You are on page 1of 204

[09/09, 10:03 AM] Matar Sayyadee: 🦜 *_K'ANWAR MATATA_*🦜

_Matar Sayyadee_
_Wattpad @Matar_Sayyadee_

_K'anwar Matata ba kirkirarren labari bane! Sai da na samu yarda da aminta sannan na soma rubuta shi.
Dan haka idan yayi shige da naki irin labarin, arashi aka samu. Sannan ina gargad'i da babbar murya, ban
yarda a juya min labari ta ko wani siga ba, ba tare da izini na ba ko kuma a d'aura min a YouTube!_

_K'anwar matata isn't free wooo! Na fad'i tun wuri saboda kar ki soma karatu kiji free pages sun k'are ki
soma k'orafi baki san cewa na kud'i bane tun farko. Naira d'arin ki biyar ya ishe ki samun karanta labarin
daga farkonsa har k'arshe. Wannan karon babu please matar Sayyadee dan Allah ki saka ni a paid group I'll
pay later yanzu bani da kud'i ne. Matar Sayyadee baza ta tab'a saka ki a group ba sai kin yi payment. Ehe,
pay before service!_

Page 1

Kuka take yi sosai a gaban doctor d'in tana fad'in, "Na rantse da girman Allah doctor ban tab'a yin sex
ba a rayuwa ta! Ban san ta yanda aka yi wannan ciki ya shiga ba. Sai dai idan ture aka yi min." Shuru doctor
Kamal yayi yana kallonta irin kallon ta raina masa hankalin nan. Daga shigar jikinta gaba d'aya ya fahimci ita
d'in ba mai kamun kai bace. Wando ne pencil a jikinta sai monkey jacket d'in da ta daura a kai. Kanta kuwa
wani uban kitson attachment ne wanda aka yi mata shuku _Ghana weaving_ dashi kalar maroon da bak'i.
Gaba d'ayanta bata yi kalar mutunci ba. Hatta k'umbar hannunta artificial ne irin zaro-zaro d'in nan. Gashin
idanunta ma artificial d'in ne suma zaro-zaro dasu. Kallon results d'in dake hannunsa yayi wanda ya nuna
masa 2weeks pregnancy a jiki sannan ya kuma d'agowa ya kalleta tare da mik'a mata yana fad'in,
"Scanning machine ba zai tab'a maki k'arya ba! Sau uku kenan ina tura ki kina yin scanning, na k'arshen
nan ma da kai na naje nay maki saboda confirmation. Amma still the results is same. Dan haka, ya rage a
gare ki da ki koma kiyi tunani da kyau a inda kika samo cikin jikin ki. Lot's of patient are waiting outside. I'm
done with you!" Fad'in doctor Kamal yana nuna mata hanyar waje. Don tuntuni yake ta danne fushinsa. Ya
tsani yaga mace mara kamun kai a rayuwarsa. Wani irin kuka ta kuma fashewa dashi tare da fad'in, "Please
doct...." Bata kai ga k'arisa maganar ba ya nuna mata k'ofa a fusace tare da fad'i, "Out of my sight right
now before I call security to throw you out. Y'an iska yara k'anana daku sai biye-biyen maza saboda abun
duniya. Sai bayan sun d'ura maku ciki sai kuzo kuna mana kuka wai baku san ta yanda akai kuka yi cikin ba
saboda kun raina mana hankali. Idan kuma aka sakar maku fuska sai ku fara rok'o akan a zubar maku da
cikin. Dama Allah ya rik'a d'aukar rayuwar ku lokacin da ake k'ok'arin cire maku cikin. Y'an iska kawai!"
Doctor Kamal ya fad'i. Ita kuwa tun lokacin da ya buga tsawa na farko tayi saurin d'aukar handbag d'inta da
paper d'in da ya turo mata ta fita da sauri gabanta na fad'uwa don ta tsorata sosai da yanayin doctorn. Fita
tayi daga asibitin gaba d'aya. Sai da tayi nisa da asibiti sannan ta nai mi wani waje gindin bishiya ta zauna
tana kuka sosai. Wata mota ce tazo ta wuce ta gabatar da gudu, can kuma motar ta dawo da baya da baya
har inda take. Sauke glass mai motar yayi tare da fad'in, "Sssss, hi babe! Wani irin d'agowa tayi tare da
watsa masa harara sannan ta mai da kanta tsakankani cinyoyinta tana kuka. Mai motar kuwa yaja motarsa
ya bar wajen ya bar mata k'ura. Tashi tayi ta soma tafiya a hankali dai-dai lokacin da aka yi wani irin tsawa
alamar hadari ya had'u sosai. Da sauri ta kalli sama taga gab ake da a tsuge da ruwan sama. Bata damu ba
ta cigaba da tafiya. Ko taku biyar bata yi ba aka tsuge da tuwan kamar da bakin kwarya. Bata fake ba ta
cigaba da tafiya a k'afa, don ji take dukan ruwan kamar shi zai yaye mata halin da take ciki. Sai da taga bata
iya ganin gabanta da kyau sannan ta samu wani d'an rumfa da few mutane ke tsaye a wajen wanda kusan
gaba d'ayan su y'an achab'a ne da passengers. Ruwan nan ya kai tsayin awa guda kamun ya sassauta
saboda lokacin gab da magriba ne. Yayyafi ake yi irin wanda zai iya jik'e jikin mutum jagab. A hakan ta
kuma shiga ruwan ta dunga tattakawa. Duk da irin nisan da gidansu ke dashi haka ta tako a k'afa tun daga
wani k'aramin private hospital dake fire brigade dake tudun nupawa har Jos road by Abeokuta Street. A
wannan lokacin har d'iga take yi tun daga tsakiyar kanta har cikin pant d'inta. Ko da ta tura k'ofar gidan su
ta shigo, babu kowa a tsakar gidan as she expected, sai tayi saurin shiga d'akinsu. Kwance ta taras da
Na'ima a kan gado tayi d'ai-d'ai tana waya sai mulmula take yi from edge to edge d'in gado. Kallo d'aya tayi
mata ta d'auke kai tare ajiye handbag d'inta a kan side drawer sannan ta soma cire boyfriend jacket d'in
jikinta ta ajiye a gefe ta zame dogon jeans d'in jikinta ta kasance daga ita sai pant sannan ta nufi wajen
wardrobe ta d'auki zani ta d'aura a k'ugu sannan ta zame pant d'in jikinta ta cire tare da unbuttoning shirt
d'in jikinta ta cire har da bra sai ta ja janin sama. Zare ribbon d'in kanta tayi ta had'a da jik'ak'k'un kayan da
ta cire ta saka a wani bokiti yellow mai tambarin Maggi Star da ba ruwa a ciki sannan ta dauki towel wanda
ke hannun wardrobe ta rufe kanta tare da d'aukar butanta da babu mai tab'awa a cikin gidan ta fita ta nufi
bayin su dake tsakar gida tayi fitsari ta kama ruwa ta fito daga bayin ta d'aura alwala sannan ta koma
d'akin. Wardrobe d'in ta bud'e ta d'auki doguwar riga jallabiya ta saka. Towel d'in da ta fita dashi kuma, ta
yi amfani dashi ta goge jik'ak'k'an attachment d'in kanta sannan ta dauki hijjab ta saka tare da shimfid'a
darduma ta tada sallar magriba. Har ta idar da sallah Na'ima bata gama waya ba, kuma babu abunda take
fad'i sai dirty talks ita da wanda take wayar dashi. Juyawa tayi ta kalleta for 3seconds sannan ta cire
idanunta ta mayar kan kwan fitilar da ya kawo haske a d'akin alamar an kawo wutan lantarki. Mik'ewa tayi
ta nannad'e dardumar ta mayar inda yake sannan ta cire hijjab d'in jikinta ta ninke ta ajiye sannan ta dauki
kettle ta cika ruwa a ciki ta jona. Tana jonawa ana d'auke wuta kamun kuma tayi wani yunk'uri suka sake
dawo da nepar. Hamdala tayi a cikin zuciyarta sannan ta bar wajen ta dawo kan kujera one sitter dake
d'akin guda d'aya tal ta zauna tare da had'a kai da guiwa tana tunanin ta ina ciki ya shiga jikinta ba tare da
d'a namiji yayi penetrating a jikinta ba. Wasu hawaye masu zafi suka shiga gudu a kuncinta. "What I'm
doing to tell him now? Our marriage is in 4weeks now. Kuma nayi masa rantsuwar ban tab'a sanin wani d'a
namiji ba a rayuwata. Sai kuma ga ciki yanzu! Ta ina zan fara yi masa wannan bayanin ya yarda dani. I'm
dead! Shikenan wannan ma zai gudu kamar sauran. Nima bazan tab'a aure ba kamar sauran y'an uwa na.
Na shiga uku na!!" Ta fad'i a cikin zuciyarta tana hawaye daidai lokacin da ta soma jin wani shuuuuu alamar
ruwan da ta saka a kettle ya soma tafasa. Cikin sauri ta isa wajen ta kashe socket d'in sannan ta zare igiyar
kettle d'in tare da d'aukar kettle d'in ta juye ruwan zafin a cikin wani bokiti ta fita ta nufi wajen pampo ta
kunna ruwa. Kasancewar ruwan na zuba da uban gudu, sai take yi tana saka hannunta domin jin yanayin
zafin ruwan. Kashe pampo d'in tayi bayan yanayin zafin ruwan yayi mata ta d'auki bokitin ta kai ruwan bayi
sannan ta dawo d'akin ta d'auki soso da sabulun wankanta ta fita, kuma har lokacin yayarta Na'ima bata
gama wayar da take yi da saurayinta ba. Bayan kamar 15mins ta fito daga bayin dai-dai lokacin da
mahaifiyar su Lami ta fito daga nata d'akin tana fad'in, "Sarah, ashe kin dawo cikin gidan nan shine baza ki
iya zuwa d'aki ki fad'a mi kin dawo ba saboda bak'ar mugunta irin naki! Duk saboda kar ki sammun abunda
kika samo ko? Dad'in abun ba ke kad'ai na haifa ba" Turo baki Sarah tayi tare da fad'in, "Ni fa Lami asibiti
naje ba wani waje ba. Allah ya kiyaye inyi yawon banza." Rik'e baki Lamin tayi tare da fad'in, "Iyeeh! Za kici
ubanki ne shegiya asararriyar yarinya. Da kyawun ki zaki je ki lalata kanki. Uban wa kika ga yayi aure a cikin
yayyinki su hud'u gasu nan kina gani? Kuma a cikinsu babu wacce bata kawo abun arziki cikin gidan nan. Ku
shidda mata Allah ya kashe ya bani domin ya wanke min bak'in cikin da mahaifin ku ya saka min a zuciya
shekara da shekaru. Amma babu wulak'antacciya mara mutunci da rashin son cigabar uwarta sai ke
Saratu! Kai Allah yayi wadaran naka ya lalace. Kin nane a jikin namiji guda d'aya, d'an iska yaron da ba wani
abun arziki gare shi ba. Kin kafa k'ahon zuk'a shi kike so sai kin aure shi, to don ubanki shine ajalinki da y'an
k'ananun shekarunki. Yaro d'an iska sai fankama shi ba uban kowa ba. Zan ga yanda za'ayi auren nan
wallahi. Zaki ci uban ki! Dani kike zancen." Da kallo Sarah ta bita har ta shige d'akin da shine mallakin
mahaifin su a gidan. Ta jima tsaye da bokiti a hannu sanyi na busata kamun ta ja k'afafunta da suka yi mata
sanyi ta shige d'akin su. Turus ta tsaya lokacin da ta d'aga labule tana kallon Na'ima wacce ke rik'e da
takardar result d'in dake nuna Sarah wanda ke nuni da tana d'auke da juna biyu. Cikin sauri Sarah ta fad'a
d'akin tare da warce takardar a hannunta tana mai hararar Na'ima. Na'imar ma hararan take maka mata
tare da fad'in, "Munafuka annamimiya! To yau asirin ki ya tonu. Ashe kema shek'e ayar ki kike yi a wajen,
amma idan kin shigo gida sai ki rik'a nuna kamar ke ta Allah ce. To yau dai asirin ki ya tonu. Kuma wallahi
sai na fad'awa Lami." Tana fad'in haka tayi saurin sauka daga kan gadon ta bangaje Sarah ta fice daga
d'akin tana kwala kiran sunan Lamin. Da sauri Lami ta fito daga d'akin mijin nata tare da fad'in, "Lafiya
haka Na'ima kike kwala min kira? Ko wani abun alkhairin ne ya same mu" fad'in Lamin dai-dai lokacin da
Nuratu, Hassana da Marfu'a suka fito suma suna tamabayar lafiya. Na'ima kuwa wani shewa tayi tare da
nuna k'ofar d'akin su inda Sarah ke ciki tana mai fad'in, "Yau dai anyi walk'iya a cikin gidan nan. Mai mana
gori da mun aje y'ay'an shegu ita ma tana gab da ajiye maki shegen jika." Ta k'arisa maganar tana mai
kallon Lami da ta saki baki tana kallonta. "Ke ban fahimta ba, fitar damu cikin duhu dan Allah Na'ima."
Fad'in Nuratu. Sai da Na'imar tayi wani shegen gud'a sannan tayi nuni ta baya izuwa ga d'akin su tace,
"Ustaziyar gidan nan dai ciki ne da ita. Dama kwana biyun nan kullum sai inga tana ta kuka, idan ta
tambayeta mai ke damunta, sai tace min babu komai. To yau dai bayan ta fita zuwa bayi domin wanka, sai
na bud'e jakarta don in d'auki turarenta in fesa saboda Ajeeb ya kira ni yana k'ofar gida, kawai sai ganin
takarda nayi a ciki, shine na fiddo na bud'e, nan kuwa nayi arba da ciki har na sati biyu a jikin takardan.
"Gaba d'aya wani irin shewa suka d'auka dashi har da tafawa. Nuratu tace, "Zancen gori ya k'are a cikin
gidan na. Wallahi Lami yarinyar ta k'ara min rashin kunya ko kuma ta dukan mu y'ay'ana a cikin gidan nan
sai naci uwarta yasin. Shegiya y'ar iskan yarinyar mai mugun hali. Dama fa ni Lami tuntuni na gane Sarah
tana biye-biyen maza a waje. Abunda ya saka take nuna mana kamar bata yi, duk dan saboda kar ta kawo
wani abu cikin gidan nan ne a amfana da ita saboda bak'ar rowarta da mugun hali. To yanzu dai anyi
walk'iya. Wallahi duk abunda kike fita kina samowa sai kin fito dashi kowa yaci a gidan na. Tun da muma
duk abunda muka samo dake ake cinsa. Ehe! "Sai a lokacin Lami tayi magana, "Lallai yau naga abunda ya
girmi kakana! Dama haka halinki yake Sarah? Lallai! Dama ance makashin ka na tare da kai. Wai ni yau y'ar
da na haifa da ciki na ce take kyamatar bani abunda take fita tana samowa. To Wallahi fitowa za kiyi fi fad'a
min uban da yayi maki ciki, don billahil lazi bazan kyale sa ba, list zan yi masa na abubuwan da zai kawo
cikin gidan nan. Don ba zai yuwu in ciyar da ku y'ay'ana ba, kuma sannan in ciyar da y'ay'an ku ba. Ko su
y'an uwanki da kika ga ina d'awainiya da y'ay'ansu, biyana suke yi su da samarin nasu. Ki fito don ubanki
Nuhu kamun nazo d'akin nan na idda ke!"

_Ya kuka ji labarin?_

https://chat.whatsapp.com/J22NLS9qVTz0L9CatOjFr7

08128755583 WhatsApp only!


[09/09, 10:03 AM] Matar Sayyadee: 🦜 *_K'ANWAR MATATA_*🦜

_Matar Sayyadee_
_Wattpad @Matar_Sayyadee_

*ZAFAFA WRITER'S ASSOCIATION*


☀️

Page 2

Sarah dake matsar hawaye zaune a bakin gado ta mik'e ta fito ta tsaya nan daga bakin k'ofa ba tare
da ta kalli inda su Lamin suke ba. Sama kawai ta zubawa idanu tana kallon hadarin da ke k'ara had'uwa.
"Oh ni inzo nan ke nan in same ki ko, shafaffa da mai!" Fad'in Lami a fusace kamar zata yo kanta. A hankali
Sarah ta sauko daga kan dandamalin k'ofar d'akin ta nufi inda su Lamin suke tana kallon k'asa. "Munafuka
annamimiya, makira! Sai ki rik'a yi sumumi-sumumi kamar ta kirki, ashe a bayan fage Allah kad'ai ya san
abubuwan da kike shukawa. Ya kiyi magana ko sai na hamb'are ki a nan wajen?" Lami ta fad'i tana mai kai
mata duka Sarah tayi saurin kaucewa. "Lami wannan yarinyar fa ba magana za tayi ba sai ki had'a mata da
duka. Kin fi kowa sanin irin taurin kai da kafiyarta tun tana k'ank'anuwarta. Ke kika bamu labari idan tayi
zuciya ko nono kika bata bata karb'a, idan kuma kika matsa mata ta kama, to ranar kan nonon ki kamar zai
tsinke tsabar cizon da take ganna maki. Ai wannan yarinyar jaraba ce a gidan nan. Ita ta d'ebo halin tsoho
kaf!" Fad'in Hassana tana hararar Sarah. Sarah kuwa wani d'agowa tayi ta watsa mata harara tare da fad'in,
"Idan ni annoba ce, ke kuma wulak'antacciya tsinanniya mai zagin uban da yayi sanadiyar zuwan ki duniya!
Na gwammaci inyi ta d'ebo hali da dabi'un mahaifina har k'arshen rayuwata da in d'auki irin naku halin. Ko
kunya bakya ji, babu aure amma kin ajiye y'ay'a uku duk shegu. Kuma a hake kike fita kina yawo kowa ba
kallon ki yana nuna ki a unguwa. Ku jawo mana abun fad'a da zai bibiyi tsatson mu har k'arshen mu. Allah
ya isa tsakani na daku kun hana ni aure saboda mugayen halayen ku. Duk wanda ya fara zuwa waje na,
k'ark'arinsa sati d'aya, shima kamun ya gano asalin su wanene y'an gidan mu. Yana ganowa yake blocking
d'ina kuma ba zai sake dawowa ba." Ta k'arisa maganar tana mai fashewa da kuka. "Kutumar bura uba......!
Lami kina jin irin maganganun da y'ar iskar yarinyar take min a cikin gidan nan ko!" Fad'in Hassana tana
mai nuna Sarah da hannu tare da girgiza jiki. Kau da fuska Sarah tayi tana mai kallon gefe. Lamin kuwa
d'aga hannu tayi ta wanke fuskan Sarah da mari sai da tayi taga-taga zata fad'i, sai Allah ya taimaka ta tsaya
da k'afafunta tare da dafe fuskan tana kallon Lamin hawaye na zubo mata. "Dan uban ki Nuhu, ita sa'ar ki
ce da zaki tsaya kina mata rashin kunya? Ta tara y'ay'an shegun dan ubanki! Ke menene wannan yanzu a
cikin ki? Shegiya kema kina tare da abun gorin amma kike yiwa wata. Za kici ubanki dani a cikin gidan nan
idan na kafa maki k'ahon zuk'a." Fad'in Lami tana mai nuna ta da yatsa. "Lami ke baki gano ta bane? So
take ki mance da maganar da kika soma na sai ta fad'a maki uban cikin dake jikinta." Fad'in Marfu'a.
"Kwarai sai yanzu na fahimci zancen Marfu'a. To ban mance ba dan ubanki. Uban wa ya yayi maki tsirara ya
kwashi albarkatun roman jikin ki? Nace wani shegen ne yanzu in fita in kwankwasi gidan su?" Fad'in Lami
tana mai jawo Sarah gabanta. Sarah kuwa wani kukan ta kuma fashewa dashi tare da duk'awa a wajen tana
fad'in, "Ni dai Allah ya san cewa babu namijin da ya tab'a kaiwa ga jikina. Ni ban ta yaya ciki ya shiga jikina
ba wallahi." Baki sake Lami da y'an uwan ta suka bita da idanu. Na'ima ce tayi k'arfin halin fad'in, "To a
ruwa kika sha dab kutumar uban ki? Kuji min shegiyar yarinya zata mai damu y'an iska wanda basu san
inda ke masu ciwo ba." Lami kuwa tsabar takaici bata san lokacin da ta kai k'asa inda Sarah take duk'e ta
shak'o wuyarta tare da wanke fuskanta da mari hagu da dama sannan ta tura ta baya ta fad'i dab'as sai da
ta dafi k'asa da duka hannayenta biyu. "Ku shiga d'aki ko waccen ku ta d'auko lafiyayyan bulalanta kuyi ta
jibgar shegiya har sai ta magantu tukun zaku kyaleta. Ni anya kuwa ba canje aka yi min a asibiti ba kuwa?"
Lami ta fad'i tana shurin Sarah da k'afafunta. Gab'a d'ayan su kuwa dama cike suke da ita, ko wacce ta
d'auko bulalanta a hannunta tayo kan Sarah suka shiga lafta mata bulala ta ko'ina a jikinta. Tsabar zuciya
irin na Sarah ko gezau, kuma gashi tana jin azaba duk sanda bulalar ta sauka a fatar jikinta. Don har rige-
rige suke yi wajen aje bulalar a kan fatarta. Ita burinta d'aya, Allah yasa wajen dukan nata su zubar da cikin
dake jikinta ta huta da mugun abun kunyar nan da take d'auke dashi. "Wallahi duk wacce ta k'ara kai duka
jikinta sai ta bar gidan nan a cikin daren nan tunda ba gidan uwar ku bane." Fad'in mahaifin su da
fitowarsa kenan daga cikin d'akinsa. Wani yamutsatstsan tsohe wanda wahalar rayuwa duk ta gama
cinyesa ya fad'i hakan hannunsa rik'e da sanda yana dogarawa har ya k'ariso inda Sarah ke duk'e a k'asa.
D'aga sandar yayi kamar zai makawa Na'ima da ta kuma d'aga bulalar zata zabgawa Sarah, sai tayi saurin ja
baya tare da fad'in, "Kul! Wallahi kar ka kuskura ka tab'a ni da k'azamar sandan nan naka. Don kana sauke
min sandar a jiki, kaji na rantse maka sai na rama." Ta fad'i hakane tana mai zaro masa idanu kamar shima
zata kai masa bulalar dake hannunta. Mik'ewa Sarah tayi a zafafe tare da fad'in, "Wallahi kika tab'a jikin
mahaifina sai na kashe ki a cikin gidan nan, ai nafi shekaru sha takwas a duniya, hakan na nufin na isa
d'auri." Matsowa kusa da Sarah yayi yana d'ingishi tare da fad'in, "Kul, Saratu! Kar in kuma jin kin sake
furta irin wannan maganar. Ke d'in yarinyar albarka ce. Ki barta, duniya ta ishi kowa riga da wando, wanda
bai shigo bama jiransa take yi. Kiyi hak'uri kin ji. Koma d'aki. Idan kowa be yarda da ke va, bi na yarda dake
y'ata. Ke kuma, kije Allah ya isa tsakani dake. Allah zai min sakayya Lami." Wani irin gud'a Lami ta saki tare
da fad'in, "Wallahi Allah ya isar ka babu inda zata je sai dai ta koma kanka. Ai nice ma ya kamata nayi maka
Allah ya isa irin wannan uk'uba da na sha a gidan ka kamun Allah ya wanke y'ay'a mata shidda ya bani. Dan
ma dai gud'a d'aya a cikin su azzaluma ce mai irin halin ka wacce bata son share min hawaye. Yanzu
wannan akurkin kake tutiya dashi har kake kira gida? Lallai! Bayan da ba dun taimakon su y'ay'an da kullum
kake zagi da ikirarin zaka kore su sun taimaka sun d'an yi gyare-gyare a gidan ba, har zai kallu balle ma a
kira sa gida. Ka dai ji kunya wallahi Nuhu. Kuma y'ay'ana babu inda zasu je. Zama a cikin gidan nan dole,
idan kaji ana daram dam-dam to ni da y'ay'ana kenan a cikin gidan nan. Sai dai idan kai ne zaka fice ka
bamu waje don billahil lazi naci gida! Y'ay'a bakwai na haifar maka, d'aya namiji, sai tsala-tsalan mata har
shidda. Ni ai wallahi har yau tsinewa soyayya nake yi da har ta rufe min idanu ta jani da kyawuna na fuska
da na jiki amma na b'uge da auren fak'iri irin ka wanda aka haifesa da bak'in fentin talauci. Nuhu ka fita
harkata da ta y'ay'ana tun kan in kai ka k'ara kotu a raba tsakanin mu." Wani dogon tsaki Nuratu taja tare
da fad'in, "Ni wallahi Lami ban san mai kike yi har yanzu da wannan tsohon ba da baki rabu dashi ba. Ke
kan ki da zaki d'au wanka ki fara shafa mayuka masu gyare jiki kina hawa leses masu tsada da atampofi,
wallahi da wani mayen mai kud'i zai yi wuff dake kema kije kici arziki ki bar arziki inda yake. Don wallahi ba
wani tsufa kika yi ba, kawai wahalar wannan tsohon ne ya mai da ki haka." Ta k'arisa maganar tana hararen
mahaifin nata. Shi kuwa wani irin kukan bak'in ciki ya fashe dashi tare da dogara sandar shi ya juya ya
koma d'akinsa wanda ba k'aramin abu yake fitowa dashi ba, ko alwala da sallah a ciki yake yi. Yana da
bahon da yake alwala a ciki, sannan kuma akwai wani bokitin penti k'arami da yake yin fitsari ko ba haya a
ciki wanda Sarah ce ke d'awainiyar fitar dasu tana zubar da abunda yake ciki tare da wankewa sannan ta
dawo masa dashi ta ajiye. Da sauri Sarah tabi bayansa ita ma tana kukan tana kuma bashi hak'uri. Lami
kuma harara ta bisu dashi tare da fad'in, "Munafukan banza da wofi! Kin ga yarinyar nan, wallahi za'a iya
had'a baki da ita a kashe mu. Kuma zan yi maganin ta." Tana gama fad'in haka taji an banko gidan da k'arfi
an shigo da gudu tare da afkawa d'akin ta. Da idanu duk suka bishi a tsorace, dai-dai lokacin da wani
matashi shima ya fad'o gidan ya tsaya tsakar gida hannunsa rik'e da k'atuwar adda yana huci. Gaba d'aya
su Na'ima suka koma bayan Lami a tsorace. Shi ko matashin ya k'ariso har inda suke fuska babu rahama
tare da karta addan a k'asa yace, "Na rantse da ubangijin Yunusa da Musa, idan ba'a fiddo min da wayar
k'anwata da d'an ki ya kwata yanzu ba, duk sai na sassare ku a cikin gidan nan. Ni dashi kar ta san kar
billahil lazi. Dalla malama ware ki amso min waya a hannun kafurin d'an ki ko kuma yanzu lahira tayi
bak'o." Ya k'arisa maganar yana zarowa Lami idanu. Jikin Lami da y'ay'anta gaba d'aya babu inda bai rawa
saboda kaf cikin gari babu wanda bai san *Naliliyo* ba. D'an daba ne sosai wanda kisan mutum a wajensa
kamar take kiyashi ne. Da sauri Lami ta juya zata shiga d'akinta domin karb'o wayar, sauran y'ay'an zasu
rufa mata baya ya daka masu wata uwar tsawa tare da fad'in, "Duk wata kafurar da ta motsa a cikin ku sai
na kashe a nan waje." Gaba d'aya suka k'ame k'am kamar an dasa bishiya. Mintuna kad'an sai ga Lami ta
fito hannunta d'auke da iPhone 7plus a hannunta ta mik'awa *Naliliyo* har da d'an duk'awa. Fizge wayar
yayi tare da nuna Lami da hannu sannan yace, "Ki hawa kafurin d'an ki kunne, wallahi ko da wasa na k'ara
ganinsa ya gitta ta k'ofar gidan mu, to gawarsa ma sai tayi maki wuyar gani." Yana gama fad'in haka ya juya
ya fice daga gidan. Na'ima ta saki dogon tsaki tare da fad'in, "Wannan d'an iskan wata rana sai ya jawo
mana abunda zai saka a k'ona mu da ran mu a cikin gidan nan. Kullum fa sai kin bashi kud'i amma duk da
haka sai ya fita ya jawo mana magana. To gashi nan dai yau ya d'auko mana maganar *Naliliyo* har yana
ikirarin zai kashe shi. Wallahi kiyi masa magana Lami ya fita harkan gidan jarababben d'an DABAN nan.
Tom!" Kamun Lami tayi magana Lukman (lucky boy) ya fito a fusace yana mai tsira mata hannu tare da
fad'in, "Zan ci uwarki a gidan nan idan kika k'ara saka mun baki a cikin al'amura na. Ke uban wanene bai
san cewa ke tantiriyar karuwa bace mai y'ay'a har biyu na shegu, dan ma d'ayan ya fad'i ta hannu hagu
(Mutuwa) da yanzu y'ay'an ki uku duk shege. Wallahi kika k'ara saka min baki a cikin al'amura na, sai na
maki mugun duka a cikin gidan nan. Y'ar iska taxi no garage!" Kallonsa Lami tayi a fusace tare da fad'in,
"Kai! Kai Lukman!! Kayi min shuru a wajen nan. Kar in kuma jin bakin ka. Ba yarka bace ita? To ban so ka
k'ara fad'in wannan maganar. Ka shiga d'aki ina zuwa akwai wasu kud'i da na ajiye maka." Juyawa Lucky
boy yayi yana wani tafiya a b'ankare tare da fad'in, "Karfa ki dad'e kin san ban son jira." Lami kuma mai da
dubanta tayi izuwa wajen Na'ima tare da fad'in, "Kin san dai ba hankali bane ya ishe sa, ki rik'a fita harkan
sa." Turo baki Na'ima tayi tare da wucewa fuuuu tana fad'in, "Ai ke Lami sam baki son laifinsa, kullum sai
dai ki rik'a d'iban kud'i kina bashi yana zuwa yana shaye-shaye dasu." Lami bata ce komai ba ta wuce d'aki
domin bawa Lucky boy dubu biyar d'in da tayi masa alk'awari jiya. Sauran y'an matan ma duk suka shige
d'aki. Sai da Sarah taji shuru a tsakar gidan sannan ta fito ta nufi pampo ta d'auro alwala saboda kwala
kiran sallar isha'i da taji ana yi a masallacin dake gaban gidan su kad'an. Dawowa d'akin tayi ta taras da
duka yayyinta a ciki ko wacce sai cab'a kwalliya take yi saboda lokacin fitar su yayi. Dama haka suke yi,
wasu idan sun fitan ma, sai suyi kwana biyu, uku har sati basu dawo ba. Wata rana kuma a ranar suke
dawo can cikin dare. Darduma Sarah ta shimfid'a ta tada sallar isha'i, don dama ita kad'ai ce a cikin su take
yin sallar, to Lamin ma bayi take yi ba balle ta saka su a hanya. Sai bayan ta idar ta sallah ne ta saka
doguwar riga irin mai kama jikin nan, sai ta d'aura k'atuwar suwaita a kai sabida sanyin da take ji. Tana
cikin zuge zip d'in suwaitar aka kwad'a sallama a cikin gidan nasu tare da fad'in, "Wai ana sallama da Sarah
inji Farouq." Ras gaban Sarah ya yanke ya fad'i, don gani take yi kamar tana fita suka hada idanu zai gane
akwai ciki a jikinta. Da sauri ta lek'o tsakar gidan tare da fad'in, "Kace tana zuwa yanzu." Tana gama fad'in
haka ta dawo d'akin domin d'aukar hijjab d'in da ta cire yanzu bayan ta idar da sallah. "Kanin ubanta yazo,
jikinta sai rawa yake yi domin taje ta gaida shi." Fad'in Nuratu tana hararar ta. K'ala Sarah bata ce ba, sai
ma hijjab d'inta da ta fara k'ok'arin sakawa. "Shegiya ko irin jan ajin nan baki iya ba. Daga ya turo jikin ki na
rawa zaki fita." Fad'in Marfu'a. Sarah kuwa ko kallo basu ishe ta ba, ficewa ma tayi daga d'akin bayan ta
gama sanya hijjab d'inta. A k'ofar gidan ta ganshi sanye da wando jeans da blue T-shirt, kansa sanye da
facing cap ya jingina da wani k'arfe dake jikin gidan mak'otan su yana kallon d'aid'aikun mutanan da suke
fitowa daga masallacin kasancewar ba'a jima sosai da idar da sallah ba. Juyowa yayi tare da zuba mata
idanu har ta k'ariso inda yake tare da fad'in, "Sannu da zuwa. Ina wuni?" Kallonta yake yi for almost 2mins
kamun ya bud'e baki yace, "Ina kika je d'azu na ganki kin ruwa ya maki duka?" Saurin d'agowa tayi ta zuba
masa idanu, sai kuma ta sunkuyar da kanta gabanta na fad'uwa don gani tayi makar zai ga an rubuta _Ina
d'auke da ciki_ a kan goshin ta. "Tambayar ki nake yi kin yi min shuru." Farouq ya sake magana a karo ba
biyu. Sai a lokacin Sarah ta bud'e baki tare da fad'in, "Asibiti naje." Kallonta yayi tare da maimaita "Asibiti."
K'ara d'agowa tayi ta kallesa a karo na biyu, sai kuma tayi saurin kau da kai tana kallon k'asa tare da wasa
da zoben dake hannunta. "Are you sick Sarah?" Girgiza kai tayi tare da fad'in, "Dubiya naje yi. Lokacin da
na fito kuma ban samu abun hawa ba saboda hadari. Shine ruwan ya duke ni, amma kuma ba fake. Da
ruwan yayi sauk'i ne shine na fito shiyasa ka ganni a jik'e." Ajiyar zuciya Farouq ya sauke tare da fad'in,
"Amma baki san hakan da kika yi zai iya jawo maki rashin lafiya ba. Mai yasa ma baki kira ni nazo na d'auko
ki na dawo dake gida ba? And ina ta kiran wayar ki bakya d'aga wayar." Ya fad'i hakan yana mai folding
hannunsa. Ko kamun Sarah tace wani abu an banko k'ofar gidan su, cikin sauri duka su biyun suka juya
suka kalli k'ofar gidan. D'an duk'awa Farouq yayi tare da fad'in, "Mama ina wuni?" Harara Lami ta watsa
masa tare da fad'in, "Uwar ka ba, ka baro ta can gida. Ni ba mamarka bace. Kaga wacce ta haifa nan." Ta
k'arisa maganar tana mai nuna Sarah da hannu sannan ta cigaba da fad'in, "Ba gaisuwa ka na taho nan in
amsa ba, zuwa nayi ka fad'a min shin kai ne uban cikin dake jikin Saratu ko kuwa. Don idan kai ne, wallahi
na rantse list d'in ka daban ne. Kuma kar kayi tunanin zan yi maka ragi." Hannu Sarah ta d'aura a kai tare
da fad'in..................

*_Chart me up 08128755583_*
[09/09, 10:03 AM] Matar Sayyadee: 🦜 *_K'ANWAR MATATA_*🦜

_Matar Sayyadee_
_Wattpad @Matar_Sayyadee_

*ZAFAFA WRITER'S ASSOCIATION*

Page 3

Hannu Sarah ta d'aura a kanta tare da fad'in, "Haba Lami wannan wani irin magana kike yi haka? Mai
yasa a kullum burin ki, ki zubar min da mutunci a idanun Farouq? So kike kiyi ta danka mu a cikin gidan
babu aure?" Sarah ta fad'i tana kuka sosai. Shi kuwa Farouq da idanu kawai yake bin Sarah da mahaifiyarta
kamar wawa. Don sam bai son gasgata abunda kunnuwansa suke ji. "Bak'ar munafuka! To sai nayi magana.
Wato baki so nima na samu rabo na ko? To wallahi komai dani za ayi shi. Juyo nan ka bani amsar
tambayata, shin kai ne uban cikin dake jikinta?" Wani irin b'acin rai ne yake tasowa tun daga can k'asan
zuciyar Farouq, bai iya magana ba sai kallon fuskan Sarah yake yi yana son jin wani k'arin bayani ko kuma ta
k'aryata zancen da mahaifiyar nata take yi. Amma maimakon haka, Sarah sai girgiza kanta kawai take yi
hawaye na zubowa daga idanunta. "Wai ba da kai nake yi bane Umar da kayi min banza kamar wata sa'ar
ka!" Lami ta fad'i a zafafe. Gyara tsayuwa Farouq d'in yayi tare da kallon Lami k'asa-k'asa sannan yace, "Ban
san maganar da kike yi akai ba! Kwata-kwata ma ban fahimci mai kike cewa ba Mama." Dak'uwa Lami tayi
masa tare da fad'in, "Uwarka nace kaji? Ai nasan ka fahimci wannan ko! To ni menene ma na tsayawa sai
naji ko kai ne kayi cikin ko ba kai bane. Bayan na san kai d'in fak'iri ne ba wani abun kirki zan samu daga
gare ka ba. Amma sai dai ka sani, daga yau ban k'ara bata ko loma d'aya daga cikin abincin gidana, don sai
taci ne abun cikinta zai ci, kuma ni da in ciyar da jinin ka, gwara na ciyar da karuwai goma babu lada."
K'asa-k'asa Farouq yace, "Ai yanzu ma karuwan kike ciyarwa a cikin gidan." Kallonsa Lami tayi tare da
matso da kunnanta tace, "Kace me?" Kau da kai Farouq yayi tare da fad'in, "No babu abunda nace!" Dogon
tsaki taja sannan ta juya ta shige cikin gidan har da bugo masu k'ofa. Kicib'is suka ci da Na'ima taci uban
kwalliya ta tsuke cikin k'ananan kaya kamar d'iyar arna, "Y'ar albarka har zaki wuce?" Yamutsa fuska tayi
tare da fad'in, "Eh! Idan kun ji shuru ku rufe gidan kawai, don ba lallai na dawo gida na kwana ba." "To
Allah ya tsare." Fad'in Lami har da d'aga mata hannu. Duk abunda Na'ima da Lami suke cewa, tsaf a
kunnan Sarah da Farouq. Fitowa Na'ima tayi daga cikin gida tare da gallawa Farouq harara ta saki tsaki tare
da tsirtar da yawu. Har tayi gaba, sai kuma ta dawo dai-dai inda Farouq d'in yake a tsaye tare da sauke
glasses d'in fuskanta k'asa kad'an sannan tace, "Ina fatan masoyiyar taka ta fad'a maka tana d'auke da ciki
har na tsawon sati biyu." Ta k'arisa maganar tana daga yatsunta biyu a fuskan Farouq d'in. Wani banzan
kallo Farouq ya bita dashi mai cike da tsana. Sarah kuwa ji tayi dama tana da layar b'ata ta danna kawai ta
ganta a cikin gida saboda tsananin kunya mai had'e da tsoro da take ji. Farouq yana kallo Na'imar ta bud'e
gaban motar wani mutum wanda a haife ta haife ta, yaja motar suka bar layin. Juyowa yayi tare da kallon
Sarah wacce kanta ke k'asa, ya jima yana kallonta tare da had'iye wani miyau mai d'aci da ya tokare masa
mak'oshinsa sannan yayi k'arfin halin fad'in, "Sarah mai nake ji haka daga bakin mahaifiyarki da y'ar
uwarki?" Kuka kawai Sarah ta fashe dashi do ita kanta abun jinsa take yi kamar hauka ko rainin hankali ta
bud'e baki tace bata san ta yanda aka yi ciki ya shiga jikinta ba. D'agowa tayi ta kallesa tare da fad'in, "Ni
wallahi tallahi....." D'aga mata hannu yayi tare da fad'in, "Na fahimta, basa son alak'ata dake ne shiyasa
suke son raba mu da wannan zancen na su. Ni kuma idan har ba canza hali za kiyi ba Sarah, babu mai raba
mu idan ba mutuwa ba. Ni dai alfarma d'aya nake rok'o a wajen ki Saratu, dan girman Allah ko sau d'aya
kada rayuwar da y'an uwanki suke yi ya burge ki. Idan kika mun haka, ni kuma zan cigaba da tsaya miki duk
rintsi, kunnuwata zasu kasance a toshe, haka babu wani suka naki ko kuma laifin y'an uwanki da za ayi
amfani dashi wajen nuna min bak'inki har yayi tasiri a waje na." Kuka Sarah take yi har da shasshek'a, ita
kad'ai tasan mai take ji a cikin zuciyarta. "To wai kukan na miye ne haka? Idan har ba b'acin rai na kike son
gani ba, ki share wad'annan hawayen naki." Bayan hannu Sarah ta saka ta share hawayen fuskanta tare da
k'irk'iran murmushin babu babu inda ya tsaya sai iya lab'b'anta. "Yauwa ko ke fa! Sannan abu na gaba, ban
ji dad'in yanda ba ganki d'azu ba, na d'auka tuntuni mun riga mun gaba magana akan irin shigar da kike yi.
Kin san fa da shigar jikin mutum kad'ai akan iya gane wanene shi. Dan girman Allah ki daina saka wannan
zaro-zaron gashin idanu nan da wannan k'umbar dake hannunki. Ni wallahi kyama yake bani. Wanda Allah
yayi maki ma ya ishe ki Sarah." Hawaye na zuba a idanunta ta furta, "In sha Allah daga yau ba zan k'ara
saka d'aya daga cikin abunda ka lissafo ba." Ajiyar zuciya Farouq yayi tare da fad'in, "Allah ya miki albarka
amaryata ta sati hud'u masu zuwa. Ki shiga gida hadari ne sosai a gari. Sai mun yi waya." Bata iya cewa
komai ba sai murmushin da tayi tare da yi masa bye-bye ta shige cikin gidan. Tana turo k'ofa ta jingina da
k'ofar tare da dafe k'irjinta da hannu d'aya sannan ta toshe bakinta da d'ayan hannun tana kuka sosai.
Juyawa tayi ta lek'a ta wani d'an rami a jikin k'ofar, ga mamakinta sai ganin Farouq tayi tsaye a wajen
amma ba k'ofar gidan yake kallo ba, wani wajen yake kallo daban. Can kuma ya saki ajiyar zuciya tare da
tsallake kwatar dake gaban gidan ya wuce. Sai a sannan Sarah ta zame k'asa ta fashe da wani irin kuka mai
tafasa zuciya. Ta jima a wajen tana kuka kamun ta mik'e ta nufi cikin gidan. D'akin su ta shiga ta cire hijjab
d'in jikinta ta ninke tare da rataye sa a hannun wardrobe sannan ta cire suwaitan jikinta ta mak'ale a abun
rataye jaka sannan ta kashe wutar d'akin don babu kowa a ciki, sauran y'an uwanta suna d'akin Lami
kamun masu zuwa fita dasu su k'araso. Hawa kan gadon tayi ta kwanta rigingine tana sak'awa da
warwarewa akan cikin dake jikinta. Sosai tayi zurfi a tunanin ta yanda aka yi ta samu ciki, sai dai duk iya
zurfin tunaninta, bata gano bakin zaren ba, don zata iya dafa Qur'ani tayi rantsuwa bata tab'a sanin wani
d'a namiji ba a duk tsayin rayuwarta. Daren ranar bacci b'arawo ne ya kwasheta. Kiran sallar asubahi kuwa,
a kunnanta ladani ya kwad'a shi. Saukowa tayi daga kan gadon tare da kunna wutan d'akin haske ya kawo,
babu kowa a d'akin, hakan ne ya tabbatar mata da ita kad'ai ta kwana a d'akin. Don da ace y'an uwanta
sun dawo daga yawon banzan su jiya, babu abunda zai saka su kyale ta ta kwanta a kan gado ba tare da
sun turo ta k'asa ba. Kai tsaye d'akin mahaifinta ta nufa, kamar yanda tayi tsammani hakan ce ta faru.
Zaune ta samu mahaifin nata ya fuskanci gabas yana sallah a zaune. Don ciwon k'afar nasa bai barin sa yayi
sallah a tsaye. Tun kusan shekaru biyar baya sallah dare ta zame masa tamkar jinin jikinsa. K'arfe uku
kamar a kunnansa take bugawa saboda sabo da tashi. Bai kuma komawa bacci sai gari yayi tarwai tukun.
Sarah d'aukar roban pentin da yake yin bowali tayi ta fitar dashi tare da zubar dashi a makewayi sannan ta
dawo dashi ta ajiye sannan ta fita ta koma bayin ta kamo ruwa sannan ta fito ta d'auro alwala. Kamar zata
wuce, sai kuma wani zuciyar ta jata ta nufi d'akin Lami. Tun daga bakin k'ofar take jin wani wawan
munshari mara dad'in sauraro kamar an danne rago. Hannu ta d'an d'aura akan k'ofar ta tura, sai taji k'ofar
a bud'e. Tura kai tayi ta shiga d'akin tare da lalubar bango ta kunna globe d'in dake d'akin. Lami ta hango
tayi wani irin washarere a kan gadon kamar gawa, babu riga a jikinta daga ita sai d'aurin k'irji, shi kansa
zanin yayi gefe, mamukanta kuwa d'aya ya kalli arewa, d'aya ya kalli kudu. Gata Ma sha Allah irin jibga-
jibgan matan nan ne. Hatta bakinta a bud'e yake. Kau da kai Sarah tayi ta kalli d'ayan gefen da autarsu y'ar
shekaru goma sha bakwai da watanni take. Ita ma dai bacci take yi cike da rashin tsari domin bacci ne irin
wanda ba'a son musulmi ya rik'a yi wato ruf da ciki. Hannu Sarah ta kai ta d'aka mata duka cinyarta ta baya
da yake a kwaye. Da sauri Aina'u ta kai hannu wajen ta Sosa ba tare da ta yanke baccin da take yi ba. Wani
dukan Sarah ta kuma kai mata, wannan karan a furgice ta mik'e tana mitsitsitsike idanu tare da sakin wani
irin hamma kamar d'iyar arna. Sai da ta ware rass sannan ta k'arewa Sarah kallo wutar balbalin bala'i na
taruwa a kwayar idanunta. Don Aina'u irin fitsararrun yaran nan ne wad'anda duk girman mutum ko da
kuwa jikinsa kaf furfurace bata raga masa. Y'an unguwanmu sun ce ita ce tayo sak halin Lami, wasu sun ce
tafi Lami d'in ma. Tun tana k'ank'anuwarta makirar yarinya ce ta bugawa a jarida. Ga salo kamar wata uwar
mata. "Uwar me zan maki cikin daren nan da zaki zo ki katse min bacci na!" Fad'in Aina'u kamar harcenta
zai zazzago, don ta kasance irin matan nan masu harshe. Duk yanda tayi magana a hankali, ji za kayi kamar
a kwar gida take magana. Da dare da rana basu da bambamci a wajenta. Yanzu haka da tayi magana
kasancewar dare mai d'aukar sauti, har sai da mahaifinsu dake d'akinsa ya jiyo sautin muryanta. Hatta
Lami mai bacci kamar gawa sai da ta farka a firgice tana sambatu. "Sallah nazo tashin ki kiyi. Don gashi can
shirin tada sallar ake yi a masallaci. Ace duk k'arar speaker d'in masallacin can ba zai iya tada ku kuyi sallah
ba!" Fad'in Sarah tana mai k'ok'arin juyawa ta bar d'akin duk da kuwa ta san cewa ba sallar za suyi ba.
"Dan ubanki baza muyi sallar ba. Idan mun d'aga k'afa zamu shiga aljanna sai ki dawo damu baya saboda
ta ubanki ce! Fita ki bar d'akin nan tsohuwar annamimiya!" Fad'in Lami tana mai nuna mata hanyar k'ofa.
Komai Sarah bata ce ba, sai ma ficewa da tayi daga d'akin ta koma nata d'akin ta shimfida darduma ta tada
salla. Tana nan zaune ko da ta idar da sallar har sai da gari ya waye tass, lokacin k'arfe bakwai sannan ta
soma jin bacci a idanunta, amma kuma bata son yin baccin. Burinta ta shirya ta kuma fita domin yawon bin
asibitoci ko za tayi dace da asibitin da scanning machine d'insu zai k'aryata cikin da wasu asibitocin da suke
cewa tana dashi. Ta yunk'ura zata tashi daga kan sallayar taji muryoyin mata na tashi a tsakar gidan su.
Gabanta ne ya buga da k'arfi sai tayi saurin d'aga labule kad'an ta lek'a waje. Da sauri ta saki labulen tana
mai dafe k'irjinta da zuciyarta ke barazanar fasowa ta fito saboda arba da tayi da yayyin Farouq mata uku
da kuma aunties d'insa guda biyu, gaba d'aya fuskokinsu a turbud'e..............

_Ko mai zai faru a gaba?🤔_

*AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE*


_Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya
tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda
ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu
almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki
da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da
'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace
idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa
kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA
KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah. Please don Allah duk
wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu 'batawa kai
lokaci🙏🏻_

_*infection*_
_Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye! infection
yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu'amula mussaman ga ma'aurata, sanyi
ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za'a dace_ _*SAI AN
GWADA AKAN SAN NA KWARAI*_
_07084653262_
[09/09, 10:03 AM] Matar Sayyadee: 🦜 *_K'ANWAR MATATA_*🦜

_Matar Sayyadee_
_Wattpad @Matar_Sayyadee_

*ZAFAFA WRITER'S ASSOCIATION*

Page 4

"Ah'aaa! Yaya haka, menene haka kuma zuwa da sassafen na sai kace karb'an kud'in bashi? Ni fa bani
son irin wannan naci tun ba'a je ko'ina ba." Fad'in Lami wacce fitowarta kenan daga d'aki baki duk miyan
bacci. Bayanta kuma Aina'u ce ke mik'a tare da hamma babu addu'a sai wani "umm'iyyyyyyy!" Take fad'i
kamar k'atuwar rago ko kuma bijimin sa. D'aya daga cikin matan wacce sai jijjiga take yi, ga dukkan alamu
tafi kowa a cikin su hassala tace, "To dama uban me zai kawo mu wannan wulak'antaccen gidan wanda
babu albarka cikinsa in ba tsautsayi ba. Banda fitina da jawowa kai jidali irinta Umar Farouq, menene abun
so a cikin y'ay'an gidan nan wanda gaba d'aya kowa ya gama sanin karuwan gida ne su." D'ayar siririyar
cikin sy tayi saurin cafe zancen wajen fad'in, "Aunty Bilkisu ai gansama-gansaman zaurawar gidan nan sun
wuce karuwan gida, don ni kam ba zan Kira su da y'an mata tunda tun daga kan babbar har k'aramar babu
wacce bata san dad'in d'a namiji ba." Saurin cafe zancen k'aramar cikin su tayi tare da fad'in, "Yo aunty
Halima ai ga zahiri tunda kina ganin shegu ta kowani lungu na gidan an ajiye. Kai Allah yai wadaran naka ya
lalace. Wallahi ko wucewa ta kwar gidan nan ban k'aunar yi balle har in tako k'afata cikin gidan nan." Lami
kuwa dake tsaye suke fad'in duk abunda yazo bakinsu, wani shewa tayi tare da nuna wacce aka kira da
aunty Halima tace, "Alhamdulillah, ko yau na fad'i na mutu za'a nuna abunda na bari ace Allah sarki ga
y'ay'an wance da ta bari. Ke kuwa fa? Ko b'ari kin tab'a yi ne? Idan fitsari banza ne, kaza tayi ma. Kuma
y'ay'ana Kainuwa ne, babu yanda aka iya dasu. Duk wani munafurcin ku da k'ananun maganganunku,
kanku zai koma." Aunty Halima wani tsalle ta daka kamar za tayi wasar y'ar gala-gala sannan ta bugi k'irji
kare da fad'in, "Haihuwa idan har irin taki ce Lami, kada Allah ya bawa ruwan maniyy d'in mijina isa ga
mahaifata. Ai da Haihuwa irin y'ay'anki wallahi gwara b'arinsu. Lami haihuwa irin taki ko, na gwammaci har
in koma zuwa ga ubangijina ban ajiye ko kwai d'aya a duniya ba. Kuma ki bud'e kunnuwanki dakyau kiji,
idan har ni k'anwar mahaifiyar Umar Farouq ce, to wallahi auren sa da Sarah sai dai bayan raina. Domin
Na'ima har gida taje ta samu mahaifiyar Umar ta fad'a mata y'arki da ake son mak'alawa d'ana, tana
d'auke da ciki. Dama kuma banda hauka da rashin hankali, mai Farouq zai ci da d'iyar karuwa, tubabbiya
wacce sana'ar danginsu kenan karuwanci! Mun bar maku duk wani abu da aka kawo gidan nan da sunan
naiman auren y'arku, sai dai amma ki sani, babu aure tsakanin zuri'arki da namu zuri'ar." Wani irin
rushewa da kuka Sarah tayi jin abubuwa da Aunty Halima take fad'i
A bayyyane ta soma fad'in, "Shikenan, Farouq d'in ma ya sub'uce min. Dama na sani ba zan tab'a aure ba a
rayuwata." Ta fad'i hakane tana mai kaiwa cikinta duka da duka hannunta biyu. Lami kuwa kitchen d'in
dake tsakar gidan ta nufa tare da d'auko katoton tab'aryarta mai nauyi da tsayi tayo kan su Aunty Halima
don har cikin ranta taji zafin maganganun da aunty Haliman tayi mata. "Aunty Halima, aunty Halima!"
Siririyar mai suna Najma ta kwad'a kiran sunan aunty Halimar tare da fizgo hannun aunty Bilkisu ta janye ta
baya saboda kawo tab'aryar da Lami tayi. "Barta, barta ta jawowa kanta bala'i Najma. Wallahi ba zan gudu
ba, karyar hauka take yi, idan ta isa ta buga min taga abunda zai faru da ita yau d'in nan." Fad'in aunty
Halima amma deep down tana jin tsoran kar Lami ta buga mata zabgegiyar tab'aryar dake hannunta. Lami
kuwa k'ara yowa kansu tayi da tab'aryar ta d'aga sama zata kwad'awa aunty Halima da tayi k'arfin hali tak'i
guduwa. Caraf taji an rik'e tab'aryar ta baya, a fusace ta juya suka yi idu hud'u da Sarah wacce idanunta
suka kad'a suka yi jazur alamar tayi kuka. "Cika min tab'aryana ko inci ubanki cikin gidan nan!" Lami ta fad'i
da k'arfi tana mai zarowa Sarah idanun. "Dan girman Allah Lami kar ki tab'a su, ki kyale su. Yanzu idan kika
bugawa d'aya daga cikin su, RAI kuma yazo yayi halinsa, ya za kiyi?" Fizge tab'aryar tayi tare da fad'in, "To
idan na kashe sai me? Ko kotu aka je babu wanda za tuhume ne don sune suka biyo ni har cikin gidana.
Duba kiga cikin zuri'ar da kike son shiga, su kansu tun daga yanayin shigarsu zaki fahimci babu abun arziki a
gidan. Daga ganin kayan jikin wannan shanyayyiyar matan (Tai nuni da aunty Bilkisu) kayan jikinta kwance
ne. To a nan wajen mai na sama yaci balle ya baiwa na k'asa. Shashasha! Ni Allah ya yiwa Na'ima albarka
da har taje gidan su Farouq d'in ta fad'awa mahaifiyarsa kina d'auke da juna biyu. Dama kuma nayi
rantsuwa idan har ni y'ar Samuel da Debora ce ba zan tab'a bari kiyi aure da d'an iskan yaron nan ba. Sai
gashi Allah ga kawo hanya mafi sauk'i. Ke bama shi ba, babu ke babu aure da kowani namiji a duniya nan."
Salati gaba d'aya su Aunty Halima suka d'auka suna tafi. "Eh lallai! Yau na tabbatar da ke d'in cikakkiyar
arniya kuma bakatafiya ce ke. Kin fi k'aunar suyi ta gantali a titi suna yawon hotel-hotel suna kawo maki
kud'i kina musu goyon shegu ko? Tirr! Shiyasa aka ce idan za kayi aure ka auri uwa ta gari domin ta haifo
maka y'a'yana nagari. To kema kan ki ba tarbiyar gare ki ba balle ki bawa y'ay'anki tarbiyan." Kamun Lami
tayi magana, sai ga Na'ima da Nuratu sun shigo gidan a tare ko wacce hannunta rik'e da manya-manyan
ledoji. Washe baki Lami tayi tare da fad'in, "Ka ga y'ay'an albarka wanda aka haife su tsiya na barci!" Baki
sake su Aunty Halima suke kallon su Na'imar da sai wani yatsine-yatsine suke yi. "Lami akwai ruwan wanka
kuwa a gidan nan? Don ni wallahi a mugun gajiye na dawo. Mutun hud'u suka yi ciniki na." Amshe
maganar Nuratu tayi tare da fad'in, "Wallahi nima a gajiyan nake tib'is. Ni mutum d'aya ne ma ya d'auke ni
muka tafi _Asa pyramid_, wallahi ko runtsawa banyi ba. Ruwan zafi nake buk'ata sosai in galgasa jikina."
Washe baki Lami tayi tare da fad'in, "Y'ay'an albarka, y'ay'an gwal kenan. Babu ruwan zafi amma yanzu nan
zan had'a wuta na d'aura maku, ku shiga daga ciki naga alama babu k'arfi a jikin ku gaba d'aya duk kun yi
laushi." Su aunty Halima kuwa, wannan ta kalli wannan, sai wannan ta kalli wannan, haka su kayi tayi
tsakanin su suna mamakin hali irin na Lami. "Way'annan kuma mi suke yi a nan gidan?" Fad'in Nuratu tana
kallon su d'ai-d'ai. Sai da Lami ta balla masu harara sannan tace, "Wai zuwa suka yi su fad'a mana sun
janye auren da suke nema na Sarah. Baki ganni da tab'arya a hannu ba, ai tahowa nayi in sheme y'an iska."
Gaba d'aya daga Nuratun har Na'ima kallon Aina'u suka yi tare da fad'in, "Ke dan ubanki tsayuwar mi kike
yi da baku tare ke da Lamin kun kakkarya k'ashin bayansu ba!" Aina'u tayi wani tafi tare da fad'in, "Ai ni jira
kawai nake yi Lami ta fara kai hannu kiga suga yanda ake yi a cikin gidan nan, don billahil lazi babu wacce
zata fita da kaya a jikinta. Sai na tabbatar mun yi masu tsirara sannan mu hankad'a su waje." Cire siririn
gyalenta Na'ima tayi sannan taci d'ammara dashi tare da kallon Nuratu tace, "Maza je rufo mana k'ofar
gida saboda kar su samu damar fecewa." Da gudu Nuratun ta nufi k'ofa ta saka lock tare da sakata sannan
ta dawo. Wani dogo sanda wanda aka ajiye a barandar d'akin mahaifinsu Nuratu ta d'auko, Na'ima kuma ta
d'auko muciya, ita kuma Aina'u ta koma d'aki ta d'auko wata murd'ad'd'iyar bulala. "Inna lillahi wa'inna
ilaihir raju'un! Nasiba sai da nace maku kar muzo gidan nan. Mu kira kawai a waya ya wadatar. Yanzu kinga
d'aya daga cikin jahilci da rashin hankalin nasu ko." Fad'in aunty Lubabatu wacce bata cika fitana ba,
asalima ita taso abi komai a hankali amma Mama ta matsa su tafi su fad'a masu sun janye neman auren.
"Wai nan tsoro kike ji? Ai wallahi sarkin yawa yafi sarkin k'arfi, mu biyar ne fa!" Fad'in Rahima wacce ita ma
tunda aka fara fad'an bata ce komai ba sai yanzu. "Baki da hankali hala? Gidansu fa muka iske su. Wallahi
mune a ciki ko kotu aka je!" Ko kamun wani ya fara magana a cikin su, Nuratu ta shak'o wuyar aunty
Halima ta baya ta kaita k'asa. Ganin haka ya saka gaba d'ayan su suka hau Nuratu da duka domin ceton
aunty Halimar don tana kaita k'asa ta hau dukanta da sandar da ta d'auko. Suma su Lami na ganin haka, sai
suka hau kansu da duka. Aina'u sai zabgawa ko waccen su zambad'ed'iyar bulalan hannunta take yi, Na'ima
kuma tana maka masu muciyar hannunta. Kan kace kwabo, kasancewa su Nuratun da makami a hannunsu,
tuni jini ya fara sharara a goshin aunty Luba, Aunty Halima da Najma. Don sun fi kowa buguwa. Ga shaidan
bulala ta ko'ina a jikinsu. Sarah kuwa gefe ta koma tayi ta rusa kuka don ita kanta ta samu nata rabon
wajen ceton su aunty Halimar. Baba ne ya samu ya fito da kyar don k'afar na matsa masa da ciwo sosai.
Yana fitowa tsakar gidan ya tsaya turus, don tun shigowar su aunty Halimar yake sauraran komai daga ciki
yana share hawayen bak'in ciki. Babu wacce yake tausayi banda Saratu don ya san ba k'aramin damuwa
zata shiga ba na fasa auren nan nata da ake shirin yi. "Ke! Nuratu, Na'ima, Lami, Aina'u, wallahi kamun na
iso wajen nan ku rabu da mutanan nan. Ku wasu irin yara ne kamar dabbobi. Kai ko dabba baza tayi
abunda kuke yi ba. Babu wawuya mara hankali a cikin su kamar ke Lami. Wallahi kuka yi kisa a cikin gidan
nan, nine nan zan bada shaida duk a tafi a rataye ku." D'agowa Lami tayi tana haki tare da fad'in, "To sai
me idan mun kashe sun? Ai dama ni na jima da sanin ba k'aunar mu kake ba ni da y'ay'ana. Kana d'aka
kana jin duk maganganun da matan nan suke fad'a min, amma baka iya fitowa ba, sai da kaji muna d'aukar
mataki tukun zaka fito kana wani maganar banza da wofi, yara, ku cigaba da d'umamun su!" Ko rufe baki
bata yi ba, su Nuratu suka cigaba da dukansu aunty Halima. Tsabar azaba aunty Luba kuka take yi tana
basu hak'ura amma basu saurara ba. Baba kuwa dogaro sandar shi yayi tare da isowa inda suke ya d'aga
sandar ya makawa Lami, sannan ya kuma d'agawa ya bugawa Nuratu da Aina'u, ya d'aga zai bugawa
Na'ima, tayi caraf ta rike sandar tare da tura shi baya sai da ya kai k'asa k'afarsa ta markwad'e, Aina'u kuwa
d'aga k'afa tayi dagangan ta take yatsun k'afarsa har da murzawa. Wani irin salati Baba ya saki tare da
fashewa da kuka yana mai kai hannu kan k'afarsa da Aina'un ta mitstsike. Nuratu kuwa hannu ta saka ta
dungure masa kai tare da fad'in, "Wallahi kar ka kuma ka kai hannunka jikina." Da mugun gudu Sarah ta iso
wajen ta d'auke Aina'u da gigitaccen mari, sannan ta kuma d'aga hannu ta zabgawa Nuratu da Na'ima
mari, sannan ta kuma d'auke Aina'u da mari don a idanunta ta mitstsike k'afar mahaifinsun. "Dan uwarki ni
kika mara?" Fad'in Na'ima tana mai nuna kanta, Nuratu kuwa muciyar dake k'asa ta d'auka ta bari Sarah
dashi a fuska, nan da nan fuskan ya tashi, bakinta kuma ya kumbura ya soma fidda jini don har ta wajen
bakinta dukan ya samu. "Allah ya isa shegiya y'ar iska! Kuma wallahi nima sai na rama!" Fad'in Aina'u tare
da yin hanyar pamfo da gudu ta d'auko bokitin da aka cika ruwa aka ajiye tayo kan Sarah wacce ke
tsugunne dafe da kuncinta da Nuratu ta buga mata muciya. Sai ji tayi shaaaaa an antayo mata ruwan sanyi
tun daga tsakar kanta har cikin pant d'inta. Saurin kallon gefenta tayi inda Baba yake saboda jin wani ajiyar
zuciya da ya sauke, sai tayi arba dashi a jik'e shataf, don ba ita kad'ai Aina'un ta jik'a ba har da baban. Baba
kuwa kallon Aina'u da Na'ima yayi yana fad'in, "Ni! Ni ko? Ina mahaifinku zaku saka hannu ku ture ni har
sai da ba kai k'asa ko? Aina'u ni kika kwarawa ruwan sanyi a jiki har mitstsike min k'afa ko!" Sai kuma ya
kalli Nuratu ya ce, "Nuratu ni kike saka hannu kina dungurewa kai kamar d'anki ko?" Ya fad'i hakan yana
nuna kansa wasu zafafan hawaye na biyo kuncinsa. "Kuje! Duniya zata koya maku hankali." Ya fad'i yana
mai fashewa da kuka tare da k'ok'arin mik'ewa. Sarah kuka take yi sosai ganin yanda jikin mahaifinsu ke
wani irin rawa kuma yana kuka sosai. "Lami dan ubanki kizo ki bani abinci yunwa nake ji!" Fad'in Safwan
d'an Na'ima. Saurin kallon Lami Na'imar tayi tare da fad'in, "Yanzu Lami dama yaran nan basu karya ba?
Haba Lami! Haba!! Wannan wani irin wulak'anci ne. Nafa bar komai na abincin yaran nan." Marairaicewa
Lami tayi tare da fad'in, "Yi hak'ura Na'ima, dama fitowa ta kenan domin in d'aura masu abincin sai ga
wad'annan fitinannun mutanan sun shigo." Kallon su Na'imar tayi tare da fad'in, "Zaku fita ku bar gidan
nan ne ko kuwa sai kun sake ji a jikinku?" Babu wanda yayi magana cikinsu sai ma kama junansu da suka yi
suka nufi k'ofar gida. "Sake ni Saratu kije ki bud'e masu kwar gidan ki basu hak'uri ki dawo." Fad'in Baba
yana mai share hawayen da suka kasa tsayuwa a idanunsa. Sarah bata sake shi ba sai da ta kai shi wajen
barandarsa sannan ta nufi k'ofar gida da gudu, nan tayi arba dasu suna ta kiciniyar bud'e gidan. Hannu
Sarah ta kai bayan sun bata hanya ta bud'e masu gidan tare da saurin kai guiwowinta k'asa ta shiga fad'in,
"Aunty dan girman Allah kuyi hak'uri da abunda y'an uwana suka yi maku. Ku......" Katseta aunty Bilkisu
tayi tare da fad'in, "Matsa mana a hanya mu wuce tun kamun nayi ball dake a nan wajen." Aunty Luba
kuwa saurin cewa tayi, "Mai ya kawo maganar Ball kuma! Ke jeki gida mun ji mun yi hak'uri. Bamu hanya
mu wuce tun kamun shan ruwan mu a duniya ya k'are. Wannan da muka sha ma, ya ishe mu ishara!" Ta
fad'i hakan tana mai bud'e gidan. Karaf gaba d'ayan su suka yi ido hud'u da Farouq dake k'ofar gidan. Da
sauri Sarah ta mik'e tana kallonsa, kallon irin na bankwana. Najma kuwa tana arba dashi ta fashe da kuka
tare da soma labarta masa abunda ya faru. Wani irin yunk'uri Farouq yayi zai fad'a cikin gidan ganin yanda
jini ya b'ata gaba d'aya gaban rigar aunties d'insa da k'annan nasa. Saurin rik'osa aunty Luba tayi tare da
fad'in, "Bada yawuna ba wallahi ka shiga cikin gidan na, yaran da har mahaifinsu duka suke yi, to uban
waye baza su daka ba a cikin fad'in duniyar nan. Farouq dama inda kake nai man aure kenan? Wallahi,
tallahi ko da ace yarinyar nan ba ciki bane a jikinta, kai da ita sai dai a lahira idan da rabon auren a can.
Sam wannan gidan ba gidan had'a zuri'a dasu bane." Sarah kuwa da sauri ta fito daga cikin gidan ta zube a
gaban Farouq, ko kamun ta bud'e baki ya d'aga hannu ya wanke fuskanta da gigitaccen mari tare da nuna
ta da hannu yace............

