai juyi take bacci ya gagari idonta,
ba abinda take sai tinanin kowane hali 'yarta take ciki,
Wasu zafafan hawaye suka zubo daga idonta, tasa hannu ta goge,
Lokacin kuma taji Uciyarta tayimata nauyi kamar an d'ora mata wani katon dutse,
lokaci guda taji yun'kurin amai, aiko tatashi zaune tafara amai, babban tashin
hankalin da inna tagani duk yun'kurin datayi maimakon taga aman abida taci, jini ne
take amayowa hadda gundarinsa,

Cikin 'kan-kanin lokaci ta galaibaita tafita hayyacinta,

Da gudu Laraba tashigo gidan, wata irin 'kara tasaki dan ganin halin da inna take
ciki, sauri ta 'karaso gareta, takamata tana kuka tana kiran sunanata,
inna....inna...inna... Da 'kyar inna ta iya d'aga ido ta kalleta tace "Laraba nasan
tawa ta 'kare amma bazan gusheba inamaki addu'ar Allah fiddaki daga mawuyacin halin
da kike ciki.

Fad'uwa tayi rai yayi halinsa, ```Allahu akbar inna tarigamu gidan gaskiya```

Wata uwar 'kara Laraba tasaki, dan ganin inna ba Alamar numfashi tattare da ita,

Wani irin duhu taga ya gufta mata, kokacin kuma kanta yayi wata irin sarawa, jiri
ya ibeta ta fad'i kasa sumammiya,....

🖊Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:10 PM] +234 816 616 9254: [24/08 7:45 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

2⃣3⃣to2⃣4⃣

🖊washe gari tunda asuba Habu yanufi gidan iyayenshi, yana isa innarshi taganshi da
uban rauni a kai, ga jikinshi jage-jage da jini, dan be canja kayaba haka ya kwana,
wani uban salati ta buga tace "Habu lafiya meya faru dakai, ina Larabar,? Lokaci
d'aya ta jero mashi wad'annan tambayoyin, Habu bayaso ya fad'i gaskiyar Al'amarin
abinda yafaru dashi saboda besan wani halin fad'in ze jefa laraba ba, saboda haka
shiru yayima innar tashi.

Innar taga bayada niyyar bata amsar tambayoyin datayi mashi, kawai saita d'ora
hannu a kai tafashe da kuka, wanda yin hakan ya jawo da hankalin mutanen gidan
garesu, duk akayo d'akinta ana tambayarta lafiya meya faru, dayake gidan irin
gidan yawa ne,
Ganin habu dasukayi zaune ga jini duk ya 6ata jikinsa yasa suka ba kansu amsa,
tabbass koba tambaya sun san larabace ta tasarma kasheshi Allah beyiba dayake
yanada sauran shan ruwa.

Wata mata cikin mutanen dake tsai-tsaye Bakin 'kofar d'akin tace "ina kabaro
amaryar angon Laraba?
cike da takaici habu ya kallesu yace "Laraba na gidansu na saketa,

Wani uban salati matan suka d'auka lokaci guda, sukace "yo habu ya akayi haka
tafaru?
Be basu amsaba illah fita dayayi yabar gidan dan bayaso ana can-cana maganar.

Wata tsohuwar mata ta kalli innar Habu tace "Wallahi atika kinyi ta barka, dan
wannan maganin da 'yar me ganye tabada tace ki binne a gidan, amma da badan haka ba
da yanzu habu sai dai wani bashiba.

Innar habu tayi murmushin takaici tace "Hmmm Wanda beji bari ba ay yaji hoho, cikin
gidanan waye be ba Habu shawarar kada ya auri Laraba ba amma yakafe, ay dama me
rabon shan duka bayajin kwa6a, bata jiran me sauran matan zasu fad'aba tashige
d'aki tana matsar kwalla.

Ganin haka yasa kowace takama gabanta, suna fad'in albarkacin bakinsu,
Abinka ga matan 'kauye kad'an suke jira su 'kara, kafin kace me labari ya bud'e
gari.

Mutanen gari anata yayatawa, Laraba takusa kashe Habu Allah ya taimakeshi ya
saketa.

Aiko labari yakaima mal Lawal, a fusace yanufi gidansu Laraba da niyyar yaci masu
mutunci itada uwarta wacce ke d'aure mata gindi tana kashe mutane.

Bako sallama ya bankad'a 'kyauren gidan yashiga,


Laraba yagani ta had'a kai da gwiwa tana kuka, gefe kuma ga innarta kwance cikin
jini.

"Ke.....ya daka mata tsawa, da sauri ta d'ago da fuskarta ta kalleshi, saitaji wata
dama-dama a ranta, tunda tariga tasan inna tamutu, kuma batasan wa zata gaya
mawaba, tunda mutane yanzu da sun ganta guduwa suke.

Da sauri ta taso tazo gabanshi ta dur'kusa, yanzu kam idonta ba hawaye ko kad'an
dan tayi kuka har hawayenta sun 'kafe, tace "dan Allah baffa Lawal ka taimakeni
inna ta mutu, tun jiya da dare, ban san yazanyiba, shiyasa ban fitaba dan nasan duk
inda na nufa ba wanda ze saurareni,

Wata irin dariya mal Lawal yayi sannan ya kalli Laraba yace, "watako maitar taki
har takai ga uwar data haifeki, to wallahi ki shiga hankalinki, danni idan kikace
zaki cinyeni sai inci ubanki, 'yar iska kawai, yakai mata wani hauri har saida ta
fad'i, sannan yafita yabar gidan.

Zuwa yayi yasanar da mutane, innar Laraba ta mutu, amma kowa sai yace Allah
ji'kanta, da ance suzo ayimata sutura akaita makwancinta sai kaga mutum yafara
zame-zame Alamar dai baya zuwa.

Haka akayita fama da muatanen Gari, karshe dai saida me gari yasa Baki, yasa liman
da wasu tsirarun mutane akaje akayima innar
Laraba wanka akayimata sutura aka kaita makwancinta,
Kuka kau Laraba yanzu ta daina na hawaye, sai dai na zuci, dan zuciyarta tariga
tagama soyewa, tasaba da ba'kin ciki da takaici.

*_BAYAN KWANA BAKWAI_*

Yanzu Laraba ita kad'ai ke kwana gidansu babu me ra6arta, ga yunwa dan ba wanda
kebata koda sauran abinci, idan kuma tafita dan tasiyo abinda zataci dataje shago
sai muatane sukama gudu, haka zata dawo gida takama kuka, abin dai gwanin ban
tausayi, duk ta rame ta kod'e idanun nan sun kara fitowa sunyi zuru-zuru, ga wani
ciwon ciki datake fama dashi sakamakon yunwar datake fama da ita,

Ruwa kawai take banka ma cikinta koda yaushe, to yanzu ma idan tasha ruwan sai ya
'kulle mata ciki tayita amai,

Yau dai tagaji da bala'in datake ciki, saboda haka tayi niyyar zuwa gidan baffa
Lawal dan ya taimaka mata.

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:11 PM] +234 816 616 9254: [25/08 7:08 am] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

2⃣5⃣to2⃣6⃣

🖊 Baffa Lawal ne cikin gonarshi yanata noma, yanayi yana 'yar wa'ka irin ta mutanen
'kauye, abin yayi masa dad'i har gyad'a kai yakeyi, zuwa can kuma sai yatashi
yanufi inda ya ajiye kayansa ya fiddo da wata 'yar madai-daiciyar radio, yasanya
sabbin batura ya 'kunna, ya kuwa yi sa'a gidan redio an sanyo wa'kar d'an kwairo,
aiko sai ya rataye redion jikin bedi yana ji yana aikinsa,

Befi minti shidda da kunna red'ion ba sai yaji d'if redion ta d'auke, ya d'ago
kansa ya duba bega kowaba, yaje ya ta6a redion sai yaji kashe take, nan ya sake
kunnawa ya maida yarataye ya juya ze cigaba da aykinsa sai yaji an 'kara kashewa,
yana juyowa wa ze gani,

Laraba ce tsaye jikin bedin tana yimashi wani mugun kallo,


Cike da masifa da bala'i baffa Lawal ya tunkarota na niyyar ya wanka mata mari,
amma kafin yayi wani Abu sai jin saukar mari yayi, a fuskar shi.

Cike da tsoro yakai dubansa ga Laraba, wacce tana dai tsaye inda take ko motsi
batayiba, wani wawan mari aka 'kara d'aukeshi dashi, lokaci guda kuma aka rufeshi
da duka ta ko'ina, Laraba dai na tsaye har yanzu bata motsa ba,
Haka akayita jibgar mal Lawal saida ya daku sannan aka 'kyaleshi, wata irin
mahaukaciyar dariya Laraba ta she'ke da it'a sannan ta 6ace, mal Lawal yashiga
rud'ani, hankalinsa yayi matu'kar tashi, jikinsa yakama 6ari, aiko da sauri ya
tattare 'yan kayanshi yanufi gida,

Ganin ya shigo hajaran-majaran yasa matarshi tamabyarshi, "mal lafiya, meya faru
naga ka dawo tun 'yanzu gashi ko azahar batayiba,
Mal Lawal bayaso yafad'i gaskiyar Al'amari dan kada mutane suyi Mashi dariya, sai
cewa yayi "gajiya nayi kuma jikina ba dad'i d'an dafamin ruwan d'umi inyi wanka,
cike da mamaki matar tace "ruwan dumi kuma malam 🤔, kaida idan kadawo daga gona
kake son ka watsa ruwan sanyi amma yau ruwan d'umi kake nema,

Aiko nan yarufeta da bala'i "keni banison shashanci, Idan zaki dafamin ki dafamin,
idan kuma bazaki dafaba ni in tashi in dafa da kai.........

Be ida rufe bakiba, Laraba tashigo gidan da sallama, mal Lawal naganinta jikinsa
yafara kyarma, yace "la......la....la...raba miya kawoki nan? Ba yanzu kikaje gona
kika sameni,

Cike da ladabi Laraba ta dur'kusa har 'kasa tace "wallahi baffa banje gonarkaba, ni
yanzuma daga gida nake, dan Allah baffa ka taimakamin da abinci yunwa nakeji,

Cike da tsoro baffa Lawal yace "bamu dafa ba, ki koma idan mun dafa zan kawo maki
har gida, jiki ba 'kwari Laraba tanufi hanyar fita daga gidan, matar baffa Lawal ce
taji wani irin tausayinta yakamata, ta kirata taje d'akinta ta d'auko mata wata
tsantsamar fura tace anshi kisha ko wannan ce kafin ayi abincin akawo maki, jiki na
'kyarma Laraba ta kar6a ta kafa kai ta shanye sannan ta ajiye kwaryar tace "nagode,
sannan tabar gidan zuciyarta cunkushe da ba'kin ciki da takaici.

Laraba kuwa daga gidan baffa lawal maimakin tayi hanyar gida saita yanki hanya
tayita tafiya cikin daji, saida tayi nisa da Gari, wani wawakeken rami ta iske
gabanta, nan ta tsaya tana kallon fad'in ramin da zurfinsa, take wasu zafafan
hawaye suka wankemata fuska, a fili ta furta "'kara in mutu da rayuwar ba'kin cikin
danake ciki, lokacin kuma taji kanta ya sara,idanunta sun rufe, bata ganin kome,
nan ta fad'i war-was gata gab da ramin, dan motsi kad"an zatayi ta ida afkawa ciki.

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°
Tafiya yake cikin had'ad'd'iyar motarshi 'kirar Camry mai ruwan sumunti, tu'ki yake
cikin kwanciyar hankali, cikin motar kuwa ba abunda ke tashi sai sanyin a,c daya
had'e da kamshin freshener, sai kuma 'kirar'ar sheik Abdurrahama sudais dake tashi,

Tafiya yake amma zuciyarshi na raya mashi abubuwa da dama, game da 'kauyen kwata-
kwata babu titi ko d'aya sai dai mutum yayita bi cikin jar 'kasa da burji,

Kamar ance yakai dubansa gurin, lnnalillahi yafad'a yayin da ya hango mutum kwance
'kasa, gab da wani wawakeken rami, da sauri yayi fakin din motarshi yafito, addu'a
yafarayi kafin yakai hannunshi gareta, saida ya tabbatar da sauran numfashi jikinta
sannan ya kinkimeta ya sata bayan motar shi,

Juya akalar motar yayi yakama hanyar komawa cikin gari, tafiyar awa ukku ta dadashi
da garinshi, asibiti ya wuce kai tsaye, da sauri aka amshi Laraba aka shiga wani
d'aki da ita domin duba lafiyarta.

Awon farko aka gano yunwace ke neman halaka ta, nan aka d'aura mata drip, sannan
akayimata Allaurai, bata farka ba amma likitan ya tabbatar mashi da lafiya lau babu
wata matsala zata iya tashi koda wane lokaci, saboda haka asamo mata abinda zataci,
dan tana tattare da yunwa kuma tana bu'katar abinci mai kyau.
🖊Zee Elkaseem
Mmn khady💋
[10/16, 8:11 PM] +234 816 616 9254: [25/08 8:21 am] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

2⃣7⃣to2⃣8⃣

🖊Motarshi yanufa a zuciyarshi yana tausayama halin da yarinyar take ciki, mintina
da basu wuce sha ukku ba suka sadashi da gidan iyayenshi, wani 'katon gida ne
had'adden gaske, bakin get yayi horn me gadi ya bud'e mashi get yashiga da
motarshi, gurin ajiye motoci ya ajiye motarshi, motocine gurin kusan guda shidda,
sai lokacin nagane ashe wacce naganshi ciki batada kyau, dan manya- manyan moticine
masu tsadar gaake ajiye gurin, wannan yafita da itane dan yasan yanayin garin da
zaya.

Hanyar da zata sadashi da ainafin cikin gidan yanufa, kai tsaye falon hajiyarsa
yanufa.

Wata dattijuwar mata ce zaune cikin falon, cikin shiga ta Alfarma, idonta sanye
cikin wani siririn farin glass, wanda da alama medical ne, hannunta ru'ke da Al
Qur'anic, tana nazari, gefe kuma wata 'kya'kyawar yarinyace wacce bata wuce shekara
sha biyarba, ita kuma ta maida hankalinta gun kallon TV, tashar sunnah tv take
kallo.

Sallamar yayan nata yasa tayi saurin kai dubanta gareshi tare da amsa sallamar,
tace "lah Yaya Mukhtar, ya akayi ka dawo yanzu, ko baka kai da tafiya bane, yace
"naje mana, amma ban kai ga isaba wata 'yar matsala ta maidoni, tace matsala kuma
Yaya, Tame?

"To tambai, wannan tamaboyoyi haka, kamar wata 'yar jarida, tace "hm Yaya Mukhtar
ai ko banzama 'yar jaridaba kasan abinda nake burin zama,
Yasan kullum burinta be wuce na tazama lawyer ba, murmushi yayi yace "Allah
taimaka, inaso ki shiga kitchen keda Uwani me aiki ku dafamin abinci, jallouf d'in
wake da shinkafa zakiyi, ayi amfani da hanta gurin girkin, dan bani bu'katar wani
kalan nama, sannan a dafamin ruwan zafi ahad'a kayan tea,

zatayi magana yayi saurin tarbarata "banison tambaya kiyi sauri ina jiranki yanzu,
haka Jidda tanufi kitchen a zuciyarta tana tinanin me Yaya zayayi da abinci yanzu
kuma harda kayan tea.

Sai da yagama da Jidda sannan yanufi inda mahaifiyarsa take, wacce duk abinda suke
shida Jidda tana jinsu, itama zuciyarta cike take da tambayoyi da dama gareshi.
Cike da ladabi ya isa gurin hajiyar tashi, yasamu guri ya zaune kusa da 'kafafunta,
yace "Hajiya barka da hutawa, cike da fara'a ta kalleshi tare da rufe Qur'anic dake
hannunta tace "yauwa, kafin tayi wata magana yace "nasan zakiyi mamakin ganina
yanzu, wata yar matsalace ta maidoni, nan ya kwashe yanda ya tsinci Laraba ya gaya
mata, take tausayin yarinyar yakamata, kuma tayi alwashin taimakamata.

Saida sukayi sallar magrib sannan suka nufi asibiti, Mukhtar ne ke driving, sai
Jidda dake zaune gefensa duk ta isheshi da surutu, sai Uwani me aike dake bayan
motar,

Jidda ta kalli yayan nata tace, wallahi yaya har na 'kagara inga yarinyar nan,
wallahi ta matu'kar bani tausayi, ko ina iyayenta suka barta, har yunwa na neman
halakata, kai wallahi mutanen 'kauye basuda hankali, wai sai mutum yayi zaune da
yunwa har sai tayi mashi lahani,

Mukhtar dai jinta kawai yake tanata zuba, be cemata uffan ba har suka iso asibitin,
Parking d'in motarsa yayi inda aka tanada dan ajiye motoci sannan suka nufi cikin
asibitin uwani na d'auke da kwandon da aka jero kayan abincin ciki.

Sun shiga d'akin da Laraba take, zaune suka isketa, tayi zuru da alama tafad'a
kogin tinani, saida sukayi mata sallama sannan ta dawo hayyacinta, binsu kawai tayi
da kallo dan su duka ba wanda tasani, jidda ce tafara magana, tace "Yaya wannan
itace yarinyar daka tsinta d'in, kai Amma ky'k'kyawa da ita, amma gaskiya mutanen
'kauye basuda wayo da har sukayi sakaci da wannan 'kya'k'kyawar yarinyar... Wata
uwar harara yayan nata ya daka mata, hakan yasa tayi saurin jan bakinta tayi shuru,

Sannan ya maida kallonshi ga uwani yace "Uwani gatanan ki bata abincin, Uwani da
tunda suka shigo take kallon Laraba, tana yaba irin kyawun da Allah ya zuba mata,
tace "to amma yakamata ta d'an watsa ruwa taji dad'i kafin taci wani abu, sai dai
kuma babu kayan da zata canja idan tayi wanakan, jidda tayi saurin cewa "yaya muje
gida in d'auko mata cikin kayana, Mukhtar ya gyad'a kai yace barshi kawai bari inje
in siyo mata, ya kalli uwani yace a taimaka mata tayi wankan kafin indawo, sannan
yafice daga d'akin.

Bayan fitarshi uwani tahad'ama Laraba ruwan d'umi ta kaita kewaye, ta gwada mata
yanda zatayi, dayake Laraba yarinyace mai nutsuwa batayi wani karanbani ba, yanda
aka gwada mata haka tayi, ta dade tana wanke jikinta da sabulu mai 'kamshi, wanda
rabon datayi wanka da ruwa ma har ta manta, sai da ta tabbatar da tayi fess sannan
tafito daga kewayen.

Bata dade da fitowaba mukhatar yashigo da wata 'katuwar Leda a hannunsa, ya mi'kama
Uwani, sannan yafita daga d'akin yabasu guri dan suji dad'in aiwatar da kome.

Jidda ce tayi saurin zazzage kayan tana dubawa, kayane kusan kala takwas duk na
kanti, wasu riga da siket wasu kuma dogayen riguna,
Wata doguwar riga jidda ta d'auko, kalar sararin samaniya daga gaban rigar anyi
mata kwalliya da duwatsu dark blue tace wannan zaki sanya, Laraba dai binsu kawai
take da ido, dan ita har yanzu batasan a ina take ba, ba musu ta 'kar6i rigar ta
sanya sannan jidda ta d'aura mata d'an kwalin rigar, wani irin kyau tayi duk da ba
wata kwalliya bace a fuskarta, jidda kasa yin shiru tayi tace "kinga yanda kikayi
kyau, wai miye ma sunanki, sai lokacin karaba ta iya bud'a Bak tace "sunana Laraba,
jidda tayi murmushi tace wallahi na d'auka larabci zanji kinyi, dan kwata-kwata
kinfi kama da jinsin larabawa, to amma miye asalin sunanki dan Laraba ba suna
bane...