_08128755583 WhatsApp only dan Allah. Ban da kiran waya._


[09/09, 10:03 AM] Matar Sayyadee: 🦜 *_K'ANWAR MATATA_*🦜

_Matar Sayyadee_
_Wattpad @Matar_Sayyadee_
*ZAFAFA WRITER'S ASSOCIATION*

Page 5

A gigice Sarah ta d'ago tare da dafe kuncinta tace, "Farouuuuq." sai da ta ja sunan cike da tausayi tana
kallon fuskansa hawaye na shatata a idanunta. Bakin Farouq har rawa yake yi wajen fad'in, "Kar ki kuskura
ki k'ara kiran sunana anan wajen idan ba haka ba karya ki zan yi billahil lazi. Wawuya shashasha mai fuska
biyu. Ashe watsatsatsiya ce ke kamar sauran y'an uwanki. Kin cucuni Saratu da har kika saka ni na d'auki
dakon sonki a cikin zuciyata har tsawon shekara. Allah ya isa tsakani na dake. Kuma ki sani, ko da ace daga
ni sai ke muka rage a duniya, har sai dai na mutu babu aure. Banza budur-bazar." Kuka Sarah ta fashe dashi
jin zafafan kalaman da Farouq ke fad'a mata. So take yi ta bud'e baki tace wani abu, amma rawar da
bakinta yake yi ya hana ta iya furta ko kalma d'aya. Ji tayi an watso mata papers a fuska. Bin papers d'in
tayi da idanu, sai kuma ta kai hannu ta dake rawa ta dauki paper d'in ta bud'e. Waro idanuwa tayi ganin
papers d'in scanning d'inta ne har guda uku wanda tayi jiya. Bata iya cewa komai ba don ta san babu
abunda zata fad'i wanda zai saka Farouq ya yarda da ita. Tsirtar da miyau Farouq yayi tare da kama hannu
aunty Luba yace, "Aunty mu wuce anan kada amai ya kama ni dan Allah. Don ganin fuskan yarinyar nan
kawai yana saka ni tashin zuciya." Rintss idanu Sarah tayi tana jin bugun zuciyarta na k'aruwa tamkar yanda
jirgin k'asa ke malala gudu akan titinsa. Bata iya tashi a wajen ba sai da ta kwashi mintuna kamun ta mik'e,
shima sabida mutanan da suke wucewa suna zund'enta ne ya saka tayi k'arfin halin tashi ta tura k'ofar gida
ta shiga. Kai tsaye d'akin mahaifinsu ta wuce duk da maganar da Lami take mata a tsakar gida tana yiwa
yaran Na'ima wanka, amma bata kula ta ba. Tana shiga dakin ta zube a k'asa sai da guiwowinta suka bugu
da k'asa, amma bata damu da zafin da taji ba. Wani irin kuka mai tsuma zuciya ta fashe dashi tare da
fad'in, "Wallahi, tallahi, billahil azim Baba ban tab'a sanin wani d'a namiji a rayuwata ba. Baba namiji da na
tab'a bawa kaina. Ban san ta yanda akayi ciki ya shiga jikina ba. Na shiga uku na lalace Baba. Shikenan nima
ba zanyi aure ba?" Sunkuyar da kai Baba yayi yana mai zubar da hawayen tausayin Sarah. Dakyar ya iya
d'ago kai ya kalleta tare da fad'in, "Saratu da badin manzon Allah SAW yayi hani da d'auke mace a burni a
kaita k'auye ba, da nace ki tattara kayanki ki koma _Wamba_ kiyi auren ki acan. Amma kuma Saratu babu
ta yanda za ayi ki samu ciki ba tare da d'a namiji ba. Kin tabbata baki tab'a zuwa wani waje ba an baki abun
sha kin sha ba? Watak'ila ta nan aka yaudare ki." Girgiza kai Sarah tayi tare da fad'in, "Baba ban tab'a zuwa
party ba. Ko k'awaye bani da balle su gayyace ni." Shuru Baba yayi na kayan tsawon mintuna biyar sannan
ya nisa tare da d'agowa ya kalleta yace, "Jeki d'akin ki Saratu. Allah shi yasan abunda ke b'oye. Duk wanda
yake k'ok'arin cutar dake, in Sha Allah, Allah ba zai bashi dama ba. Kina gani da idanunki Saratu, kina ganin
irin wulak'ancin da mahaifiyarku da sauran y'an uwan ki suke min a cikin gidan nan. Kina tunanin ko ban
bud'e baki nayi masu baki ba, Allah ba zai tsine masu ba. Ni dai Sam ban yi sa'ar mace ba. Haka zan koma
ga Allah da bak'in cikin Lami da y'ay'anta. Sai da y'an uwana suka yi min gargad'i, amma kuma nayi kunnar
uwar shegu dasu. Gashi yanzu ina girbe abunda na shuka." Baba ya k'arisa yana mai fashewa da kuka.
Itama Saratu kukan ta fashe dashi tare da fad'in, "Kayi hak'uri Baba. Dan Allah ka cigaba da hak'uri dasu
kamar yanda ka saba." Bai d'ago ba ya ce, "Saratu y'ay'an ciki na suke duka na! Wallahi tallahi har
mahaifina ya koma ga ubangiji, bai tab'a fad'i na fad'a ba balle har in d'aga in kallesa inyi masa k'unk'unai.
Wannan jarabta ce kawai daga Allah!" Shuru Saratu tayi tana mai jin k'una sosai a cikin ranta. "Na'ima
y'ay'anta uku babu aure, dan ma Allah yayi wa d'ayan cikawa da yanzu y'ay'anta hud'u duk babu uba.
Nuratu biyu, Marfu'a nada d'aya, Hassana kuma tayi y'an biyu, ko wata uku ba'ayi ba da d'aya daga cikin
y'an biyun ya koma. Wannan bak'in cikin kawai ya isa ya kashe ni Saratu. Gashi itama autar taku Aina'u
tana so ta fad'a cikin halakar da y'an uwanta suke ciki. Yanda idanunta suke a tsatstsaye, wallahi ni sai nake
ganin ma kamar sai tace duk abunda y'an uwanta suke yi basu yi komai ba akan wanda zata yi ita." "A'a
baba, addu'a zaka yi mata. In Sha Allah hakan ma ba zai faru ba. In Sha Allah Aina'u baza tayi halin su
Na'ima ba." Girgiza kai Baba yayi tare da fad'in, "Uhm! To Allah yasa. Amma da kamar wuya. Hatta shi
kansa namijin da Allah ya bani tilo, sakarai ne. Tunda shima shaye-shaye babu wanda bai yi da kuma
d'aukar kayan mutane. Jiya da daddare, ina jin lokacin da wannan yaron wa yake da suna?" " *_Naliliyo_*"
Fad'in Sarah. "Yauwa eh shi! Ina jinsa yana karta adda a k'asa yana zage-zage. Kuma uwar na d'aure masa
gindi. Ya Allah idan wani laifi nayi maka kake min wannan jarabawar, Allah na tuba ka yafe min dan tsarkin
mulkinka." Da "Ameen." Sarah ta amsa tana mai jin tausayin kansu ita da mahaifin nata. "Tashi kije Sarah.
Kije kiyi ta addu'a. In Sha Allah, Allah zai kawo maki mafita. Ki k'addara dama can Umaru ba mijinki bane.
Idan kuma mijinki ne, wallahi duk wannan abun da ya faro, babu makawa sai anyi wannan auren." Share
hawaye Saratu tayi tare da fad'in, "Nagode Baba. Amma dan Allah idan ka yi min izini, zan koma asibiti
domin ganin likita." Sai da ya gyara k'afarsa sannan yace, "Saratu ki bari gobe kyaje. Yanzu ki koma d'akinki
ki huta." Mik'ewa Saratu tayi tare da fad'in, "To Baba, nagode Allah ya baka lafiya." Da Ameen ya amsa, ita
kuma ta fice daga d'akin. Sanye yake cikin jeans d'in _Secret Circus_ da shirt na kamfanin _Saint Laurent_,
sannan ya sanya takalmin _Stuart Weitzman_. Babu abunda ke tashi a jikinsa sai turaren _Imperial
Majesty_, kallon kansa yayi a cikin k'aton madubin dake d'akinsa ya saki lallausar murmushi ganin irin
kyawu da yayi. Juyawa yayi ya nufi wani katoton showglass wanda ba komai bane a ciki sai mahaukantan
expensive sunglasses, wani waje ya danna sai ga glass d'in ya zuge, rabi yayi sama, rabi yayi k'asa. Sai da ya
k'arewa glasses d'in idanu sannan ya kai hannu ya d'auko _Bulgari Flora_ wanda duk cikin sunglasses d'insa
yana matuk'ar k'aunar wannan. Madannin ya kuma dannawa glass d'in ya rufe sannan ya juya ya koma
wajen madubi ya d'auki Microfiber cloth ya goge glasses d'in sannan ya saka a fuskansa. Yanda yayi
matuk'ar yi masa kyau, zaka d'auka dan shi kawai aka yi glasses d'in. Sai da ya k'ara kallon kansa from head
to toes yaga he's perfectly dress sannan ya d'auki iPhone d'insa a kan bed ya nufi k'ofa ya murd'a ya fito.
"Barka da fitowa ranka ya dad'e" Shi gaba d'aya tsorata yayi don bai tsammaci ganinta a k'ofar d'akinsa ba.
"Laure! Kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un. Wai ni Ibrahim ya zanyi dake ne wai dan Allah? Sau nawa zan
fad'a maki ki daina zuwa kina tsayuwa a k'ofar d'akina kamar wata security. Dan Allah, dan Allah Laure ki
daina firgita ni. Ni wallahi babu abunda ke tada min hankali da tsoro kamar wad'annan kacakoren
hakwaran na...." Tun kamun ya kai k'arshen zancen ta fashe da dariya wanda ya bayyanar da manya-
manyan hakwaranta na sama guda hud'u da suka turo suka yi curko-curko a waje. Sam bata iya rufe
bakinta ruf saboda hakwaran. "Precious Lord in heaven! Laure bar nan wajen tun kamun na zubar da
wad'annan kacakoren hakwaran wallahi." Ja da baya tayi tare da fad'in, "Ni hwa tsaya kaji Ya Khalif (Khalil),
Hajiya ce tace nazo nayi kiranka tana can parlor kai take jira. Kuma ni kayi mani wanin (warning) akan kar
ba kuskura na kuma shigar maka d'aki kai tsaye. Kuma nayi k'ok'arin danna wanna madannin amma na
kasa. Kasan ni d'in ce kamar a duk'e aka haifo ni sabida rashin tsaho." Harara ya maka mata tare da fad'in,
"To naji bar nan wajen." Washa bakin ta kuma yi sai da ya matsa baya don da gaske shi hakoran nata tsoro
suke bashi. Gaba tayi kad'an, sai kuma ta juyo tare da fad'in, "Nace dan Allah yaya khalif ko zaka d'an
sammun wannan turaren naka mai shegen k'amshi anan, ko baka cika min ba wallahi nagode." Ta k'arisa
maganar tana mai ciro wata k'aramar kwalba irinta fiya-fiya a k'ark'ashin zaninta. Yunk'urowa yayi kamar
zai kai mata duka ta juya a guje ta nufi dogon corridor d'in da zai fitar da kai katoton parlorn gidan. Tsaki
yayi sannan ya jawo k'ofar d'akina nasa ya murza key tare da saka key d'in cikin aljihun wandonsa ya soma
tafiya majestically har ya iso parlor. Tsaye yaga Laure da mopa a hannunta, maimakon tayi abunda za tayi,
sai ta b'ige da kallon katoton tv na bango dake manne a jikin bango. Wani film d'in India mai suna
*_Sultan_* ake haskawa d'ai-d'ai inda yake gudu domin kamo jirgin leda. Babu abunda Laure kayi sai
kyalkyalewa da dariya. Khalil na k'arisowa ya d'auki remote dake hannun kujera ta jefi Laure dashi a goshi,
don Hajiya tayi kiran sunanta har sau hud'u amma film ya d'auke mata hankali. Kuma ita ta zubar da juice
d'in da Hajiya ke sha sabida rawar kanta. Saurin susa goshin Laure tayi tare da fad'in, "Laa! Wallahi kuma
naji kamshin turaren ka, wata zuciyar tana ce min kai ne ka k'ariso, amma wanna gayen ya tafi da imani na.
Dan Allah Hajiya zaki biya min kud'in jirgin inje indiya mu gaisa tare da d'aukar hoto dashi? Na san wallahi
zai ji dad'i idan ya ganni. Na san har fim sai mun yi tare in fito a budurwarsa." Harararta Khalil yayi tare da
fad'in, "To dan gidan ku matsayin saka ki a cikin keji ana zuwa ana ganin ki ba zaki samu ba, shashasha
kaiwa. Za kiyi abunda ke gabanki ko sai na isko ki nan wajen." Marairaicewa tayi tare da fad'in, "Allah sarki
yaya khalif. To na rantse maka fad'in k'asar indiya samu mai kyawuna abune mai matuk'ar wuya. Ko kai
d'innan da kad'an ka fini kyawu." Zama yayi kuwa da Hajiya yana mai fad'in, "Tabbas, babu shakka. Dama
ai samun irin ki a indiya ai sai an tona. Don ko namun dajinsu sun fiki kyawun gani." Turo baki tayi tare da
fad'in, "Kina dai jin sa ko Hajiya!" "Kar ma ku soma saka ni cikin shirmen ku. Ke da Khalil dai kamar kuna
ganin hanjin juna." Fad'in Hajiya dai-dai lokacin da Maryam matar wan Khalil tayi sallama ta shigo d'akin
hannunta rik'e da wani kyakkwar kula. Dai-dai inda Hajiya take ta ajiye kulan tare da fad'in, "Tom and
Jerry! Kun soma fad'an naku ko." Kallon kukan da aunty Maryam ta ajiye a gaban Hajiya yayi sannan ya kalli
aunty Maryam d'in tare da fad'in, "Ai kin san Allah, sai na kori yarinyar daga gidan nan. Ni da gidanmu
amma bani da sakewa. Babu ranar duniya da wannan yarinyar bata tsora tai da muggan hakwaran nan
nata." murgud'a baki Laure tayi tare da fad'in, "Halittar Allah kake zagi. Idan ka isa halicci kiyashi anan
wajen mu gani. Sai rowar tsiya, d'an turaren da mutum zai baka kad'an cikin kwalba amma ya kiya sabida
rowar tsiya. Wallahi Hajiya dai kowa ya san ita d'in hannunta a bud'e yake kamar kasuwar kwari ta Kanon
mu. Ko ina kayo rows oho! Kuma Hajiya kice ya bani makulli in tai in gyara masa d'aki." _Mastika gum_ da
yake matuk'ar k'aunar ya fiddo daga aljihunsa ya jefa a baki ya hau tauna a hankali yana lumshe idanu.
Allah ya had'a wani strong love tsakaninsa da chewing gum. Da yuwa kaga bakin Khalil babu gum a
bakinsa. Kuma gaba d'aya chewing gum d'in da yake ci daga waje ake kawo masa. Yasan expensive gum da
yawa. Yana biyan kud'in jirgi ya keta hazo kawai domin sayo chewing gum. Kullum cikin browsing yake
domin ganin sabon chewing gum d'in da aka yi. Hajiya tayi-tayi har ta gaji akan yi masa fad'a ya daina ci
amma Sam yak'i bari. Har hak'ori an tab'a cire masa tsabar cin chewing gum amma hakan bai saka ya
daina ci ba. "Dan gidan ku ina yi maka magana shine ka d'auki d'an iskan abun nan da ba tsana ka jefa a
baki kana tauna." Tsayawa da taunar yayi tare da fad'in, "Dan Allah Hajiya ki daina saka damuwar uncle
Ridwan a zuciyarki. Ya kamata ki saba da riginarsu yanzu. Wai shi so yake na auri Nina, ni kuma da in auri
wacce wani namijin ya riga ni saninta, gwara na mutu babu aure. Na tsani mace mara kamun kai. Hajiya
Nina fa bata san iya adadin mazan da ta kwanta dasu ba...........

08128755583
🦜 *_K'ANWAR MATATA_*🦜

_Matar Sayyadee_
_Wattpad @Matar_Sayyadee_

*ZAFAFA WRITER'S ASSOCIATION*

Page 6

"Ni kai min shuru da wannan zancen banzan naka. Sam Khalil baka k'aunar gudun b'acin raina ko? Kafi
kowa sanin su wanene y'an uwan mahaifinku, sam basu raina abun magana. Mahaifin naku ya kwanta
dama, amma duk da hakan baza'a bar ni na sarara ba. Menene a ciki idan ka auri Nina d'in. Kuma da kake
zancen y'ar iska ce, kai ka tab'a kamata red-handed ne? Nifa bani son sharri da k'azafi." Mik'ewa Khalil yayi
tare da fad'in, "I love you Hajiya. Sai na dawo. Ki cewa Laure taje laundry ta kwaso min kayana ta kai
d'akinki. Kada ta sake ko wajen k'ofar d'akina taje." Yana gama fad'in haka ya nufi k'ofa. Aunty Maryam sai
k'umshe dariyarta take yi ganin irin uban tagumin da Hajiya ta buga tana k'arewa Khalil kallo har ya gama
ficewa daga d'akin. Mai do da dubanta ga aunty Maryam tayi tare da fad'in, "Saki, saki dariyarki Maryam."
Dakyar aunty Maryam ta iya gimtse dariyar tare da fad'in, "Hajiya ba dariya zan yi ba." Gyad'a kai Hajiya
tayi tare da fad'in "Uhm, Maryam ban san mai Ibrahim ya maida ni ba. Gaba d'aya ya mai dani kakarsa.
Kina ji a gabanki ina yiwa yaron nan magana amma don tsabar wulak'ancin sai ce min yayi wai wani I
lobiyu sai na dawo. Har da bani sak'o in fad'awa Laure. Dani yake zancen. Allah ko yak'i Allah sai yayi aure
nan kusa. Idan har yace bai son Nina, ba zan takura masa ba, amma kuma dole ne ya fiddo wacce yake so.
Na gaji da zagin da iyayensa suke min a kansa. Shekaru talatin da biyar, yana da aikin yinsa, to uban mai
yake jira kuma. Muhalli dai ga b'angarensa nan kullum cikin kwaskwarima da gyararraki yake yi. Yaron sai
shegen k'arya da kashe kud'i kamar bai san zafin nema ba. Kina gani akan dank'on da kullum bashi da aiki
sai na taunawa kamar tsohuwar karuwa sai yayi takakka ya biya kud'in jirgi har wata k'asar. Zai ci gidansu
dani yake zancen." Fad'in Hajiya tana mai jawo kulan ramar dake gabanta ta bud'e ta soma ci. "Hak'uri za ai
Hajiya. Addu'ar tagari za kiyi masa ya zab'o tagari a hankali." Rama cike a bakinta tace, "Rabu dashi
Maryam. Idan ya kai ni bango, bazawara shikan wawa zan samo masa kuma sai ya aure ta." Dariyar da
aunty Maryam keta rik'ewa ta kufce tare da fad'in, "Lallai Hajiya kin so rigima. Tun Khalil na yaro ke kike
bamu labari komai sabo yake so. Duk wani abu da wani ta riga sa amfani dashi bai tab'a amfani da abun
balle kuma ace matar da zai aura wani ya riga sa auran ta. Lallai Hajiya kin d'auko da zafi. Har na hangi
Khalil gashi can da auran bazawara. Kin san Allah Hajiya barin garin nan zai yi baza ki sake ganinsa ba sai an
d'ebi shekaru." Rufe kulan Hajiya tayi tare da fad'in, "To ya tafi mana Maryama. Ni na huta ma da magana.
Ni da na san haka zai rika jawo min zagi, da ban takura sai ya bar wannan k'asar ya dawo Nigeria da aikin sa
ba. Sai shegen kwalliya da fesa manya-manyan turaruka masu shegen k'amshi da tsada, amma duk uban
kwalliyar nan abokansa sunce min ko hakoransa y'an mata basu gani a waje. Ni ko ya yake kula da marasa
lafiyan oho! Kin tuna wannan yarinyar Salma da ta mak'ale masa daga ya dubata a asibitinsa? Yarinyar
arziki har gida nan take zuwa gaishe ni. Amma yaron nan sai da ya koreta ta daina zuwa. Kai ni lamarin
Khalil na ban takaici. Ni ko dai aljana ce ta aure shi?" Aunty Maryam gyara zama tayi tare da fad'in, "Hajiya
babu wata aljana lokacine kawai bai yi ba. Amma idan yayi shi da kansa zai kawo maki budurwarsa har
gida." "Allah ya amsa Maryamu ko na huta da mita da kiraye-kirayen wayar dangin ubansa." Fad'in Hajiya.
B'angaren Sarah kuwa, ko da ta koma d'akinsu, can k'uryan gado ta hau ta nannad'e cikin bargo sabida
wani zazzafan zazzab'i daya lullub'eta. Can kamar kusan mintuna talatin, lokacin zazzab'in ya k'aru sosai taji
shigowar Hassana wacce dawowarta kenan daga yawon ta zubar d'inta. Zama tayi a bak'in gadon ba tare
da ta lura da Sarah dake kwance cikin bargo ba can k'arshen gadon. "Honey wai kana nufin baka gaji dani
ba? Mu kwana muna abu d'aya amma ace ka kasa gajiye dani." Wani dariya Hassana ta saki har da
kwanciya flat tana kallon ceiling ga dukkan alamu taji dad'in amsar da wanda take waya dashi ya bata. Don
har da wani mik'a tayi. "Kamar ka sani kuwa. Wallahi duk ka tada min da sha'awata. Kasan fa muryanka
kad'ai ma kawai na sakani haniniya." D'an shuru tayi sai kuma tace "Allah ko! To ban mintuna uku kacal zan
kira ka yanzu." Tana gama fad'in haka ta yanke wayar tare da mik'ewa ta cire kayanta gaba d'aya har da
P&B. Kasancewar idanun Sarah a kulle suke, bata san abunda Hassanar ke aikatawa ba. Sai bayan kamar
mintuna goma ta jiyo nishi sama da kuma maganganun batsa. A hankali ta bud'e idanunta tare da d'an
d'ago kanta da take jinsa kamar zai tsage. Gabanta ne yayi wani irin mugun fad'uwa ganin yar tata tsirara
da wani abu mai shape d'in al'aurar namiji yana wani irin k'ara ita kuma tana turawa tare da gogawa a
gaban nata. "Hasbunallahu wa ni'imal wakeel! La'ilaha illallah Muhammadur Rasulillah!! Allahumma arji'ini
fi musibati." A razane Hassana ta d'ago ta kalli Sarah, ita kuma Sarah saurin kawar da kai tayi saboda ganin
al'aurar wanda take video call dashi ta cikin wayar don lokacin da Hassanar ta razana wayar ta fad'i kuma
ba kifawa tayi ba. Mugun tsaki Hassanar taja ganin Sarah ce, don ta d'auka wani abun tsoro ne. D'aukar
wayarta tayi tare da fad'in, "Baby mu cigaba. Wannan banzan K'anwar tawa ce da nake baka labari ce."
Fad'in Hassana. Sarah kuwa duk da rashin k'arfin jikinta da kuma sarawar da kanta yake yi, haka nan ta
mik'e ta dafa bango ta fice daga d'akin don baza ta iya wannan mummunar ganin ba. Tana fitowa daga
d'akin wani irin yunk'uri ya taso mata na amai, cikin sakwanni biyu ta soma kakari tana kelaya wani irin
amai mai mugun wuya kasancewar ba wani abun kirki bane a cikinta. Don hatta ruwa idan tasha dawowa
yake yi. Ruwan bohol ko kuma fanta mai mugun sanyi ne kawai yake iya d'an zama a cikinta. Shima kuma
sai tana sha tana hutawa. Lami, Aina'u da Nuratu na tsakar gidan amma babu wanda ya iya mik'ewa yazo
domin taimakonta. Tsabar yanda take amai d'in hatta fitsari zuba yake yi a jikinta. Tun tana amai a duk'e
har ta zauna dirshan a k'asa tana bubbuga kanta da hannunta amma babu wanda ya tanka balle ya kawo
mata d'auki. Nuratu ma Wak'a ta soma yi na habaici da isgilanci. Azaba ya ishi Sarah, bata san lokacin da ta
soma d'aga hannu tana fad'in, "Babu mai taimako nane? Lami ki taimaka min dan girman Allah. Nuratu,
Aina'u, ku taimaka min zan mutu, wallahi mutuwa zanyi." Lami ce ta soma magana, "Dan ubanki ki mutun
mana. Kowa da kike gani a cikin gidan nan kud'insa yake cirewa ana yi masa hidima. Kema da kin cire
mugun hali sa son kin fad'i uban cikin dake jikinki, da yanzu shalele kike a cikin gidan nan. Amma tunda
kince mugun hali kika saka a ranki, mugun halin ya cece ki." Tana gama fad'in haka ta sab'a Yabo d'an
wajen Na'ima a baya, shi kuma ya tak'ark'are ya ganna mata wani arnan cizo a tsakiyar bayanta
sakancewar baya k'aunar goyo, ita kuma Lami burinta tayi ta kima sa a baya don Na'imar tace tana kula
dashi sosai. Don duk cikin y'ay'anta, tafi k'aunar Yabo. Zafin cizon ya saka Lami tafiya ta gaba a gigice ta
had'a kai da wani dogon k'arfe dake kan barandar d'akinta sai da goshinta ya k'umu kuma yayi k'ulu
k'atoton. Dariya Aina'u ta fashe dashi tare da fad'in, "D'an bura uban yaro! Kema ai Allah ya k'ara Lami. Kin
fi kowa sanin Yabo bai k'aunar goyo amma sabida naiman suna kika kima shi a baya. To ai ga babbar Yabo
nan kin samu a kan goshin ki." Kwance zanin Lami tayi ta sauke sa tare da dungure masa kai, aikuwa take
ya b'are baki ya fashe da kuka. Da sauri Lami ta saka tafin hannu ta rufe masa baki tare da fad'in, "Na shiga
uku zai jawo min jidali da safen nan. Yi hak'uri d'an lele. Yanzu zan shiga d'aki na d'auko maka sweet mai
tsinke." Sarah kuwa dake jibge a k'asa tana ta faman bugun goshi kamar zata fita hayyacinta, kira sunan
Aina'u ta shiga yi tana fad'in, "Aina'u dan girman Allah ki taimaka min, Wallahi zan baki dubu d'aya." Mere
baki Aina'u tayi tare da fad'in, "Now you're talking. Amma kuma yasin dubu d'aya tai min kad'an, dubu
biyu zaki bani." Dai-dai nan Baba ya fito da sandarsa a hannu ya kalli inda Sarah take tausayinta ta kashe sa
a tsaye, mai da dubansa yayi izuwa wajen Aina'u tare da fad'in, "Aina'u yanzu taimakon y'ar uwar taki ce
sai da kud'i?" Mik'ewa tayi tare da fad'in, "A'a fa Baba! A'a! Walleh gwamnati ta hana aikin banza. Ta biya
yanzu taga aiki da cikawa. Don ma ta samu zan karb'i kud'in in taimaka mata. Duk cikin gidan nan waye
zata bawa kudi ya amsa don taimakonta idan ba niba. Idan zata bada 2k ta bayar a taimaka mata, idan
kuma baza ta bada ba, ta sha zamanta." Girgiza kai Baba yayi tare da fad'in, "Ungo nan gashi ni zan cika
mata. Karb'i ki taimaka mata ta gyara jikinta ku tafi asibiti." Wani kallo tabi baban dashi tare da fad'in, "Oh
wai har da su zuwa asibiti? To lallai kud'i ya k'aru. Ni na d'auka taimaka mata kawai zanyi ta d'auraye jikinta
ta koma d'aki! To kud'in ku dubu uku, idan kuna dashi, a cika aiki, idan babu, in koma in zauna." Shuru
Baba yayi yana kallon Aina'u, sai kuma ya mayar da dubansa ga Sarah yaga halin da take ciki. Sai ya koma
d'akinsa, bayan kamar mintuna biyu ya fito tare da fad'in, "Zo Aina'u, ga dubu uku kamata ki taimaka mata
ta wanko jikin nata sai ku tafi asibitin." Mik'ewa Aina'u tayi don har ta zauna tare k'arisawa ta amshi kud'in
sannan tace, "Ko kai fa d'an tsoho. Tsohon nan kud'i fa gare ka naga alama!" K'ala bai cewa Aina'u ba, sai
ma kallon Sarah da yayi tare da fad'in, "Allah ya baki lafiya." Sannan ya juya ya shige d'akinsa. Aina'u kuwa,
k'arisawa wajen Sarah tayi ta kamata ta mik'e ta kaita har gindin pamfo ta wanke mata jiki. "Aina'u taimaka
min da fanta mai sanyi a shago dan Allah. Akwai naira dubu d'ari biyu, ki d'auki d'ari biyun ki sayo min."
Matsawa baya kad'an tayi tare da fad'in, "To ki tabbata shima akwai kud'insa daban. Don yasin ban aikin
banza." Sarah na nishi tace, "Naji ji ki sayo min. Idan muka fita zan cire kud'i a POS sai in biya ki." Ba tare da
Aina'u tace komai ba ta juya ta nufi d'akinsu Saran ta d'auko d'ari biyun ta fito ta nufi waje don sayo
Fantan. Sarah kuma da kyar ta iya jan jiki ta koma d'akin. Sai da ta d'an yi jimm kamun ta tura k'ofar ta
shiga saboda bata son ganin abunda ta baro a cikin d'akin. Alhamdulillah Hassanar ta gama abunda take yi,
kwance ma same ta tana kwasar barci. Kai tsaye wajen wardrobe ta nufa ta canza kayan jikinta ta zauna a
k'asa tana nishi. Don wani irin juwa take gani. Aina'u ce ta hankad'o labulen ta shigo d'akin tare da dire
mata kwalbar fanta a gabanta mai sanyi. "Nagode Aina'u!" Shine abunda Sarah ta fad'i tare da kai kwalbar
bakinta ta cire kwankwalatin ta hau shan fantar. Kad'an tasha taji kamar za tayi amai sai ta mayar da
kwankwalatin ta rufe ta ajiye a gefe tare da mik'ewa ta d'auki hijjab ta saka ta cewa Aina'u, "Muje Aina'u.
Zamu d'an tsaya a shagon Nura zan cire kud'i, taimaka min ki d'au min jakata." Jakar ta d'aukar mata suka
fita daga d'akin. "Lami mun tafi." Fad'in Aina'u. "To sai kun dawo. Ki tabbatar kin karb'i kud'inki." Wani
murmushi Aina'u tayi tare da fad'in, "Kin san wannan dole ne Lami, sai dai mun dawo d'in." Ita dai Sarah
bata ce komai ba ta nufi hanyar k'ofar gida. Sai da suka biya ta shagon Nura Sarah ta cire 11k ta bawa
Aina'u 1k na sayo mata fanta da tayi sannan suka tsari napep suka shiga. "Ina zamu je Hajiyoyi?" Fad'in mai
napep. "Ka kai mu wani asibiti mai kyau da kasan sun san aikin su sosai." "An gama Hajiya!" Fad'in mai
napep d'in. Sun d'an yi tafiya mai tsayi mai napep d'in ya tsaya a bakin wani katafaren asibiti kamar ba a
k'asar Nigeria ba, a saman asibitin an rubuta *_Khalilullah Specialist hospital_* "Kai! Kana hauka ne da
zaka kawo mu wannan asibitin? Shin baka san tsadar asibitin bane?" Fad'in Aina'u. Ko kamun mai napep
yace wani abu, Sarah ta sauko daga keken tare da zaro dubu d'aya ta mik'a masa ya cire kud'insa ya bata
canji. Sai a sannan ya kalli Aina'u tare da fad'in, "Ai gani nayi kunyi kalar asibitin shiyasa na kawo ku nan
d'in." Harara ta zabga masa tare da bin bayan Sarah da har ta kusa shiga cikin gate d'in. Sai da ta d'an had'a
da gudu tukun ta isketa tare da fad'in, "wannan wani irin iskanci ne haka zaki wuce ki barni? Don kin samu
na rakoki ko? Gobe rana ce ai!" Ba tare da Sarah ta kalleta ba tace, "Yau d'in ma kud'i nane dana Baba ya
sakaki taimako na, gobe ma idan kika ga kud'in, biyo ni za kiyi." Aina'u bata kuma cewa komai ba har suka
shiga reception d'in asibitin. Gaba d'aya numfashinsu ya kusa d'aukewa sabida tsabar had'uwar da asibitin
yayi. Aina'u kuwa baki bud'e take bin lungu da sak'on asibitin da kallo. "Baiwar Allah dan Allah Ina zan je na
bud'e file?" Fad'in Sarah bayan ta tab'o wata nurse da tazo wuce wa. Da hannu nurse d'in tayi mata nuni
da wajen sannan ta wuce. Sarah kuwa k'arisawa tayi tare da yin sallama ta gaishe da saurayin da ta gani a
wajen sannan tace, "File nake so a bud'e min. Ina son ganin doctor." Wani file ya d'auko tare da kallonta ya
mik'a mata wani k'aramar paper tare da fad'in "Je ki biya wannan a wajen cashier sai ki dawo min da
receipt d'in." Karb'a tayi tare da fad'in, "Ina ne wajen dan Allah?" Shima da hannu ya nuna mata wajen.
Tana zuwa ta mik'a masu papern, matar dake wajen ta d'ago ta kalleta tare da fad'in, "Kud'in ki dubu
bakwai. Don kinyi sa'a babban doctor ne zai duba ki. Bud'e file dubu biyu, sai kud'in ganin likita dubu biyar.
Shuru Sarah tayi, domin idan ta bada 7k saura 2k a jikinta. Da mai zata biya kud'in scanning? Don ta san
tabbas za ayi mata scanning. Aina'u ce tazo wajen ta tsaya, Sarah tayi saurin cewa, "Dan girman Allah
Aina'u aramin dubu hud'un hannunki, idan mun koma gida zan baki." Ciro kud'in Aina'u tayi ta mik'a mata
tare da fad'in, "Amma fa ki sani, wallahi sun haifu. Ba dubu hud'u zaki mayar min ba." Komai Sarah bata ce
mata ba. Sai mik'awa cashier kud'in tayi tare da mik'a mata receipt ita kuma ta karb'a ta koma wajen
wanda ke bud'a file ta mik'a masa. Sunanta ya tambaya tare da age, adresss da kuma phone number
sannan ya nuna mata inda zata je tare da shaida mata ya turawa doctor file d'inta ta computer. Consultant
room taga an rubuta a sama. Har zata murd'a sai kuma ta d'an tsaya jim ta juyo ta kalli Aina'u dake zaune a
kan kujera ta d'aura k'afa d'aya a kan d'aya tana danna waya. Ajiyar zuciya ta sauke tana fatan ace wannan
karon idan an dubata ace wani ciwo ne daban a jikinta ba ciki ba. Kwankwasa k'ofar tayi sannan ta tura ta
shiga. Wani gaurayayyen sanyi Ac taji ya ratsata mai tafe da wani k'amshi mai shiga zuciya da b'argon d'an
Adam. Har sai da Sarah ta lumshe idanu tana mai fatan ace ta cigaba da jin wannan k'amshi har abada
saboda yanda yayi mata wani irin dad'i da salama a cikin zuciyarta. Ba tare da ya d'ago kai ba yayi mata
nuni da kujerar dake gaban teburinsa. Zama tayi tana mai wasa da hannunta. Shi kuwa doctor wani
rubuce-rubuce yake yi a jikin wani file. Ya d'auki mintuna uku kamun ya ajiye file d'in ya zare glasses d'in
dake fuskansa sannan ya juyo da computer yayi danne-danne tare da fad'in, "Saratu Nuhu ko?" Ya fad'i
hakane tare da juyowa ya kalleta dai-dai lokacin da itama ta d'ago kai idanunsu suka sark'e dana juna. A
mugun firgice Sarah ta mik'e tare da tura kujeran da take kai baya gabanta na wani irin mugaba kamar
yanda dak'ik'an agogo yake bugawa. Bakinta na rawa tace, "kkkk.... Kai!" Shima da matuk'ar mamaki
ganinta ya furta, "Ke ce?" Da sauri ta juya ta fita daga office d'in har tana k'ok'arin kifawa tayi saurin dafe
bango. Aina'u dake charting ganinta kawai tayi ta fito kamar wacce aka biyo ta tayi waje da sauri. Ita ma
mik'ewar tayi tana fad'in, "Sarah! Sarah!! Lafiya?" Dai-dai lokacin ya fito shima ya bita a baya, Aina'u na
ganin haka ta rufa masu baya amma suna isa wajen gate d'in suka ganta har ta hau napep, napep d'in ya
wuce. Juyawa Aina'u tayi ta kallesa tare da fad'in, "Lafiya? Mai ka mata? Ko HIV kuka gano tana d'auke
dashi?" Wani irin kallo Khalil yayi mata tare da fad'in, "Ni ko dubata ban yi ba. Kin santa ne?" Ya tambaya
duk da kuwa yana ganin kamannin jini a fuskar Aina'un. "K'anwarta ce ni. Ni ke binta." Ajiyar zuciya ya
sauke tare da fad'in, "Ko zaki shigo mita muje in sauke ki sai in san gidan naku daga nan." Wani kallon up
and down tayi masa, ganin babu k'arya sai tace, "To amma kai mai yasa kake son zuwa kaga gidan mu?" Kai
tsaye ya bata amsa da, "Saboda ina son had'uwa da yayarki. Auren ta nake son yi. Na jima ina naimanta sai
yau Allah ya had'a ni da ita." Wani dariya rainin hankali Aina'u ta kwashe dashi tare da fad'in, "Lallai! To ka
ko san abunda ya kawota nan asibitin? To bud'e kunnuwanka da kyau in fad'a maka. Ciki ne da ita har na
tsawon watanni uku, kuma zuwa tayi nan domin a zubar mata da cikin. Mu gidan mu bamu aure. Kar ka
wahalar da kanka don baza ka tab'a samun Sarah matsayin mata ba. Ko da yake, ban san tsananin son da
kake mata zai saka kayi auren ragowar wani ba. Ni na barka lafiya." Tana gama fad'in haka tayi gaba. Shi
kuwa Khalil mutuwar tsaye yayi kansa na wani irin juyawa jin wai wacce yake matuk'ar k'auna ce take
d'auke da juna biyu. Tirr ya auri mazinaciya a rayuwarsa. Idan kuma hakan ta faru, daran ranar da ya
fahimci haka, a ranar zai korata gidansu. Don ya san zama da zargi babu aure, shi kuma ba zai tab'a iya
auren yarinyar da zuciyarsa zai rik'a kokwanto a kanta ba. Har ya fara tafiya ya tsaya cak tare da maimaita
abunda Aka Aina'u tace masa cikin zuciyarsa "Ciki wata biyu? Kai ba zai tab'a yuwuwa ba." ya fad'i a
bayyane tare da bin bayan Aina'u da sauri.............

_AKWAI FA SAURAN CHAKWAKIYA A GABA SOSAI. DON HAR YANZU BA'A SOMA LABARIN BA. SHIN TA YAYA
SARAH TA SAMU CIKI BAYAN TAYI RANTSUWA DA ALLAH BATA TAB'A SANIN D'A NAMIJI BA, WANENE
DOCTOR D'IN DA SARAH TA GANI HAR TA TSORATA DA GANINSA TA GUDU BA TARE DA TAYI ABUNDA YA
KAITA ASIBITIN BA? MAI DOCTOR KHALIL YAKE NUFI DA YACE BA ZAI YUWU BA ACE SARAH NA DA CIKIN
WATA BIYU? A INA YA SAN SARAH, KUMA MENENE ALAK'ARSU? WACECE LAMI? WANENE BABA NUHU?
SHIN MAI MAI K'ANWAR MATATA YAKE NUFI? TUN FA DA AKA SOMA LABARIN BAMU GA MATAR BA,
BAMU GA MIJIN BA, BARE KUMA K'ANWAR. HMM WALLAHI Y'AR UWA KAR KI BARI AYI WANNAN LABARIN
BABU KE. DOMIN AKWAI CHAKWAKIYA MAI ZAFI A CIKINSA._
*_A NAN NA KAWO K'ARSHE. FREE PAGES, GA MAI BUK'ATAR KARANTA LITTAFIN K'ANWAR MATATA, SAI YA
TURO D'ARINSA BIYAR ZUWA WANNAN ASUSUN BANKIN 0592412800, ZULFAU SAID GT BANK, SAI KI TURO
DA SHAIDAR BIYANKI DA WANNAN NUMBER 08128755583_*
[12/09, 7:31 PM] Matar Sayyadee: Da sauri yabi Aina'u yana kwala kiran "Ke! Ke!! Dan Allah tsaya." Aina'u
najin muryansa ta k'ara sauri don bata fata ko cikin mafarkinta wannan doctor d'in ya kasance mijin Sarah.
Cikin sauri ta tari Napep ta fad'a ciki. Cak Khalil ya tsaya yana mai bin napep d'in da idanu har ya daina
ganinsu. Ya jima tsaye a wajen yana jin wani abu na tasowa a k'asan zuciyarsa. Hannu ya kai ya yamutsa
gashin kansa kamun yayi wani irin tsayuwa tare da tura hannunsa cikin aljihun wandonsa yana kallon
sama. Can kuma ya juya da sauri tare da komawa office d'insa. Yana jin ana gaishesa amma ko juyawa bai
yi ba balle ya amsa. Direct wajen computer ya nusa ba tare da ya zauna a kan kujera ya d'an rankwafo yayi
danne-danne jikin computer tare da saurin d'aukar wayarsa ya kwashi numbers d'in Sarah dake rubuce a
file d'inta sannan ya kashe computer d'in ya zira wayarsa cikin aljihu ya fita daga office d'in bayan ya rufo
k'ofar ya saka key. Wayarsa ya fiddo ya danna ya lalubo numbern doctor Kamal tare da shaida masa ya bar
asibiti yazo yayi replacing d'insa akwai wani abun gaggawa da zai je ya aiwatar. Yana gama waya da doctor
Kamal ya fita ya nufi parking space. Wata arniyar mota *_Pagani Zonda HP Barchetta_* that worth 17
million ya shiga tare da yi mata key ya bar asibiti. Sai da ya hau titi kuma sai ya rasa inda zai je. Juya kan
motor yayi ya nufi Sokoto road inda gidan su yake. A wani k'atoton mansion ya danna horn, cikin sauri mai
gadi ya wangale gate shi kuma yayi shiga tare da yin parking anan harabar gidan ba tare da ya isa parking
space ba. Fitowa yayi daga cikin motar ya shiga cikin gida da sassarfa, babu kowa a parlor do haka kai tsaye
ya haura sama ya saka key ya bud'e d'akinsa tare da shiga ya maida key d'in ya rufe k'ofar sannan ya nufi
wajen wani wawaken waje da aka rufe sa da tinted glass ya danna wani abu glass d'in ya zuge. Wata jaka
ya fiddo y'ar karama mai hannun chain kalar pink. Sai da ya jujjuya jakar a hannunsa sannan ya k'arisa
wajen gado ya zauna a bakin gadon tare da zuge zip d'in jakar ya zazzage a kan gado. Abunda ya fara cin
karo dashi shine d'an kunne guda d'aya kalar bak'i hook d'insa ya b'alle. Murmushi yayi tare da maida d'an
kunnan cikin jaka sannan ya d'auki kud'in dake kan gadon wanda a cikin jakar ya fad'o. Dubu d'aya ne da
d'ari bakwai, Sai turaren soft da lipgloss. Sune kawai abunda yake cikin jakar. Mai da komai yayi a cikin
jakar tare da kwantawa rigingine yana tuno wasu abubuwa da suka wuce a cikin idanunsa kamar yanzu
komai ke faruwa. Cikin sauri kamar an tsikaresa ya tashi zaune tare da zaro wayarsa k'irar Samsung mai
matuk'ar kyau da tsada yayi dialing number Sarah da ya d'auka. Sai dai tayi ringing har ta gaji ba'a d'auka
ba. Ya kira yafi sau goma amma babu amsa. Tsaki yayi tare da jefar da wayar a kan gado. Yana bala'in bak'in
cikin ya kira waya ba'a d'aga ba. Shi a k'a'ida sau d'aya yake kira bai k'ara na biyu. Mirginawa yayi tare da
mik'a hannunsa ya jawo drawer ya tura hannu ya d'auko _Mastika Gum_ ya b'are ya watsa a baki ya hau
tauna yana mai lumshe idanu. B'angaren Sarah kuwa tun da ta hau keke napep gabanta ke wani irin
bugawa sai da ta saka hannunta ta dafe k'irjinta don ji take yi kamar zuciyarta zai faso k'irjin ya fito. "Inna
lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Shine abunda ta dunga maimaita tun tana yi cikin zuciyarta har ya soma
fitowa fili. Matar dake kusa da ita ta kalleta tare da fad'in, "Baiwar Allah lafiya?" Sarah bata bata amsa ba
sai cewa mai napep d'in tayi, "Tsaya, tsaya zan sauka anan." Parking mai napep yayi ita kuma ta sauko gaba
d'aya bata cikin hayyacinta. Mik'a masa d'ari biyar tayi tare da juyawa ta soma tafiya ko karb'an canji bata
tsaya yi ba. Shi kuwa mai napep yaja napep d'insa yayi gaba. Sarah kuwa tafiya ta cigaba dayi a k'asa tana
kalle-kalle. Tayi tafiya mai nisa kamun Allah ya had'a ta da wani asibiti a gabanta. Hamdala tayi tare da nufa
cikin asibitin kai tsaye. Bud'e kati tayi sannan ta zauna domin jiran layi yazo kanta. Kamun layi yazo kanta
har wani zabura take yi tana mik'ewa saboda tsabar k'aguwa. Sai da mutane takwas suka ga likita sannan
aka kira sunanta. Cikin sauri har tana tuntub'e ta fad'a cikin office d'in a burkice. Doctor yayi saurin
d'agowa ya kalleta, ganinta a hargitse sai yayi mata nuni da wajen zama tare da fad'in, "Have a sit." Zama
tayi da sauri dama kuma abunda take jira kenan. K'ura mata idanu doctor Alpha yayi kamun yace, "Young
lady, how can I help you?" Ai kamar Sarah jira take sai ta fashe da kuka, bai yi yunk'urin hanata ba, sai ma
jingina da yayi da jikin kujera yana kallonta, sai da tayi mai isarta sannan ya mik'a mata tissue ta karb'a ta
goge hawayen. A karo na biyu doctor da ya kasance bayarabe kuma bai jin hausa sannan kuma a haife ya
haifi Sarah, yace, "My daughter what's the problem? Feel free to tell me exactly what's wrong with you.
Let's have heart to heart conversation." Ajiyar zuciya Sarah ta sauke tare da fad'in, "Sir can I ask you a
question?" Hannunsa biyu ya d'aura akan desk d'in dake gabansa ya bata full attention d'insa tare da
fad'in, "You can ask any question. I'm here for you." Sai da ta sunkuyar da kai sannan tace, "Doctor can
someone get pregnant without sexual penetration?" Sai da doctor yayi wani murmushi sannan ya kalli
Sarah tare da fad'in, "What's your name young lady?" Ba tare da ta d'ago ba tace, "Sarah, Saratu Nuhu."
Murmushin ya k'ara yi a karo na biyu tare da fad'in, " *_Pregnancy happens when a sperm fertilises an
egg, which can happen even if you've not had sexual intercourse (penetration)._*
During vaginal penetrative sex (where the penis enters the vagina) semen can be ejaculated. Semen is the
liquid produced during ejaculation and contains millions of sperm.
As soon as the penis is erect, (before ejaculation), a liquid called pre-ejaculate or "pre-cum" is produced.
This liquid can contain thousands of sperm. The ovaries release 1 or more eggs (ovulation) 12-16 days
before a period starts.
The sperm enters the body through the vagina, then travels through the cervix and womb to the fallopian
tubes, where the egg is usually fertilised (conception). The egg can be fertilised by sperm contained in
semen or pre-ejaculate." Kallon doctor Sarah kawai take yi alamar bata fahimce sa ba. Ganin hakan a
fuskanta, sai ya sake yin murmushi tare da fad'in, "Here is the explanation, *_It is possible to get pregnant
if sperm comes into contact with the vagina, if for example:_* *_your partner ejaculates very close to your
vagina your partner's erect penis comes into contact with your genital area (vagina or vulva)_* *_The risk
of getting pregnant in this way is very low because sperm can only live for a short time outside the
body._*" A tsorace Sarah ta mik'e tsaye, shima doctor mik'ewa tsayen yayi tare da fad'in, "Hey calm down.
Have a sit let talk." Da kyar ta iya zama tare kallon doctor babu kyaftawa. Shima doctor zama yayi tare da
fad'in, "Sarah are you pregnant?" Ai fad'in haka da yayi Sarah bata san lokacin da ta mik'e da sauri ba ta
fice daga office d'in har da had'awa da gudu. Shima doctor da mamaki yabi bayanta yana kiranta amma
bata jo juyo ba ta bar asibitin. Tana fitowa ta nufi asibitin _ZAKARIYYA_ dake magajin gari. Cikin sa'a ita ce
mutum na biyu da doctor ya gani, tana shiga tayi ta soma rab'e-rab'e har sai da doctor Usman ya d'ago
yana kallonta har ta naimi waje ta zauna. Bai ce mata komai na tsawon mintuna biyu, ita kuma sai wasa da
jelar hijjab d'in jikinta take yi. "Me ke damun ki?" Taji saukar muryansa a cikin kunnanta har sai da hantar
cikinta ta kad'a. A hankali ta d'ago hawaye shab'e-shab'e a fuskanta. Doctor Usman bai yi mamaki ba don
idan da sabo sun saba da ganin haka a wajen y'an mata sabon shigan fara iskanci idan sun yi ciki ko kuma
masu fama da cutar HIV sabon shiga, ko kuma irin shagwab'ab'b'un yaran nan masu kuka idan basu da
lafiya. "Me ke damun ki?" Ya sake tambaya karo na biyu. Bud'e baki Sarah tayi zata fara magana bakinta ya
soma rawa sai ta kuma fashewa da kuka. Bai yi yunk'urin hanata kukan ba, ita da kanta tayi mai isarta
sannan tace, "Doctor da gaske ne mace na iya d'aukar ciki ba tare da namiji ya kasanceta ba?" Cikin zuciyar
doctor Usman yace, "Anzo dai-dai wajen!" Amma a zahiri sai kallonta yayi tare da fad'in, "Ciki gare ki?"
Gyad'a masa kai tayi tare da fad'in, "Duk asibitin da naje sai ace ina d'auke da juna biyu, kuma ni wani
namiji bai tab'a kusantata ba." Mik'ewa doctor yayi tare da fad'in, "Tashi ki hau wancen gadon zanyi maki
scanning." Babu musu Sarah ta hau kan gadon tare da d'age rigar jikinta sama tana mai lumshe idanu
hawaye na zirarowa daga k'urmin idanunta. _AquaSonic_ (gel d'in da ake zubawa a ciki kamun scanning)
ya zuba mata tare da soma yi mata scanning. Kallon fuskanta dake a rufe yayi tare da mayar dashi kan
screen d'in computern dake nuna b'aro-b'aro tana d'auke da ciki. Bai fad'a mata ba sai mik'awa mata
tissue yayi tare da fad'in, "Goge jikinki ki koma ki zauna ina zuwa." Gaban Sarah na fad'uwa ta goge cikin
nata tare da sauka daga kan gadon sannan ta koma inda ta taso ta zauna tare da had'a kai da guiwa tana
addu'a a zuciyarta Allah yasa wannan karon an gano babu ciki a jikinta. Dawowa Doctor yayi hannunsa
d'auke da paper d'in da yayi printing ya zauna sannan ya kalleta na kusan second goma sannan yace,
"Saratu Nuhu!" A firgice ta d'ago gabanta na bugawa. Kallon paper d'in hannunsa yayi sannan ya kalleta
tare da fad'in, "Scanning machine ya nuna kina d'auke da ciki har na tsawon sati a jikinki. Fad'a min gaskiya
tsakaninki da Allah ko na iya taimakonki, ta yaya kika yi ciki?" Kuka Sarah ta fashe dashi sosai tare da soma
bubbuga k'afarta a k'asa tana jujjuya kanta. "Ba kuka za kiyi ba, fad'a min gaskiya za kiyi ko hakan zai iya
sakawa na taimaka maki." Jin haka ya saka Sarah ta tsayar da kukanta cak tare da fad'in, "Wallahi tallahi
doctor ni ba y'ar iska bace." Murmushin yayi don idan da sabo ya saba da jin haka a wajen wasu y'an
matan. "Naji, fyad'e aka yi maki?" Girgiza kai tayi tare da fad'in, "Bai kai ga jikina ba wallahi. Bai kusanceni
ba." Shuru yayi yana kallonta, sai can kuma yace, "Bari na amsa maki tambayar farko da kika min lokacin da
kika shigo. Cewa kika yi, Doctor da gaske ne mace na iya d'aukar ciki ba tare da namiji ya kasanceta ba? To
amsarki ita ce, dagaske ne mace na iya d'aukar ciki ba tare da d'a namiji ya shiga cikin jikinta ba. Amna idan
har mace zata bari namiji yayi wasa da al'aurarsa a jikin nata al'aurar har ya kawo, ma'ana ya fitar da
maniyi a kan al'aurarta, to tabbas zata iya samun ciki sai dai kuma sai dai the risk is very low sabida
kwayoyin halittar dake cikin maniyi zasu iya rayuwa ne na k'ank'anun lokacin a wajen jikin mace, amma a
cikin jikin mace zai iya d'aukar kwanaki biyar zuwa shidda kamun su mutu. Idan har mace ta soma jinin
al'ada (Menstruation) to a ranar idan ta fara k'irge, d'aya, biyu har zuwa kwana goma sha hud'u, to a ranar
take samar da kwai, kuma a wannan lokacin she's not safe, namiji na kusantarta, zata samu ciki. Kuma
sannan kar ki manta na fad'a maki sparm zai iya rayuwa a cikin jikin mace har na tsawon kwana biyar,
hakan na nufin idan aka kusanceta 11, 12, 13, ko ba'a kusanceta 14 ko 15 ba zata iya samun ciki. Shiyasa
yake da tsananin kyau mace ta rik'e kanta ko da wasan banza kada ta bari wani namiji yayi da ita idan ba
mijinta ba. Amma ban san mai yake janku ku y'an mata ba kuke fad'awa tarkon *_Samarin Shaho_*! Su
babu abunda suke so sai jikinku, kuma da sunyi amfani daku a k'arshe yar daku zasu yi sune su naimi ta
kirki su aura." Kuka sosai Sarah keyi, bata san ta yanda za tayiwa doctor bayani ba, sai cewa kawai tayi,
"Nagode doctor da bayanin da kai min." Sosai yaji tausayinta, amma har ga Allah babu wani abunda zai iya
yi mata. Kuma ba zai iya bata shawara a kan ta zubar da cikin ba. Sarah kuwa mik'ewa tayi tana jin kanta
kamar zai tsage tsabar yanda yake mata azabar ciwo, gashi irin bayanin da wancen doctor d'in yayi mata,
shi wannan doctor d'in yayi mata. Sabida haka babu wani buk'atar sake zuwa wani asibiti domin
tabbatarwa. Doctor Usman na kallonta har ta fice ta bar cikin office d'in. Ko da ta fito, a wajen asibitin ta
samu wani d'an dandamali ta zauna saboda jirin dake d'ibanta sosai. Ga wani uban yunwa dake kwakwular
cikinta. Had'a kai da guiwa tayi tana tariyo abunda ya faru kwanaki goma sha takwas da suka
wuce................

*_DAN DARAJAR GIRMAN UBANGIJI KAR KI FITAR MIN DA BOOK. WALLAHI TYPING AKWAI MATUK'AR
WAHALA DA CIN RAI. KI TAIMAKA MIN Y'AR UWA!_*

*_DUK MAI SONA TA HANYAR SAYAN BOOK D'INA KAWAI ZAI GWADA MIN, TURA D'ARIN KI BIYAR KI SHA
KARATU CIKIN SALAMA BISA WANGA ACCOUNT 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK SAI KI TURA DA
SHAIDAR BIYANKI ZUWA GA 08128755583_*

*_MATAR SAYYADEE_*
[13/09, 12:40 PM] Matar Sayyadee: Kuka take yi sosai har da shashshek'a tana jin ina ma bata zo duniyar
ba balle wannan abun ya same ta. Taso ta kasance ta daban a cikin y'an uwanta, sai gashi ita ma an rubuto
a cikin k'addararta akwai samun ciki ba tare da aure ba. Sosai ta tsani rayuwar da y'an uwanta suke yi
wanda mahaifiyarsu ita ce ta d'aura su a kan wannan turba saboda son abun duniya. Da ana canza
mahaifiya da tabbas ta jima da canza nata mahaifiyar. Mahaifinta ne ya fad'o mata a rai, ta san tabbas shi
zai fahimceta, to amma wanda zata aura fa? Tuno hakan ya saka ta kuma rushewa da kuka. "Shikenan ni
ba'a rubutomin aure a nawa littafin ba. Na shiga uku! Ni wallahi da nayi ta zama a cikin gidan mu ina
kwasar bak'in ciki, gwara na tafi *_Wamba_* wajen dangin mahaifina nayi zama na a can. Ban damu da ko
k'auye bane ko birni! Buri na in ganni a d'akin mijina ina bautar ubangiji!" Sarah ta fad'i a bayyane tare da
mik'ewa ta soma tafiya a k'afa kasancewar layuka shidda ne ya rabasu da inda take. Kan titi _Kasuwar
gwari_ ta mik'e tayi ta tafiya har ta iso _Jos road_ sannan tayi k'asa kasancewar can k'asan Jos road d'in
suke. Ga zafin rana, ga kuma zazzab'in dake damunta da matsanaici ciwon kai wanda ya ninku sakamakon
kukan da tasha. Tana isa k'ofar gidansu gabanta ya yanke ya fad'i ganin motar y'an sanda da kuma y'an
sandar a kwar gidansu ga kuma uban cincirundon samari da y'an mata har da wasu matan auren layin da
suka fito suna baiwa idanunsu abincin. Tana isowa gaba d'aya idanun jama'a ya dawo kanta. "Yauwa, ga
d'aya karuwar ta dawo. Da gani ba gida ta kwana ba. Ai mu dai Allah bai had'a mu da makwaftar kirki ba.
Ni dama tashin su za ayi daga unguwar nan don muna da y'ay'a mata dake tasowa kada suga abunda suke
yi suma su soma jin sha'awar yi." Fad'in wata mata tana hararar Sarah. Sarah kuwa kutsawa tayi cikin
mutanan nan ta shige cikin gidan. Turus ta tsaya ganin Baba a tsakar gida dafe da goshi gaban rigarsa duk
jini yana kuka, gefe kuma su aunties d'in Farouq ne da k'annansa maza da mata a gefe sai girgiza suke yi
suna fad'in wallahi baza su yarda ba. Nuratu, Aina'u, Na'ima, da Hassana kuma a waje d'aya suna fad'in
babu inda zasu je kuma babu uban da ya isa fitar dasu zuwa police station. Lami kuwa sai fad'i take, "Ko
kotu za'a je, aje ban jin tsoron uban kowa, sune suka biyo mu har gida da fitina, mu kuma muka kare
kanmu." Baba dake kuka ya kalli officer d'in da yake magana cikin lalama akan su Lami su biyosa zuwa
station yace, "Bawan Allah d'an sanda, ni na baka umarnin ka tafi dasu da tsiya, idan sunk'i kuyi amfani da
k'arfin ku na hukuma ku fitar dasu, amma kuma banda wancen da ta shigo yanzu, don babu hannunta a
kan duk abunda ya faru." Ya k'arisa maganar yana nuna Sarah. Police d'in kuwa, bai saurari maganar Baba,
sai bada baki yake yi, don babu yanda za ayi ya nuna power ya fitar dasu Nuratu zuwa police station domin
Hassana budurwarsa ce, Marfu'a kuma yanzu haka ma tana d'akinsa a wajensa ta kwana jiya. Hassanar ya
kira gefe, da kyar taje tana wani cin magani. Sun jima suna magana, a yanda yake lallaminta, zaka d'auka
uwarsa ce ita. "To naji, amma wallahi baza mu wuce mintuna ashirin ba a can." Da sauri yace "Na maki
alk'awarin haka." Sai da taja tsaki sannan ta koma tayiwa y'an uwanta magana sannan suka fita su duka
banda Sarah da ta jingina da bango abun duniya duk ta ishe ta. Ta gaji da matsalar mahaifiyarta da y'an
uwanta. K'arisawa tayi wajen Baba duk da jirin da take ji domin taimaka masa ya tashi. Rik'e mata hannu
yayi tare da fad'in, "Bari zan iya tashi Saratu. Kema naji jikin naki da zafi sosai. Ya aka yi Aina'u ta rigaki
dawowa daga asibitin, ko fad'a kuka yi?" Sai da ta taimaka masa ya mik'e tukun sannan tace, "A'a ba fad'a
muka yi ba, nice na baro ta a can asibitin." Baba bai k'ara cewa komai ba sai nufa wajen pamfo da yayi ya
wanke goshinsa sannan ya nufi kan baranda ya zauna a kan tabarma tare da fad'in, "Saratu, kiyi hak'uri duk
laifi nane da na kasa zab'a maku uwa ta gari. Y'an uwana sun nuna basu son na auri Elizabeth (Lami) amma
na nace ni ita nake so sabida yanda ta nuna min k'auna a wancen lokacin. Ban tab'a d'auka Elizabeth za
tayi min butulci a rayuwata ba." Kallonsa Sarah tayi tare da fad'in, "Baba ka bani labari, ta yaya ka had'u da
Lami har kuka yi aure, kuma mai yasa danginka suke fushi da kai har yanzu? Bamu san kowa naka ba, haka
suma basu san mu ba. Dangin Lami ma babu wanda ya san mu, muna bamu san kowa ba sai aunty Rose
Merry wanda Lami tace mana y'ar uwarta ce." Sunkuyar da kai Baba yayi tare da fad'in, "Rose Merry ba
y'ar uwar mahaifiyarku bace, asali ma itace mai d'aura mahaifiyarku akan turba mara kyau. Taso
mahaifiyarku ta koma addininta da ta baro, amma kuma sai mahaifiyarku ta nuna ita tana son addinin
musuluncin da ta karb'a." Sarah tace, "To amma Baba Lami bata sallah, bata azumi, duk wani abu na
musulunci Lami bata yi. Kuma a hakan ne take cewa tana son musuluncin?" Ajiyar zuciya Baba yayi tare da
fad'in, "Nima na jima ina wannan zargin Saratu. Anya kuwa mahaifiyarku bata koma addinin kiristancinta
ba kuwa? Domin duk ranar lahadi da sassafe take barin gidan nan, kuma bata dawowa Sia wajajen d'aya ko
biyu." Shuru Sarah tayi tana tuno wata rana da mahaifiyar tasu ta dawo daga inda take zuwa duk ranar
lahadi, sai ta ganta d'aure da wani zani mai hoton k'atoton cross a jiki, zanin biyu ne, da ta d'aura d'aya a
k'ugu, sai ta d'aura wani a sama kasancewar dama farar rigar less ce a jikinta. Ga wani k'aramin Bible a kan
gado. "Lami! Wannan wani irin kaya ne haka a jikinki irin na y'an coci?" Saurin kallon jikinta Lami tayi tare
da fad'in, "Kai, kin ganni nan d'azu da na fita, shine wata mota tayo kaina, garin na kauce mata sai na fad'a
cikin kwata, kuma dama kusa nake da gidan auntynku Rose Merry, shine ta bani wad'annan kayan na saka.
Yanzu ma Allah-Allah nake in cire su." Sarah ta kalli Bible d'in tare da fad'in, "Wannan kuma fa Lami!" A
harzuk'e tace, "Ke dan ubanki uwata ce ke? Kin cika ni da tsinannun tambayarki. To Rose Merry d'in ce ta
bani na ajiye mata a nan anjima idan zata wuce gida zata biyo tanan ta karb'a." Kallonta Baba yayi tare da
fad'in, "Lafiya Saratu kike dogon tunani haka?" Sauke ajiyar zuciya Sarah tayi tare da fad'in, "Baba ina tuna
wani abu ne. Ina ji a jikina Lami ta koma addinin kiristanci." Daga nan ta kwashe duk labarin abunda ya
faru wancen ranar ta fad'a masa. Da mugun mamaki Baba ke kallon Sarah, sai kuma ya girgiza kai tare da
fad'in, "Babu abunda Lami ba zata iya aikatawa ba. Lami ta daina bani mamaki sai dai tsoro. "Baba mai ya
same ka a goshin ka?" Fad'in Sarah ganin har goshin ya tasa. Sai da ya shafa wajen sannan yace, "Lami ce
taje jifan y'an uwan saurayinki da suka yi cincirundo domin d'aukar fansar abunda suka yi shine ta same ni
a goshi, kuma kin san budar ba ta roba bace. Don ma Allah ya tsare." Cike da tausayi Sarah yace, "Allah ya
k'ara tsareka Baba." Da ameen ya amsa tare da kallonta yace, "To Sarah ya ake ciki? Mai likitocin suka ce
wannan karon?" Fad'in Baba yana kallon Sarah data sunkuyar da kai tana hawaye. "Baba akwai cikin?" Sai
da gaban Baba ya fad'i da jin haka, amma ya d'aure tare da fad'in, "Kuma Saratu har yanzu baki gano bakin
zaren ba?" Shuru Sarah tayi don bata san ta inda zata fara yiwa Baba bayani ba. Hawaye ne kawai ke
zubowa daga idanunta yana d'iga a kan tabarmar da suke kai. "Saratu ni mahaifinki ne. Kuma kin san duk
fad'in gidan nan babu wanda na shak'u kuma nake jinsa har cikin raina cikin y'ay'ana idan ba ke ba. Kar ki
damu, zan fahimceki. Zan kuma yi maki nasiha matsayina na mahaifinki kuma in karb'i k'addararki da
hannu bibbiyu. Sai dai ba zan tab'a jin dad'i ba idan har ke da kanki kika kai kanki wajen wani namijin
bayan kin yi mi alk'awarin baza ki tab'a yin irin rayuwar da y'an uwanki suke yi ba." Kuka Sarah ta fashe
dashi tare da fad'in, "Na rantse da girman ubangijin halittu ban tab'a kaiwa wani namijin jikina ba domin
yayi amfani dani. Wallahi, tallahi duk abunda ya faru tsausayi ne Baba. Ban san ta yanda zanyi maka bayani
ba Baba. Amma wallahi ban tab'a karya maka alk'awarin da ba d'auka ba." Ko kamun Baba yayi wata
maganar wani yaro ya kwad'o sallama tare da fad'in, "Wai ana sallama da Sarah a waje. Wai dan girman
Allah ta fito mintuna biyar kawai!"