Mukhatar ne yashigo da sallama, yakai dubansa ga Laraba, wani dum yaji gabansa ya
fad'i dan bacin yasan uwani da jidda suna d'akin da sai yace wannan ba yarinyar
daya tsinta bace, saboda wani masifaffen kyau datayi mashi.
Tambaya yayi taci abincin kuwa, Uwani tace "jira nake agama shirin sai in zuba mata
abincin, wata harara yayima jidda dan yasan kicifin tane, mutumin da beda lafiya
har wani shiri za'ayimashi.

Da kanshi ya had'a tea mai kauri Wanda yaji madara da Milo ya mi'ka mata.
Ba musu ta 'kar6a ta kafa kai ta shanye, dayake tanada bu'kata dama, sannan aka
zuba mata jallouf d'in wake da shinkafa wanda yaji kayan lambu da hanta, nan ma
taci amma kad'an kasancewar tean data sha yacika mata ciki.

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady💋
[10/16, 8:11 PM] +234 816 616 9254: [26/08 12:13 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

2⃣9⃣to3⃣0⃣

🖊sai bayan sallar isha'i sukayi niyyar barin asibitin bayan sun yanke cewa Uwani
zata zauna gurin Laraba, aiko itama jidda kafewa tayi dole sai an barta ta kwana
gurin Laraba, saida mukhtar yayimata fad'a sannan suka tafi, ranta yayi matau'kar
6aci dan an hanata kwana gurin Laraba,

Haka suka tafi tanata zum6ura baki ita a dole fushi take, dan ko surutun data
sabayima yayan nata yau batayiba tunda ya 6ata ranta,
Yana lura da ita yanda taketa cika tana batsewa, amma sai yayi kamar besan
tanayiba,
A haka suka iso gida, bakin get sukayi horn me gadi ya bud'e masu get suka Shiga,
gurin ajiye motoci yayi parking d'in motarsa, kafin ya gama gyara parking tafito
daga mortar tanufi cikin gida da gudu, tana zuwa falo bata taradda Hajiya ba,
saboda haka bedroom d'inta ta wuce kai tsaye, zaune ta isketa kan abin sallah tana
tasbihi, fad'awa tayi jikinta tana kuka,

Cike da mamaki Hajiya ke tambayarta "lafiya jidda meya faru, meya saki kuka ina
yayan naki,? Kafin ta bata amsa sai gashi yashigo, cikin ladabi yake gaisheda
hajiyarsa, sannan yace "Hajiya bafa wani abune yafaruba, kawai dan nace bazata
kwana asibiti bane shine take fushi,

Murmushi Hajiya tayi tace "haba Jidda yaza'a barki ki kwana, asibiti ayba gurin
zaman yaro bane, kibari idan Allah ya kaimu gobe tunda ba school sai mu tafi tare
nima zanje in gano yarinyar,

Haka Hajiya tayita rarrashinta har tasamu ta saki ranta, tayi murmushi tace "Hajiya
bakiga yarinyar ba wlh kya'k'kyawa da ita, ni naji dad'i nasamu 'kawa, Hajiya tayi
murnushi tace daga ganin sarkin fawa sai miya tayi za'ki, daga ganin yarinya sai
kice kinyi 'kawa,
Mudai iyakarmu taimako, kuma data samu lafiya ta warware zamu maidata ga iyayenta,
nasan yanzu duk inda iyayenta suke suna can hankalinsu ba kwance ba,

Jidda tayi saurin tashi daga kwancen datake kan cinyar Hajiya tace "dan Allah
Hajiya kada a maidata, inasonta inaso tazama 'kawata,
Hajiya bata cemata komeba sai murmushi kawai tayi, *(Yaro man kaza)* sai
lokacin Mukhtar yayi magana yace "kedai baki gajiya da shirme, ke yanzu kinaso
arabaki da Hajiya wasu su ri'keki,
ta turo baki tace to ayni hajiyata na sona bazata barni da yunwa ba,har in
kusa mutuwa wasu su tsinceni, harara yayi mata sannan yafita yabar d'akin.

'Dakinsa yanufa kai tsaye zuciyarshi cike da tausayin Laraba, shi kanshi yanda
jidda tafad'a hakane bayason rabuwa da Laraba, dan tsakanin wannan d'an lokacin
wani irin abu yakeji dangane da ita,

Da wannan tinanin yafad'a toilet ya she'ka wanka, sannan yafito ya canja kaya,
jallabiya yasa me gajeren hannu sannan yanufi babban falo, can ya iske Hajiya da
jidda kan dining suna niyyar cin abinci, shima kujera d'aya yajawo ya zauna kusa da
hajiyarsa, jidda ce ta zuba mashi tuwon shinkafa da miyar Alayyahu, sai 'kamshin
curry ke tashi,
Haka suka ci abincin kowanensu cikin nutsuwa da kwanciyar hankali, bayan sun
'karasa suka kora da kunun aya me sanyi, sannan suka ta6a fira

Sai gurin 'karfe goma sannan, sukayi bankwana, mukhtar ya wuce d'akinsa, jidda kuwa
d'akin Hajiya tanufa, Hajiya ta kalleta tace "kika biyoni nan d'akin naki kuma fa?
Cikin shagwa6a tace "Hajiya ki barni in kwana anan idan aka sallamo Laraba ta dawo
nan gidan sai mu koma d'akin nida ita kinga nasamu abokiyar fira, murmushi Hajiya
tayimata sannan ta canja kaya zuwa kayan bacci, itama jidda kayan baccin ta sanya
sannan suka haye katafaren gadon wanda yasha wani lallausan bedsheed, sukayi addu'a
suka shafe jikinsu.

Mukhtar kuwa koda ya koma d'aki tinanin Laraba ya zauna a kwa'kwalwarsa, cikin
zuciyarshi yari'ka ro'kon Allah sa iyayenta su yarda ta zauna tare dasu, dan shima
har ga Allah baya son rabuwa da ita, yarinya 'kya'k'kyawa amma dayake 'kauye ta
taso sukayi sakaci da rayuwarta har tana neman halaka.

Da wannan tinanin bacci yayi awon gaba dashi bayan yayi addu'a Ayatul kursiyyu da
qula'uzzai ya shafe jikinsa.

_```Waye Mukhtar```_?

Mukhtar Abass shine asalin sunanshi, haifaffen d'an garin katsina ne, a wata unguwa
me suna 'yan,shuni.

Mahaifinshi Alh Abass, mutum ne mai ilimin addini, kuma yana aiki dashi, dan duk
wani abu daya shafi addini yana fidda dukiyarshi yayi hidima da ita, shiyasa kullum
Allah ke 'kara bud'a mashi, kuma dama yana dukiya me yawa ga kuma taimakon na 'kasa
dashi da miskinai, ga fidda zakka duk shekara kamar yanda Allah ya hukuta.

sunyi auren saurayi da budurwa da matarshi wato Hajiya Zainab, bayan aurensu da
shekara ukku Allah yabasu haihuwa inda suka haifi namiji aka sanya mashi suna
Aliyu, har Aliyu ya shekara bakwai Hajiya Zainab bata kuma haihuwa ba, wata rana an
taso su Aliyu makaranta yafito bakin titi yana jiran driver yazo d'aukarsu wata
mota ta bankeshi, kafin akaishi asibiti rai yayi halinsa, Hajiya Zainab da Alh
Abass sunyi kukan rashin d'ansu, 'karshe suka ha'kura suka fawwalama Allah
lamuransu, kuma daga lokacin Hajiya Zainab bata kuma samun cikiba sai bayan shekara
biyu tasamu cikin mukhtar, bayan an haifeshi ne da shekara bakwai aka haifi jidda,
wanda daga ita hajiya Zainab bata kuma haihuwaba.

Jidda nada shekara ukku Allah yayima mahaifinsu Alh abass rasuwa bayan yayi fama da
gajeruwar rashin lafiya,

Bayan rasuwar Alh Abass da shekara d'aya 'yan'uwan Hajiya zainab sunso takoma
garesu amma sai tace sam bazata komaba zata zauna ta ri'ke yaranta dan bataso ta
dorama wani nauyinsu.

Haka Hajiya Zainab tacigaba da kula da karatun yaranta da tarbiyarsu, amma haka be
hana 'yan,uwan Alh Abass taimakonsuba, dayake mahaufinsu mutum ne mai taimakon
'yan,uwa.

lokacin da muke yanzu, mukhatar yazama cikakken d'an kasuwa, dan sana'ar babansa
kenan kafin ya rasu, hakan yasa mukhtar karantar business, ga kuma kiyo da suke a
gidan gonarsu da mahaifinsu ya bar masu gado, lokcin da mukhatar ya tsinci laraba
gidan gonar tasu yanufa, sai Allah ya had'ashi da ita.

Jidda kuwa yanzu take junior secondary, j.s.s 3 bana zasu zana jarabawa.

*_WANNAN SHINE TAKAITACCEN TARIHIN MUKHTAR_*

🖊Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:11 PM] +234 816 616 9254: [26/08 9:30 pm] 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

3⃣1⃣to3⃣2⃣

🖊 Haka Uwani tacigaba da kula da Laraba, yayinda mukhatar kullum sai yayi zuwa
yakai shidda asibitin, dan bayaso anemi wani abu baya nan, hajiyar Mukhtar kuwa sau
ukku tana zuwa ganin Laraba, jidda kuwa 'yar rigimar kullum nan take yini, kuma sai
anyi daga da ita gun komawa gida, dan kullum kafewa take sai ta kwana,

Satin Laraba d'aya asibitin taji sauki sosai, ta'kara fari tayi wani fresh, dan har
'yar 'kiba tayi, tana samun kulawa sosai daga malaman asibitin zuwa ga mukhtar sai
kuma Uwani me aiki itama tana bakin 'ko'karinta.

Yau Likitan dake dubata yazo round nan ya duba jikin uwani ya tabbatar da kome
normal, sannan yarubuta masu sallama.

Mukhtar ne ya d'aukesu a mota, jidda ce gaban mota kusa da yayanta, yau dai farin
ciki fal a zuciyarta, dama kullum addu'a take a sallamo Laraba 'kawarta ta dawo
gidansu da zama,
uwani da Laraba kuwa bayan motar suke sunata sauraren jidda da keta zuba uban
surutu.

Dai-dai get d'in gidan sukayi horn me gadi ya bud'e masu get suka shiga,
Tunda sukazo Laraba kebin gidan da kallo, saboda tsananin 'kyawunsa, cikin
zuciyarta tace _"Anya ba mafarki nake ba, dan bani tinanin akwai irin wad'annan
gidajen nan duniyar da muke_

Niko nace *Hmm Laraba kenan sai ma kin shiga gidan zaki tabbatar da ba irin duniyar
da kk sani bace, (wani hanin ga Allah baiwa ne)*

Jidda ce takama hannun Laraba sukayi cikin gida, wani irin tsoro yakama Laraba dan
ganin 'kawatuwar falon, kai lallai dama ashe akwai masu irin wannan jin dad'in a
duniya, haka kawai take fad'a a zuciyarta.

Cike da murna da sakin fuska Hajiya ta tarbesu tanayimasu sannu da zuwa, jidda kuwa
murna yau gurinta bakin har ya'ki rufewa, da kanta ta zaunar da Laraba kan kujera
tace "Zauna 'kawata ki huta kafin anjima kiyi wanka,
Laraba dai kallon mutanen kawai take, duk abinda sukace shi take yi, tazama tamkar
ra'kumi da akala,

Bayan sallar azahar suka zauna kan dining suna cin abinci, jidda ce ta matsama
Laraba ta zauna suci, amma ita duk d'arare take ba kamar idan da mukhtar gurinta
dan wani irin kwarjini yake mata.

Bayan sun kammala ne jidda ta kama hannun Laraba tace 'kawata zo muje ciki kiyi
wanka ki canja kaya, ba musu Laraba tabita zuwa d'akinta,
Toilet taje ta had'a mata ruwan wanka, tare da zuba mata turarurrukan wanka masu
'kamshi gaske, sannan tazo ta kama hanunta ta kaita har toilet ta gwada mata yanda
zatayi, sannan ta jawo mata 'kyauren tafito tana jiran ta.

Laraba ta dad'e tana dirje jikinta a kewaye, kafin tafito d'aure da zanin atamafa
jikinta, dan 'kin yarda tayi da d'aura tawul, dan bata ma san yanda zata d'aura
shiba.

Jidda tace "harkin fito, ta kamo hannunta zo inyimaki kwalliya irinna larabawa,
laraba tayi murmushi tace " Hmm jidda kenan'har wata kwalliyar larabawa akeyi,
jidda tayi dariya tace kedai bari kigani idan nayimaki ke kanki sai kin kasa gane
kanki, murmushi kawai Laraba tayimata, dan abun jidda har mamaki yake bata yanda
take nan-nan da ita, tun batayi mata magana har tad'an fara sakin jiki tana maida
mata amsa idan tayimata.

Haka jidda ta zaunar da Laraba gaban mirror tafara d'and'asa mata kwalliya, make-up
tayi mata sosai, fuskar nan tafito ta larabawan sak yanda jidda ke fad'a, dan ba
'karamin kyau Laraba tayiba, dan koda ta kalli fuskarta a madubi kasa sheda kanta
tayi, in baccin ma jikinka jikinka ne da Laraba tace ba fuskarta bace a madubin.

Jidda kanta tsayawa tayi tana kallon kyawun da Allah yayima Laraba, kasa yin shuru
tayi tace _"tsarki ya tabbata ga ubanjin daya halitta wannan 'kya'k'kyawar sura_,
juwowa Laraba tayi dan ganin wace kya'k'kyawar sura ce jidda ke fad'i amma bataga
kowaba sai jiddar hakan yasa ta tabbatar da ita jidda take.

Murmushi tayi tace, kai jidda wallahi baki gajiya da zaualaya, yanzu nice kikema
wannan zuzutawar, bayan nasan kin fini kyau nesa ba kusa b....... Jidda tayi saurin
sa hannu ta rufe bakin Laraba tace, bari kada kiyi sa6o, inani ina had'a kaina
dake,

Wadrope d'inta tanufa ta d'auko ma Laraba wasu riga da zani na less cikin kayanta,
tace "amshi ki saka wannan nasan zeyi maki 'kyau.

Laraba ta gyad'a kai tace "jidda da kinbar kayanki na sanya cikin wanda Yaya
Mukhtar ya siyomin, tunda akwai ma wanda ban sanyaba har yanzu,

Jidda ta harareta cikin wasa tace banison haka, ay nice nace ki sanya idan kuma
bazaki sanyaba to ki gayamin, bata jira me Laraba zata fad'aba tashige toilet domin
itama ta watsa ruwa.

Haka laraba ta rin'ka juya less d'in a hannunta tana yaba kyawunsa, dan ko a
mafarki bata ta6a tunanin zata sa irin wannan kayanba, Allah mai yi yanda yaso da
bawanshi, wasu siraran hawaye suka zubo daga idonta dan tunowa datayi da Innarta,
tasa hannu tayi saurin gogewa dan kada jidda tafito taga tana kuka ta isheta da
tambaya, dan tagama karantar halin jidda ahegen surutu gareta, ga kuma tambayar
tsiya kamar tamabai......

🖊Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:11 PM] +234 816 616 9254: [27/08 8:02 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

3⃣3⃣to3⃣4⃣

🖊Bayan sun kammala shirinsu tsaf, Laraba ta sanya less d'in da jidda tabata ta
Sanya, aiko less d'in yayi masifar yimata kyau ya zauna d'as ajikinta, itama jidda
less ta sanya tayi kyau sosai, ta kalli Laraba tace kin san wani abu,? Laraba ta
gyad'a kai Alamar a'a, Jidda tace wannan kwalliyar gurin Yaya kawai yakamata muje
yaga yanda kikayi kyau, 'kilama idan ya ganki baze ganekiba,
Laraba tayi murmushi tace, "sai dai idan wata fuska na canja, to sannan na yarda
baze ganeniba, amma fuskar da yayi kusan sati biyu yana tare da ita yaushe dan yau
d'aya kinyi min kwlliya kice baze ganeniba.

Jidda ta kyal'kyale da dariya tace "lnda ba 'kasa nan ake gardamar kokowa, inaji ai
yayan yana gidan ba inda yaje saboda haka muje araba gardama,

Laraba ta zaro ido tayi dariya tace "kefa dad'ina dake jidda baki gajiya da shirme,
to idan munje muce masa me?

Jidda tayi dariya tace kedai kibar komi a hannuna, yau zaki tabbatar ma kanki
tsananin kyawun da kikayi idan ni baki yarda da maganata ba,
bata jira me laraba zata fad'a ba ta kama hannunta tace "zo muje, laraba ba yanda
zatayi da jidda haka yasa tabita kawai, cike da mamakin shirme irinna jidda..

A falo suka iske Hajiya tana hutawa, suduka suka iso gareta suka rissana sukace
"barka da hutawa, ta kai dubanta garesu, wani irin fad'uwar gaba Hajiya taji dan
ganin wani irin kyau da Laraba tayi mata, cikin zuciyarta tace *Allah sarkin
halitta lallai Allah ya ajiye kyau tattare da Laraba ga nutsuwa da sanin ya kamata*

Cikin fara'a Hajiya ta amsa "yauwa 'yan matana, wannan kwalliya haka, kamar 'ya'yan
saraki, murmushi laraba tayi cike da jin kunya, Jidda kuwa dariya tayi tace "Allah
Hajiya laraba tafi 'ya'yan sarki kyau, murmushi kawai Hajiya tayi masu,

Jidda takama hannun Laraba, suka nufi hanyar fita daga falon, Hajiya tace "ina zaku
haka,? Jidda tace zamu gurin Yaya ne, Hajiya tace to 'yan gidan Yaya, idan kunje
kuce ina nemansa yanzu, kutaho tare, tare suka had'a baki suka amsa da "to.

A lambun gidan suka tarar dashi, yana zaune kan wasu fararen kujeru, gabanshi kuma
wani 'karamin table ne d'auke da laptop d'insa yana danne-danne, gefe kuma fresh
milk ne da cup d'in glass, besan isowarsu ba saboda haka jidda tace ma Laraba
"kawata ki tsaya bayan wannan flower so nike inba Yaya mamaki, laraba tace "wane
irin mamaki zaki bashi kuma? Jidda tayi saurin rufe mata baki tare da jan hannunta
ta turata bayan wata flower, sannan ta isa ga yayanta wanda hankalinshi na kan
computer shi, bema san sun zo gurin ba.

Sallama jidda tayi mashi, d'ago kanshi yayi yakai dubanshi gareta sannan ya amsa
sallamar, murmushi yaga tanayi, saboda haka yasan akwai magana tattare da ita,
hakan yasa ya tambayeta "ya dai 'kanwata? Ta 'kara fad'ad'a murmushin dake fuskarta
tace Hajiya ce ta aikoni gurinka, amma kafin in gaya maka sa'kon inaso in baka
*surprise* yayi murmushi yace mamakin me za'a bani kuma? Tace kaidai ko miye
zakagani amma ka rufe idonka tukun.

Yasaba da shirmen 'kanwarsa saboda haka beyi musuba yasa hannu ya rufe idonsa, yana
jiran yaga yau kuma da wane shirman tazo mashi.

Tana ganin yarufe idonshi tayi saurin zuwa inda ta 6oye Laraba ta kamo hannunta
suka nufi inda Mukhtar yake zaune.

Laraba nagani haka tarin'ka bin jidda kamar ra'kumi da akala, saida sukaje gaban
mukhtar sannan tace "Yaya bude idonka,

Ahankali ya sauke hannuwanshi daga idonshi ya saukesu kan laraba, kallonta yacigaba
dayi, cikin zuciyarshi yace *tsarki ya tabbata ga ubangijin daya halicci wannan
'kya'k'kyawar yarinya, lallai Allah ya ajiye kyau a nan* .

Laraba ta kula da yanda mukhtar ya tsareta da ido hakan yasa taji duk ta tsargu,
takama hannun jidda tana janta Alamar tazo su tafi, dariya jidda tayi, wacce ta
dawo da mukhtar daga dogon tinanin dayake, tace "Yaya dama hajiyace tace kazo yanzu
tana nemanka.

Basu jiran amsarshiba suka wuce cikin gida, Jidda na dariyar yanda yayanta ya tsare
Laraba da ido, Ita kuwa Laraba bata ji da'din hakan ba amma bata nuna ma jidda taji
haushi ba ko kadan.

_*Kuyi ha'kuri da wannan 👆🏻 yau ina busy be*_


3⃣5⃣to3⃣6⃣ very 🔜
🖊Zee Elkaseem
Mmn Khady💋
[10/16, 8:11 PM] +234 816 616 9254: [28/08 12:50 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

3⃣5⃣to3⃣6⃣

🖊 Laraba na ri'ke da hannun jidda suka shigo falon, suka samu guri suka zauna,
basufi minti biyar da zama ba sai ga yayan su yashigo, cike da ladabi ya zauna kan
kujerar dake facing d'in Laraba ya zuba mata idanunshi masu tsananin kwarjini yana
kallonta, itako ta lura da yanda yake kallonta hakan yasa duk ta daburce.

Hajiyace tayi gyaran murya tare da 'kara gyara zamanta tace "am mukhtar abinda yasa
nace akira mani kai shine kan maganar Laraba,
Wata irin fad'uwar gaba laraba taji dan jin maganar da Hajiya tayi, a zuciyarta
tace _"shikenan nasan lokacin barina gidannan yayi, dan nasan muddin suka San
Matsala ta bazasu kuma zama daniba_.

Hajiyace ta maidota daga dogon tinanin datake, tace "Laraba, laraba ta d'ago
fuskarta ta kalli Hajiya, sannan t sadda kanta 'kasa tana kallon kafet d'in dake
malale tsakiyar falon.

Hajiya tacigaba da magana "kamar yanda kika Sani mun taimakeki kuma Alhmdulillahi
kin samu lafiya kin warware, kuma nasan bazaki rasa sanin inda 'yan,uwanki da
iyayenki sukeba, saboda haka inaso ki sanar damu ke wacece? Kuma miye ya jefaki
cikin mawuyacin halin da shi mukhtar ya tsinceki a ciki?
Saboda munaso mu maidake gurin iyayenki.

Shiru Laraba tayi takasa ko motsi dan jin tambayoyin da hajiyar ta jero mata lokaci
guda, wasu zafafan hawaye suka zubo daga idanunta, batada niyyar d'ago fuskarta,
saida Hajiya tayi mata magana karo na biyu tace "laraba ke muke sauraro.

Laraba ta d'ago da fuskarta wacce tayi sharkaf da hawaye, ganin haka yasa
hankulansu tashi su duka, cike da damuwa jidda ke rarrashin Laraba tasa hannu tana
goge mata hawaye "kiyi ha'kuri 'kawata ki gayama Hajiya abinda ta tambayeki, ni
nasan hajiyata mai tausayice zata taimaka maki a kan abinda kike Neman taimako,
inshaAllahu.

Haka jidda tayita rarrashinta da kalamai masu taushi, hartayi shuru sannan ta goge
hawayenta tafara basu Labarinta, kamar haka:

_*Sunana Fatima amma amfi kirana da laraba kamar yanda kuka Sani, mahaifiyata yar
Asalin 'kasar camaron ce, sun h'ad'u da babana ne lokacin yana zuwa fatauci can
'kasar.*_

_*Mahaifina kuma d'an nan cikin garin karsina ne a wani 'kauye dake 'karamar
hukumar malumfashi me suna 'kurungafa' Allah yayima mahaifina rasuwa tin ina 'yar
shekara ukku a duniya, kamar yanda naji mahaifiyata tana fad'a,*_

_*Haka yasa muka taso cikin wahala nida mahaifiyata, kasancewar batada kowa a nan
'kasar shikuma babana su biyu ne gurin iyayensu daga shi sai 'kaninsa baffa Lawal,
baffa Lawal mutum ne wanda bashida taisayi ko kad'an hakan yasa baya taimaka mamu
da koda ruwan sha,*_

_*Haka mukacigaba da rayuwa nida mahaifiyata, yau da dad'i gobe babu har nakai
shekara shidda lokacin kuma mahaifiyata tasakani makarantar bokon dake 'kauyenmu,
bayan na kammala aji shidda ne samarin 'kauyen sukayo ca Kowa nason Neman aurena,
lokacin inada shekaru sha ukku a duniya*_

_*An tsaida wani saurayi matsayin wanda baffa lawal ya amince dashi, dan baffa
Lawal Isa da ta'kama ba wanda bayayi mamu amma kuma idan neman taimakone sai ya
nuna be sanmu ba, ana gab da bikinane Allah yayima mahaifiyata rasuwa, Al'amarin
daya sakani cikin mayuwacin hali, dan bayan rasuwarta da sati biyu saurayin dazan
aura ya aiko a maida mashi duk wani abu daya kawo gidanmu yafasa aurena, nan fa
tashin hankalina ya 'karu.*_

_*Baffa Lawal da kanshi yazo har gida yacimani mutunci, yana cewa ai nasan abinda
nayimashi yace yafasa aurena, saboda haka tsinke baze barmin ba cikin kayan da
yaron ya kawo, inaji ina gani ya tattare kome yasa kai yabar gidan, haka na zauna
na had'e kai da gwiwa ina kuka ni 'kad'ai cikin gida babu me rarrashina, dan dama
tunda mahaifiyata ta mutu yazamana ni d'aya ke kwana gidan, tun ina jin tsoro har
zuciyata ta saba*_

*_Ban fuskanci babbar matsalaba sai da na wayi gari banida abinda zanci, yunwa
tayimani mugun kamu wanda har wani matsanancin ciwon ciki ya kamani, hakan yasa na
lalla6a naje gidan baffa Lawal ko ze taimakamin amma sai yayimin korar kare,
lokacinne na 'kudiri niyyar kashe kaina ta hanyar fad'awa wani 'katon rami dake
nesa kad'an da 'kauyenmu, dan lokacin na 'kwammace mutuwa da halin da nike ciki, ga
ba'kin cikin rayuwa ga ALHININ rabo da iyayena....._*

Wannna shine labarina, laraba ta fad'a tana goge hawaye,

Jidda ma kuka take saboda tusayin larabar, "Lallai laraba kinsha gwagwarmaya, Allah
Sarki, ta fad'a tana sharar kwalla.

37to38 very 🔜💃🏻


3738

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:11 PM] +234 816 616 9254: [28/08 5:07 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

3⃣7⃣to3⃣8⃣

🖊 Haka jidda takama hannun Laraba suka wuce d'aki, tashiga rarrashinta "kiyi
ha'kuri Laraba ki d'auki rayuwar da kikayi a baya amtsayin jarabawa, kuma kiri'ka
yima iyayenki Addu'a Allah kai haske kabarinsu, kuma ina me tabbatar maki bazamu
gujekiba, zaki zauna damu har 'karshen rayuwarki inshaAllah, Laraba tasa hannu ta
goge hawayen dasuka zubo a kumatunta tace "ko yanzu nabar gidannan nasan kunyi min
hallacin da 'kanin mahaifina yakasa yimin wanda shi kad'ai yarage a dangina, nagode
Allah saka maku da Alkhairi.

Jidda tace ba kome laraba ki d'aukeni a matsayin 'yar'uwarki Hajiya kuma a matsayin
mahaifiyarki Yaya mukhtar kuma a matsayin yayanki, inshaAllah bazaki 'kara
fuskantar Matsala a rayuwarki ba.

Haka jidda tayita rarrashin Laraba har zuciyarta tayi sanyi, ta goge hawayenta,
Nan jidda tacigaba da bata labarai kala-kala tun tana jinta kawai harta biye mata
ta saki jiki tana dariya kamar ba itaba.

A falo kuwa Hajiya ta kalli mukhtar jiki a sanyaye tace "kaji abinda yarinyar nan
tafad'a ya ka gani, Mukhtar Wanda shima duk illahirin jikinsa yayi sanyi dan jin
labarin Laraba, yace Hajiya kawai abinda ya kamata shine mu ri'keta ta zauna
gurinmu muga abinda Allah zeyi.

Hajiya tace hakane, zatacigaba da zama gurinmu kuma zaka samo mata form a
islamiyyar su jidda suri'ka zuwa tare.

Sannan idan su jidda zasuyi Exam ayi 'ko'kari asakata ciki, tafara daga s.s.1 tunda
kaga yanzu takai kimanin shekaru sha hud'u baze yiyu asata j.s one ba tayi girma,
sai asamo Wanda zeri'ka mata lesson a gida kafin sufara karatun.

Cike da jin dad'i mukhtar ya amsa ma Hajiya, zuciyarshi cike da farin ciki, dan ko
kad'an dama bayaso ayi maganar maida Laraba garinsu.

Jidda Kuwa dataji hukuncin da Hajiya ta yanke na zaman Laraba gidansu murna
tashigayi hada tsalle.

Laraba kuwa cikin ranta tana tsoron ranar da zasu gane gaskiyar labarinta data 6oye
masu, dan tasan muddin suka gane to zasuyimata korar kare.

_```BAYAN SHEKARA UKKU```_

Wasu kyawawan yan mata na hango su biyu tsaye bakin titi kusa da school d'insu
sanye suke cikin uniform d'insu rigar chek pink, sai wando brown, sai 'yar karamar
abayar da bata ko rufe hannuwansu ba, kafafunsu sanye cikin brown sandals sai farar
safa computer, sunyi kyau sosai kamar 'ya'yan larabawa.

Wata ba'kar mota 'kirar 4matic tayi parking gabansu, sannan matashin dake cikin
motar ya sauke glass d'in motar yakai dubansa ga 'yan matan, da gudu 'yan matan
wad'anda basu wuce shekara sha bakwai ba suka nufi motar suka shige, kowace baki
ya'ki rufewa saboda farin ciki.
Sun fara tafiya a motar jidda dake gaba, kusa da yayan nata ta juyo ta kalli
Laraba ta kashe mata ido, murmushi kawai Laraba tayi mata dan tasan jidda da
surutun tsiya, yanzu haka akwai abida takeson fad'a...

Bata gama tunanin datakeba, ta tsinkayi muryar jidda tana cewa "Yaya bakayi mana
congratution ba yau munyi graduated, ya juyo ya kalleta yace tun nan a mota zanmiki
congrat d'in, to ke bari inyimaki amma Fatimana sai munje gida zan mata, yafad'a
yana kallon Laraba yakashe mata ido, itako wata irin kunya ke kamata idan yakirata
fatimarsa, jidda kuwa cewa tayi eh na yarda ayimin anan, ya juyo ya kalleta yace
"lna tayaki murna 'kanwata, yanzu saura musha biki keda Usman, cike da jin kunya
jidda tarufe idonta, daga lokacin bata 'kara magana ba, dan wata irin kunyace
takamata, Usman shine saurayin datake masifar so kuma shine Wanda zata aura, dan
maganar harta kai ga iyaye, dama makaranta kawai ake jira ta kammala.

Laraba kuwa na kula da ita, saboda haka tari'ka kallonta ta madubin motar tana mata
dariya 😜 itakuma girgiza kai tayi, Alamar zasu had'e........

Haka suka Isa gida cike da farin ciki, bakin get sukayi horn megadi yabud'e masu
get suka shige, sukayi parking, da gudu suka nufi cikin gida suna kiran Hajiya,

Hajiya na bedroom tajiyo haniyarsu da sauri tafito tana masu sannu da zuwa, nan
suka zauna anata labarin makaranta, Hajiya tayimasu congrat, sukaji dad'i har cikin
ransu.

Sai lokacin mukhtar yashigo fuskarshi d'auke da fara'a yasamu guri ya zauna,
lokacin kuma Hajiya takoma d'akinta dan cigaba da aikin datake,

Tasowa yayi yazo gaban laraba, ya du'ko inda take zaune har numfashinsu na gauraya
dana juna, hannu yasa aljihu yaciro wata had'ad'iyar waya mai kyan gaske, kirar
tecno H³ yami'ka mata, tare da cewa *"Congratulation on your graduation Fatima na*
cike da jin kunya ta amsa tace *Thank you very much, My Brother*.

Duk abinnan jidda na zaune tana kallonsu, a zuciyarta tagama yarda yayanta son
laraba yakeyi.

juyawa yayi yanufi hanyar barin falon, da sauri jidda dake zaune tana jiran ami'ko
mata tata wayar tayi saurin kamo hannunshi, cikin shagwa6a tace "Yaya nifa, cike da
zaulaya yace "kikace iyimaki murna tun a mota, kuma nayi maki.

Cikin shagwa6a tace ay ba cewa nayi kada kabani phone ba, dariya yayi sannan ya
fiddo wayar itama ya mi'ka mata iri d'aya data Laraba.

Da gudu tanufi inda laraba take tana tsalle,......

39to40 Very 🔜 💃🏻
3940

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:11 PM] +234 816 616 9254: [29/08 7:32 am] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

3⃣9⃣to4⃣0⃣

🖊maganar Auren jidda da Usman d'inta ta kankama, dan har ansa ranar biki wata
hud'u, jidda kuwa dad'i har cikin zuciyarta, amma takaicinta d'aya yanda Laraba
bata kula maza ko kad'an, dan akwai wani abokin Usman daya nuna yana sonta kamar
zeyi zauci amma ta bad'e ido toka ta nuna ita bata soyayya, tome hakan ke nufi?
Amma ko badad'e ay dole tayi aure tunda tsarin gidansu ne mace bata wucewa gaba da
karatu daga secondry, barantana tace karatun tasa gaba.

_```Bayan kwana biyu```_

Yaune Hajiya ta tara 'ya'yan nata tana masu magana, kamar haka "Alhmdlh ke jidda
banda ke cikin wannan fad'an da zanyi, ta maida kallonta ga Laraba tace "Fatima
saboda me bakison ki fidda miji kiyi aure? Bata jira abinda laraba zata fad'aba
tacigaba da magana "ita mace duk yanda take jin dad'i gidan iyayenta to gidan
mijinta yafishi, kome duk Kyan mace da dukiyarta ko mulkinta darajarta shine d'akin
mijinta.

Haka Hajiya taketayi masu nasiha, suduka sunyi kasa'ke suna sauraronta, shikuwa
mukhtar tsoro yake acikin zuciyarshi kada Fatimarsa tafad'i wani namiji tace shine
wanda ta tsaida a matsayin miji, bayan shekarun daya d'auka yana fama da dakon
soyaryyarta a zuciyarsa.

Hajiya tayi gyaran murya tacigaba da cewa "kodayake ga yayanku nan shima tun yaushe
nake fama dashi akan ya fiddo mata yayi aure amma yayi biris da maganar, amma 'kila
so yake insamo wata koda 'yar Almajirace in had'ashi da ita, jidda ta kyalkyale da
dariya, tace "kai Hajiya Yaya yafi 'karfin Almajira, itama hajiyar dariya take tace
to kada ya fiddo matar kusha mamaki daga ke har shi,

Sai lokacin mukhatar ya d'ago da idonshi wanda suka kad'a zuwa ja, ya kalli
hajiyarshi cike da jin kunya yace "Hajiya ayni na dad'e da samun matar da zan aura,
sai kuma ya sadda kanshi 'kasa yana shafa kanshi da Alamar kunya tattare dashi,
Hajiya tace "uhum ina saurarenka wace mai sa'ar ce wannan, shiru yayi yakasa furta
kome.

Jidda tace Allah Hajiya nasan ko wacece, Hajiya ta harareta "ke banison shirme ina
sauraronka, "dama...hm..dama ba wata bace sai Fatima, cike da jin kunya yake
maganar.

Jidda tace dama nasan wlh Hajiya Yaya ya dad'e yana son Laraba, Hajiya tace "to
uwar surutu wai waya sanyo bakinki cikin maganar nan, tayi saurin sa hannu tarufe
bakinta 🙊.

Cike da farin ciki fuskarta kuma d'auke da fara'a tace kai amma naji dad'in wannan
abu, ta kalli laraba wacce tunda mukhatar ya furta Kalmar so gareta duk illahirin
jikinta kyarma yake.

Haka Hajiya tagama dasu ta sallamesu, tawuce d'akinta, Shima Mukhtar d'akinsa ya
wuce zuciyarshi cike da farin ciki.
6angaren laraba kuwa tun lokacin da Mukhtar ya furta Kalmar so gareta tayi sukuku,
kamar marar lafiya, jidda na kula da halin datake ciki takan tambayeta ko lafiya,
sai ta 'ka'karo murmushin 'karfin hali tace mata ba kome, itakuma jidda sai
tacigaba da tsokanarta tana cewa amaryar yayanmu, Laraba sai dai tayimata murmushi
amma ita kad'ai tasan abinda takeji a zuciyarta, dama ranar data dad'e tana gudun
zuwanta kenan, dan dama ta dad'e da lura da take-taken mukhtar na sonta, amma ba
kome dole ta samarma kanta mafita, bawai son mukhtar ne batayiba, dan ko itace ta
d'aurema butulci gindi a duniya bekamata tace bata son mukhtar ba, matsalarta d'aya
shine abinda yabarota daga 'kauyensu, mutum nawa suka mutu dalilin aurenta, tabbas
tasan idan mukhtar yadage akan aurenta shima 'karshen rayuwarsa yazo, wasu irin
hawaye masu rad'd'i suka zubo daga idonta tasa hannu ta goge, duk abinnan bata
yarda ta nuna damuwarta fili dan kada mutanen gidan su gane.

_```Bayan wata d'aya```_

Soyayya me 'karfi ta 'kulle tsakanin mukhatar da Laraba, wacce a yanzu ta canja


suna takoma sunanta na Asali wato *Fatima*

Ranar ne kuma Hajiya takira Laraba tace mata, yakamata ki bada address d'in baffa
Lawal saboda za'a tura magabatan mukhatar suje neman aure.

Laraba cike da damuwa da far gaba tace "Hajiya kibari da safe zan bada yanzu kaina
yana min ciwo, Hajiya ta tausaya mata tace "eyyah Allah sauwa'ke to kisha magani
kafin ki kwanta kinji, tace "to, sannan tanufi d'akinsu zuciyarta cike da tunani
kala-kala, *gaskiya bekamata ta sakama mutanen nan da sharri ba, yanda suka
d'auketa amatsayin 'ya suka ri'keta suka nema mata gata wanda ko a mafarki batayi
tunanin samun irinsaba, gaskiya dole tasamoma kanta mafita*

Haka ta isa d'akin ta iske jidda tana chat da Usman d'inta tana dariya ita kad'ai
kamar mahaukaciya, laraba ta kalleta batayimata magana ba ta haye gadon tayi
kwanciyarta.

Jidda ta kaimata duka, "ke yau baki chat da yayana, nasan yana online yana jiran
zuwanki, Fatima tayi wani d'an guntun tsaki ta 'kara gyara kwanciyarta tace "kaina
ne yakemin ciwo nasha magani bacci zanyi, cike da tausayawa jidda ta dafa kanta
tace "Allah sauwa'ke, itama sai taji chat d'in yafita ranta haka sukayi sallama da
Usman yanata magiyar kada ta tafi ta barshi, tace "kayi ha'kuri sister d'inace ba
lafiya bazanji dad'in yin chat d'ina, yace "Allah sauwake sukayi sallama.

Itama jidda kwanciya tayi bayan tayi addu'a tashafe jikinta, sannan tayima Fatima
addu'ar dan ta lura da lokacin data kwanta batayi addu'ar ba.

Duk abinnan Laraba na jinta dan ba bacci tayiba, tunanine kala-kala cikin
zuciyarta.

Jidda bata dad'e da kwanciyaba bacci yayi awon gaba da ita, haka laraba tayita juyi
kan gado bacci ya gagari idanunta, wayarta ta d'auko ta duba 'karfe 1:58 am na
dare, a zuciyarta tace yanzu ne yakamata in samoma kaina mafita, dan muddin nasan
idan nabari mutanen nan sukaje 'kauyenmu sunan dana 6oye masu nawa na *mayya* zai
bayyana.