*_Kuyi hak'uri da wannan, anticipate a long page tomorrow _*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

*_ZULFA'U SA'EED IBRAHIM AKA 👉MATAR SAYYADEE_*


[14/09, 1:26 PM] Matar Sayyadee: Kallon yaron Sarah tayi, sannan ta maida kallonta izuwa wajen Baba
tare da fad'in, "To kuma wanene? Na san dai Farouq ba zai sake dawowa k'ofar gidan nan domin ni ba."
Baba yace, "Kije kiga ko wanene ke kiran naki. Allah yasa dai lafiya." B'ata rai Sarah tayi tare da fad'in, "Da
kuma so nake na kora yaron yaje yace bazan zo ba." Girgiza kai Baba yayi tare da fad'in, "Ba'a haka Saratu.
Ba'a wulak'anta d'an Adam. Kije kiga ko wanene." "Je kace tana zuwa!" Sarah ta fad'i tare da mik'ewa don
har yanzu tana ganin jiri-jiri ga kuma yunwar dake kwakwular cikinta. D'aki ta koma ta canzo hijjab d'in
jikinta ta saka wani brown wanda ya kai mata har guiwa sannan ta fito tana dafa bango ta nufi waje. Baba
na kallonta har ta fice kamun ta ya sunkuyar da kai yana tsiyayar da hawayen tausayinta. Sarah kuwa tana
fita taci karo da wata arniyar motar da bata tab'a ganin irinta ba k'irar *_Aston Martin Vulcan_* kalar ash
mai duhu. Ba ita kad'ai ba, hatta jama'ar layin fitowa suka yi suna kallon motar. Shi kuwa _Khalilullah_ sai
da ya gama k'are mata kallo ta cikin tinted glass d'in motar sannan ya bud'e tare da ziro k'afarsa d'aya.
Farar kyakkwar k'afar ta soma bi da kallo kamun taga ya fiddo da gangan jikinsa, tun daga d'an yatsan
k'afarsa take kallo har ta sauke a kan fararan manya-manyan idanunsa masu matukar d'aukar ido. Wani irin
lumshe idanu tayi jin daddad'an k'amshin turaren *_Imperial Majesty_* da ya bugi hancinta. Sosai take
matuk'ar son k'amshi musamman a yanayin da take ciki. Folding hannunsa yayi tare da jingina a jikin motar
yana kallonta. Bud'e idanu tayi a hankali ta kuma sauke idanunta a kansa karo na biyu tayi saurin b'ata
fuska tare da k'ok'arin juyawa zata koma cikin gida. Cak ta tsaya sakamakon jin abunda yace, "Kul! Kar ki
sake ki bar wajen nan idan ba haka ba zan baki mamaki." Juyowa tayi ta watsa masa harara tare da bud'e
baki za tayi magana shi kuma ya d'aura d'an yatsansa a kan bakinsa tare da fad'in, "Ssshh! Ko kalma d'aya."
Yana fad'in haka ya tako cike da isa ya iso inda take a tsaye tare da fad'in, "Kin yi missing d'ina ko?" Karo na
biyu ta kuma watsa masa harara tare da d'an matsawa baya kad'an jin kamar zasu had'e da juna ga kuma
wannan mayataccen k'amshin nasa dake naiman sumar da ita a tsaye. "Zan kwakwule idanun nan naki
idan suka kuma hararata." Kallon gefe Sarah tayi tare da fad'in, "Menene matsalar ka dani ne? Mai yasa ka
addabi rayuwata? Dan girman Allah ka kifa daga rayuwata in samu salama. Ka barni da bala'in daka jaza
min dan girman Allah!" Sarah ta k'arisa maganar tare da fashewa da kuka. Kallonta ya dunga yi ba tare da
ya ce mata tayi hak'uri ta daina kuka ba. Sai da tayi mai isanta sannan ya saka hannu cikin aljihu ya fiddo da
wani d'an ma daidaicin handkerchief ya mik'a tare da da fad'in, "Come on, wife those tiers of yours!"
Karb'an handkerchief d'in tayi tana mai watsa masa harara sannan ta kai kan fuskanta, kamun ta share
hawayen sai da ta zuk'i k'amshin turaren tukun. "To bani abuna." Ya fad'i yana mai mik'a mata hannunsa.
Mik'a masa tayi tare da fad'in, "Ai dama bani na rok'a ba." Amsa yayi tare da yin murmushi ya maida cikin
aljihunsa sannan yace, "Kin matuk'ar bani wahala Sarah! Kin san kuwa irin naiman ki da nayi?" Kamar ta
shak'e masa wuya haka take ji, wani tsaki tayi tare da fad'in, "Idan abunda ya kawo ka wajena kenan, juya
ka bar k'ofar gidan nan yanzu. You're not welcome here. Out of my sight. Kuma yanda ka tarwatsa min
farin ciki, kai ma baza ka tab'a samun farin ciki ba." Maimakon maganganunta su bashi haushi, sai yayi
wani irin murmushi mai sauti tare da fad'in, "Idan har bazan tab'a samun farin ciki ba, to kema baza ki
tab'a samu ba Sarah. Domin an halicceki ne domin ni kawai. Farin cikina yana tare dake, haka kema farin
cikinki yana tare dani ne. Sannan kuma ina so ki saka wannan maganar da zan maki yanzu cikin
kwakwalwarki, ba ai min tsaki! Kar ki sake." D'ago jajayen idanunta tayi zata saki masifa sai ga keke napep
ya tsaya a bayan motar _Khalil_. Aina'u, Nuratu, Na'ima da Hassana a baya, sai Lami dake zaune a gaba ta
rik'e k'arfe. Fitowa suka yi gaba d'ayansu suna k'arewa motar _Khalil_ kallo. Lami ce ta riga kowa magana
tare da fad'in, "Kun ga wata arniyar mota! Wallahi tunda uwata ta haife ni ban tab'a ganin mota mai kyawu
ba irin wannan." Na'ima ta kalli Nuratu tare da fad'in "Kamar fa *_Aston Martin Vulcan_* nake gani."
Nuratu tace "Ya kike fad'i da kaya a jikinki! Ai kuwa tabbas ita ce wallahi." Zagayawa suka yi domin su
k'arewa motar kallo dakyau. Idanunsu ya sauka akan Sarah dake kallonsu tana addu'ar Allah yasa kar su
nuna halinsu _Khalil_ ya raina ta. Sai dai Addu'arta bata karb'u ba domin da sauri Lami ta k'arisa wajen
tana k'arewa _Khalil_ da Sarah kallo. "Eh lallai! To yau dai Allah ya tona asirinki kin kawo sa har k'ofar
gidanku. Wato saboda kin ga bama gidan ko?" Sai ta maida dubanta ga _Khalil_ tare da fad'in, "Samari
kalle ni nan, nice mahaifiyar Sarah." D'an sunkuyar da kai _Khalil_ yayi tare da risinawa yace, "Sannu da
zuwa Mama, ina wuni, mun sameku lafiya?" Shan mur Ki tayi tare da waigawa ta k'ara k'arewa motar
_Khalil_ kallo sanna ta maido dubanta ga _Khalil_ d'in tare da fad'in, "Bafa lafiya ba. Domin dai yanzu haka
daga police station muke ni da sauran y'ay'ana gasu nan kana kallonsu." Tayi nuni da su Nuratu da suka
k'ariso suma. Kallo d'aya yayiwa Aina'u ya shaidata, kuma itama ta gane sa. Kau da kai tayi tana tsaki cikin
zuciyarta. Shuru _Khalil_ yayi yana sauraran Lami. Ita kuma ta cigaba, "To ni bama duk wannan ba, ashe kai
ne uban cikin dake jikin Saratu, amma don tsabar iskanci da mugunta irin nata, sai tak'i fitowa ta fad'a min
gaskiya don kar a dangwali arzikin dani, to yau dai Allah yayi sai mun yi foureyes da kai. Don haka akwai list
d'in da nake rubutawa in ajiye sabida irin haka. Don fisabilillahi bazan iya ciyar da y'ay'ana kuma in ciyar da
nasu y'ay'an ba. A k'a'ida ta zama cikin gidana, a cikin su kaf...." Tayi nuni da su Nuratu tare da cigaba da
fad'in, "Duk wacce tayi ciki to kawo saurayin take gidan nan muyi tsada dashi domin d'awainiya da cikin,
bayan ta haihu kuma, ni can cigaba da kula da babyn, cinsu, wankansu da duk wani abun da suke buk'ata.
Don haka kai ma zan baka wannan list d'in, na ganka da maik'o a jikinka, don haka list d'inka daban ne."
Kuka Sarah ta fashe dashi tare da durk'ushewa a wajen. Lami kuwa da baki ta nuna ta tare da fad'in,
"Munafuka! Kiyi kukan jini ma. Wallahi sai na kawo masa list d'in nan kuma sai anci arzikin dani." Turo baki
Aina'u tayi tare da watsawa Lami harara tace, "Sai kuma aka ce maki shi yayi mata cikin? To bashi bane!" Ta
k'arisa maganar a tsawace. _Khalil_ kuwa mutuwar tsaye yayi yana kallon Lami da sauran y'ay'anta. So
yake yaji ana tashinsa ana fad'a masa cewar mafarki yake yi, amma sai tsungulin cinyarsa yake yi ta baya,
da yaji zafi sai ya tabbatar fa lallai ba mafarki bane. "Wannan wani irin gida ne na kawo kaina?" Fad'in
_Khalil_ cikin zuciyarsa, amma a zahiri bakinsa ko motsi ya kasa yi sai bin Lami da idanu yake yi. Zuciyarsa
na tabbatar masa da cewar Lami ba ita bace mahaifiyarsu Sarah. Ga dai y'ay'a nan kyawawa Allah ya bata,
amma kuma babu tarbiya. "Jira ni, bari na shige na kawo maka list d'in." Fad'in Lami tare da shigewa cikin
gidan. Na'ima kuwa, kallon Sarah tayi tare da fad'in, "Lallai Sarah kinyi babban kamu babu k'arya! Ina jiran
nawa kason a cikin jira. K'anina a bata nawa kason ta kawo min." Fad'in Na'ima tare da shigewa. Nuratu
kuwa sai kallon motar take yi ita da Hassana suna Santi. Don har hotuna suka yi a jikin motar kamun suka
shige cikin gidan. Aina'u kuwa wani kallo tabi Sarah dake duk'e a k'asa tana kuka tayi tare da jan dogon
tsaki ta kalli _Khalil_ tare da fad'in, "Baka dai ji warning d'in da nayi maka ba kenan? Kana wahalar da
kanka ne. Don tabbas gidan mu ba'a aure." Tana gama fad'in haka ta fad'a cikin gidan. _Khalil_ ya jima a
tsaye mamaki kamar ya kashe sa kamun ya duka ya kalli Sarah cike da dakewa yace, "Mik'e.!" Yanda yayi
maganar cike da command ya saka bata san lokacin da ta mik'e tsaye ba. Jiri ne ya kwashe ta tayi baya zata
fad'i yayi saurin tarota ta fad'o jikinsa dai-dai lokacin da Lami ta fito hannunta rik'e da wata doguwar
paper. Wani dariya tayi tare da fad'in, "Kaiii jama'aa! To ai da shigowa kuka yi daga ciki sabida idanun
jama'a. Ka san fa unguwar nan an saka mata idanu." Wani irin kallo ya jefi Lamin dashi, don wani irin
tsanarta yaji ya darsu cikin zuciyarsa. "Ungo amshi nan!" Fad'in Lami tana mai mik'a masa paper d'in. Da
kamar ba zai amsa ba, sai kuma ya mik'a hannu ya amshi paper d'in yana kallon cikin idanunta. "Sai na ji
sak'on ka, kuma da kanka nake son kazo." Tana gama fad'in haka ta juya ta koma ciki. Da idanunsa da suka
rikid'e suka koma jazur yake kallon Sarah tare da daga mata wani gigitaccen tsawa yace, "Mai kike nema?
Nace mai kike so da baza ki iya fad'a min ba? Mai yasa kika min haka? Mai yasa kika bawa wani kanki
Saratuuu??" Bakinsa har rawa yake yi don har hasaso yanda abun ya kasance yake yi a idanunsa. Kuka
Sarah ta fashe dashi don sosai ta tsorata dashi. "Ke! Ba kuka nace kiyi min ba, bayani zaki yi min. Uban wa
yayi maki ciki?" Yanda yake maganar da k'arfi da kuma tsananin b'acin rai sai ya sanya jikin Sarah soma
wani irin rawa tana kallonsa. "Ki bar kallo na ki bani amsa. Waye kika bawa budurcinki?" Bata san lokacin
da ta bud'e baki tace, "Na rantse da girman Allah babu namijin da ya tab'a sanina matsayin mace." Wani
kallo ya watsa mata tare da fad'in, "Ke nan karya ko kuma ince k'azafi aka miki." Da k'arfi kuma cike da
tsoro tace, "Eh ina da ciki kuma uban cikin......." Bai bari ta k'arisa ba ya fizgi hannunta da k'arfi tare da
nufar inda motarsa yake yayi. Da dannu d'aya ya bud'e gaban motar tare da jefa ta ciki ya kunne sannan ya
zagaya ya koma mazaunin driver tare da shiga yayiwa motar key, "Ina zaka kai ni? Ka bud'e min mota in
fita. Na shiga uku mai zaka min?" Wani irin kallo keep quiet yayi mata tare da jan motar ya figeta a guje ya
bar layin. Kuka sosai Sarah keyi tana fad'in, "Stop the car I'm begging you. Dan girman Allah ka tsayar da
motar nan inyi maka bayani. Kar ka cutar dani a karo na biyu bawan Allah! Ka dubi girman Ubangiji! Idan
har baka da y'ay'a, kana da k'annai ko kuma y'ay'an y'an uwa. Dan Allah ka mai dani gidan mu." "Quite!" Ya
fad'i da mugun k'arfi tare da taka wani irin burgi dai-dai gate d'in asibitinsa. Sai da Sarah tayi gaba ta dawo
ta buge guiwarta. Kallon asibitin tayi a firgice, sabida tsananin rud'ewa bata gane asibitin ba, ta d'auka
hotel ne. "Na shiga uku ni ka mai dani gida dan Allah!" Ko kallonta bai yi ba sai ya danna wani mahaukacin
horn mai kashe kunnuwan mai sauraro. Da mugun sauri mai gadi ya bud'e gate d'in shi kuma ya danna
hancin motar ciki tare da naiman waje yayi parking tare da fitowa daga cikin motar ya zagaya ya bud'e side
d'in da Sarah take ya bud'e ya fizgo hannunta. Hankali tashe take kallonsa tare da, "Na rok'e ka da girman
ubangijin ka barni na koma gida." Bai saurareta ba sai jan hannunta da yayi zuwa cikin asibitin. Nurses da
idanu suka bisu ganin yana janta tana ita kuma tana kuka. Dai-dai nan doctor Kamal ya fito daga wani
office daban. Da idanu shima ya bisu don kallo d'aya yayiwa Sarah ya gane itace wacce tazo tana kuka tana
fad'a masa is bata san ta yanda aka yi tayi ciki ba, bayan kuma sau uku yana tura ta yin scanning kuma yana
ganin cikin. Mamaki yake yi sosai ta ina _Ibrahim_ ya santa. Kai tsaye office d'in da yake mallakinsa ya
bud'e tare da tura Sarah ciki sannan ya shiga ya kallo k'ofar tare da murza key. Yanda gaban Sarah ke
bugawa da k'arfi har ana iya ganin hakan ta gaban hijjab d'inta sabida yanda yake d'agowa. Nuni yayi mata
da gadon da yake duba marasa lafiya tare da fad'in, "Kwanta a can!" Ja da baya Sarah tayi tare da fashewa
da kuka tace, "Bazan Kwanta ba, wallahi bazan kwanta ba ko zaka kashe ni." A fusace yace "Ni kike fad'awa
haka?" Ya fad'i hakane yana mai matsowa, sai kawai ji tayi ya d'agata cak tare da d'aura ta a kan gadon.
Yunk'urawa tayi zata sauko ya danneta da hannunsa guda d'aya tare da zuba mata tsinannun idanunsa
yace, "Na rantse da ubangijin da ya busa min numfashin kika k'ara yunk'urawa da niyyar saukowa sai na
maki abunda har ki mutu baza ki manta ba." Sarah na jin haka ta sadak'ar tare da komawa ta kwantar da
kanta ta rintse idanunta hawaye na silalowa daga k'urmin idanunta. Gani take yi kamar tarihine zai
maimaita kansa. Bata k'ara tabbatar da haka ba sai da taji hannunsa yana yaye doguwar rigar dake jikinta
zuwa cikinta. Da sauri ta rik'e hannunsa da k'arfi ba tare da ta yunk'uro ba tana mai fashewa da kuka.
"Sake min hannu!" Ya kuma fad'i da k'arfi. "Kayi hak'uri! Kayi hak'uri!! Kayi hak'uri d'an girman Allah!!!"
Shine abunda Sarah tayi ta maimaita. Shi kuwa _Khalil_ ko sauraronta bai yi ba sai ma zame pant d'inta da
yayi k'asa tare da ware mata k'afafunta. Wannan karan ta yunk'uro ya maida ta da k'arfi sai da bayanta ya
bugu tare da tura yatsarsa d'aya ciki, hakan yayi dai-dai da wani irin ihu da Sarah ta kwala da uban k'arfi.
K'ara k'ok'arin tura yatsar yayi cike da mamaki a karo na biyu. Wannan karan gaba d'aya Sarah ta d'ago
tana fad'in, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Zare hannunsa yayi tare da jawo Vaginal Examination lamb
ya haska wajen sosai. Cikin da tsananin mamaki yake kallon fuskanta bayan ya d'agota. Tausayinta sai ya
rufe shi tare da dana sanin abunda yayi mata yanzu. Ja mata pant d'in yayi sama tare da kwantar da ita flat
ya zuba mata _AquaSonic_ gel sannan ya soma scanning cikin. Wani mugun ajiyar zuciya ya saki ganin ga
ciki nan b'aro-b'aro ya nuna a jikin screen d'in computern. "Tashi ki zauna." Ya fad'i politely. Mamaki ne ya
cika Sarah jin yanda yayi mata magana a sanyaye. Babu musu ta tashi ta zauna tana kallon tiles d'in dake
shimfid'e a office d'in still her heart is beating soo fast. Sauko da ita yayi tare da kai ta kan kujera ta zauna.
A gabata ya duk'a yana kallon fuskanta tare da fad'in, "Sarah hakan na nufin cikin nan dake jikinki, nine
ubansa?"

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*
Kuka Sarah ta fashe dashi tare da fad'in, "Tun da na taso nake tsan-tsan da jikina. Bana k'aunar irin rayuwar
da y'an uwana suke yi. Abun yana mun ciwo sosai a zuciyata, hakan ya saka na d'auki alwashi in Sha Allah
babu wani d'a namijin da zai sanni matsayin y'a mace, sai mijin da ya biya sadaki ya aure ni. Amma ka rusa
min tsari, ka cuce ni kayi min ciki. Ka jefeni da bak'in fentin da ba zai tab'a goguwa ba a rayuwata. Aure na
saura sati hud'u, na dad'e ina burin zama matar aure, amma ka rushe min wannan burin, ka jefa ni a sahun
sauran y'an uwana masu tab'o a goshi. Yanzu mai zan ce da wannan d'an idan ya fito duniya. Ta yaya zan yi
masa bayani idan ya tambayeni ina mahaifinsa. Tabbas ka aikata abunda kace zaka aikatan, dama wancen
ranar kace min sai ka min abunda har abada ba zan tab'a mancewa ba, kuma tabbas har abada bazan
mance ba, kuma wannan abu zai ta bibiyata har mutuwata. Mai nayi maka bawan Allah? Mai yasa zaka
min wannan cutar? Shin baka da k'anwa ne? Idan wani yayi mata abunda kayi min, ya zaka ji a zuciyarka?
Baka tunanin Allah zai iya rama min abunda kayi min a kan y'ay'anka! Duk abunda kayi sai an......" Bai bari
ta k'arisa ba ya saka tafin hannu ya toshe mata baki tare da k'ureta da idanu kamar zai fashe da kuka. "Nayi
maki rantsuwa da girman ubangijin daya halicceki, ya halicceni da duk abunda yake cikin duniya, wallahi,
tallahi ban tab'a zina ba, ba d'abi'ata bace. Na bar abunda ya faru tsakanina dake matsayin K'addara ko
kuma ince maki jarabawa. Sarah tun lokacin da wannan abun ya faru, ina dai rayuwa ne kamar ina cikin
farin ciki amma kuma a bad'ini abun ba haka bane. Shaidan ne da kuma zafin zuciya ya rinjayeni. Amma ni
banda niyyar cutar dake. Ke shaida ce a wancan ranar da niyyata shine cutar dake, duk da na fahimci ke
d'in cikakkiyar budurwace, da ba zan kyaleki ba sai na ratsa jikinki. Allah yayi sai nayi ajiya a cikin shiyasa
har na samu natsuwa a wajen jikinki. Ki yafe min Saratu! Ki yafe min tabbas na b'ata maki record. Amma
ina so ki saka cikin ranki, wallahi tallahi tun bayan da abun nan ya faru Allah ya jarabceni da zazzafar
soyayyarki, kuma nayi maki alk'awarin sai na share maki hawaye na cika maki burinki na zama matar aure.
Ni nan _Ibrahim Khalil Nasuruddeen_ zan aureki in killaceki a cikin gidana. Zan taya ki rainon d'anmu ko
y'armu har ya fito duniya, bayan nan kuma ko sati baza ki k'ara a gidanku ba zan aureki." Mik'ewa Sarah
tayi tare da fad'in, "Bana fatan ka kasance matsayin mijina. Domin ban san a matsayin mai zan rik'a
kallonka ba. Cuta dai ka riga ka gama cutata. Ka b'ata min record. Idan har na aureka zan rik'a kallo kamar
ba don Allah ka aureni ba. Kaje kayi rayuwarka nima nayi tawa. Kaje ka samu y'ar masu kud'i da asali dai-
dai kai, nima kuma idan ina da rabon auren a duniya, Allah zai had'a ni da dai-dai ni." Da sauri _Khalil_
yasha gabanta tare da fad'in, "Kar ki min haka Sarah, dan Allah kar ki hukuntani ta haka. Wallahi tallahi,
Allah shine shaida na akan irin k'aunar da nake maki. Dan Allah don't reject me Saratuuu." Gitta shi tayi
tare da fad'in, "Y'ay'an masu kud'i zasu iya yin komai saboda suna da wanda ya tsaya masu, ko da kud'in su
zasu iya taka kowa kuma ya taku. Na san idan kaso yau ba zan k'ara kwana a duniya ba, sai dai ina rok'onka
da girman ubangijin ka fita daga harkata, kar ka k'ara kusanto inda nake ko kuma ka nuna ka sanni. Idan
kayi min haka, wata k'ila in iya ji a zuciyata zan iya yafe maka." Kallonta ya dunga yi yana jin k'una cikin
zuciyarsa, "Sarah rayuwarki a hannuna take da zaki ce idan naso ba zaki kwana a duniya ba yau? Dan Allah
kar ki k'ara wannan maganar. Da mai kud'i da talaka duk d'aya ne a wajen ubangiji. Ke baki san talaka yafi
mai kud'i kwanciyar hankali ba. Bama wannan ba, kin san da cewar idan Allah yaga dama sai ya kwace
dukiyar da ya bawa mai kud'in ya bawa talaka har sai wannan mai kud'in ya dawo yana naima k'ark'ashin
talaka. Dani dake bamu da wani bambamci Sarah. Dan girman ubangijin ki gafarceni kar ki min azaba da
rashin amincewarki." Kau da kai Sarah tayi tare da fad'in, "Bud'e min k'ofa in wuce gida, don idan zamu
wuni mu kwana mu kuma k'ara kwana amsa ta d'aya ce a gare ka. Kaje ka naimi dai-dai da kai." Wani
abune yazo ya tokare wuyarsa, tun da yake a duniya bai tab'a furtawa wata mace Kalmar so ba a
rayuwarsa, sai dai shi ba zai iya k'irga adadin matan da suka furta masa kalmar ba. Y'ay'an masu kud'i,
turawa har da indiyawa, amma bai tab'a bawa d'aya daga cikinsu full attention d'insa ba balle har soyayya
ta k'ullu. Amma wai yau gashi gaban k'aramar yarinya yana rok'onta akan ta soshi tana wasa da zuciyarsa.
Ajiyar zuciya ya sauke, miskilancinsa suka hau kai tare da jik'imarsa, wani irin kallon gefen idanu ya bita
dashi tare da fad'in, "Haka kika ce? So be it! Amma kuma ni zan tabbar maki babu wannan macen da
_Khalil_ zai bud'e baki yace yana sonta ta k'i. Kamar yanda d'ana yake kwance a cikin mahaifarki, to haka
_Khalil_ zai kasance cikin zuciyarki, sannan kuma wallahi babu wannan namijin da ya isa ya shiga gonar
_Khalil_. Idan har ba _Khalil_ zaki aura ba, to zo rubuta ki ajiye babu ke babu aure!" Yana gama fad'in haka
ya koma ya zauna ya soma danne-danne cikin computer yayi kamar ya manta tana cikin office d'in. Sarah
kuwa da ta gaji da tsayuwa sai ta sulale k'asa ta zauna tana mai da numfashi. Da gefen idanu ya kalleta, sai
kuma ya d'ago gaba d'aya tare da fad'in, "Wallahi wallahi idan baki tashi a k'asan nan ba kika bari nazo
wajen nan zan baki mamaki!" A fusace Sarah tace, "Wani mamaki? Nace wani mamaki ne kuma ya rage
baka bani ba." Ba tare da yace komai ya mik'e a fusace. Ko kamun yayi taku d'aya ta mik'e da sauri ta zauna
a kan kujeran dake fuskantarsa. Wani dariya ne ya taho masa amma yayi saurin mayar dashi tare da kau da
kai yana murmushi don dama ba zuwa wajenta zai yi ba, kawai barazana ce domin ta bar tiles d'in saboda
sanyi. Zama yayi tare da cigaba da abunda yake yi. Ita kuma Sarah sai harare-harare take yi. Sun kwashi
kusan awa guda sannan ya mik'e tare da fita ya kullo k'ofar. Sarah na ganin ya fice kuma ya kullo k'ofar ta
kifa kanta akan desk d'in ta fashe da kukan bak'in ciki. Shi kuwa _Khalil_ yana fita suka ci karo da doctor
Kamal dama kuma wajen _Khalil_ d'in zai zo. "Wajenka dama zan zo." Gyara tsayuwa yayi tare da yin bake-
bake a k'ofar office d'in ya wani ci d'aci tare da fad'in, "To gani!" Sai da doctor Kamal ya kalli k'ofar office
d'in sannan yace, "Ka kira ni emergency akan inzo nan kai zaka je yin wani abu, sai kuma gaka na ganka
tare da wannan yarinyar. _Khalil_ ba halinka bane. Dan Allah kar kace zaka zubar mata da cikin dake jikinta.
Y'an iskar yara sai sun gama yawon banzan su a tit....." A mugun tsawace _Khalil_ yace, "Enough! Enough
doctor Kamal Isah Bashir! Kar ka k'ara jifan Sarah da wad'annan kalmomin. Sarah ba irin matan da kake
tunani bane." Baki bud'e doctor Kamal ke kallon _Khalil_ don bai tab'a ganinsa a irin wannan yanayin
sabida mace ba. Macen ma mai d'auke da cikin shege. A iya sanin da yayi wa _Khalil_ ya tsani y'an iskan
mata. " _Khalil_ this lady that you're protecting haka, she's prostitude! Duk abunda zata fad'a mak......" Bai
kai k'arshen zancen ba yaji wani gigitaccen mari ya sauka akan kuncinsa sai da yayi saurin saka hannu ya
dafe kuncin yana mai kallon gefe-gefe. Ganin babu kowa kuma babu wanda yaga komai sai ya kalli _Khalil_
tare da fad'in, "Ibrahim ni ka mara? Ni ka mara saboda ina fad'a maka gaskiya." Wani kallon banza yayi
masa tare da fad'in, "To hell with the fucking stupid gaskiya gaskiyarka. Idan bakinka ya kuma kuskuran
kiran matar da zan aura da karuwa, na rantse maka da ubangijin rana da wata sai na d'aureka kuma babu
uban da ya isa ya fito da kai. Kuma cikin jikinta it's mine. Na fad'a da babban murya, cikin dake jikin Sarah,
nawa ne! Kuma duk uban da ya isa ya kira ta da karuwa yaga abunda *_Ibrahim Khalilullah Nurudden_* zai
aikata." Yana gama fad'in haka ya wuce fuuuuuu ya nufi pharmacy domin d'auko mata magunguna don tun
d'azu yake lura da ita jiri take gani kuma babu k'arfi a jikinta. Shi kuwa doctor Kamal da mugun tsananin
mad'aukakin mamaki yabi _Khalil_ d'in da idanu. Don ya mugun sanin hakinsa. In fact tare suka yi karatu a
_London_ har kammalawan su. Yasan yanda ya tsani Zina da kuma mazinatan. Sannan yaga mata kyawawa
iri-iri, turawa, indiyawa, larabawa duk bai fad'a halaka ba sai akan wannan tatsitsiyar yarinyar duk da ita
ma kyakykyawar ce. Shafa kumatunsa da suka ji mari yayi tare wucewa ya bar wajen. _Khalil_ kuwa sai da
ya d'auko duk magungunar da yasan Sarah zata buk'acesu sannan ya dawo office d'in hannunsa d'auke da
leda mai tambari da sunan asibitin still kuma fuskansa a mugun d'aure. "Ki tashi in mayar dake gida." Ya
fad'i sounding command. Cikin sauri ta mik'e shi kuma ya fita tabi bayansa. Kulle k'ofar yayi tare da fad'i,
"Kiyi tafiya a hankali kar ki fad'i. Ko in rik'e ki?" Da jin haka tayi saurin yin gaba don taga alama sam bai da
kunya. Har wajen motarsa suka isa, shi ya bud'e mata gidan gaba ta shiga sannan ya zaga ya shiga driver sit
sannan ya tada motar yayi reverse ya bar cikin asibitin. A hankali ya dunga tafiya ba tare da ya k'ara ce
mata ko uffan ba har suka isa k'ofar gidansu Sarah. Parking yayi tare da kashe motar ya juyo ya tsura mata
idanu. Tana jin idanunsa na yawo a jikinta amma tak'i kallon wajen. Ledan maganin ya d'auko tare da fiddo
da magungunan ciki sannan yace, "Hey, kalle ni nan." Kamar baza ta juyo ba, sai kuma ta juyo ta kallesa
tana mai turo baki gaba. Tsurawa kyakkwar bakinta kallo yayi yana tuno ranar da tsautsayin ya afka. "Kin
san wani abu? Tsiwarki ita ke ja mutun yayi maki abunda bai yi niyya ba. Ko wancen ranar ke kika ingiza ni
har mai afkuwa ta afku. Idan kika b'ata rai ko kuma kika turo baki, wani irin kyawu kike k'ara yi sosai. Sai ki
rik'a looking very sexy!" Wani irin kuka Sarah ta fashe dashi jin abunda yace. Bak'in ciki take ji idan yana
maganar cikin dake jikinta. "Kin san Allah idan kina kukan nan, wancen ranar ba'ayi na gaske ba, amma ina
ganin soon an kuwa zuwa wajen." Hannu ta kai zata bud'e k'ofar taji sa a gark'ame. Kallonsa tayi tare da
shagwab'e fuska tace, "Dan girman Allah ka bud'e min, kaji ma kiran sallah ake yi!" Kallon maganin da ta
fito dashi yayi tare da fad'in, "Kalli nan, wad'annan guda ukun kullum sau d'aya zaki rik'a sha, wannan
kuma safe da dare. Allah ya k'ara maki lafiya Matata. Kiyi min magana da Mama idan kin shiga ciki. And
lastly, wallahi kar in k'ara kiranki a waya kik'i d'agawa. Don wallahi komai dare sai nazo, kuma ni kai na ban
san mai zai faru ba idan nazo d'in." Yana gama fad'in haka ya cire lock d'in yana kallon fuskanta. Bud'e
motar tayi ta fita a hankali ba tare da ta d'auki ledar ba, sai da ta rufe k'ofar sannan ta lek'o ta window
kasancewar ya zuge glass d'in tare da fad'in, "Ba zan d'auka ba, dan girman Allah kar ka fasa abunda kace
za kayi. Kuma bazan sha maganin ba. Ka tafi da tsiyarka. Kuma cikinka dake jikina, a leda zan juye na watso
maka shi a fuska na huta da jaraba." Da wani irin hanzari ya cafki hijjab d'inta ya cukuikuyota da hannu
d'aya tare da fad'in, "Maimaita mai kika ce?" A gigice tace, "Na rantse cewa nay na manta ga ledan
maganin nan baka mik'o min ba. Kuma wancen farin ma ya ma kace ayi amfani dashi." Dariya ce ta taho
masa sosai amma bai yi sai murmushi ya saki tare sa d'aukar maganin da d'aya hannunsa ya mik'a mata.
Da sauri ta amsa har da fad'in, "Nagode" shi kuma ya saki hijjab d'in nata tayi saurin barin wajen ta nufi
k'ofar gidansu ba tare da ta waiga ba. Tana bud'e k'ofar suka ci karo da Baba ya fito karo na bakwai ko
Allah zai sa ya ganta. Don lokacin dasu Na'ima suka baje a tsakar gida babu labarin da suke yi sai na
_Khalil_ da irin motar da yazo da ita. Jin hakan sai ya tada hankalin Baba ya soma tunanin ko Sarah ta soma
hawa layin y'an uwanta ne. Ya jira kusan mintuna ashirin ko Sarah zata dawo amma yaji shuru, ya daure ya
k'ara goma akai, ganin har lokacin shuru sai ya mik'e ya d'auki sandarsa ya fito waje amma wayam. Yana jin
sanda su Na'ima suke dariyar ya fita nemo y'ar gwal. "Baba dama dawowa kayi kar ka wahalar da kanka.
Don saurayinta yazo sun fita tare." Fad'in Hassana. Bini-bini Baba ke fitowa ya duba ko Sarah ta dawo
amma wayam. Sai a karo na bakwai sannan ta turo k'ofar suka yi ido hud'u. Wani ajiyar zuciya Baba ya
sauke tare da fad'in, "Saratuuu!" Sai kuma ya fashe da kuka. Da sauri Sarah ta waiga taga motar _Khalil_ na
nan, sai taji hankalinta ya tashi don bata son yardar da Baba yayi mata ya rushe. A gigice ta soma magana,
"Wallahi Baba ba abunda kake tunani bane. Dan Allah ka daina kuka." Ta fad'i tana mai fashewa da kukan.
Da sauri _Khalil_ ya bud'e mota ya fito tare da k'arisowa wajen ya duk'a tare da fad'in, "Ina wuni Baba?"
Baba dake matsar hawaye ya d'ago ido ya kalli _Khalil_ tare da fad'in, "Bawan Allah na rok'e ka da girman
ubangijin idan ba alkhairi bane ya kawo ka wajen Saratu kayi tafiyarka Allah ya had'a ka da dai-dai da kai.
Ka dubi Allah da annabi kar ka lalata min tarbiyan y'ata guda d'aya da ta fita zakka!" Shuru _Khalil_ yayi na
y'an dak'ik'u tare da fad'in, "Baba wallahi alkhairi ne ya kawo ni wajen 'yarka ba sharri ba. Ni da niyyar aure
nazo k'ofar gidan nan ba da niyyar yaudara ba." Da sauri Sarah ta kalli Baba tare da fad'in, "Baba kar ka
yarda da maganarsa, fatar bakinsa ne fad'i amma cikin zuciyarsa ba haka bane. Shine sanadiyar duk
abunda ke faruwa dani yanzu. Shine dalilin rugujewar farin cikina. Shine dalilin fasuwar aure na. Baba
wannan dake durk'ushe a gabanka shine uban cikin dake jikina." Ta k'arisa maganar tare da fashewa da
kuka. Baba kuwa ji yayi kamar an d'iga masa dalma a kunne. Rintse idanu yayi cike da k'una a zuciya yace,
"Bawan Allah mai muka maka? Mai d'iyata tayi maka ka tarwatsa mata rayuwa? Kana ganin kayi min adalci
kenan? Ban tab'a b'ata d'iyar wani ba, wannan jarabawace kawai daga mahalicci!" Idanun _Khalil_ gaba
d'aya sun kad'a kun yi jazur ya d'ago tare da kallon Baba yace, "Baba, dan alfarmar ubangiji halittu ka
saurare ni ko da na mintuna biyar kacal. Wallahi, tallahi rantsuwar musulmi ban zo nan da niyyar cutar
kowa ba, zuwa na nan k'ofar gidan nazo ne domin in auri 'yarka." Hakanan baba ya d'an ji _Khalil_ ya
kwanta masa. Kallon Khalil d'in yayi tare da fad'in, "Shiga masallaci kayi sallah, idan an idar kayi sallama zan
aiko Saratu ta shigo da kai har ciki. Bari na shiga nima nayi sallar." Wani sanyi ne ya ziyarci zuciyar _Khalil_,
cike da ladabi yace, "Nagode Baba!" Ya fad'i hakane tare da mik'ewa ya nufi masallacin gaban gidansu
Sarah wanda yake daga hannun hagu, yayin da nasu gidan yake daga dama. Baba ma shigewa yayi Sarah na
biye dashi kanta a k'asa hannunta rik'e da ledar magungunan da _Khalil_ ya bata. Gaba d'aya suna tsakar
gida har da y'ay'ansu. Rabo d'an wajen Na'ima ya kalli Sarah tare da fad'in, "Lami ga Saratun ta dawo daga
wajen saurayin nata." A fusace Sarah tace, "Daga wajen ubanka na dawo." Na'ima mahaifiyarsa ta taso a
fusace tare da fad'in, "Zan ci ubanki a cikin gidan nan wallahi idan kika ce zaki rik'a takurawa d'ana. Babu
ruwana da cikine a jikinki duka zan maki." Harararta Sarah tayi tare da fad'in, "To ai sai ki kashe ni kawai.
Banza kawai." Yunk'urawa Na'ima tayi zata taho wajen Sarah karaf Lami ta rik'e ta tare da fad'in, "Barta!
Yanzu haka duk salon kar ta bamu abunda ta samo ne daga hannun saurayin nata." Juyowa Baba yayi tare
da kallon Sarah yace, "Saratu wuce ciki kinj." Babu musu Sarah ta shige ciki. "Ban gane abunda kake nufi ba
Nuhu anyi yamma da kare!" Ko kallonta Baba bai yi ba ya shige d'aki. "Ahafff! Ba na fad'a maki ba Lami.
Baba fa ya san duk tsiyar da Sarah take shukawa. Raba kud'in suke yi a tsakanin su shiyasa kike ganin yafi
sonta akan mu gaba d'aya." Fad'in Aina'u. "Na ko tabbatar da maganarki yanzu Aina'u. Aikuwa dani suke
zancen." Fad'in Lami tana kwafa. Dai-dai nan Sarah ta kuma fitowa ta nufi fanfo Lami na harararta. Alwala
da d'auro sannan ta kuma komawa d'aki. Tana idar da sallah ta jiyo muryan Baba yana kwad'a kiran
sunanta. Da sauri ta fito ta nufi baranda inda ta ganshi tsaye a bakin k'ofar d'akinsa, "Yi maza gashi can
yana kwad'a sallama, je shigo dashi." Da "To Baba" Sarah ta masa tare da juyawa. Na'ima kuwa kallon
Hassana tayi wacce itama kallon nata take yi sannan gaba d'aya suka mai da dubansu ga Lami wacce tayi
suman tsaye tana kallon Baba cike da mamaki. Mintuna biyu sai ga Sarah tafe, _Khalil_ biye da ita a baya.
Bai kalli kowa a cikinsu ba, don har yanzu bai gama tabbatar da cewar Lami ita ce cikakkiyar mahaifiyarsu
Sarah ba. Dama kuma tuni baba ya shige cikin d'aki. Sallama _Khalil_ yayi tare da shiga don tuni baba ya
amsa tare da bashi damar shiga. Yana shiga Sarah ta bar wajen zata wuce d'aki Lami ta shak'o ta tare da
fad'in, "Dan ubanki shine zaki kai sa wajen mahaifinku! Wato kin fi k'aunarsa dani ko? To wallahi baku isa
ba komai dani za'a ci." Tana gama fad'in haka ta fad'a d'akin babu sallama lokacin _Khalil_ suna k'ara
gaisawa da Baba. "Na rantse da, girman Allah Nuhu baka isa Kaci kud'in nan kai d'aya ba. Ai nice na d'auki
cikin Sarah wata har tara na kuma sha wuya nayi nak'uda na haife ta. Fito da duk wani abu da yaron nan ya
baka ayi kaso." Sai kuma ta mayar da dubanta ga _Khalil_ wanda kansa ke a k'asa tare da fad'in, "Kai kuma
Munafuki................

*_Na rok'e ke ki da girman ubangiji kar ki fitar min da littafi. Kud'in karatu kawai kika biya ba kud'in
mallakar littafi ba. Kiji tausayin marainiyar Allah don wallahi Sana'a na d'aukesa ba nishad'i ba. 🙏_*

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*
"Kai kuma Munafuki! Ya muka yi da kai d'azu?" _Khalil_ ko d'agowa bai yi ba, balle ya kalleta har ya amsa
maganar ta. "Lami wannan wani irin rashin hankaline haka? Yaya zaki shigo min d'aki babu sallama kuma
kin san ina da bak'o! Wannan ai rashin hankaline. Malama fitar min daga d'aki." Harara ta makawa Baba
tare da fad'in, "Ba zan fita ba wallahi. Sai anyi komai a idanuna. Wato daga kai sai y'arka ne zaku rik'a cin
kud'in ko? To wallahi baza ta sab'u ba bindiga a ruwa!" Karkacewa _Khalil_ yayi ya fiddo da rafar kud'i y'an
dubu-dubu ya mik'a mata tare da fad'in, "Gashi. Ni magana nazo muyi da Baba ba wani abu ba." Fizge
kud'in Lami tayi da sauri don a zatonta Baba zai kawo hannu ya warci kud'in tana mai sakin murmushin
ganin tashin farko an bata dubu d'ari. "Yauwa to ko kaifa. Ai wallahi da baka ban kud'in nan ba, Sarah baza
ta k'ara cin ko loma d'aya a cikin gidan nan ba. Kuma duk aikin wahalar gidan nan ita zata rik'a yinsa. Babu
ruwana da tana d'auke da k'aramin ciki." Taga gama fad'in haka ta harari Baba tare da ficewa daga d'akin.
Da idanu _Khalil_ yabi Lami yana mai tabbatar wa kansa ba ita bace mahaifiyarsu Sarah. Baba kuwa kunya
ce ta kama shi kamar k'asa ta tsage ya shige ciki. Da kyar ya iya bud'e baki tare da fad'in, "Dan Allah kayi
hak'uri. Haka halin Lami yake. Sam bata da girma sai na jikinta." Kallon Baba _Khalil_ yayi tare da fad'in,
"Baba wacece ita?" Sai da Baba ya sunkuyar da kai don kunya yake ji ainun ya nuna Lami matsayin matarsa
uwar Y'ay'ansa. A hankali cike da rauni Baba yace, "Matata ce. Uwar y'ay'ana!" Fad'in Baba hawaye na
wanke fuskansa kasancewar mai sauri kuka. "Amma Baba ba ita bace mahaifiyarsu Sarah ko?" Hannu Baba
ya kai ya sharce hawayen idanunsa tare da fad'in, "Ita ce. Wallahi samari ita ce ta haifi duk Y'ay'an dake
cikin gidan nan." Wani irin ajiyar zuciya mai k'arfi _Khalil_ ya saki yana mai jin matsanaicin mamaki. "Kana
mamaki ko? Na san za kayi mamaki Samari. Ba kai kad'ai ba, da yawan mutane basu yarda Lami itace ta
haifi su Sarah sabida irin tarbiyan da tayi masu sakamakon son abun duniya. Ita gaba d'aya kallon
wad'annan yaran take yi matsayin babban jarinta. Sam ta mance su d'in amane Allah ya bata. Na'ima ita ce
y'arta ta fari, sai Nuratu, Lukman, Hassana, Marfu'a, sai auta Aina'u. Duk Y'ay'an Lami ne. Ita ta haife su da
cikinta." Hassana ma y'an biyu ne, d'ayan tun a ciki ya mutu. Da yanzu su takwas ne, shidda mata maza
biyu." Da tausayi _Khalil_ ke kallon Baba tare da fad'in, "To Baba ya aka yi irin haka yake faruwa a cikin
gidanka, amma baka da ta cewa?" Sunkuyar da kai Baba yayi yana mai jin d'aci da k'una sosai cikin
zuciyarsa tare da fad'in, "Lami tafi k'arfi ba Samari! Duk yanda zanyi maka bayani, baza ka gane ba. Amma
Lami ta raina ni, bata ganin mutunci da darajana tun da na samu karayar arziki. Shiyasa y'ay'ana suma suka
taso da d'abi'un da suka ga tana yi min. Guda d'aya ce ta fita zakka. Saratu na tausayina sosai, tana bani
girma, tana kula dani kuma tana gudun b'acin raina. Tana sona sosai kuma duk abunda nace tayi, shi take
yi, idan na hane ta kuma har abada ta bar abun nan kuma baza ta kusance shi ba." Gyara zama _Khalil_
yayi tare da soma fad'in, "Baba da farko dai hak'uri zan soma baka, dan Allah ka yafe min domin na cutar
da kai. Tabbas 'yarka Sarah mutuniyar kirki ce. Kuma duk wani abu da ya faru tsakani da ita, wallahi ba da
son ranta bane. Ban san ta yanda zanyi maka bayani ba Baba. Amma wallahi nima ba mazinaci bane.
Tsautsayine ya afka mana daga ni har ita Saratun. Kuma wallahi ban d'auka sanadiyar abunda ya faru
tsakani da ita ta samu ciki ba. Na jima ina naiman ta, amma ban ganta ba sai yau da Allah ya kawo ta
asibitina. Baba dama ni ina son Sarah, kayi hak'uri ya yafe min kar kace zaka hanani ita saboda wannan abu
da ya faru, ni nayi alk'awarin Sarah na haihuwa sati baza ta zagayo ba sai da aure na a kanta. Tun daga yau
da na san Sarah na d'auke da cikina, d'awainiyarta gaba d'aya ya dawo kai, cinta, shanta da komai nata.
Dan Allah Baba kar ka hana ni Saratu." Shuru Baba yayi yana wani tunani a cikin zuciyarsa. Ya jima bai yi
magana ba, kuma bai d'ago ba. _Khalil_ kuma addu'a kawai yake yi Allah yasa Baba ya amince. Ajiyar
zuciya Baba ya sauke tare da fad'in, "To! Ni bazan ce ban amince ba, matsalar guda d'aya ce. Shin idan kai
ka amince zaka auri Saratu, iyayenka fa? Kai da kanka kaga irin gidan da kake neman aure. Kasan su
wanene y'an uwan Sarah da kuma mahaifiyarsu. Gaba d'aya unguwarnan anyi masu tambari. Karo na biyar
kenan ana fasa auren Saratu saboda bak'in fentin da y'an uwanta suka goga mata. Kud'in goro ake yi masu.
Gani ake yi ita ma Saratun yawon banza take yi. Idan kai ka amince, iyayenka zasu amince ka auri Saratu
ne?" Sai da _Khalil_ ya d'ago suka had'a idanu da Baba sannan ya sunkuyar da kai yace, "Baba mahaifiyata
sam bata da matsala. Mace ce mai fahimta sosai. In Sha Allah baza'a samu matsala da family na ba.
Amincewar ka shine kawai nake buk'ata Baba." Fad'in _Khalil_ amma deep down ga san k'arya yake yi, ya
san tabbas za'a sha daga da Hajiya, duk da yana da yak'inin zata amince musamman idan ta samu labarin
yayiwa Sarah ciki, amma y'an uwan mahaifinsa ne yasan za'a mugu-mugun kai ruwa rana dasu. "To
shikenan, Ubangiji Allah ya shige mana gaba yasa muna da tsawancin kwana." Da "Ameen" _Khalil_ ya
amsa yana mai jin farin ciki a zuciyarsa. "Baka shaida min sunanka ba." Fad'in Baba. "Sunana Ibrahim
Baba." Jinjina kai Baba yayi tare da fad'in, "Ma sha Allah!" _Khalil_ kallon k'afar Baba yayi tare da fad'in,
"Baba ka dad'e kana ciwon k'afar nan ne?" Kallon k'afar Baba yayi tare da fad'in, "Shekaru talatin da biyu
kenan ina fama da ciwon nan, tun Na'ima na da shakara d'aya a duniya" da mamaki _Khalil_ ya kalli Baba
tare da fad'in, "Kuma baka je asibiti ba?" Murmushin Baba yayi tare da fad'in, "A kan ciwon k'afar nan sai
da na rasa komai nawa. Da wannan gidan kawai na tsira. Ai da abun yafi muni ma. A hankali Allah ke ta
kawo sauk'in." K'urawa k'afar idanu yayi kamun yace, "Allah ya baka lafiya Baba. Zan rik'a zuwa lokacin
bayan lokacin. Sannan in Sha Allah zan zo na d'auke zuwa asibitina a duba k'afar sosai." Ya fad'i hakane
tare da saka hannu a aljihu ya fiddo rafar kud'i y'an dubu-dubu guda biyu ya ajiye a kan yaloluwar katifar
Baba. "Zo-zo-zo, d'auke kud'inka dan girman Allah. Wanda ka bawa Lami ma ya isa haka." D'ukawa _Khalil_
yayi tare da fad'in, "Baba dan girman ubangijin kada ka k'i karb'an kud'in nan. Ka d'auke ni matsayin dank'a
na cikinka. Nasan baza ka k'i karb'an kud'in hannun dank'a ba. Kayi min wannan alfarmar Baba." Ajiyar
zuciya Baba yayi tare da fad'in, "To d'auke daya ka bar d'aya dan Allah Ibrahim." Hannu _Khalil_ ya kai ya
d'auka tare da fad'in, "Nagode da karamcin ka Baba. Allah ya saka da alkhairi. Sai na sake zuwa." D'aga
masa hannu Baba yayi tare da fad'in, "To d'ana nagode nima. Allah yayi albarka." Da ameen ya amsa tare
da fitowa daga d'akin. Gaba d'ayansu suna tsatstsaye a tsakar gidan suna kallon k'ofar d'akin Baban, sun
k'osa ya fito ya basu nasu rabon don Lami tace kwandala baza ta basu ba. Yana fitowa suka saki murmushi
tare da fad'in, "K'aninmu har an fito." Babu yabo babu fallasa yace "Eh" tare da mik'a masu kud'i da Baba
ya sashi ya d'auki d'aya tare da fad'in, "Ku raba!" Yana fad'in haka ya fita. Da sauri Lami ta bishi a baya, sai
da ya kai k'ofa sannan ya tsaya tare da juyowa, sam baya ganin girmanta matsayinta na surukarsa. Fuska ya
tsuke sosai tare da fad'in, "Lafiya?" Murmushin tayi tare da kwance zanintata sake d'aurawa sannan tace,
"Dama maganar abincin Sarah ne. Dama na fad'a maka tun farko, ni ban ciyar da y'ay'ana kuma in ciyar da
nasu Y'ay'an. Kaga ai yanzu Saratu tana d'auke ne da cikinka, dole ne duk wani abincin da zata ci da duk
wani abu da zata nema kai zaka kawo kud'i a sayo. Ko baka duba list d'in da na baka bane?" Fuskan nan a
tsuke _Khalil_ yace, "Ban duba ba, amma zuwa anjima za'a kawo komai. Sannan a kula da ita sosai. Duk
abunda take buk'ata a kira ni a waya a sanar min. Kar a bari ta sha wani magani idan ba wanda na kawo ba.
Idan wani waje nayi mata ciwo, immediately a kira ni a sanar min. Sannan abu na gaba, idan wani abu ya
samu ciki na, ba zan kyale kowa ba. Ki turo min ita idan kin koma." Fad'in _Khalil_ tare da bud'e gidan ya
fita. Don wani irin haushi da tsanar Lamin yake ji. Sam bata cancanci zama surukarsa ba. Lami kuwa tab'e
baki tayi tare bud'e gidan ta kallesa tsaye jikin k'arfen gidan mak'otansu, mik'a masa wayarta tayi kirar Itel
tace, "Saka min number d'inka don ban da shi." Karb'an wayar yayi tare da danna digits d'insa ya mik'a
mata. Ita kuma ta amsa tare da juyawa ta koma cikin gidan. D'akin su Sarah ta shiga, zaune ta same ta a
k'asa hannunta rik'e da kwalbar fantan da Aina'u ta sayo mata d'azu kamun su tafi asibiti. Da fantan ta iya
shan maganin da _Khalil_ d'in ya bata. Don ruwa bai wuce mak'ogoronta. "Sai ki tashi ki fita yana jiranki a
waje." Fad'in Lami tana kallon Sarah dake maida numfashi. "Waye?" Fad'in Sarah tana kallon Lami. "Ubanki
ne. Idan kin fita zaki gansa." Lami ta fad'i tare da juyawa ta bar d'akin. Sarah kuwa turo baki tayi tare da
mik'ewa ta saka hijab d'inta da ta cire ta fita. Yana nan inda Lami ta barsa. Tana bud'e k'ofar suka yi ido
biyu dashi. Kwafa yayi tare da fad'in, "Na d'auka ai baza ki fito ba." A shagwab'e tace, "To wai ni mai zanyi
maka ne? Dan Allah ka fita daga harkata." Gyara tsayuwa yayi tare da fad'in, "Zaki fara shagwab'an naki
ko? Ki dai kiyayi kan ki, tom! Dama zan fad'a miki Baba ya riga ya damk'a min ke. Don haka ke tawa ce.
Kuma sannan ki kular min da kanki da kuma babyn mu. Mai kike so in kawo miki a idan zan zo gobe?" Kuka
ta saki tare da fad'in, "Wallahi kar ka k'ara zuwa mana gida. Ni bana son ganinka. Kuma babu abunda zai
saka na aure ka. Ina haihuwa zan baka abunda na haifa maka, shikenan mun rabu!" D'age gira yayi tare da
fad'in, "Za dai ki haifa min ko? In dai zaki haifa min baby d'in ai shikenan. Sai muyi deal ni dake. Idan kin
amince, kamar yanda kika ce d'in, kina haihuwa zan karb'i d'an nawa shikenan kowa sai ya kama gabansa."
Da sauri Sarah tace, "Eh na amince!" Waro idanu _Khalil_ yayi tare da fad'in, "Tun kamun ma kiji deal d'in
har kin amince. Ok, to shikenan. Na farko, duk lokacin da nazo, zaki fito, kar fa kiyi tunanin don in ganki zan
zo, sam baby na nazo gani. Sannan idan na kira ki a waya, dole ki d'auka, shima ba don inji muryanki bane,
lafiya babyna zan ji. Sannan duk abunda kike son ci zaki fad'a min, shima fa kar kiyi tunanin ke zan sayo
mawa, a'a sam baby na na sayo mawa don nasan shi ke saka ki kwad'ayin. And dole ki rik'a shan magani
tare da kiyaye duk wani abun da zai damu cikin jikin ki, sannan idan lokacin zuwa asibiti yayi, zaki je dole
domin a duba min baby na. Idan kin amince da wannan sharad'in, bayan kin haihu ni da kaina zan
shaidawa Baba na janye maganar auren ki, amma kuma idan baki harda ba, duk wad'annan abunda na
lissafo dole ayi su, kuma a k'arshe sai na aure ki dole." Zaro idanu Sarah tayi tare da fad'in, "Kuma duka
wad'annan sharad'in sai na cika?" D'aga k'afada tare da tab'e baki _Khalil_ yayi tare da fad'in, "If you wish,
ki karya d'aya daga ciki. Amma ki sani, karya d'aya daga ciki yana nufin rushe deal d'in gaba d'aya. Kuma
kin san dai abunda zai faru." Marairaicewa tayi tare da fad'in, "To ta yaya zaka gane idan ina son wani abu,
kuma nak'i in kira in fad'a maka? Kuma misali idan ka kira wayar bana kusa fa?" Dariya ne ya kama
_Khalil_, amma sai yayi murmushi kawai tare da fad'in, "Zan yi connecting CCTV camera ta inda zai r'ika
hasko min duk wani motsin ki, idan ma bakya kusa na kira waya, zan sani, idan kuma da gangan ne, shima
zan sani." Turo baki tayi tare da fad'in, "To amma baza a rik'a dad'ewa ba ko idan ka kira wayar?" D'aga kai
sama yayi tare da fad'in, "Eh to, sai yanda babyn cikin ko yayi suggesting." Shuru tayi tana tunani, can
kuma tace, "To amma kayi alk'awari idan na haihun zaka amshi babynka ka tafi baza ka sake dawowa ba?"
B'ata rai yayi tare da fad'in, "Ohh wato baki ma yarda dani ba ko? Wato ga k'atoton mak'aryaci ko? To na
ma fasa deal d'in. Zan yi duk abunda nace da k'arfi da yaji." Da sauri har da d'aga hannu Sarah tace, "A'a
dan Allah kayi hak'uri ba haka nake nufi ba. Na amince da deal d'in." Wani mugun dariya ne ya kama shi
cikin zuciyarsa. K'are mata kallo yayi ya tabbatar da yarinya ce ita. "Shekarunki nawa?" Ya tambayeta.
Kanta a k'asa tace, "I'm 21years old." Sai da ya kuma kallonta daga sama har k'asa sannan yace, "I see.
Yanzu to ki shiga gida. Deal d'in mu zai fara daga yau. Bye ki kular min da kanki." Sarah bata san lokacin da
tace, "Bye" ba har da d'aga masa hannu. Sai bayan ta shiga cikin gida sai haushin kanta ya kamata. _Khalil_
kai tsaye gida ya nufa, cikin mota sai sak'e-sak'e yake yi na yanda zai tari Hajiya da maganar Sarah. Ya san
dai akwai k'ura. Shi yafi jin nata ma akan nasu Uncles d'insa. Don idan har ta amince, to shafawa idanunsa
toka zai yi. Ai ba wani zai zauna masa da matar ba. Beside shi ya lalata masu yarinya don haka shi zai d'auki
abunsa. Horn yayi mai gadi ya wangale masa gate ya shigo. Sai da tayi parking mai kyau sannan ya fito
daga motar. Gani Honda anyi parking d'insa daga gefen motarsa, ya saki siririn tsaki don ya shaida ko su
wanene suka zo gidan. Kamar ba zai shiga ba, sai kuma ya doshi hanyar cikin gida amma ta baya ta yanda
babu wanda zai fahimci ya dawo gidan. Sai dai abunda bai sani ba, tun shigowarsa Uncle Ameeru ya gansa,
don shi ya fito harabar gidan domin amsa waya. Kuma yana kallonsa lokacin da yabi ta baya ya shige cikin
gidan zuwa d'akinsa. A fusace Uncle Ameeru ya shiga ciki tare da Fad'in, "Bilkisu! Bilkisu!! Wallahi babu
abunda za muce maki sai Allah ya isa! Yanzu tsabar yanda baki nunawa _Ibrahim_ mahimmancin mu ba
matsayinmu na k'annai da yayyin mahaifinsa, shine zai dawo cikin gidan na don bai son ya ganmu sai ya
zagaya ta baya ya shige ciki. Na san ma kece zaki kira sa a waya ki fad'a masa mun zo don ya doje mana.
Wallahi Bilkisu ki kiyayi kanki damu. Kuma yanzu-yanzu ki tashi ki wuce ki kira mana shi dan ubansa."
Hajiya da ranta yayi mugun b'aci da abunda _Khalil_ yayi, mik'ewa tayi tare da fad'in, "Kuyi hak'uri dan
Allah. Bari na kira sa." Tana gama fad'in haka ta nufi wani corridor da zai sadata da matattakar da zai kai ta
d'akin _Khalil_ d'in. _Khalil_ na shiga d'aki ya zauna bakin gado tare da kai hannu ya jawo side drawer ya
d'auko *_MASTIKA GUM_* ya jefa a baki ya hau tauna yana mai kwanciya rigingine tare da saka
hannayensa biyu ya tallabo kansa yana tunanin hanyar da zai bi yayiwa Hajiya bayanin Sarah da kuma cikin
dake jikinta. Ya san Hajiya sai ta kusa kashesa da masifa. Don da ana aro baki, sai ta aro tabbas. Da ace
mahaifinsa nada rai ne, to da worse kenan, don ko da ace zai amince ayi auren, to sai ya kullesa a prison ko
da na sati biyu ne tukun. He's father *_Nurudden Muhammad Ibrahim_* was the chief justice of Kaduna
state before he died. Sam baya d'aukar raini da rashin adalci. He raised all his children very well. "I really
miss you papa. I miss everything about you daddy. Allah ya jik'anka da rahama ya gafarta maka." Yana
fad'in haka ya lumshe idanu siraran hawaye na zubowa daga idanunsa. Dai-dai nan jai ana danna doorbell
da k'arfi. Da sauri ya tashi zaune yana kallon k'ofar. Wani abu ya danna daga gefen gadonsa, sai ga hoton
Hajiya b'aro-b'aro ajikin wani screen dake saman k'ofarsa. Kai baza ka tab'a ganin screen d'in ba sai idan
shi ya danna wannan madannin. Da sauri ya sauka daga kan gadon tare da isa wajen k'ofar ya bud'e. Ido
hud'u suka yi da Hajiya ranta a mugun b'ace. "Ai sai ka fito tun da kai a rayuwarwa kafi so kaga raina yana
ta b'aci." Tana gama fad'in haka ta juya tabi corridor d'in da ta biyo. Shima bayanta yabi don yasan dama
tatsuniyar gizo bata wuce ta k'ok'i. Fuska babu yabo babu fallasa ya isa parlor. A zazzaune ya taras da gaba
dayansu su biyar k'annai da yayyin mahaifinsa. Zama yayi a kan carpet tare da fad'in, "Barkan ku da zuwa
Uncles." Uncle Ameeru ya kallesa tare da fad'in, "Kalle ni, ungo nan!" Ya fad'i haka tare da yi masa
dak'uwa............