Saboda haka ahnakali ta tashi cikin sand'a ta d'auko site bag d'inta ta bud'e
wadrope ta d'auki kaya kala 2 sannan ta cire rigar baccin jikinta ta Sanya wata
doguwar riga ta atamfa sannan tasa wando legis daga ciki, sannan ta Sanya wata 'yar
'karamar hijab, ta d'au takalminta a hannu, ta lalla6a tayi sa'ar barin gidan
batare da Kowa ya gantaba kokuma yaji motsinta.
Bakin titi ta tsaya ta 'karema unguwar kallo bakajin kome sai kukan maguna da
karnuka, da tsintsaye, haka ta yanki hanya tacigaba ta tafiya, zuciyarta cike da
tsoro.......

41to42 Very 🔜💃🏻


4142

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:11 PM] +234 816 616 9254: [31/08 8:21 am] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_written by_
*_Zee Mmn khady_*😘

4⃣1⃣to4⃣2⃣

🖊 Tafiya take batare da tasan inda zata dosa ba, ta d'anyi nisa kad'an da gidan
zuciyarta cike da tsoro, sai tajiyo Alamar tafiyar mutane bayanta suna tafiya suna
magan-ganu wanda bata iya jiyo abinda suke cewa, saboda suna d'an nesa kad'an da
ita, hakan yasa zuciyarta kara tsorata, tayi maza ta 'kara sauri cikin sa'a tayi
karo da wani gida da aka fara ginawa amma ba'a karasaba, aiko tayi saurin shigewa
ciki dan ta 6uya, da sauri ta shige wani guri a cikin gidan wanda da Alama d'aki ne
amma ba'a karasaba dan ko rufi ba'ayiba, gidan dai kamar kango ne dan duk illahirin
gidan ba 'kofar da aka sanyama 'kyaure, sai uwayen karikitai da Shara a cikinsa.

Tana cikin kangon gidan data 6uya 'kirjinta na dukan tara², sai ji tayi wad'annan
mutanen data 6uya dominsu sun iso gurin, jitayi sun tsaya bakin 'kofar kangon gidan
data 6uya suna magana, muryar guda taji yace "gaskiya nifa na gaji da abinda
mutuminnan yake samu muna aykatawa, kawai hakanan yasa muri'ka kawo mashi 'ya'yan
mutane yana 6ata Masu rayuwa.

Gudan yayi dariya, cikin wata muguwar murya marar dad'in sauraro yace "nikam bazan
ta6a barin wannan sana'ar danikeba, dan in baccin ita ina zamu ri'ka samun 'kudin
da muma zamuji dad'in rayuwarmu, haba baba, kazo muje kawai mucigaba da neman
abinda ya fiddo mu, gudan yace to yanzu ina zamu nufa? Kasan dai yanzu duk wata
d'iya mace indai tanada mutunci to tana gidan iyayenta, gudan ya gagga6e da wata
irin dariya yace "yo dama duk wacce muka kama yanzu ay bata mutunci bace, dama mu
irin 'yan iskan nan muke nema masu yawon dare, idan sunsha sun bugu mukuma sai muyi
awon gaba dasu, suduka sukasa dariya marar dad'in sauraoro.

Duk abinda suke Fatima na La6e cikin wannan gidan tana jinsu in banda kyarma ba
abinda take, lokaci guda ta had'a wani uban gumi, dan tariga ta fahimci inda
zancensu ya dosa,
A gida kuwa da misalin 'karfe ukku da minti sha shidda na dare jidda ta farka zata
shiga toilet sai taga bataga Fatima ba, hakan yasa tayi tunanain ko tana toilet
d'in ta dad'e tana jiran fitowarta amma kusan minti goma shiru saboda haka saukowa
tayi daga kan gadon da niyyar ta duba toilet d'in.

Abinda idanunta yafara karo dashi shine ya d'aga mata hankali, kayan baccin Fatima
yadde a 'kasa, bata tsaya d'auka ba ta tura 'kofar kewayen, nan ma ba Laraba, cikin
tashin hankali tayo baya sai tayi karo da wadrop bud'e tayi sauri dubawa cikin
wadrop d'in saitaga kaya yamutse da Alama an d'auki wani abu aciki, nan tashiga
matsanancin tashin hankali lokacin data ta6a kofar fita daga d'akin tajita bud'e.

Cikin tsananin tashin hankali tanufi d'akin hajiyarta ta sanar da'ita abinda ke
faruwa,

Mukhtar ma an tasoshi an fad'a mashi halin da ake ciki, cikin tashin hankali
yafito, haka suka shiga duba ko'ina na gidan Amma ba Alamar Fatima, an tambayi me
gadi yace shikam bega fitar Kowa a gidan ba.

Lokacin idan hankalinsu yayi dubu tashe yake, mukhtar d'akinsa yanufa ya d'auko
key d'in motarsa yacema Hajiya "Zan fita in duba ko Allah zesa in ganta.

Lokacin itakuma jidda ta d'auko wayarta dan ta lura duk inda Fatima take ta tafi da
waya dan ta duba bata gantaba, lokacin ta lalubo sunan sister Fatima, sunan data
sanyama Laraba kenan ta danna mata kira.

Dadai lokacin da wad'annan mutanen guda biyu suka tashi daga 'kofar kangon gidan da
Fatima ke la6e a ciki guda na cewa "baba yakamata fa mu'kara gaba ko mun samu, ya
duba agogon hannunshi yace 'karfe ukku da rabi kada gari ya waye mamu anan, kasan
oga mayen mata ne duk ranar dabamu samo mashiba bamuda jin dad'i, d'ayan wanda tun
farko yace yagaji da sana'ar yace "waallahi ni abin na oga yana bani mamaki, ga yan
mata nan karuwai masu Neman mazan da kansu meyasa baya ri'ka d'aukosu yabiya
bukatarsa yabiyasu 'kud'insu hankalinshi kwance suma hankalinsu kwance, gudan yace
"kai dai banzane baka ta6a ganewa, ai a cewar oga duk macen data kai kanta ga
naminiji batada wani fa'ida yafison wacce za'a d'auko Mashi ya mata fyad'e, yafi
jin dad'in hakan dan duk wacce aka kawo tana tirjewa yasan ba 'yar iska bace, ko ka
manta lokacin damuka kawo mashi wata yarinya tanata ihu tana zillewa, ta d'auka
yankata za'ayi koda tagane ba yankata za'ayiba, tagane manufarsa kawai sai tace
"dakasan wannan ne da baka sa nayi wahalar hawayena ba, kawai mallam bissmillah,
yana ganin haka yace afita da ita, wallahi beyi amfani da itaba, dan ya lura
sana'arta ce.

Zasu tafi kenan wayar fatima tashiga ruri lokacin, kiran jidda ya shigo, cikin
tsananin tsoro da kad'uwa ta sa hannu ta danne wayar, harta tsinke bata d'aukaba
sai kuma aka 'kara kira karo na biyu, tayi ko'karin takashe wayar baki d'aya amma
sai ta kasa saboda tsananin rud'ewa.

Da sauri wad'annan mazan suka shigo cikin kangon gida suna dubawa dan jin waya nata
ringing, lokacin kuwa Fatima tagama sadaukar da rayuwarta, cikin sa'a kuwa suka
ganta basuyi wata-wata ba suka sungumeta, guda ya d'orata kan kafad'arsa tanata ihu
tana dukansa tana yagunsa, hadama cizo amma ko a jikinsa, ganin zata tona masu
asiri yasa gudan ya fiddo wani salatif ya toshe mata baki.

Tafiya marar nisa ta sadasu da inda suka ajiye motarsu wata bakar Hummer jeef mai
ba'kin glass suka jefata ciki, sannan sukaja motar, tafiya mai nisa sukayi wacce
fatimar batasan inda sukeba, bata iya ganin kome, saboda duhun dare ga kuma ba'kin
glass d'in motar.
Bakin wani 'katon gida wanda zamu iya kira aljannar duniya saboda 'kyawunsa, sukayi
horn me gadi ya bud'e masu get suka shiga, wani had'adden bedroom suka jefata kan
gado sannna suka kware salatif d'inda ke bakinta, saboda tsananin azaba saida
tafasa 'kara.

Haka suka fita suka barta sukaja 'kofar, itakuma banda kuka ba abinda takeyi.

'Karar bud'e d'akin yasa ta d'ago kanta wani 'katon mutum tagani, dogo ne fari me
dogon hanci da manyan idanuwa, ga bakinshi ma barakallahu babbane, ga 'kiba dake
gareshi kamar basamude.

Tsayawa yayi ya 'karema Fatima kallo, sannan ya matso yana lasar baki kamar tsohon
maye, yace "kai amma yau nayi dace tunda ake kawomin 'yan mata ba'a ta6a kawomin
'kya'kyawa kamarkiba, yasa hannu ya cire hijabin dake jikinta, ganin surar jikinta
yasashi 'kara rikicewa dan rigar datasa tad'an kameta, ga kanta ba d'an kwali, yayi
dariya yace amma kinada ala'ka da india ko? Wannan 'kya'kyawan gashi haka, yakai
hannu yana shafa kanta, itakuma kuka kawai take takasa ta6uka kome, a zuciyarta sai
addu'a take Allah kada yaba wannan mutumin ikon aikata abinda yake nufi akanta.

Haka yacigaba da shafata yana latsata, inbanda kuka ba abinda take, nan yashiga
'kokarin rabata da 'kayan jikinta, tasa hannu ta rirri'ke koda yaga zata kawo mashi
gardama sai ya nunamata 'karfi lokaci guda ya rabata da rigarta, jikinta yarage
daga ita sai bes, sai wando lagis data Sanya lokacin dazata fito, ganinta haka da
bayyanar 'kya'ky'kawar surarta ya'kara rikitashi, ya fita hayyacinshi gaba d'aya ya
rungomota jikinshi....

_*Ina barar addu'arku masoyana a duk inda kuke, shekaran jiya anyima babana theatre
Emergency, amma yaji sauki, kutayani addu'a Allah 'kara Mashi lafiya da duk musulmi
baki d'aya*_ 👏🏻😭

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:12 PM] +234 816 616 9254: [03/09 4:10 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

4⃣3⃣to4⃣4⃣

🖊 kuka Fatima tashiga yi ganin yana neman keta mata haddi, tana cewa "dan Allah
kayi ha'kuri kada ka cuceni kada ka 6ata min rayuwa, tana fad'ar haka tana wani
irin kuka me tsuma zuciyar me sauraro, amma mutuminnan ko ajikinsa, dan ko kad'an
bata bashi tausayiba illah 'kara kwad'aituwa dayayi da ita.

'Ko'karin rabata da sauran kayan dasuka rage jikinta yakeyi, itakuma banda addu'a
ba abinda takeyi, dan batada wani sauran kuzari tattare da ita.
A 6angaren Mukhtar kuwa yasha yawo har kusan 'karfe biyar na asuba amma bega Alamar
zega laraba ba, be 'kara shiga tsananin tashin hankaliba saida yafara jiyo kiraye-
kirayen sallar asuba,
haka yakoma gida zuciyarshi cike da takaici da ba'kin cikin rabuwa da
masoyiyarshi.

Yana shiga gidan a falo ya iske Hajiya da jidda sun buga uban tagumi, suna tunanin
ko yaga fatimar,.....
Ganin shigowarshi shi d'aya batare da laraba ba yasa jidda saurin tashi cikin
muryar kuka tace "yaya baka gantaba? Innalillahi munshiga ukku, ta fashe da wani
sabon kuka.

Jiki sanyaye mukhatar yasamu guri ya zauna.


Sai lokacin Hajiya ta kalleshi jiki a sanyaye tace "Mukhtar Yaya ba'a gantaba ko?
Wata nannauyar ajiyar zuciya yayi sannan ya d'ago da idanunshi wad'anda suka kad'a
sukayi ja saboda tsabar damuwa, yace "Hajiya Fatima ta su6ucemin shikenan Hajiya
narasa Fatima, lokacin wasu zafafan hawaye suka zubo daga idanunshi, yace "Hajiya
me mukayima Fatima ta gujemu? Me tanema a gidannan tarasa?.

Lokacin wani irin tausayin Mukhtar tashige hajiya, a zuciyarta tace tabbas mukhtar
yana cikin halin damuwa, dan na lura da yanda ya gama dam'ka duk illahirin
soyayyarshi ga Fatima, a Zahiri kuwa cewa tayi "inshaAllah duk inda Fatima take
zata dawo garemu, kudai kucigaba da Addu'a Allah tsareta a duk inda take,
Lokacin jidda ta fashe da wani sabon kuka tana cewa "ya Allah ka bayyanamin
'yar'uwata a duk inda take, Allah kareta da duk wani mugun abu.

Sai da sukaji an kabbara sallah a masallacin kusa dasu sannan kowanensu yatashi
yanufi sashensa dan gabatar da sallah, mukhtar kuwa koda yayi Alwala masallaci ya
wuce zuciyarshi cunkushe da ba'kin ciki da takaicin halin daze tsinci kanshi inhar
yarasa Fatima.

A 6angaren laraba kuwa haka mutumin yari'ka jagulata amma har yanzu Allah be bashi
ikon cimma burinshiba na keta mata haddi,

Amma duk illahirin jikinta yagama jagulata, hannu yakai yana kokarin ida rabata da
bes d'in jikinta wacce ita kad'ai tarage sai lagis d'inda tasa hannu ta rirri'ke
lokacin dataji yana Neman rabata dashi,

Wani irin 'karfi yazo mata a lokacin hannuwanta tasa duka biyun ta d'ora kan
'kirjin mutumin Wanda gaba d'aya yayimata rumfa dashi, ta turashi iya 'karfinta.

Jiyayi kamar wasu 'katti goma sun angizashi, yayi baya,yafad'i 'kasa, lokacin kuma
Fatima ta taso mashi hai'kan kamar wata tsohuwar damisa, lokaci guda duk wani haske
na fuskarta ya dishe, idanunta suka canja launi zuwa ja, tayo kan mutumin hai'kan,
a tsorace yatashi yafara ja da baya, dan ya masifar tsorata dan yanda take
tunkaroshi.

Saida ya dangane da bangon d'akin lokacin yashiga laluben 'kofa dan tsira da
rayuwarshi, amma kafin yayi yun'kurin bud'e dakin yafita ta kaimashi wani wawan
bugu da hannunta d'aya, wani irin duhu yaga ya gifta mashi, kanshi ya bugu da
bangon d'akin, take yafashe jini yafara ambaliya, yana wanke mashi jiki, a tsorace
yafasa wata uwar 'kara yana Neman taimako,

da gudu yaranshi suka nufo d'akin dan jin ogansu yana neman taimako, suka shiga
tura 'kofar amma ko kad'an ta'ki bud'ewa, da sauri guda yanufi wani d'aki ya d'auko
wani makullin ya bud'e, da sauri suka nufi inda ogan nasu yake kwance yana maida
numfashi sama-sama ga jini duk ya gama wanke mashi jikinshi, suka d'agoshi suna
fad'in "oga lafiya meke faruwa? cikin dusashshiyar murya ya nuna Laraba, yace
"ita....itac...itace... Nan kafin yagama fad'a masu yafad'i sumamme.

A harzuke suka nufi Fatima wacce hankalinta yayi masifar tashi da ganin halin da
mutumin dayayi niyyar yimata fyad'e yake ciki, dan ita bata San meya faru da
itaba, tun lokacin da mutumin yanemi ida rabata da kayan jikinta.

Amma me kafin su 'karaso gareta sai ji sukayi an d'aukesu da wasu mahaukatan


marurruka, kowanensu ya dafe kunci yana duba d'an uwansa, kafin suyi wata magana
aka rufesu da duka ta ko'ina, nan suka shiga ihu suna neman taimako, amma ba wanda
ke jinsu, dan dama haka gidan yake ihunka banza ne, dan da haka ogansu ke samun
damar keta haddin 'ya'yan mutane batare da anji koda ihunsuba.

Saida suka daku sukayi li'kis sannan aka 'kyalesu,


Fatima kuwa banda kuka ba abinda takeyi, dan ita kanta abin ya tsoratata yabata
mamaki dan ganin yanda mutanen keshan jibga batare da su duka sunga me dukan nasu
ba,

Lokacin jikinta yashiga 'kyarma takama kuka tana 'yarfa hannuwa tana kiran
innalillahi,
Hanyar guduwa tashiga nema dan tsira da rayuwarta, lokacin idonta yakai kan 'kofa
dake bud'e tun lokacinda yaran oga suka shigo dasukaji yana neman taimako.

Bata tsaya d'aukar kayan taba tanufi 'kofar tashiga falon d'akin tari'ka shiga
'kofofi na gidan, tashiga nan tafita nan amma har yanzu Allah besa taga 'kofar da
zata sadata da wajen gidan ba, 'karshe ma idan tashiga wata 'kofar sai taga ta
'kara maidota cikin gidan.

Haka tayita zagayen gidan, har 'karfe bakwai da kimanin minti sha shidda na safe,
lokacinne kuma oga ya farfad'o daga doguwar sumar dayayi, yayi saurin kai dubanshi
gurin da laraba take amma be gantaba, cikin tsananin rud'ewa ya kai dubanshi ga
yaranshi dake kwance suma basu san inda kansu yakeba, lokacin ya ta'kar'kara
yatashi yakai masu duka, "kutashi kai dan uwarku ku tashi ina yarinyar nan take, a
firgice suka kai dubansu ga ko'ina na d'akin basu gantaba.

Cikin d'aga murya oga yake magana, kuyi sauri ku nemomin ita, kada ku kuskura tabar
gidannan, da sauri suka tashi suka shiga zagaya gidan suna nemanta, dan sun tambayi
me gadi yakuma tabbatar masu da bata fitaba, aiko suna cikin dubawa sukayi kici6is
da ita a cikin wani korido, wata 'kara ta fasa tayi baya, kafin tayi wani yun'kuri
har sun cafkota.

Cikin gidan suka koma da ita, wannan karon wani d'akin suka kaita ba wanda suka
fara ajiyeta da farko ba.

Wata igiya suka sa suka d'ad'd'aureta, sannan sukaja 'kofar d'akin sukasa key suka
kulle.

Banda kuka ba abinda Fatima keyi, wannan karon tariga ta gama sadau'kar da
rayuwarta,

Bayan kamar awa d'aya da d'auretane, taji ana murd'a kofar, takai dubanta ga 'kofar
dan ganin me shigowa.

Oga ne yashigo cikin shigar ba'ka'ken jacket da wando sai wani ba'kin 'katon glass
dake fuskarshi me suna no respect 😎.

sai yaranshi guda biyu suma cikin 'kananan kaya suna take mashi baya.
Bakin 'kofa yaran suka tsaya, kowane gefe guda yayinda sukasa 'kofar tsakiya,
Shikum oga ya ida shigowa d'akin inda fatima take d'aure yanufa yashiga zagayata
yana tafa hannuwa, itakuma sai binshi take da ido duk illahirin jikinta 'kyarma
yake,
Wani shu'umin murmushi yayi yace.......

45to46 Very 🔜💃🏻


4546

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:12 PM] +234 816 616 9254: [04/09 3:57 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

4⃣7⃣to4⃣8⃣

🖊 Cigaba yayi da kallonta, sannan yace "A gaskiya na kwad'aitu da kyakkyawar surar
da Allah yayimaki, kuma iya tsawon rayuwata ban ta6a d'ora idona kan wata mace ba
tabani sha'awa in kyaleta batare dana biya bu'katataba, amma ke sai gashi na kasa
aiwatar da kome a kanki.

"Ianso zan miki wasu 'yan tamaboyoyi yanzu, ki tabbatar da kin bani amsarsu iyakar
gaskiyarki, hakan zesa in fiddaki daga gidannan da kaina batare da wani abu yafaru
dakeba.

Binshi kawai takeyi da ido, dan ita ahalin yanzu tariga ta sadaukar da rayuwarta,
kuma yanzu take danasanin gudowa datayi daga hannun mutanen dasukayi mata halacci,
yanzu batasan halin da guduwarta ya jefasu cikiba, tabbas ko ba'a fad'aba tasan
idan hankalinsu yayi dubu yatashi, ba kamar masoyinta Mukhtar Wanda ya d'auki son
duniya ya d'ora mata, a zuciyarta tace _(ya Allah ka fitar dani daga hannun wannan
mugun mutumin, Allah ka maidani gurin masoyina abin 'kaunata Mukhtar)_.