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

[30/09, 7:11 PM] Rahamanatu: Tab'e baki _Khalil_ yayi tare da kau da kai dai-dai lokacin da magensa ta
fito daga k'atoton kitchen d'in dake parlourn, "Mus-mus-mus, Madhuuuu." Fad'in _Khalil_ yana kiran
magen tare da bud'e hannunsa. Da mugun gudu katuwar farar magen mai ratsin ash, baki da kuma brown
a jiki ta nufosa tare da hawa kansa, shi kuma ya shiga shafa jikinta zuwa bindinta. "Inna lillahi wa'inna
ilaihir raju'un!" Da sauri _Khalil_ ya kalli Uncle Ridwan dake rafga salatin tare da fad'in, "Uncle mutuwa aka
yi?" A fusace Uncle Ridwan d'in yace, "Ubanka ne ya mutu, d'an iskan yaro!" Wani murmushi mai k'ona
zuciyar wanda akai wa _Khalil_ ya saki tare da fad'in, "Shekaru takwas kenan da mutuwarsa. Allah ya
jik'ansa da rahama." Uncle Ridwan kallon Uncle Ameeru da sauran Uncles d'in dake parlourn yayi tare da
fad'in, "Kuna jin maganar da yaron nan yake fad'a min ko!" Uncle Shamsu yace, "Ai ina ganin wallahi gab
Ibrahim yake da ya fara zaginmu. Kuma ka sani idan har baka mutuntamu ba, uban kak'i mutuntawa. Don
Nura yayi min biyayya iya biyayya." Kallon Uncle Shamsu _Khalil_ d'in yayi tare da fad'in, "Uncle kayi
hak'uri. Ni har abada babu wannan ranar da ni zan iya bud'e baki na zage ku. Ai ku d'in tamkar Baba haka
kuke a waje na." Harara Uncle Ameeru ya jife sa dashi tare da fad'in, "Da abunda ka fad'i da gaske kake,
babu yanda za'ayi mu zab'a maka mata amma ka watsa mana k'asa a idanu. Koda yake ba laifin ka bane,
laifin uwarka ce da take d'aure maka, idan ba haka ba, kai har ka isa mu fad'i abu ka saka k'afa ka shure. Ai
bamu yi tunanin ko musaka maka kawo maka matsayin mata zaka k'i amsa ba. To yanzu dai ka saurare mu
da kyau da kyau kaji, wata d'aya cur muka baka ka fiddo matar aure don mun gaji da zuba maka idanu haka
nan. Sai dai ko idan bamu sani ba ka ajiye dadiro a wani wajen. Don namiji mai k'arfi a jika kamar kai ga
kud'i amma ace har yanzu baka ajiye iyai ba, ai abun dubawa ne. To wallahi idan wata d'aya ya cika baka
fiddo matar aure ba, to ka rubuta ka ajiye Nina zamu baka kuma ba sai mun shawarceka ba. Don mun
yarda da tarbiyanta kuma y'ar dangi ce ba bare ba. Kowa ya san Nina y'a ce a wajen d'an uwanmu Zayyanu
gashi nan. Don haka, dabara ya rage ga mai shiga rijiya. Wata d'aya babu ragi babu k'ari. Ku tashi mu tafi
mun gama isar da sak'on mu, kuma sannan muna buk'atar naira miliyan hamsin da bakwai. Kamun mu isa
gida, ina son jin alert." Wani irin d'ago idanu _Khalil_ yayi tare da fad'in, "Shi kuma na menene wannan
uncle?" Hajiya sai hararar _Khalil_ take yi, shikuma yana kallonta ta gefen ido amma yayi kamar bai gani
ba. "nNa ubanka ne! Ke har ka isa mu tambayi kud'i sai mun fad'a maka abunda za muyi dashi!" Wannan
shegen murmushi _Khalil_ ya sake yi tare da fad'in, "Ai naga sati biyu da suka wuce na tura maka 60million
wanda kace za'a kai 30m gidan marayu, sauran 30m d'in kuma zaku cire 15m ku rabawa gajiyayyu sauran
15m d'in kuma zaku gina masallaci da madaidaicin makarantar Islamiyya. To yanzu kuma ban san mai za
kuyi da kud'i masu yawa har 57million ba." Ko kamun Uncles d'in suyi magana Hajiya ta dakawa _Khalil_
wani irin tsawa tare da fad'in, "Wallahi _Ibrahim_ ka kuma yarda iyayenka suka fad'a ka fad'a zan mugu-
mugun sab'a maka. Kuma umarni na baka yanzu-yanzun nan ka tura masu kud'in nan. Ko miliyan d'ari suka
ce ka basu, ka tura yanzu nan." Tsaki uncle Ridwan yayi tare da fad'in, "Don kin ga idanun mu shine zaki
rik'a acting kamar ta kirki? To ba million d'ari muka buk'ata ba, miliyan hamsin da bakwai muke buk'ata.
Kuma dole ne a tura, don kud'in d'an uwanmu ne ake handama da babakere a kai." Hajiya dariya ma
maganar ya bata, don a bayyane yake suke handama da babakere akan dukiyar marayu. Kuma wuta suke
ciwa kansu. Don bada dukiyar gado suka dogaro ita da Y'ay'anta ba, gaba d'aya Y'ay'anta babu wanda bashi
da na kansa. _Khalil_ kuwa a take ya fiddo wayarsa yayi transfer d'in kud'in zuwa account d'in uncle
Shamsu tare da sauke Madhuu dake jikinsa don ransa yayi mugun b'aci ya wuce d'akinsa. Da kallo dukansu
suka bisa dashi tare da fad'in, "Shege mai halin yahudawa. Ji yanda yake taunar cingam kamar wani
karuwa. Shiyasa fa tura y'ay'a k'asashen waje sam bai yi ba, don a nan ne y'ay'a suke koyo mummunar
d'abi'u da taurin kai. Don su komai sai kaji ana fad'in human right. A can fa ko uwa ce ta daki d'anta, d'an
yana da damar kai ta kotu domin a naima masa hak'k'i! Kai Allah wadaran naka ya lalace." Fad'in uncle
Ameeru. Uffan Hajiya bata k'are cewa ba har suka k'are fitinarsu suka fice daga gidan. _Khalil_ yana shiga
d'aki ya cire rigar jikinsa ya wurgar a k'asa tare da saka k'afa tattaka kamun yayi ball da ita sannan ya saka
hannu ya chakud'a gashin kansa kamar zai yi hauka. K'ugu ya rik'e yana wani irin huci. K'arar k'ofar d'akinsa
ne ya dawo dashi tunaninsa tare da k'arisawa ya bud'e k'ofar. Kaucewa yayi ya bata hanya ta shigo sannan
ya kulle k'ofar tare da danna wani madanni glass ya zuge. Wani irin mahaukatan kayan saka suka bayyana a
jikin hanga, wasu kuma a ninke a cikin loka. Hannu ya kai ya zaro wata shirt mai botura sannan ya danna
madannin glass d'in ya zuge. Saka shirt d'in yayi sannan yayi buttoning tare da zauna a k'asa dai-dai
k'afafunta Hajiya tare da d'aura kansa a kan k'afarta sannan ya soma magana, "Hajiya bak........!" D'aura
hannunta tayi a kan leb'ansa tare da fad'in, "Ba komai ake magana akai ba _Khalilullah_, wani abun kana
gani k'iri-k'iri ana cutarka, amma sai ka kau da kai kamar Allah ya amsar maka hak'k'inka. _Khalilullah_
wad'annan mutanan y'an uwan mahaifinka ne. Idan har ka raina su kamar mahaifinka ka raina. Don Allah
ka rik'a kiyaye abunda zaka jawo min magana. Baka ganin d'an uwanka Abdul-Hakeem, ko ni ta kansu bai
yi, sabgar gabansa kawai ya saka a gaba. Kai ma da zaka daure ka cire idanu a kansu, da ka taimaka min."
Kamar ba zai ce komai ba, sai kuma ya d'ago tare da fad'in, "Hajiya kin fi kowa sanin su Uncle sunfi saka
min idanu akan Yaya Abdul-Hakeem. Kina jin fa abunda suke cewa sai kace a kansu nake, wai wata guda
suka bani in nemo matar aure ko kuma su aura min Nina, wallahi da na auri yarinyar nan, gwara na mutu
babu aure. Lokacin da Papa yake da rai, wani abune basu yi mana ba, shi kansa papa ba kyalesa suka yi ba.
Ko shishshige masan da suke yi suna had'a mu fad'a dashi, au duk sabida dukiya ne. To yanzu dai gashi ya
mutu ya bar masu duniya, but still they're after his money. Ni wallahi Hajiya ban dogara da kud'in Papa ba
ke kin sani, kud'in da na tara a yanzu haka, ko da babu ko sisi daga cikin kud'in Papa, zan iya rik'e gidan nan
kaf har dasu kansu Uncles d'in, ba tare da na girgiza ba. Kuma wallahi Hajiya duk kud'in da nake bawa su
Uncles, a cikin dukiyata nake cirewa sabida ba zan iya tab'a kud'in marayu ba. Idan har su basu da wannan
imanin da tsoran Allah, to ni ina da shi. Kud'in nan ba nawa bane ni d'aya. Ko yaya Musaddiq da yake cewa
ya yafe, ai wallahi bai yafu ba, don hakkinsa ne." Ajiyar zuciya Hajiya ta sauke tare da fad'in, "Yanzu
_Khalilullah_ ashe kud'i gare ka haka? Kana nufin duk mak'udan kud'ad'en nan da kake fitarwa kana
turawa iyayenka, a cikin guminka ne?" Murmushi _Khalil_ yayi tare da fad'in, "Hajiya ai kece baki bani
damar yi maki bayani akan dukiya ta. Da na fara maki magana kike dakatar dani. Kar ki manta asibitoci na
bakwai a nan Nigera, akwai _Khalilullah Specialist hospital_ anan Kaduna har guda uku, akwai biyu a
Abuja, d'aya a Jos, sannan akwai d'aya a Kano. Kuma ina da hannun jari a *_WAZIRI GOLD STUCK
COMPANY LIMITED_*, kuma bayan CEO d'in nine mai babban share a ciki. Sannan ga 400houses da na gina
a millennium city. Kin ga kuwa ai d'an naki matashin multibillionaire. *_THE YOUNG BILLIONAIRE_*" Ya
k'arisa maganar yana dariya. "Duk nasan dasu, amma ban tab'a d'auka kana samun mahaukatan kud'i haka
ba. Allah ya cigaba da saka maka albarka a kasuwancinka. Dukanku gaba d'aya." Da "Ameen" _Khalil_ ya
amsa. Kallonsa ta kuma yi with very serious face tare da fad'in, " _Khalilullah_ dagaske nake yi, wannan
karan akan maganar aure ina bayan iyayenka, gaskiya nima na gaji da ganinka haka babu matar aure.
Maganar da babanka yayi d'azu bai min dad'i ba ko kad'an. Ni nasan tarbiyan da na bawa y'ay'ana. Babu
yanda za'ayi d'ana ya ajiye dadiro a wani wajen. Kullum cikin addu'a nake masu akan Allah ya kare ku daga
sharri Zina, da duk wani aikin alfasha. Dan Allah _Khalil_ kayi k'ok'arin ka fitar da matar aure kamun
wa'adin da suka baka ya cika." Hannunta ya kama tare da fad'in, "Hajiya ki kwantar da hankalinki, surukarki
na zuwa nan kusa, na riga na fitar da matar aure, lokaci kawai nake jira. Ki taya ni da addu'a Hajiya. Amma
dan alfarmar ubangiji ina so Hajiya, duk abunda za kiji, ko kuma zaki gani nan gaba a kaina, kar kiyi fushi
dani, domin fushinki a gare ni masifa ce. Wallahi ban tab'a yar da tarbiyan da kika d'ora ni a kai ba. Ki ajiye
batun wa'adin da Uncles suka bani, ki dai taya ni da addu'a kawai. Ai ba a kansu nake ba, kuma babu
wanda ya biya kud'in makaranta a cikinsu balle ya naimo min aikin yi. Babu wanda ya isa yayi min auren
dole." Mik'ewa Hajiya tayi tare da fad'in, "Naji _Khalilullah_, amma ko ba dan su ba, kayi danni don ina son
ganin y'ay'anka kamun rai yayi halinsa. Allah yayi maka albarka." Har k'ofa ya rakata yana fad'in, "Ameen
Hajiyata. Ina son ki." Hajiya na ficewa ya rufe k'ofar tare da zama dab'as a kan gadon yana tunanin kurar
dake gabansa. Shi sam ba ta Uncles d'insa yake yi ba, abunda ya sani shine babu uban da ya isa yayi masa
auren dole. Wayarsa da ya fara ringing ya kalla, ganin wacce ke kira sai da ya waro idanu kamun ya mik'a
hannu ya d'auki wayar, kallon screen d'in ya dunga yi har kiran ya tsinke sannan yabi kiran, ringing uku ta
d'aga tare da fad'in, "Assalamu alaikum!" Sai da ya lumshe idanu jin sautin muryanta a dodon kunnansa.
Kwanciya yayi flat yana kallon sama ba tare da yace komai ba. "Hello! Hello!! Ba'a ji nane? Yi magana
mana. Naga miss call ne d'azu wajajen k'arfe sha d'aya na safe. Hello!" Yana jin ta amma yak'i yin magana.
"Ina ga network ne." Ta fad'i tare da yanke wayar. Cire wayar yayi daga kunnansa ya tsurawa screen d'in
idanu kamar Saran yake gani ta ciki. Wani murmushi mai sauti ya kuma saki tare da fad'in, "Wato sai yanzu
ta d'auko wayar taga miss calls d'insa kenan. Na tabbata da ta san nine, baza ta kira ba." Ya fad'i hakane
tare da ajiye wayar a gefe jin ana kwad'a kiran sallar la'asar a masallacin dake cikin gidan. Bayi ya fad'a tare
da d'auro alwala sannan ya fito daga d'akin, a parlor ya taras da Saude sai bala'i takewa magensa,
"Shegiyar kuliya kin san dai ban k'aunar ki rab'o jikina, amma sabida naiman jidali da masifa sai ki rik'a
rab'ata kina sunsunani. Kai wannan mage da muni kike. Ni tafi can dan Allah." Ta fad'i hakan tare da yin
amfani da sandar hannunta ta tura magen baya. "Ke! Ke!! Ke!!! Kul kika kuma tab'a min mage. Madhubala
wutar kyau d'in ce kike cewa mummuna? To ya take dake kenan da uban kachakoren hak'ora a gaba? Kin fi
kowa sanin takanas na hau jirgi har Paris na taho da Madhu. Ke ko a idanu ai bata yi maki kama da ordinary
maguna ba. To Allah Saude ki kiyayi kanki dani a cikin gidan nan. Kin san Allah, saboda Madhu ina iyawa
Hajiya pampo ta mayar dake k'auye ko kuma billahi in cire wad'annan shegun hakoran da suka fito suke
hana bakinki rufuwa. "Wallahi halittar Allah. Yanzu kai yaya _Khalif_ kana iya halittar ko k'umba ne da kake
kushe halittata. Maza hau sama ka gyarawa rana tsayuwarta. Kuma bari in fad'a maka kagi, baza ka tab'a
samun kyakkwar mace irina ba." Dafe k'irji _Khalil_ yayi tare da fad'in, "In mutu maza su kai ni ba mata ba.
Yanzu ace an kawo min mata mai irin muninki, ai nasan wabillahi ba k'aramin zunubi na aikata ba. Ni bari
ma na wuce masallaci gashi can za'a tada salla kar in rasa Jam'i wajen sauraron shirmen ki." Yana gama
fad'in haka ya fice da sauri don sallar za'a tada. Laure kuwa isa gaban wani madubi dake jikin bango ma
shape d'in heart tayi tare da kallonta kanta tana jujjuyawa, "Wallahi kyakkyawa nike, dube ni fa! Na tsani
kyau wallahi. Abun d'aya ne yayi mani cikas, wad'annan hakwaran da suka turo." Ta fad'i tana mai bud'e
baki tare da fiddo hakwaran waje. "Miyauuuuuoou!" Magen tace tare da mimmikewa kamar dai irin ta
firgita d'in nan. "Kuga min shegiya. Ba dai hak'oran nau bane suka tsorata ki!" "Ai ko ni na tsorata Laure!"
Aunty Maryam ta fad'i tana mai k'arisa shigowa d'akin. "Kai aunty Maryama, menene abun tsoron a
jikina." Kallon mopan hannunta tayi tare da fad'in, "Yi abunda ke gabanki Laure. Ke kullum idan aka saka ki
aiki, sai kin tsaya shirme. Aiko tabbas zamu had'a kai ni da _Khalil_ cikin gidan nan a mai da ki k'auye tunda
ba aikin kike son yi ba, gwara a kawo wacce za tayi." Turo baki Laure tayi tare da fad'in, "Allah kana gani
kuma kana ji, ka shiga tsakanin nagari da mugu. Ni da Hajiya in Sha maka Allahu mutuwa ce zata raba mu!"
Waro idanu aunty Maryam tayi tare da fad'in, "Har gidan mijin tare za kuje? Ko kuma da Sadi mai gadi za'a
had'a ku aure sai ku tare a wancen d'akin nasa na bakin gate, kin ga kenan mutuwar ce zata raba ku da
Hajiyar." Sai da Laure ta saki mopa ya fad'i sannan ta shiga fad'in, "Tuf-tuf-tuf! Allah kar ya biye bakinki
aunty Maryam. Yanda nake kyakkyawar nan, ai sai kyakkyawa iri na. Kin ganni nan, idan ba irin samarin
nan da ake nunawa a bullihud (Bollywood) ba na k'asar indiya, to bafa zan auri kowa ba. Ni da cewa nayi
Sulamankan (Salman Khan) zan aura, amma sai na samu labari ashe bala'in zuciya ne dashi, kuma duk
shekarun nan nasa bai tab'a aure ba. Kuma yanzu yayi man tsufa, sharakan kuwa, Hajiya shaida ce, har
lambata aka basa domin ya shawo kai na, amma na nuna sam ni ban amince ba, don ni ba zan tab'a auren
mai mata ba." Ta k'arisa maganar tare da kai hannu ta d'auki mopa, aunty Maryam kuwa dariya ta kwashe
dashi tare da fad'in, "Shi sharakan (Sharukh khan) d'in ne ya samo lambar taki yake ta bibiyarki akan ki
taimaka masa?" Sai da Laure ta juya idanu sannan tace, "Kwarai kuwa!" Dariya aunty Maryam ta kwashe
dashi kamun tabi corridor d'in da zai sadata da d'akin Hajiya. Khalil kuwa yana fitowa daga masallaci, ya
dawo cikin gida ya wuce d'akinsa kai tsaye don lokacin abokiyar fad'an nasa ta gama mopping d'in ta bar
parlourn. Wanka ya sake yi ya shirya cikin shadda gezna kalar emerald green. Kallon kansa yayi a madubi
ya saki murmushi ganin yanda kayan suka yi masa matuk'ar kyau. Links ya d'auko a cikin wani madaidaicin
glass box ya saka a hannun nasa sannan ya d'au cumb ya taje sumansa da yake shek'i. Don _Khalil_ d'an
gayu ne na bugawa a jarida. Turarensa ya d'auko _Imperial Majesty_ ya fesa kad'an sannan ya mayar ya
d'auko oud shima kad'an ya saka ya mayar, ya kuma d'auko _Boadicea The Victorious_ ya kuma fesawa. Sai
gaba d'aya turaren uku suka bada wani irin fitinannan k'amshi mai sanyaya zuciya. Half cover shoe na
_Roberto Cavalli_ ya d'auko na kalar emerald green ya saka sannan ya d'auki key d'in motarsa da waya ya
fito. Gaba d'aya ya same su su hud'u a parlor, Hajiya, aunty Maryam da y'arta Maimoon sai abokiyar
fad'arsa Laure. Tun kamun ya k'ariso parlourn k'amshin turarensa ya sanar da zuwansa. Laure ce ta soma
magana, "Dan Allah yaya _Khalif_ ka taimaka min ko a d'an kwalbar fiya-fiya ka d'an d'iga min turaren nan
naka mai saka mutum cikin nishad'i yayin da ya shak'i k'amshinsa." Harararta yayi tare da fad'in, "Sai dai ki
mutu, mayya kawai!" Aunty Maryam kuwa cewa tayi, "Uhm, wannan irin kwalliya haka? Ko dai nayi k'anwa
ne?" Dariya _Khalil_ yayi tare da fad'in, "Very soon aunty. Moon har an dawo daga school d'in?" Ya k'arisa
maganar yana kallon d'iyar aunty Maryam. "Uncle na dawo tun d'azu. Ai yau Thursday babu Islamiyya."
Hannu ya saka cikin aljihu tare da fiddo _MASTIKA GUM_ ya mik'a mata d'aya shima ya b'are d'aya ya saka
a baki. Da harara Hajiya ta bishi tana mai sakin tsaki tare da fad'in, "Ita ma kana so ka koya mata d'abi'ar
banzan ko? Ka kiyaye ni _Khalilullah!_ Tom." Dariya yayi tare da fad'in, "Allah huci zuciyar Ummi ne. Daga
yau ba zan rasa k'ara bata ba, nayi alk'awarin." Remote ta jehosa dashi yayi saurin kaucewa yana dariya.
Laure kuwa cewa tayi, "To ya _Khalif_ tunda ban samu turaren ba, nima a bani dank'on in tauna?" Da sauri
ya kalleta tare da fad'in, "Da wasu hak'oran?" Murgud'a baki tayi tare da fad'in, "Wallahi halittar Allah.
Hajiya kina dai jinsa ko?" Harararta Hajiyar tayi tare da fad'in, "Allah ubangiji ya k'ara. Ai kina jin ina
maganar banso ana cin dank'on amma saboda kin raina ni shine kike tambaya a baki. Wato idan mutuwa
zanyi in mutu. Allah ya k'ara." Dariya aunty Maryam da _Khalil_ suke yi har da Maimoon. Ita kuwa Laure
sosai ta shak'a tare da turo baki gaba. "Hajiya sai na dawo!" Fad'in _Khalil_. "A dawo lafiya." Ta fad'i.
"Uncle a taho min da tsaraba." Moon ta fad'i tana mai d'ago masa hannu, shima hannun ya d'aga mata
tare da fad'in, "In sha Allah" sannan ya fice ya nufi parking lot ya danna key wata had'ad'd'iyar mota k'irar
*_Mercedes-Benz GLB-Class_* fara k'al tayi k'ara. Bud'e murfin motar yayi tare da yin reverse dama tuni
driver ya bud'e masa gate ya fice daga gidan. Yana hawa titi ya fiddo wayarsa yayi connecting da redion
motar ya kunna wak'a ya shiga bin wak'ar,
Oh oh oh oh oh oh oh oh oh oh, oh oh oh oh oh.
Oh oh oh oh oh oh oh oh oh oh, oh oh oh oh oh.
Give me freedom,
Give me fire,
Give me reason,
Take me higher.
See the champions
Take the field now.
Unify us,
Make us feel proud.
In the streets our
Heads are liftin'
As we lose our
Inhibition.
Celebration.
It surrounds us.
Every nation.
All around us.
Staying forever young,
Singin' songs underneath the sun.
Let's rejoice in the beautiful game.
And together at the end of the day,
We all say,
When I get older,
I will be stronger,
They'll call me "Freedom",
Just like a wavin' flag.
When I get older,
I will be stronger,
They'll call me "Freedom",
Just like a wavin' flag.
So, wave your flag.
Now, wave your flag.
Now, wave your flag. Dai-dai wani dank'areran supermarket ya tsaya tare da shiga ciki yayi parking motar
sannan ya fito, yana shiga ciki ya nufi wajen foodstuff. Tashin farko buhun shinkafa biyar ya nuna, k'aton
d'in superghetti, macaroni, couscous, mangyd'a, manja, golden morn, cornflakes, babban gwangwani
madarar gari, milo, Suger cube carton, carton d'in kifin gwangwani sardine har uku, semovita, doya, da
Irish kasancewar duk akwai anan supermarket d'in. Create d'in kwai goma, 5alive irin manya-manyan
goran nan carton uku, exotic, chocolate kala-kala. Frozen chicken, beef da sauransu duk ya saya masu uban
yawa sannan ya bada ATMcard d'insa aka cire kud'in sannan gaba d'aya aka kwashi kayan aka kai masa
boat. Yawan kayan ya saka har a back seat sai da aka saka kaya wasu ma har front seat. Kai tsaye daga nan
ya wuce Jos road gidansu Sarah...............

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*
[30/09, 7:11 PM] Rahamanatu: Sai da ya isa k'ofar gidan sannan ya d'auko wayarsa dake gefensa ya lalubo
number Sarah da yayi saving da *_My endless bliss_* yayi dialing, ringing uku ya amsa kiran tare da fad'in,
"Hello, Assalamu alaikum." Tab'e baki yayi kamar tana kallonsa tare da amsawa da, "Hi, wa'alaikissalam."
Da sauri Sarah ta cire wayar daga kunne tana k'arewa special number d'insa kallo wanda ya k'are da 3 guda
shidda a k'arshe. Turo baki tayi don sarai ta gane muryansa, gashi kuma tana tsoran yanke kiran don bata
manta da deal d'in su na d'azu ba. "Wake magana!" "Bugun zuciyarki!" Kai tsaye ya bata amsa yana mai
sakin murmushi. Sarah kuwa yana fad'in hakan zuciyar nata ta soma bugawa. Shuru tayi bata k'ara cewa
komai ba. Sun d'au lokaci har na tsawon mintuna biyar babu wanda ya sake yin magana. _Khalil_ ya ciro
wayar daga kunne, kamar yanda itama Sarah ta fiddo nata domin ganin is he still their. Sai taga yana
reading kamar yanda shima ya gani daga can, mayar da wayar yayi kan kunnansa tare da fad'in, "Tun ba'a
je ko ina ba, har kin fara karya dokar ko?" K'ara turo baki Sarah tayi daga can tare da fad'in, "To ni ai kai ne
baka yi magana ba, kuma ni ban san mai zan ce ba." Gyara zama yayi cikin motar tare da fad'in, "Ki fito ina
waje." Waro idanu Sarah tayi tare da fad'in, "Waje kuma? Ni dai......." Sai kuma tayi shuru bata k'arisa ba.
"K'arisa maganarki mana, ke dai baza ki fito ba ko?" Kwanciya tayi rigingine tare da fad'in, "Ni dai Allahna
yana sama yana kallo ba haka nayi niyyar cewa ba." D'age gira yayi kamar tana kallonsa tare da fad'in, "Au
Allah d'in naki ne ke d'aya mai son kai. To idan ba tsoro ba ki fad'i abunda kika yi niyyar fad'i daga farko
mana." Sai da ta juya idanuta sannan tace, "Ni dai so nake in ce maka, ni dai gaskiya.... Gaskiya, ummm-
ummm...." Dariya ya saki tare da fad'in, "Kin ga k'aryar ma ta kasa fitowa. To bari na juya kawai kin ga
kenan deal d'in mu ya rushe." Waro idanu Sarah tayi tare da mik'ewa da sauri tana fad'in, "Wallahi a'a,
wallahi ni dai a'a ba haka nake nufi ba. Gani nan zuwa yanzu." Sosai ya saki dariyarsa tare da fad'in,
"Matsoraciya, ana so ana kaiwa kasuwa." "To mai ake so d'in." Ta tambaya tana hararar wayar. "
_Khalilullah_ mana." "Khalilo." Ta fad'i cikin zuciya har da Allah ya kiyaye. Bata san cewar a zahiri tayi
maganar ba sai da taji yace, "Ni ne _Khalilo_ d'in?" "Na shiga uku na!" Ta fad'i jin ashe a bayyane tayi
maganar. "Ki fito maman twins kar ki b'ata min lokacina." "Mene? Ni wallahi ba maman Twins bane. D'aya
kawai zan haifa maka. Shima don babu yarda zanyi ne. Ai don dai zubar da ciki haramun ne, kuma tamkar
kisan kai mutun yayi, da zubarwa zanyi wallahi." Fad'in Sarah. "Don Allah ki gwada! Da na baki tsan-tsan
mamaki don kin san Allah sai na kuma yi maki real ciki kin haihu." Kuka Sarah ta saka tare da fad'in, "Kuma
ba zan fito d'in ba. Mugu kawai!" "Dan Allah ban rok'eki ba, kar ki fito d'in cikin mintuna biyu rak." Yana
gama fad'in haka ya katse wayar. "Kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Wannan wani irin jaraba ce haka?
Ga duka ga tsinke jaka." Fad'in Sarah tare da share guntun hawayen da suka zubo mata ta nufi wardrobe ta
d'auki Vail madaidaici ta yafa a kan riga da skirt d'in jikinta wanda ya amshi k'irar jikinta cif-cif. Babu ko
hoda a fuska sai wani d'aure fuska take yi tare da fita waje ba tare da ta kalli y'an uwanta dake tsakar gidan
ba. Babu mai shigar arziki a cikinsu. Marfu'a ma shayar da y'arta Fadwa take yi y'ar shekara d'aya da wata
biyu. Ko kasheta za ayi baza ta iya nuna uban y'ar ba saboda yawan samarinta. Ga y'ar fara tas kyakkyawa
kamar mahaifiyarta. Don duka Y'ay'an Lami kyawawa ne, duk da Lamin ita ma ba laifi tana da kyau, Sai dai
ita bak'a ce, hasken Baba suka yo da kamannin fuskansa shiyasa gaba d'aya suke kama da juna sai dai
wancen tafi wancen dogon hanci, ko kuma k'irar jiki. Wata kuma dimple gareta, wata kuma wushirya.
Masu dimple d'in sune, Sarah, Na'ima da Hassana, masu wushirya kuma, Aina'u, Nuratu da Marfu'a,
Lukman ne kawai ya d'auko Lami kaf, kamanni da hasken fata. Sai Aina'u da itama ba fara bace sosai kamar
sauran y'an uwanta. Kuma ita tana da d'an jiki irin na mahaifiyarsu. Da kallo suka bi Sarah dukkan su, kuma
babu wanda ya tambayeta ina zata je. Tura k'ofar gida tayi tare da fita ta coge a k'ofar gidan tana k'arewa
motar da yake ciki kallo ta gefen ido tana mamaki shi motoci har nawa gare shi haka. Shima kuwa ta cikin
tinted glass window d'in yake k'are ma halittar jikinta kallo yana mai jin wani irin matsanaicin kishi na taso
mata. Domin gyalen dai bai da maraba da babu don babu abunda ya b'oye a jikinta. Ga shape d'inta da ya
fito kamar zanata aka yi. Hannu ya kai ya d'auki glasses d'insa ya mak'ala a idanunsa tare da bud'e motar
ya fito, luckily sai ga wasu almajirai su biyar zasu wuce, da hannu ya yafito tare da bud'e boat ya nuna
masu abunda zasu kwashe su kai gidansu Sarah. Sarah na ganin uban kayan da ake fitowa dasu a cikin
boat, back seat da kuma front seat ta bud'e ido tana mamaki don kamar za'a bud'e shago. Sai da aka gama
kwashe kayan tsaf ya sallamesu sannan ya nufi wajenta don tuni ta bawa almajiran nan waje ta koma gefe.
Fuskan nan b'utu-b'utu ya kalleta tare da zare glasses d'in fuskansa. Lokacin da Sarah ta d'ago ta saka
idanunta cikin nasa, sai da gabanta ya fad'i ganin yanda launin idanunsa suka canza, duk lokacin da ta kalli
idanunsa a wannan yanayin, tuno mata da ranar da aka samu cikin jikinta yake yi. "Ke har yanzu baki yi
hankali ba ko Sarah!" Duk lokacin da ya furta sunanta, sai taji duk duniya babu wanda ya iya kira kamarsa.
"To ni kuma mai nayi yanzu?" Ta fad'i tana mai turo baki. Ko kamun yayi wata magana, Lami ta turo k'ofar
gidan tare da fad'in, "Sannu-sannu! Sannu da k'ok'ari yaron arziki! Wannan irin uban kaya haka? Kai an
gode sosai. Ai irin ku ake so masu hannu a bud'e. Allah yayi maka albarka." Fad'in Lami tana washe baki.
Sarah kuwa ji tayi kamar ta kwalla ihu tsabar takaici. Don Lami ta riga ta gama zubar mata da mutunci. Shi
kuwa _Khalilullah_ ko kallonta bai yi, sai cewa kawai yayi, "Ameen." Yana kallon fuskan Sarah da ta gama
b'ata masa rai. Juyawa Lami tayi ta koma ciki. Sarah kuwa sunkuyar da kai tayi tana jin hawaye na taruwa a
idanunta. "Kar ki yarda wannan hawayen su zubo _Mine_, kar ki yarda su zubo don idan suka zubo nayi
maki alk'awari sai na lashe su tsaf kuma a titin nan." Da kyar Sarah ta iya maida hawayenta suka koma, don
ta san tabbas duk abunda _Khalil_ ya fad'a zai iya yin fiye da haka tun da dai yanzu haka cikinsa ne a
jikinta. "Dan Allah kayi hak'uri da halin mahaifiyata." Mai makon yayi sharhi akan maganar da tayi, sai cewa
yayi, "Sarah idan kina son zaman lafiya dani, kuma kina gudun abunda zai je ya dawo, to kar in kuma
ganinki da irin d'an iskan gyalen nan. Wai ke baki san ba irinku bane suke saka gyale ba? Wallahi yawancin
mata ku kuke ja ana yi maku fyad'e. Kin san cewa Allah yayi ku ma Sha Allah ta yanda ba kowani namiji zai
iya had'iye miyansa akan ku ba, amma sai ku rik'a fitar da surar jikinku. Wasun ku ma har k'ari suke yi don
kawai su burge samarin. To ni wallahi ban so, kuma ban so na sake ganin irin haka. Ki kiyaye ni _Mine_.
"Wai wani _Mine_ sabida kinibibi. Ko ta ina na zama na shi oho!" Fad'in Sarah amma a zahiri sai cewa tayi,
"Zan kiyaye daga yau in Sha Allah!" Politely ta fad'i maganar. Shi kuma _Khalil_ yace, "That's very good.
Allah ya baki iko. Yanzu menene kike buk'ata?" "Turaren jikinka." Ta fad'i a cikin zuciya saboda yanda
k'amshin yake fizgarta, don na yau ma yafi mata dad'i akan wanda ya saba sakawa. Amma a zahiri sai cewa
tayi, "Babu komai. Ni babu abunda nake buk'ata. Abunda ka kawo yau ma yayi yawa." Harararta yayi tare
da fad'in, "To ke na kawo mawa? Ni su Baba da mama da y'an uwanki da kuma babyna dake cikinki na
kawo mawa. Akwai chocolate, wannan duka naki ne, au na baby na. D'an kai hannu cikinki ki fad'awa
babyna daddynsa na gaishe sa." Ko kallonsa bata yi ba, balle tayi abunda yace, kuma dama shima ya san ba
yi za tayi ba. Yana kallonta sosai, bini-bini zata shak'i iska ta lumshe idanu, ya karanci psychology, hakan ya
fahimtar dashi abunda Sarah take shak'a. Murmushi yayi tare da fad'in, " _Mine_ akwai abunda kike so
amma jik'imarki ta hana ki bud'e baki ki fad'a min ko?" Bud'e idanunta tayi a kansa tare da fad'in, "Ni babu
abunda nake so. Kawai zuciyarka ce ta fad'a maka gaibu." Kallonta yayi na second hud'u sannan yace, "Ki
rantse da girman Allah turaren jikina baya fizgar hankalinki har yake saka ki lumshe idanu." Mamaki ne ya
kashe Sarah ganin ya d'ago jirginta. Sai ta diririce ta rasa mai zata ce sai kawai tayi shuru tana kallon k'asa.
Komawa mota yayi, mintuna biyu sai gashi ya dawo da kwalin turaren *_Imperial Majesty_*, bakinsa kuma
yana taunar masoyin nasa _Mastika gum_. "Wai kai baka gajiya da cin chewing gum ne?" Fad'in Sarah
wacce bata ma san lokacin da tayi masa wannan tambayar ba. "Kin tuna wancen ranar haka kika ce min
mai d'abi'u _KARUWAAA_?" Sai da ya,ja waa d'in yana dariya. Rufe fuska da hannunta Sarah tayi tare da
fad'in, "To ai kai d'in ne ka cika cin chewing gum." "Shikenan kuma duk mai cin chewing gum ya zama
karuwa ko? To ai gashi kin tunzurani kin saka nayi maki halin karuwan har gaki da tsaraba." Da gudu Sarah
ta juya zata gudu ya rik'e hannunta tare da saka mata kwalin turaren a hannunta sannan yace "A sauka
lafiya, a kuma gaishe min da Baba." Yana gama fad'in haka ya sakar mata hannu ita kuma ta shige cikin
gida da sauri. Da gudu Lami ta rungumeta tare da zabga gud'ar da ya karad'e gidan, hatta Baba dake d'aki
sai da ya toshe kunne yana fad'in, "A'uzu billahi minash shaid'anir rajim!" Lami kuwa sai ta hau yiwa Sarah
kirari, "Yarinyar mai goshin arziki, yarinya mai k'irar matan manya! Gabanki fari bayanki fari k'al, d'awisu
duk inda kika gitta sai an kalleki. Wuhuhuuuu ina gwanin wani ga nawa gwanar. Ni na san banyi asarar
haihuwa ba wallahi. Kai jama'aa." Tana fad'in haka sai ta hau rawa da wak'a irin na matan zumunta, sai dai
bata kiran sunan yesu almasihu sabida kar Y'ay'an su b'aro jirginta don duk da basu sallah, sai sun ga
dama, baza suji dad'i ba idan suka fahimci ta koma addinin kiristanci wanda take ganin shine addinin
gaskiya a gareta. Sarah kuwa sarai ta faminceta, a zuciyarta sai addu'ar shiriya take nemawa mahaifiyar
tasu akan ta gane gaskiya ta natsu. Aina'u kuwa wani dogon tsaki tayi tare da fad'in, "A dai yi mu gani idan
tusa zata hura wuta." A cikin zuciyarta. Sarah kuwa kaucewa tayi ta shige d'akinsu ta kwanta a kan gado
tana tuno ranar data fara ganin _Ibarahim Khalilullah_ a rayuwarta. Tun da ta taso k'awa d'aya tal tilo take
dashi a rayuwa, Muniba. Muniba na d'aya daga cikin mutanan da suka d'aura ta a kan hanyar madaidaiciya
domin if not because of her she would have joined her siblings. Amma kasancewar Muniba ta taso gidan
mutunci da tarbiya, don babanta shine limamin masallacin _Mai duguri road_, kuma an d'aura su akan
ingantacciyar tarbiya. Makarantar bokonsu d'aya tun daga primary five har suka kammala secondary
school, Muniba tayi k'ok'ari sosai wajen saita Sarah a kan hanya madaidaiciya, don farko itama ta soma
d'auko rawan kai da y'an gidan. Irin su shigar banza, zagin d'an Adam duk tsufansa, rashin kunya da
saurarsu. Muniba ita tayiwa Sarah registration na islamiyar da take zuwa *_MADARASATUL TATBIQUT
TA'ALLIMUL ISLAMIYA_*, kuma makaranta ce da ba'a wasa ko kad'an. Kuma da ikon ubangiji sai da Sarah
tayi sauka sai dai bata samu damar cigaba ba kamar yanda Muniba ta cigaba. Baba Nuhu sosai yaji dad'in
haka, don ko a wancen lokacin, Sarah ita mai k'aunar mahaifinta, kuma tana jin maganarsa sab'anin Lami.
Don ita b'ata tab'a sha'awar karuwanci ba kamar yanda sauran y'an uwanta suke yi. Burinta shine tayi aure
ta zauna a d'akinta k'ark'ashin kulawar miji. Sai dai Baba Nuhu bai da k'arfi sosai wanda zai iya biyawa
Sarah kud'i both islamiya da boko don lokacin ta kammala secondary school har ta yi jamb kuma ta samu
admission a polytechnic na tudun wada, kuma Evening. Kuma registration kawai 63thousand ne. An buga
an buga babu ta inda kud'in nan zasu fito, kuma Lami tayi rantsuwa da Allah kwandala baza ta biya mata
ba, tunda ita bata taimaki kanta ba, babu yanda za'ayi ita ta taimaka mata. Haka Sarah tayi ta fad'i tashi har
ta samu aiki wa wani babban restaurant wanda zasu rik'a biynata 20k duk wata. A kuma wannan lokacin
wani babban yayan Muniba ya gansu tare da Sarah a bakin titi lokacin zata tafi restaurant inda take aiki, ita
kuma Muniba zata tafi poly don ita ba evening lectures take yi ba. Ai kuwa yana dawo gida ya fad'awa
mahaifinsu yaga Muniba da yarinyar gidan karuwai. Bayan ta dawo daga school aka mata dukan tsiya kuma
ana zama mata jan layi akan idan ta ketara ta kuma had'uwa da Sarah kashinta ya bushe kuma baza ta
k'ara zuwa makaranta ba sannan aure za ayi mata kamun ta jawo masu abun kunya kuma da ko wanene
aka samu za ayi mata auren. Wannan shine dalilin rabuwarsu da Muniba. Ko a hanya basu k'ara had'uwa
ba tun bayan da Muniban ta fad'a mata abunda mahaifanta suka yanke. Don ko a wannan lokacin Sarah
bata daina saka k'ananun kaya ba shiyasa kowa yake mata kallon y'ar iska. A restaurant d'in nan ta soma
ganin _Khalil_ yaje cin abinci. Shi kuma idan bai ci abinci a gida ba, babu inda yake zuwa yaci abinci
hankalinsa a kwance kamar wannan restaurant d'in. Don abincin gargajiya suke yi kala-kala mai dad'i da
tsafta. Sau uku ana aikenta kai masa menu, kuma duk taje sai sunyi fad'a don kallon y'ar iska yake mata, ita
ma kuma kallon da take masa kenan don kullum da chewing gum a bakinsa, duk da kuwa ba k'as-k'as-k'as
yake yi ba. Amma ganin duk lokacin da tazo kawo masa Menu wani harara take jifansa dashi tana magana
k'asa-k'asa, shi kuma sarai yana jin ta sarai, don ce masa take yi karuwa. Shi duk wajen babu wacce ya
tsana irinta, haka itama. Dad'inta ma sai ya kwashi watanni bai zo ba. Ta kwashi tsawon shekara biyu tana
aiki a wajen har ta kammala diploma d'inta. Ranar da suka yi sign out, bak'ar skirt ta sanya iri straight d'in
nan mai tsagu ta baya, sai fara k'al d'in shirt da mutane suka yi signing da maka ta ko'ina a jikin rigar gaba
da baya. Kanta kuma tayi parking d'in gashinta a tsakiyar kai da yaci uban acuci maza na attachment, babu
d'an kwali a kanta, sai wani siririn Chantilly Vail da ta yafa. K'arfe shidda ta tashi a aiki, bayan ta gyara
jikinta ta kuma fesa turare sannan ta nufi wajen madam za tayi mata sallama don ita take bata kud'in
motar komawa gida. "Aunty na gama zan wuce." "Yauwa Saratu, karb'i wannan hanyar wucewa gidanku
ne, zaki kai wannan sak'on *Golden diamond hotel*, wani customer d'in mu ne ke son tuwon shinkafa
miyar egushi. Kuma shi abinci idan ba na nan wajen ba, bai son na wani waje. Please ki tsaya ki kiyi
delivery d'in wannan sai ki wuce gida. Ga kud'in transport." Ta k'arisa maganar tare da mik'a mata 1k da
kuma ledan take away a ciki. Karb'a tayi tare da juyawa ta fita daga restaurant d'in. Zuciyarta d'aya ta nufi
hotel d'in kasancewar har numbern d'akin aunty ta fad'a mata. Tana zuwa reception ta samu wani
inyamuri tayi masa magana, duk a tunaninta shi zai karb'a ya kai masa abincin. Amma sai taga inyamurin
ya daga waya ya kira can d'akin yayi magana da wanda zata kaiwa abincin. "Ok Sir!" Shine kawai abunda
taji ya fad'a tare da yanke wayar sannan ya kalleta tare da fad'in, "Madam you can go in!" Da kamar za tayi
musu, sai kuma ta nufi hanyar da zai sadata da matattakar da zai kaita room number d'in da yake ciki.
Knocking tayi, daga ciki aka ce "Yes come in!" Tura k'ofar tayi tare da shiga kanta a k'asa. Shi kuwa juyowa
yayi hannunsa rik'e da waya yana amsa kira yana fad'in, "Hajiya Allah idan basu bar gidan nan ba bazan
dawo ba. Haka kawai sun bi sun takura mana mu da gidan uban mu!" Dai-dai nan ya d'ago idanu ya sauke
a kan Sara dake tsaye. "Hajiya zan kira ki ina zuwa." Yana fad'in haka ya katse wayar tare da jifan Sarah da
mummunar kallo sannan yace, "Ko ina sai kin nuna rashin kamun kanki ko? Idan banda zubda da kai da
rashin aji, duk mazan dake restaurant d'in naku a rasa wanda za'a aiko ya kawo min abinci sai ke." "Ni dai
ba y'ar iska bace tunda de bana zaman hotel, kuma ba'a tab'a gani na ina taunar chewing gum kamar
karuwa ba. Kallo d'aya za ayi maka a fahimci kai wani irin mutum ne. Kai ne mara kamun kai ba ni ba. Kuma
ni ga abunda ya kawo ni hotel nan na ajiye maka." Ta fad'i haka tare da ajiye masa ledan a kan center table
zata juya. Fizgota yayi tare da fad'in, "Ke wanene d'an iskan?" Fizge jikinta tayi tare da fad'in, "Kada
hannunka ya k'ara tab'a jikina. Jikina yafi k'arfin ka wallahi. Ni ba gantalallun y'an matan daka saba
kwanciya dasu bane anan hotel d'in. A fita a samu dai-dai da kai. Ni ba sa'ar ka bace!" A tsawace yace,
"Wallahi idan kika k'ara magana sai na baki mugun mamaki anan d'akin." A tsawace Sarah tace, "Iya kaci
kace zaka kashe ni ka b'oye gawata. Ni dalla malam matsa min a hanya in wuce don wari da k'arni zina ya
ishe ni." Tana maganar ne gabanta na fad'uwa amma tsaurin idanunta ya hanata yin shuru. Wani
gigitaccen mari ya dauketa dashi tare da fad'in, "Zan nuna maki halin karuwan da kike ambata na dashi
kullum." Yana gama fad'in haka ya danna switch d'in d'akin wuta ya d'auke tare da d'agata cak ya jefa kan
gado. Wani irin ihu ta saki tare da mik'ewa zata duro daga kan gado amma ya riga ta hawowa kan gadon
tare da yi mata rumfa kuma ya sakar mata nauyinsa gaba d'aya a jiki sannan yayi amfani da hannunsa ya
zame shirt d'in jikinta. Jin ta damesa da ihu ya kai hannu ya bige bakinta tare da fad'in, "Dama ai kin saba
bin mazan, ihun uban mai kike min." Duk da tana cikin mugun tsoro da tashin hankali hakan bai hanata
magana ba tace, "Mugu azzalumi, mai halin karuwai. Wallahi sai na kashe ka idan kayi min wani abu." Bai
saurareta ba ya kai hannun ya d'aga rigar jikinta ya cire, jikinta sai rawa yake yi, da taga fa tabbas dagaske
yake yi zai rabata da mutuncita da take tak'ama dashi, kuma ga alk'awarin da tayiwa Farouq wanda da kyar
iyayensa suka amince ya turo gidansu har aka tsaida maganar aure. Sai ta fashe da kuka ta soma rok'ansa
tana bashi hak'uri. Shi kuwa tuni ya cire hook d'in bra d'inta ya shiga wasa da ilahirin lallausar jikinta.
Abunda bai tab'a tun da uwarsa ta haifesa, sai gaba d'aya ya rasa nutsuwarsa, don bai tab'a body contact
da mace ba a tsawon rayuwarsa. Don ko side hug bai yarda dashi ba. Tunaninsa ya bar jikinsa har bai san
lokacin da ya zame wandon jikinsa ba ya ware k'afafunta tare da yunk'urin shiga jikinta. Wani mahaukacin
ihun da ta saki ne ya dawo dashi hankalinsa, da mad'aukakin mamaki ya kuma tura jikinsa a karo na biyu,
amma still gan ya jita. Tun da yayi yunk'uri na biyu bai kuma yi ba, sai ya canza salon wasan kasancewar ya
riga ya d'ad'd'ago sha'awarsa gaba d'aya. Jikinsa ya dunga gogawa a nata jikin kusan tsawon mintuna sha
biyar har ya samu nutsuwa sannan ya mirgina ya bar jikinta yana maida numfashi. Ita kuwa Sarah kuka take
yi sosai duk da kuwa ta san bai isa ga jikinta ba. "Mugu azzalumi kawai." Ta fad'i tana kuka. Shi kuwa
idanunsa a rufe yake fad'in, "Naji, duk nine. Kiyi hak'uri ki yafe min. Kin ga ai ban raba ki da budurcinki ba."
A fusace tace, "Wallahi ba zan tab'a yafe maka ba. Karuwi kawai. Mijina ma ba zai tab'a yafe maka ba don
ka cutar dashi ka shiga gonarsa." "Haka be naji duk ba amince. Kiyi hak'uri amma ki min afuwa. Tsautsayine
wallahi ba hali ba bane." "Halinka ne Allah kuwa. Mugu mai lalata yaran mutane a hotel." Mik'ewa yayi ya
tashi zaune. Da saurin ta mirgina sai ji kake tim a k'asa ta d'auka wani abun zai kuma yi mata. "Wayyooooo
Allah na shiga uku k'afata." Ta fad'i da k'arfi dai-dai lokacin da ta d'auki boxer d'insa ya saka tare da
saukowa ya kunna switch d'in d'akin. Da sauri Sarah ta jawo zanin gadon ta rufe jikinta tana kuka sosai da
bak'in cikin abunda yayi mata. Matsowa yayi domin yaga halin da k'afar take ciki, wani irin ihu ta saki tare
da k'ank'ame jikinta. Matsawa yayi yana kallonta. Ita kuwa sai k'ara kakkare jikinta take yi tana kuka. "I'm
sorry kin ji. Ina zuwa yanzu bari na dawo." Ya fad'i hakan tare da d'aukar dogon wandonsa ya saka da riga
ya fita da sauri. Sarah na ganin ta fita ta mik'e da sauri ta d'auki kayanta ta saka. Ko tsayawa d'aukar jakarta
bata yi ba domin kada ya dawo ya idda ita. Da sauri ta bud'e d'akin ta fice daga hotel d'in tana b'oye-
b'oyen fuska. Lokacin da _Khalil_ ya dawo bai d'auka bata d'akin ba ganin ga jakarta a kan gadon. Zama
yayi a gefen gado hannunsa rik'e da wani magani yana jiran fitowarta daga bayi, mintuna biyar suka shud'e
yaji shuru, wani biyar d'in ya k'ara shud'ewa nan ma shuru. Mik'ewa yayi tare da isa k'ofar bayin ya soma
kwankwasawa, jin shuru sai ya tura k'ofar. Wayam ya gani. Da mugun sauri ya tashi ya fita ya dunga dube-
dube ko zai ganta, amma babu ita babu dalilinta. Gashi babu wani makama da zai gane inda take, ko
sunanta bai sani ba. Komawa cikin hotel d'in yayi tare da bud'e d'aukar jakarta da wani abu kamar d'an
kwali da ta bari ya fita ya bar hotel d'in. Tun daga wannan ranar _Khalil_ bai sake farin ciki ba, kullum cikin
neman Sarah yake yi. Kuma Allah bai k'ara had'a su. Sai bayan kwanaki ashirin da uku a asibitinsa. Aina'u
ba k'aramin tashin hankali ta shiga ba ganin irin uban kaya da _Khalil_ ya jido. Ji take kamar zuciyarta zata
hudo k'irjinta ta fito tsabar bak'in ciki. "Hajiya tun d'azu ake kiran wayarki." Fad'in Laure tana mai mik'awa
Hajiyar waya. Amsa Hajiya tayi bayan ta shafa addu'a don sallar magriba ta idar kuma dai-dai nan aka
kuma kiran wayar. "Assalamu alaikum" Fad'in Hajiya bayan ta amsa kiran ta kara a kunne.
"Wa'alaikissalam, dan Allah Ina magana da Hajiyar doctor _Ibrahim Khalil_ ne mai asibitin *_Khalilullah
specialist hospital_*?" Kallon Laure Hajiya tayi tare da mata nuni da hannu alamar ta fita bayan ta amsa da
"Eh ita ce. Allah yasa lafiya?" Daga can aka d'an yi jim kamun wacce ta kira wayar ta soma fad'in, "Hajiya
akwai wani abu da d'anki yake b'oye maki mai matuk'ar muni wanda ke baki sani ba. Kuma a irin tarbiyan
da kuka bashi idan na fad'a maki abunda yake aikatawa, sai kin girgiza." Hankalin Hajiya tuni yayi wani irin
mugun tashi ta soma fad'in, "Baiwar Allah ya zaki kira ni kina fad'a min irin wannan maganganun masu
d'aga hankali? Mai _Khalilullah_ yake aikatawa wanda ban sani ba?" "Uhm! Hajiya idan d'an ki ya dawo, ki
tambayesa wacece Saratu?" Mik'ewa Hajiya tayi tana fad'in, "Dan Allah yarinya kiyi maganarki kai tsaye,
mai _Ibrahim_ yake aikatawa wanda ban sani ba?" "Hajiya d'an ki dai yana da budurwa, ko kuma ince maki
dadironsa! Don kuwa yanzu haka da nake fad'a maki, ki fara tanajin jiran isowar jika nan da wata takwas
masu zuwa, don kuwa d'an ki yana neman wata yarinya wacce gaba d'aya gidansu karuwai ne kowa ya
sani. Sunanta Saratu ana ce mata Sarah. Tana da yayyi mata hud'u, kuma gaba d'ayansu babu wacce bata
ajiye shege ba a cikin gidan. Sannan kowa ya san su karuwai ne. Kuma abunda zai baki mamaki, a gaban
uwarsu da ubansu suke. Idan kuma baki yarda da maganata ba, idan _Khalil_ ya dawo tambayar da zaki
fara yi masa shine wacece Saratu. Yanayin da zai nuna kawai ta isa ya tabbatar maki da zance na. Na barki
lafiya Hajiya." Tsabar tashin hankali da rikicewa Hajiya fitsari ta soma saki ba tare da sani ba, da rarrafe ta
shiga bayi ta soma sakin zawon tashin hankali............

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

*_MATAR SAYYADEE_*
[30/09, 7:11 PM] Rahamanatu: D'aga k'afa yayi zai kai masa wani mahaukacin harbi, _Khalil_ yayi wani irin
tsalle ya fad'a bayan kujera amma duk da haka sai da k'afar _LTG Abdullah_ ya same shi a bombom d'insa,
kuma ba k'aramin zafi yaji don sai da yaji kamar mazaunansa baza su k'ara moruwa ba. "Yaya Abdullah
listen to me please. I can explain. Ba yanda kuke tsammani bane" fad'in _Khalil_ bayan ya koma ta inda
Hajiya take zaune. Don gwara Hajiya sau dubu malala gashin tinkiya a kan ya Abdullah. Yanzu sai ya karya
shi, kuma ya karya banza hofi. "Ya Abdullah, let give him a listening ears. Don wallahi a zaunen nan da
nake, tafarfasa zuciyata take yi. Jiya-jiya nan na gama wani case akan wata k'aramar yarinya da aka yiwa
fyad'e kuma ta mutu har lahira, kasancewar iyayan yaron da suka yi abun suna da kud'i, sai suke ta musu
barazana akan idan suka fitar da maganar sai sun b'atar dasu. Har sun hak'ura sun bar maganar, shine wani
d'an uwansu yazo daga Legos ya samu labarin abunda ya faru, yayi tsalle ya ce shi kuma ko da zai mutu sai
ya nemawa yarinyar da dududu baya wuce 11years ba adalci. Shine aka had'a shi dani. Kuma Alhamdulillah
munyi nasara. Yanzu ka bar shi yayi bayani sai mu san ta yanda zamu b'ullowa lamarin, don wallahi har
gaban iyayan yarinyar sai munje. Kuma idan suna son adalci, ni da kaina zan nema masu. Kar kaga ni d'an
uwanka ne wallahi. Ba haka papa yayi mana tarbiya ba." Mugun kallo yaya Abdullah ya jifesa dashi tare da
fad'in, "Muna jinka!" Maganarsa yaya Abdul har cikin dodon kunne yake shiga. Don idan yayi magana da
k'arfi wani lokacin zaka dauk'a gidan sama ne yake rugujewa. "Dan Allah ayi min alfarma mu kasance mu
hud'u kawai a nan sai in yi maku bayani. Don maganar tsauri za tayi min a gaban Hajiya." Harara Hajiya ta
watsa masa tare da fad'in, "Lokacin da kake lalata y'ar mutane, baka ji kunya ba sai yanzu." Sunkuyar da kai
_Khalil_ yayi don dagaske kunyar Hajiyar yake yi kuma ga k'annansa mata a wajen. Kallo d'aya ya Abdullah
yayiwa su Nafeesa da Aysha suka tashi suka fita daga d'akin ya rage daga, Ya Abdullah sai Ya Barrister, da ya
Abdul-Hakeem da shi _Khalil_ d'in sai Hajiya wacce tayi mirsisi tak'i fita don so kawai take yi _Khalil_ ya
k'aryata abunda kunnanta suka jiye mata jiya ko ta samu salama a zuciya. "Muna sauraronka." Fad'in ya
Barrister don ya Abdullah ko tari bai kuma yi ba ban da harare-harare da yake ta aikawa _Khalil_ d'in.
Sunkuyar da kai _Khalil_ yayi tare da soma fad'in, "Hajiya idan baza ki manta ba, kwanaki ashirin da uku
zuwa da hud'u da suka wuce, su Uncle Ameeru sun zo gidan nan sun tada fitina akan lallai sai na fiddo duk
wani document na mahaifinsu kama daga duka takardun gidajensa, ATM d'insa duka da dai sauransu
wanda hakan ya saka na tattara na bar masu gidan na tafi na kama d'aki a _Golden diamind hotel_ don sun
ce baza su bar gidan ba idan ban dawo ba ko da hakan na nufin zasu kwana." Gyad'a kai Hajiya tayi tare da
fad'in, "Kwarai na tuna." "Ni ma na tuna ranar." Fad'in ya Abdul-Hakeem. _Khalil_ ya cigaba, "To ni kuma
ban ci abinci ba tun breakfast d'in da nayi a gida na wuce asibiti. Kuma Hajiya ke shaida ce idan har ban
samu abincinki ba, restaurant d'aya nake zuwa naci abinci hankali na a kwance. To kuma ranar na gashi
sosai, sai naji ba zan iya fita naci abincin a can ba, sai na kira waya akan a kawo min abinci a inda nake
kasancewar suna hakan. Ban tab'a saka raina ita za'a turo ba don akwai maza a wajen sosai kuma su suke
yin delivering don har mashin mai gidan abincin ta saya saboda irin haka. Na san yarinyar don duk lokacin
da naje cin abinci, sai munyi fad'a da ita don kullum ina taunar chewing gum take samu na. Sai ta rik'a ce
min mai hali irin na karuwa. To ranar wallahi Allah shine shaida ta bani da wani niyya na cutar da kowa,
kuma wallahi ban tab'a sha'awar zina ba don na san illarta. To da ta kawo min abincin, sai naga ita ce. Sai
haushi ya kamani ganin mai zai kawo mace mai mutunci hotel kawo abinci. Zai zuciya ta yunk'uro ni na
gaggaya mata maganganu marasa dad'i har ita ma ta soma mayar mani tana fad'a min jikinta yafi k'arfi na
ita ba y'ar iska bace inje in samu dai-dai ni. Ni kuma sai zuciya ta yunk'uro ni tare da shaid'an muka fara
kokuwa har nayi k'ok'arin kusantarta. Sai dai jin da nayi dagaske ita d'in cikakkiyar budurwace don akwai
budurcinta a tare da ita, sai na fasa kaiwa ga jikinta, amma kuwa yanayin da na fad'a na muguwar sha'awa
ya saka ban iya hak'ura ba duk da ban kai ga ainahin jikinta ba, amma sai da na samu natsuwa ta wajen
jikinta wanda hakan ya saka ta samu juna biyu. Amma kuma munyi magana da mahaifinta kuma ya
fahimceni. Kuma nayi masa alk'awarin ni zan aure ta na killaceta a gidana. Wallahi tun kamun na san tana
d'auke da cikina, Allah ya jarabceni da matsanaicin sonta. Wallahi ina sonta yaya Abdullah!" Tsit d'akin
yayi, daga Ya Abdullah har ya Barrister basu yi mamaki ba don sun san hakan na iya faruwa. Musamman
ma ya Barrister da ya tab'a Shari'a akan irin haka. Iyayen yarinya suka kawo k'ara saurayi yayiwa y'arsu ciki,
shi kuma ya daka tsalle tare da rantsuwa bai tab'a kusantarta ba. Da Barrister ya tambayesa ya tab'a wasa
da al'aurarsa a jikinta ko da kuwa bai shigeta ba har ya kawo, sai yace eh. A nan alk'ali ya shaida masa ciki
na iya shiga jikin mace ta wannan hanyar. Bayan kuma yarinya ta haihu, binciken likitocin suka tabbatar
jariri na saurayin ne. Kamun nan ma jariri da ubansa yayi kama tsaf. "Wai wani bayanin banza yake yi
haka?" Hajiya ta fad'i don sam bata fahimci kan zancen ba. Yace bai lalata y'ar mutane ba, kuma a k'arshe
yace tana d'auke da ciki. "Hajiya kwantar da hankalinki, zan saka Aysha tayi maki bayani." Fad'in Barrister
kasancewar Aysha ma'aikaciyar jinya ce (Nurse). Turo baki Hajiya tayi tare da fad'in, "To a wani matsayi ake
kenan yanzu? Kun san dai halin y'an uwan mahaifinku." Gyara murya yaya Abdullah yayi tare da fad'in,
"Hajiya abunda za'a fara yi yanzu shine, zuwa gidansu iyayen ita yarinyar da yayi wa cikin. Sannan na biyu,
ya zama wajibi ya auri wannan yarinya idan har da gaske ne duk abunda ya fad'a kuma idan ta fito daga
gidan mutunci. Don ba zai yuwu ya cuci mijin da yarinya zata aura ba. Dole shi da yayi lalatar, shi zai aure
ta. Sannan kuma, cikin dake jikin yarinyar, ko da wasa kar a kuskura ya zubar dashi, idan har ya zubar dashi,
to babu shi, babu auren yarinyar ko da kuwa mutuwa zai yi." Da sauri Hajiya ta kalli ya Abdullah tare da
fad'in, "To amma marmari wacce ta kira ni ta fad'a min halin da ake ciki, ta shaida min gidan yarinyar ba
gidan mutunci bane, wai gaba d'aya yayyin yarinyar babu wacce bata ajiye shege ba. Kaga kuwa ma had'a
zuri'a da irin wannan gida?" "Maganar had'a zuri'a kuma ai an gama Hajiya tunda kin kusa samun jika daga
gidan idan ma abunda da aka fad'an da gaske ne." Fad'in ya Barrister. Yaya Abdullah kuwa cewa yayi, "Ina
bayan Hajiya, domin baza mu d'aukowa kanmu abunda zai je ya dame mu ba. Idan har bincike ya nuna ba
gidan mutunci bane, to fa za muyi masu duk abunda ya kamata, idan yarinya ta haihu mu karb'i d'an ko
y'ar, amma kuma maganar kawo uwar cikin zuri'ar mu, an soke ki. Hajiya duk ku shirya, _Khalil_ d'in ya
tashi yayi mana jagora zuwa gidansu yarinyar. Ni kuma daga nan, zan yi bincike sosai akan ita yarinyar, idan
babu wani nak'asu, to _Khalil_ zai aureta, idan kuma akwai, to fa sai dai ya hak'ura." Tun da aka fara
maganar sai yanzu Abdul-Hakeem yayi magana, "Amma yaya Abdullah, idan iyayen suka ce basu yarda ba
fa? Misali suke sai sun kai abun ga hukuma. Bakwa ganin hakan zai tab'a k'imar Papa da ake ganin
mutuncinsa duk da baya da rai, kuma mutuncin gidan da da mu gaba d'aya sai ya tab'u. Musamman kai da
babban mutum da aka sansa da kuma ya Barrister da yayi fice sabida sunan papa da yake bearing." Wani
mugun numfashi Hajiya taja tare da fad'in, "Nima wallahi tunanin da nake ta yi kenan cikin zuciyata. A
gaskiya _Mu'azzam_ baka kyauta mana ba sam. Ka shafawa gidanmu bak'in fenti." Mik'ewa tsaye yaya
Abdullah yayi jin kiran sallar azahar tare da fad'in, "Babu abunda zai faru in Sha Allah! Ku tashi muje muyi
sallah." Gaba d'aya suka tashi suka fita. Hajiya kuma cike da mamaki ta yanda ake samun ciki ba tare da d'a
namiji ya kusance mace ba ta koma d'akinta. A nan ta taras da Nafeesa da Aysha ko wacce ta d'auro
alwala. Aysha ma hannunta rik'e da darduma tana k'ok'arin shimfid'awar Hajiya ta shigo. "Hajiya har kun
gama meeting d'in?" "Uhm, idar da sallah Aysha kizo ki fitar dani cikin duhu, dama Barista yace min kece
zaki fitar dani." Hijjab Aysha ta saka tare da fad'in, "To bari na idar da sallar." Kasancewar juya masu
dardumar tayi, gaba d'aya suka tada sallar, ita kuma Hajiya ta mik'e ta shiga bayi tare da d'auro alwala ta
fito. Sai da suka idar da sallar har Hajiya sannan Hajiya ta kalli Aysha tare da fad'in, "Yi min bayanin nan
Aysha. Ta yaya za ayi mace ta samu ciki ba tare da d'a namiji ya kusance ta ba." Kallon juna Aysha da
Nafeesa suka yi kamun Aysha tace, "Eh to, akwai hanyoyi biyu da mace ka iya samun ciki ba tare da namiji
ya shiga jikinta ba. Hanya ta farko, akwai wani abu da turawa suke cewa Invitro fertilization ko kuma
artificial insemination. Ma'aura sun fi yin wannan idan matar ta kasa samun ciki sai suje ayi masu wannan.
Ruwan miniyy namijin zai bada, sai a saka ita macen, idan kuma macen baza ta iya d'aukar cikin ba, sai a
sawa wata macen a mahaifarta domin ta raini cikin ta haifesa. Hanya ta biyu kuma, akwai mazan da suke
wasa da y'an matansu ba tare da sun shiga ainahin jikinsu ba, sai su rik'a goga al'aurarsu a jikin y'an matan
na su, kuma idan har namiji sai gamsu, ma'ana ya kawo a jikin ita budurwa, to akwai yuwuwar ta samu ciki
a wannan lokacin don Y'ay'an halittun dake jikin d'a namiji kamar iska haka suke wajen sauri. Amma Hajiya
mai yasa kika yi min wannan tambayar." Wani ajiyar zuciya Hajiya ta saki tare da fad'in, "Abunda d'an
uwanku ya aikatawa wata yarinya da k'arfin tsiya kenan. Kuma sai Allah ya kama shi yarinyar ta samu ciki."
Gaba d'aya suka kaure da salati. "Amma ya _Khalil_ bai kyauta ba wallahi." "Uhm! Ai ni na jijjiga da na
samu labarin jiya, wallahi har sai da na kwanta ciwo. Kuma yanzu haka da za'a gwada jinina sai anga ya
hau. _Mu'azzam_ ai ya b'ata wayansa. Ku fita muci abinci a parlour don gidansu yarinyar zamu je yanzu
haka. Don ina tunanin Marmari yau zai koma Habujan." Mik'ewa suka yi suna jimamin labarin da Hajiya ta
basu tare da fita daga d'akin lokacin tuni su Ya Abdullah sun dawo. Aunty Maryam da Laure kuwa Sai kaiwa
da komowa suke yi wajen dinning suna jera abinci. Sai da suka gama tsaf sannan gaba d'aya suka nufi
dinning d'in. Aunty Maryam ce tayi serving kowa sannan ta koma ta zauna tayi serving kanta. _Khalil_
kuwa ko ta kan abincin bai yi ba don ko cokali bai tab'a ba. Gaba d'aya tunanin sun tafi wani wajen sabida
furucin da ya Abdullah yayi akan idan har bincike ya nuna gidansu Sarah ba gidan mutunci bane, to babu
aure tsakaninsu. Gashi kaf unguwar duk wanda za'a tambaya to ba zai tab'a bada shaidar arziki a kan gidan
nan ba. Saukar cokali da yaji a goshinsa ya saka ya dawo cikin hayyacinsa da sauri yana kallon saitin da yaya
Abdullah yake tare da susa goshin don ya same sa sosai. "Tunanin mai kake yi da bazaka ci abinci ba."
Fad'in ya Abdullah fuska a d'aure. Hannu ya saka a abincin ya soma jujjuyawa cokalin kamun ya kai loma
d'aya baki. Gaba d'aya ji yayi abincin ma d'aci yayi masa. Da kyar ya iya had'iye wanda ya kai baki. Gudu
b'acin ran yaya Abdullah haka ya dunga tura abincin a bakinsa duk da kuwa ba dad'i yake yi masa ba. Yaya
Abdullah ne ya soma mik'ewa bayan ya goge bakinsa da tissue ya koma kan kujera ya zauna. Yana tashi
_Khalil_ ya ajiye cokalinsa tare da jingina da kujera ya lumshe idanu. Harara Hajiya ta watsa masa cikin
zuciyarta tace, "Mai ka gani ma! Ai yanzu ka fara shiga tashin hankali." Kwafar da tayi ne ya saka ya bud'e
idanu ya kalleta ita kuma ta yi kamar bata gansa ba ta cigaba da cin abincinta. Sai da suka kammala gaba
d'aya sannan suka shiga shirin zuwa gidansu Sarah. Su shidda ne kawai za suje, Ya Abdullah, ya Barrister, ya
Abdullah-Hakeem, Hajiya da shi _Khalil_ d'in. Mota d'aya suka shiga su uku, kuma Khalil ke jan motar, yayin
da convoy d'in motar sojoji suke biye dasu, motar ya Abdullah a tsakiya wanda Hajiya kad'ai ke ciki. Gaban
_Khalil_ babu abunda yake yi sai fad'uwa har yayi parking a dai-dai k'ofar gidansu. Gaba d'aya layin ya
kaure da siren d'in motocin soldiers d'in nan. Gaba d'aya layin sai ya rud'e, mutane sai fitowa suke suna
lek'e musamman da sauke inda motocin suka yi parking kuma gaba sojojin sun fito sun k'ame a k'ofar
gidan da kuma ko wani lungu da sak'on na layin. Daga sama har k'asa sojojine kai kace yak'i za ayi. Wani
soldier ne ya bud'e murfin motar da ya Abdullah yake ciki tare da sara masa sannan ya matsa ya k'ame
k'am. Lami da Y'ay'anta dake cikin gida kuwa, tsurewa suka yi kowa na neman wajen b'oyo. Hankalinsu bai
gama tashi bai sai da suka ga soldiers kusan goma sun shigo gidan ko wannensu ya samu position ya k'ame
sabida shigowar Hajiya cikin gida. Kuulululuuuu cikin Lami ya bada wannan sautin. Baba NUHU kuma da
kyar ya mik'e tare da dogaro sandarsa ya fito yana fatan Allah yasa ba wani magana su Lamin suka kuma
jawo masa ba. Ganin sojoji cike a gidansa bai san sanda ya k'ame k'am ba yana salati cikin zuciyarsa har ta
kai ga fitowa fili. Hajiya kuwa ganin yanda duk gidan suka tsorace don hatta Y'ay'ansu Na'ima kuka suka sa,
sai ta saki murmushi tare da fad'in, "Kuyi hak'uri mun shigo ba tare da izini ba kuma mun tsorata ku." Tana
gama fad'in haka sai ta juya baya tare da fad'in, " _Khalil_ kana ina, shigo mana kayi masu bayani." A
wanda kwai ya fashewa a ciki _Khalil_ ya k'ariso tare da d'an d'ukawa yace, "Barka da rana, ina wuni Baba?
Tare muke da mahaifinta da y'an uwana sun zo wajenka ne." Lami na jin haka ta saki wani k'aramin ajiyar
zuciya tare da jinjina kud'i da k'arfin iko irin nasu. Amma kuma duk da hakan a tsorace take. Don kamar an
cire mata haukar kanta ita da sauran y'ay'anta. Aina'u kuwa sai bin su take yi da idanu gabanta na fad'uwa.
"Ku shigo daka ciki mana. Marabanku. Sannunku da zuwa. Ku k'ariso ciki." Fad'in Baba yana mai dogara
sandarsa tare da basu hanya. Allah yaso yau da safe Sarah ta biya Aina'u dubu biyar ta gyara d'akin Baba
tsaf duk da kuwa babu komai a ciki sai yaloluwar katifarsa, don ko ledar tsakar d'aki babu sai siminti kawai.
Na'ima taho ki shimfid'a masu tabarmar." Fad'in Baba. Babu musu da sauri Na'ima ta nufi d'akin Baba tare
da shimfid'a k'atuwar wankakkiyar tabarmar baban tare da saurin fita. Su Hajiya da su ya Abdullah suka
shige cikin d'akin Baba tare da zama a kan tabarmar ba tare da nuna kyama ba. Na'ima kuwa da sauri ta
fad'a d'akinsu tare da soma d'akawa Sarah duka don ita bata ma san mai ke faruwa ba don tun k'arfe goma
take bacci bayan ta gama kelaya amai mai kashe jikin d'an Adam. "Dan ubanki ki tashi ga dangin saurayinki
sun zo." Da sauri Sarah ta tashi jin abunda Na'ima tace. "K'anwata wallahi kin tako arziki. Kin san su
wanene suka zo gidan nan kuwa. Bud'e window ki fara lek'a waje tukun." Fad'in Na'ima. Da sauri Sarah ta
tashi ta nufi window kasancewar ta waje yake tare da bud'ewa. Da sauri ta jawo ta rufe tana kallon Na'ima
tare da fad'in, "Na'ima sojoji na gani a layin? Wa aka kashe. Ba dai _Lucky boy_ bane ya d'auko mana
magana. Yanzu hakan wayar wani sojan ya sato. Mun shiga uku mu kan yau." Fad'in Sarah tana neman
fashewa da kuka. "Banza kawai! Nace maki dangin saurayinki ne yazo. Ina ga fa babansu baban Soja ne.
Don yanzu haka har da mahaifinsa da y'an uwansa suna d'aki wajen Baba." Waro idanu Sarah tayi tare da
fad'in, "What! Mai suka zo yi to?" Hannu Na'ima ta watsa gefe tare da fad'in, "To to wa ya sani. Watak'ila
dai sha tara na arziki suka zo baki. Ke dai wallahi kin tako! Bari na fita na bawa idanuna abinci." Na'ima na
fad'in haka tayi waje. A can d'akin Baba kuwa, bayan gaishe-gaishe da suka yi a tsakaninsu, sai Hajiya tayi
nuni ga yaya Abdullah tace, "Wannan shine babban d'ana, soja, lutanan genaral ne, sai wannan, shi kuma
barista ne, wannan kuma d'an sandan farin kaya. Na san ka san wannan ko? (Tayi nuni ga Khalil) tare da
cigaba da fad'in Shi kuma dakta ne. A jiya na samu labarin b'arnar da ya aikatawa 'yarka, kuma mun
tsaresa ni da y'an uwansa sai da ya fad'a mana gaskiya na cewar fyad'e yayi mata" dai-dai nan Lami ta
shigo d'akin ita dasu Nuratu hannunta d'auke da farantin wanda aka sanya ruwan gora mai sanyi da kuma
kwalin exotic d'in da _Khalil_ ya kawo ta ajiye tare da rab'ewa tace, "Sannunku da zuwa. Ina wunin ku?"
Hajiya da yaa Abdullah suka amsa yayin da Barrister da ya Abdul-Hakeem suka gaisheta. Don a girme ya
Abdullah ya girmi Lami sai dai suyi sa'a da Baba Nuhu. "Ita ce mahaifiyar yarinyar." Baba ya fad'i yana mai
nuni da Lami wacce ta sunkuyar da kai kamar mutuniyarki. Baba da _Khalil_ kuwa mamaki ne ya kashe su
ganin yanda Lami ta natsu. Kuma natsuwarta nada nasaba da kwarjinin da ya Abdullah yayi mata da kuma
tsoron uban sojojin da ta gani a waje. Hatta su Nuratu wani irin natsuwa suka yafo suka daurawa kansu.
Cike da ladabi suka gaishe da su Hajiya sannan suka fita. Hajiya ta cigaba da fad'in, "Dan girman Allah
muna neman yafiyarku duk da kuwa mun san an cuce ku, domin duk wanda ya b'ata maka y'a yayi maka
cuta mafi muni don ya b'ata mata record. Amma fa baza mu tilasta ku ba, ga d'ana nan Muhammad Kabir,
a shirye yake da ya tsaya maku idan har kuna neman adalci a kotu. Wallahi d'ari bisa d'ari na bashi goyon
baya da ya tsaya maku tsayin daka har sai alk'ali ya yanke hukunci bisa adalci." Murmushi Baba yayi yana
mamakin karamcin irin na Hajiya tare da fad'in, "Duk bata kai haka ba Hajiya. Kuskure dai an riga anyi, sai
dai a tari gaba kawai. Allah dai ya yafe maka kura-kuran mu gaba d'aya ya kuma kiyaye na gaba. Amma
maganar zuwa kotu duk bata taso ba. Kuma har gida kamun zuwan ku, shi Ibrahim ya shigo har nan d'aki
ya bani hak'uri kuma ya shaida min kuskure ne da sharrin shaid'an. Tun a wancan lokacin ni na yafe masa
wallahi. Kuma ina mai tabbatar maku itama Saratun ta yafe masa." Kallon Lami Hajiya tayi tare da fad'in,
"Baiwar Allah nasan sai kin fi kowa jin zafin wannan abu, kiyi hak'uri ki gafarci d'ana. Nasan zafin da kike ji
matsayinki na uwa." Da sauri Lami tace, "Wallahi babu komai ai ya wuce. Ibrahim ya wanke laifinsa ai."
Lami ta fad'i tana washe baki. Baba da _Khalil_ kuwa addu'a suke ta yi cikin zuciyar Allah yasa kar Lami ta
nuna halinta. "Ina ita yarinyar take?" Fad'in Hajiya. Da sauri Lami ta mik'e tare da fad'in, "Bari a kira ta."
Tana fad'in haka ta fice. Kai tsaye d'akinsu Sarah ta nufa. Tsaye ta same ta duk tayi jugum-jugum. "Ki fito
mahaifiyar uban cikin nason ganinki." A rud'e Sarah tace, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Wayyo Allah
mai zan yi mata." A zafafe Lamin tace, "Zaki fito ko sai naci ubanki. Shegiya y'ar bak'in ciki. To kyauta za tayi
maki." Sarah bata k'ara cewa komai ba sai d'aukar dogon hijjab d'inta har k'asa da tayi ta saka tare da
fitowa ta nufi d'akin Baba gabanta na fad'uwa. Sallama tayi sannan ta shiga tare da rab'ewa waje d'aya.
Tun da ta shigo _Khalil_ ke binta da idanu. Kuma a kallon farko da yayi mata ya gane halin da take ciki na
tsoro. "Ina wunin ku?" Sarah ta fad'i muryanta na cracking. "Taho nan d'iyata. Zo nan kin ji." Fad'in Hajiya
tana mai mik'a mata hannu. A hankali Sarah ta mik'e ta nufi inda hajiyar take tare da zama kusa fa ita kanta
a k'asa. "Kiyi hak'uri d'iyata. Sannun kin ji. An cuce ki tabbatas. K'aramar yarinya dake." Ita dai Sarah bata
ce komai sai zuciyarta dake bugawa da sauri da sauri. Ga wannan k'amshin turaren _Khalil_ wanda ya riga
ya kama jikinsa da yake kashe mata jiki. Gyaran murya yaya Abdullah yayi tare da fad'in, "Baba mun yanke
hukunci a kan _Ibrahim_ shi zai auri Saratu idan har ka amince." Baba ya d'ago ya kalli ya Abdullah tare da
fad'in, " _Ibrahim_ yazo min da wannan maganar na kuma amince masa a wancen lokacin amma kuma
nace masa sai da amincewarku, kuma shi yasan dalilin da yasa nace hakan." Yaya Abdullah yace, "Yarinyar
nada wani matsala ne wanda ya kamata mu sani?" Girgiza kai Baba yayi tare da fad'in, "Yarinya bata da
wani matsalar komai. Sai dai yayyinta basa jin magana wanda hakan yasa ake masu kud'in goro har da ita
Saratun. Amma Saratu natsatstsiyar yarinya ce. Na fad'a maku hakane da baki na ba sai kunji a waje ba.
Don na san dole ne kuji. Don karo ba bakwai kenan ana fasa aurenta. Wannan na k'arshen ma sabida
abunda ke cikinta ne yasa aka fasa. Don kowa kallon mara kamun kai yake mata." Kamun ya Abdullah yace
wani abu Hajiya tace, "Wannan ba matsala bane, don laifin wani baya tab'a shafar wani. Mu baza muyi
maku butulci ba musamman ma da ya kasance har da sanadin abunda _Ibrahim_ yayi mata wajen
rugujewar aurenta. In Sha Allah _Khalilullah_ shine mijin uwata Saratu. Da zarar Sarah ta haihu lafiya, satin
suna shine zai zamo ranar d'aurin aurenta da _Khalil_, ko yanzu haka ma sabida ba zai yi ayi aure da ciki
bane, da sai ince a d'aura auren kawai. Sai dai ina mai gargad'in ku da babban murya kar hakan ya saka ku
zubda cikin nan dake jikin yarinyar nan don hakan zai zama zunubi biyu, kuma idan har da gangan aka yi
hakan, to ina mai tabbatar maku _Khalil_ ba zai auri uwata Saratu ba." _Khalil_ ji yayi kamar ya tashi ya
taka don dad'i. Bai tab'a d'auka abun zai zo da sauk'i har haka ba. "Nagode Allah ya saka da alkhairi Hajiya.
Ya Abdullah Allah ya k'ara girma ya dad'a kareka daga sharrin mak'iya. Baba na gode da ka bani Saratu." Da
ameen duka d'akin suka amsa. Lami kuwa ta gama cika faaam bisa hukuncin da Baba ya yanke. Don bata
shirya aurar da y'arta ba. So kawai tayi su tatsi kud'i iya kud'i a jikin _Khalil_ amma kwarjini da tsoro sun
hanata ko kwakkwarar tari. Aina'u dake labe jikin windon d'akin Baba, wasu irin mak'udan hawaye ke zubo
mata, bata tab'a tunanin kiran Hajiya a waya zai haifar da wannan abu da ya faru ba. Ta d'auka Hajiya za
tayi fushi sosai ta kuma jawa _Khalil_ d'in kunne akan kar ya kuskura ya k'ara zuwa nan gidan sannan kuma
ya k'aryata cewar cikin jikin Sarah nashi ne. Barin wajen window d'in tayi da sauri tana toshe bakinta tare
da soma magana cikin zuciyarta, "Ba zai tab'a yuwuwa ba, ba zan tab'a bari Sarah tayi aure ba. Baza ta
tab'a auren _Khalil_, sai na jawo mata bala'i da masifa a rayuwarta idan har ta matsa sai ta aure sa." Ya
Abdullah kud'in da bai san adadinsu ba ya ajiyewa Baba a kan katifarsa tare da fad'in, "Mun gode Allah ya
saka da alkhairi. Ni zan wuce. Jirgin k'arfe biyar zan bi." Hajiya ma mik'ewa tayi tare da fad'in, "Mun gode
fa sosai. Allah ya bar zumunci. Y'ata, Allah yayi maki albarka." Ta fad'i hakan tare da kamo hannun Sarah ta
saka mata wasu warwaro guda biyu na zinari. Barrister da Abdul-Hakeem dukkan su sai da suka ajiyewa
Baba kud'i a kan katifarsa kamun su fice daga d'akin. Har wajen k'ofa Baba ya raka su Hajiya yana d'aga
masu hannu. Mutanan unguwar kuwa dank'am suna jiran suga an fara wurgo su Lami waje ana kakkarya
k'asusuwansu. Sai suka ga har da su rakiya suna d'agawa mutanan wajen hannu. _Khalil_ kuwa wani irin
natsuwa da kwanciyar hankali yaji don sai yanzu ya soma yin walwala har dasu dariya. Bayan sun tafi, Baba
ya dawo d'aki ta taras gaba d'aya Lami ta kwashe kud'in da su ya Abdullah suka bashi. Murmushi kawai
yayi tare da zama a bakin gadon yana mai d'aga hannu sama tare da kwararowa Allah godiya na ganin
Sarah ta kusa tafiya d'akin mijinta gidan mutunci da karamci. Addu'a ya soma yiwa sauran y'an uwanta
akan suma Allah ya shiryesu su samu suyi auren suma. A can gidansu _Khalil_ kuwa, fad'a sosai ya
Abdullah ya rufe _Khalil_ dashi akan yana ganin irin d'akin da surukinsa na gobe yake kwana amma ba zai
iya wani abu a kai ba. Sannan kuma menene amfanin na zama likita tunda ba zai iya taimako ba yana ganin
uban wacce zai aura a cikin rashin lafiya. Bayan nan kuma ya kankara masa warning akan kar ya kuskura ya
cire cikin dake jikin Sarah don yana tak'amar shi likita ne. Shi kuwa _Khalil_ ko sau d'aya hakan bai tab'a
zuwa masa zuciya ba. Hak'uri ya bawa ya Abdullah tare da sheda masa hakan dama na daga cikin budget
d'insa ya gyara gidan ya kuma kai baban nata asibiti. Har airport suka raka ya Abdullah ya hau jirgin sojoji
da zai tashi zuwa Abujan a ranar suka wuce shi da Aysha. Nafeesa kuma sai yamma _Khalil_ ya mayar da
ita gida. Su ya Barrister kuma dama kwana biyar za suyi kamun su koma. Da daddare misalin k'arfe takwas
ta fito daga gidan ta nufi wani k'atoton chemist fuskanta sanye da facemask tare da shiga, sai da ta bari ya
sallami kowa ya rage saura ita d'aya sannan ta nufesa tana murmushi. "Su Ain sai yau aka tuna damu."
Murmushi tayi tare da d'an jan facemask d'in k'asa kad'an tare da fad'in, "Kai dai bari, wallahi yanzu ma
zuwa nayi ka bani maganin abortion mai tsinannan k'arfi dan Allah." Dariya yayi tare da fad'in, "Anyi abun
kenan? To wata nawa ne?" Sai da tayi farrr da idanu sannan tace, "Bai girma ba fa, bai wuce 2weeks ba fa."
"Au, ai wannan ba zai yi wahalar fita ba. Amshi wannan ki shanye duka, bana tunanin ko thirty minutes za
k'ara da cikin nan a jikinki." Amsa Aina'u tayi tare da fad'in, "Thanks. Shiyasa nake sanka." Ta fad'i hakane
tare da fiddo 5k a a purse d'in hannunta ta bashi sannan ta juya ta fita ta shiga wani shagon provision ta
siya fanta mai sanyi..............

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

*_MATAR SAYYADEE_*
[30/09, 7:11 PM] Rahamanatu: *👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

Abu kad'an ke saurin d'aga mata hankali. Babu mamaki yanzu idan aka duba BP d'inta aga ya hau. Ta jima
duk'e a bayin kamun ta iya cire kayan jikinta tayi wanka sannan ta sake d'auro alwala ta fito ta sauya kaya.
Tuni wani zazzafan zazzab'i ya rufeta sai kakkarwa take yi a bakin gado. Dai-dai nan Laure ta shigo bakinta
d'auke da sallama tana fad'in, "Hajiya a kawo maki zogalen yanzu?" Da sauri ta k'arisa shigowa d'akin tana
fad'in, "Hajiya lafiya? Mai ke damun ki? Yanzu fa na barki lafiya kina amsa waya." Dakyar Hajiya tace, "Tafi
ki kira min Maryamu yanzu a b'angarensu." da sauri Lauren ta juya ta bar d'akin har da had'awa da gudu ta
nufi side d'in aunty Maryam tare da danna doorbell. Mijinta Yaya Abdul-Hakeem ne yazo ya bud'e k'ofar
tare da fad'in, "Lafiya Laure na ganki a rud'e?" Ya fad'i don shima dawowarsa kenan daga wajen aiki. Yanzu
nan kuma yake son shiga wajen Hajiyar. "Yaya Abdul Hajiya ce ba lafiya shine tace in kira mata aunty
Mar....." Ko kamun ta k'arisa maganar har ya tureta ya fito da sauri ya nufi side d'in Hajiyar kamar zai tashi
sama. Aunty Maryam ma da sauri ta fito don fitowarta kenan daga kitchen taji abunda Laure ke fad'awa
mijin nata. Bin bayansa suka yi ita da Lauren hankali tashe. Ko da yaya Abdul ya isa d'akin Hajiya, gaba
d'aya ta gama firgicewa. Jikinta yayi mugun zafi musamman ta wajen kanta. Zama yaya Abdul yayi tare da
tallabo Hajiyar yana fad'in, "Inna lillahi! Hajiya mai ya same ki. Ai bamu ga ta zama ba. Mu tafi asibiti
kawai." Dai-dai nan aunty Maryam d'in ta shigo ita da Laure. "Abdul-Hakeem d'au wayarka yanzu ka kira
min _Khalilullah_." Hajiya ta fad'i hakan da kyar. Yaya Abdul bai kawo komai a ransa ba sanin k'anin nasa ai
doctor ne. Maybe don yazo ya duba tane don Hajiya ta tsani zuwa asibiti. Wayarsa ya fiddo tare da kirar
_Khalil_ d'in. Ringing yayi har ya katse ba'a d'aga ba, zai sake kira kenan sai ga shigowar kiran _Khalil_ d'in.
D'agawa Abdul-Hakeem yayi tare da fad'in, "Kana ina?" Daga can _Khalil_ yace, "I'm sorry yaya, na fito da
wayar kenan zan d'auka sai katse. Gani kusa da gida." "To kayi maza ka shigo yanzu. Hajiya ba lafiya." Yana
gama fad'in haka ya katse wayar. _Khalil_ kuwa ji yayi gaba d'aya hankalinsa ya tashi. K'ara gudun motar
yayi duk da yana gab da layin. Mintuna biyar suka k'ariso dashi gidan. Ko parking mai kyau bai yi ba ya
shigo gidan ya nufi d'akin Hajiya kai tsaye. Nan ya tarar dasu sun yi curko-curko. "Hajiya mai ya same ki,
taso mu tafi asibitina dan Allah." Da kyar Hajiya ta d'ago kanta ta zubawa _Khalilullah_ idanu tare da fad'in,
"Abdul-Hakeem ku d'an bamu waje." Tana fad'in haka gaban _Khalil_ ya yanke ya fad'i. Don har ji yayi wani
k'aramin zufa ya gangaro daga goshinsa. Abdul-Hakeem babu musu ya mik'e ya fita, aunty Maryam da
Laure suka bi bayansa tare da rufo masu k'ofa. _Khalil_ shuru yayi kamar ruwa ya cinyesa, don hakanan
jikinsa Hajiya ta gano abunda yake b'oyewa. " _Ibrahim_" Hajiya ta kira sunansa da muryanta da yayi rauni.
Hankalin _Khalil_ ta tashe yace "Na'am Hajiya." "Wacece Saratu?" A mugun furgice duk da kuwa zuciyarsa
na bashi ta gano ko kuma wani ya fad'a mata ya d'ago bakinsa na rawa yace, "Haj..... Hajiya ban gane
abunda kike fad'i ba." Hannu Hajiya ta d'aga ta wanke masa fuska dashi tare da fashewa da kuka tace, "
_Khalilullah_ ka b'ata wayanka. Baka kyautawa kanka ba. Dadiro _Ibrahim_? Yanzu har kayi rik'an da zaka
ajiye dadiro a waje _Khalil_. Kana da kud'i, kana da wajen zama, duk wani abu da namiji zai mallaka kamun
yayi aure, ka mallaka _Mu'azzam_, amma shine sabida shaid'an ya buga maka gangi, giyar kud'i na janka,
shine zaka butulcewa Allah ta hanyar yin abunda ya haramceka dashi. Ka bani mamaki _Khalil_. Ashe irin
tarbiyan da muka gina ku a kai ni da mahaifinku, watsar dashi kayi? _Khalil_ baka yi wa kanka da mu adalci
ba. Ka b'atawa zuri'ar suna. Ashe dai da gaskiya su Ameeru da suke cewa ka ajiye dadiro. Shiyasa a kullum
burinsu shine suyi maka aure sabida sun san lalatar da kake yi a waje. Baka min adalci ba _Mu'azzam_!" Ta
k'arisa maganar tana mai fashewa da kuka takaici. Shima _Khalil_ d'in kukan ya soma yana fad'in, "Hajiya
dan girman Allah kar kiyi mani kuka. Kukanki bala'i ne a gare ni. Ki tsaya inyi maki bayani. Duk wanda ya
fad'a maki na ajiye dadiro wallahi sharri yake min kawai yana son shiga tsakanina dake ne. Wallahi tallahi
ban tab'a ajiye dadiro ba a rayuwata. Kuma Hajiya ban tab'a ratsa jikin wata y'a mace ba. Ban san ta yanda
zan yi maki bayani ba ki fahimceni ni." Hajiya tsagaita kukanta tayi tare da fad'in, "Kenan sharri ake maka
baka san wata Saratu ba." Girgiza kai yayi tare da fad'in, "Na santa Hajiya, amma ba ta yanda kike
tsammani ba. Ita ce wacce nake fad'a maki ba tsayar matsayin wacce zata zama uwar y'ay'ana." Wani
ajiyar zuciya Hajiya ta saki, sai kuma tace, "To maganar ciki fa? An ce kayi mata ciki in tsammaci zuwan jika
nan da wata takwas. Ya matsayin wannan maganar take?" Shuru _Khalil_ yayi yana kallon k'asa. Sai kuma
ya d'ago tare da kama hannayen Hajiya duka biyun yace, "Hajiya dan girman Allah kiyi hak'uri da abunda
zan fad'a maki yanzu. Amma ki saurare daga baya sai ki yanke hukuncin da kika ga ya dace. Dagaske Sarah
tana d'auke da ciki, kuma nawa ne." Tass Hajiya ta sauke masa mari tare da nuna masa k'ofa tace, "Fita!
Fita nace ka bar min d'aki yanzun nan!!" Ta kuma fad'i a tsawace. Da sauri ya mik'e tsaye tare da fad'in,
"Haj......" "Fita _Khalil_ kar ka sa nayi abunda zan dawo ina dana sani. Fita nace kar in fad'i mummunar
kalma a gare ka." Fad'in Hajiya tana matsar hawaye. Da sauri _Khalil_ ya fita tare da rufo mata k'ofar. Shi
babban tashin hankalinsa, kar jininta ya hau. Yana fitowa daga d'akin ya nufi waje ya zauna tare da kama
kansa har akai kiran sallar Isha sannan ya mik'e ya nufi masallaci. Hajiya kuwa kuka tayi sosai har da
majina. Bayan ta idar da sallar isha'i wanda tayi sa da kyar, sannan ta lalubi wayarta ta dannawa babban
wansu soja mai muk'amin *_LTG (Lieutenant general)_* dake zaune a abuja, a can yake da iyalansa gaba
d'aya kasancewar aikinsa a can yake. Bugu d'aya yayi rejecting tare da karanta, "Assalamu alaikum Hajiya."
"Amin wa'alaikassalam." Tun daga yanayin yanda ta amsa kiran ya tabbatar babu lafiya, mik'ewa yayi d'aga
kwancen da yake ya zauna tare da fad'in, "Hajiya lafiya? Mai ke faruwa?" Kuka Hajiya ta fashe dashi tare da
fad'in, "Marmari daga nesa (Bata kiran sunansa kasancewarsa d'an Faari) duk abunda kake yi ka d'auki
sakuis (excuse) kazo gida gobe, kuma ka kira wancen yaron na Kano shima ina son ganinsa har da
k'anwarku Aisha. Duk kuzo ina neman ku gobe." Gaba d'aya tunanin _LTG Abdallah_ akan maganar
gadonsu ne, don wani lokacin haka uncles suke sako mahaifiyar nasu a gaba duk akan dukiyar da mahaifin
nasu ya bari. "Dan Allah Hajiya ki kwantar da hankalinki, in Sha Allah gobe zan biyo jirgi ni da Aysha. Zan
kira mijinta yanzu ina gama waya dake." Fad'in LTG Abdullah don Aysha d'in a nan Abuja tayi aure, kusan a
hannunsa take, don shi ya aurar da ita. Ita ma soja take aure ana Abujan. Katse wayar Hajiya tayi tare kifa
kanta a kan pillow tana zuciyarta na mata zafi, gaba d'aya Y'ay'anta daga maza har matan lafiya k'alau ta
aurar dasu, Nafeesa ta je gidan mijinta lafiya, haka Aysha. Mazan ma gaba d'aya babu wanda ya d'auko
mata abun kunya sai _Khalilullah_. Kuma duk cikin y'ay'anta shi, yana da wani special guri a zuciyarta. Don
shi d'in favourite d'inta ne. Duk da kuwa ba shine auta ba. Nafeesa ce autarta. B'angaren _Khalil_ kuwa
yanda yaga rana, haka yaga dare. Abun duniya duk yabi ya ishesa. Sam ba ta haka yaso hajiya taji wannan
maganar ba. Yaso ya shaida mata da kansa ta hanyar da ko zata jijjiga ba kamar haka ba. Tunani ya dunga yi
wanene ya san abunda ke faruwa har ya d'aga waya ya kira Hajiya, "Doctor Kamal!" Fad'in _Khalil_ a
bayyane. Da sauri ya mik'e zaune yana jin wani irin matsanaicin b'acin rai da tsanar doctor d'in. "Wallahi
sai na baka mamaki Kamal. Ni zaka had'a da mahaifiyata. Zaka san koni wanene. Daga kai na baza ka k'ara
irin wannan munafurcin ba." Saukowa yayi ya nufi bayi yayi alwala tare da fitowa ya shimfid'a darduma ya
dunga yin sallah yana rok'an Allah sauk'i da sassauci akan lamarin. Bai tashi daga kan darduma ba sai da
yaji kiran sallar asubahi na shiga masallaci sannan ya mik'e ya fito. Sai da ya fara bi ta d'akin Hajiya tukun,
da sand'a ya murd'a k'ofar a hankali tare da bud'ewa. Karaf suka had'a idanu da Hajiyar dake zaune a kan
darduma, don kamar yanda ya kwana sallah haka ita ma. Da sauri ya jawo k'ofar ya rufe tare da barin
wajen ya nufi masallaci. Sai bayan da aka idar da sallah har fito zai koma cikin gida yayansa Abdul-Hakeem
ya tare sa, bayan sun gaisa yake ce masa, " _Khalil_ mai ke faruwa Hajiya tayi kiran kowa na gidan nan cikin
gaggawa? Yaya Abdullah ma yana hanya zuwa anjima zai biyo jirgi shi da Aysha. Kuma nima Hajiya ta saka
na kira mijin Nafeesa akan ha kawo ta gobe. Wani irin meeting kuma za ayi yau a gidan nan? Allah yasa ba
dai akan rigimar gado bane. Nifa wallahi abunda Papa ya tafi ya bari bai tab'a d'ad'ani da k'asa ba, abun na
tara da gumina ma ya ishe ni zaman duniya." Tun da ya fara maganar _Khalil_ jinsa kawai yake yi amma
kwakwalwarsa da tunaninsa sun yi nisa tun lokacin da yace masa yaya Abdullah na hanya. Wannan
masifaffan mai bak'ar zuciya kamar da taurin kai. Don shine ya d'auko Papa sak. Shi kaifi d'aya ne, idan
yace yes, to ko duniya zata tashi yes d'in ne, idan kuma yace no, tofa ko ana ha maza ha mata babu mai
canza shi. Kuma duk gidan tsoransa ake ji. Shine babba kuma zai iya kaiwa shekaru hamsin da biyar a
duniya. Daga shi sai yaya Barrister (Muhammad Kabir) kenan, shi yana da sanyi hali. Ba k'aramin abu ke
b'ata masa rai ba. Idan kaga yana zafi da magana sosai, to fa a kotu ne musamman idan Shari'a ake yi akan
fyad'e. Shi yaci gajiyar Papa don tun yana k'aramin yake fad'in "Papa idan na girma irin aikinka zan yi in
rik'a Yankewa mugaye hukunci. Daga Barrister sai Abdul-Hakeem wanda shi kuma SSS ne, (D'an sandar
farin kaya). Daga shi sai _Doctor Khalilullah_, sai Aysha, sai auta Nafeesa. "_Khalil_ kana jina kuwa." Fad'in
ya Abdul yana tab'a hannunsa ganin yayi zurfi a tunani. "No, babu komai ina zuwa." Fad'in _Khalil_ tare da
nufa part d'in Hajiya. Kai tsaye d'akinsa ya shige yana safa da marwa. Kwankwasa k'ofar d'akinsa aka yi, da
sauri ya juya yana kallon k'ofar. Hannu ya kai ya danna wani switch sai ga Laure ta bayyana akan screen d'in
dake saman k'ofarsa. Ajiyar zuciya yayi tare da nufa k'ofar d'akin ya bud'e, "Yaya _Khalif_ ina kwana?"
Saude ta fad'i a sanyaye don tun jiya take jinta wani iri ganin uwar d'akinta babu lafiya. "Lafiya k'alau ya
aka yi?" Ya amsa tare da jefa mata tambaya. "Hajiya ce tace in fad'a maka yau kar ka bar gidan nan akwai
bak'in da zasu zo anjima." Shuru yayi yana kallon Laure kamar ita ce Hajiyar, can kuma ya nisa tare da
fad'in, "Ok, to jeki." Yana gama fad'in haka ya rufo k'ofar tare da zama a bakin gado ya rik'e kai. Gaba d'aya
natsuwa ta bar jikinsa. Gabansa sai dukan tara-tara take yi. Bai isa sakawa cikinsa ko ruwan Lipton ba har
k'arshe sha d'aya yana nan zaune a d'aki yana sak'awa da warwarewa. Su aunty Maryam da Laure kuwa,
sai kaiwa da komowa suke yi a kitchen suna had'awa bak'i abinci. Nafeesa ta riga kowa zuwa kasancewar
ita mazauniyar Kaduna ce. Ana tayi aure a kabala shooting range. Hankalinta sosai ya tashi ganin halin da
mahaifiyarsu take ciki. Don har a wannan lokacin jiri hajiye take gani, kuma idanunta sunyi luhu-luhu
alamar taci kuka. "Hajiya dan girman Allah mai ke faruwa? Idan dai akan su uncle ne, dan Allah ki fitar da
damuwarsu a zuciyarki. Har kuka gama zaman ku da Papa bai saka maki ciwo ba, sai y'an uwansa ne zasu
buwayeki. Dan Allah Hajiya ki bari." Girgiza kai Hajiya tayi tare da fad'in, "Uhm, baza ki gane ba Nafeesa,
bari dai sauran y'an uwanki su iso. Ni ba akan y'an uwan mahaifinku bane. Da sune ne abun da sauk'i."
Shuru Nafeesa tayi tana tunani a zuciyarta to mai ya faru idan har ba su uncle bane. K'arfe sha d'aya da
mintuna arba'in, yaya Barrister ya iso gidan shi da matarsa aunty Khairat da yayansu uku, Sam'an, Sahla da
Nu'aima. Nan aka dunga oyoyo-oyoyo. Ko mintuna goma basu yi da zuwa ba, soja marmari daga nesa, LTG
Abdullah ya iso shi da Aysha da kuma tawagar sojojin da suka yiwa unguwar k'awanya. Don gaba d'aya
unguwar sai da suka shaida *_Lieutenant General Abdullah Nurudden Muhammad_* ya shigo unguwar.
Tun da _Khalilullah_ ya lek'o ta window ta can saman d'akinsa yaga uban sojojin sun gewaye gate d'in
gidan, wasu ma har ta cikin gidan yaji kamar an cire lakar dake jikinsa. Laure gaba d'aya ta rud'e don har
wani zawo-zawo take ji sabida ba k'aramin tsoro da shakkar _LTG Abdullah_ take yi ba. Don shi fuskansa
ma bata cika fara'a ba. Kai tsaye gaba d'aya suka wuce d'akin Hajiyar ban da _Khalil_ da ko lek'owa parlor
bai yi ba. Har k'asa k'asa ya _LTG_ ya duk'a gaban gadon da take tare da fad'in, "Hajiya ina wuni, mun same
ku lafiya? Ashe baki ji dad'i ba. To menene amfanin _Ibrahim_ a cikin gidan nan da ba zai iya kai ki asibiti ya
duba ki ba. Wallahi wani irin iskanci ne. Ina yaje?" Hawaye Hajiya ta soma yi tare da fad'in, "Ni na hana a
kai ni asibitin, don ciwon dake damuna, _Khalil_ d'in ne sanadiyarsa. Marmari, _Khalil_ ya b'ata mana
sunan famili. Ya rusa duk wani tarbiyar da muka ginasa akai. So mu had'u mu duka a parlor, bayan anci
abinci, sa muyi maganar." Kai a k'asa zuciyarsa na tafasa ganin mahaifiyarsa na hawaye yace, "Hajiya abinci
ba zai ciwu ba, har sai naji abunda yake damunki nayi maki maganinsa tukun." Gaba d'aya su Barrister,
Aysha da Nafeesa har da yaya Abdul suka ce, "Hajiya abinci tabbas ba zai ciwu ba har sai munji matsalarki."
"Ku aika Laure ta kira _Mu'azzam_ a d'akinsa ya fito mu tafi can parlor ayi maganar a can." Mik'ewa
Nafeesa tayi tare da nufa corridor d'in da zai sadata da d'akin yayan nata tana mamakin wani irin laifi ya
aikata da har Hajiya take cewa ta b'ata masu sunan family. "To ko zubar da ciki yake yi a asibitinsa?" Fad'in
Nafeesa cikin zuciyarta dai-dai lokacin da take knocking d'in k'ofar d'akina. Bud'ewa yayi, kallon fuskansa
kawai za kayi ka tabbatar yana cikin tashin hankali. Kuma ba komai ke d'aga masa hankalin ba irin fushin
Hajiya. "Nafeesa!" Ya fad'i a hankali yana kallonta. "Na'am yaya _Khalil_. Tun d'azu gaba d'aya muka zo
amma babu kai a wajen. Hajiya tace kaje parlour duk muna can." Fitowa yayi gaba d'aya tare da kullo
k'ofar yace, "Muje Nafeesa. Hankalina ne gaba d'aya a tashe. Har da ya Abdullah ko?" Gyad'a masa kai tayi
suna tafiya a jere tare da fad'in, "Yaya _Khalil_ wai don Allah mai ke faruwa ne Hajiya ta kira mu gaba
d'aya? Wani abun kayi ne?" Bai ce mata komai ba har suka k'ariso parlourn. Bai iya d'aga kai ya kalli kowa a
cikinsu ba. Neman waje tayi daga gefe ya zauna kansa a k'asa tare da fad'in, "Ina wuni ya Abdullah? Sannu
da zuwa ya Barrister. Kun zo lafiya?" Babu wanda ya amsa gaisuwarsa. Bai damu ba don dama ya san dole
hakan zata kasance. Ya Abdullah kuwa duk ba sai ainahin abunda _Khalil_ d'in ya aikata ba, sai jifansa yake
yi da wani irin mugun kallo. Su kad'ai ne a parlor, don ko Barrister da yazo da matarsa, tana can ita da
Y'ay'anta a part d'in ya Abdul-Hakeem. Sune kawai isu-isu a parlourn. Don maganar tasu tana buk'atar
privacy. "Abdul-Hakeem bud'e mana taro da addu'a." Fad'in Hajiya wacce ke hakimce a kan kujera tana
girgiza k'afa. Sai bayan yaya Abdul-Hakeem d'in ya gama addu'ar sannan Hajiya tace, "Na kira ku ne anan
wajen ba don komai ba, sai don saboda _Ibrahim_. Na san dukkan ku kun san bak'ak'en maganganu da
kuma zagi da nake jurewa daga wajen dangin ubanku. Tun yana da rai suka kafa min k'ahon zuk'a har ila
yau da ya kasance babu shi a raye. Kuma kun san cewa iyayenku suna son had'a _Khalil_ aure da Nina
wanda shi kuma yak'i bada fad'in kai a cewarsa bata da kamun kai ita mazinaciya ce." Da sauri yaya
Barrister yace, "Hajiya idan dai a kan wannan maganar ce ta Nina, to ba wai bane. Don ni da kaina na tab'a
ganinta a wani babban hotel a Kano ita da wani sa'an mahaifinta." Da k'arfi Hajiya tace, "Kayi min shuru! Ai
ita da _Khalil_ d'in zani ce ta tadda muje." Da sauri _Ya LTG_ yace, "Hajiya ban fahimta ba." Gyara zama
tayi tare da fad'in, "Yanzu kuwa zaka fahimta. Kai _Khalil_ yi masu bayani abunda ka aikata." Kansa a k'asa
gabansa na fad'uwa ya d'ago ya kalli Ya Abdullah, wata uwar hararar da ya watsa masa ya saka yayi saurin
sunkuyar da kai k'asa." Wani mahaukacin tsawar da yayi, ba _Ibrahim_ kad'ai ba, hatta ita kanta hajiyar sai
da ta tsorata. "Za kayi magana anan wajen ko sai na taso na taka cinyarka tayi dagwa-dagwa!" A razane
_Khalil_ yace, "Hajiya wallahi, tallahi wa billahil azim ba halina bane. Tsautsayine ya saka nayi mata fyad'e
har ta samu ciki." A mugun mamakance da bak'in ciki ya Barrister da ya Abdullah suka ce "Fyad'e!" Wani
mik'ewa _Lieutenant Abdullah Nurudden Muhammad_ yayi tare da isa inda _Khalilullah_ yake tare
da............

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

*_MATAR SAYYADEE_*
[30/09, 7:11 PM] Rahamanatu: Here are the list of my books:
👇
1. Anya uba nane?
2. Auren cikin gida (paid)
3. Ni da shi abu d'aya ne
4. Zina babbar bala'i ce
5. Bani da gata (paid)
6. Garwashi
7. Sai a lahira (paid)
8. D'an Faari (First born) (paid)

Wani irin murmushi mugunta ta saki bayan ta kalli goron fantar. Bud'ewa tayi tare da jefa duka kwayoyin
sannan rufe da k'arfi ta girgiza tare da saka shi cikin aljihun doguwar rigar dake jikinta ta nufi hanyar gida
cike da jin dad'i. Ko da ta shiga d'akin, bata samu Sarah a ciki ba lokacin Baba yayi kiranta tana d'akinsa
domin tattauna da ita game da batun aurenta da iyayen _Khalil_ suka yi. Sai ta ajiye fantar a dai-dai inda ta
san Sarah na shigowa zata gani sannan ta bar d'akin ta koma d'akin Lami inda ta same su duka a d'akin
suna tattauna game da zancen aure da iyayen _Khalil_ suka yi. "Kuma ke Lami sai ki yarda? Tabd'ijam!
Bayan kin hana d'aya daga cikin yin soyayya mai zurfi balle har hakan ya saka mu bujire maki wata ran
muce aure muke so. Ai kamar yanda muke zaune a gida har wannan lokacin, haka ita ma zata zauna babu
wani zancen aure." Fad'in Aina'u wacce ta tsinci maganar daga sama kawai ta tsumbula baki. "Kuji min
shegiyar yarinya! Ke da Naima wanene babba da har zaki bud'e baki kiyi wannan maganar. Ke da ko b'ari
baki tab'a yi ba cikin gidan nan har kyayi wannan maganar. Wai ma Lami tana da samari ne masu fita da
ita?" Fad'in Nuratu. "Ina fa!" Lami ta bada amsa a gajarce. "Har wani fad'i take kamar yanzu har yanzu
bamu yi aure. Dudu-dudu fa bata wuce sha bakwai sha takwas ba amma har take wannan maganar. To
Na'ima tace me ita da take da shekaru talatin da d'aya a duniya?" Dogon tsaki Na'ima taja tare da fad'in,
"Bar y'ar iska. Lami dube ni nan in baki shawara idan zaki amsa. Kin ga, kar ki sake kice zaki ja game da
batun auren Sarah da _Khalil_. Kin ga dai uban sojojin da suka zo gidan na d'azu, kuma da bakinki kike
bamu labari Y'ay'anta gaba d'aya hukumomine, daga soja, sai d'an sandar farin kaya da kuma lauya. Kuma
kin san akwai dukiya babu k'arya a wajen su. Wallahi Lami sai kin fi jin dad'i idan Sarah ta shiga gidan
matsayin mata ba dadiro ba. Kuma kince mana dagaske fyad'e yayiwa Sarah ba kanta ta kai ba. Yanzu idan
kika k'i amincewa, da zarar ta haihu karb'e y'ar ko d'an kawai za suyi, shikenan ku da k'ara ganinsu sai
Allah. Amma idan auranta yayi, arziki har mu sai mun ture don Sarah ba marowaciya bace kowa ya sani.
Maganar gaskiya idan ta fito a fad'eta ko yaya take." Shuru Lami tayi tana auna maganganun Na'ima.
Aina'u kuwa wani dogon tsaki taja tare da fad'in, "Wallahi idan har tsautsayi yasa aka yi wannan auren, sai
na zame wa Sarah bala'i daga ita har su dangin mijin nata." A zuciya tayi maganar. "Ke Na'ima, Saratu fa
tana da mugun hali. Ina tsoron kar ta shiga gidan arziki ta manta cewar nice wacce tayi sanadiyar zuwanta
duniya. Da ace zata iya shawo kanta kawai yayi ta d'ura mata ciki a waje yana kashe mata kud'i ni kuma ina
kula da yaran ina kame y'an currencyn zai fi min. Amma zuwan gidan matsayin matarsa sai inga kamar
akwai matsala. Don a irin kallon rainin da yaron yake min, sai inga kamar zai iya hana ni zuwa gidan ko
kuma ita ya hana ta zuwa nan d'in. Kuma tsaf ubanku zai goya masa baya." Marfu'a tayi karaf tace, "Kuma
wallahi Lami zai iya hakan. Don ko mu baki ga irin kallon da yake mana ba matsayin yayyin budurwarsa."
Gyara zama Lami tayi tare da fad'in, "To ya kuke ganin za ayi kenan?" Karaf Aina'u tace, "Lami, zubar da
cikin kawai za ayi!" Da sauri gaba d'aya suka kalleta tare da fad'in, "Baki da hankali ne Aina'u? Ai idan aka
zubar da cikin kamar rabasu aka yi. Halan baki san abunda baban wansu yace ba ko?" Fad'in Hassana.
Yamutsa fuska Aina'u tayi irin ban san komai d'in nan ba tare da fad'in, "Mai yace shi babban wan nasu?"
"To cewa yayi idan har aka zubar da cikin to babu aure tsakaninsu." Fad'in Lami. Tsaki Aina'u tayi tare da
fad'in, "To dama ba auren ake so a samu hanyar fasuwarsa ba?" "Ke dak'ik'iya ce wai? Idan har haka ta faru
ai fita za suyi daga harkan mu gaba d'aya kuma su hana shi _Khalil_ d'in zuwa gidan nan. Kin ga kenan anyi
two-zero babu ciki, babu auren." Murmushi Aina'u tayi tare da fad'in, "To ku saurare ni da kyau. Shin ke
Lami baki lura da irin son da shi _Khalil_ d'in yake wa Sarah ba? Idan da ace ba sonta yake yi ba, babu
abunda zai saka ya nemi gidansu har yazo ya samu mahaifinta suyi magana, kuma sannan ba zai tab'a
d'auko iyayensa ya kawo su gidan nan ba. Sannan da baya sonta ba zai tab'a yarda shine uban cikin jikinta
ba. Kar ki manta shi likitane. Da zai iya duk dabaru ya cire cikin ya kuma koreta. Idan ta nemi tona mata
asiri yayi amfani da dukiyarsa ya kulle ba ita kad'ai ba har damu y'an uwanta ko kuma ya kai mu kotu yace
zamu b'ata masa suna da sharri. Duk k'auna ce mai zafi ya kawo haka. Kuma wallahi kinji na rantse maki
Lami, da ace _Khalil_ bai son Sarah, babu abunda zai kawo shi, shi da iyayensa gidan nan a yau. Kuma a
gaban idanunsu ya dunga kwarara godiya bayan Baba da y'an uwansa sun amince ya auri Saratu." Hannu
Marfu'a ta bata suka tada tare da fad'in, "Shegiya k'anwata! Ina maki kallon k'aramar yarinya ashe
kwakwalwarki na ja. Na yarda da maganar Aina'u yasin Lami. Ko ya kuke gani y'an uwana?" Ta k'arisa
maganar tana kallon su Nuratu. Na'ima tace, "Ni dai maganar zubar da cikin nan har yanzu bai gama
kwanta min ba. Duk da kuwa zuciyata tana rawa akan wata rana Sarah zata iya juya mana baya sabida
mijinta. Babu wata shawara ce sai wannan Lami?" "Gaskiya ni dai babu a waje na." Fuska kumbure Aina'u
tace, "Shikenan Lami tunda ni kun d'auke k'aramar yarinya wacce shawararta bai da wani amfani. Idan
komai ya kwab'e maku nan gaba, zaku tuna wannan ranar wallahi." Tana gama fad'in haka ta tashi ta fice
tana mai dana sanin yin maganar zubar da cikin kasancewar basu amince da shawararta ba. Sarah zaune
gaban Baba tana hawaye, "Saratu, ba zan tilasta maki ki auri _Ibrahim_ ba, sai dai a matsayina na
mahaifinki, ina mai baki shawara da ki bawa zuciyarki hak'uri ki amince da wannan yaro don Shi kad'ai ne
rufin asirinki. Na yaba da hankalisa da kuma karamci irin na iyayensa. Kuma ina da kyakkyawar zato akan
zasu rik'e ki bisa amana tamkar y'ar cikinsu ba suruka ba." Jan majina Sarah tayi tare da fad'in, "Baba ba
kukan nake yi ba sabida ban son zab'in da kayi min, kukan farin ciki nake yi sabida zab'a min kai da Allah
yayi matsayin mahaifi. Wallahi ko mahaukaci ka zab'a min matsayin mijin da zan zauna dashi, zan amshe
shi hannu bibbiyu in kuma yi biyayya a gare shi. Nagode sosai Baba, Allah ya k'ara maka lafiya. Sannan nayi
maka alk'awarin yiwa _Khalilullah_ biyayya har k'arshen numfashina idan har Allah ya rubuta ni matarsa
ce. Bazan tab'a baka kunya ba Baba." Tausayi da k'aunar Sarah ya lullub'e Baba, "Allah ya maki albarka
Saratu, Allah ya saka maki da alkhairi ya kuma zab'a maki abunda yafi zama alkhairi a rayuwarki ya shirya
sauran y'an uwanki. Ubangiji ya jib'anci lamuranki. Je ki kwanta ki huta. Allah ya tashe mu lafiya." Da
"Ameen" Sarah ta amsa bayan ta matso masa da duk wani abunda za zai buk'ata cikin dare sannan ta fice.
Sai da tayi alwala a fanfo tukun ta nufi d'aki domin yin sallar shafa'i da wuturi. Tana shiga babu abunda
idanunta suka fara gani sai wannan robar fanta mai sanyi da Aina'u ta ajiye sai naso yake yi. Hakanan Sarah
taji bai wani burgeta ba. Sallaya ta shimfid'a tare da tada sallah. Tun bayan shigowarta d'akin Aina'u ta
shigo ya kai sau biyar amma tana ganin robar fantar a inda ta ajiye. Ji take kamar ta shak'o wuyar Sarah da
bacci ya kwashe bisa darduma ta d'ura mata wannan fantar. Da k'afa ta dunga shurin Sarah har sai da ta
farka, "Ga Fanta nan mai sanyi idan zaki sha. Na sayo ne d'azu domin in sha, sai kuma ya fitar min a rai. Ki
shanye ba sai kin biya. Tun d'azu dama ke na ajiyewa ganin duk gidan nan kece mai son Fanta." Bacci a
idanun Sarah ta mik'e zaune tare da fad'in, "Bar mi shi a wajen. Sai zuwa anjima nasha yanzu cikina a cike
nake jinsa." Ba tare da Aina'u tace komai ba ta fice haushi kamar ya kashe ta na rashin shan fantar da
Sarah bata yi ba yanzu. Tana fita daga d'akin wayar Sarah ta soma ringing. Kai hannu Sarah tayi tare da
d'auko wayar dake kan one sitter dake d'akin. Kallo d'aya yayiwa numbern ta gane _Khalil_ ne duk da kuwa
bata yi saving number d'in ba sabida 3 d'in guda shidda da ya k'are da numbers d'in. Sai da ta turo baki
sannan tayi picking tare da mik'ewa ta hau kan gadon sannan tace, "Assalamu alaikum!" Ajiyar zuciya
_Khalil_ ya sauke tare da fad'in, "Amin wa'alaikissalam amaryata. Har kin fara bacci ne baki jira naji yanda
kuke ba?" Bata ce masa komai ba sai ma mirginawa da tayi zuwa k'arshen gadon. "Baza kiyi magana ba?"
Ya fad'i yana mai gyara kwanciyarsa. "To ni mai zan ce? Bacci fa nake ji sosai." Ta fad'i tana mai lumshe
idanu." "To kiyi baccin ki mana. Na hana ki ne?" _Khalil_ ya fad'i yana murmushi. "To ta yaya zan yi bacci
bayan ka hana ni? Ka kashe wayar to sai in kwanta." "Wato kin manta da deal d'in mu kenan ko?" Ya fad'i
har da yiwa wayar hannunsa gwalo kamar tana ganinsa. Itama hararar wayar tayi tare da fad'in, "Tab! Ai
yanzu babu wani zancen deal kuma." Waro idanu yayi tare da fad'in, "Inji wa ya fad'a maki haka? To ni dai
har yanzu deal d'in mu na nan." Bata san lokacin da tace, "Duk da manya sun shigo cikin zancen?" Dariya
ne ta kama shi, amma sai ya gimtse tare da fad'in, "Da kin haihu zan yi abunda nace maki zanyi. Zan karb'i
baby na sai in fad'awa Baba na janye. Kin ga ai shikenan na zama mai cika alk'awari." Nan da nan Sarah taji
bacccinta ya washe har da tashi daga kwance ta zauna tare da fad'in, "To ni ya zanyi da Baba kenan bayan
nayi masa alk'awarin zan yi maka biyayya? Ni dai gaskiya a rushe....." Sai kuma tayi saurin yin shuru tana
mai toshe bakinta da hannunta. Dariyar da yake ta rik'ewa ta kufce tare da fad'in, "Ashe dai ana son
_Khalil_ d'in ake masa yanga." K'ok'arin yanke kiran take yi yayi saurin fad'in, "Kar ki fara ki yanke min waya
tunda ba ke kika kira ba, ni na kira ki." "To wai ni kai aljani ne? Ta yaya kasan yanke wayar zanyi?" Sarah ta
fad'i tana sauraran jin abunda zai ce. "Da motsin hannunki na gane. Kar kiji tsoro _Khalil_ d'inki ba aljani
bane. Yanzu dai yaya kike?" "Lafiya." Ta bashi amsa kai tsaye. "Menene wani Lafiya! Sai kace yak'i. A haka
ne zaki min biyayyar da kika ce kin yiwa Baba alk'awari." "Ni dai to ai babu abunda nayi maka. Tambayata
kayi ni kuma na baka amsa." Ta fad'i tana mai lumshe idanu do hirar tana mata dad'i, hatta d'an bacci da
take ji sai da ya gudu. "Hirar na maki dad'i ko?" "inji wa?" Sarah ta fad'i da sauri don mamaki _Khalil_ yake
bata kamar wani aljani. Shi kuwa ya dai fad'a ne kawai don yaji mai zata ce. "Saurara in yi maki wata wak'a
kiji." Yana fad'in haka ya soma fad'in, " _Ina kewaaa ina kewar masoyiya! Ina kewaaa ina kewar aminiyaa!!
Abokiyar shawara, kece kin d'ara, kin sab In ba dake ba sai in hak'ura. Ki bani y'ar dama, a san dani nima, ki
mini alfarma ki sanya ni a zuciya. Ki kau da y'an gulma, irinki ke nema, suna ta shan famaaa sun zaga ko
ina. Mace ba ai ba kece, kuma kin san mun dace, a kanki na zauce! Magana d'aya ba shakka, hannu d'aya
kan jinka, ta yaya zai d'auka, samunki baiwaa ce. Bakya fushi, ki murmushi, don sanki na shiga raina, ko
babu ni in kin tunani wannan shine muradina. Nasan kina da buri kuma sannan kina da tsaarinki, da zaki sa
cikin ranki, nine zan zama angonki. Farar tumfafiyata, daban cikin mata, a sonki nai rata a kanki na gane
kaina. Kece nai wa alk'awari, mace d'aya kuma kin zarce d'ari, kin zam min bangon sukari, ko a ina kece.
Sirrin ciki yazo fili, kin iya ado da d'an kwali, mai kyan ido da sa kwalli, an iya miki zanen lalli. Tun da na
same ki na huta, saura sunka nazarta, bana iya kallon mata kiji kalmar dana furta. Akwai dad'i abunda kake
so in ya soka, shi fatan da kakewa wasu sai ya bika. So sa'a ce, samun nasarace, ke sa ai daceee, ni kam na
samu. So akwai tsada, sanyi sai randa, shanu ke hud'a furar mu nai damu. Nai nasara samunki, barni na
zam jigonki, zan b'oye sirrinki ba ran da zan tona. kewa, keee, kewa! Ina kewaa, ina kewar masoyiyaaaaaa!
_" Gaba d'aya ya gama kashe mata jiki da zazzak'ar muryansa, sai taji wak'ar ma a bakinsa yafi dad'i kamar
shi ya rera ba auta wazirin ba. "Ka tab'a shiga studio ne?" Ta jefe shi da tambaya. "A kanki dai zan fara
_mine_" "Kuma ka iya wak'ar sosai wallahi." Sosai yaji dad'in yabawa da tayi har sai da ya saki siririyar
murmushi tare da fad'in, "Kullum zan rik'a rera maki wak'ok'i kala-kala a kunnanki idan kika dawo kusa
dani. Kina so?" "Ni dai babu ruwa na Allah!" Dariya ta bashi kuma sai da ya daran kamun yace, "Da aka yi
me?" "Ai dai babu kyau irin maganganu da kake yi" d'aga idanu sama yayi tare da fad'in, "Wanne kenan a
ciki?" Ya fad'i yana k'umshe dariyarsa. "Oho!" Ta fad'i don ta gane so yake ta maimaita mai yace. "To yanzu
dai abunda nake so dake, ki d'aura hannunki a kan cikinki kiyi addu'a sosai, sannan kiyi addu'ar bacci ki
kwanta. Will call you in the morning kamun na tafi asibiti. Bye I love you." Yana gama fad'in haka ya katse
kiran tare da rungume wayar yana jin kamar Sarah ya rungume ita da cikin dake jikinta. Allah ya d'aura
masa k'aunar wannan ciki. B'angaren Sarah itama wani murmushi ta saki bayan ya katse wayar. Sai
muryansa yake tayi mata echoing a cikin kanta lokacin da yake rera mata wak'ar kewa na auta waziri. Cike
da farin ciki bacci mai dad'i ya kwashe ta bayan tayi addu'a kamar yanda ya umarceta. Aina'u kuwa ko da ta
sake shigowa d'akin taga Sarah nata sharar bacci kuma bata sha fanta ba, sai taji kamar ta danna mata
pillow ta mutu kowa ya huta. Fita tayi bata sake dawowa ba sabida yanda ta shak'a. Da asubahi Sarah ta
tashi domin yin salla, babu kowa a d'akin don duka yayyin nata ba gida suka kwana ba. Tana jiyo kukan
Fadwa daga d'akin Lami sabida ba'a yayeta ba haka Marfu'a take tsallaketa ta barta wajen Lami ta tafi
gantalin da ta saba. Fitowa Sarah tayi ta kama ruwa sannan ta d'auro alwala. Sai da ta dubo Baba taga
shima ya d'auro alwalar sannan ta koma d'aki dan yau bata yi gigin zuwa d'akin Lami domin tada su ba.
Bayan ta idar da sallah, wani baccin ne ya kuma fizgarta. Kiran da _Khalil_ yayi mata ne ya farkar da ita.
Amsa wayar tayi cike da muryan bacci tana fad'in, "Ina kwana, an tashi lafiya?" Daga can _Khalil_ yace,
"Lafiya k'alau. Halan baki tashi ba?" Gyara kwanciyarta tayi tare da fad'in, "Kiran wayarka ne ta farkar
dani." "I'm sorry ki koma baccinki. Amma kuwa ki sanar da Baba zuwa anjima wasu zasu kawo kaya. A fitar
da duka abubuwa dake cikin dak'unan gidan please. D'akuna uku ne ko?" Da "Eh" Sarah ta amsa tana
mamakin mai kuma za'a kuma kawo masu a gidan. "Yauwa to ki koma barcinki. In Sha Allah by 11:00am
zasu zo." "Allah ya kawo su Lafiya." Sarah ta fad'a shi kuma ya yanke wayar tare da saka safa sannan ya
saka takalmi dama kuma abunda ya rage ya saka kenan ya fito daga d'akinsa ya kulle ya nufi d'akin Hajiya.
Sai da ya kwankwasa sannan ya turo ya shiga. A zaune a gefen gado ya samu hajiyar sai ninke kayan
sawanta take yi. "Ina kwana hajiya?" Lafiya kawai tace masa tare da cigaba da abunda take yi don har
yanzu haushinsa take ji. "Hajiya ina Laure da kike wannan aikin da kanki." "Tuni ta koma gidan ubanka da
zama. Tashi ka fice ka bani waje. Sha-sha-sha kawai." Da sauri ya mik'e yana mai fad'in, "Allah ya huci
zuciyarki Hajiya. Sai na dawo." Ko kallonsa bata kuma yi ba har ya fice sai a sannan ta d'ago ta watsawa
bayansa harara. Bai had'u da kowa ba kasancewar ko k'arfe takwas na safe bai yi ba. Kai tsaye wajen
motarsa ya nufa tare da shiga yayi reverse ya fice daga gidan zuwa asibiti. Sarah kuwa bata iya komawa
bacci ba ta sauko daga kan gadon ta nufi d'akin Lami. Sai da tayi sallama sannan ta shiga, a zaune ta samu
Aina'u tana shan tea da, bread da kwai. Gefe kuma Lami ne sai gyangyad'i take yi don bata samu bacci ba
jiya sabida damunta da kuka da Fadwa tayi tayi jiyan. "Ina kwana Lami." Lami bata amsa ba sabida wani
gyangyad'i mai dad'i da ya kwashe ta. "Lami." Karo na biyu Sarah ta kuma kiran sunanta, firgigit ta farka
har miyau na zubo mata daga baki. "Wannan wani irin iskanci ne haka Saratu? Ya zaki tashe ni kuma na san
kin san ban samu ishashshen bacci ba jiya." "Kiyi hak'uri, dama _Khalil_ ne yace in fad'a maku a fitar da
duka kayan d'akunan gidan b'aki za suzo anjima." Tuni Lami ta watstsake tare da fad'in, "Da gaske kike yi
Sarah. Wayyo Allah arziki yazo mana har cikin gidan mu. Maza tashi Aina'u a fara aiki tun yanzu kamun
sauran y'an uwanki su dawo." Tsabar bak'in ciki Aina'u ko magana bata yi ba sai ma mik'ewa tayi ta bar
d'akin don ji tayi bread d'in da ta saka a baki d'aci yayi mata kamar tana taunar magani. Lami kuwa tashi
tayi ta soma fitar da wasu kayan. Ganin Aina'u ba taya ta za tayi ba, sai ta fita ta kira almajirai suka shiga
fitar da kaya. Sai da suka fitar da kayan d'akinta kaf sannan suka soma fitar da na Baba kasancewar Sarah
taje tayi masa bayani. Zuwa k'arfe goma sun gaba fitar da duka kayan gidan har da nasu d'akin Sarah. Lami
tsabar zari har ta kira dillaliya ta saye gado da katifar d'akinta da na Sarah. Taso had'awa har da katifar
Baba amma ya hanata. Sai da hakan ya kai su ga rigima har Lami na zaginsa tana kiransa matsiyaci. Lokacin
da sauran y'ay'an nata suka dawo suka ga gaba d'aya babu komai a d'akunan gidan suka shiga tambayar
ba'asi. Nan Lami ta shiga fad'a masu cewar ai _Khalil_ ne zai kawo masu sabbin kayan d'aki yau shiyasa aka
fitar da komai ta sayar. Sarah kuwa mamaki ne ya cika ta ko yaushe suka yi hakan da Lami d'in. Ita dai ta
san _Khalil_ ce mata kawai yayi a fitar da kayan d'akunan gidan. Gaba d'aya su Na'ima suka hau murna
banda Aina'u da ta bar gidan sabida mugun hali. K'arfe sha d'aya dai-dai kamar yanda _Khalil_ ya fada sai
ga tsayuwar motar company a k'ofar gidansu Sarah. Kwalaye suka dunga shigowa dasu suna ajiyewa a
tsakar gidan. Sai da suka gama kwaso kayan tsaf sannan suka tambaya inane d'akin Baba. Da hannu Sarah
dake tsakar gidan ta nuna masu, caraf Lami tace, "Wallahi tallahi babu uban da ya isa, da d'aki na za'a fara.
Ai ni ce na sha wuyar mak'uda ba shi ba." Ma'aikatan ba tare da musu ba suka d'auki kwalayen tare da
shiga d'akin Lamin da aka share tsaf aka goge, don ita d'akinta akwai tiles. Cikin mintuna talatin saboda
kwarewarsu har sun kammala had'a gado da komai. D'akin ba k'aramin kyau yayi ba. Gadon kalar b'aki da
purple. Wardrobe d'in kuma irin mai cin bangon nan ne mai k'ofa shidda. Hatta labule sabo suka saka mata
sannan suka mak'ala mata TVplasma sannan suka fita suka koma d'akin Baba. Shima haka suka jera masa
nasa kayan irin na Lami sak sai dai akwai bambamcin launi. Shi nayi farare ne k'al. Kuma kamun su saka sai
da suka shimfid'a masa lallausar carpet da ya mamaye d'akin mai tsada kalar blue-black. Sannan suka saka
masa TVplasma irin flatscreen d'in nan wanda kud'insa zai kai 250k zuwa 300k, dama kuwa akwai masu
had'a dish a waje kuma har sun kammala, sai kawai suka shigo suka yi settings kasancewar ko wani d'aki
yana da decoder d'insa. D'akin Baba har da tvstand mai kyau. D'akin su Sarah suma ab had'a masu nasu
furniture d'in wanda ga kasance white and baby pink. Kuma gadonsu six by seven ne yayin da su d'akin
Baba ya kasance six by six. Gaba d'aya gidan sai ya koma kamar gidan amare. Komai sabo. Don har da
dank'areran deepfreeze da kuma fridge _Khalil_ ya siya masu. Wajejen k'arfe biyu suka kammala komai
suka wuce. Lami kuwa sai uban gud'a take yi. Lokacin da ta shiga d'akin Baba domin taga irin nasa gyaran,
sai bak'in ciki ga rufe ta ta shiga surfa bala'i mai yasa ita ma ba'a saka mata Tvstand stand ba. Baba
kasancewar baya son tashin hankali yace ta d'auka ta kai d'akinta. Babu kunya kuwa ta kama ita da Nuratu
suka mayar d'akin nata. Aina'u kuwa ba ita ta dawo gidan ba, sai bayan magriba. Tana sauka daga napep
ta taras da zambad'ed'iyar motar _Khalil_. Wani mugun tsaki ta saki tare da isa k'ofar gidan ta tura ta shiga
kuma a dai-dai lokacin ta hangi bayan _Khalil_ d'in zai shiga d'akin Baba. Tsayawa tayi tana k'arewa
d'akunan kallo ganin ko Wanne da sabbin labulaye. Dai-dai nan Sarah ta fito daga bayi hannunta rik'e da
buta, tazo dai-dai inda Aina'u take, sai ta saka mata k'afa tayi wani irin mugun fad'uwa, ji kake tim. "Inna
lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Sarah ta fad'i da k'arfi tana mai kai hannu k'asan mararta. Aina'u kuwa sai
tayi saurin sunkuyawa tana fad'in, "Sannu Sarah, garin yaya kika fad'i haka." Gaba d'aya gidan suka fito,
_Khalil_ ya riga kowa fitowa da gudu jin muryan Sarah tana salati. Ita kuwa Sarah sai cewa take "Inna lillahi
wa'inna ilaihir raju'un, cikina, wayyo Allah cikina." Rintse idanu _Khalil_ yayi da k'arfi ganin zini na
gangarowa daga k'afafunta...............