Wata uwar tsawa ya daka mata, wacce tayi saurin maidota daga duniyar tunanin data
afka, yace "miye sunanki?
Jiki na 'kyarma ta kalleshi idanunta na zubar da hawayen nadama tace
"Sunana Fatima...
Murmushi yayi sannan ya maiamaita sunan fatima koh? Ya'kara tambayarta, ta d'aga
Mashi kai alamar eh.

Yayi shuru na kimanin mintuna biyu sannan ya'kara jeho mata wata tambayar,
"Fatima ke mutum ce ko Aljan?
Tace "ni mutum ce.
"Amma ke matsafiyace,
Jiki na 'kyarma ta girgiza kai tace
"Ni ba matsafiya bace ban ta6a tsafiba.

Shuru yayi na wani d'an lokaci sannan yace "to fatima abinda yafaru jiya miye
kikayi idan kince keba Aljana bace, cikin muryar kuka tace "minayi,? Wallahi banyi
kome ba.

Cikin takaici ya kalleta yatuno da irin 'karfin data nuna mashi jiya lokacin dayake
'ko'karin yimata fyade, da ciwon data jimashi, yashafa kanshi inda ta dokeshi gurin
ya fashe, take wani irin mugun tsoronta ya dirar mashi a zuciya, ya maida kallonshi
gareta yace "yanzu zaki iya gane gida?
Kai kawai ta d'aga mashi alamar "eh badan tasa ran ze maidata gidan ba.

Hannu yasa ya kwanceta daga d'aurin da sukayimata, sannan yace "zaki iya shiga
toilet ki watsa ruwa ki canja kaya ni zan maidaki gidanku da kaina, dan barin
irinki suna zuwa hannun masu irin halinmu babban had'arine.

Be jira abunda zata fad'aba yafita daga d'akin yaranshi suka take mashi baya.

Tana ganin yafita jiki na 'kyarma taje ta kulle d'akin hada sa key da sakata,
sannan tafad'a toilet tahad'a ruwan d'umi tayi wanka, tad'an gasa jikinta dan duk
illahirin jikin ciwo yake mata, sannan ta d'auro Alwala tafito tasa kayanta sannan
ta d'ora hijab ta kabbara sallah, dan bata manta da batayi sallar asuba ba.

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Zaune suke jugum-jugum kowanensu yabuga uban tagumi bakajin kome sai sheshekar
kukan jidda, dan tunda aka tabbatar da 6atan fatima jidda ke kuka, idanunta sun
kumbura ga matsanancin ciwon kai dake damunta sakamakon kukan datake ba
'ka'k'kautawa.

Mukhtar ma kukan yake kamar mace, kokuma 'karamin yaro, sun tasa hajiya gaba, wacce
itama duk illahirin jikinta mace yake, dan ta d'auki fatima kamar 'yar data Haifa
da cikinta saboda haka dole taji 6atanta har cikin ranta, amma ganin yanda yaranta
suka d'aga hankalinsu yasata daurewa tari'ka rarrashinsu.

Suna cikin wannan zaman ne megadi yashigo da sallama, bayan Hajiya ta masa sallamar
yace Hajiya sallama ake a waje, cikin damuwa Hajiya ke tambayarshi "wanene me
sallamar, yace "eh to Hajiya gaskiya ban shedashiba amma yace maganace me mahimmaci
ke tafe dashi idan da hali yanaso ayimashi iso yashigo,
Hajiya tace "OK shigo dashi.

Bayan fitar me gadi da kamar minti biyar saigashi yashigo, cikin shigar manyan kaya
shaddace jikinsa, light blue, sai hularsa light blue, sai takalmi ba'ki, kallo
d'aya zakayimashi ka gane mutum ne wanda naira ta zauna mawa...

Bayan yasamu gu ya zauna yafara magana "ni sunana sadiq kuma ni d'an cikin garinnan
ne, idan bazaku damuba inaso insan yara nawane a gidannan, ma'ana 'ya'ya nawa kuke
dasu.....

Wani 'kululun ba'kin ciki ya tsayama mukhtar a wuya, a fusace ya kalli mutumin yace
"wannan wane irin rainin wayone zakazo kana mana tamabayar da bata shafekaba,
Sadiq yabud'e baki zeyi magana kenan sukaji tafiyar mutum ana shigowa gidan, da
sauri suka kai dubansu gurin....

Da gudu jidda ta tashi taje ta rungumeta tana kuka, tana cewa "sister ina kika
shige kika barmu cikin tashin hankali, fatima kasa furta kome tayi sai hawaye
datake zubarwa, cike da murna da fargaba Hajiya tazo takama hannun Laraba tashigo
da ita falon, mukhtar kuwa kasa furta kome yayi, illah bin fatima da yayi da ido.

Maganar Sadiq ce tadawo da hankalinsu gareshi, yayinda yake sanar dasu abinda
yafaru tsakaninshi da Fatima, be 6oye masu kome ba ya sanar dasu gaskiyarshi, dan
yariga ya tuba daga mummunar d'abi'ar dayake ta 6ata yaran mutane.

Wani irin takaici da ba'kin ciki da kishi suka taru suke rufe Mukhtar dan jin
labarin da Sadiq yafad'a saboda haka ido rufe ya tunkareshi kamar wani tsohon
mayunwacin zakin daya kwana beciba.......

49to50 Very 🔜💃🏻


4950

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:12 PM] +234 816 616 9254: [04/09 10:48 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

4⃣9⃣to5⃣0⃣

🖊 A zuciye mukhtar yakaima Sadiq wani wawan naushi a fuska, take gancinsa yafara
zubar da jini, cikin 'kankanin lokaci jini ya 6ata mashi tsadaddiyar shaddarsa
wacce tasha d'inkin computer, ganin jinin dake zuba daga hancin Sadiq besa Mukhtar
ya saurara mashi daga dukan dayake mashi ba, cigaba yayi da dukanshi ta ko'ina,
sannan yacimashi kwala ya tadashi tsaye ya angizashi, cikin fushi da d'aga murya
yace "kafita daga gidannan tun kafin inzama ajalinka, mugu azzalumi barin irinka
cikin Al'umma had'arine.

Duk abinnan da Mukhtar yayima Sadiq beyi 'ko'karin hanashiba, kuma be kare kanshi
daga dukan dayayi mashiba, badan beda 'karfin daze ramaba, dan a girme sadiq yakai
d'aya da rabin mukhtar, dan acewarshi duk abinda Mukhtar yayimashi ya can-canci
hakan.

Jidda ce taga abin na yayanta yayi yawa dan dukan sad'iq yake kamar baze barshi da
rai ba, ta kalli Hajiya tace "dan Allah kihanashi kada ya kasheshi,
Bata jira hajiyaba tanufi gurin tari'ke hannun mukhtar tana cewa "dan Allah yaya
kayi ha'kuri ka 'kyaleshi tunda Allah be bashi ikon aiwatar da kome kan Fatimar ba.

Ganin beda niyyar sauronta yasa ta kama hannunshi tari'ke tana bashi ha'kuri a
zuciye ya hankad'ar da ita tafad'i zaune tafashe da wani irin kuka.
Ganin abin na Mukhtar bana hankali bane yasa Hajiya tazo ta kamashi, tace "kai
mukhatar ka daina dukanshi nace, be saurari hajiyaba sai 'ko'karin tura Sadiq waje
yake, yana cewa "kafita kabar gidannan ban 'kaunar ganinka, wallahi idan ina
ganinka zan iya illataka dan ban had'a fatimana da kowaba.

A fusace Hajiya ta fincikoshi, cikin fushi take magana "wai kai Mukhtar wane irin
mutum ne, yaushe kafara rainani da inama magana baka saurarena.

Wasu zafafan hawaye suka zubo daga idonshi, baya yayi yasamu guri ya zauna kan
d'aya daga kujerun falon yana cika yana batsewa, jiyake dama Hajiya tabarshi da sai
yakusa halaka sadiq.

Fatima kuwa tunda suka shigo gidan taga halin data iskesu hankalinta yatashi, bata
'kara shiga wani tashin hankalinba saida taga yanda Mukhtar ke dukan Sadiq gashi
harya fitar mai da jini amma be daina dukansaba.

*_Innalillahi'wa,inna'ilaihirraji'un_* tashiga furtawa, tana kuka kamar zata cire


ranta, jidda ce takamata tace "ki daina kuka fatima ki godema Allah daya tseratar
dake da mutuncin ki,
Cikin dusashshiyar murya Alamar tayi kuka tagaji tace "jidda dole inyi kuka, duk
halin damuwar da kuka shiga nice na jefaku, sannan abinda mukhtar yayi yanzu duk
saboda ni yakeyi, wayyo Allah na ina zani da Alhaki, nazama butulu, na guji mutanen
dasukayimin hallaci a rayuwa, mutanen dasuka sharemin hawayen da 'kanin mahaifina
yakasa sharemin,

Zuwa tayi gaban Hajiya ta dur'kusa gwiwa biyu, tana kuka tace "dan Allah Hajiya Ku
yafemin nasan nashiga rayuwarku na jefaku cikin damuwa.

Cike da damuwa da tausayi Hajiya takama hannun fatima ta zaunar da ita kan kujera
tana gogemata hawayen dake zuba Daga idonta.

.
Hajiya takai dubanta ga Mukhtar Wanda keta cika yana batsewa, tace "ba haka
akeyiba kawai ka kama mutum kayita duka har ka jimasa ciwo, duk da abinda yafad'i
yana aikatawa ai bekai ga aikatashi ga ita fatimar ba,
Kuma tunda kaga yakawota har gida ina tunanin akwai dalilin sayasa yakawota.

Sannan ta maida dubanta ga Sadiq tace ina jinka yaro, cike da nadama Sadiq yafara
magana,cikin muryar tausayi da nadamar abubuwan daya aikata a baya.
_ ```na kasance ni 'kadai iyayena suka haifa, kuma iyayen nawa sun kasance masu
tarin dukiya, tun ina 'karami suke nunamin tsantsar so da 'kauna, hakan yasa
natashi banajin magana ko kad'an kuma duk abinda naga dama shi nakeyi, tun ina
secondary school nake 6ata yaran mutane, ta hanyar yimasu fyade idan sun'ki
amincewa, a lokacin nama fi so inyi fyaden dan nafi jin dad'in hakan, kuma idan aka
ganeni aka kawo 'karata babana sai yakama fad'a yace anjamin sharri dan ana ba'kin
ciki da dukiyar da Allah yayi Mashi, kuma yabani shi amatsayin d'a d'aya tilo haka
yake fatattakar mutane, wasu su fita suna kuka wasu kuma suje suna Allah ya isa,
ana cikin wannan halinne mamana da babana sukayi tafiya, kan hanyarsu ta dawowa
suakayi had'ari suduka suka mutu, nayi kukan rashin iyayena sosai, bayan kome ya
lafa aka raba gado aka bani, kasancewar bani ganin Kowa da gashin arzi'ki yasa ba
wanda yayi gigin cewa ze ri'kemin dukiyata, cikin dangin mamana, kona baba na, haka
nacigaba da bushasha, har basamu yarana wad'anda sune ke d'aukomin 'yan mata ina
keta masu haddi ta 'karfin tsiya```

Wasu hawaye masu zafi suka zubo daga idanunshi, yace amma sanadin zuwan fatima
gareni yasa natuba na daina wannan mummunar d'abi'ar danikeyi, kuma inaso dan Allah
fatima ki yafemin, yafad'a yana kallonta.

Mukhtar be tausayama sadiq ba ko kad'an illah wani irin haushi daya 'kara bashi
yace "dallah Malam kafita kabar gidannan munji duk bayaninka Allah shiryeka, bani
son ganinka cikin gidannan kuma bani bu'katar jin muryar ka.

Cikin fad'a Hajiya ke magana, dan mukhtar yafara 6ata mata rai tace "wai kai wane
irin mutum ne, mutum yazo har gida yaro'ki yafiya amma kakama cimasa mutunci, ay
inajin koda kafirine yazo neman gafara gareka zaka gafarta mashi kodan yasan
musulunci akwai Alfarma acikinsa, barantana d'an uwanka musulmi, Allah yana son
masu yafiya ga junansu, wai Mukhtar ina iliminka yake,?
Kuma kafin wannan ma ay komiye fatima itace babbar mai laifi, da bata fitaba da duk
haka be faruba.

Sadiq yace "ni najin dad'in fitar tata dan tazama sanadin shiriyata, fatana shine
tace ta yafemin, yafad'a yana zubar da hawaye...

Cikin muryar kuka fatima take magana "tabbas kome yafaru nice na jawo, dan daban
fitaba da hakan bata faruba,
Ta kalli sadiq tace nayafema, Allah 'kara shiryaka, kuma naji dad'i dana zama
sanadin shiriyarka.

Tana gama fad'in haka Sadiq yami'ke yace nagode Hajiya sai anjimanku, yafice daga
gidan.

Fatima kuwa durkusawa tayi tsakiyar falon tana kuka, tana ro'kon Hajiya da jidda da
mukhtar su yafemata,
Mukhtar har cikin ranshi yakejin kukanta, baze iya juraba saboda haka barin d'akin
yayi zuciyarshi na tafarfasa.

51to52 Very 🔜💃🏻


5152

*_'kya'k'kyawar gaisuwa ga 'kanwata, NASIBAT ELKASEEM_*


_Love u my sister_😘

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:12 PM] +234 816 616 9254: [06/09 3:22 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

5⃣1⃣to5⃣2⃣
🖊 washe gari bayan kome ya lafa, da misalin 'karfe tara da rabi na safe,
Zaune suke a general falo, bayan sun kammala kalacin safe, Kowa yayi shiru, amma
akwai abinda yake sa'kawa cikin zuciyarshi, yayinda Fatima takan goge guntayen
hawayen dakan zubo mata daga idanunta akai-akai.

Mukhtar yana lura da halin datake ciki saboda haka hankalinshi duk yana gurinta,
fatanshi Hajiya ta wuce d'akinta ya rarrashi fatimarsa ya kwantar mata da hankali,
dan idan akwai abinda yafi tsana a duniya shine 6acin ran hajiyarsa sannan kuma
yaga fatimarsa cikin damuwa.

Hajiyace ta maido da kowanensu daga duniyar tunanin daya Lula, yayinda ta kalli
Fatima tace "Fatima inaso ki nutsu ki kwantar da hankalinki ki fad'amin gaskiyar
dalilin dayasa kikayi 'ko'karin guduwa daga hannunmu wanda hakan yajefamu cikin
matsanancin tashin hankali.

Shuru tayi na d'an wasu mintoci bakajin kome sai sheshshekar kukanta, sannan tafara
magana cikin sarkewar murya tace "da farko inaso in ro'keku yafiya akan halin
damuwar dana jefaku na 'ko'korin guduwa danayi,
Bawai nayi hakan bane dan kun gaza da ri'kon da kukemaniba, ba kuma dan na raina
hallacin da kukayimani bane, a'a nayi hakane saboda baniso in sakamaku da sharri
akan Alkhairin da kukayimani.

Sannan inaso Ku gafarceni akan 6oye maku wasu abubuwa da dama danayi dangane da
labarina, yau inaso zan sanar daku kome bakin gaskiyata, dan baniso nazama sanadin
rushewar farin cikinku.

*_HAKA LARABA TA KWASHE LABARINTA KAF TA FA'DA MASU BATARE DATA 6OYE MASU KOME BA_*

Bayan tagama basu labarinta ne tacigaba da cewa "muddin na yarda da auren mukhtar
nasan shima 'karshen rayuwarsa yazo, nasan shima ze mutune kamar yanda maza ukku
suka mutu sanadiyyar aurena, a 'kauyenmu' yayinda na hud'unsu yasha ba'kar azaba
har yarabu dani ranar dana tare gidanshi, shima na tabbata kwanasa ne be 'kareba da
yanzu shima sai labari.

Jidda wacce tunda Fatima tafara bada labarinta take kuka tace "Fatima duk wanda
yamutu kwanansa ne suka 'kare kuma inshaAllah yayana ze aureki kuma ze zauna dake
ba abinda ze faru daku.

Hajiyama saida ta goge guntayen hawaye dan tausayin da Fatima ta bata, tace ki
kwantar da hankalinki Fatima ni nayi Al'kawarin zama dake kuma inshaAllah ko miye
ze rabu dake, kuma aurenki da Mukhtar ba fashi muddin kuna son junanku.

Wani sanyi Fatima taji har cikin ranta, dan son mukhtar ya dad'e da d'arsuwa a
zuciyarta.

Shima mukhtar haka yaji,


Cike da farin ciki yace "Hajiya inaga Al'amarin Fatima kamar hada iska cikinsa,
saboda haka inaso zan kaita gurin wani friend d'ina wanda shida babanshi sun 'kware
gurin magance irin wannan matsalar ta hanyar amfani da ayoyin Allah da kuma
magungunan musulunci wanda babu shirka a cikinsa.

Cike da jin dad'in yanda d'anta keson taimako Hajiya tace "to Allah taimaka Allah
sa a dace.
Su duka suka amsa da Ameen.

Sannan jidda takama hannun Fatima suka nufi d'akinsu, kai tsaye toilet suka shiga
suka d'auro alwala suka kabbara sallar nafila da niyyar Allah yayema Fatima lalurar
dake tattare da ita.

°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°°

Washe gari da musalin 'karfe goma na safe sun fito cikin shiri, jidda da faima suna
sanye da riga da wando na fakistan sannan suka d'ora hijabansu, sunyi kyau abinsu,
Mukhtar kuma cikin shigar manyan kaya shadda ash colour sai ba'kin takalmi sai
'kamshin turarensa daya buge ko'ina,

Har mota Hajiya tayi masu rakiya, suka shiga me gadi ya bud'e masu get suka d'au
hanya.

Mintuna talatin suka sadasu da gidan mal bature, shine mutumin daya 'kware gurin
magance matsalar jinnu ko asiri ko sihiri, ta hanyar amfani da ayar Allah batare da
an kauce hanya ba.

Suna Isa Mukhtar yayima abokinshi waya me suna Usman ya sanar dashi isowarsu,

Da far'a ya fito ya tarbesu, sannan yayimasu iso,


Bayan sun shiga sun gaggaisa Mukhtar ya sanar dashi abinda ke tafe dasu, duk da dai
kamar 'karin bayanine yake mashi dan sun riga sun gama maganar kome ta waya, har
Usman d'in ya Sanar da babanshi zuwansu.

Nan ya nunamashi Fatima matsayin wacce za'ayima maganin, Fatima wacce tunda sukazo
kanta ke sadde 'kasa Usman yakira sunanta "Fatima, sai lokacin tad'ago ta kalleshi,
suna had'a ido gabanta yayi mummnar fad'uwa wanda ita kanta batasan dalilin hakan
ba.

Cewa yayi su biyoshi zuwa gurin babnshi, haka suka bishi Fatima jikinta sai 6ari
yake kamar wacce ake girgizawa....

53to54 very 🔜💃🏻


5354

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:12 PM] +234 816 616 9254: [06/09 7:00 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

5⃣3⃣to5⃣4⃣
🖊 Bakin 'kofar d'akin Fatima ta toge ta'ki shiga, mukhtar ya kalleta yace "muje
mana Fatima ko wani abu kk jira, banza tayi ta 'kyaleshi ta tsaya gurin batada
niyyar matsawa ciki, saima 'kokarin komawa da baya take.

Jidda da tayi gaba harta shiga inda malam yake saida ta waigo taga Fatima da
mukhtar basu shigoba, dawowa tayi dan ganin ko lafiya, nan ta iske mukhatar na fama
da ita akan ta shiga d'akin ta 'kiya.

"Haba Fatima ki shigo mana' gurinfa maganinne mukazo nasan kinfi kowa son rabuwa da
lalurar dake tattare dake, jidda tafad'a cikin rarrashi.

Ganin Fatima batada niyyar tanka mata kuma batada niyyar shigowa yasa jidda kama
hannunta da niyyar tashigo da ita.

Saukar wani lafiyayyen mari jidda tayi a kumatunta, Wanda saida ta gigice saboda
tsananin zafin marin, takai dubanta ga Fatima wacce ke cika tana batsewa tace "me
nayimaki zaki mareni.