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

*_MATAR SAYYADEE_*
[30/09, 7:11 PM] Rahamanatu: _Jinjina a gare ku my fans, kuna nishad'antar dani musamman y'an
K'ANWAR MATATA comments section, irin su my besty (Queen Zarah), Rahamanatou, Oum Muslim, Mrs
dimples, Halimatouu, Maman auwal k'awata, Jik'amshi collection, Mrs Z A musawa, Hadiza Mbello,
Tatiesha Rufa'i, My Rabi'a, Yayata maman Islam, Babyshamas, da abokiyar fad'ata Ummu Muhammad da
sauran da basu ji sunasu ba duka. Ina maku sonso. Allah ya bar k'auna mutanan Lami da Aina'u😜_

Ba tare da jin wani kunya ba _Khalil_ ya ciccib'i Sarah yayi waje da ita Lami biye dashi ita da Nuratu da
Na'ima. Aina'u kuwa wani irin murmushi jin dad'in hak'arta ta cimma ruwa duk da bata tab'a kawo cewar
abunda ya faru da Sarah zai iya faruwa da ita ba sanadiyar fad'uwar da tayi. Ita tayi ne kawai sabida
mugunta. A baya ya shimfid'ar da ita, da sauri Lami da su Na'ima suka shiga cikin motar, _Khalil_ kuma ya
zagaya ya shiga mazaunin gaba tare da tada motar ya bar unguwar da gudu ganin ba k'aramin jini ke zuba
daga jikin Sarah ba. Baba kuwa kamar ya fashe da kuka, gashi babu k'afar bin bayansu. Sai dai abunda yayi
matuk'ar bashi mamaki ganin Aina'u tana bin jinin Sarah da ya zuba a k'asa tana wani dariyar k'ata. Kwata-
kwata bata lura da Baba dake bakin k'ofa yana kallonta ba. "Aina'u kar dai kece sanadiyar abunda ya samu
y'ar uwarki yanzu?" Da sauri ta kalli inda baban yake a tsaye tare da fad'in, "Da aka yi yaya kenan Baba?
Shikenan babu damar nayi dariya. To ni dariyata wani abu take nufi can daban." Juyawa Baba yayi tare da
komawa d'akinsa don ya dad'e da sanin Aina'u ba k'aramar muguwar yarinya za ayi ba. Sai tace Lami bata
yi komai ba a duniya. Amma abunda har yanzu ke bawa Baba mamaki shine, don me za tayi hakan? "Ya
ubangijin sammai da k'assai, ga Baiwar ka nan ka jib'anci lamuranta. Allah ka bata lafiya." A bayyane yayi
maganar yana mai d'aga hannu sama. A can asibiti kuwa, gudun laifi, tun kafun ya k'arisa ya fiddo baya
tare da danna kiran number Hajiya domin shaida mata abunda ke faruwa. Don babu abunda gabansa ke yi
sai fad'uwa ganin jiya-jiya suka gama kankara masa warning akan kar ya kuskura yace zai cire cikin dake
jikin Saran. Ringing uku Hajiya ta d'aga tare da fad'in, "Assalamu alaikum." "Amin wa'alaikissalam, Hajiya
dan Allah ki saka driver ya kawo ki asibitina yanzu. Saratu ce ba lafiya gamu tare da y'an uwanta zuwa
asibiti. Fad'uwa tayi kuma jini ya b'alle mata." Da sauri Hajiya ta soma fad'in, "Inna lillahi wa'inna ilaihir
raju'un! Ai babu wani driver da zai kawo ni, tunda ga Muhammad Kabir a gida, bari na kira na fad'a masa
abunda ke faruwa sai ya kawo ni." "To Hajiya nagode." Yana fad'in haka ya katse wayar tare da cigaba da
driving da gudu yana yi yana juyowa yana kallon Sarah da ta jima da fita cikin hayyacinta sabida irin jinin da
take zubarwa. Suna isa asibitin ya fito da sauri tare da bud'e gidan ya kuma ciccib'ota gaba d'aya jinin
jikinta ya gama b'ata jikinsa amma ko a jikinsa. Cikin asibitin ya nufa da ita don ko tsayawa nurses su
gunguro gadon marasa lafiya bai yi ba. Doctor Hayat, Doctor Nurain da doctor Kamal sune suka amshi
Sarah tare da shiga da ita emergency kuma suka hana _Khalil_ shiga sabida ganin yanda ya rud'e, koma ya
shigan ba wani abu zai iya yi ba. Mintuna goma tsakani sai ga Hajiya ita da aunty Maryam, aunty Khairat
matar ya Barrister da shi kansa Barrister d'in. "Ina uwata take?" Fad'in Hajiya lokacin da ta k'ariso. Waro
idanu tayi ganin gaba d'aya jikin _Khalilullah_ ya b'aci da jini. "Subhanallah!" Hajiya suka fad'i a tare ita da
au aunty Maryam. Yaya Barrister kuwa cewa yayi, "Garin yaya haka ta faru?" _Khalil_ kuwa sai danne
hawayen dake taho masa yake yi tare da fad'in, "Baban ne yace tayo masa kira na yana son magana dani,
to naje ko zama ban kai ga yi ba, sai kawai jin talatin ta muka yi. Gaba d'aya muka fito muka taras da ita
kwance a k'asa jini na zubar mata." Fuska cike da damuwa hajiya tace, "Kai Inna lillahi wa'inna ilaihir
raju'un! Fad'uwa tayi kenan? Allah ya bata lafiya alfarmar ubangiji. Kai jama'a ni Mai gado!" Fad'in Hajiya
tana da zabga tagumi. Can kuma ta kalli _Khalil_ tare da fad'in, "Ka d'auke kaje gida ka canzo kaya sai ka
dawo. Gaba d'aya jikinka ya b'aci da jini." " _Hajiya_ dan Allah kiyi hak'uri wallahi bazan iya yin ko taku
d'aya ba har sai naga halin da baiwar Allah nan take ciki." Kallon Hajiya Barrister yayi tare da fad'in, "No,
Hajiya kyale shi bari naje gidan na d'auko masa wasu kayan sai ya canza a cikin office d'insa." "Yauwa Allah
yayi maka albarka. Maza je ka d'auko masa." Fad'in Hajiya. Aunty Maryam da aunty Khairat so suke su
tambayi wacece babu lafiya, amma babu fuska wajen kowa don kowa cike yake da tashin hankali kar ma
ace _Khalil_. Har yaya Barrister ya dawo daga gida ya kawo wa _Khalil_ kaya babu labarin Sarah. Sai da
Hajiya tayi jan idanu sannan ya karb'i kayan ya nufi office domin canzawa. Sauri-sauri ya wanke jikinsa
sannan ya saka kaya tare da fitowa. Duk k'aunarsa da turare yau ya manta anan saka wani abu wai shi
turare a jiki. Nufa k'ofar emergency d'in _Khalil_ yayi gadan-gadan don ya gaji da tsayuwar gawon shanu.
"kai! Maza dawo nan ka barsu suyi aikinsu. Idan ma ka shiga, mai za kayi." Fad'in Hajiya. Dawowa _Khalil_
yayi dai-dai lokacin da doctor Kamal shi da doctor Hayat. Da sauri ya nufeso tare da fad'in, "Ina Matata?
How is she?" Da mamaki gaba d'aya suke kallonsa sabida Kalmar wife da ya kira don sun san bai da wata
mata. Amma sai suka shanye mamakin. Doctor Kamal bai yi magana ba, doctor Hayat ne yace, "She's
conscious now, amma tana buk'atar jini sabida ta zubar da jini da yawa. Sannan kuma I'm sorry to say, "She
loose the baby. Babu cikin!" Zamewa _Khalil_ yayi ya duk'a a wajen tare da rik'e kansa yana nanata Inna
lillahi wa'inna ilaihir raju'un! "Kai, dakta mai ke faruwa?" Fad'in Hajiya ganin yanda _Khalil_ ya duk'e tare
da kama kai yana salati. Barrister ya soma yi mata bayani don yaji komai, "Hajiya ita uwar ta farfad'o, sai
dai tana buk'atar jini sabida ta zubar da jini da yawa, sannan kuma an rasa cikin jikinta." "La haula wala
quwata illah billahi. To Allah yasa hakan shine alkhairi. Sai ayi gaggawa bata jinin ko. Amma kai dakta, ka
tabbatar ba wani abu tasha ba cikin ya zube?" Fad'in hajiya tana kallon doctor Hayat. Girgiza kai doctor
yayi tare da fad'in, "Gaskiya Hajiya babu wani abun da tasha wanda yayi sanadin fitar ciki. Mahaifar dama
bata yi wani kwari ba. So sanadin mummunar fad'uwar da tayi ne ya jawo hakan." Dogon ajiye zuciya
Hajiya ta sauke, don ta riga ta raya a zuciyarta in dai har zubar da cikin nan aka yi, to fa har abada d'anta ba
zai auri Sarah ba ko da kuwa _Khalil_ d'in ne ya zubar da cikin. Mik'ewa _Khalil_ yayi tare da shiga cikin
emergency d'in don har a lokacin ba'a fitar da ita zuwa ward ba. Kallonta ya dunga yi ganin lokaci k'ank'ani
har tayi wani irin mugun rama tayi haske. Da sauri ya juya ya fita tare da nufa lab domin a d'ibi jininsa don
jininsa irin wanda zai iya bawa kowa ne idan aka cire O-negetive. Leda biyu aka d'iba a jikinsa. Tuni har an
maida Sarah d'akin hutu an kuma d'aura mata jinin _Khalil_. Lami kuwa da y'ay'anta sai tararrabi akan
hukunci da za su yanke ganin cikin jikin Sarah ya zube. Lami kwata-kwata damuwarta ba rashin lafiyar
Sarah bane. Damuwarta d'aya kada jin dad'in nan da suka soma samu a jikin _Khalil_ ya yanke sakamakon
zubewar cikin jikin Sarah d'in. Sam basu gane yanayin Hajiyar ba, don fuskanta babu yabo kuma babu
fallasa. Hajiya bata bar asibitin nan ba, sai da Sarah ta farfad'o sosai har tana ina gane kowa da kowa
lokacin har anyi sallar magriba. Amma su Aunty Maryam tuni ya Barrister ya maida su gida sabida girkin da
za'a kawo nan asibitin. Ya Abdul-Hakeem ne ya kawo abincin a cikin manya-manyan kula masu matuk'ar
tsada sannan ya d'auki Hajiya ya mayar da ta gida. _Khalil_ kuwa sallar magriba ce ta fitar dashi, don tun
tuni yana gefen Sarah tana yin motsi yake soma tambayarta ko wani wajen nayi mata ciwo. Sarah kuwa tun
da ta samu labarin cikin dake jikinta ya zube, wani irin numfashin rahama da natsuwa ta sauke tana mai
godewa ubangiji don ita kad'ai ta san halin da take ciki. Sam bata son shiga cikin sahun y'an uwanta na
ajiye d'a ko y'ar shege. "Allah na gode maka da ka cire cikin ta hanyar mafi sauk'i. Allah na gode maka."
Duk a cikin zuciya tayi maganar. Baba kuwa na can hankalinsa a tashe jin babu wani feedback game da
Sarah. Sai da yayi kamar zai yiwa Aina'u kuka sannan ta kira masa Lami kasancewar shi bai da waya. Shi
d'in ma sai da ya bata dubu d'aya sannan ta kira. Bayan sun gama waya da Lami ta fad'a masa halin da ake
ciki, sai ya mik'awa Aina'u wayar dake tsaye tana jin matsanaicin farin ciki jin ciki ya zube. "Shegiya! Ai nayi
wa kaina alk'awarin sai na raba ki da _Ibrahim_. Wallahi ba zan bari ki shiga gidan na ba. Mayya kawai!"
Tana gama fad'in haka ta juya ta fice daga d'akin tare da komawa nasu d'akin ta kwanta a kan gado tare da
jawo ledar tsire mai kulin da ta siya ta hau jefawa a baki tana tauna tana lumshe idanu. A can asibiti kuwa,
wajajen k'arfe tara da rabi, bayan su Lami sun gana hani'an da abincin da Hajiya ta saka su aunty Maryam
suka yi, sai _Khalil_ yace masu ya kamata su tashi ya kai su gida, don mutum d'aya aka amince ya kwana da
majinyaci. "Lami tunda ga yara a gida, ku tafi kawai ke da Nuratu, ni zan kwana anan da ita." Lami ji tayi
kamar ta shak'o Na'ima, amma jin abunda _Khalil_ yace sai tayi shuru. "Eh hakane. Mama ke ki koma gida,
ita sai ta kwana da itan. Idan yaso gobe sai ku dawo da safe. Dare nayi. Muje na sauke ku a gida." Fita Lami
tayi ba tare da ta k'ara cewa komai ba. Don gani take kamar wani abun dad'in Na'ima zata ci idan ta tafi. Ko
kuma _Khalil_ d'in yayi mata wani kyauta. Har gida ya sauke su tare da shiga wajen Baba ya kwantar masa
da hankali tare da shaida masa in Sha Allah nan da wasu y'an kwanaki Sarah zata warware. Hajiya tana isa
gida ta d'aga waya ta kiran number d'in ya Abdullah. Kamar kullum ya yanke kiran tare da kiranta.
"Assalamu alaikum, marmari sai kaji abunda ya faru ko?" Fad'in Hajiya. "Wa'alaikissalam, Muhammad
Kabir ya kira ni ya fad'a min komai, amma Hajiya an tabbatar da a asibitin ba wani abu tasha ba? Don jiya
kamun na bar Kaduna sai da na wakilta wad'anda zasu min bincike yarinyar. Kuma binciken ya iske ni tun a
jiyan. Hajiya maganar dai babu dad'in ji, don sai da nayi dana sanin amincewa da wannan maganar auren.
Don fisabilillahi gaba gidan tun daga kan uwarsu babu tarbiya. Dama-dama ita yarinyar ma, an samu
mutane hud'u zuwa biyar da suka yabi halinta." Shuru hajiya tayi tana sauraran ya Abdullah kamun tace,
"To marmari ya za muyi, _Khali_ dai ya riga ya jawo mana magana. Tunda har yaji ya gani, kuma ita
yarinyar ta samu shaida ko yaya ne, hakanan za muyi hak'uri ayi auren kawai don nan gaba bamu san wani
irin magana zai je ya d'auko mana ba. Kuma maganar ciki, dagaske b'ari tayi amma ba ta hanyar shan
magani ba. Allah ne ya kawo hakan ta sanadin fad'uwa da tayi." Ajiyar zuciya ya Abdullah yayi tare da
fad'in, "To shikenan Hajiya. Tun da har hakan ya kasance, ba sai an d'au wani dogon lokaci ba, da zarar
Yarinyar taji sauk'i, zan zo Kaduna sai muyi magana dasu uncle Ridwan sai aje a kai kud'in auren." "Kaga
inda matsalar take kenan. Allah yasa dai kar su tada k'ananun maganganu dai!" Fad'in Hajiya, "Ki kwantar
da hankalinki, in Sha Allah baza a samu matsala ba." "To Allah yasa!" Fad'in Hajiya. A can asibiti kuwa, sai
da gaba d'aya nurses suka fahimci Sarah budurwar _Khalil_ ce sabida yanda yake nan-nan da ita. Kwanan
Sarah uku a asibiti, amma ko sau d'aya Aina'u bata tab'a zuwa dubata ba. A asibitin nan kuwa, wani irin
soyayya ce da shak'uwa mai zafi ta shiga tsakanin Sarah da _Khalil_ ta yanda har idan bata ganshi ba, ta
dunga kallo agogo tana kuma duban hanya. Da taji motsin bud'e k'ofa take saurin kai idanunta wajen.
Satinta biyu aka sallameta, baza ka tab'a cewa daga ciwo ta tashi ba sabida wani irin haske da kyau har da
d'an k'iba da ta k'ara. Cike da murya da farin ciki ta isa d'akin Baba tana mai jin kewarsa. Abunda ya bata
mamaki ganin Baba a tsaye babu sandar da yake dogarawa. Da mamaki take kallon Baba har da zagaya shi.
Dariya yayi tare da fad'in, "Bar mamaki Sarah, mahaifinkin ne dai a tsaye gabanki. Kin ga ikon ubangiji ko?
Allah dai ya yiwa _Ibrahim_ albarka domin shi ya zo ya d'auke ni ya kai nj asibitinsa na k'ashi aka duba
k'afata. Kuma har gida kullum ake zuwa ana min gashi. Kuma Alhamdulillah k'afar ta soma warkewa don
yanzu haka zan iya zagaye tsakar gidan nan babu sanda." Da matsanaicin farin ciki Sarah ta soma fad'in,
"Alhamdulillah! Alhamdulillah!!, Allah mun gode maka. Baba Ashe zaka samu lafiya? Kai Alhamdulillah."
Baba yace, "Ki godewa ubangiji sannan ki godewa _Ibrahim_ Saratu. Domin sanadinsa ne kika ganni a haka
yau a gabanki. Saratu don girman Allah, kiyiwa yaron nan biyayya, babu abunda za kiyi ki b'ata min rai
Sarah kamar ki k'i yin zaman lafiya dashi. Hakan zai b'ata min rai kuma zan rik'e ki a zuciya domin yaron
nan ya gama yi mana dukkan alkhairi shi da iyayensa." Sarah wani irin matsanaicin soyayyar _Khalil_ ne taji
yana hud'a ko wani sak'o da lungu na zuciyarta. D'ukawa tayi tare da fad'in, "Baba nayi maka wannan
alk'awarin na zama da _Khalil_ da zuciya d'aya, kuma ko da sab'ani ya shiga tsakanin mu wata rana, ba zan
tab'a juya masa baya ba. Kuma ba zan tab'a rabuwa dashi ba har sai idan shine ga gaji da zama dani."
"Allah yayi maki albarka Saratu. Allah yasa auren da za kuyi mutuwa ce zata raba shi." Sai da Sarah ta saka
gyale ta rufe fuskanta sannan tace, "Ameen" tare da mik'ewa ta fita daga d'akin ta koma nasu d'akinsu ta
d'auko wannan turaren da _Khalil_ ya bata tare da fesawa sosai sannan ta canza hijjab ta saka wani don a
waje suka bar _Khalil_ d'in. Sarah tayi alk'awarin yau zata bayyanawa _Khalil_ baki da baki cewar tana
sonsa. A tsaye a k'ofar gidan ta same sa yayi folding hannunsa yana kallon k'ofar gidan. Tana fitowa ya saki
ajiyar zuciya tare da fad'in, "Har na k'agu ki fito." Murmushi tayi tare da fad'in, "To ba yanzu muka rabu
ba." "To ba kece kika ce kar na wuce na jira ki ba. Na k'agu inji mai zaki fad'a min." Murmushi ta k'ara yi
karo na biyu tare da fad'in, "Wai sanyi kake ji?" Harararta yayi tare da fad'in, "K'arshen sanyi, a Atlanta
nake." Dariya ta saki wanda ya k'ara bayyanar da bayyannar kyawunta, gaba d'aya kumatunta sai da suka
lob'a. "Ban da Allahn musuru, amma ina ji a jikina da d'a ko y'ata ya fito duniya, da dake zai yi kama sak. Ke
kyakkwa ce." Rufe fuska tayi da hijjab d'inta tare da fad'in, "Har na kai ka kyau? Kai fa kama kake min da
wannan matashin kudancin indian _Ram Charan_" waro idanu _Khalil_ yayi tare da fad'in, "Haba dai! Ke
kuma kin san dawa kike kama, _Aishwarya Rai_, wallahi kin ma fita kyau." Rufe baki Sarah tayi tare da
fad'in, "Kar ka yarda Na'ima taji, don ita ce aka cewa suna kama da Aishwarya." "Wa, to ai kin fita kyau
wallahi." Dariya tayi tare da fad'in, "Beauty is in the eyes of the beholder." "Eh d'in naji, ko ma dai menene,
ke d'in kyakkyawa ce kuma ta musamman. Wani albishir za'a fad'a min ne aka hana ni tafiya gida." Sai da
Sarah tayi farr da idanu sannan tace, "Abunda kake muradin ji kullum daga baki na kuma fuska da fuska."
Gyara tsayuwa yayi tare da fiddo wayarshi ya danna recording ba tare da ta san me yayi ba. "Gwara in
gyara tsayuwa da kyau kar inzo in fad'i in suma don dad'i." Dariya tayi tare da fad'in, "Ba zan bari ka kai
k'asa ba zan taro ka. Idan har ina waje, baza ka tab'a fad'uwa ba in Sha Allah!" Da mamaki yake kallonta
don bai tab'a tsammani zata iya magana haka ba. "Yanzu kina da k'arfi taro ni?" Ya tambaya yana mata
gwalo. "Ba da k'arfin cin tuwo zan rik'o ka ba, zuciyata ce zata rik'o ka. Ka manta kai da kanka ka fad'a an
halicceni ne domin kai, kuma kai ma an halicceka ne domin ni? To ai zuciyoyinsu a had'e suke kuma tare
suke bugawa kuma gangan jikinmu a tare suke sarrafuwa, sabida haka d'aya ba zai tab'a barin d'aya ya fad'i
ba. Ka saka hakan a ranka." Mutuwar tsaye _Khalil_ yayi yana jin maganganunta na shiga ko wani sak'o da
lungu na jikinsa har sai da tsikar jikinsa ya tashi. Wani irin kallon k'auna ya dunga binta dashi kamar zai
had'iyeta. "Ina sonka _Khalilullah_, Ina k'aunarka har cikin zuciyata." Dum yaji wani abu kamar guduma ya
bugi dodon kunnensa, wani irin shauk'i na mamaye ilahirin jikinsa. Ji yake dama yana da dama da jawota
zai yi jikinsa ya rungume sosai. Aina'u dake lab'e jikin k'ofa tana sauraransu, don tun lokacin da Sarah ta
fita ta biyota a baya. Wasu irin ruwan hawaye ne ke gudu a fuskanta. Ji take kamar ta koma cikin gida da
gudu ta d'auko kaifaffiyar wuk'a ta soki zuciyar Sarah dashi ta tafi ta bar duniyar. "Sarah, nagode ba
wannan alfarma da kika min na sanya ni cikin zuciyarki da kuma bani damar kasancewa dake har mutuwa.
Ina so ki sani, zan killaceki a nan, (yayi nuni da zuciyarsa), ba zan tab'a bari kiyi hawayen bak'in ciki ba, idan
har za kiyi hawaye, to na farin cikine, nayi maki wannan alk'awarin. Zamu dunk'ule mu zama d'aya Sarah.
Zan tarairayeki ta yanda ko bugun zuciya mai k'arfi bazan bari kiyi ba. Zan kula dake fiye da yanda ake ririta
kwai. Zan mayar dake sarauniya, sannan in kasance bawanki. Sarah baki ba zai iya musulta yanda zanji
dake ba. Allah ya nuna min ranar da zan mallakeki matsayin mata. Wannan ranar kawai nake jira. Zan
gwada maki practically abunda ake nufi da k'auna. In Sha ni da ke, _couples for eternity_ ne. Rayuwar
aurena dake, babu condition Sarah, unconditional love nake maki Sarah. Ko da zaki zama mara k'afa da
hannu, soyayyarki baza ta tab'a canzawa ba a gare ni. Allah yayi mana jagora." Hawayen farin ciki kawai
Sarah take yi, bata tab'a tunani ko cikin mafarki akwai wanda zai iya fad'a mata wad'annan kalaman ba.
Ashe dai ita ma za tayi farin ciki a rayuwa. "Wallahi idan har ina da rai, ni Aina'u ba zan tab'a bari
alk'awarin daka d'auka ya zama cikakke ba, ba zan tab'a bari kuyi farin ciki ba nayi maku wannan
alk'awarin." Aina'u ta fad'i cikin zuciya tare da saurin barin wajen tana kuka don kalaman da _Khalil_ ke
fad'awa Sarah ba k'aramin k'ona zuciyarta yake yi ba. Sarah da _Khalil_ kuwa basu san da ita ba, sai cigaba
da kwararo kalaman love wa junansu suke yi har kusan goma na dare sannan suka yi sallama kamar kar su
rabu. Bayan da ta dawo d'aki kuma, _Khalil_ na isa gida suka dasa soyayyar ta waya. Bayan sati biyu da
sallamo Sarah, Ya Abdullah ya diro Kaduna, ko sauka gidan Hajiya bai yi ba, kai tsaye ya tafi family house
d'in mahaifinsu domin ganawa dasu Uncles d'in nasa akan batun auren _Khalil_ d'in kuma dama tuni sun
d'an fara maganar a waya. Kasancewar suna d'an shakkarsa, basu wani tattada jijiyoyin wuya ba, sun tsayar
da magana akan zuwa gobe sai suje can gidansu iyayen Sarah a tsayar da magana. Bayan Ya Abdullah ya
dawo gidan Hajiya, sai ya sanar mata yanda suka yi da Uncles d'in nasa. Sosai Hajiya taji dad'i jin babu wani
tashin hankali da aka yi, duk da ta san dama basu cika yin haukar da suka saba yi ba a gaban Abdullah
sabida suna shakkarsa. _Khalil_ kuwa da ya samu labari, sai da ya shiga d'aki ga kulle k'ofa sa hau tik'ar
rawa kamun nan ya kira Sarah ya shaida mata abunda ake ciki. Itama dad'i ne ya kasheta. Bayan sun gama
wayar ta fita tayi alwala ta dawo d'aki tayi raka'a biyu ta dunga rok'on Allah akan Allah yasa ayi wannan
auren kada shima ya rushe kamar na baya. Don sosai ta saka _Khalil_ a cikin ranta. Bayan magriba _Khalil_
yazo har gida ya fad'awa Baba in Sha Allah gobe iyayensa zasu zo domin neman auren Sarah. Baba ya
shaida masa babu komai sai sun zo. Bayan fitar _Khalil_ sai da Baba yayi hawaye tuno y'an uwansa na
_Wamba_ don da yana tare dasu, da su zasu karb'i wannan aure. Haka nan ya aiki Sarah ta kira masa
abokansa guda uku wanda suka had'a Sana'a tun suna matasa. Da sukan zo gidan su dubasa, amma ganin
irin tijara da zagi da Lami take masu, sai suka d'auke k'afarsu a gidan, sai dai idan suka had'u da Sarah sai
su aiketa da gaisuwa, idan kuma suna da d'an wani abu, sai su bata ta kai masa. Har gidan suka zo, da suka
ji dalilin kiran kuwa, ba k'aramin farin ciki suka ji ba, kuma suka tabbatar masa da goben in Sha Allah dasu
za ayi komai. Washa gari misalin bayan la'asar, sai ga jiniyar motocin sojoji, su kawu suna cikin nasu motar,
shi kuma ya Abdullah yana cikin nashi a tsakiyar convoy, sai kuma wata sabuwar mota dal da wani soldier
ke driving. A k'ofar gidan suka yi parking. Soldier ya bud'ewa ya Abdullah mota tare da sara masa ya k'ame.
Bai fito ba, nuni kawai yayi masu da wata mota. Cikin k'ank'anin lokaci sojoji suka kwashe gaba d'aya
abunda ke cikin motar suka yi ciki da su. Buhunhunan shinkafa kamar za'a bud'e shago, manya-manyan
galolin manja da mangyad'a, huhunan goro, katon-katon na sweet da chewing gum, wani k'atoton centre
carpet wanda kud'insa ya kai 500k, sai wasu had'ad'd'un takalma k'afa ashirin da wani k'atoton akwati
wanda babu komai a cikinsa sai lesses da atamfofi masu tsadar gaske da kuma Key d'in mota. Gaba d'aya
uban kayan, kayan saka ranar auren Sarah da _Khalil_ ne. Har dasu gas da manya-manyan stainless steel
irinsu bokiti da. Irin dai al'adar da ake yi. Ga manya-manyan juices na kwali da na goro har da ruwan gora
kala-kala. Lami kuwa mad'aukakin mamaki ne ya kamata don bata san da zuwansu ba. Baba bai fad'a mata
ba, haka ita ma Sarah bata ce komai ba. Sai da aka gama shigar da kayan tsaf sannan ya Abdullah ya ziro
k'afarsa ya fito dai-dai lokacin da su uncle suma suka fito. Abokan Baba su suka yi masu jagora har cikin
d'akin Baba, sosai ya Abdullah yaji dad'in ganin gyaran da _Khalil_ d'in yayi wa baban da kuma ganin ya
soma samun sauk'i. Bayan gaishe-gaishe sai suka fara magana akan abunda ya kawo su. "Aure dai bama so
a saka ki da tsayi. Idan ma baku shirya ba, mu ashirye muke don bama buk'atar komai naku." Fad'in uncle
Ridwan. Sam maganar bata yiwa ya Abdullah dad'i ba. Kuma sai da hakan ya nuna a fuskansa. A natse ya
Abdullah ya soma magana, "Baba, uncle yana nufin idan babu takura, muna so kar bikin ya wuce sati biyu.
Kar ka takura kanka, Saratu kawai muke buk'ata a gidanmu, amma idan kana ganin kana da naka uzurin, za
muyi na'am da duk lokacin da ka saka." "Kaji d'an iskan yaron nan yana k'ask'antar damu a gaban wannan
wulak'antaccen fak'irin mutumin. Shi har ya isa yana talaka ya ja da maganar mu" fad'in Uncle Ameeru
amma cikin zuciya. Ba Baba bane yayi magama, abokinsa Baba Isma'ila ne yace, "A'a babu komai. Lokacin
da kuka saka d'in ma yayi. Allah ya sa hakan shi yafi alkhairi." Cike da girmamawa ya Abdullah yace, "To
mun gode Allah ya saka da alkhairi. Ga wannan makullin motar, Hajiya ce ta bada kyauta a bawa mai sunan
mahaifiyarta Sarah, kaya kuma gasu nan duk Hajiya ce ta lissafa mana muka sayo, tace na al'ada ne da ake
yi idan za'a saka rana. Ga kuma sadaki nan." Ya fad'i hakan yana mai mik'a bunch d'in dubu-dubu guda
biyar, jimilla ya kama dubu d'ari biyar cif. "Wannan kud'in ai sunyi yawa. Ba sayar da Saratu za muyi ba ai.
Makullin mota kuma, ina naiman alfarma ku rik'e a wajenku duk lokacin da Sarah ta shigo gidan, sai ku
damk'a mata." Sosai ya Abdullah yaji dad'in rashin ganin kwad'ayi a fuskan baba, sai yayi murmushi tare da
fad'in, "Baba ai sadaki bai yawa duk da albarkan ake nema. Amma duba ga yanayin da muke ciki yanzu, ko
billion aka bada kud'in sadaki, ai bai yi yawa ba. Zan dai mayar da makullin motar sai tazo tukun kamar
yanda ka buk'ata, amma maganar rage sadaki kam ayi hak'uri." "To Allah ya sanya alkhairi ya sa ayi damu."
Gaba d'aya d'akin aka amsa da amin. Bayan tafiyarsu, Baba ya ce su Baba sama'ila ko wannen su ya d'auki
buhun shinkafa d'aya ya tafi dashi. Nan Lami ta daka tsalle tace ba zai yuwu ba tunda ba ubansu ya kawo
ba. Ai kuwa Baba ya haukace mata kuma basu bar gidan nan ba sai da buhun shinkafa kowa d'aya. Don
buhunar shinkafar guda ashirin ne ciff. Nan Lami ta dunga surfa bala'i ba'a fad'a mata za'a zo kawo kud'in
auren Sarah ba, sannan kuma tace dole a fito da sadakin a raba. Ko kallonta Baba bai kuma yi na ya koma
d'akinsa tare da yiwa sadakin Sarah mummunar b'oye don yayi rantsuwa kwandala ba zai bata ba tunda ba
hakkinta bane shima kuma ba nashi bane. Gaba d'aya yaran gidan basa nan lokacin da aka kawo kayan
auren Sarah. Sarah d'in ce kawai ke gida don ita bata zuwa ko ina. Lokacin da suka dawo kuwa, ba k'aramin
rud'ewa suka yi ba ganin uban kayan saka ranar Sarah da aka kawo. Da Lami ta fad'a masu har da mota,
yanke jiki Aina'u tayi ta suma, babu wanda yayi tunanin bak'in ciki ya saka ta ta suman. Data farfad'o kuwa
kuka ta fashe dashi. Tambayarta suka soma yi, sai tace masu ciwon kai da basir ne ke damunta. Mintuna
biyar bata k'ara yi a gidan ba. Ameeru, duba nan kaga abunda aka turo min da b'oyayyiyar number, karanto
muji don Allah. Ni na kasa fahimta. _ASSALAMU ALAIKUM. NA SAN ZA KAYI MAMAKIN WANNAN SAK'ON
DA NA TURO MAKA. ABUNDA YA SAKA NA TURO KUWA, GANIN GIDANKU GIDAN MUTUNCI NE, KUMA
MAHAIFIN KHALIL YA RASU KOWA NA GANIN GIRMA DA K'IMARSA HAR KUWA YAZU DA BAYA CIKIN
DUNIYAR. NA SAN BAKU YI BINCIKE BA GAME DA GIDAN DA KUKA JE KUKAI KAYAN AURE BA. TO INA MAI
BAKU SHAWARA KU KOMA DA KYAU KUYI BINCIKE, DOMIN DAI YARINYAR NAN BA TA KWARAI BACE. BATA
JIMA DA ZUBAR DA CIKI BA. RUFA-RUFA AKAI MAKU. GIDAN NAN BA GIDAN MUTUNCI BANE DOMIN
TAKEN GIDAN SHINE *GIDAN KARUWAI* IDAN KUMA BAKU YARDA DA MAGANATA BA, ZA KU IYA YIN
BINCIKE DOMIN TABBATARWA. DON YAYYIN YARINYAR BABU WACCE BATA AJIYE SHEGE BA. IDAN KUMA
HAR KUKA AMINCE WANNAN YARINYA TA SHIGO CIKIN ZURI'ARKU, TO KAMAR FA RUWAN KWATA KUKA
D'IBA DA HANNUNKU KUKA ZUBA A CIKIN RUWA MAI KYAU!_

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

Paid book 08128755583

*_MATAR SAYYADEE_*
[30/09, 7:11 PM] Rahamanatu: A zafafe Uncle Ameeru ya mik'e tare da fad'in, "Na rantse da Allah ba zan
tab'a bari ayi auren nan ba. Dole ne muje gidan can yanzu mu saka su a gaba muje mu kwaso duk abunda
muka kai gidan. Mun janye maganar auren." Wani murmushi uncle Ridwan yayi tare da fad'in, "Gaskiya
baka da hankali Ameeru!" "Rabu dashi mana, ni ai kallon wawa nake masa daga nan zaune. Ko ka manta
cewa yayi ba zai auri y'armu ba saboda ta lalace? A gaban idanunmu gaba d'aya babu kunya ya fad'a mana
wannan maganar. Har yanzu maganar tana sukar zuciyata. Ai ni wannan abu ba dad'i yayi min wallahi. Naji
dad'i sosai da ya zam yarinyar gantalalliya ce. Kun ga kenan mun samu hanya mafi sauk'i da zamu cimma
burinmu. Kawai had'a kai za muyi da yarinyar mu kashe d'an iska da ransa, musamman ma Bilkisu da ta
hana mu rawar gaban hantsi. Shegiya duk hukumomi ta haifo, daga soja, sai d'an sandar farin kaya da
kuma d'an iskan nan Barrister da ya gaji ubansa." Fad'in uncle Zayyanu. Uncle Shamsu kuwa cewa tayi, "Ni
wallahi duk cikin y'ay'an Bilkisu nafi tsanar d'an iskan yaron nan _Khalil_ da wansa Abdullah. Kun ga da ace
yaron nan soja a Kadunan nan yake, wallahi watarana sojoji zai saka su b'alla k'afafuwanmu. Bakwa ganin
yanda yake nuna isa yana wani fankama kawai don ya kasance soja. Ni dama a kashe d'an iska acan
wallahi." "Shegu taurin rai garesu kamar ubansu. Wani irin farmaki ne bamu kaiwa Nura ba, amma yana
nan kamar kainuwa har sai da lokacinsa yayi. Mun sha wuya wallahi." Fad'in uncle Ameeru. Uncle Shamsu
yace, "To yanzu dai mu tsayar da mafita. Mai kuke ganin za muyi? Ta yaya zamu b'ullowa ita yarinyar da zai
aura?." Uncle Ridwan ya fad'i. "Ku bar min duk wannan a hannuna." Fad'in uncle Ameeru. "Yauwa Ameeru.
Na sanka indai ta wannan fannin ne. Da ace yarinyar nan da ta turo sak'o ta bar wani makama da za mu
bibiyeta, da ta cab'a don ta hanyarta zamu samu bayanai masu dama. Don ga dukkan alamu bak'in ciki
take yi shiyasa ta tona asirin wancen, watak'ila kuma k'awa ce. Duk da hakan dai kuma za mu bincike
gaskiyan labarin da ta bamu a kan gidan sabida mu san ta yanda zamu b'ullowa abun." "Yauwa nima
abunda nake so in fad'a kenan." Uncle Zayyanu ya fad'i. Hajiya babu abunda take yi sai shirye-shirye. Gaba
d'aya ta gama kiran dangi na kusa da na nesa na shaida masu auren _Khalil_ da za ayi nan da sati biyu.
Aunty Maryam kuwa har ta gaji da zuwa kasuwa ita da aunty Khairat, don tun da aka saka bikin Aunty
Khairat tazo don tuni har sun koma Kano, sai dai can ta baro Barrister shi sai ana saura 2days biki zai zo
sabida aikinsa. Duk da kayan lefen kusan gaba ki d'aya a Dubai suka sayo har da akwatin, don private jet
suka bi suka yo sayayyar kasancewar duka bangarori hud'un sun saki kud'i, Yaya Abdullah 5million ya bada,
ya Barrister kuma ya bada 3million, ya Abdul-Hakeem ya bada 2.5million, shi kuma mai gayya 10.million ya
bada. Hajiya kuma ita ta saya akwati set d'aya mai guda goma sha biyu. Gaba d'aya jimillar kud'in suka
kama 20.5million. Dasu gaba d'aya su aunty Maryam, aunty Khairat da wata autar su Hajiya suka tafi
Dubai. Sai da suka sayo akwatina set uku, na hajiya dozen, sauran biyun kuma mai guda six-six sai dai masu
d'an karan tsada kuma gaba d'aya sai da aka cika su da mahaukan kaya masu tsada, don lesses d'in da aka
saka babu na k'asa da 200k, kaya dai kamar za'a bud'e shago. Bayan sun dawo gida Nigeria kuwa, haka
suka dunga yawon kasuwa suna k'aro wasu abubuwa don sai da suka dawo Hajiya tayi ta fad'a ganin babu
kayan uwa da uba. Ana Nigeria suka k'ara had'o set d'in akwatuna guda uku irin mai biyu d'innan da kit.
D'aya shaddojine da takalmar maza da turare da huluna masu tsada wanda ya kasance na Baba, sai d'ayan
set d'in kuma aka zuba atamfofi da lesses da manya-manyan mayafai da takalma da turare. Shi kuma na
Lami, sai d'ayan set d'in akai wa y'an uwan Sarah komai kala biyar-biyar, lesses kowa ta samu biyu, haka
shadda da atamfa, sai takalma uku-uku da jakunkunarsu har da sark'a da y'an kunne. Gaba d'aya a
parlourn Hajiya aka zube kayan. Sosai Hajiya taji dad'i don gaba d'aya babu k'arya. Yawan kayan ya saka ba
komai Hajiya ta iya gani ba daga cikin kayan Sarah don akwatuna har set uku, wanda gaba d'aya jimillar
akwatunanta kawai sun kama 24. _Khalil_ kuwa sai dad'a gyara b'angarensa yake yi wanda ya kasance four
bedroom a k'asa da wawakeken parlour guda biyu mai d'auke da, dinning sai kitchen da store wanda
girmansa da tsaruwarsa ma kawai abun kallo ne. Sama kuma two bedroom da parlour d'aya. Can gidansu
Sarah kuwa, Lami da Aina'u ne kawai basa farin ciki da wannan aure da za ayi, gwara ma Lami ita gani
kawai take yi idan akai auren shikenan za'a daina kawo mata abun arziki, yayin da Aina'u ita tsabar hassada
ce da mugun hali. Babu kuwa kullum bakinsa bai rufuwa sabida farin ciki, sai shirye-shirye yake yi. Don
yanzu Alhamdulillah har waje yana iya fita ba tare da sandar ba. Yana zuwa wajen abokansa suna ta shirye-
shirye don Baba yace har walima sai yayi. Sarah kuwa babu wacce ke fad'o mata a rai irin K'awarta Muniba,
duk duniya ita kad'ai ce k'awarta, gashi kuma tuni iyaye sun raba tsakaninsu. Kamar Baba ya san halin da
take ciki, har gida yaje ya samu liman (Mahaifin Muniba) ya bashi katin gayyata sannan kuma ya rok'eshi
alfarmar ya bar Muniba tazo wajen Sarah suyi shirye-shiryen biki don duniya bata da wata k'awa sai
Muniba. Mahaifin Muniba yaji dad'i sosai jin Sarah za tayi aure kuma yace wa Baba in Sha Allah Muniba
zata zo. Sarah na zaune tana sak'awa da warwarewa, don basu jima da waya da _Khalil_ ba yake shaida
mata zuwa anjima zai zo suyi maganar shirye-shiryen da za tayi na auren tunda gaba d'aya bikin yanzu ya
rage saura kwana bakwai don har anci sati d'aya daga cikin ranakun auren da aka saka. "Assalamu
alaikum!" Da mugun gudu Sarah ta fito jin kamar muryan Muniba. "Munibaaaaaaaaaa!" Ta fad'i sunanta
da k'arfi cike da farin ciki ta rungumeta tana fad'in, "Wayyooooo Allah na, Muniba kece? Zo mu shiga daga
ciki." Ta kama hannunta suka shiga cikin d'aki. Sakin labule Aina'u tayi, don tun jin sallamar Muniban ta
d'aga labulen d'akin Lami tana kallon su. Dogon tsaki taja tare da fad'in, "Duk ku gama zumud'inku, wallahi
wannan aure ba mai yuwuwa bane. Bamu y'an iska marasa sanin darajar kai irin y'an uwan mahaifin
_Khalil_ d'in ma, ace a tura maku irin wannan sak'o amma baza ku tashi kuyi bincike tare da d'aukar mataki
ba. Y'an iska kawai!" Duk a zuciya tayi maganar tare da shigewa tana mai yin kwafa tare da fad'in, "Ina da
shiri a k'asa mai zafi, duk sai kunci ubanku." "Ke kuma dawa kike kwafa?" Fad'in Lami. A zafafe tace, "Babu
ruwanki dani. Tom!" Tana gama fad'in haka ta zari gyale tare da ficewa daga gidan. "K'awata nayi kewarki.
Ya aka yi su Baba suka bari kika zo gidan nan?" Sarah ta fad'i bayan ta bud'e d'an k'aramin fridge d'in dake
d'akin ta d'auko mata ruwan sanyi da exotic. "Masha Allah! Haka kuka yi gyara a gidan? Wuri yayi kyau.
Wannan irin makeken gado haka!" Ta fad'i hakan tare da hawa kan gadon tana shafawa. "It's a long story
Munee, naji dad'i da Baba yaje yayiwa babanku magana don wallahi ke kad'ai ce k'awata a duniya gashi
kuma d'azu muka gama waya dashi akan zai zo ya sallami k'awayen amarya." Saukowa Munee tayi tare da
fad'in, "K'awata wa kika kamo haka? Kwanaki nake ta jin rumours wai kin yi cikin Shege Farouq ya fasa
auranki. Ni ina jin maganar ta shiga kunnan hagu ta fita ta dama. Kuma kin san wake fad'awa mutane?
Aina'u fa!" Tab'e baki Sarah tayi tare da fad'in, "Uhm, kyaleta. Kin san su suna goyon bayan Lami ne, basu
son inyi aure. Ni kuwa zaman mai zan yi a gidan. Ai gwara na tafi nawa gidan nayi bautar ubangiji." Hannu
Munee ta bawa Sarah suka kashe sannan tace, "K'awata kenan! To shi angon naki a ina yake." Gyara zama
Sarah tayi ta d'an bata labarin in brief saboda ciki ba don abinci kawai aka yisa ba, duk da kuwa ta yarda da
Muneeban. "K'awata na taya ki murna wallahi. Allah ubangiji ya sa mijinki ne ya kuma baku zaman lafiya
mai d'orewa." "Ameen k'awar arziki." Daga nan suka fad'a hirar yaushe gamo har har lokacin da _Khalil_
yayi kiran Sarah a waya ya shaida mata yana waje. Tare suka fita da Muneeba zuwa wajen _Khalil_ d'in.
Lokacin da Muneeba tayi arba da _Khalil_ rud'ewa tayi don b'ata tab'a hasaso haka yake ba. "Wannan
itace k'awar tamu?" Fad'in _Khalil_ yana murmushi don tsabar rud'ewa Muneeba ta kasa gaishe shi har sai
da Sarah ta d'an tsunguleta a cinya sannan ta dawo hayyacinta. "Kamar mai asibitin _Khalilullah specialist
hospital_ ko? Ka tab'a duba ni sau d'aya a asibitin ka." Dariya yayi tare da fad'in, "K'aninsa ne, ba shi bane."
Ya k'arisa maganar yana mai kashewa Sarah idanu. Dariya Sarah tayi tana kallon Muneeba dake masa anya
kuwa. "Gaskiya kamannin sun b'aci. Kai ne mijin k'awar tawa kenan?" "In Sha Allah!" _Khalil_ yayi saurin
fad'in. "Ma sha Allah! To bud'e kunnuwanka da kyau zan baka amana." Hannu biyu _Khalil_ ya saka ya rik'e
kunnuwan nasa tare da fad'in, "Ina jinki k'anwarmu." Dariya Sarah ta kwashe dashi ganin yanda yayi tare
da bada full attention d'insa wa Muneeba. "Wannan k'awata ce kuma aminiyata. A yau karo ba farko ina
mai damk'a amanarta a hannunka, kar inji ko a cikin mafarkina tana kuka, idan ma za tayi, to ya kasance na
farin ciki. Sannan a rik'a lallab'ata kamar kwai. Baka da matsala in dai aka zo fannin biyayya, don k'awata
akwai biyayya kuma na tabbata za tayi maka biyayya. Yi, nayi, bari, na bari. Duk zata kiyaye su. Kai ne
babba, key na controlling gidanka yana hannunka, Sarah kamar motarka ce, duk inda ka nufa da ita, nan
zata bi. Saboda haka, dan girman Allah, kar inji Sarah tayi kuka da kai." Sosai _Khalil_ yaji Munee ta kwanta
masa a rai. Murmushi yayi tare da fad'in, "An gama aunty Muneeba. Hud'ubarki ta shiga sosai." Juyawa
tayi ta kalli Sarah tare da fad'in, "K'awata na dawo kanki, kin ga, wallahi kiyi masa biyayya domin aljannarki
na k'ark'ashin k'afarsa. Idan ya take, sunanki sorry, don haka kema kar inji yayi kuka dake. Irin tarairayan
duk ki rik'a masa. Kamar irinsu, Gwandi, zaka sha gwanda, honey zaka sha Honey, Sweety zaka sha
swee....." Kamun ta k'arisa cewa sweet d'in daga _Khalil_ har Sarah suka fashe da dariya. Ita kanta
Muneebar dariyar take yi. "Gaskiya k'awar mu naji dad'in wannan hud'uba naki. Mun gode Allah ya saka
da alkhairi kuma mun d'auka." Murmushi a fuskanta tana mai taya k'awarta farin cikin samun miji kamar
_Khalil_ tace, "To ma Sha Allah. Haka nake so ai." Gyara tsayuwa _Khalil_ yayi tare da fad'in, "To yanzu
wani shirye-shirye kuka tsara ta wajenku?" Kallon Sarah Munee tayi sai kuma ta kalli _Khalil_ tare da fad'in,
"Gaskiya ta wajen mu, walima kawai za muyi da k'awayen mu na makaranta da kuma mutanan anguwa. Ko
ya kika ce k'awata?" Ta k'arisa maganar tana kallon Sarah. Gyad'a mata kai Sarah tayi tare da fad'in, "Eh
hakane." "To ustazai. Ni dai abokaina sun had'a min dinner. Don haka bayan an d'aura aure akwai dinner
sai ku kasance cikin shiri. Allah yasa k'awar tamu tana da account?" Ya k'arisa maganar yana kallon Munee.
"Eh ina da shi." Fad'in Munee. Fiddo wayarsa yayi tare da fad'in, "Fad'a min account number d'in." Bayan
ta fad'a masa da sunan bank d'in, a take yayi mata transfer d'in 500k. Waro idanu Munee tayi lokacin da
tayi arba da kud'in da ya turo don har sai da ta murza idanu. Tun da take kud'i dubu ashirin ma basu tab'a
zama cikin account d'inta ba ko da mistake, sai ga dubu d'ari biyar sun shigo yau. "Wad'annan kud'in fa?
Wallahi sun yi yawa. Duk na minene haka." "Duk na walimar ce." Ya fad'a kai tsaye. "Dan Allah sunyi yawa
wallahi." With serious face yace, "Basu yi ba. Kuma kar ki sake magana. Kuje kuyi duk wani hidimar da za
kuyi dasu. And in Sha Allah two days before the wedding za'a kawo maku raguna guda uku da drinks. Yanzu
haka ma idan kun koma gida kuyi list d'in duk wani abubuwan da zaku buk'ata sai ku turo min." Gaba d'aya
Muneeba is speechless. Sai gyad'a kai kawai take yi. B'ata tab'a yin y'an matan amare ba, amma ta sha gani
da ji, wani lokacin ma da fad'a ake k'arewa da abokan angon domin wasu dakyar suke fitar goma zuwa sha
biyar. "Bari na baku waje, sai kin shigo k'awata." Fad'in Muneeba. "To k'awarmu, mun gode sai ta shigo
tunda ni baza amin sallamar ba." Dariya Muneeba tayi tare da fad'in, "Sai da safe asha soyayya lafiya."
Tana gama fad'in haka ta shige gida tana dariya. Sun jima a waje suna hirar su ta soyayya, sai da zai wuce
yake fad'a mata ta fad'a a gida gobe za'a kawo akwati. Tana shigowa gida ta nufi d'akin Baba kai tsaye ta
fad'a masa sak'on _Khalil_ shi kuma ya cire dubu hamsin a cikin kud'in da _Khalil_ ke basa idan yazo gaishe
sa yace taje gidan su Muneeba ta kaiwa mahaifiyarta ayi y'an soye-soyen fulawa da kuma kaji. Sannan ya
ware wasu kud'i ya ajiye wanda idan y'an kawo kaya sunzo a basu tukwuici. Da Muneeba zata wuce gida
tare suka tafi wajen mahaifiyarta tayi mata bayanin sak'on da Baba ya turo ta ta fad'i. Hannu biyu Mama ta
karb'a har ta bada sautu saboda a sayo komai da wuri kasancewar gobe bak'in za suzo. Anan ne kuma
Sarah da Muneeba suka fad'a mata yanda suka yi da _Khalil_ game da walimar da za suyi da kuma kud'in
da ya turo. Ita kanta mama tayi mamakin kud'in, amma da taji anan mahaifin _Khalil_, sai mamakin ya sake
ta don ta san irin kud'in da suke dashi. Mama tambayar Sarah tayi shin akwai wani gyara ne da ake mata
na jiki a gida, sai Sarah ta fad'a mata babu abunda ake mata. A take mama ta kira waya aka turo mata
number d'in wata kwararriyar mai gyaran jiki da yake tana home service. Cikin awa d'aya ta iso da duka
kayan gyaran jiki. A cikin kud'in _Khalil_ da ya turo aka tura mata 200k domin soma fara yiwa Sarah gyaran
jiki daga yau da daddare. Ai kuwa na dare d'aya tal sai da Sarah ta tabbatar an soma gyara jikinta. Baba da
kansa yaje har d'akin Lami ya shaida mata y'an kawo akwati za su zo, sai da tayi masa kallon sama da k'asa
tukun sannan tace, "To wata uwar zan yi masu da kazo ka tsaya min a kai?" Murmushi kawai baba yayi tare
da juyawa ya koma d'aki don dama yaji a jikinsa babu wani abu da Lami za tayi shi yasa ma ya tura Sarah
can gidan su Muneeba. Na'ima ce ta kalli Lami tare da fad'in, "Gaskiya Lami ba haka ake yi ba. Idan fa za'a
kawo akwati, dangin amaryar sha tara na arziki suke yiwa dangin ango kamar irin su soye-soyen kaji, su
meatpie, samosa, spring rolls da sauraransu har da tukwuicin kud'i. Kuma ni ina ji a jikina ba k'aramin kaya
za'a kawo wa Sarah ba." Harara Aina'u ta makawa Na'ima tare da fad'in, "Munafuki annamimiya!" A cikin
zuciyarta. Amma a zahiri sai cewa tayi, "Wallahi Lami kar kiyi komai. Kin san halin masu kud'in nan da
shegen raini da d'aga kai kamar dan su Allah yayi duniyar." Da sauri Na'ima tace "Ke dai Aina'u annamimiya
ce. Idan baza ki kashe wuta ba, to kar ma ki soma hurawa. Shegiya gwara dai ki fito da naki nashinshinin
bar yiwa wata hassada. Ko sau d'aya bam tab'a jin wani yazo yana sallama dake ba." A fusace Lami tace,
"Wannan wani irin maganar banza ce haka Na'ima? Ban so! Kar ki kuma yi mata irin wannan maganar. Ni
kaf y'ay'ana babu wanda bai da farin jini. Farin jini a nono na kuka tsotsa." A fusace Aina'u tace, "Ni ko mai
zan yiwa Hassana a jikin wannan banzan da zata aure! Allah ya kiyaye in auri wanda zan zama baiwarsa. Ai
duk wata shegiyar da tayi aure ta san inda ta kai kanta. Daga wanke min kayana, dafa min abinci sai goge
min takalmi. Sannan idan dare yayi ya kwashi romon albarkan jikin banza a banza ya tashi ya kakkab'e
jikinsa kuma ba shi zai hana gobe yayi maki muzurai ba. Watak'ila ma naira d'ari biyu sai kinyi kamar za kiyi
kuka ka mun ya cire ya baki. Allah ya sawake nayi aure! Ita ma da kuka ga ina nuna kamar ina jin haushi,
sabida y'ar uwata ce ina hango mata wahala musamman da zata shiga gidan masu arziki. Kun ga sun samu
y'ar aiki a sama wacce bata da salary." "Nace ba, da kike wannan hak'ik'icewar, ina naki tsayayyan
kwarton?" Fad'in Na'ima tana harararta. Aina'u za tayi magana kenan Luckyboy ya fad'o d'akin tare da
fad'in, "Ke Aina'u, gasu can a waje suna jiranki." Kwafa Aina'u tayi tare da mik'ewa babu ko gyale ta fice
daga d'akin. "Kina ji ko Lami, dan Allah kar kibi shawarar Aina'u, kiyi amfani da kud'inki kiyi masu sha tara
ta arziki, sannan gayya fa ake yi. Dole sai kin kira k'awayenki domin su zasu karb'i kayan ba ke ba." Fad'in
Na'ima. "Wai maganar me kuke yi haka? Ni sallame ni kawai Lami in ware. Kuma eh, naga anyi eh ya ne a
cikin gidan nan, amma ba'a bani rabona ba. Ke nan ni ba d'an gidan bane?" "Ungo wannan, tafi ni ka ishe
ni." Fad'in Lami tare da mik'a masa dubu talatin. Da idanu Na'ima tabi kud'in sannan ta juyo ta kalli Lami
bayan fitar Luckyboy tare da fad'in, "Lallai ma Lami! Dama duk uban kud'in da muke baki, da wanda
_Khalil_ yake baki Lucky kike tattarawa kike ba yana tafiya shi da abokai suna shaye-shaye." Lami ko taro
bata yi ba sai zurawa plasma TV tayi tana kallon arewa kamar bata san mai Na'imar ke cewa ba. Washa gari
wajajen k'arfe biyu sai ga dirar motoci masu kawo lefe sun zo. Dama kuma Munee na gidan, da sauri ta
fiddo waya ta kira mahaifiyarta ta shaida mata sun zo don ita ce tace su fad'a mata a waya idan sun k'ariso.
Cikin k'ank'anin lokaci sai ga mama da tawagarta su k'ariso gidan hannunsu nik'i-nik'i da manyan kuloli. A
nan tsakar gidan aka shimfid'a masu k'atoton tabarma. Su suka yi insisting sabida d'akin ba d'aukar su zai
yi musamman da irin kayan da suka zo dashi. Aunty Maryam, aunty Khairat, kanwar Hajiya, matan uncles
da matar ya Abdullah ne suka kawo kayan. Su suka fara shigowa, sai da suka gama gaisawa da mahaifiyar
Munee da mutananta da ta gayyato. Na'ima kuwa hana Lami fitowa tayi don cewa tayi sai tayiwa Baba da
mahaifiyar Munee tujara akan abunda suka yi mata. Sai zage-zage take tana fad'in akwai wani banzan
alak'a tsakanin Baba da mahaifiyar Munee. Allah yaso babu wanda yaji abunda take fad'i sai Na'ima da
take ta faman bata baki a d'aki. Kuma ta kulle d'akin ta ciki duk da kuwa tana so ita ma taje taga kayan da
ta hanga ta window driver na wucewa dasu yana ajiyewa a nan tsakar gidan. Sai da ya kawo duka sannan
aka soma bubbud'ewa. Babu abunda ke tashi sai kabbara da gud'an mata. Tun mata na irge har suka
hak'ura don b'ata lissafi suke yi. Mata sai uban santi suke yi da gud'a. Gaba d'aya gidan ya cika da mutanen
dake ganin kayan Sarah. Aina'u kuwa zawonta uku a cikin wando ganin mahaukatan kayan da aka zubawa
Saran. Bayan an gama gani, mama ta ware na Baba, Lami da kuma wanda aka ce na k'annai da yayyin
amarya ne ta ajiye a gefe, sauran kuma aka bar su nan tsakar gida. Dubu d'ari uku Baba ya bada matsayin
tukwuicin duk da kuwa bai san adadin kayan da zasu kawo ba. Y'an kawo akwati sun mik'e zasu wuce
kenan sai ga tawagar matan zumunta sun shigo gidan da wani irin mahaukacin gud'a suna tafi tare da yin
wak'ok'in coci. Gaba d'aya sai kallo ya koma sama. "Elizabeth kina ina? Ashe aurar da yarinyarki za kiyi
amma shine baza ki gayyaci mutanan coch ba. Baki kyauta ba sam. Pasto William yayi fushi dake kuma
yace idan baki kai Sera (Sarah) ya saka mata albarka ba, auren ba zai yi albarka ba. Yace ya baki kwana biyu
ki kaita ayi mata wankan zunubi kamun ta shiga gidan miji. Da k'arfi aunty Rose Merry take maganar duk
da kuwa bata ga Lami a tsakar gidan ba. Aunty Maryam da aunty Khairat da kanwar Hajiya, sai wannan ta
kalli wancen, sai wancen ta kalli wannan. Da suka ga abun ba na k'arewa bane, sai suka yi salama suka tafi
domin sosai dai aunty Rose Merry da tawagarta suka baje suna wak'ok'in suna kiran sunan yesu almasihu.
Idan suka buga wani ihu har hanjin mutum sai ya kad'a. Baba dake d'aki kuka kawai ya fashe dashi. Don bai
tab'a kawowa Lami zata iya yin wannan iskancin ba. Lami dake d'aki ita ma mamaki ne ya kamata don ko
da wasa bata tab'a fad'awa mutanen coch d'insu zata aurar da y'a ba. Ko aunty Rose Merry da take
k'awarta bata fad'a mata ba. "Na'ima wallahi bani na gayyace su ba, kuma ban san wanda ya kira su ba."
Na'ima kuwa kallon mahaifiyarta take yi cike da tuhuma tare da fad'in, "Lami dama kina zuwa coch? Wa za
ayiwa wankan zunubin?" Lami bata ba ta amsa ba, sai wucewa da tayi ta bud'e k'ofar ta fita ta samu ce
aunty Rose Merry dake ta kwasar ihu da kiran yesu suna d'ad'd'aga kayan akwatin Sarah. "Hajiya kina bacci
ne aka kwaso maki dangin arna matsayin surukarki?"

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

*_MATAR SAYYADEE_*
[30/09, 7:11 PM] Rahamanatu: "Hajiya kina barci ne zaka kwaso maki dangin arna matsayin surukarki?
D'iyar Elizabeth ce kuma Wallahi matan zumunta cike da gidan har da zancen zuwa wajen Pasto domin
ayiwa ita matar _Khalil_ d'in wankan zunubi." "Wankan Zunubi?" Hajiya ta fad'i cike da mamaki tana kallon
K'anwar tata Marwanatu. "Wallahi tallahi Hajiya kar ki yarda da wannan aure idan ba haka ba akwai
mummunar matsala. Wannan wani irin bahagon gida ne haka." Fad'in Inna Marwanatu. Amma abunda ya
matuk'ar d'aure mata kai da bata mamaki shine ganin hajiya tayi murmushi tare da cigaba da ware anko da
take yi wanda ta sayawa y'an uwa da abokan arziki. "Hajiya dariya fa kika ki. Na fad'a maki irin wannan
magana mai d'aga hankali shine kike murmushi mai makon ki fusata ki kira waya a fasa wannan aure."
Ajiye kayan da ta d'auko tayi tare da kallon Marwa sannan tace, "To ai ni ban fahimceki bane Marwa. Shin
laifin uwar ne zai shafi y'ar ko kuwa? Ba ita bace arniyar idan rrtkq a kina magana akan a fasa auren. Ko da
kuwa itace, ai addininmu bai haramtana mana kawo su cikin mu, mu dai matsayin mata addini bai amince
mana da mu zauna dasu ba. Kuma wannan yarinyar da _Khalil_ zai aura, bayan binciken da marmari yayi,
na saka anyi min nawa da kai na a kanta. Don haka ita kad'ai zamu kawo cikin gidan nan ba ba mahaifiyarta
ko kuma matan zumunta ba. Idan aka kawo ta cikin gidan kowa ga watse ai shikenan ko? Don Allah Marwa
bana son in k'ara jin wannan maganar, ya tsaya tsakanin mu kawai." Da sauri Marwa tace, "Amma
Hajiy....." "Dan girman Allah ki bar wannan maganar haka Marwanatu." Tsit Marwa tayi bata kuma cewa
komai ba sai ma juyawa da tayi ta bar d'akin. Tana fita Hajiya ta jingina da gado tare da fad'awa duniyar
tunani don fisabilillahi ta daure ne kawai a gaban Marwa ta kare surukar tata da gobe amma ba wai don
bata firgita da labarin da taji ba. "To ko dai in d'auko yarinyar nan ne har sai anyi biki? To kuma ai ba'a tab'a
haka ba a al'adar hausawa. Kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Allah kana gani, kafi kowa sanin dalilin
wannan had'i. Allah kasa alkhairi ne albarkacin soyayyar da kakewa fiyayyan halitta." A bayyane tayi
magana tare da jan dogon ajiyar zuciya. "Baba, shawara zan baka, ka saka a kwaso duka kayan can na waje,
idan ba haka ba wallahi duk yawon kayan can Sarah baza ta tafi da abun arziki ba." Na'ima ta fad'i ba tare
da ta damu da kukan da ta iske baban nayi ba. D'agowa Baba yayi ya kalli Na'ima, bai tab'a d'auka za'a
samu wacce zata iya wannan maganar hankalin a cikinsu Na'imar ba. "Na'ima kuje ku kwaso kayan tsaf ku
kai gidan liman Muhammadu mahaifin k'awar Saratu. Ku kira yara su kwashe kayan zan biya kud'in." Da to
Na'ima ta amsa tare da fita dama kamun tazo d'akin Baba ta saka su Nuratu sun saka idanunsu sosai a kai
gudun y'an sibaren na ayye. Cikin abunda bai wuce mintuna ashirin ba, Na'ima ta had'a kan yaran anguwa
da almajirai sun kwashe kayan tsaf an tafi dasu gidan mahaifin Muneeba. Lokacin Lami na d'aki ita da
k'awayenta matan zumunta. Sai da ta fito domin d'ibar masu nasu kayan kamar yanda suka yi mata fanfo,
sai taga wayam duk da kuwa tana jin hayaniyar yara lokacin da suka zo tafiya da kayan, amma sai tayi
tunanin ko y'an ganin kaya ne. Da masifa ta hau tambaya ina kayan. "Suna gidan k'awar Saratu. Can Baba
yace a kai sabida yawan mutanen da suke shigowa gudun sata." Fad'in Na'ima. "Kutumar kaza-kazan
can......... To wallahi ku fita ku dawo da kayan nan yanzu. Uwar wani ce ta haifar min y'ar da har za'a ce an
kai kayan y'ata wani gidan. Wallahi ba liman ba ko sarkin makka ne sai naci kaza-kazansa (Ta wulwulo zagi)
idan bai saka an maido mi da kaya y'ata ba." Fad'in Lami. Baba dake d'aki ya kai wuya, bai san lokacin da ya
fito daga d'aki ba tare da fad'in, "Lami, na gaji da halinki. Wallahi tallahi idan kika k'ara magana akan
wannan kayan sai na sake ki. Haba! Kin takura min kin hana ni shan iskan duniya cikin salama. Kuma
wallahi idan y'an iskan k'awayenki basu fito sun bar gidan nan ba, sai na masu itace. Idan kuma sun ce
k'arya ne, su k'ara mintuna biyar suga abunda zai faru." Matan zumunta na jin haka suka fara fitowa d'aya
bayan d'aya. "Ku koma, babu inda za kuje. Wallahi dai-dai nake da kai Nuhu a cikin gidan nan. Idan ka fasa
saki na, Allah ya tsine maka albarka. Kuma kaya sai an dawo dasu gidan nan." A zuciye Baba yace, "Kije na
sake ki saki d'aya, bi........" Da wani irin mahaukacin gudu Sarah ta fito tare da jan burki ta kifa guiwarta a
k'asa tare da fashewa da kuka tana fad'in, "Kar ka k'arisa, kar ka k'arisa Baba dan girman Ubangiji. Wallahi
in har ka saki mama akan kayan akwati na, ba zan tab'a yin auren ba na fasa. Dan girman Allah ba dan halin
Lami ba Baba ka mayar da ita. Baba ina wannan hak'uri da ka dad'e kana yi ya tafi? Haba babanmu." Ta
k'arisa maganar tana mai fashewa da kuka. "Na gaji ne, na gaji Saratu. Saratu nayi iya hak'urin da zan iya yi
da mahaifiyarku. Ta tafi kawai ai tana da dangi." D'aya daga cikin matan zumunta ta soma fad'in, "Yesu
almasihu kayi mana tsari da irin wannan mutanan da ka tsine masu." Zabura Baba yayi tare da rarumo
wani narkekiyar langen ya rafka mata a tsakiyar baya, sauran kuma yayi kansu. Da gudu har da k'undunbala
suka fice daga gidan. D'aya har tana sakin tusa. K'afafunta Baba Sarah ta rik'e tana fad'in, "Baba dan Allah
kayi hak'uri ka mayar da Lami." Baba yace, "Kiyi hak'uri Sarah, zamana da Lami akwai cutarwa. Gwara
kawai ta tafi." Wani irin kuka Lami ta fashe dashi tare da fad'in, "Azzalumi ka rabo ni da y'an uwana ka
kawo ni nan kana cutar dani. Yesu ba zai tab'a yi maka albarka ba. Shiyasa sabida mugun halinka ya maka
mummunar tsinuwa ka zama talaka. Kuma ko ka sake ni, ina nan gidan sai dai kai ka fita ka bar gidan."
"Haba Lami, kukan me kike yi. Muje na kama maki d'aki ki zauna ki bar masa gidansa." Fad'in Aina'u tana
hararar Baba. "Ban yi mamaki ba Aina'u. Banyi ba! Ai kina da abunda kike rabawa maza suna baki kud'i
dole kice zaki kamawa mahaifiyar taki d'aki." Su Nuratu kuwa ko uffan basu ce ba. Na'ima kuwa kumbarta
take yankewa yayin da Marfu'a ke wankewa yarinyar ta kashi bayan ta cire mata pampas. "Eh d'in. Da ace
ka sauke duk wani hak'k'inmu dake kanka, ai baza mu kasance a yanda muke haka ba. Kai ne mugun daka
cutar dam......" Ba tare da ta k'arisa ba Sarah ta sauke mata tagwayen maruka a fuska hagu da dama sai da
tayi zaman y'an bori. Dama kuma kamar jira Ainau take ta rarumo wani sanda tayi kan Sarah dashi. Da
sauri baba ya shiga tsakaninsu, Aina'u bata yi wata-wata ba ta saukewa Baba sandar a k'agu kasancewar ya
d'aga hannu wajen k'ok'orin kare Sarah. "Wasssh Inna lillahi!" Baba ya furta hawayen azaba na sauko masa
har kan kuncinsa. Wani irin fuzgewa Sarah tayi ta kai Aina'u k'asa ta hau kai mata wani irin duka ko ta ina a
jikinta. Da kyar Lami da Na'ima suka d'aga Sarah a kan Aina'u wacce bakinta bai mutu ba sai auno ashar
take yi marasa dad'in fad'e. "Ki kashe ta shegiya y'ar iska. Allah ya tsine maki albarka Sarah. Yesu ina
rok'onka a yau ka hana Sarah kwanciyar hankali ita da Nuhu mahaifinta. Ba dai ubanki kika zab'a a kaina
ba, to kije yesu ya tsine maki ke da ubanki. Ba dai ya sake ni ba." Ta k'arisa maganar tana mai jan kwafa.
Wani irin kuka Sarah ta fashe dashi don ta san illar bakin uwa a wajen y'ay'anta. Da gudu ta k'ara kama
k'afafun Baba tare da, fad'in, "Baba kayi min rai ka rufa min asiri kar bakin uwa ya kama ni ka mayar da
Lami d'akinta. Dan Allah Baba. Wallahi idan baka mayar da Lami ba, ba zan tab'a zaman aure ba. Ko an
d'aura auren sai na gudu na bar gari." D'agota Baba yayi tare da fad'in, "Share hawayenki Saratu. Bakin
Lami ba zai tab'a kama ki ba don babu abunda kika yi mata. La'anarta kanta zai koma. Ki bar kuka, na
mayar da ita d'akinta sabida ke. Domin ke nayi hakan ke d'aya." Fad'in Baba. "Aikin banza kawai!" Fad'in
Aina'u. "Banza yi maki baki ba Aina'u, Allah ya shirye ki." Baba ya fad'i yana girgiza kai. Sarah kuwa wani
d'an sauk'i taji a zuciyarta jin Baba ya mayar da Lami d'akinta. Da daddare har d'aki Sarah ta sami Lami
tana kuka tana bata hak'uri akan ta janye tsinuwar da tayi mata, amma ko kallonta bata yi sabida ba
k'aramin fanfo Aina'u tayi mata ba akan Sarah d'in. Sarah d'aki ta koma ta zari mayafi ta nufi pos ta ciro
kud'i har dubu d'ari ta dawo gida ba bawa Lami akan ta karb'i kud'in amma ta yafe mata ta janye batun
tsinuwa. Ganin Aina'u bata nan, sai ta amshe kud'in tace mata taje ta yafe mata. Ajiyar zuciya Sarah ta saki,
sai a sanan taji hankalinta ya kwanta har ta iya tafiya gidansu Muneeba domin a cigaba da yi mata gyaran
jikin da ake mata kullum da safe da kuma daddare. Don yanzu basa had'uwa da _Khalil_ sai dai a waya
kawai. Don Mama (mahaifiyar Muneeba) da kanta tayi magana dashi a waya a kan yayi hak'uri ba zai k'ara
ganin Sarah ba sai ranar aure. Ya amsa ne kawai don yana jin nauyinta. Amma kullum mak'ale take da
waya. Wani lokacin sai mai gyaran jikin ta kwace wayar ta kashe sannan ake yin gyaran a nitse. Aina'u
kuwa, kwana d'aya, biyu, uku, bata ji wani motsi daga gidansu _Khalil_ ba duk da gayyato matan zumunta
da tayi sabida komai ya rushe. Karo ba uku kenan plan d'inta bai yin aiki. "Dole in tafi matakin k'arshe na
hana auran nan." Tana fad'in haka ta fiddo wayarta tare da danna wata number tayi magana tsayin
mintuna goma sannan ta yanke wayar tana murmushi. Tun daga wannan ranar Aina'u bata k'ara nuna
komai ba. Daga k'arshe ma shiga cikinsu Sarah tayi ana ta hidima da ita. Sarah ba k'aramin wani irin
tsananin kyau ta k'ara ba. Sosai dilkan da ake mata ya amshi jikinta. Sai wani glowing take yi kamar wata
kulb'a. Ana gobe d'aurin aure, mai gyaran jiki tayi mata lalli ja da b'aki wanda ya kuma fito da kyawunta
kasancewarta farar mace. Ba k'aramin kyau lallin nan yayi ba. A ranar kuma _Khalil_ ya kasa jurewa ya
dunga rok'on Muneeba akan ta taimaka masa ta fito masa da Sarah da dabara ya ganta ko na mintuna
biyar ne. Muneeba tace masa kar ya damu bayan Isha zata fito masa da ita. Don tun saura kwana biyar biki
Sarah ta koma gidansu Muneeba da zama gaba d'aya. Kamar yanda suka yi alk'awari kuwa, ana idar da
isha'i _Khalil_ yayi parking ta bayan gidansu ga kira Munee a waya. Sarah bata san shirinsu ba, kama
hannunta kawai Munee tayi tare da ce mata tazo ta nuna mata wani abu. Har gaban motar _Khalil_ ta kaita
ta, a jingine ta same sa jikin motar yaci kwalliya cikin wasu k'ananan kayan da suka yi masa matuk'ar kyau.
Da kallo kawai yake ta bin Sarah da idanu ganin wani mahaukacin kyau da ta k'ara yi masa. Sai yaga kamar
canzo masa ita aka yi. "To gata nan, dan Allah kar ku dad'e kaga mama ta fahimci bama cikin gidan." Sai a
sannan _Khalil_ ya kalli Muneeba tare da fad'in, "Godiya nake k'awarmu. In Sha Allah baza mu jima ba."
Wucewa tayi ta bar su tsaye suna kallon juna. "Nayi kewarki" a tare suka fad'i. "Ba wani nan kin ba kiyi
kewa ta ba tun da baki tab'a cewa mu had'u ko a sace ba." Fad'in _Khalil_. "To ai ni tsoro nake ji kar mama
ta gane." Sarah ta fad'i a shagwab'e. Shima shagwab'ewar yayi kamar yanda tayi tare da maimaita tace.
Rufe fuska tayi da hijjab d'inta tare da fad'in, "Ni dai bana so." Nan ma ya kuma kwaikwayonta. K'afa ta
bubbuga a k'afa tare da fad'in, "Ni dai ka bari." dariya yayi tare da fad'in, "To naji, mu shiga mota naga
kamar tsayuwar yana damunki." Da sauri tace, "A'a ni dai na sai na shiga ba. Ai ka ganni, zan wuce kada
mama ta gane bana nan." Waro idanu yayi tare da fad'in, "To ai ko mintuna biyar d'in basu cika ba. A hakan
d'in ne kike cewa kin yi kewata?" Ko kamun Sarah tayi magana wayarta ta soma k'ara, ganin Muneeba ce
duk sai ta rud'e ta shiga fad'in, "Munee ce ke kira na, shikenan na shiga uku watak'ila Mama ta gane bana
gidan. Dan Allah zan wuce gida." ta k'arisa maganar tare da marairaicewa. Bud'e mota yayi tare da fiddo
leda ya ya kama hannunta tare da fad'in, "Ungo wannan inji Hajiya. Amma dan Allah ki tsaya in miki hoto
guda d'aya kawai." ya fad'i tare da fiddo wayarsa yayi mata hoto a jikin motar. Kallonta yayi tare da fad'in,
"Haba mana, smile." Yanda ya fad'i smile d'in ne ya bada dariya. Sai hoton yayi kyau sosai don hatta
dimples d'inta sai da suka lob'a duka. "Kayi wa Hajiya godiya, bye sai da safe." Ta fad'i hakan tare da saurin
juyawa ta soma tafiya. _Khalil_ bai bud'e motarsa ya shiga ba sai da yaga tasha kwana. Taku uku tayi taji an
jawota da k'arfi an toshe bakinta tare da shak'a mata wani abu a cikin tsumma. Take ta sune jikinta gaba
d'aya ya saki. Cikin sauri maza ukun suka tura ta cikin wani k'atoton buhu suka d'aura akan wheelbarrow
tare da turawa har zuwa wajen wata mota golf sannan suka bud'e booth suka jefa ta ciki Sannan suka rufe
tare da shiga suka bar wajen..........

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

*_MATAR SAYYADEE_*
[30/09, 7:11 PM] Rahamanatu: "Ke, bana son hauka! Kaza ce ita da zata b'ata? Ba ke kika kira wayarta ba?
Kamun na juyo yanzu ki nemo min matata a duk inda take idan ba haka ba a kaf zuri'arku bana tunanin
akwai wanda zan iya kyalewa ko jaririne." Yana gama fad'in haka ya katse wayar tare da yin reverse ya fizgi
motar da gudu don har yayi nisa da layin. Muneeba kuwa jikinta ne ya soma wani kakkarwar tsoro zufa na
yanko mata. Wayarta ta haska ta soma bin hanya tana kwala kiran "Sarah" ko Allah zai saka ta amsa. "Inna
lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Fad'in Munee tare da saurin d'ukawa ta d'auki takalmi da kuma ledar da
_Khalil_ ya ba Saran. Kuka Munee ta fashe dashi tare da fad'in, "Inna lillahi wa'inna ilaihir, Allahumma
arji'ini fi musibati. Saratu kina ina? Mun shiga uku, wayyo Allah, Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un." Haka ta
dunga yin gaba tana dawo baya tare da ambatan sunan Allah. _Khalil_ nayin parking ya nufi hanyar da
Sarah tabi a gaban idanunsa, kicib'is suka yi da Muneeba dake kuka tana kiran sunan Allah. "Ke!" Ya daka
mata wani irin tsawa tare da fad'in, "Ki bar wannan haukan kukan ki fad'a min ina matata take." Gaba
d'aya sai Muneeba ta sake rikicewa saboda yanda yake daka mata tsawar. Takalmin Sarah da ledan
hannunta kawai ta mik'a masa jikinta na rawa. Hannu ya kai ya amsa yana kallon ledar da kuma takalmin.
Tabbas ledar da ya bata ne kuma takalmin ma nata ne. Ransa ne ya k'ara b'aci, bai iya yi mata wani magana
ba sai wayarsa da ya fiddo ya danna number d'in ya Abdullah-Hakeem. Ringing uku ya d'auka yana fad'in,
"Ango kasha k'amshi." Shi kuwa _Khalil_ cewa yayi, "Yaya motocin mutanan ku uku nake so yanzu. An sace
Sarah. So nake gaba d'aya daga farkon Jos road har zuwa k'arshe a zuba mutanan ku, duk wanda aka yayi
kala da rashin gaskiya a kama shi." Tashi zaune ya Abdul-Hakeem yayi tare da fad'in, "An sace Saratu?
Wannan ma k'arya ne. Ka kwantar da hankalinka yarinyar nan in Sha Allah baza ta kwana ba. Yanzu zan kira
yaya Abdullah domin ya turo mana da sojoji, kuma zan kira abokina ACP Lawal Yakubu domin a bamu
police guda talatin. Gamu nan zuwa yanzu. Koma wanene yayi wannan aikin zai san ya tab'o jinin Chief
Justice Nurudden Muhammad Ibrahim." Yana gama fad'in haka ya katse wayar tare da soma kiran yaya
Abdullah. Yaya Abdullah ya fisa ma d'aukar zafi don kamar zai fito ta wayar. Kuma take yayi waya bariki aka
turo motar sojoji har biyar. Tun daga Katsina round about mutanan dake Jos road suke jin jiniyar y'an sanda
da sojoji. Matasa gaba d'aya hankalinsu ya tashi. Mutane sai firfitowa suke daga gidajansu suna kallo, wasu
kuma suna dannawa nasu gidan sakata. Y'an daba da y'an shaye-shaye kuma sai nemar mab'oya suka
soma yi. Tun daga farkon Jos road y'an sanda da sojoji suka samu position suka tsaya fuska babu rahama
ko kad'an har k'arshe layin. Su Hajiya Lami kuwa cewa tayi, "Yanzu haka saboda d'aurin auren da za ayi
gobe ne aka turo so domin su bamu tsaro." Na'ima tace, "Babu shakka kam!" Baba dake d'aki kuwa
hakanan yaji hankalinsa bai kwanta ba. Aina'u kuwa gaba d'aya ta kasa sukuni sai lek'e take yi tana kiraye-
kirayen waya. Muneeba kuwa sai kuka take yi a gaban _Khalil_ tana mashi rantsuwar ba da ita aka had'a
baki ba kuma wallahi bata san inda Sarah take ba, bata san ko wa ya sace ta ba. Shikuwa _Khalil_
kwakkwarar motsi ya hanata don cewa yayi bai yarda da ita ba. K'aran jiniyar motocin sojoji da y'an sandan
da suka iso inda suke ne ya k'ara hargitsa mata tunani ta saki wani marayan kuka tana k'an'k'ame jikinta.
"Ke!" Wani soja ya buga mata uban tsawa sai gata a zube a k'asa ta sume dai-dai lokacin da ya Abdul-
Hakeem ya iso wajen. Shi da kansa ya zira hannu ta cikin motar _Khalil_ ya d'auko ruwa tare da yayyafawa
Muneeba. A firgice ta farfad'o tana fad'in, "Wallahi bani bace, ban sa wanda ya sace ta ba, kuma wallahi
bani na kirata a waya ba." Hannu ya Abdul-Hakeem ya saka a baki tare da fad'in, "Shssh! Kwantar da
hankalinki babu abunda za ayi maki a nan wajen. Yi min bayani mai ya faru." Ajiyar zuciya Muneeba ta
sauke tare da fad'in, "Sarah tu a gidan mu take kwana tun saura kwana biyar bakinta. Kuma mama ta hana
mu fita kuma ta cewa _Khalil_ ya hak'ura da zuwa tad'i har sai an kawo masa ita gida sabida ana mata
gyaran jiki. To kullum sai suyi ta damuna su biyu suna cewa suna kewar juna. Shine jiya muka yi waya da shi
_Khalil_ akan in taimaka masa in fito masa da Sarah suga juna ko mintuna biyar ne, shine na fito da ita ba
tare da sanin mama ba na kawo ta wajensa sai na koma gida domin basu waje suyi magana. To K'anwar
Sarah tazo gidan mu tana neman ita Sarah har mama taji shine ta tambaye ni ina Sarah, sai nayi mata
karyar tana ban d'aki shine nayi sauri na fito domin in kira ta mu koma gida. To da nazo nan d'in sai naga
babu motar _Khalil_ sai nayi ta kiran number d'in Sarah amma ba'a d'agawa, daga k'arshe ma aka kashe.
Shine na kira shi _Khalil_ d'in ina tambayarsa Saratu, sai ya fara min ihu wai ai nice na kira ta har ta tsora
tace wata k'ila an gane bata gidan ne sai suka yi sallama ta tafi. Kuma ni wallahi, tallahi ban kira ta ba."
Haushi ne ya kama _Khalil_ jin rantsuwar da tayi akan bata kira Sarah ba, bai san lokacin da ya d'aga hannu
zai wanke fuskanta da mari ba, da sauri Abdul-Hakeem ya tare hannunsa tare da fad'in, "Baka da hankali
ne? Ko in barka kayi binciken ne da kanka? Ashe babu amfanin kiran mu da kayi kenan?" Matsawa baya
_Khalil_ yayi tare da fad'in "I'm sorry." Kallon Muneeba yaya Abdul-Hakeem d'in yayi tare da fad'in, "Ina
wayarki?" Da sauri ta mik'a masa wayar hannunta na rawa shi kuma ya mik'a wani dake gefensa. Cike da
ladabi ya amshi wayar sannan ya sara masa tare da koma cikin mota ya kunna computer ya soma danne-
danne cikin sauri da kwarewa. Muneeba kuwa da mararta ke cike da fitsari, ihu d'aya za'a kuma buga mata
ta saki fitsari. Mintuna biyar sai ga wannan da aka ba waya ya dawo tare da fad'in, "An kira number d'in
sau bakwai mintuna goma sha bakwai baya amma ba'a d'aga ba kuma daga baya aka kashe wayar. Lokacin
da ake kiran wayar ba'a d'aga ba, nabi diddigin layin, makwamusan suna dai-dai round about d'in stadium,
kuma an kashe wayar ne a dai-dai wajen tare da jefar da waya. Don har yanzu diddigin layin na wajen.
Sannan kuma an kira wayar k'arfe bakwai da mintuna arba'in da uku, sai dai har ya gama ringing ba'a
d'auka ba." Da sauri _Khalil_ yace "Lokacin muna tare, kuma a wannan ne Sarah hankalinta ya tashi ta
wuce gida." Abdul-Hakeem ya kalli Muneeba tare da fad'in, "Kin ce baki kira Sarah ba, kuma gashi bincike
ya nuna kin kira da misalin 7:43." Kuka Munee ta saka tare da soma rantsuwa tana fad'in, "Na rantse da
ubangijin da ya halicceni ban kira taba, bani na kira ta ba." "To idan baki kira taba, waye ya kira ta? Kin ba
wata wayar ne a wannan lokacin?" Shuru Muneeba tayi tana tunanin wa ta ba wayar a wannan lokacin?
Kallon Abdul-Hakeem tayi tare da girgiza kai tace, "Ban ba kowa wayata ba a wannan lokacin. Kuma wallahi
ban kira ba." "Oga wannan yarinyar fa baza tayi magana ba har sai mun tafi da ita." Fad'in wani police. Tuni
Muneeba ta soma sakin fitsarin da ya dad'e da cika mata mara tare da durk'usawa a k'asa tace, "Na rantse
da girman Ubangiji da ya halicceni ban sace Saratu ba. Wallahi bani bace. Dan Allah kar ku tafi dani." Yaya
Abdul-Hakeem tun kallon farko da yayi wa Muneeba ya san cewar bata da hannu a cikin sace Sarah da aka
yi, sai dai tabbas duk wanda yayi hakan yana tare da ita amma ita bata san hakan ba. "Wa kika ce tazo
neman Sarah har mamanki taso ta fahimci bata gidan?" Da sauri Muneeba tace, "Aina'u!" Wani harara
_Khalil_ ya watsawa Muneeba tare da fad'in, "Aina'un ce za ta sace Sarah?" Girgiza kai Muneeba tayi tare
da fad'in, "Ba haka nake nufi ba." yaya Abdul-Hakeem kuwa cewa yayi "Aina'u tayi amfani da wayarki ne
lokacin da tazo?" Da sauri Muneeba ta girgiza kai tare da fad'in, "Bata yi ba. Cewa kawai tayi ina Sarah. Ni
kuma nayi saurin janta gefe nace tayi shuru kar mama taji don ta hana mu fita ni kuma na saci hanya na kai
Sarah wajen _Khalil_. Ita kuma sai ta mik'o min kayan Sarah tace in bata baza ta iya jiran Sara ta dawo ba,
don itama jiranta ake yi saurayinta yazo." "Wani irin kaya ta kawo mata, kuma dama Sarah ce tace ta kawo
mata kayan?" Fad'in ya Abdul-Hakeem. "Eh ita ce tace ta kawo mata doguwar rigar baccinta da kuma
hula." Jinjina kai Ya Abdul-Hakeem tare da fad'in "Jeki gida, zan neme ki idan buk'atar hakan ta taso." Da
sauri Muneeba ta juya har da had'awa da gudu ta bar wajen. Shi kuma _Khalil_ a fusace ya kalli ya Abdul-
Hakeem tare da fad'in, "Ya ka barta ta tafi? Ita ce suspect d'in fa." Ko kallonsa ya Abdul-Hakeem bai yi ba,
sai daga ma d'aga kiran da aka yi masa yayi tare da sakawa a kunne. "Ok kar ku tab'a komai gamu nan
zuwa." Yana gama fad'in haka ya yanke wayar tare da kallon _Khalil_ yace, "Shiga mota ka biyo bayan mu."
Shi kuma ya nufi motar da ya shigo bayan ya bawa sauran y'an sandan umarni akan kar ku yarda su bar
wajen har zuwa gobe shi kuma ya shiga motar da ta kawo sa suka nufi Barnawa inda wanda ya kira yanzu
ya fad'a masa. Kasancewar gudu suke yi kuma ga shi dare ne babu mototi akan titi sosai, cikin k'ank'anin
lokaci suka isa. Wasu cincirundo y'an sanda ne a zagaye da wata mota k'irar golf, sai wasu matasa su
shidda an fito dasu sun yi kneeling a k'asa fuskokinsu a kumbure. Abdul-Hakeem na isowa wajen ya fiddo
pistol tare da kicking ya d'aura akan goshin d'aya daga cikin su, zawo ne ya soma zubowa daga jikinsa na
tsoro tare da fad'in, "Kar ka kashe ni dan Allah. Wallahi ba muyi mata komai ba. Tana cikin buhu a bayan
mota." Da jin haka haka ya Abdul-Hakeem nufi bayan motar bayan ya saka hand gloves sannan ya bud'e
tare da warware saman buhun. Da mugun gudu _Khalil_ ya iso wajen zai kai hannu ya d'auko Sarah da
bata da maraba da gawa amma ya Abdul-Hakeem ya tare sa tare da fad'in, "Wait a minute!" _Khalil_ bai
saurari ya Abdul-Hakeem ba ya ciccib'o buhun ya fito dashi tare da fiddo Sarah da gaba d'aya jikinta a sake
yake ya nufi motarsa da ita ya bud'e back seat da d'ayan hannunsa ya shimfid'ar da ita tare da soma ceto
ranta don ya duba pulse d'inta yaga akwai rai a jikinta. Tsabar wahala kawai tasha da kuma abunda suka
shak'a mata. Numfashi ya soma bata ta bakinsa yana hura mata. Sai da ta d'au tsayin lokaci kamun ta ja
wani irin dogon numfashi tare da rirrik'e damatsen _Khalil_ d'in da k'arfi. Wani irin ajiyar zuciya ya saki
tare da d'agota ya had'a da jikinsa ya rungume k'am-k'am. Yana jin yanda bugun zuciyarta ke tafiya da
k'arfi. A can waje kuwa, wani irin mahaukacin duka sojoji hud'u suka rufe su dashi. Sai da suka karya
k'afafun su da hannaye sannan suka jefa su cikin mota. Yaya Abdul-Hakeem kuma k'arisowa yayi ya
kwankwasa motar _Khalil_ sai a sannan ya saki Sarah dake kuka a hankali ya fito daga motar. "Ka mayar da
yarinyar gidan iyayenta. Sojoji da y'an sanda zasu cigaba da bata tsaro har sai an d'aura aure gobe an kawo
ta gida tukun zasu bar layin." _Khalil_ yace, "To yaya. Amma ya akai aka gano su?" Murmushi ya Abdul-
Hakeem yayi tare da fad'in, "Tun da muka gama waya da kai na kira wani daga wajen aikinmu, kwararren
masanin na'ura na tura masa number d'inka. Na number d'inka yabi diddigin layin Sarah. Ko da nake wa
yarinyar nan tambayoyi, wasu na can tuntuni sun bi bayansu har Allah yasa suka damk'o su. Sai dai kuma
koma wanene wanda ya saka aka sace Sarah, ba k'aramin wayau gare shi ba, don bai yarda ya bar wani
makama ba, ko su wanda muka kwamushe yanzu, basu san ko wanene ya basu aikin ba. Kuma da
boyayyiyar number ake basu umarni. Kuma sun ce muryan namiji ne ke basu umarnin." Da mamaki
_Khalil_ yace, "To wanene wannan yake son ganin baya na ta hanyar raba ni da Sarah?" Kai tsaye ya Abdul-
Hakeem yace "Makiyi!" "Allah ya shiga tsakanin mu da koma wanene. Kuma in Sha Allah aure babu fashi.
Gobe za'a d'aura aure." Fad'in _Khalil_. "In Sha Allah. Ma mai masu yarinya gida dare nayi." "To yaya sai na
dawo gidan. Don Allah kar ka fad'awa Hajiya ka santa nan da nan hankalinta ke tashi" Sai da ya hararesa
sannan yace, "To yaya _Khalil_, ai ka san dama bani da hankali." Dariya _Khalil_ yayi tare da bud'e gidan
baya inda Sarah take ciki ya shiga. "Stop crying my baby. Gani a kusa dake. Bazan k'ara bari haka ya faru
dake ba. I'll always protect you my wife. Kiyi hak'uri laifina ne. Da ban zo ba, hakan ba zai faru ba." Share
hawaye Saratu tayi tare da fad'in, "Ko kazo, ko baka zo ba, haka sai ya faru tunda rubutaccen al'amari ne."
Hannu ya kai ya share mata hawayen da suka gangaro tare da fad'in, "Gobe, by this hours, kina kwance a
k'irjina, ba zan bari ko sauro ya hau kan jikinki ba bare kuma d'an Adam." Hannu sara ta saka ta rufe
fuskanta tare da fad'in, "Ni dai ka bari. Mu tafi gida dare nayi." Dariya yayi tare da fita daga motar ya koma
mazaunin drive ya kunna tare da barin wajen ya hau hanya. Sarah ganin basu yi hanyar gidansu Muneeba
ba, sai tace, "Gidan su Muneeba zaka kai ni fa." Sai da ya juyo sannan yace, "Babu gidan wata Muneeba da
zaki k'ara kwana. Gida zan kai ki. Ni ban yarda da Muneeba d'in nan ba. Ina zargin har da saka hannunta a
sace kin da aka yi. Don tana ta rantsuwa wai ita bata kira ki ba lokacin da muna tare dake." Waro idanu
Sarah tayi tare da fad'in, "Dan Allah kar kace haka. Wallahi Muneeba baza ta tab'a cutar dani ba. Babu
hannunta wallahi." Kallon titi yayi tare da fad'in, "love, mugu bashi da kama. Ki bar wannan maganar. Gida
zaki kwana." Kuka Sarah ta saka tana fad'in, "Wallahi Muneeba ba muguwa bace." Banza yayi da ita har
yayi parking a k'ofar gidansu. Uban dandazon sojojin da ya ta gani a k'ofar gidansu sai da ta tsorata. Ganin
da sauri sojoji kusan hud'u sun nufo su tare da bud'e gidan baya ina take, baya san lokacin da ta kwala ihu
ba sai da _Khalil_ ya tsorata tare da fitowa da sauri ya ture wani soja yana fad'in, "Baby lafiya?" Da hannu
tayi masa nuni da, sojan dake tsaye k'ik'am kamar an dasa shi. "Malam matsa mana. Baka ganin tsoranka
take ji." Da sauri sojan ya matsa, shi kuma ga kamo hannunta ya fito da ita. Har tsakar gidansu ya raka ta
dai-dai lokacin da Baba ya fito daga d'aki yana fad'in, "Wanene nan wajen?" Amma ganin _Khalil_ da Sarah
tsaye sai hakan ya bashi mamaki don ga san Sarah a gidan Liman Muhammadu take kwana. "Ibrahim
lafiya? Wani abun ya faru ne? Shiyasa naji jiniyan sojoji ko ta ina kenan d'azu?" Baba ya jero tambayoyi
gabansa na fad'uwa. Jin muryan baba sai gaba d'aya mutanan gidan suka fito. Aina'u kuwa har da cin
tuntub'e tana waro idanu ganin Sarah a tsaye. "Baba wani tsautsayine ya d'an afku, amma Alhamdulillah
yanzu." Daga nan ya kwashe komai ya sanar da baban. Salati Baba da su Na'ima suka d'auka. Lami kuwa
wani uwar yare mai tsawo ta dire tare da fad'in, "Yesu almasihu kana ganin komai. Mak'iya sun fara bina
don sun ga y'ata zata auri babban mutun d'an gidan manyan mutane." _Khalil_ kuwa kunnansa ne suka yi
masa wani duum jin Lami tace _Yesu almasihu_. Bai gama dawowa daga duniyar mamaki ba, Lami ta kuma
cewa, "Ya Uba mai-iko duka, mai-yawan jinkai, mun rantse, mun bache daga tafarkokinka kaman batattun
tumaki. Mun cika bin dabarun zukatanmu da muradinsu. Mun sab'a dokokinka masu-tsarki. Abin da ya
wajabba garemu, mun bari: Abin da ya wajaba mu bari, shi muke yi; Babu lafiya garemu. Amma, Ya
Ubangiji, ka yi mana jinkai, mu masu-sab'o abin tausai. Ya Allah ka yafi masu fad'in laifinsu, Masu tuba kwa
ka amshe su: bissa alkawalin da ka furta ma yan Adam. Almasihu Isa Ubangijinmu, Uba kuma mai-yawan
jinkai, ka sa duk mai neman mu da sharri ya koma masa, kada kayi duba da laifinmu a gare ka. Ya Almasihu
mai-tsarki ka amsa addu'armu Amin." Ba _Khalil_ kad'ai hatta su Nuratu sun firgita da jin maganganun
mahaifiyarsu. Marfu'a kuwa kallon Lami tayi tare da fad'in, "Lami dama ki koma addinin kiristancinki? Inna
lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Gaskiya Lami baki kyauta ba. Shikenan baki da rabo a lahira." Aina'u tayi caraf
tace, "Tunda kece da aljannar sai ki hanata ai. Ai gwara ita an san cewa kirista ce, ke kuma fa? Kina amsa
sunan musulma amma ban tab'a ganin kin aje goshinki a k'asa ba. To Menene marabarku kenan? Kowa dai
yasan bambamcin musulmi da kirista shine Sallah." A fusace Marfu'a tace, "Dan uwarki dake nake
magana? Alhamdulillah tunda da na furta kalma La'ilaha illallah Muhammadur Rasulillah. Kuma dai ai ance
duk wanda ya furta Kalmar bai dauwama a wuta." _Khalil_ gaba d'aya ji yayi kamar ana zare nasa wani abu
a jiki, yayi dana sanin shigowa cikin gidan. Sai yaji dama a k'ofar gida ya tsaya har Sarah ta shige ciki. "Ke,
ba kowa bane yake da rabon shiga addinin kiristancin. Addini na shine addinin gaskiya. Kuma ni tun farko
ban tab'a yin wani addini bayan addinina ba. Addinin ku ya cika tsauri da yawa, mutum yayi da dungure
sau biyar a rana, wata d'aya ana azumi, ba'a sata, ba'a k'arya ba'a saduwa, ba'a shan burkutu. Abubuwa da
yawa addininku sun hana. Addininku addinin takura ne." Sai a lokacin Baba ya bud'e baki tare da fad'in,
"Ke Lami! Ki kiyaye harshenki. Addinin Musulmi addinine na gaskiya kuma addini ne mai bawa kowa y'anci.
Duk abunda kika lissafo addinin da kike ik'irararin shi kike yi, shima yayi hani akai. Babu wani Bible d'in da
ya halasta duk abunda kika lissafo. Idan kinga dama ki zama mara addini gaba d'aya, wannan ruwanki ne. A
gaban sirikinki kike wad'annan maganganun sabida baki da hankali da tunani." Da sauri _Khalil_ yace
"Baba sai da safe, sai da safe Sarah." Yana fad'in haka ya juya. Aina'u kuwa wani farin ciki taji ya ziyarci
zuciyarta ganin reaction d'in _Khalil_. Tana ji a jikinta auren Sarah dashi ba zai yuwu ba gobe. Baba juyawa
yayi tare da shiga d'aki Sarah ta bishi a baya. Su Nuratu ma suka shige d'aki. Aina'u kuwa, hanyar toilet ta
nufa. Tana shiga ta rufo k'ofar tare da kiran wata number bayan ta shiga magic voice ta mayar dashi na
tsofaffi sannan ta b'oye number. Ringing uku aka d'aga wayar tare da fad'in, "Zance ya b'aci, su Arowa suna
state CID yanzu haka. Sai dai sunana bai fito ba, don kamar yanda ake b'oye number ana canza muryoyi
ana kirana, nima haka nake musu. Ni dai koma wanene nake magana dashi yanzu haka, bamu da matsala
domin babu wanda ya san mu." Aina'u wani murmushin jin dad'i tayi duk da tasan ko ta fashe babu wanda
zai kamata don bata bada k'ofar da za'a ganeta ba. "Yayi kyau! Zan kira ka idan wani aikin ya kuma
b'ullowa." Tana gama fad'in haka ta yanke kiran ta fito daga bayin ta koma d'aki." "Baba wallahi ban san ko
su wanene suka min haka ba. Amma ga dukkan alamu anso ayi garkuwa dani domin kud'i. Tunda kaga da
zan ba'a yi hakan ba sai da aure na ya kusa kuma da d'an Chief Justice Nurudden Muhammad." Ajiyar
zuciya Baba yayi tare da fad'in, "Ubangiji Allah ya kare ki daga sharrin mutum da aljan. Wannan aure kuma,
idan ma anyi hakan ne domin a fasa,in sha Allah an riga an d'aura a sama, shaidar duniya kawai ake jira.
Tashi kije ki kwanta, in Sha Allah da safe zan je can gidan liman Muhammadu inyi masa bayani komai. Ni
kai na ban ji a jikina Muneeba zata had'a baki da wasu domin a sace ki. Amma zan je gidan gobe da safe."
"To Baba Allah ya kai mu." Sarah ta fad'i tare da ficewa daga d'akin ta koma nasu. "Sarah kin tab'a karanta
littafin hausa mai suna _Ayi dai mu gani_?" Fad'in Aina'u tana mai danna wayarta. Kallon Sarah tayi tare da
fad'in, "Kin fara karatun novels ne na hausa?" Sarah ta fad'i tana mai kallonta. Ba tare da Aina'u ta kalleta
ba tace, "Eh, yau kwana uku da na fara da wani littafi mai suna _Iska na wahalar da mai kayan kara_, yanzu
kuma _Ayi dai mu gani_ nake karantawa." Girgiza kai Sarah tayi tare da fad'in, "Gaskiya ban karanta ba.
Ban ga kinyi lalle ba, kuma har nan na turo mai lalli d'azu da safe. Su Na'ima duk anyi masu ja da b'aki."
Tab'e baki Aina'u tayi tare da fad'in, "Ni kinsan lalli bai dame ni ba. Kuma da safe bani nan naje kitso. Za
kuyi wani program ne?" Zama Sarah tayi a bak'in gadon tare da nannad'o gashin ganta ta tura cikin hula ta
k'eya tare da jawo hulan har zuwa goshinta saboda kar gyaran kan da akai mata ya lalace. Tace, "Eh, naga
duk su Na'ima ma sunyi kitson ai. Ni ko da da nake saka attachment, ba zan iya yin wannan uban k'ananan
kitson ba. Na'ima muga naki, kamar yafi na Aina'u k'anana ko?" Sarah ta fad'i maganar tana kallon kan
Na'ima wacce taja hulan kanta baya. "Wai! Gaskiya kitson yayi k'ana. Sauk'in ta ma a can inda kukai kitson
ake tsefe maku." Nuratu tace, "Ni ko kinga nawa bai kai nasu k'anana ba. Ghana weaving akai min manya."
Ta fad'i maganar tana mai jan hular kanta. "Ni da Hassana fixing kawai akai mata. Don wallahi naji bazan
iya zaman kitson ba. Basir!" Fad'in Marfu'a tana mai zame Fadwa da ta gama shayar da ita daga jikinta ta
kwantar. "Amma dai ba anan zata kwana ba ko? Don na tsani kukan daren nan da take yi. Duk ta hana
mutum bacci." fad'in Aina'u. "To nan zata kwana. Ni ban san wani uban gulmar ce ta dawo dake kwana
anan d'akin ba, ai da a d'akin Lami kike kwana." Cike da rashin kunya Aina'u tace, "To nan d'in naga damar
dawowa da kwana. Ai gidan ubana ne." Ficewa daga d'akin Sarah tayi ganin zasu fara raba halin nasu da
suka saba. D'akin Baba tayi sallama ta shiga. Zaune ta same shi a kan gado yana kallon Sunna Tv. "Baba dan
Allah wayarka zaka ara min." Ba tare da yace komai ba ya d'auko wayar a gefensa ya mik'a mata ita kuma
ta amsa tare da ficewa. Number d'in _Khalil_ tayi dialing, ringing biyu yayi sai yayi rejecting tare da biyo
kiran. Sarah na d'agawa yace, "Assalamu alaikum Baba." Sarah sai ta canza murya tare da fad'in,
"Wa'alaikassalam d'ana." A tare suka saki dariya, _Khalil_ yace, "Ke nine d'an naki? Za kiyi bayani gobe a
irin wannan lokacin." Hararar wayar Sarah tayi tare da fad'in, "Bayanin mai zan yi? Ni babu wani bayani da
zan yi." Dariya _Khalil_ yayi tare da fad'in, "Kuma kin san na mance y'an iskan da suka d'auke min ke sun
yar da wayarki, wallahi na kira yafi sau shurin masak'i, dole ma gobe da sassafe in kawo maki waya. Ba zan
juri rashin jin muryanki ba." "To bayan gobe zamu kasance tare har abada." Sarah ta fad'i a kunyace.
"Na'am, maimaita dan Allah love." K'it ta kashe wayar tare da mayarwa Baba wayarsa. Daga can kuwa
_Khalil_ kamar ya fasa ihu, yana tsoron kira yaji wayar a hannun Baba. Washa gari da sassafe kamar yanda
_Khalil_ ya fad'i, sai gashi da sabuwar waya k'irar LG mai tsananin kyau da tsada, wani tsohon MTN sim
d'insa ya saka mata a ciki ya kawo mata. Na'ima ta fito zata shago ta gansu a tsaye suna magana. Wani irin
kyau suka mata, sai taga kamar anyi su don juna ne don ba k'aramin dacewa suka yi ba. "K'anina ayi hak'uri
haka, anjima kad'an zamu kawo maka ita." Murmushi kawai _Khalil_ yayi ita kuma ta wuce. Dai-dai nan
Muneeba ta iso wajen, tana ganin _Khalil_ ta juya da sauri. Shima _Khalil_ da sauri yabi bayanta yana kiran
sunanta don jiyan sunyi magana sosai da ya Abdul-Hakeem ya fahimtar dashi Muneeba bata da hannu a
ciki. "K'awarmu dan Allah kiyi hak'uri da abunda ya faru jiya. Tashin hankali ne ta saka nayi abunda nayi.
Koma wanene a matsayina abunda nayi shi zai yi. Kiyi hak'uri kinga ma na kama kunnena. Kar ki manta ke
kika ce min in kula da k'awarki sosai kada tayi kuka. To hud'ubarne ya shiga kunnena." Kuka Munee ta
fashe dashi tare da fad'in, "Naji tsoro jiya, banyi bacci ba. Mama kwana tayi tana mun fad'a. Sai da baban
Sarah yazo gidan mu yayi mana bayanin anga Sarah sannan hankalinmu ya kwanta. Wallahi ko a cikin
mafarkina bai tab'a zuwarmin in cutar da Saratu ba." "Naji na yarda dake Muniba. Dan Allah kiyi hak'uri."
Fad'in _Khalil_. Sai da ta murgud'a baki sannan tace, "Na hak'ura dan ba halinka ba." Sai ta juya ta kalli
Sarah data k'ariso ta rungumeta tare da fad'in, "Alhamdulillah k'awata. Duk wanda yayi maki wannan abun
Allah ya tona asirinsa." Da Ameen Sarah ta amsa tare da jan hannunta bayan ta d'agawa _Khalil_ hannu.
Baki _Khalil_ ya bud'e tare da fad'in, "Har munyi sallama." Muneeba tace, "Anjima zamu kawo maka ita sai
kaga dama ka barta tazo wajen mu." _Khalil_ kuwa cikin zuciyarsa cewa yayi, "Kamar kuwa kin sani. Don
ina raba Sarah da wannan gidan, ko zata zo to tabbas ina jiranta a waje, tana gama gaishe da Baba zata fito
mu wuce." Kan kace me, gaba d'aya gidan su Sarah ya cika da mutane har da y'an unguwa da basu tab'a
shigowa ba. Don Na'ima gida-gida tabi ta kai masu chewing gum. Bamu abunda ke tashi sai k'amshin soye-
soyen nama sa, rago da kaji. Don shanu k'osassu biyu aka yanka, raguna hud'u kaji d'ari da hamsin. Y'an
matan zumunta kuwa sun fi hamsin sunyi ankon wani koriyar atamfa sai hada-hada suke yi baki na motsi.
Sarah kuwa komawa gidansu Munee tayi don acan suke sitting. Mai make-up tazo ta tsan-tsara mata
kamar ka sace ka gudu. K'arfe d'aya da mintuna sha biyu wasu uban jiniya mai tafe da convoy na ya
Abdullah suka shigo layin kasancewar k'arfe d'aya da rabi za'a d'aura auren anan masallacin layinsu. Sai ga
tawagar manya-manyan mutane da abokan mahaifinsu. Jos road kamar zata tsage sabida mutane.
Muneeba hannun Sarah ta kama suka koma can d'akin Baba mahaifin Muneeban sabida kiran wayarta da
_Khalil_ d'in yake ta yi don wayar Sarah na hannunta. Kuma nan gidan ma a cike yake da k'awayensu na
islamiya da poly. Don duk sai da Na'ima ta gayyace su. Bayan ta bata wayar ta fita. Sarah na picking ta jiyo
zazzak'ar muryan _Khalil_ na mata wak'a, If you make me clean I will be clean. If you make me whole I will
be whole. If you make me yours I will be yours And I won't run anymore. If I seek you, will I find you there.
If I call your name will you still hear
Is it too late or can I start again
Can I begin again
Oh. Don't ever let me go
Oh... Don't ever let me go
Oh... Don't ever let me go
Don't ever let me go
Can you drown it in the deepest sea. Can you cast it far as west from east
Can you raise me up to live again
So I can live again
Oh... Don't ever let me go
Oh... Don't ever let me go
Oh... Don't ever let me go
Don't ever let me go
I'm surrendering my will
You are crumbling all the walls I've built
My defence is coming down
Down
I can't deny you
I am broken open wide
Now you can come inside
My defences have come down
Down
I can't deny you
I'm surrendering my will
You are crumbling all the walls I've built
My defence is coming down
Down
I can't deny you
I am broken open wide
Now you can come inside
My defences have come down
Down
I can't deny you
Oh... Don't ever let me go
Oh... Don't ever let me go
Oh... Don't ever let me go
Don't ever let me go
Oh... Don't ever let me go
Oh... Don't ever let me go
Oh... Don't ever let me go
Don't ever let me go
Don't ever let me go
Don't ever let me go. "I will never let you go. Never, ever!" Fad'in Sarah. "And I'll always be there for you
my love. Sai mun had'u anjima." Yana gama fad'in haka ya katse wayar. Aina'u na tsaye a tsakar gida abun
duniya duk ya isheta ta jiyo shalar da ya tsayar da bugun numfashin ta zube a k'asa sume. "An d'aura auren
_Ibrahim Khalil Muhammad Nurudden_ da amaryarsa _Saratu Nuhu_ akan sadaki naira na gugan nera har
dubu d'ari biyar, lakadan ba ajalan ba."

_KANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 THROUGH THIS ACCOUNT NUMBER, 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH 08128755583_

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*
*MATAR SAYYADEE*
[30/09, 7:11 PM] Rahamanatu: Da gudu mutane suka yo kanta suna mata firfita. Lami kuwa kuka ta fashe
dashi tare da, "Mun dawo gareka Yesu, munyi tuba mun nemi yafiyarka. Masu bin mu da sharri ka jefesu
da mutu. Almasihu kayi tsinuwa mai tsayi a garesu." Aunty Rose Merry tace, "Elizabeth me ke faruwa? Mai
ya sami Lili (Aina'u)." Ita haka take kiran Aina'u. Lami ta fyace majina tare da fad'in, "Rose, don anga yarana
suna da farin jini kamar ni dai, shine ake binsu da sharri, jiya ma haka aka sace Sarah sai can dare aka
ganta, yau kuma Aina'u. Kwana biyun nan haka take suma. Idan na tambayeta ko wani waje na mata ciwo
ne, sai tace min basir da zazzab'i ke damunta." Wata mak'ociyar Lami tayi wufff tace, "Aikuwa Lami ki tashi
tsaye, don basir mummunar ciwo ne don har hauka yana sakawa." Hannu biyu Lami ta d'aga ta kyasta
yatsunta tare da fad'in, "Yesu almasihu mai tsarki ba zai tab'a bari y'ata tayi hauka ba. Over my dead
body!" Dai-dai nan Aina'u ta farfad'o tana mai fashewa da kuka tare da tambayar, "An d'aura da gaske?"
Y'an biki sai aka koma kallon juna. Aunty Rose Merry tace, "Lili mai aka d'aura?" Jin katob'arar da tayi sai
tayi tsit ba tare da ta cewa aunty Rose d'in komai ba. D'aga ta Lami tayi tare da fad'in, "Basir d'in ne
Aina'u?" Kai kawai Aina'u ta d'aga mata tare da nufa d'akinsu domin canza kaya don ruwar da aka zubar a
wajen na girki ya b'ata mata jiki. Can gidan su Muneeba kuwa, a kunna Sarah aka d'aura auren don ana
shirye-shiryen fara siga ya kirata a waya tana sauraran komai tana hawayen farin ciki. Ana fad'in salati
goma ga annabi ta zube a k'asa tayi sujjada. Ta jima bata d'ago tana tsiyayar da hawayen farin ciki
kasancewa mata aure da wanda take so. Sai da Munee dake kusa da ita ta d'ago ta tukun. Sai ta fashe da
kuma tare da rungume Muneeba tana fad'in, "Alhamdulillah!" Gaba d'aya d'akin sai su hau fad'in *_ ‫باَرَك‬
‫ َو َج َم َع َبْيَنُك َم ا ِفي َخ ْيٍر‬، ‫ َو َباَرَك َع َلْيَك‬، ‫ُهَّللا َلَك‬._*
*_Barakal-lahu lak, wabaraka ‘alayk, wajama’a baynakuma fee khayr._* Ma'ana, _Allah Ya sanya albarka a
gareki, yayi maki albarka kuma ya hada tsakaninku da alheri._ A tare gaba d'aya suka amsa da ameen. Ya
Abdullah ba k'aramin b'arin kud'i yayi, don duk wanda ya samu halartar d'aurin auren nan ya samu kyautar
k'atuwar jaka mai d'auke da kwalbar turare mai tsada wanda kud'insa ya kai 75k da agogo da kuma take
away mai d'auke da lafiyayyar friedrice with chicken da kwalin exotic da ruwan gora da kuma kyautar kud'i
har dubu biyar. Ko ina labarin d'aurin auren ake yi. Layin kuwa damk'an kamar ana d'aurin auren shugaban
k'asa ko kuma y'ar sarki. Don ma akwai uban sojoji da y'an sanda da aka zuba sabida tsaro. Can cikin gidan
su Muneeba kuwa, nan naga y'an gayyar sod'i, su Hajiya akarammiya Queen Zarah sai zazzare idanu ake yi
ana yagar tsokar kaza, bayanta kuwa gaba d'aya y'an comments section ko wacce da plates d'inta mai
d'auke da uban abinci da kaji ga kuma k'atuwar jaka rataye a hammata wanda za ayi guzuri.😜 K'arfe bakwai
dai-dai sai ga wasu had'ad'd'un mota sun shigo layin na d'aukar amarya. Wata arniyar mota *_Czinger
21clC_* wacce kyauta ce ga ango zuwa ga amarya ita ce a tsakiyar convoy d'in motocin, kuma a itan ne
za'a saka amarya. Y'an comments section sai tureniyar shiga mota ake yi. Can na hango Oum Muslim dake
fama da laulayi suna y'ar matsatsi ita da Mrs dimples. Su takwas suka gwamutsu a bayan motar,
Rahamanatou kerere na hangota a saman cinyar Hadiza Mbello. Mama mahaifiyar Muneeba ta kama
hannun Sarah wacce ke rizgar kuka har gaban Baba ta durk'usar da ita sannan ta fita daga d'akin. Baba ma
hawayen yake yi, don duk kaf Y'ay'ansa babu kamar Sarah. "Saratu! Ni dai alfarmar da nake nema a
wajenki shine, ki tausaya min ki tausayawa kanki ki natsu a gidan mijinki. Yi, nayi, bari na bari. Dan girman
Allah ko da wasa kada ki yarda ki b'ata masa rai, kar ki cutar dashi kuma kar a had'a baki a cutar dashi, ki
rik'e sirrinki, duk rintsi kar ki yarda ki rik'a yad'a tsakaninki da mijinki. Ki koyi tauna magana kamun ki
firtawa mijinki, ko kiyaye cikinsa, sannan ki kar ki yarda ki nuna farin ciki yayin da yake cikin bak'in ciki,
haka kar kiyi b'akin ciki yayin da yake cikin farin ciki. Kar ki yarda ki soma kai k'ararsa wajen mahaifiyarsa
idan ba abun bane da ya zama dole iyaye suji, yawan kai k'ara na sa duk yanda mutum yake jinki a ransa
lokaci guda ko gunduresa tare da fita ransa. Saratu ina baki shawarar nan ne cike da umarni a matsayina na
mahaifinki. Idan har kika rik'e wannan abubuwan da ba fad'a maki, zaki ci ribar zaman aure in Sha Allah.
Allah yayi maki albarka ya baku zaman lafiya da zuri'a d'ayyiba." Yana kawowa nan Sarah ta fashe da wani
irin kuka tare da rungume Baba k'ank'am tana fad'in, "Ka yafe min duk wani laifin da na tab'a yi maka
wanda na sani da wanda ban sani ba. In Sha Allah nasiharka babu wacce zata bar kunne, ruhina har zuwa
gangan jikina. Baba ka yafe min." Hawaye Baba yake yi yana fad'in, "Baki min komai ba sai biyayya Saratu,
na yafe maki duniya da lahira. Allah ya maki albarka. Kuzo ku tafi da ita gidan mijinta." Baba ya k'arisa tare
da d'aga murya don su Maman Muneeba suji. Dakyar maman Muneeba suka janyeta zuwa d'akin Lami,
"To, Lami ga y'arki nan zata wuce gida miji. Kiyi mata nasihar zaman aure." Gaba d'aya k'awayen Lami y'an
Zumunta suka had'a baki wajen fad'in, "Yesu almasihu ya tsareki a gidan mijinki, ya kare ki daga idanun
mak'iya da munafukai. Yesu ya kawo zuri'a mai yawa da albarka." Lami kuwa cewa tayi, "To Sarah, ni dai
abunda zan fad'a maki shine kar ki dai manta duk rintsi nice na kawo ki duniya, idan kika samu hutu da
abun arziki kika kyale ni, daga nan zanyi rok'o Yesu ya tsinewa zaman aurenki. To, ni dai babu ruwana." Da
sauri maman Muneeba tace, "Haba Lami ke kuwa, ke da zaki saka albarka sai ko b'ige da wannan irin
maganganu haka. Bai dace ba." Mik'ewa Lami tayi tare da fad'in, "Naji k'arar bus d'in da nayi maku haya ta
iso. Ku firfito kuje kada motoci d'aukar amarya su tafi, ni bazan samu zuwa ba sabida har yanzu Aina'u na
kwance babu lafiya." A cikin zuciya maman Muneeba tace, "To ai mu Alhamdulillah za muce da wannan
rashin lafiya, don da kije ki bar abun kunya gwara kinyi zamanki. Dama kuma mai zai kai uwar amarya kai
amarya." Amma a zahiri sai d'ago Sarah tayi tare da fad'in, "Tashi muje Allah zai albarkaci aurenki in Sha
Allah." Sai da ta saka ta cikin motar sannan ta shiga, mutane biyu daga cikin mak'ota suma suka shiga tare
da rufe motar sai da motocin suka yi gaba kamun sauran tawagar y'an sanda da sojoji suka bisu a baya har
gidansu _Khalil_. Matan zumunta sun buga uban layi biyu a k'ofar gate, sanye suke da koriyar atamfa da
farar less kan nan yasha d'aurin gwargwaro orange mai ratsin green hannunsu sanye da farin safar hannu.
Sai wak'a suke yi suna layi kamar zasu fad'i sai kuma su zabura su saki wani irin ihu suna fad'in, "praise the
Lord!" Sai sauran suce, "Halleluyah!" Mai gadi kuwa k'in bud'e masa gate yayi sai da K'anwar Hajiya wacce
aka je d'auko amarya tare da ita tayi masa magana sannan ya bud'e suka shiga da ihu suna fad'in, "Yesu
almasihu mai girma mun gode maka da ka kawo yarinyarmu cikin wannan gida mai girma da kyau." Gaba
d'aya y'an biki dangin hajiya da na mahaifin _Khalil_ suka fito suna kallon abun mamaki. Motar amarya
kuwa har k'ofar d'akinta ya ajiye ta. Maman Muneeba ta kama hannunta har k'ofar d'akin sannan tace,
"Saratu yi Bismillah ki shiga da k'afar dama." Sarah tayi kamar yanda mama ta umarceta. Gaba d'aya kusan
zuciyoyinsu tsayawa yayi da bugawa lokacin da suka yi arba da had'ad'd'en parlourn Sarah wanda yaji
Turkish furniture masu kyau da tsada. Curtains da lallausar center carpet d'in d'akin kawai abun kallo ne.
Tv d'inta irin curve d'in nan rafgege dashi. Tsaruwar d'akin baki ba zai iya misaltawa ba. Y'an matan
zumunta da suka shigo, wani irin gud'a suka saki tare da soma wak'a. Sune har d'ayan parlourn da yake
k'asa kasanslcewar parlour biyu ne a k'asa. Basu ga tsan-tsan kyau da tsaruwa ba sai da suka haura sama.
Daga parlour har zuwa bedrooms abun kallo ne. Su Na'ima kuwa ko wacce sai da ta d'au video a waya.
Bayan an gama kallon d'aki har kitchen da aka loda uban kayan abinci a store, don babu abunda _Khalil_
bai zuba ba har da kaji da naman rago a deep freezer. Daga nan suka d'auki Sarah suka nufi cikin gida
wajen Hajiyan _Khalil_ don mik'a ta amana, sai dai nan suka bar matan zumunta a parlourn Sarah gudun
kar kuje suyi abun kunya. Hannu bibbiyu hajiya da y'an uwanta suka amshe su. Don lokaci da suka iso
gidan tare da tawagar y'an matan zumunta, dangin hajiya suka yi gangami domin isar da gulma, tuni Hajiya
tayiwa tufkar hanci kuma tace bata son tsegumi da tashin hankali. Sai kowa ya gumtse guntun gulmarsa
yayi shuru.

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*
[30/09, 7:11 PM] Rahamanatu: Sai da suka je gaban Hajiya sannan suka durƙusar da Sarah. Da sauri Hajiya
ta taro ta tare da faɗin, 'Ɗiyata dawo nan kusa dani ki zauna, kar ki zauna a ƙasa." Faɗin Hajiya bayan ta
zaunar da Sarah kusa da ita wacce fuskarta ke lulluɓe da gyale. "To Hajiya ga ƴarki nan Sarah, don Allah a
saka mata idanu, idan tayi ba dai-dai ba a kwaɓa mata. A riƙa nuna mata abunda ya kamata, sannan dan
Allah a riƙa hakuri da ita yarinya ce. Ki ɗauke ta tamkar _Khalil_, yanda zaki hukuntasa idan yayi laifi, haka
itama zaki hukuntata. Basu da bambamci a wajenki." Faɗin maman Muneeba. Murmushi Hajiya tayi tare
da kamo kafaɗun Sarah tare da faɗin, "Sarah ɗiyata ce ba suruka ba. Ba kuda damuwa domin gida kuka
kawota. Allah ubangiji ya basu zaman lafiya mai ɗorewa da zuri'a ɗayyiba." Da ameen duka ƴan ɗakin suka
amsa. "Laure, fito min da akwatin nan." Hajiya ta faɗi da ƙarfi saboda Lauren ba a kusa da ita take ba.
Laure ta fito tare da akwatin da hajiyan ta umurceta da ta fito dashi tana ja da kyar don danƙam yake da
kaya a ciki. "Ga kyauta nan zuwa ga ɗiyata. Allah ya bada zaman lafiya mai amfani." Godiya su maman
Muneeba suke tayi sannan suka ɗauki akwatin, har ƙofa Hajiya ta rako Sarah tana ta saka mata albarka.
Bayan sun dawo ɗakin Sarah sai suka buɗe akwatin tare da fiddo kayan ciki. Turaruka ne irin na gida su
humra masu ƙamshi da su turaren wuta na rushi na jiki, kaya, ɗaki da kuma tsuguno. Sai abayoyi da lafayas
masu yawa da kuma tsana. Bayan kowa ya gama gani sai suka mayar da komai suka rufe suka ɗaura mata a
saman wardrobe. A parlour kuwa, matan zumunta kowacce ta fiddo da hoda da jan baki tana ƙara gyara
fuskarta saboda samun labarin za'a tafi dinner yanzu. Su maman Muneeba kuwa, faɗa suka ƙara yiwa
Sarah sosai kamun suka yi mata sallama. Kuka Sarah ta fashe dashi ganin zasu tafi su barta har da
Muneeba don mahaifinta yace ƙafarta ƙafar mahaifiyarta. Munee rungume Sarah tayi suna kukan tare.
Dakyar mama ta raba su ganin zasu ɓata masu lokaci kuma ana jiransu a waje domin a maida su gida.
Bayan sun tafi sai yarage daga ita sai matan zumunta da kuma ƴan uwanta dake ta shirye-shiryen zuwa
party. Kowacce sai ƙure a daka take yi. Wata budurwa ce ta shigo hannunta riƙe da wani ƙatoton kit na
makeup. "Dan Allah ina amaryar da za'a shirya? Lokaci na ƙurewa." Da hannu Na'ima tayi mata nuni da
hanyar ɗakin da Sarah take ciki tare da cigaba da shafa powder ɗinta. Budurwar ta haura sama tare da
shiga ɗakin da Sarah take ciki, waya ta sameta tana yi. Sai da ta gama wayar da take yi da _Khalil_ sannan
ta juyo ta kalli budurwar. Murmushi budurwar tayi tare da faɗin, "Angonki ne ya turo ni inyi maki kwalliyar
zuwa dinner." Murmushi Sarah ta mayar mata tare da faɗin, "Ok, amma dan Allah kiyi min haƙuri inyi sallar
isha'i." Zama makeup artist ɗin tayi tare da faɗin, "Babu matsala. Yi sallar ki." Ko da Sarah ta idar da Sallah,
gaba ɗaya an gama kwashe su Na'ima da ƴan matan zumunta zuwa wajen dinner. Sai da mekeup artist
ɗinnan ta fiddo mata da wata lafiyayyiyar gown a cikin wani dogon kwali kalar milk ta saka sannan ta soma
yi mata kwalliya. Ba ƙaramin kyau tayi ba. Rigar kamar don ita aka yi sa saboda yanda ya amshi jikinta. Ita
kanta makeup artist ɗin bata taɓa yiwa amarya kwalliyar da ya ruɗa ta ba irin Sarah. Ba ƙaramin kyau tayi
ba. Tuni tayi mata mahaukatan pictures ta watsa a whatsapp status, Facebook da instagram sannan ta
rubuta _The beautiful bride of Ibrahim Khalilullah Nurudden Muhammad son of late ChiefJustice
Nurudden Muhammad)_ a ƙasan hoton. Sai ga uban likes. Comment kuwa babu adadi, na masu addu'a da
kuma masu mamakin auren don ba'a yaɗa a social media ba. Ƙarfe takwas da arba'in wata auntyn _Khalil_
ta shigo tare da kamo hannun Sarah suka fita daga dakin tare da rufowa. Har gaban lafiyayyiyar sabuwar
motar _Khalil_ ta kaita tare da buɗe gidan baya ta saka ta a ciki sannan ta rufo ƙofar. Lumshe idanu tayi
tare da shaƙo kamshin turaren _Imperial Majesty_. A hankali ta buɗe idanunta jin hannun _Khalil_ a cikin
nata hannun. Kai hannun saitin bakinsa yayi tare da kissing sannan yace, "You look very beautiful wifey."
Ɗagowa tayi suka haɗa idanun, kasa ƙifta idanun tayi saboda wani irin kyau da yayi, shi sanye yake cikin
ɗanyan shadda golden colour wanda ɗinkin ya amshi kayan da kuma jikinsa. Hura mata iskar bakinsa yayi a
fuska tare da ɗage gira yace, "Wannan kallo haka, cinyeni za kiyi?" Kau da kai tayi tare da faɗin, "Kayi kyau
da yawa ne ai." Juyowa yayi yana facing ɗinta sosai tare da faɗin, "Juyo ki kalli mijinki da kyau, naki ne ke
ɗaya. Ni wallahi duk kishi ya kama ni kamar mu juya kawai mu koma gida abun mu. Kyawun da kika yi is
over love." Ya faɗi hakan yana mai jawota jikinsa gaba ɗaya. Da sauri ta tashi a kan jikin nasa tana mai
nuna masa driver da idanunta. Ɗage gira yayi tare da faɗin, "Kar ki damu makaho ne baya ganin mutanen
dake cikin motarsa musamman da daddare. Bar ni naji ɗumin matata." Ya faɗi yana mai ƙara jawota
jikinsa. "Ni dai kwalliyata wallahi!" Ta faɗi cike da shagwaɓa. "Ai ni akai wa. Barni na more abuna." Ya faɗi
hakan ba tare da ya sake ta ba har suka cikin wajen da ake taron. Sai da aka shiga aka sanar da zuwansu
sannan su Na'ima suka fito tare da abokan _Khalil_ ɗin waɗanda za suyi masu jagora zuwa ciki. Su Na'ima
sune a gaba sai ango da amarya a tsakiya, abokan ango kuma a baya. Sai da suka zo kofar shiga hall ɗin sai
suka tsaya, MC kuma ya saki wakar _Laye_ ta kiss Daniel. Gaba ɗaya hall ɗin ya kaure da tafi saboda
shigowar ango da amarya. Sai da suka ɗan taka kamun suka isa wajen da aka tanada domin su suka zauna.
Mc ya kira sunan Hajiya umaima k'anwar mahaifin _Khalil_ tazo ta buɗe taro da addu'a tare da yiwa ango
da amarya fatan alkhairi. Tun tana yi aunty Rose Merry taje ta yiwa Mc raɗa a kunne. Aunty Umaima na
komawa wajen zamanta Mc ya kira aunty Rose Merry daga da dangin amarya domin itama tayi jawabi tare
da sakawa ango da amarya albarka. Da taku ɗai-ɗai aunty Rose Merry ta fito tare da karɓan mic ɗin tace,
"Da farko dai ina godiya ga Yesu Almasihu da ya nuna mana wannan rana na auren ƴata Sera (Sarah).
Praise the Lord!" Ta faɗi da ƙarfi yayin da matan zumunta suka haɗa baki da ƙarfi suka bata amsa da
"Hallelujah!" Gaba ɗaya hall ɗin ya ɗau wani irin shuru kowa da abunda yake faɗi a zuciya. Aunty Rose
Merry ta cigaba da faɗin, "Na dawo gareka ɗana. Wannan yarinya dake kusa da kai, ka riƙe ta gaskiya bisa
amana. Idan kayi haka, Allah zai yi maka albarka. Praise the Lord!" Ta ƙarisa maganar da ƙarfi ƴan matan
zumunta suka amsa mata da "Hallelujah!" Ta cigaba, "Ka bata duk hakkinta da yake kanka. Kar ka barta da
yunwan ciki. Sannan kar ka riƙa yin nisa da ita, ka kasance kullum a tare da ita kusa-kusa sosai. Kar ka barta
da yunwarka, ka bata kanka da lokacin ka duk lokacin da ta buƙata. Kar ka bari ta kalli waninka da sha'awa,
ka kasance jarumi sosai." Tana kawowa nan gaba ɗaya hall ɗin aka fashe da dariya don kowa ya fahimci
mai take nufi. Ita kuwa sai cigaba da magana tayi ko a jikinta, "Ke kuma amarya na dawo kanki, kar ki
kuskura ki bari mijinki yaji sha'awar wata mace, ki bashi hakkinsa gaba ɗaya, kiyi masa girki mai daɗi, ki
bashi a baki, idan yazo saduwa dake kar kiyi masa yanga. Duk position da ya saki, ki tsaya cak, idan kuma
kince za kiyi yanga, kina kallo karuwai za su tafi da kurwar mijinki. A toh!" Nan ma Wani dariyar aka kuma
fashewa dashi, Sarah kuwa kunya kamar zata kashe ta. _Khalil_ kuwa murmushi kawai yayi tare da girgiza
kai. Aunty Rose Merry kai mic dai-dai bakinta tayi kamar zata cinye tare da soma waƙa, " _Ango idan kayi
da kyau, akwai sakamo, kar kayi mugunta zaka girbe watarana!" Ƴan matan zumunta an kunnosu, gaba
ɗaya suka fito suka hau amshi da, " _Amarya idan kinyi da kyau akwai sakamakon, kar kiyi mugunta zaki
girbe watarana_" Mc yace, "Mun gode, mun gode, mun gode. Dan Allah jama'a a tafa masu" Gaba ɗaya
wajen ya kaure da tafi shi kuma ya karɓi Mic ɗin hannun aunty Rose Merry suka koma mazauninsu. Daga
nan aka shiga shagulgulan biki. Mc ya kira ango da amarya domin su ɗan taka tare da nishaɗantar da
mutane. Hannun Sarah cikin na _Khalil_ suka taso daga wajen zaman su tare da tsayuwa a filin. A kunna
_Khalil_ yayiwa Mc magana, shi kuma MC yace, "To jama'a, magana ake yi na ango da amarya. Ango yace a
saka masa wak'ar soyayya mai daɗi don tare zasu waƙe kansu shi da amaryarsa. Dj idan ka shirya." Ya faɗi
hakan tare da miƙawa Sarah mic kasancewar ya riga ya bawa _Khalil_ nashi. Ɗagewa Sarah gira _Khalil_
yayi tare da faɗin, "Wannan gasa ce tsakanina dake. Kuma ni zan ci" Itama ɗage masa girar tayi tare da
faɗin, "Da gaske kai zaka ci?" Gaba ɗaya a idanun mutane suka yi komai, sai hall ɗin ya kaure da tafi har da
masu fito da cike da wani irin salo mai tafe da ƙauna sukai maganar. Dai-dai nan DJ ya saki waƙar auta
MGboy ina ji dake. *_Ina ji da ke ni ba zan barki ba, ni kullum a fatana mu kai har ga ran aure*
*_Ina ji da kai nima bazan barka ba, kullum tunanina yaushe ne za muyo aure_*
*_Idan lokaci yayi ni naki ne, idan lokaci yayi ni mijin ki ne. Idan lokaci yayiiiii! Idan rabbi yaso na aureki
ƴan mata_*
*_Ba mai kai ni jin daɗi idan munyi aure, cikin zuciyata kai kaɗai ne ka tare. Taho sahibinaaaa! Idan so ya
kai so dole ne ai batun aure_*
*_Kin game ko ina dukka jiki kin mamaye, ke kika ban ƙauna wanda kuɗi basa saye. Naji ana cewa kyan
tafiya ai waiwaye nawa da na fara kanki na dosa kai tsaye. Ni kuma soyayya gadonta nayo ba wai haye, ki
zo muyi batu, amma batun zuciya ya fiiii*
*_Zan iya rantsuwa ba wanda yaffika, ba wai kyauba ko wanka azo gunka, ko mai ka haɗa ni dai ina
yinka. Ba laifi bane inna yi kishinka. Kai zan sa a zuciya can na ɓoyeka. Ba wata ƴa da zata gane ka sai de a
ran aure_*
*_Da sanki a ƙirjina na baki wajen kwana_*
*_Nayi mafarki ma har ka zama angona_*
*_To ki sani sahun farko kar aji kukana_*
*_Baza kayi kuka ba zauna daga dama na_*
*_Kin zama komi na kin haɓɓaka ƙarkona_*
*_Na soka iya sone da yadda da ƙarfina_*
*_Shine sanadi nima bazan miki ƙarya ba_*
*_Kai zaka zamo Sarki a fadata nima_*
Gaba ɗaya wajen babu wanda basu burge ba don gaba ɗaya waƙar na tafiya ne daidai da motsin jikinsu,
don har jawota zuwa jikinsa yake yi. Kuɗi kuwa kamar za suyi kuka saboda yanda aketa liƙa su. Ƙarfe sha
ɗaya aka tashi. Kuma taro ya tashi tafiya. Mota har gida ta kwashi kowa ta mayar. Su Na'ima ma daga
wajen dinner suka yi gida a mota guda. _Khalil_ ma daga shi sai matarsa. Karfe sha ɗaya da rabi suka iso
gida. Kasancewar babu kowa a farfajiyan gidan, kowa ya shige ɗaki yana huta gajiya, sai _Khalil_ ya cicciɓi
matarsa kamar baby yayi side ɗinsu da ita. A ƙofar ɗaki ya direta tare da buɗe ɗakin ya kuma cicciɓanta
bayan ya kullo ɗakin da key yayi sama. Kai tsaye ɗakin da ya kasance nashi ya direta a kan gado tare da cire
takalmin ƙafarta ya ajiye sannan ya hawo gadon ya kai hannu ya warware igiyoyin bayan rigar tare da soma
zuge zip tayi saurin kai hannu ta baya ta riƙo hannunsa. Matsowa yayi dai-dai kunnanta tare da janye
gashin da yake wajen ya kama kunnanta kaɗan ya ɗan ciza sannan ya hura. Tsikar jikinta yayi wani irin yarrr
har bata san lokacin da ta lumshe idanu ba. A kunna ya soma yi mata raɗa, "Please kar ki kasance cikin
matan dake yiwa mijinsu ƙudundune. Ni mijinki ne, ki saki jikin dani. Ko kin manta abunda ƙasar mama ta
faɗi ɗazu a wajen dinner ne." Rimtse idanu tayi saboda hucin numfshinsa dake sauka a cikin kunnanta yana
saukar mata da wani irin kasala. Cikin dabara ya saka hannu ya zuge zip ɗin duka tare da ɓalle hook ɗin bra
ɗinta. Da sauri ta kuma rimtse idanun jin lallausar hannunsa akan fatar jikinta. Bata ankara ba ya Juyo da
ita gaba ɗaya ta faɗo jikinsa, wani irin runguma yayi mata tare da saɓule hannun rigar jikinta ya zaro bra
ɗin ta ya wurgo shi ƙasa ya shiga wasa da jikinta. Gam ta rintse idanunta saboda wani matsanaicin kunya
da ya rufeta. Ɗago da fuskanta yayi tare da faɗin, "Buɗe idanunki kiga wani abu." Ƙin buɗewa tayi saboda
kunya, cakulkuli yayi mata da hannu biyu tayi wani irin zillo tare da faɗawa jikinsa ta saki kukan shagwaɓa."
Kwantar da ita yayi tare da yi mata rumfa yana kallon idanunta da yake a kulle gam. Babu abunda yake
tunowa sai ranar da ya suka taɓa kasancewa a haka a _Golden diamond_ she was screaming kamar zata
tsaga masa kunne duk da bai kai ga jikinta ba. "I love you Soo much Sarah!" Ya faɗi hakan tare da haɗe
bakinsu ya shiga bata deep kiss na kusan 5minutes sannan ya ɗagata don ya fara sauka daga kan layi.
Hannunta kare da ƙirjinta ya ɗagota tare sauke gown ɗin ƙasa gaba ɗaya sannan ya ɗagata cak ya zareta ya
ajiye a gefe. Saurin juya baya tayi shi kuma ya tattaro gown ɗin ya kai cikin wardrobe ya ajiye sannan ya
ɗauke ta cak zuwa bayi tana noƙewa. "In yi maki wankan ne ko zak....." Tun kamun ya ƙarisa tace, "Zan yi
da kaina." Murmushi yayi tare da fita daga bayin ya kullo mata ƙofa ya koma ƙasa. Ko da Sarah ta gama
wanka, towel ta ɗaura kuma gaba ɗaya da kaɗan ya wuce mazaunanta don idan ta duƙa mazaunan zasu
kasance a wajen. Kaɗan ta buɗe Ƙofar ta fito, ganin babu kowa sai ta fito da sauri domin ta shirya kamun
ya dawo ɗakin. Wata red nightgown ta gani a kan gadon. Ɗagawa tayi ta jujjuya tare da faɗin, "h'umm!
Waye zai saka wannan ɗin? Ba dai Saratu ba." Tana gama faɗin haka ta nannaɗe tare da ajiyewa dai-dai
lokacin da _Khalil_ ya turo ƙofar ya shigo hannunsa riƙe da tire. Wani irin sufa tayi tare da faɗawa kan
gadon ta cukuikuye kanta da zanin gadon. Ajiye turen yayi tare hawowa kan gadon. Riƙe zanin tayi ƙam
tana faɗin, "Don Allah ka fita in saka kaya." Bai saurareta sai da ya janye zanin gadon sannan ya haɗata da
jikinsa yana raɗa mata, "Allah idan baki natsu ba, shi kansa towel ɗin, ciresa zanyi." Tsit tayi jin abunda
yace. Tiren ɗin ya ɗauko ya ɗaura a kan gadon tare da faɗin, "Oya come let me feed you." Girgiza kai tayi
tare da faɗin, "Ni dai na ƙoshi." Ta faɗi. Janyo ta yayi jikinsa tare da yago kazar ya saka mata a baki, sau
uku kawai ta ƙarba tare da narke masa tana kukan shagwaɓa akan ta ƙoshi. Lafiyayyan madaran shanu ya
zuba a cup ya kafa mata a baki, bai zame ba sai da yaga ta shanye tsaf sannan ya zuba shima ya sha tare da
ɗaukar tire ɗin da sauran kazar ya fita dashi zuwa kitchen. ko kamun ya dawo tayi saura ta saka wata
rigarsa da ta kawo mata har guiwa sannan tayi saurin gyara gadon. Hannunsa ɗauke da hijjab da wata
doguwar rigar abaya ya shigo. Dariya ya kwashe dashi ganinta sanye da rigarsa da yayi mata yawa. Juya
masa baya tayi tana turo baki. "Mrs _Khalil_ tashi ki ɗauro alwala kizo mu godewa Ubangiji." Ba tare da
musu ba ta sauko ta nufi toilet. Bayanta ya dunga bi da kallo har ta shige bayin. Mintuna biyu ta fito ɗaure
da alwala lokacin tuni shi har ya shimfiɗa darduma. Da hannu yayi mata nuni da abaya da hijjab. A kan
rigarsa dake jikinta ta saka abayan sannan ta saka hijjab yaja su sallah. Raka'a biyu suka yi. Bayan sun
sallame ya kwararo masu addu'o'i sannan ya dafa goshinta tare da faɗin, " _Allahumma innee as'aluka min
khairiha wa khairi maa jabaltaha 'alaihi wa'a uzhubika min sharriha wa sharri maa jabaltaha 'alaihi_" yana
kaiwa nan ya jawota ya rungume k'amk'am tare da raɗa mata, "Finally, you're mine Sarah!" Ya faɗi hakane
yana mai kaiwa ko ina na jikinta kiss. Tuni ya gama kashe mata jiki gaba ɗaya domin saƙonninsa suna amsar
ko wani saƙo da lungu na jikinta har bata san lokacin da ta saki jiki gaba ɗaya ba. Cak ya ɗauke ta zuwa
gado ya shimfiɗe tare da yi mata rumfa ya cigaba da kashe mata jiki da zafafan romance. Sai da ya bari ta
kunnu iya kunnuwa don gaba ɗaya ba tare da ta ankara ba ya gama fatali da duk wani suturar jikinta
sannan ya soma karanto addu'ar saduwa. Sarah bata dawo hayyacinta ba sai da taji baƙon lamari da
gigitata har bata san lokacin da tayi wani irin yunƙuri ba tare da buɗe baki za tayi ihu yayi saurin tare ihun
da bakinsa ya shiga shafa kanta yana hura mata iska. Hawaye kawai suke gangarowa daga idanunta suna
sauka a kan gadon. Sosai _Khalil_ yana ƙoƙari tare da dauriyanta. Don tun yunƙurin farko bata kuma yi ba
sai hawayen da take yi sai kuma wnit lokacin da take faɗin, "Wayyo Allah na zaka ji min ciwo!"