Cikin wata gur6atacciyar murya Fatima tafara magana, wacce ko alama ba muryarta
bace dan muryar tafi kama data maza, "an mareki d'in tafad'a tana wani irin huci,
"ke har kin isa ki shigar dani gurin dabanyi niyyaba.

Mukhtar naganin haka yasan ba Fatima bace, saboda haka ya kalli jidda yace "maza
kiramin Usman ya taimakamin dan wannan abin nayine.

Jiki na 'kyarma jidda tatafi kiran Usman, abin kamar jira tana fita kokowa ta kaure
tsakanin Fatima da Mukhtar, dan niyyar guduwa tayi shikuma ya ri'keta.

Saida Usman yazo da taimakonshi aka shiga da ita inda malam yake.

Suna shiga tafasa wata uwar 'kara wacce duk illahirin mutanen dake gurin saida suka
firgita, banda Malam wanda dama yasaba ganin irin haka.

Fad'uwa tayi 'kasa bakinta na fitar da wani irin kumfa, Malam yataso ya tsaya
gabanta yace "waye kai, ko wacece? Shiru Fatima tayi sai wani gurnani takeyi, Malam
ya'kara magana karo na biyu nan ma shuru tayi, wani ruwa ya d'auko ya karanta wasu
addu'oi yatofa aciki ya watsa mata, wata irin 'kara tasaki firgigi tatashi zata
gudu kamar wacce aka watsama garwashin wuta, mallam ya daka mata tsawa yace "koma
ki zauna, ba musu ta zauna tanata wani layi kamar wacce tasha ta bugu.

Sannan yace ina jinka waye? Cikin muryar daba ta Fatima ba take magana tace "nine,
hakan yasa Malam yagane namijine yace "Kaine wah?
Yace "nine masoyinta.
"Masoyinta kamar ya?
"Me shirin aurenta
"Me shirin aurenta kome shirin cutar da ita.
"Niba cutarta zanyiba, dan na dad'e ina dakon soyayarta tun tana cikin tsumma nake
tare da ita ina rainonta da niyyar idan ta girma in aureta.
"Kasan dai babu aure tsakanin mutum da aljan saboda haka kayi gaggawar barin
jikinta.
"Bazan iyaba ina sonta.
"Kafita da arzi'ki kokuma in fidda kai da tsiya.
"Bazan fitaba ko zaka kasheni.

Haka akayita daga tsakanin aljani da Malam, 'karshe dai mallam yayita karanto ayoyi
yana tofa mata, tashiga birgima tana ihu, hakan besa mallam ya daina karanto ayoyin
Allah yana tofa mata ba.
.
Kusan awa d'aya da rabi ana abu guda, sannan daga 'karshe Fatima ta fasa wata uwar
'kara tafad'i 'kasa war-was,

Wani abin al'ajbi dai-dai wannan lokacin kuma wannan 'katon ramin wanda laraba tayi
niyyar fad'awa a 'kauyensu lokacin da mukhtar ya tsinceta, yakama da wuta,
Ashe dama nan ne mazaunin wannan Aljanin da yake jikin Fatima.

Mallam ya kalkesu yace Alhmdulillahi kome ya wuce, babu sauran wani jinnu a jikinta
zaku iya tafiya gida, cike da tsoro jidda ta kalli malam tace "mallam a haka zamu
tafi da ita bata fa farfad'o ba, mallam yace "kada ku damu zata tashi wannan
nannauyan baccin dole tayishi, ga wannan garin habbatussauda ne tar'ika amfani
dashi tana zubawa a abinci ko cikin abinsha, kamar kunu ko koko, ko tea, sannan ya
mi'ko wani maganin yace wannan 'kuma haya'kin shaid'anune, tarika turarashi kullum
kafin ta kwanta, sannan ta ri'ke addu'oi da azkar da salatin annabi, Allah
sauwa'ke, suduka suka amsa da "Ameen.

Sun kar6i maganin sukayi godiya,mukhtar ya ajiyema mallam kud'i me tarin yawa yace
"mallam ga sadaka, mallam yace Allah ya kar6a.

Haka mukhtar da jidda suka kama Fatima wacce batasan inda kanta yakeba, suka
sakata mota,
Har gurin mota Usman yazo sukayi bankwana yaimasu Allah kiyaye tare dayima Fatima
fatan samun lafiya me d'orewa.

Tunda suka tafi a mota jidda ke faman kuka dan fatima ta masifar bata tausayi,
Mukhtar kanshi 'karfin hali yake gurin driving dan duk illahirin jikinshi kyarma
yake, haka suka iso gida bakin get sukayi horn megadi yabud'e masu get suka shige.

Suna shiga jidda tabud'e motar tafita, cikin gida tayi tana kuka, Hajiya dake zaune
falo tayi uban tagumi tana tunaninsu, tajiyo sallamar jidda, kafin tayi magana
jidda tafad'a jikinta tana kuka,
Cikin tashin hankali Hajiya ke tambayar jidda "ina fatimar meya faru da ita?

Sallamar Mukhtar tajiyo, yashigo falon d'auke da fatima kamar wata jaririya,
Shimfid'ar da ita yayi tsakiyar falon sannan yasamu guri ya zauna suka zubama
sarautar Allah ido.....

55to56 Very 🔜💃🏻


5556

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:12 PM] +234 816 616 9254: [07/09 9:30 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```
_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

5⃣5⃣to5⃣6⃣

🖊 *_BAYAN WATA BIYU_*

Fatima ta samu lafiya, kuma acikin 'yan kwanakinne soyayyarta da mukhtar tayi
'karfi wanda sukayi tsananin shakuwa, da so da 'kaunar juna.

Wata rana suna zaune a falo su duka kamar yanda suka saba idan sun gama cin abinci,
Hajiya ta kalli fatima tace "yakamata kibada izini aje 'kauyenku gurin baffa Lawal
Neman aurenki,
*'Rassss* Fatima taji gabanta yayi mummunar fad'uwa, lokaci guda tanemi
nutsuwarta ta rasa dan ko kad'an bataso ayimataaganar 'kauyensu dan yariga yafitar
mata arai, garin da aka 'kuntata mata aka muzantata, garin data wayi Gari yunwa da
'kishirwa sun kusa halakata saboda tsana da tsangwama da suka nuna mata.

Hannu tasa ta goge hawayen dasuka 6ata mata fuska, Hajiya tace "ki saurareni
fatima, kinsan indai mace na neman mutunci to anemi aurenta gun dangin mahaifinta,
shiyasa kikaga na matsa akan aje gun baffa Lawal d'in....

Fatima ta fashe da wani sabon kuka tace "dan Allah Hajiya ki taimaka min ki barni
kada inje 'kauyenmu, wallahi banison zuwa, ba yanzu bane lokacin dana yanke zanje
'kauyenmu, nayimaki Al'kawarin idan muna raye inshaAllah ba sai kinyimin maganar ba
da kaina zan gayamaki zanje....

Jidda tayi karaf cikin fuskar tausayi tace "dan Allah Hajiya ki barta, idan lokacin
yayi zataje da kanta.

Cike da tausayi Mukhtar yace "Hajiya dan Allah kiyimata Alfarma ki barta duk
lokacin data bu'kata sai taje....

Hajiya tayi murmushi tace "tayaro kyau take bata 'karko, idan kunce inbar fatima
kada taje 'kauyensu waye ze zama wakilinta ranar Aurenta?

Jidda tayi sauri tace "Hajiya ga 'yan'uwankinan, dan Allah su zama wakilanta.

Fatima ta taso jiki sanyaye ta dur'kusa gaban Hajiya ta d'ora hannunta kan
'kafafunta tace "Hajiya kece uwata, kece ubana, kece dangina, nasan Hajiya zaki iya
tsayamin akan kome, dan Allah kiyimin kome ba sainaje 'kauyeba, idan lokaci yayi
zanje...

Cike da tausayi Hajiya tace "to shikenan Allah shige mana gaba, suduka suka amsa
da Ameen, jidda hada yin wani gajeren murmushi dan jin Hajiya ta Amince da bu'katar
Fatima, dan ita a duniya tana masifar son abinda Fatima keso.

*_BAYAN SATI BIYU_*

Ansaka ranar Auren Laraba da mukhtar, lokaci d'aya aka sanya dana jidda, hakan yayi
dai-dai da saura wata d'aya da sati daya ayi bikin.

Wai kada kaga farin ciki tsakanin masoyan, jidda kuwa tafi kowa murna, dan tana
masifar son kasancewar fatima amatsayin matar yayanta.
Tun daga ranar da'aka saka biki hankali ya kwanta hidima ta kankama,

Bayan sati biyu mukhtar yasa akayo ma amaren odar kayan d'aki kome da kome yasa
sukayi Mashi list,

Ankawo kaya abin gwanin ban burgewa, mukhtar kuwa angama 'kera mashi gidanshi a
unguwar dutsin safe malali quaters, gidane nagani na fad'a dan ba 'karamin 'kerashi
akayiba.

Ana saura sati biyu biki aka kawo lefen jidda daga gidansu sahibinta Usman, akwati
shidda nar'ke da kaya nagani na fad'a.

Washe gari kuma mukhtar ya dam'kama Fatima nata lefen akwatina takwas, nar'ke da
kayan arzi'ki, ranar saida Fatima ta zubar da hawaye na abu biyu, wani 6angaren
farin ciki wani 6angaen kuma tana _*ALHININ*_ rashin mahaifiyarta lokacin dazatayi
aure, tasan datana raye datafi kowa farin cikin kasancewar zuwan ranar.

A 6angaren Hajiya kuwa hidima takeyi sosai dan duk wani Abu daya dace uwa tayima
'yarta lokacin aurenta Hajiya tayima jidda da Fatima, babu wani banbanci take had'e
kome tanayimasu tare.

Maman Ummi itace 'Kanwar Hajiya wacce sukafi sha'kuwa, saboda haka ita Hajiya
tabarma 'kwangilar kome na gyaran amare.

Ana saura sati d'aya bikin Maman Ummi tazo har gida tatafi da amare dan gyaresu.

Gyara kuwa sosai amare sukasha, cikin kwana biyar, idan kagansu dole ka 'kara
kallonsu dan wani masifaffen 'kyau dasukayi, jikinnan nasu har wani she'ki yakeyi,
dan dilkar da Maman Ummi kemasu irin wacce ake yiwa larabawace daga 'kasar
saudiyya, tataho da ita musamman saboda gyaran amaren,

Dan Maman Ummi saudiyya take zaune saboda bikin kawai tazo, dan sune *Amara 'Kirjin
biki*_{Littafin badi'at lbrahim}_ dan batada biki kamar na jidda *Autar
Hajiya*_{Littafina daya gabata}_
Aiko sunsha gyara gurin Maman Ummi dan wani abun idan tashafe masu jikinsu dashi
jin fatarsu suke kamar ta jarirai saboda laushi, 'kamshi kuwa ajikinsu kamar anyi
6arin turare.

Gurin 6angaren kayan tsumi kuwa, ba'a magana, dan suma Maman Ummi tazo dasu daga
'kasar saudi, _*(Hmm ni su Maman Ummi mutanen saudia, kome na larabawa)*_😜

🖊Zee Elkaseem
Mmn khady💋
[10/16, 8:12 PM] +234 816 616 9254: [08/09 9:37 am] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

5⃣7⃣to5⃣8⃣

*_RANA BATA 'KARYA SAI DAI UWAR 'DIYA TAJI KUNYA_*

🖊 Ni zee da inada dogon hanci dana rangad'a guda, amma ko yanzuma bata 6aciba dole
ince 👃🏻 Ayuuririri........ 💃🏻

Yau nahango dandazon dubban jama'a 'kofar gidan su jidda da mukhtar wad'anda suka
halacci d'aurin auren Mukhtar da amaryarsa fatima (laraba) sai jidda da angonta
Usman, kowanensu akan sadaki dubu sittin-sittin.

Wai kada kaso kaga farin ciki gurin masoya aranar, mukhtar na hango ansha shadda
hada uwar babbar riga, ga hula an d'ora, takalminnan nasa designer massaraci abin
dai yabadada kala, kallo d'aya zakayima angwayen kagane suna cikin farin ciki, dan
kowannensu bakin ya'ki rufuwa.

Amare kuwa acikin gida Mmn Ummi tagama shiryasu cikin wani rantsatstsen material,
kalar purple sai takalmin 'kafafunsu fari kowace da Jakarta fara, sai manyan
mayafinsu fari da aka yafa musu, sunyi wani masifaffen 'kyau kamar yayan sarakuna,
kome iri d'aya akayimasu musamman Hajiya tayi masu kaya kala shidda-shidda domin
yin hidimar biki, dan suduka ba wacce tayi amfani da kayan lefenta.

Da misalin 'karfe biyar na yamma Hajiya ta tara amaren a bedroom d'inta tana yimasu
nasiha, ba abinda sukeyi sai kuka, jidda na kukan rabuwa da hajiyarta da kuma farin
cikin kasancewa da masoyinta, yayinda Fatima kukanta ya kasu kashi ukku, wani
6angaren farin ciki wani 6angaren kukan rabuwa da Hajiya matar data zama tamkar
uwa uba dangi agareta, sannan babban jigon yin kukanta shine *_ALHININ_* rabuwa da
innarta, taso ace inna na raye a dai-dai wannan likacin itama taga Auren 'yarta
tayi farin ciki, amma ina ba haka Allah ya 'kaddaraba...

Ana cikin haka motar Alh mansir tayi parking a harabar gidansu jidda, Alh Mansir
'kani ne ga mahifinsu Mukhtar kuma shine ke shige masu gaba akan kome idan bu'katar
hakan ta taso.

Ganin shigowarsa yasa Ameeno saurin tashi daga zaman datayi kusa da Maman Ummi
wacce keta bata labarin saudiyya, dama Ameenoo da Mmn Ummi 'kawayene, tun kafin
Maman ummin tayi aure sukoma saudiyya itada me gidanta, Ameeno kuwa a gombe take
aure amma duk da haka suna waya da Maman ummin.

'Dakin Hajiya tanufa ta iske ta tasa maren gaba tanayimasu nasiha, guri tasamu ta
zauna itama ta d'ora da nata nasihar, dama Amino badai nasihaba, dan kan nan nata
cike yake da wa'azi da nasihohi.

Ahaka mutanen dake falon suka fara magana afito da amaren, jidda najin haka tafad'a
jikin hajiyarta tana kuka, da 'kyar aka 6am6areta jikin Hajiya aka fita dasu kowace
na sharar hawaye.

Alh Mansir da kanshi yakai kowace gidanta, sauran mutane kuwa sai dai sukabi daga
baya dan ganin gidajen amaren.

Alhmdulillahi jidda ma gidanta ya had'u a unguwar layout aka kaita, fatima kuwa
malali quaters mukhtar ya 'kyan'kyara masu 'kerarren gidansu.

Bayan mutane sunje anga gidajen amaren anyimasu duk abinda yadace bayan sallar
isha'i kowace takama gabanta, anbar amare su kad'ai a gidajensu.

Fatima zaune tsakiyar gadonta ta had'e kai da gwiwa tana sharar hawaye wanda ita
kanta ta kasa tantance na minene, farin ciki ko *_ALHINI_* A haka angon nata ya
risketa, tanajin shigowarshi amma bata d'ago ta kalleshiba.

Hawowa yayi kan gadon ya zauna gab da ita har jikinsu na gugar na juna, hannu yasa
ya yaye lullu6in dake kanta, yasa hannu ya d'ago da 'kya'kyawar fuskarta wacce duk
ta 6aci da hawaye, yace fatimana miye yasaki kuka, Baku far in ciki da kasancewa
mallakina ne,? Shiru tayi mashi tacigaba da zubar da hawayenta wani na bin wani.

Farin handkerchief ya fiddo daga Aljihunsa yasa yana goge mata hawayen dake zuba
daga idonta, wani daddad'an 'kamshi dake jikin handkerchief ya doki hancinta
batasan lokacin data saki wata ajiyar zuciyaba,
"Plz fatimana ki dainamin asarar hawayenki, baniso, idan kuma kinaso nima kiga nawa
hawayen to kicigaba da zubar danaki, kinriga kinsan damuwarki damuwatace, farin
cikinki shine nawa, ki taimakeni ki daina kukannan.

Haka yayita rarrashinta harya samu tayi shiru, sannan ya tashi ya nufi kitchen da
kansa ya d'auko plate da duk wani abu dayasan zasu bu'kata.

Dan'kara² kajine guda 2 ya baje musu da kanshi yari'ka yaga yana samata abaki, da
tana d'an nonno'kewa tanajin kunya har dai tasaki jikinta taci, shima yaci sosai
sannan yazuba musu lemu cikin glass cup suka sha sannan sukabi da ruwan roba, bayan
sun kammala ne ya kalleta yace "kinyi sallah isha'i kuwa kai kawai ta iya d'aga
mashi alamar eh dan duk illahirin jikinta 'kyarma yake sakamakon wani mayen kallo
dataga mukhtar namata, yace "to sai ki tashi mu d'auro Alwala mu gabatar da sallar
nafila domin nuna godiyarmu ga Allah daya cika mana burinmu,
Nan fa ta daburce tarasa wacce amsa zata bashi dan tasan tana fashin sallah ne kuma
bazata iya fad'a mashi ba.

Tashi tayi tafad'a toilet tashe'ka wanka ta gyara jikinta, sannan tafito shima
wankan yashiga, kafin yafito ta shafe jikinta da mayukan masu dad'in 'kamshi tare
dayima jikinta 6arin turarruka masu 'kamshin gaske, sannan tanufi wadrope ta d'auko
rigar baccinta tasaka tabi lafiyar gado.

Mukhtar kuwa daya gama wanka sai ya d'auro alwala, yana fitowa yaganta kwance,
beyimata magana ba saida ya d'auko wata jallabiya milk me gajeren hannu ya Sanya
sannan yace "ki taso muyi sallar, shiru tayimashi tare da lumshe idanunta kamar
bata jinsa, ganin tayimashi shiru yasa ya hawo kan gadon ya tallafo ta yace my fati
kitashi muyi sallah, ahankali ta baud'e idonta tace nayifa sallah yace "eh
kinfad'amin sallah nafila nake nufi, cike da jin kunya tace "uhm ina fashi ne, wani
irin fad'uwar gaba yaji dan jin tace tana fashin sallah dan yau yayi niyyar suci
amarcinsu, amma ba hali, haka ya kwantar da ita yaje ya kabbara sallah nafila
raka'a biyu yayi sanan yayi addu'a yashafa, kafin yagama bacci me dad'i yayi awon
gaba da ita.

Yana kan prayer mat yajuyo ya kalleta baccinta take cikin kwanciyar hankali, ya
'kurama 'kya'k'kyawar fuskarta ido yayi wani 'kyawataccen murmushi, addu'a yayi ya
shafe jikinsa sannan itama yayi addu'ar yashafe mata jiki, sannan ya kashe fitilar
d'akin ya kunna masu ta gefen gado, sannan ya haye gadon ya rungumota jikinshi
zuciyarshi cike da farinciki, a haka har bacci me nauyi yayi awon gaba dashi.

A 6angaren jidda kuwa a ranar Usman ya more kud'in sadakinsa dan be d'aga mata
'kafaba, ba 'karamar hawala tasha ba, haka ya rin'ka raraahinta yana shimata
Albarka, wani irin sonta ya'karaji cikin zuciyarshi dan yanda yasameta yaji dad'i
sosai.
🖊 Zee Elkaseem
Mmn Khady 💋
[10/16, 8:12 PM] +234 816 616 9254: [08/09 9:40 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

5⃣9⃣to6⃣0⃣

*_BAYAN SATI BIYU_*

🖊 da misalin 'karfe biyu na rana fatima na hango kitchen tanata ha'kilon had'ama me
gidanta abinci.

Cikin awar da bata wuce d'aya da rabi ba tagama shirya kome kan dining, sannan
tanufi d'akinta bayan tagyara kitchen d'in tsaf ta goge ko'ina kamar ba yanzu
tagama girki ciki ba.

Kai tsaye toilet tafad'a ta she'ka wanka, sannan ta d'auro Al'wala tafito ta
kabbara sallar azahar, bayan ta kammala sallar gaban dressing mirror ta zauna
tafara d'and'asa kwalliya, bayan tagama wadrope tanufa ta d'auko wasu riga da siket
na atamfa ta Sanya, kayan kuwa sun zauna da6as jikinta kamar a jikin nata aka
d'inkasu, sannan takashe d'aurin d'an kwali, turarruka ta feshe jikinta take
'kamshin jikinta ya gauraye da 'kamshin preshner dake d'akin da 'kamshin girkin
datayi, yabada wani kalar 'kamshi me dad'in sha'ka.

'Karar tsayuwar motar angonta taji, da sauri tafito ta zauna falo tana jiran
shigowarshi, dan yahanta zuwa tarboshi harabar gidan saboda me gadi na kallonta
shikuma yana masifar kishinta.

Da sallama yashigo falon, da sauri ta tashi ta tako zuwa gurinshi tana wani yanga
tana karairaiya kamar wacce batasan taka 'kasa, rungumeshi tayi tare dayimashi
'kya'k'kyawan Sumba a kumatu tace "welcome my husband, yace welcome fatimana,
nasameki lafiya, cikin zazza'kar muryarta tace "lafiya lao, kadawo lafiya yace
"lafiya.

Tace kafin kome muje ka watsa ruwa tukun, ba musu yabita zuwa toilet dinshi tahad'a
mashi ruwan wanka sannan yashiga itakuma ta jawo mashi 'kyauren toilet d'in, sannan
tazauna bakin gado tana jiran fitowarsa.

Bayan ya fito ya sanya kaya marar nauyi sannan tayimashi jagora suka nufi dinning.

Cike da jin dad'i da farin ciki suke cin abincin, har suka kammala, sukayima Allah
godiya,
Mukhtar ne yafara tashi daga dinning d'in yakoma kan kujera three seater ya kwanta,
itakuma fatima tsayawa tayi tana tattare kayan dasukaci abinci.
Bayan takai kuloli kitchen tadawo zata d'auki jug da cup's, sai taga wani
had'ad'en zobe kan table d'in, dariya tayi sannan ta d'auki zoben tace nayi
tsintuwa, mukhtar najin haka yatuno da zobenshi daya ajiye kan table din, da sauri
yataso yace kibani ring dina, 💍 nasan dai shine kika gani, cike da tsokana tace
bazan bayar ba, saika fad'amin wacece tabaka, cike da tsokana yace budurwata
tabanishi kuma zoben Al'kawarine, bekamata ta ganni babu shi a hanuna ba, fatima ta
yamutsa fuska tace "idan taganka babu shi ta tambayeka kace mata wacce tafita power
a gurinka tarabaka dashi, matsowa yayi gab da table d'in yace "kibani abuna tun
muna wasa da juna, cike da nishad'i ta 'kyal'kyale da dariya tace "bazan bayarba,
yana kallo ta zirashi a yatsanta, aiko da sauri yanufota yana dariya yace "kkkkk
kada ki Sanya........

Kafin yazo harta Sanya aiko ya nufota ze kar6a da gudu ta ruga tana dariya yabita
haka suka rin'ka zagayen falon amma besamu ya dam'keta ba, bedroom tanufa dagudu
yabita tana 'ko'karin turo 'kofar yayi saurin turawa yashiga, dariya takamayi
tafad'a kan gado tana maida numfashi, shima kan gadon yafad'a kusa da ita yana
maida numfashi, rungumota yayi jikinsa yace "waye nakama, dariya tayi tace baka
kama kowaba, dariya yayimata yace zakiyi bayani zaki san ban kama kowaba,
Nan fa wasa ya canja salo, a lokacin saida suka samu ladar aure,
Saida sukaji amfara kiran sallar la'asar sannan suka dawo hayyacinsu, toilet suka
nufa suka she'ka wanka sannan suka d'auro alwala, mukhtar yawuce masallaci, itakuma
fatima Bakin gado ta zauna zuciyarta cike da farin cikin yanda mukhtar d'inta ke
nuna mata tsantsar so da 'kauna.

Wayarta ta lalubo ta 'kira jidda, ringing biyu ta d'auka "hellow sister ya kike,
"lafiya lao sister ya amarci, to Alhmdlh zamuce, haka sukasha firarsu, kusan kullum
dama sai sunyi waya akalla sau hud'u ko sau shidda.

Bayan sunyi sallamane fatima ta tashi domin gabatar da sallar la'asar.

Rayuwa me dad'i da so da 'kauna tsakanin masoyan abin gwanin birgewa,

6angaren jidda ma tana samun kulawa sosai daga gurin Usman d'inta.

Fatima da jidda sukam sunyi dacen mazaje saidai suyima 'yan baya fatan samun mazaje
kamar nasu.

Sai dai lokaci zuwa lokaci fatima na kukan *_ALHININ_* Innarta, kuma tanason zuwa
'kauyensu amma lokacin data tsarama kanta na zuwa 'kauyen beyiba.

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:12 PM] +234 816 616 9254: [11/09 9:00 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 _*ALHINI*_ 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```
_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

6⃣1⃣to6⃣2⃣

*_BAYAN SHEKARA 'DAYA_*

🖊 Fatimana......Fatimana.....tun daga falo yake kwalamata kira, amma yaji shiru,


cike da mamaki ya nufi d'akinta dan yasan muddin tana lafiya to dataji tsayuwar
motarshi take zowa bakin 'kofar falo tajira shigowarshi ta tarbeshi, amma yau sai
yaga akasin haka, cike da fargaba yanufi d'akinta dan yimata Albishir Wanda yasan
idan tajishi har 'kyauta sai tayimasa, dan kuwa so yake ya gayamata haihuwar jidda,
dan kullum batada magana saita haihuwar jiddar, duk da itama tana fama da tsohon
cikinta haihuwa ko yau ko gobe koma yanzu.

Ringing d'in wayarta yajiyo bedroom d'inta hakan ya tabbatar mashi da tana ciki,
dan haka da sauri yanufi d'akin.

Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un ya furta tare da saurin 'karasawa ya tallafota ya


had'ata da jikinshi yana fad'in "lafiya fatimana meya sameki, meya faru, cikin
tsananin azabar rad'ad'in ciwon dake addabarta ta nuna mashi mararta, sannan ta
dafe bayanta tana wash....
Can ciwon ya'kara tsinkulota tafara salati cikin wata wahalalliyar murya "wayyo
yayana zan mutu ka taimakamin bayana ze 6alle 'kuguna, tana fad'i tana 'kara
shigewa jikinsa tana kuka, cikin tsananin rud'ewa Mukhtar ke rarrashinta ga kuma
wayarta gefe tanata ringing amma bebi kantaba, lalla6ata yayi ya kwantar da ita
tare da fita domin yakira wata makwabciyarsu malamar asibiti, da sauri yashiga
gidan sister safiyya ya sheda mata halin da Fatima take ciki, ba'afi minti gomaba
suka shigo gidan tare,tana zowa tasa safa ta dubata taga ta kusa haihuwa, nan ta
rubutama Mukhtar duk abubuwan da ake bu'kata.

Da sauri yaje chemist d'in kusa dasu ya siyo, yana dawowa yabata kayan ba'afi
mintuna 5 da dawowarsaba laraba tayi wani 'kwa'k'kwaran nishi me 'karfi tare da
santalo sankad'ed'en yaronta.

Sister safiyya tayi hamdala sannan ta gyara yaro tayima Fatima duk abinda ya dace,
mukhtar kuwa dan tsananin murna bakinshi ya'ki rufewa nan ya fiddo yawa yakira
Hajiya ya sanar da ita haihuwar Fatima, sannan yacigaba da 'kiran 'yan'uwa da
abokan arzi'ki yana sanar dasu.

Bayan sister safiyya ta taimakama Fatima tayi wanka ta gyarata itada baby.
Fatima ta fito shar da ita kamar ba itabace wacce ta haihu sai buga uaban 'kamshi
take itada baby, sister safiyya da kanta ta shiga kitchen tahad'oma Fatima tea me
kauri Wanda yaji milo sosai takawomata tana zaune bakin gado, saida ta tabbatar
data shanye duka sannan tabata magungunanta tasha sannan tafito da niyyar tafiya
gida.

A harabar gidan tagamu da mukhtar yana niyyar fitowa daga mota, da Alama wani wuri
yaje amma bame nisaba saboda be dad'e da fitaba, ganinta yasashi saurin ida fitowa
daga motar yace "ah sister har kin fito?
Cikin fara'a da sakin fuska tace "harna fito Baban baby, zanje gidane kafin in
'kara zagayowa inga lafiyar baby da momynsa.
Cike da jin dad'i mukhatar yayimata godiya sannan ta wuce, shikuma yashiga cikin
gidan kai tsaye bedroom d'in fatima ya nufa da sallama yashiga.

Zaune take gefen gado ta rungume babynta tanata murmushi abinta, da murmushin shima
ya 'karaso yasa hannu ya 'kar6i baby yayimashi addu'a sannan yayimashi hud'uba
kamar yanda addinin musulunci ya tanada,ya dad'e yana kallon babyn sannan ya maida
dubanshi gareta yace "ammafa babyn nan dani yake kama,cikin shagwa6a tare da
marairaice murya tace "Ba wani dani yake kama, cikin tsokana mukhtar yace "Ba wani
ki duba kiga hancinsa irin nawane da manyan idanunsa, yafad'a yana kallonta cikin
tsokana dan yasan kallo d'aya zakayima idanun yaron kasan irin na Fatima ne,
bandasu amma duka face d'in mahaifinshi ya d'auko,
Cikin murya kamar zatayi kuka tace "ka tambayi sister safiyya kaji tun tana mashi
wanka tace dani yake kama......

Mukhatar ya 'kyal'kyale da dariya dan ganin yanda Fatima ta ha'kikance akan yaro
yana kama da ita...

Cikin nishad'i yacigaba da magana ammafa gaskiya sister safiyya tanada kirki,
kiduba kiga yanda take hidima dake, fatima tace "hmm kaidai bari wallahi ni har
kunyartama nakeji, yanzu abinda tayimin ko asibiti naje baza'a kula dani kamar
hakaba........

Wayartace ta katse masu firar dasukeyi tahanyar yin ringing Alamar ana kira, da
sauri ta tashi ta d'auko amma kafin ta danna OK har kiran ya tsinke, 18missed call
tagani...

Fiddo idan tayi waje tare da kallon Mukhtar tace "18 missed call, yace ki duba
kigani nasan dai bewuce jidda, kinsan itama ta haihu....

Cikin zumud'i tace "dan Allah fa banda tsokana, yace "kirata kiji d'azu da Albishir
d'in nazomaki saina taras kina labour shiyasa hankalina ya d'auke ban gaya makiba.

Wayarta ta Shiga dubawa aiko 15missed call tagani na jidda sai 3 na Hajiya, Hajiya
tafara Kira ta gaisheta, nan hajiyar ke nunamata cikin tsananin farin cikin datake
na samun jikoki biyu Lokaci guda....

Nan Fatima ta ida tabbatar da maganar haihuwar jidda, saboda haka sunayin sallama
da hajiya number jidda takira, lokacin itakuma jidda tanada labarin haihuwar
larabar haka suka dad'e suna waya sunama juna barka sannan sukayi sallama.

Itakuma jidda da asubane ta haihu tasamu baby girl, fatima kuma bayan azahar.

_````ZEE```_ *Wishes u*
```HAPPY SALLAH```
*IN*
_*ADVANCE*_

💞```EID MUBARAK```💞

📝note
Inaba masu bin wannan Littafin ha'kuri akan jina da kukayi shuru kwana biyu, hakan
yafarune saboda wasu 'yan hidimomi dasukasha kaina, gakuma hidimar sallah saboda
haka kucigaba da ha'kuri zan ri'katurowa duk lokacin dana samu lokaci kafin agama
hidimar sallah.
Love u all 💃🏻

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:13 PM] +234 816 616 9254: [17/09 8:34 am] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

6⃣3⃣to6⃣4⃣

Haka 'yan uwa da abokan arziki sukayita zuwa gidan mukhatar da gidan jidda suna
ganin baby, barakallahu.
jidda Usman yayimata kaya nagani nafad'a, akwati ukku yacikama baby da kaya,
jidda kuma akwati biyu sha'ke da kayanta,

6angaren mukhtar kuwa akwati set yacikama fatima da babynta, abin dai gwanin
sha'awa anyi kome cikin tsari.

Ranar kwana bakwai akayi suna, d'iyar wurin jidda aka samata suna Rahama, d'an
gurin fatima kuwa sunan Mahaifin mukhtar aka sanyamashi, amma suna kiranshi sultan.

Ba 'karamin abin arzi'ki fatima ta tara gun sunan ba, saboda 'yan'uwan mukhtar
sunyi mata kara sosai, a ranar ma saida jidda ta zubar da hawayen *_ALHININ_*
tunowa da mahaifiyarta, da kuma ganin duk taronnan da kuma abin arzikin data tara
babu 'yan'uwanta ko d'aya.

Yanzu gashi tayi aure har Allah ya azurtata da samun d'a amma ba rabon innarta taga
wannan ranar, *(Allah sarki laraba haka Allah ya 'kaddara)*

Haka akagama hidimar suna Kowa ya koma gidansa cike da farin ciki, washe garin suna
hajiya tace Mukhtar ya maido fatima gida dan tayi wanka anan, haka Mukhtar ya
maidota badan ranshi yasoba, yaso ace anbarta gidanta tayi wanka acan kullum yana
kusa dasu itada babynsa, ya d'auko matar dazata ri'ka kula dasu amma Hajiya ta'ki
amincewa da hakan, saboda haka dole ya tattarasu ya kaisu can badan ranshi yasoba
sai dan bin umarnin mahaifiyarsa.

Jidda kuwa dama Usman tunda aka gayamashi ya amince da tafiyarta gida wanka, saboda
haka itama washe garin suna Usman da kanshi ya tattaro ya kawota gidan da kanshi.

Haka Hajiya tacigaba da kula da 'ya'yanta da jikokinta, tare da taimakon jummai me


aiki.
_*BAYAN WATA BIYU*_

Hajiya na zaune falo ta tasa 'yan jikokinta gaba zuciyarta cike da farin ciki,
yaran sai wutsil-wutsil suke da 'kafafunsu da hannuwa alamar suna cikin 'koshin
lafiya.

Jidda kuwa da fatima suna zaune gefe sunsha kwalliya kamar wasu sabbin amare, dan
bazaka kallesu kace sun ta6a haihuwaba, kome nasu cif,

jidda kwalliyar tata ta taron me gidanta ce dan yayimata waya yana zuwa, itakuma
fatima dama tunda suka dawo gidan shima mukhtar ya dawo nan dan kwana kad'ai ke
beyi anan.

Da misalin 'karfe hud'u na yamma Usman ya iso gidansu jidda,


Bayan yayimata waya ya sanar da ita zuwanshi tayimashi masauki a a falon ba'ki,
bayan ta cikashi da kayan ciye-ciye da lashe-lashe, komawa tayi cikin gida ta
d'auko rahama, a kafad'a ta sa6ota, tana taku Ahankali cikin nutsuwa harta iso
gurinsa tasamu guri ta zauna gab dashi, 'kamshin turarensu ya gauraya dana juna,
sannan ta gaidashi, bayan ya amsa suka cigaba da firarsu.

Acikin firar nasu ne Usman yake cema jidda "A gaskiya jidda nayi rashinki kusa dani
yaufa tsawon wata biyu kenan yakamata ace kin koma hakanan, jidda tayi murmushi
tace nima nayi missing d'inka, usman yace "ban yarda da zancenkiba, jidda tayi
saurin kai dubanta gareshi "baka yardaba fa kace, yace "kwarai ko dakinyi missing
d'ina dakincema hajiya kinaso ki koma haka, domin ni gaskiya inajin kunyar
fad'amata, jidda tayi murmushi tace "indai wannan ne kada ka damu kabani kwana biyu
inshaAllah zan dawo cike da jin dad'i usman ya rungume jidda yana sumbatar ta, wani
irin feeling sukaji suduka sakamakon rashin jin d'umin junansu dasukayi na tsawon
lokaci.

Baby rahama kuwa kwantar da ita jidda tayi kan kujera tanata sharar baccinta,

Haka suka rin'ka romancing junansu, lokaci guda Usman ya rikice yafita hayyacinsa,
idanunshi sun rufe yama manta da gidan surukai yake, sai da jidda taji yana
'ko'karin wuce gona da iri sannan tayi 'ko'karin saita nutsuwarta dan itama ta
shiga wani irin yanayi, ta tureshi daga jikinta sannan ta tashi daga kujerar dayake
ta koma nesa kad'an dashi tana maida numfashi,

Shima kallonta kawai yake yakasa ta6uka kome idanunnan nashi sun kad'a sunyi ja,
kusan mintuna ishirin suna haka sannan suka dawo hayyacinsu, ya kalli jidda cikin
wata wahalalliyar murya yace "jidda zan tafi kinga magrib ta gabato amma zan shiga
mu gaisa da hajiya tukun, tace "ba damuwa amma kasa ran dawowata nan da 2 days,
yace "danafi kowa farin cikin hakan, tayi wani 'kawataccen murmushi tace kada ka
damu abban rahama, wani irin dad'i yaji dan jin sunan data kirashi dashi, sannan
yakai dubanshi ga 'kya'k'kywar babynsa rahama wacce ke baccinta cike da jin dad'i,
yace "je kiyimin iso gun hajiyar.

Haka ya shiga suka gaisa da hajiya, fatima da kanta tazo suka gaisa sannan ya
d'auki sultan yana mashi wasa, jin anata kiraye-kirayen sallar magrib yasa ya mi'ke
tare dayimasu sallama sannan ya wuce, jidda tarakashi har gurin motarshi saida taga
tafiyarshi tana d'aga mashi hannu sannan tadawo cikin gida cike da tsananin so da
'kaunar mijinta.
🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:13 PM] +234 816 616 9254: [17/09 7:30 pm] 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

6⃣5⃣to6⃣6⃣

🖊 Bayan sallar isha'i mukhatar ya shigo gidan a falo ya iskesu zazzaune suna shirin
cin abinci,
Shima zama yayi fatimace tayi serve kowa ta ajiye a gabanshi, bayan sun kammala cin
abincinne Hajiya ta kalli mukhatar tace "d'azu mijin jidda yazo kuma ya nuna yana
bu'katar matarshi saboda haka bazan tauye masu hakki ba na yanke shawara jibi zata
koma gidanta kamar yanda itada mijin nata suka yanke, sannan ta maida dubanta ga
fatima wacce keta faman rirriga sultan shikuma yanamata 'yar rigima tace "kema
fatima sai ki shirya jibin kibi mijinki.

Wani irin farin ciki ya ziyarci zuciyar mukhatar dan jin Hajiya tabashi izinin
tafiya da fatimarsa,

Fatima kuwa gyara zama tayi lokacin tasamu sultan yayi bacci ta kwantar dashi,
sannan ta kalli Hajiya tace "Hajiya Kafin inkoma ina Neman wata Alfarma, Hajiya ta
maida dubanta gareta tace ina jinki

Wasu irin hawaye masu zafi suka zubo kan kumatunta, tasa hannu ta goge sannan tace
inaso dan Allah kafin inkoma inje 'kauyenmu.....

Hajiya ta numfasa tace "to Alhamdulillahi naji dad'i da ya kasance yau da bakinki
kika furta kinason zuwa, amma bazance komeba akan tafiyar ga mijinki nan kuyi
shawara.

Mukhtar yayi murmushi mai d'auke da damuwa dan ganin fatimarsa na zubar da hawaye,
yace "Ba kome hajiya nima naji dad'i da hakan, amma tunda jibi ne aka sanya ranar
komawar tasu sai ta shirya gobe muje garin nasu.

Cike da jin dad'i laraba ta kalli mijinta tayi mashi wani 'kyawataccen murmushi,
shima murmushin ya mayar mata.

Jidda dake zaune tanajin duk abinda aka tattauna, bata tanka ba tashi tayi kawai
tanufi bedroom wayarta ta d'auko tashiga laluben sunan Usman sannan ta danna mashi
kira yana d'agawa tace "dan Allah abban rahama inaso gobe zamuje garinsu Fatima,
Usman yace "me akeyi ne?
Tace "zamuje mu gaidasu ne.
Yace "ba damuwa, ki kularmin da kanku keda baby rahama Allah kiyaye hanya
Tace "Ameen"
Sannan ta tsinke kiran ta ajiye wayar ta dawo falo.
Yanda tabarsu zaune haka ta tarar dasu gurin datake ta koma ta zauna sannan ta
kalli Fatima tace "sister goben sai muje tare ingano garin naku nima.

Wata irin harara Hajiya tayimata tace "da izinin wah zaki tafi?
Ta kalli Hajiya tayi murmushi tace abban rahama ne yace inje, Hajiya tace "yaushe
kukayi maganar ?
Tace "yanzu fa nakiraahi a waya.
Hajiya tace "to Allah kaimu goben kuma Allah kaiku lafiya ya maidoku lafiya.

Sai lokacin mukhtar yayi magana yace "Amma gaskiya Hajiya abinda jidda keyi bata
kyautawa yanzu dagajin tafiya harta sanar da mijinta zataje da son yawon tsiya
kamar taci 'kafar kare.

Jidda ta turo baki tace "ay dama tuni nake cema sister duk ranar dazata garinsu
tare zamu tafi.

Hajiya najinsu bata tanka masuba, tasan dai duk abin mukhtar tunda jidda ta
'kwallafa rai a tafiyar nan saitaje sai dai idan Allah ne be 'kaddara ba.

_```WASHE GARI```_

misalin 'karfe tara na safe na hango fatima cikin wata shiga ta Alfarma wacce
shigar tafi kama data 'ya'yan sarakuna.

Dan wani tsadadden material ne purple jikinta me Ado da wasu kalan duwatsu masu
haske, sai zanen farin flowar jikinsa, sannan wasu tsadaddun takalmi dake 'kafarta,
material d'in d'inkin riga da zani pieces hakan ba 'karamin 'karamata girma yayiba,
da kyau da kwarjini, wani babban farin mayafi ta yafa shikuma farine anyimashi ado
da flower's purple sai adon duwatsu farare.

Sultan na sa6e a kafad'arta shima anyimashi shiga ta Alfarma kayan jikinshi shima
farine da purple sai fararen kyawawan takalmashi masu tsada.

Jidda ma kwalliya tayi tagani ta fad'a dan itama ba daga bayaba gurin kyau, itakuma
material d'in nata golden colour ne haka takalmi da mayafinta da jakar data rataya,
baby rahama ma shigar golden d'in akayimata.

Sai oga mukhatar shima yayi shiga ta Alfarma dan wata tsadaddiyar wagambari ya
sanya ash colour sai hula itama kalar ruwan toka sai ba'kin takalmi, sai 'kamshin
daddad'an turarensa dake tashi.

Haka suka Shiga mota kirar Camry kalar ruwan toka me duhu, Hajiya na tsaye
tanayimasu addu'ar zuwa lafiya da dawowa lafiya,

Megadi ya bud'e masu get suka d'auki hanya, tafiya suke cikin nutsuwa da kwanciyar
hankali dan mukhatar mutumne me nutsuwa saboda haka kome nashi cikin tsari
yakeyinshi saboda haka tafiyar da bata wuce tsakanin awa ukku da rabi zuwa awa
hud'uba ya sadasu da garin su laraba.

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:13 PM] +234 816 616 9254: [18/09 6:58 am] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

6⃣6⃣to6⃣7⃣

🖊 Suna isa 'kofar gidan baffa Lawal suka sauka bayan sunyi parking d'in motor
d'insu suduka suka fito daga motar, Fatima ta kalli gabas da yamma kudu da arewa na
garin, batasan lokacin da wasu zafafan hawaye suka zubo daga idanunta ba, tasa
gefen hankchief ta goge *Lallai wani hanin ga Allah baiwa ne*
Fitowarsu daga mota yasa hankalin mutanen dake gurin yadawo garesu, Kowa kallonsu
yake kamar basu ta6a ganin mutaneba.

Dan yan yara wanda basuda hankali sosai har zuwa suke suna ta6a kayan jikinsu, tare
da tatta6a motar dasukazo da ita.

Gidan baffa Lawal suka shiga kai tsaye da sallama matar ta tarbesu tayi masu
shimfid'ar sabuwar tabarma suka zazzauna amma bata gane ko mutum d'aya daga cikinsu
ba.

Baffa Lawal yana gonarsa yanata faman aiki labari ya iskeshi wai anga wata
had'addiyar mota taxo gidanshi tare da wasu mata masu kyau, da wani namiji kuma
anga sunshiga gidanshi.

Aiko yanajin haka yayi saurin tattara yanashi-yanashi yanufi hanyar gida, da sauri
yake tafiya kamar ze tashi sama, yana Isa 'kofar gidanshi yaga mota aiko stayawa
yayi yana kallo cike da mamaki.

Sannan ya 'karasa cikin gidan, laraba na ganinshi gabanta yayi mummunar fad'uwa,
har gabansu yazo ya dur'kusa yana gaishesu, sukuma sai abin yabasu kunya cike da
ladababi suka gaisheshi ya amsa sannan yace "bayin Allah ai ba nan bane gidan
megari yanacan saman layi, amma tunda kunzo nan muje in rakaku aiba damuwa, yana
magana jiki na 'kyarma sai wannan 6a6are yake yana washe ha'kora.

Fatima tace ba gidan me gari zamuba nan mukazo, yanzu baffa Lawal baka ganeniba,
Sai lokacin ya 'kuramata idanu kamar yana neman sanin wani abu tattare da ita, yace
"kai yarinya banganekiba har yanzu, inaji ba nan bane gidan da kuke nema saboda ni
banida 'yan'uwa birni.

Kad'an yarage jidda tayi dariya dan ganin yanda baffa Lawal ya ha'kikance be gane
laraba ba,
Laraba kuwa goge hawayen dake idanunta tayi sannan tace *"baffa 'yarka ce laraba*
😳 mamaki yakamashi kuma tana fad'in itace laraba sai yaganeta, yace Laraba ina
kika shiga shekara da shekaru mun d'auka kin mutu, matar baffa lawal ma tasowa tayi
cikin mamaki tace "Laraba da kina raye Allah me iko,
Baffa Lawal ya kalli su jidda da mukhtar yace wad'annan fa su waye?
Fatima tace wannan shine mutumin daya taimakeni, ta nuna mukhtar kuma yanzu haka
shine mijina, ga kuma d'an da Allah ya azurtamu dashi,
ta mi'kama baffa lawal sultan, sannan ta nuna jidda wannan kuma 'kanwarsace lokaci
d'aya akayi bikinmu itama ga d'iyarta, ta amshi rahama daga hannun jidda tami'kama
matar baffa lawal.

Cike da mamaki baffa Lawal ke kallon fatima yace "laraba haka kika koma, ikon
Allah,
Allah kenan me d'aukaka bawansa ta kowace hanya.
Laraba dai in banda zubar da Hawaye ba abinda takeyi,
Kusan awarsu guda gidan baffa Lawal laraba nabashi labarin irin taimakon da Hajiya
da mukhtar yayimata, da kuma irin yanda suka ri'keta kamar 'yar cikinsu.

Sannan mukhtar yaje but d'in motarshi yasa aka shigo da tsarabar da sukayomasu,
buhun shinkafa katon d'in taliya dana makaroni da sabulun wanka dana wanki da
sauran kayan abinci,
Ahaka aka ri'ka shigowa da kayan baffa lawal kuwa banda godiya ba abinda yakeyi,
saboda tsananin farin ciki besan lokacin da wasu hawaye suka zubo daga idonshiba,
ya kalli laraba yace "Ashe dama akwai ranar dazanga aurenki har inga d'anki Allah
Sarki Allah maki Albarka kinji laraba, Ashe hakanan mutane suke zarginki akan
*maita* ashe Sharrin iska ne Allah dai ya'kara tsareki laraba, tana zubar da hawaye
tace ameen baba.

Bayan sun gama danan ne suka tashi, laraba tace "baffa zamu d'an shiga gari mu
gaisa da jama'a.

Cike da jin dad'i yace to laraba amma kafin kuje ko'ina ianso kuzo muje gidan me
gari ki gaisheshi, mukhtar yace ba damuwa muje, haka suka d'unguma suka nufi gidan
me gari kasancewar ba nisa tsakaninsu da gidan baffa lawal d'in shiyasa suka tafi a
'kafa, duk inda suka gifta kallonsu kawai ake kamar wasu taurari, baffa Lawal kuwa
daya gaisa da mutane a hanya sai ya nuna masu laraba da mijinta da d'anta, haka
shikuma Mukhtar ze fiddo dubu ya mi'kama wanda aka nunama larabar.

Da haka suka isa gidan megari, baffa lawal yakwashe labarin da tafad'amashi duka
yagayamasu sannan ya gwadamasu mukhtar a matsayin mijinta da kuma d'ansu sultan,
sun d'an jima suna gaisawa da jama'a kafin suyi sallama tare da cika me gari da
abin arzi'ki kafin kace me labarin zuwan laraba ya bud'e gari mutane sai zuwa ake
ganinta duk wanda yazo sai mukhtar yabashi 'kud'i wani dubu wani d'ari biyar, yara
kuwa me dari me d'ari biyu ranar garin duk wanda kagani bakinsa washe saboda murna.

Baffa lawal kuwa daga nan gida yakoma yasa aka yanka zabbi akayima su laraba soye
lafiyayye sannan aka dama masu fura wacce taji nono.

Gidan indo 'kawar laraba suka nufa, kan hanyarsu ta zuwane suka gamu da habu yadawo
daga gona yayo uwar ciyawa ya d'ora akai ga kuma hauya rataye akafad'arsa sai uban
gumi yake had'awa, Fatima ta kalleahi tace habu, cike da mamaki ya d'ago ya kalleta
dan jin wata 'yar gayu wacce batayi kama da 'yar 'kauyensuba ta ambaci sunashi,
sauke ciyawar dake kanshi yayi ya'karema fatima kallo yace baiwar Allah daga ina
kuma ina kika sanni?

Fatima tayi murnyshi tace "habu nice laraba baka ganeniba, cike da mamaki habu yace
laraba kece kika koma haka, dama wallahi abinda yasa nabaro Gona kenan inacan
labari ya iskeni wai kindawo wanda ada mun dad'e da d'auka kin mutu.

Laraba tayi murmushi tace "ina raye habu harma nayi aure, ta nuna mashi mukhtar
wannan shine mijina, ga kuma kyautar da Allah yayimamu bayan Aurenmu ta nuna mashi
sultan, sannan ta kalli Mukhtar tace wannan shine habu, mukhtar ya mi'kamashi hannu
suka gaisa sannan ya d'auko 20k sannan sukayi sallama suka wuce, habu ya tsaya yana
juya kud'in kafin daga bisani yanufi gida cike da farin ciki dan kobi takan
ciyawarsa beyiba.
🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:13 PM] +234 816 616 9254: [18/09 6:33 pm] .: 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

6⃣8⃣to7⃣0⃣

🖊 Sun isa gidan indo, da sallama suka shiga gidan sun isketa tana sharar tsakar
gida da yaronta goye, d'agowa tayi daga duken datake takai dubanta ga fatima, kallo
d'aya tayimata tace "laraba kece, cike da mamaki ta rungumeta tana zubar da hawaye,
laraba tace nice indo,
Indo tace Ku shigo, haka suka shiga d'akin indo tayimasu shimfid'ar tabarma suka
zauna, nan suka gaisa, laraba taba indo labarinta kaf bayan barinta 'kauyen, lndo
cike da mamaki tace "Allah kenan shike yanda yaso da bawansa, kinga kuwa yanda kika
koma laraba, wallahi baccin sanin danamaki ba kad'an bane da bazan shedakiba, yanzu
d'inma ba namijin 'ko'kari nayiba, dan yanzu kinfi kama da irin turawan damuke gani
a talabijin, jidda tayi dariya,

Haka sukasha firarsu sannan sukayima indo sallama bayan laraba tayimata 'kyautar
kud'i me yawa sannan tace zata aiko da katon-katon d'in sabulun wanka dana wanki
duk wata 'kawarsu dake garin abata sabulun wanka sin'ki guda saina wanki dozin,
indo tashiga godiya,
Suna gaf da fitowane ilu yayi sallama bayan indo ta amsa tanunamashi laraba, cike
da mamaki yake kallonta, sannan yace "tabbas naji ana labari a gari laraba tazo da
mijinta ance yanata rabon kud'i, indo tace kwarai dan nima ga abinda larabar tabani
ta nunamashi dubu goma sha biyar, ilu ya zare ido dan tunda yake beta6a tinanin
rike kud'i irin hakaba amma yau larabace ke bayar dasu kyauta.

Tare sukayoma su laraba rakiya, a 'kofar gidan indo ta gaisa da Mukhtar shima ilu
sun gaisa, Mukhtar yabashi kyautar dubu goma, wayyo dad'i kashe ilu ai fad'uwa yayi
yana zuba uwar godiya.

Daga nan asalin gidansu laraba suka wuce, sun shiga gidan ba abinda ya canja ga
yanda tabarshi, d'aki tanufa duk kayanta Dana innarta sunanan, wani irin kuka
tafashe dashi, jidda tashiga rarraahinta da 'kyar tasamu tayi shiru, kusan mintuna
sha biyar suna cikin gidan sannan suka fita.

Daga nan gidan baffa Lawal suka koma sun iske soyayyun zabbin da baffa Lawal yasa
aka soyamasu da fura me rai da lafiya, sunsha sosai sannan suka ci naman, bayan sun
kammala ne suka 'kara ta6a fira, saida sukayi sallar la'asar sannan saukayi haramar
tafiya gida, har mota baffa Lawal yarakosu, kafin subar garin said a suka 'kara
biyawa gidan indo suka sauke katon-katon din sabulu na wanka dana wanki wanda za'a
rabama 'kawayenta.

***********************************
Bayan sallar magrib suka iso gida,bayan sunyi horn megadi ya bud'e masu get,
mukhtar yayi parking inda aka tanada dan ajiye motoci, su duka suka shige gida cike
da gajiya tattare dasu, falo suka iske Hajiya ta tarbesu tana masu sannu da zuwa.

.
Washe gari da misalin 'karfe goma na safe Hauwa me 'kunshi tazo tayima jidda da
fatima, kunshi, itace me 'kumshin Ameeno yanzuma itace ta turota tayimasu, kunshin
ya zanu kamar wasu sabbin amare, bayan sallar azahar kuma sukaje gyaran kai, gyara
sosai saukayima jikinsu Hajiya ma ta had'amasu duk wani abu datasan ze taimaka masu
gurin gyara,

Washe gari kafin la'asar sun gama kammala kome nasu, bayan sallar magrib Mukhtar
yazo yatafi da fatimarsa, basu dad'e da tafiyaba Usman yazo ya d'auki jidda,

To Alhamdulillahi kowace takoma d'akin mijinta, suncigaba da rayuwar soyayya da


bawa junansu 'kyakkyawar kulawa.

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋
[10/16, 8:13 PM] +234 816 616 9254: [18/09 9:00 pm] . 🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇
😭 *_ALHINI_* 😭
🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇🐇

®```NWA```

_Written by_
_*Zee Mmn khady*_ 😘

_```THE END```_

7⃣1⃣to8⃣0⃣

🖊 Bayan wata biyu, yau yakama week end saboda haka Mukhtar baije ko inaba, dama duk
weekend baya fita zama yakeyi tare da fatimarsa su ri'ka debema juna kewa,

Yauma kamar kullum zaune yake kan kujera 3 seater sultan rungume ajikinsa yana
bacci, fatima ce tafito daga bedroom d'auke da wata lallusar katifa me had'e da net
ta yara ta ajiye sannan ta lalla6a ta kar6esa ta kwantar dashi, mukhtar na fad'in
"kifabi ahankali kada kuma ki tasheshi kinsan dai rigimar dayayi kafin yayi baccin.

Koda ta kwantar dashi beko motsaba dan dama rigimar ta baccin ce yayi,
Koda tasamu ya kwanta tashi tayi tadawo inda Mukhtar yake zaune kan three seater ta
kwanta tayi filo da cinyarsa shikuma yasa hannunsa kanta yana wasa da lallausan
gashinta.

Cikin nutsuwa da tausasa murya tafara magana "Abban sultan dama inaso muyi shawara
dakai, ya tattara nutsuwarshi sannan ya maida duk wani hankalinshi gurinta yace
inajinki, tace "inaso duk kud'in dake gareni zanyi amfani dasu a roshe gidanmu na
'kauye amaidashi ialamiyya wacce za'a ri'ka koyarda addini acikinta, shine nace
bari insanar dakai hakan danayi yayi kuwa?

Mukhtar ya numfasa har cikin ransa yaji dad'in wannan tunani na fatima dan d'an
zuwan dasukayi 'kauyen ya fahimci yanda jahilci ke d'awainiya da mutanen garin.

Yace kada ki damu indan wannan ne ni zan d'auki nauyin kome, kuma zanyi 'ko'kari
insayi wani fili kusa da gidan sai ayi masallaci, kuma zamuyine da niyyar Allah kai
ladar ga iayayenki,

Wani irin farin ciki taji ya ziyarci zuciyarta batasan lokacin da wasu irin hawaye
sukayo ambaliya daga idanuntaba, tace "nagode Abban sultan Allah sakama da gidan
Aljanna.

Haka kuwa akayi cikin satin Mukhtar yaje 'kauyensu laraba yasanarda baffa lawal
shawarar dasuka yanke shida laraba, baffa Lawal yaji dad'i sosai sannan aka sanar
dame gari, wani tsohon gida li'ke da gidansu laraba mukhtar yasiya aka had'e aka
roshesu baki da'aya kasancewar gidajen manyane ansamu wadataccen fili.

Ayki ya kakankama kasancewar nera ke magana, cikin wata d'aya aka kammala ginin
islamiyya da 'katon masallaci me kyau duk 'kauyen babu kamarsa.

Bayan ankammala da sati d'aya akayi walimar bud'e islamiyyar, Wanda laraba da kanta
ta kaddamar da ita, su hajiya da jidda suma sun halarci walimar, laraba kuwa a
ranar tayi kukan *ALHINI*Allah ya d'aukakata, ba rabon innarta taga wannan lokaci.
, mutanen 'kauyen sunyi matu'kar farin ciki,
Taro yatashi lafiya kowa yakoma gida duk garin bakajin maganar Kowa sai ta laraba.

Cikin satin mutanen 'kauyen suka fara karatu a islamiyyar da suke kira _*LARABA
ISLAMIYA*_

```Alhamdulillahi``` 👏🏻

_*Anan nakawo 'karshen wannan littafi nawa me suna ALHINI, ina fatan me karatu ya
nishad'antu kuma ya d'auki darussa dake cikin wannan littafi nawa*_

💞 _*Kyakkyawar gaisuwa ga masoyana a duk inda suke*_ 💞

_*JINJINA GA GROUP'S*_

Nagarta writer's association.


Wisdom Hausa writer's.
Sahaf's novel.
Deejer taheer group.
Matan kwarai group.
Presidential villa group.
Mesha Luv fan's
S.A.Azeez group.

_*MY SpECIAL GROUP'S*_

💞 *Zee Mmn khady fan's & nvl*


👉🏻👩🏻 *Ciwon ya mace group*

_*Ina gaisuwa ga duk masu bin littafina, sai kunjini a sabon buk d'ina me suna*_
👇🏻
💃🏻 *_YARINYAR BABA_* 💃🏻

*Litattafan marubuciyar*

💞 *Siyasa ko soyayya*
🌍 *Duniya juyi*
👍🏻 *Halin girma*
🏤 *Gidan ASALI*
🕊 *Autar Hajiya*
🐇 *Alhini*

Love u all my fan's 💋💃🏻

🖊 Zee Elkaseem
Mmn khady 💋

You might also like