*Wallahi ba ƙaramin wahala nasha ba tun jiya nake typing ɗin nan. Keyboard ɗin ne bai min typing da
sauri. Nafi sabawa da ɗayar wayata. Duk daɗewar nan kuga abunda nayi😭😭😭*

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

[02/10, 9:11 PM] Matar Sayyadee: Sosai yaji tausayinta kasancewar babu ƙarya ta jigata da yawa. Bayan
komai ta lafa. Da kansa ya cicciɓeta har bayi ya galgasa mata jiki. Ko a wajen sanyata cikin ruwan zafi tayi
dauriyan ba kaɗan ba. Babu abunda take yi sai ciccije baki da faɗin "Wassh!" Har ya kammala gasatan
sannan ya nannaɗota cikin towel ya dawo da ita kan gadon sannan ya buɗe ƙaramin fridge ɗin dake ɗakin
ya ɗauko ruwan gora tare da ɓallo paracetamol da pain killer ya miƙa mata, hannunta na rawa ta karɓa ta
watsa a baki tare da korawa da ruwa sannan ta kwanta tare da dunƙulewa waje ɗaya tana rawar tsari.
Kashe wutan ɗakin yayi tare da hawa kan gadon ya lulluɓesu da bargo sannan ya jawo ta jikinsa ya
rungume. Nan da nan baccin wahala yayi gaba da ita, shi kuma sai ya tashi zaune ya jawota a hankali ya
ɗaura kanta a saman cinyarsa. Hannu ya kai ya kunna bedside lamp mara haske wanda ya bashi daman
kallon fuskanta sosai, sai sauke ajiyar zuciya take yi. Baccin ma a shagwaɓe take yinsa. Don sai wani kwaɓe
fuska take yi tana ƙara shigewa jikinsa dama kuma Sarah akwai son jiki kamar mage. "You're my early
paradise, my one and only, my four in one, infact my everything. You're _Khalilullah's_ happiness! Without
you Sarah, I can't survive. Sarah a yau mun haɗe mun zama ɗaya, ke _Ibrahim_ ce, _Ibrahim_ kuma kece.
Saratu baki na ba zai iya misalta maki yanda nake jinki a raina ba, yanda kika bani farin ciki a yau, Allah yayi
maki sakayya da gidan Aljanna." Kamar a mafarki haka Saratu take ta jin maganganunsa. Gam ta kamo
hannunsa ta riƙe, cike da magagi irin na bacci ta soma faɗin, "Kai jinin dake yawo a jikina ne, duk wani
bugun zuciyata da tunaninka take tafiya, _Khalil_ tun lokacin Sarah ta soma tozali da kai ka sace zuciyarta,
kuma a kullum bata taɓa fasa addu'ar Allah ya mallaka mata kai ba. Rayuwar Sarah Nuhu, da taka take
tafiya. Tsayawar taka dai-dai take da tsayawar bugun zuciyar Sarah. Sarah ta mallaka maka komai nata, a
yau da kuka zama ɗaya kuma, ta ƙara damƙa maka akalar rayuwarta. Ka taimaka ka rungumi Sarah a ko
wani irin hali, don Sarah tayi wani oath akan cewar, no matter what, kuna tare for rever and ever." Wani
irin murginata yayi tare da yi mata rumfa ya shiga kissing ɗinta yana faɗin, "Nagode wife, nagode. And I
promise babu wanda ya isa ya shiga tsakanin mu. Mun riga mun zama hanta da jini." Wasu mahaukatan
French kiss ya soma bata. Ganin gaba ɗaya ya soma fita hayyacinsa don har ya soma ƙoƙarin komawa gidan
jiya ta soma turesa tana faɗin, "Ka tausaya min, wallahi akwai zafi. Ciwo yake min kuma bacci nake ji." A
kunne ya raɗa mata, "Kiyi haƙuri ki bani sau ɗaya kawai, zan biki a hankali ta yanda baza kiji zafi irin na
ɗazu ba, don Allah wifey." Shuru tayi hawaye na gangaro mata. "Inyi?" Ya faɗi a tausaye. Ɗaga masa kai tayi
tana mai danne kukan da yake taho mata. "Allah ya miki albarka!" Ya faɗi tare da yi mata kiss a goshi
sannan ya kai hannu ya kashe bedside lamp ɗin. Wannan karan tafi karon farko shan wahala, don sai ya
zame mata kamar fami. Sai dai ba ƙaramin dauriya tayi ba. Babu kwarorowa sai "Inna lillahi wa'inna ilaihir
raju'un" da yayi ta shan kira da kuma su Lami, Baba da kuma sauran ƴan uwanta. Bayan komai ya natsa ya
kuma yi mata gashi karo na biyu tare da wankan tsarki, shima yayi sannan suka kwanta yaja masu bargo
nan da nan bacci yayi awon gaba da dukansu don dare yayi sosai biyu ma ta wuce. Sun so makara sallar
asuba saboda jimawar da suka yi basu yi bacci ba. Da sauri _Khalil_ ya diro daga kan gadon jin alamar za'a
tada sallah a masallaci. Sauri-sauri ya ɗaura alwala tare da sanya doguwar rigar jallabiya sannan ya fita
zuwa masallaci. Bayan an idar da Sallah ya fito, a ƙofar masallacin suka haɗu da ya Abdul-Hakeem. Hannu
ya bawa _Khalil_ suka tafa tare da faɗin, "Ango-ango, ango ka sha ƙamshi. Ai na ɗauka yau an ɗauke maka
sallar asuba yau. Don tuntuni nake ta kallon hanya ko zan hangi fitowar ka." Ya ƙarisa maganar yana dariya.
Dariyar shima _Khalil_ yayi tare da faɗin, "Babu wani jin daɗin da zai zo min a cikin duniyar nan da zai
hanani gaida Ubangijina. Ai ta hakan ne zan nuna masa jin daɗin abunda yayi min domin ya dauwamar
dani a cikin farin ciki." Hannu ya Abdul-Hakeem ya kai ya mari ƙeyarsa kaɗan tare da faɗin, "Ƙanina har
wani girma da natsuwa naga ka ƙara daga jiya zuwa yau. Allah dai ya ƙaro zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba."
Da "Ameen" _Khalilullah_ ya amsa daga nan gaba ɗaya suka nufi side ɗin Hajiya kasancewar haka suke tun
farko, ana saukowa sallar asuba sai sunje sun gaidata sannan kowa ke komawa ɗakinsa. Sai da suka yi
knocking sannan ya Abdul-Hakeem ya murɗa handle ɗin sannan suka shiga. Zaune suka sameta a kan
darduma tana lazumi. Sai da ta kammala sannan suka haɗa baki wajen faɗin, "Hajiya barka da asubha. Kin
tashi lafiya?" Da murmushi ta amsa da, "Lafiya ƙalau Alhamdulillah! Ya kwanan iyalan naku?" Duka suka
amsa da, "Lafiya ƙalau." "To ma sha Allah! Abdul-Hakeem ya ake ciki da masu tafiya yau? Kasan Maiduguri
ba nan kusa bane. Jirgin za su bi koko yaya?" Hajiya ta faɗi tana kallon ya Abdul-Hakeem. "Eh jirgi zasu bi
Hajiya, don ya Abdullah kamun ya juya zuwa Abuja jiya, sai da ya bani kuɗi naje nayi masu booking flight.
Jirginsu zai tashi ƙarfe sha ɗaya na safe. Sai a faɗa masu su kasance cikin shiri." Hajiya tace, "To shikenan.
Allah ya saka da alkhairi ya ƙara buɗi da kuma kare ku daga sharrin maƙiya na kusa da na nesa." Da
"Ameen." Suka amsa sannan suka tashi suka fita. A parlour suka taras da Laure tana kakkaɓar kujeru, cikin
sauri ta gaida ya Abdul-Hakeem kasancewar basa ƴar wasan da suke yi ita da _Khalil_, a taƙaice ya amsa
tare da fita daga parlour ɗin. Sai ta juyo ta kalli _Khalil_ tare da faɗin, "Yanzu dai ko darajan amarya naci ai,
don Allah a ɗan sammin turaren." Ta ƙarisa maganar a marairaice. "Za'a sammiki albarkacin amarya kamar
yanda kika ce. Anjima kizo ki karɓa." Washa baki tayi gaba ɗaya haƙoran sai suka yo waje. Da sauri yaja
baya tare da faɗin, "Wallahi idan kina so mu shirya kar ki kuskura ki firgita min mata da wannan haƙoran
naki kamar yanda kika firgita ni." Da sauri tace, "Halit......" Sai kuma ta fasa ƙarisawa ta canza maganar, "Ba
zan ma ƙara buɗe bakin ba." "A'a ƙarisa abunda kika yi niyyar faɗi kawai. Da kuwa kinyiwa turarenki." Ya
faɗi yana hararenta. "To ai shiyasa ma nayi gum da bakin nawa. Ho na Saratu, bada kanka a sare!" "An ƙara
miki turare ɗaya." Faɗin _Khalil_. Wani tsalle ta buga na jin daɗi shi kuma yayi dariya tare da fita daga
ɗakin. Ko da ya koma ɗaki sai ya taras har Sarah tayi sallah ta koma ta kwanta. Ya gane hakanne ganin
hijjab ɗinta a kan sallaya. Jallabiyar jikinsa ya cire ya ninke sannan ya ɗauki hijjab da sallayar ya ninke ya
ajiye sannan ya hau kan gadon ya jawo Sarah jikinsa ya ja masu bargo suka. Hamdala yayi jin jikinta ya rage
zafin da ya ɗauka jiya. Don kwana tayi da zazzaɓi. Basu suka farka ba sai ƙarfe sha ɗaya. Ta riga shi farkawa
don motsinta yaji ya tashi tare da shafa fuska yace, "Good morning my angel!" Lumshe idanu tayi tare da
faɗin, "Good morning, happiness." Kiss yayi mata a goshi tare da faɗin, "Ya jikin naki?" Gyaɗa masa kai
kawai tayi tana ɗan cije baki saboda jikinta da yayi mata tsami. Naga kamar baza ki iya tashi ba, let me
carry you." Ba tare da ya jira abunda za tace ba yayi wuff da ita. "Ni bayi zan shiga, ni dai bayi zani ka sauke
ni dan Allah!" Ta faɗi tana harhaba ƙafafunta. Shi kuma ƙin ajiyeta yayi har sai da ya direta a cikin jacuzzi
tub sannan ya fita domin bata damar taimakon kanta. Wanka tayi sosai ta gargasa jikinta sannan ta saka
rigar wanka fara ƙal ta ƙulle igiyar sannan ta leƙo, sai da ta tabbatar baya nan sannan ta fito daga bayin ta
saka silipas dinsa ta fita daga dakin da sauri ta koma nata ɗakin don babu kayanta a cikin ɗakinsa. Sai da ta
fara ƙarewa ɗakin kallo tukun tana yaba kyawunsa sannan ta isa wajen mirror ta shafawa jikinta mai me
ƙamshi da saka laushin fata. Simple make-up ta tsantsarawa fuskanta sannan ta feshe jikinta da turare
sannan ta miƙe ta isa wardrobe ɗinta ta ɗauko wani haɗaɗɗan less wanda aka masa ɗinkin riga da skirt. Ya
amshi jikinta sosai. Gaban madubi ta dawo ta tsantara ɗaurinta kuma dama ita gwana ce wajen iya ɗaurin
ɗankwali. Turarensa ta ɗan fesa kaɗan a jikinta sannan ta ɗauko gyale ta yafa. _Khalil_ na kitchen yana
ƙoƙarin soya kwai yaji door bell, sai da ya juye kwan a plate ya kashe gas sannan ya fita ya buɗe ƙofa.
Washe baki Laure tayi tare da miƙa masa kwalaban fiya-fiya guda biyu. "Ke daɗi na dake rashin hankali,
wannan kwalaban kuma na minene?" Turo baki tayi tare da faɗin, "Yo ba kai kai min alƙawarin turare har
biyu ba." Riƙe ƙugu yayi tare da faɗin, "Sai kuma aka ce don nayi maki alƙawari sai kizo min ɗaki da sassafe
kina damuna da buga ƙofa." Kallon basket hannunta tayi tare da faɗin, "Aunty Maryamu ce fa ta aiko ni na
kawo maku abun kari shine na taho da kwalaban don ka saka min turaren. Ina amaryar taka? Ni ƙamshin
kwai ma nake ji yasin?" Ta ƙarisa maganar tana shinshine-shinshine. "To baƙar mayya, ban abunda aka aiko
ki ki wuce ki bani waje. Kuma ki takuran in hana ki turaren, yasin." Ya ƙarisa maganar kamar yanda take yin
magana, daidai suka ji ƙarar takalmin Sarah tana saukowa daga steps. Juyawa yayi da saurin jin daddaɗan
ƙamshin turarenta da ya daki hancinsa, don humran da Hajiya ta bata jiya da kuma _Imperial Majesty_ da
oud ta shafa, sai suka haɗu suka bada haɗaɗɗan ƙamshi mai sanya natsuwa a zuciyar wanda ya shaƙi
ƙamshin. " _Naaji na gani zan baki lokacina, tunda kinka nuna ƙauna dare da rana, baki nuna so, domin
arziki na, kikan tsare mutunci ko bakya gaba na. Ke nake gani, ke nake gani. Ke nake gani, to bani kula
kowa_." Yana tafiya ne yana waƙar har ya isa inda take ya kamo hannunta ya bata kiss a goshi. Laure kuwa
sake baki tayi tana kallon su. Ganin _Khalil_ ya manta da ita a wajen sai ta soma waƙa ita ma tana faɗin, "
_Ga abinci ku, ga abincinku, kuzo ku karɓa, a baani turare in wuce_." Da sauri _Khalil_ ya tare gaban Sarah
yana faɗin ku kuke ganinmu ba mu muke ganin ku ba. Anya Laure babu aljanu jikinki kuwa. Wannan irin
murya haka kamar na samudawan farko. To tuf-tuf-tuf. Kurwar matata kur. Maye ko aljani yaci kanshi. Ga
ƙatuwar murya ga uban kacakoran haƙora." Shigowa sosai Laure tayi tare da dire basket ɗin sannan tace,
"Wallahi tallahi halittar ubangiji. Kuma dai nafi matar kyau." Juyowa yayi gaba ɗaya ya kalleta daga sama
har ƙasa tare da faɗin, "Eh Lallai babu shakka." Sai kuma ya bushe da dariya tare da faɗin, "Ga shawara
idan zaki ɗauka, kije kuyi shawara ke da mai gadi ya samo ƙatuwar keji ya ajiye a ƙofar gate, bayan kin
gama aikinki na cikin gida sai ki fita waje ki shiga kejin nan, wallahi ba ƙaramin kuɗi zaki samu ba, don duk
wanda ya zo wucewa sai ya ajiye maku kuɗi." Kuka ta fashe dashi tare da faɗin, "Sai kace wata biranya zan
shiga keji. Kuma turaren ma ba'a so." Tana gama faɗin haka ta juya Sarah tayi saurin kai hannu zata riƙota
_Khalil_ ya riƙe hannun tare da faɗin, "Tsaya ki sha kallo." Sai da ta kai bakin ƙofa sannan ta juyo tare da
faɗin, "Baza ka bani haƙuri ba? Ke kuma amarya ko ɗan irin cin-cin ɗin nan ma baza ki bani ba. To wallahi
ban fita ko ina sai an bani turarena da cin-cin." Kallon juna _Khalil_ da Sarah suka yi suka fashe da dariya.
_Khalil_ yace, "Ahaf, ba na faɗa maki ba. Ai mayya ce! Idan ban bata turaren ba sai ta lashe kurwata!"
Murguɗa baki tayi tare da faɗin, "Eh naji ɗin komai zaka ce kace idan har za'a ban turaren." Kiss yayi ma
Sarah a kumatu tare da faɗin, "Ina zuwa love, bari na ɗauko mata ta wuce ta bamu waje." Gyaɗa kai kawai
Sarah tayi. Yana wucewa Laure ta matso kusa da Sarah tare da faɗin, "Wallahi ke kyakkyawa ce. Kin ganki
kuwa? Wane kajuli (Kajol) ta ƙasar hindiya. Gaskiya ya _Khalil_ ya iya zaɓe yasin. Ku wani yare ne?"
Murmushi Sarah tayi tare da faɗin, "Babana ɗan Nasarawa ne a wani ƙauye da ake kira _Wamba_" Riƙe
haɓa Laure tayi da faɗin, " _Wamba_? Ni ban ma taɓa jin sunan garin ba. To mamanki fa?" Ko kamun ta
bata amsa suka ji saukowar _Khalil_ hannunsa riƙe da kwalin turare guda biyu. Washe baki Laure tayi tare
da faɗin, Alhamdulillahi ni Laure! Nagode ya Ibrahim" ta faɗi tun kan ya miƙa mata turaren. Taɓe baki
_Khalil_ yayi tare da miƙa mata yace, "Sai a sakar min mara inyi fitsari." Amsa tayi bakin yaƙi rufo, haƙoran
sunyi cirko-cirko a waje. "To, to a wuce a bani waje." Sai da ta kai ƙofa sannan tace, "Aunty Saro, sai nazo
dan ya _Khalif_ ya fita." Da ƙarfi Khalil yace, "Kika ƙara kiran matata da wannan sunan sai na cire shegun
haƙoran nan. Kuma kar in sake inga ƙafafunki a ɗakina." Dariya Sarah tayi tare da faɗin, "Amma ya kuke da
ita?" Sai da ya kulle ƙofar ya saka key sannan ya dawo inda take ya rungume ta sannan ya ce, "ƴar uwa ce,
lokacin da Hajiya taje Maiduguri aka haɗo ta da ita domin ta riƙa taimaka mata da wasu ayyukan. Ance dai
abokiyar wasan mu ce, ban dai san asalin yanda muke da ita ba." Sarah tace, "Hajiya ƴar Maiduguri ce ko?"
Zama yayi a kan kujera ya ɗaurata a kan cinyarsa tare da faɗin, "Mahaifinta Shuwa ne, mahaifiyarta kuma
Kanuri, kuma duka tana jin yaren." Kallonsa tayi tare da faɗin, "Kai fa, kana jin yaren?" "Gwada yara min
naji ko zan iya mayar maki?" Faɗin _Khalil_. "To ai ni ban iya ba." Sarah ta faɗi. Kwanto da kanta yayi a kan
ƙirjinsa tare da faɗin, "Kar ki damu, wata rana zaki san ko inaji ko ban ji." "To baba fa, wani yare ne?" Sai da
ya nuna kansa Sannan yace, "Babana?" "Eh babanmu." Ta bashi amsa tana nuna ita dashi. "Sorry babanmu
har dake. Shi kuma Mahaifiyarsa bafulatana, mahaifinsa Kanuri." "Kai Kanuri ne kenan?" Faɗin Sarah.
"Kwarai da gaske!" Ya bata amsa tare da miƙar da ita zuwa dinning sannan ya ɗauko basket ɗin da Laure ta
kawo abinci ya ajiye a kan dinning ɗin sannan ya koma kitchen ya ɗauko kwan da ya soya. "Ni na soya
wannan da kaina. Ci kiji?" Faɗin Khalil cike da farin ciki don ya soya kwai. Sarah kuwa tun kallon farko da
tayi wa kwan taga tsakiya ya babbake. Hannu ta kai ta ɗan yago gefe inda bai ƙone ba ta saka a baki. Da
sauri ta furzo shi jin magi har kwakwalwar kanta. "Ya dai?" Faɗin Khalil bayan yayi saurin zuwa inda take.
Bata ce komai ba ta yanko ta saka masa a baki. Dakyar ya iya juriya ya haɗiye yana yamutsa fuska. "Wai wai
wai! Daɗi!" Faɗin Khalil yana yin haka👌da hannu. "To maza cinye shi!" Ta faɗi tana masa tuni da plate ɗin
da idanunta. "Kiyi haƙuri na kaiwa Madhu itama taci. Don duk abunda na saka a baki itama sai ta ci."
"Wacece kuma haka?" Tayi saurin faɗa. Shi kuma yace, "Madhubala wutar kyau, masoyiyata kenan?" Tuni
annurin fuskanta ya canza ta tsaya kawai tana kallonsa. Kumatunta yaja tare da faɗin, "Kishi, to mage na ce
wacce na ɗauko all the way from Paris. Zaki sota sosai idan kin ganta. Very beautiful." Sai a lokacin ta saki
fuska tare da faɗin, "Laa! Kaman ka san ina son mage sosai. Tana ina?" "Tana side ɗin Hajiya. Idan mun
gama karyawa zan kai ki, ki gaida Hajiya sai mu ɗauko abun mu daga nan." Ya faɗi hakane tare da soma
serving ɗinsu a plate ɗaya. Yana bata a baki tana bashi har suka kammala sannan suka kwashe kayan tare
suka kai kitchen yana wanke-wanke tana ɗauraya har suka kammala. Towel ya ɗauko ya goge mata hannu
dashi sannan suka fito parlour. "Bari na ɗauka maki babban mayafi sai muje wajen Hajiya." Ya faɗi hakan
tare da nufar sama. Mintuna kaɗan ya dawo ɗauke da gyale. Da kanshi ya soma nannaɗa mata gyalen a kai
dai-dai lokacin da suka ji door bell. A tare suka kalli ƙofar, sai da ya gama saka mata sannan ya nufi ƙofar ya
buɗe. Ido huɗu suka yi da Aina'u tana sakar masa murmushi.

*KIRA ZUWA GA MARUBUTA*

_A matsayinka na ɗan Nigeria bai kamata kayi murnar Independence ba, bai kuma kamata kabar wani yayi
ba!_
_dalilina kamarhaka_
_a satin daya_ _gabata an sace ɗalubai a jahar Zamfara, an kashe wasu a sakkoto, An harbe wasu a cikin
Jos, a kaduna kuwa an tare jirgin ƙasa an kwashe mutanen cikinsa wanda har yau ba'a san inda sukeba!_
_kai yanzu ko tafiye tafiyen da akeyi da an daina saboda irin wannan matsalolin!_
_Kuma duk haka yana Faruwa ne saboda sakacinmu na mutanan AREWA, ko har kun manta da ƴan matan
da aka sace a cikin jahar Barno state a shekarar 2014 su ɗari biyu da sabai'n da shida?!, ƴan matan ƴan
matan chibok, toh haryanzu ba'a san inda saura suke ba..._
_Idan mukace AREWA muna magana ne da ƴaƴan cikinta waɗanda suka sami ɗaukaka koya take kama
daga Ƴan social media, ƴan film, mawak'a, masu shirin barkwanci, tare da_ _*Marubutan mu*, mu taso
mu buɗe baki muke_ _magantuwa, muyi amfani da wannan damar ta social media, kuna ganin celebrity
ɗin nan na kudu daya mutu zargi suke akan kashe shi akayi ba tabbatarwa ba, amma ji yadda abun ke yawo
a ƙasa baki ɗaya!_
_mu kuma ƴaƴa mata ake kwasa ake shiga jeji dasu, banda tsadar rayuwa, da azaba da ƙuncin da muke
ciki, kidnapping, kwace, Haure, ana kashe mana ƴan uwan mu ɗaruruwa batare da munce komaiba!_
_shin da mukayi shirun gajiya_ _sukayi suka daina ko kuwa abin ta'azzara yayi?_
_a matsayinki/ka na *Marubuciya, Marubuci* ƴan AREWA ga dama tasamu, masu novel na kuɗi dama
free, masu ɗaukakar cikin mu dama sabbin tasowa, magana ake aji murya iri ɗaya gabaɗaya a social media
a yau first October dan already no more Independence, Dan girman Allah kar mu raina abin da zamuyi,
koda baƙya update na novel kiyi koda shot writing akan matsalar dake faruwa!_
_kar mutsaya sai abi yazo kan ƙanwarka ƙanina babana ko mamana, Kaduna Zamfara Barno Kano da
dukkan arewa muɗin duka abu ɗayane, dan Allah marubata mufito ƙwanmu da ƙwarƙwata mutaya ƴan
uwanmu ƴan_ _social media isar da saƙo, tunda mu baiwar rubutu_ _ubangiji ya bamu muyi amfani da ita
wajan yin gƴara._
_ubangiji yayi mana Jagora ya Allah ka sakawa duk wacce tayi ƙoƙarin tallafawa da gidan Aljannatul-
Firdausi_.

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_MATAR SAYYADEE_*

*Paid book 08128755583*


[02/10, 9:11 PM] Matar Sayyadee: Da sauri Sarah ta ƙariso wajen tana faɗin, "Lah, Ai'n kece? Shigo mana
kin tsaya a waje kamar baƙuwa. Ke ɗaya ce?" Hanya Khalil ya bata ta shigo tare da faɗin, "Bamu san da
zuwanki ba, ashe kina tafe" kai tsaye yayi maganar don har ga Allah bai so zuwanta ba don zata shiga
haƙƙinsa na rashin bashi damar kasancewa da matarsa. Da kallo ta bishi tana ji kamar rungumesa saboda
ƙaunarsa dake fuzgarta. Shi kuwa Khalil komawa yayi ya zauna tare da ɗaukar remote ya kunna tv ya ɗaura
ƙafa ɗaya akan ɗaya. "Ai'n mai zaki ci? Ki zauna mana." Wani kallo Khalil ya watsawa Ai'n ɗin tare da maida
kallonsa izuwa ga Sarah yace, "Babe, ba girkin da za kiyi, saboda ban so kiyi stressing kanki shiyasa na fita
da kaina na haɗa maki breakfast. Ohh nama manta, akwai sauran abincin da Aunty Maryam ta aiko mana
dashi gashi can a dining. She should go and serve herself kamun mu dawo daga cikin gida wajen hajiya.
Let go wife!" Ya faɗi hakan tare da kama hannun Sarah ya saka cikin nashi. Kallonta Sarah tayi tare da faɗin,
"Aina'u bari muje mu dawo. Hajiya zanje na gaisar in dawo yanzu." Yaƙe tayi tare da faɗin, "Ok sai kun
dawo." Suna fita Khalil ya saki tsaki tare da faɗin, "Killjoy?" "Wa?" Sarah ta tambaya tana kallonsa.
"Ƙanwarki mana. Bata iya zuwa gidan amare ba. Ita da ake bari sai irin bayan sati biyun nan, duba fa ki gani
ko 12:00 bai yi ba. Ni dai wallahi an shiga haƙƙina. Ɗaukar hutun wata guda nayi domin in huta tare da
matata, amma naga alama ana son hanani more amarcina." Tsungulinsa tayi a hannu har sai da ya furta,
"Auch! Mai nayi maki?" "Duk fa wanda zai zo ba kwana zai yi ba, dole zai tafi ya bar mu tare, to menene
abun damuwar bayan we will always sleep together babu mai raba mu?" Cak ya tsaya yana kallonta tare
da faɗin, "Haba, dagaske? Za ki biyani duk bashin soyayyar da aka hanani nunawa da ranar?" Dukan
kafaɗunsa tayi tare da faɗin, "Wallahi happiness kana da negative mind. Ni ba abunda nake nufi kenan ba."
"To ni kuma kinga abunda nake nufi kenan." Faɗin Khalil. Da sauri tayi gaba saboda kunyar da ya bata.
Haɗawa yayi da gudu ya isketa tare da faɗin, "Yarinya kina da aiki, wai kunyata kike ji? Taɓ, kina ruwa can
gaban breaker." Cak ta tsaya kasancewar sun iso daidai ƙofar part ɗin Hajiya. Shi ya ƙarisa tare da murɗa
handle ɗin ƙofar ya shiga bakinsa ɗauke da sallama. Gaba ɗayansu suna parlour ana hira, Hajiya, yaya
Abdul-Hakeem, yaya Muhammad Kabir, Aunty Maryam, aunty Khairat, aunty Zakiyyah matar yaya
Abdullahi, Nafeesa, Aysha, Laure, Aunty Jamila autarsu uncle Ameeru, sai ƴaƴansu da kuma kaɗan daga
cikin sauran mutanen Maiduguri da basu koma ba. Juyawa Khalil yayi tare da faɗin, "Babe, shigo mana."
Da sauri Aunty Khairat ta tsunguli aunty Maryam jin sunan da Khalil ya kira Sarah dashi suka bushe da
dariya. Ita kuwa Sarah a kunyace ta shigo ɗakin kanta na kallon ƙasa ƙafafuwanta na harɗewa. Har ƙasa ta
duƙa tare da faɗin, "Hajiya ina kwana?" Da murmushi a fuskar hajiya ta amsa tare da faɗin, "Zo taho nan
kinji ƴata." Zama tayi kusa da ƙafafun Hajiya a kan capet sannan tabi kowa ɗaya bayan ɗaya ta gaida su,
kowa ya amsa fuska cike da fara'a babu nuna wani kyara ko wulaƙanci. Khalil ɗin ma gaida waɗanda suka
girme shi yayi, wanda ya girma kuma suka gaida shi. "Yayanmu ka iya zaɓe fa wallahi." Faɗin Nafeesa tana
ƙara leƙo fuskan Sarah. "Kun san ni komai nawa mai kyau ne shiyasa matata sai da na hanga na waiga na
zaɓota zuƙeƙiya gata nan." Aunty Zakiyyah matar ya Abdullahi tace, "Gaskiya Ibrahim baka da kunya, a
gaban yayyin naka nake irin wannan magana haka." "To Aunty kuma ni mai nace? Yabon matata fa kawai
nayi." Faɗin Khalil yana dariya. "Wai, Hajiya sai kinyi haƙuri don zaki ga rawar kai!" Gaba ɗaya aka kwashe
da dariya. Saukowa ƙasa Khalil yayi tare da zama daidai inda Sarah take sannan yace, "Wife, na san baki
san kowa a nan wajen ba idan aka cire Laure da tazo ɗakinmu ɗazu. Bari na fara ta kan wannan babbar
aunty, (yayi nuni zuwa ga Aunty Zakiyyah), ita ce matar babban wanmu, sojane a Abuja yake aiki. Lokacin
da papa yake dai rai, we all are living there duk dani zaman na hutune don a abroad nayi rayuwata kaf,
Hajiya ce ta matsa na dawo saboda Allah ya rubuta sai na haɗu dake mun ƙunla alaƙa mai girma. Last year
suka aurar da second daughter ɗinsu mai sunan Hajiya ana kiranta little hajjaju, very smart girl don ni ta
biyo a kwakwalwa." "Ai ka san mu duka kwakwalan tunkiyoyi gare mu sai kai ɗan gwal" Faɗin yaya
barrister. Waro idanu Khalil yayi tare da faɗin, "Ni ba haka nake nufi ba. Mine saurareni kiji." Ya ƙarisa
maganar yana kallon Sarah, "Wannan sunansa ya Abdul-Hakeem, wannan itace matarsa Aunty Maryam
wacce ta aiko mana da breakfast ɗazu, ƴarsu ɗaya Maimoon... Wannan kuma shine ya barrister, shi kuma
kin ga matarsa nan, sunanta Aunty Khairat, ƴaƴansu biyu...." Haka ya dunga nuna mutanan parlour ɗin
yana mata bayani. Ita dai kai kawai take ɗaga masa. Yanda aka amsheta kowa na nan-nan da ita ya saka ta
mance da wata Aina'u. Shikuwa Khalil yana sane, addu'a kawai yake yi cikin zuciyarsa Allah yasa ta gaji da
jira ta wuce gida. Ɓangaren Aina'u kuwa, bayan fitarsu babu inda bata buɗe ta duba ba, sai faɗin, "Kan
bala'iiii!" Kawai take yi tana kwafa. Sai da ta gama tsaf sannan ta dawo parlour ta zauna a kan kujera tana
girgije-girgije ƙafa, "Wallahi in har sunana Aina'u ɗiyar Lami da Nuhu, wallahi tallahi ba zan taɓa bari kiyi
farin ciki ba, ba dai anyi auren ba, enjoy the first week of your marriage before the war begins!" Ta ƙarisa
maganar tana mai rausayar da kai. Tun tana ƙirga mintuna har ta dawo awa. A can cikin gida kuwa, kirar
sallar azahar ne ya fitar da mazan zuwa masallaci yayin da matan suka ɗauro alwala. Bayan kowa ya idar da
Sallah, sai suka haɗu gaba ɗaya a dinning don har an kammala lunch. Kujerun dinning ɗin irin mai sha huɗu
ne, kuma sun ɗauke gaba ɗaya don ma yaran an haɗa masu a parlour don suna da yawa. Khalil ƙafa ya tura
ya shafo ƙafar Sarah, ɗagowa tayi suka haɗa idanu ya kashe mata idanu, gaba ɗaya a idanun Hajiya komai
ya faru amma sai ta nuna kamar bata ga komai ba ta cigaba da cin abincinta. Zumbur Sarah ta miƙe tana
faɗin, "Inna lillahi!" Gaba ɗaya aka haɗa baki wajen faɗin, "Mai ya faru?" Khalil kuwa har ya zagaya ta
bayanta tare da jan kujeran da take kai baya. "Na manta ina da baƙuwa a ɗaki. Kuma tun ɗazu tana can
tana jirana." Hajiya tace, "Laure maza haɗo mata abinci a basket ki tafin mata dashi." Khalil kuwa tsaki yayi
a zuciyarsa don bai so ta tuna ba. Shima abincin da bai ƙarisa ci kenan ba yabi bayan matarsa. Kowa Sarah
ta murɗa handle ta shiga, a zuciye Aina'u ta juyo zata fara ruwan bala'i sai ga Khalil ya shigo rai ɓutu-ɓutu.
Washe baki Ai'n tayi tare da faɗin, "Kun jima, har nayi bacci na farka. Amma dai mancewa kuka yi nazo
ko?" Ko kamun Sarah tayi magana caraf Khalil yace, "Ni na ɗauka ma kin wuce ai. Ashe kina nan kina jira."
Sarah tace, "Kiyi haƙuri Aina'u wallahi mancewa nayi kina nan. Kinci abincin?" "Ban sani ba shegiya
munafuka. Wato kin shigo cikin arziki har kin soma wulaƙanci. Kiyi, lokacinki ne. Nawa na nan zuwa." A
Cikin zuciya tayi maganar, amma a zahiri sai cewa tayi, "Naci!" Sama Khalil ya hau yana faɗin, "Love, ɗauko
min energy drink a fridge ki kawo min sama." Da "To" ta amsa tare da nufar kitchen ɗin. Da wani irin kallo
mai tattare da shauƙi Ai'n tabi bayan Khalil. Sarah kuwa kitchen ta shige ta ɗauko drink ɗin ta dawo parlour
tare da faɗin, "Aina'u ina zuwa dan Allah. Bari na kai masa na dawo." Ko tari Aina'u bata yi ba. Sarah kuwa
dama bata jira cewarta ba ta nufi sama, kwance ta same shi daga shi sai boxer yana danna waya. Yana jin
shigowar ta ya ajiye wayar tare da miƙa mata hannu alamar ta taho garesa. Sai da ta ɗan yi jim sannan tayi
taku ta isa gareshi. Janyota yayi gaba ɗaya ta faɗo jikinsa ya saka hannu biyu ya rungume tare da faɗin,
"Taho inji ɗumin jikinki matata." Ya ƙarisa maganar yana sunsunar wuyarta. "Dan Allah ka sake ni, Aina'u fa
tana parlour." Hannu ya kai ya cire ɗan kwalin kanta ya cusa hannunsa cikin gashinta tare da faɗin, "Duk
wacce tazo gidan amare ai ta san hakan zai iya faruwa da ita, ni kuma saboda wata Aina'u ba zan ƙi hutawa
da matata ba." Ya ƙarisa maganar tare da murginata yayi mata rumfa yana kallon kyakkyawar fuskanta.
"Waiyy! Nauyi gareka, ɗaga ni." Ta faɗi duk da kuwa be sakar mata nauyi ba. Jin abunda tace sai ya ɗan
sakar mata kashi talatin a cikin nauyin nasa. Da sauri ta shiga bugun bayansa tana faɗin, "Nauyi, nauyi,
nauyi! Wallahi ka sakar min nauyi." "Au haba, dagaske?" Kukan shagwaɓa ta sakar masa tana tsungulin
damtsensa. Juyawa yayi ta koma samansa tare da zagaye ƙugunta da hannunsa ya matso da kansa ya haɗe
bakinsu ya shiga bata deep kiss, Sarah kuwa sai mutsu-mutsu take zata kwace kanta yayi saurin juyata ta
koma ƙasa yayi mata runfa ya shiga bata zazzafan romance, tun tana noƙewa har ta saki jikinta ba tare da
ta shirya ba ta shiga mayar da martani. Sai da komai ya kammala ta shiga kukan shagwaɓa tana faɗin zafi.
Shi kuwa ya biye mata yana ta lallashi. Tare suka yi wanka wanda a can bayin ma sai da suka ɓata lokaci,
suna fitowa daga bayi ana kwaɗa kiran sallar la'asar. Sauri-sauri ya shirya ya fita gudun kar yayi missing ɗin
sallah. Turus ya tsaya ganin Aina'u a zaune ta cika tayi faam, shi har ga Allah ya manta da ita a cikin gidan.
"Ashe kina nan" shine abunda ya faɗi kawai tare da fita daga parlour. Wani irin kukan baƙin ciki Aina'u ta
saki tare da miƙewa a zuciye tayi sama, kamun ta tura ƙofar ɗakin sai da ta tsaya ta goge hawayenta tukun
sannan ta tura ƙofar. Juyowa Sarah dake gaban mirror tayi, sai da gabanta ya faɗi ganin Aina'u. "Sarah don
nazo gidanki shine zaki min wulaƙanci ke da mijinki? Nagode kuma da izinin Allah ba zan sake zuwa gidanki
ba." Tana gama faɗin haka ta juya zata fita. Da sauri Sarah ta miƙe tare da kamo hannunta tace, "Dan
girman Allah ƙanwata kiyi haƙuri, wallahi ba wulaƙanci nayi maki ba. Kiyi haƙuri ki yafe min na san ban
kyauta miki ba. Dan Allah Aina'u" ta faɗi tana mai haɗe hannunta biyu. "Amma Sarah....." Sarah tayi saurin
cewa, "Dan Allah kiyi haƙuri ki bar maimaita magana. Zo ki zauna ina zuwa." Ta riƙo hannunta tare da
zaunar da ita a kan gado ita kuma ta isa gaban mirror ta busar da gashin kanta sharp-sharp sannan ta saka
riga da skirt English wear sannan ta saka dogon hijjab ta tada sallah. Bayan ta idar da sallar ta cire hijjab
tare da nannaɗe dardumar ta ajiye sannan ta zauna kusa da Aina'u tare da faɗin, "Kiyi haƙuri Aina'u, tashi
mu sauka ƙasa musha hira." Ta faɗi hakan tare da kama hannun Aina'u wacce ta gama ƙarewa gadon kallo
ganinsa a hargitse kuma dama sai ƙarewa gashin Sarah kallo take yi ganinsa jiƙe kamun ta soma busar da
kanta. Suna isowa parlour Khalil na shigowa. A gaban Aina'u ya kama kan Sarah tare da sakar mata kiss a
goshi tare da faɗin, "Allah ya yi maki albarka!" Sannan ya nufi sama. Baki sake Aina'u ta bishi da kallo har
ya ƙule kamun ta zauna tana sakin ajiyar zuciya. Aina'u ba ita ta bar gidan nan ba sai bayan magrib. Washa
gari ma ta kuma dawowa, Khalil kamar ya fasa ihu don itace ta soma danna doorbell ko taran safiya bata yi
ba kuma sai bayan magrib ta wuce duk ta hana su sakewa. A rana ta uku ce Khalil ya kai bango, don yana
buɗe ƙofa yaga ita ce ko amsa gaisuwarta bai yi ba ya juya ya koma sama kuma yaƙi faɗawa Sarah tazo,
kuma be bar Sarah ta fito daga bedroom ba ma balle ta sauko parlour taga Aina'un. Ranar har lokacin
tafiyarta yayi bata ga ko ƙeyar Sarah ba, shima Khalil ɗin sau biyu ta gansa, lokacin da ya buɗe mata ƙofa da
kuma lokacin da ya sauko zuwa kitchen ya dafa indomie da kwai ya koma saman, kuma ko kallon inda take
bai yi ba. Sallah ma azahar da la'asar a ɗaki suka yi tare. Tsabar haushin da Aina'u taji, bata san lokacin da
tayi wani irin kwallo da magen Khalil ba sai da ta karye a ƙafa sannan ta fizgi jakarta ta fita daga gidan. Tun
daga ranar bata kuma dawowa gidan ba. Khalil kuwa kamar zuciyarsa za tayi bindiga ganin Madhu ɗinsa a
karye sai kuka take yi. Haka ya kwashe ta zuwa asibitin dabbobi aka gyara mata ƙafar. Satin Sarah biyu a
gidan Khalilullah, sun yi sabo da ƴan gidan sosai, kuma kullum da rana idan Khalil ya tafi sallar azahar a
side ɗin hajiya take zama ita da Aunty Maryam har lokacin la'asar sannan kowacce ke komawa nata
ɓangaren domin ɗaura girki. Sarah ta saba da nacin Khalil yanzu, kullum suna manne da juna babu daren
banza. Ba ƙaramin soyayya suke zubawa ba a gidan. Ɓangaren kuwa, ranar da ta bar gidan Sarah keke
napep ɗinsu yayi hatsari ta samu gocewar ƙashi a cinya, kuma babu wanda ya sanar da Saran. Wata ɗaya
yazo ya wuce, biyu, har uku, Sarah tayi wani irin kyau da ƙiba da haske. Duk wanda ya ganta ya san tana
cikin kwanciyar hankali. Yau da take cikin wata uku da kwana goma a gidan miji, Khalil yayi surprising ɗinta
bayan gama nacinta akan tana son zuwa gida taga baba dasu Lami. Kamar an sakata a aljanna saboda farin
cikin Khalil yace ta shirya zasu je gaida su baba. Wata lafiyayyiyar shadda ta saka kalar ruwan toka wanda
yaji stone work iri ɗaya da na jikin Khalil. Sai da ɗauko farin gyale da farin takalmin vinci ta saka. Kaɗan ta
fesa turare saboda Khalil bai so idan zasu fita ta riƙa fesa turare sosai. "Wow! Wife kin ganki kuwa?"
Hularsa ƙube wanda Hajiya ta ɗinka masa da kanta ta saka masa tare da jawosa ta koma ta gabansa ta
kwanto a jikinsa shi kuma ya ɗaura kansa a kan wuyanta, ita kuma tayi masu hoto. Ba ƙaramin kyau hoton
yayi ba. "Wai nace ba, wani yare ne ku? Don nasan ku dai ba Hausawa bane." Yan maganar ne a cikin
kunnanta. Sai da ta lumshe idanu sannan tace, "Na faɗa maka mu ƴan Nasarawa ne can _Wamba_. Baba
yace sunan unguwarmu layin abakwa. Duk cikin mu babu wanda ya taɓa zuwa. Sunan yaren baba
_Nindire_. Kuma yana ji sosai. Don akwai abokansa ƴan can, muna ji suna yi idan sun haɗu." "To ke kina
ji?" Girgiza kai tayi tare da faɗin, "Ko zo in kashe ka." Dariya yayi shafa cikinta tare da faɗin, "Ɗana dake
nan ko ƴata, za suji Kanuri in Sha Allah, zan riƙa yi musu, kuma Hajiya ma nasan za tayi masu." Kallon
cikinta tayi sannan ta kallesa tare da faɗin, "To ai ni bani da ciki." "Ni da nayi cikin ai na sani." Ya bata amsa
yana dariya. Kallon cikinta dake a shafe tayi, bata san lokacin da murmushi ya suɓuce mata ba tana fatan
Allah ya amshi bakinsa. "Muje ko Queen" ya faɗi yana mai nuna mata hanya. Fita tayi ya biyota a baya, ji
kawai tayi an ɗauke ta cak, bai sauketa ba sai da ya kawota har ƙofar ɗaki. Ɗakin Hajiya taje domin shaida
mata zata gida, ba ƙaramin sha tara na arziki ta haɗa mata ba danginsu sabulai, turaruka, shadda da
atamfofi har da manya-manyan zannuwar gado guda biyu. Khalil ta parking ta fito da gudu tayi cikin gida,
babu kowa a gidan daga Lami sai Aina'u da ƴaƴansu Na'ima. Rungume Lami tayi tana mai farin cikin
ganinta, da idanu tabi Sarah dashi, can kuma ta murza idanunta tare da faɗin, "Sarah! Kece haka?" Ta faɗi
hakane tare da kaiwa ƙasa ta shiga faɗin, "Yesu Nagode, Nagode Yesu da kaba yarinyana kwanciyar hankali.
Almasihu na koma gareka, ka saka albarka a rayuwar ƴata. In to my heart, in to my heart, come into my
heart, Lord Jesus, come in to stay, come into my heart Lord Jesus, ameen!" Ta ƙarisa addu'ar tare da
rungume Saran. Baba Nuhu kasa haƙuri yayi Sarah ta shigo, sai gashi ya fito yana farin, da gudu ta ƙarisa
tare da faɗin, "Babaaa! Kai ne haka? Kaga yanda ka ƙara lafiya da kyau." Dariya baba yayi tare da faɗin,
"Albarkacin haihuwarki ne Sarah, ban san mi zan cewa mijinki ba sai dai kawai ince Allah ya bashi Aljanna.
Kullum cikin hidima yake mana. Ba'a haɗa cikakken sati bai zo gidannan gaishe ni ba." Zaro idanu Sarah
tayi tare da kwaɓe fuska tace, "Amma shine bai taɓa zuwa dani ba sai yau, kuma baya faɗa min yazo."
Murmushi baba yayi tare da faɗin, "Nine nan nace masa kar ya yarda ki soma fita sai kinyi wata uku da
aure, shiyasa ko kwanciyar Aina'u a asibiti nace kar a faɗa maki." Zaro idanu Sarah tayi tare da faɗin,
"Yanzu Aina'u ta kwanta asibiti baba shine ba'a faɗa min ba? Ni wallahi ba'a kyauta min ba." Dai-dai nan
Khalil ya shigo bakinsa ɗauke da sallama. Bayan baba ya amsa yace, "Ke dama tare kuke da Ibrahim ɗin
shine baki faɗa ba tuntuni saboda sakarci." Turo baki kawai Sarah tayi tana jin haushin rashin faɗa mata
kwanciyar asibitin da Aina'u tayi. Har ƙasa Khalil ya duƙa ya gaida baba sannan ya gaida Lami, baba ne
kaɗai ya amsa banda Lami don haushinsa take ji tunda Aina'u ta faɗa mata abunda yayi mata ranar ƙarshe
da ta ziyarci Sarah. Ɗakin baba ya shige sukayi ta hira, yayin da Sarah ta shiga ɗakin Lami, tayi tayi Aina'u ta
kulata amma ko kallonta bata yi ba. Da Lami kawai suka yi hira. Duba hamsin ta bawa Lami da kuma
tsarabar da Hajiya ta bata, Lami kamar ta goyata tsabar murna. Baba ma dubu hamsin ɗin ta bashi da
shadda ɗaya da zanin gado, albarka ya dunga saka mata. Anan idar da la'asar suka taho gida. Tun daga
wannan rana Sarah ta soma wani irin rashin lafiya, gwajin farko da Khalil yayi mata ya nuna ciki, ɗaukarta
yayi zuwa asibitin yayi mata scaning, sai ga cikin wata biyu har da sati biyu. Sosai take laulayi mai zafi
wanda yaci uban na farko. Sau uku tana kwanciya a asibiti, abinci kuwa ko ƙamshinsa bata so, daga ruwan
bohol sai fanta mai sanyi. Komai Khalil ke yi mata, wanka, wanki da gyaran ɗaki. Idan kuma yana asibiti,
Laure ko Aunty Maryam ke yi mata. Wata ranar labara, tana kwance a akan kujera tana maida numfashi
taji alamun ana murɗa handle ɗin ƙofa, tana ɗago kai tayi arba da ƙatuwar akwati Aina'u naja. Duk da bata
jin ƙarfin jikinta bata san lokacin da ta tashi zaune ba tana bin akwatin da kallo............

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_MATAR SAYYADEE_*

*Paid book 08128755583*


[04/10, 11:37 AM] ‫ماي ديا‬: "Aina'u, lafiya?" Faɗin Sarah cike da mamaki. Aina'u wani haɗe rai tayi tare da
faɗin, "Ban gane Lafiya ba. Ko bakya son gani nane in koma inda na fito?" Sauke ajiyar zuciya Sarah tayi
tana ƙara kallon akwatin ta gefen idanu tare da faɗin, "Ya zaki ce haka Ai'n, kawai nayi mamakin ganinki
ne." Aje akwatin tayi a nan tsakar ɗaki tare da zama akan one sitter tace, "Wash, akwatin nan ba dai nauyi
ba, daga gate zuwa nan kamar zan mutu haka naji. Nazo taimaki ne ganin baki da lafiya, ina nan har ki
haihu." Wani miyau Sarah ta haɗiye jin abunda Aina'un tace, ita damuwarta ɗaya, rashin kamun kan
Aina'un na yawan surutun faɗi ba'a tambayeka ba. Bata so kyakkyawar alakar dake tsakaninta da Hajiya da
kuma Aunty Maryam ya samu matsala sanadin Aina'u. "Ya ubangiji Allah maji roƙon bayi, kasa zuwan
yarinyar nan gidan nan alkhairi ne." Sarah ta faɗi cikin zuciya. Taɓe baki Aina'u tayi ganin Sarah ta faɗa
dogon tunani, cikin zuciyarta ta furta, "Kuma wallahi zama cikin gidan nan dole." Jiki babu kwari Sarah ta
miƙe tare da faɗin, ɗauko akwatin naki na nuna maki ɗakin da zaki sauka." Miƙewa tayi tana wani taɓe
fuska tare da jan akwatin, ta cikin second parlour suka bi zuwa bedrooms ɗin dake ƙasa, "Zaɓa ɗakin da
kike so a cikin ukun nan sai ki zuba kayanki a cikin wardrobe." A yatsine Aina'u tace, babu ɗaki a sama ne
sai nan ƙasa? Nafi son saman." Sai da Sarah ta kalleta sannan tace, "Eh babu, don can ɗin daga ɗakina sai
nashi." A gadarance Aina'u tace, "To kuma bazan iya zama a naki ɗakin ba ko? Tunda ai naga a ɗaki ɗaya
kuke kwana ke da Khalil ɗin." "Aina'u bafa zai yuwu ki zauna a sama ba, don zaki shiga haƙƙin mijina da ni
karan kaina. Kiyi zamanki anan zaki fi walawa." Ba tare da Aina'u tace komai ba ta buɗe ɗaya daga cikin
ɗakunan dake a jere ta leƙa, girgiza kai tayi irin bai matan nan ba ta buɗe ɗayan, shima dai bata shiga sai
da ta duba na ƙarshen sannan ta fito ta dawo na tsakiyar ta soma jera kayanta cikin, duk da halin da Sarah
ke ciki sai da ta taimaka mata wajen jera mata kayan. Bayan sun gama suka dawo parlour. Ko zaman
mintuna biyar bata yi ba ta tashi tare da faɗin, "Tunda ba'a man tayin abinci ba, bari nayi wa kaina." Tana
gama faɗin haka ta shige cikin kitchen tana waƙa. Da idanu kawai Sarah ta bita sannan ta girgiza kai.
Indomie ta dafa da kifin gwangwani sannan ta ɗauko avocado Juice ɗin da Aunty Maryam ta haɗawa Sarah
ko zata ta fito ta zauna a ƙasa. Wani irin kakarin amai ta soma yi tare da toshe bakinta tayi hanyar toilet ɗin
dake parlour ɗin da sauri ta soma sheƙa aman a ƙasa. Aina'u kuwa wani taɓe baki tayi tare da faɗin, "Gama
shan baƙar wahalar tukun, amma baza ki taɓa ganin kwanki ba a duniya in dai ina raye! Shegiya mayya mai
ɗuwawun saurin ɗaukar ciki. To kin ɗauki ciki ma ba tare da saduwaba, inaga kuma an sadun.. Shegiya
mahaifar zan yi sanadin lalacewarsa inga ƙarshen saurin ɗaukar cikin naki" duk a zuciya tayi maganar yayin
da tayi kwafa a fili ta cigaba da cin indomie ɗin ta." Sarah kuwa tun tana saka ran ganin Aina'un tazo kawo
mata ɗauki har ta fidda rai. Aina'u kuwa bayan gama cin indomie ɗin ko plate ɗin bata ɗauke ba ta hau kan
kujera ta ɗauki remote ta kunna kallo. Sarah kuwa ƙaramar azaba tasha ba don babu komai a cikinta sai
tsabar wuya da take sha. Da kyar bayan ta wanke jikinta ta dawo parlour ɗin ta dunga birgima a ƙasa tana
riƙe ciki. Duk abunnan da take yi ko sau ɗaya Aina'u bata ce mata sannu ba. A hankali ciwon cikin dake
damunta ya kafa, jirin da take gani shima kamar anyi ruwa an ɗauke, lokacin bacci har ya ɗauke Aina'u a
kan kujeran da take kai. Kallon Aina'un tayi tana mamakin taurin zuciya irin nata ganin duk malelekuwar da
take yi ko sannu bai haɗata da ita ba. Infact tama ɗan ɗago taga halin da take ciki bata yi ba, amma a
hakan take cewa tazo zama da ita domin taimakonta har ta haihu. Tashi Sarah tayi ta haura sama ta shiga
jacuzzii tayi wanka da ruwa mai zafi sannan ta fito ta tada sallar la'asar kasancewar ta ɗauro alwala kamun
ta fito. Riga kawai ta zura da dogon hijjab ta tada sallah, bayan ta idar ta isa gaban madubi ta tantsara
kwalliya kasancewar Khalil ya kusa dawowa don sau da dama a gida yake sallar magrib. Wando ta sanya
pallazo kalar emerald green da shirt mai button kalar grey sai ta kama jekar shirt ɗin biyu ta ɗaure ta gaba.
Gashin kanta kuma tayi parking ɗinsa in a low ponytail jelar gashin ya zuba har gadon bayanta. Turensa
_Imperial Majesty kaɗai ta fesa tare da saukowa ƙasa, tun daga kan steirs Aina'u ke ƙare mata kallo ganin
wari irin kyau da tayi, tayi haske sosai hips ɗinta kuma sun ƙara cika. Tana saukowa kai tsaye kitchen ta
nufa tare da buɗe fridge ta ɗauko can fanta wanda yayi mugun sanyi ta dawo ta zauna kan kujera tare da
ɗauka ƙafa ɗaya a kan ɗaya ta buɗe fanta ɗin ta shiga sipping a hankali tana lumshe idanun. Aina'u kuwa
babu abunda take yi sai aika mata da harara ta gefen idanu. "Zuwa anjima kamun Happiness ya dawo za
muje can cikin gida ki gaido Hajiya da sauran mutanen gida." Faɗin Sarah ba tare da ta kalli inda Aina'un
take ba." "Ok" shine abunda Aina'u tace tana mai faɗin, "Nine ajalin farin cikinki, kiji daɗinki iya jin daɗi
kamun turn ɗina ya zagayo. An kusa fara yaƙin wallahi, yaƙi ne da yafi na biafra!" Sai da tasha rabin fantan
nan sannan ta mayar dashi cikin fridge tare da komawa sama ta ɗauko ƙatoton hijjab har ƙasa ta saka ta
dawo parlour tare da faɗin, "Ki taso muje cikin gidan." Miƙewa tayi tabi bayan Sarah da tayi gaba tana yi
mata daƙuwa a baya. Sallama suka yi, babu kowa a parlour sai TV dake ƙara, "Zauna anan ina zuwa." Sarah
ta nuna mata kujera tare da wucewa tabi corridor ɗin da zai sadata da ɗakin Hajiya. Ai'n kuwa sai bin
parlourn ɗakin take yi tana jinjina kai tare da mamakin dukiyar da aka kashe wajen tsara gidan gaba ɗaya,
don ko ina ka kalla babu ƙarya. Tare Hajiya da Sarah suka fito daga ɗakin kamar ƙawaye, don ita Hajiya
ƴaƴa ta ɗauki matan ƴaƴanta ba surukai ba. "Sannu da zuwa Aina'u, ai kin kyauta da kika zo taya ƴar uwarki
jinya, Saratu na shan wuyar laulayi, don ma dai yarinya ce mai dauriya." Faɗin hajiya tana zama a kan
kujera. Har ƙasa Ai'n ta zamo tare da faɗin, "Ina wuni Hajiya, mun same ku lafiya?" Cike da jin daɗi Hajiya
ta amsa da "Lafiya ƙalau, ya wajensu mahaifiyarku?" Aina'u ta amsa da, "lafiya ƙalau" sosai Sarah taji daɗin
yanda Aina'u ta gaida Hajiya. Sun ɗan jima a nan ɗakin Hajiya kamun suka tafi ɗakin Aunty Maryam, Kallo
ɗaya Aunty Maryam tayi wa Aina'u taji sam bata kwanta mata a rai ba, sai dai ta amsheta faram-faram.
Basu jima a nan ba suka komai side ɗin Sarah ganin har shida tayi. Ko mintuna biyar basu yi da dawowa ba
Khalil ya dawo, yana danna doorbell Sarah ta saki wani murmushi don ta san shine ta tashi ta nufi ƙofa ta
buɗe tana yi masa wani irin kallon love mai sumar da wanda ake yiwa. Hannun biyu ya saka ya kama
ƙugunta tare da jawota kusa dashi yana kallon cikin idanunta tare da faɗin, "Mine, kin San fa baki da lafiya
amma shine kike neman tsokalata da irin wannan kwalliyar da dressing ɗin ko?" Aina'u dake zaune kan
kujera sai leƙo kai take yi tare da dogon wuya tana jin takaici na neman kasheta. Wani lunshe idanu Sarah
tayi tare da kwantar da kanta a kan ƙirjinsa tace cike da shagwaɓa, "Tun ɗazu ni da babynka muke son jin
ɗumin jikinka, gaskiya an kusa fara tafiya dani asibitin nan." Rungume yayi sosai tare da faɗin, "Lallai kuwa
duk lokacin da na ajiye ki a office babu abunda zan iya aikatawa, don wallahi bazan iya duba ko petient
ɗaya ba. Muje Wife ki kula dani kamun a kira sallah." "Uhm!" Aina'u tayi gyaran murya don ta lura har
Sarah ta mance da zamanta a parlourn balle kuma Khalil da bai san tana wajen ba. A tare Khalil da Sarah
suka kalli inda Aina'un take, lokaci guda fara'ar fuskansa ya ɗauke don shi tun asali bai ƙaunar Aina'u tun
da ta dunga maimaita masa ya rabu da Sarah su gidansu ba'a aure yaji ya tsane ta. Kuma haka nan duk
lokacin da zai yi arba da ita sai gabansa ya faɗi. Bai taɓa jin ya tsani Na'ima ko Hassana, Marfu'a da Nuratu
ba, su da ya sha ganinsu a hotels daban-daban da maza kala-kala, amma Aina'un da bai taɓa kamata da
kowa ba, sai yake jin muguwar tsanarta. "Ina wuni?" Faɗin Aina'u tana wani kwarkwasa. "Lafiya" kawai
yace tare da ɗaukar matarsa cak suka yi sama. Da idanu Ai'n ta bisu hawaye na zubo mata, duk suka haɗa
idanu da Khalil, babu abunda take hangowa sai wutar ƙiyayyarta. Yanzu hakan ma abunda ta gani kenan,
yana ganinta mood ɗinsa ya canza. "Wife naga Aina'u har wannan Lokacin, bata jima da zuwa bane?" Faɗin
Khalil bayan ya ajiyeta a kan gado. "Ta jima da zuwa, nan zata kwana!" Shuru Khalil yayi bai son ya fito ƙiri-
ƙiri ya nuna mata bai son zaman Aina'u da su a gidan don ko yaya Sarah zata ji zafi tunda ƴar uwarta ce ciki
ɗaya. "Kayi shuru Happiness!" Faɗin Sarah. Murmushi yaƙe yayi tare da faɗin, "She's welcome! Ai akwai
ɗakuna da yawa a gidan, idan ma nan bai yi mata ba, ga side ɗin Hajiya." Murmushin jin daɗi Sarah tayi
tare da faɗin, "Thank you love, nan ɗin ma ya ishe ta, har na saka kayanta a bedroom ɗin dake ƙasa."
Miƙewa yayi tare da faɗin, "Let me take a shower, yanzun nan zaki fara jin kiran sallar magrib." Ya faɗi
hakane tare da soma cire kayan jikinsa ya rage daga shi sai boxer sannan ya shiga bayi. In a few minutes ya
fito yana tsane jikinsa, ya samu har Sarah ta fito masa da kayan da zai saka. "Allah ya yi maki albarka Wife,
jiki dai yana ta ƙara improving, ma sha Allah! Kin yi amai yau?" Gyaɗa masa kai tayi tare da faɗin, "Sau
ɗaya kawai. Amma babu zazzaɓi sai ciwon mara, amma yanzu ban jin komai." "Ina sha Allah zaki zo ki daina
gaba ɗaya." Ita ta taimaka masa wajen shiryawa. Yana gama saka kaya yayi mata kiss a goshi tare da fita
daga ɗakin don an soma kiraye-kirayen sallah. Da ya sauko bai ga Aina'u a parlour ba, tsaki yayi tare da
faɗin, "Da ƙafafuwan da kika zo zaki gudu. Na san maganin ki." Ya faɗi tare da ficewa daga ɗakin. Bai dawo
ba sai da aka idar da isha'i. Yana shigowa ya sami Aina'u da Sarah a parlour suna hira, bai ce komai ba ya
haura sama, ko gaba shigewa bai yi ba Sarah ta miƙe tabi bayansa. "Shegiya fitinanniya mayyar miji, za kici
ubanki ne." Faɗin Sarah ƙasa-ƙasa. Tun daga nan bata ƙara jin motsi Sarah ba sai washe gari ƙarfe sha
ɗayan safe, shima Khalil ta rako wande ke sanye da ash ɗin suit na kamfanin _Tom Ford_, gashin kansa yayi
luwai-luwai yasha gyara. Sai ƙamshin _Imperial Majesty_ yake yi. Dama kuma Aina'u ta jima tana zaune
tana duban hanya ta inda zasu fito. "Ina kwana? Har zaka fita kenan? Ka tsaya kayi breakfast mana na girka
maka." Ba tare da ya kalleta ba yace matata ta riga ta bani abinci na kuma ƙoshi, Wife bye-bye ki kular min
da kanki." Ya ƙarisa maganar yana mata kiss a goshi. Hannu ta ɗaga masa tana faɗin, "Allah ya tsare, kar
dai ka bar min kanka da yunwa, ka tabbatar kaci abinci." "Ina sha Allah" ya faɗi tare da fita. Aina'u kuwa
kamar zata fashe don baƙin ciki. "Sarah mai nayi wa mijinki ne? Naga kamar bai son zamana a cikin gidan
nan." Kamo hanunta Sarah tayi tare da faɗin, "Kar kice haka Ai'n, Khalil nada kirki sosai, don dai baku saba
bane kawai. Amma da kun saba zaki ce na faɗa miki." "To ni naga sai wani shashsha min ƙashi yake yi. Idan
baku son zamana ai sai in tattara in wuce gida." Faɗin Aina'u. "kin cika ƙorafi wallahi, menene abun ɗaga
jijiyoyin wuya haka? Sai dai idan kin gaji ne sai in tashi in ɗauko maki kuɗin mota a ɗaki." Faɗin Sarah. "To
babu inda zanje ina nan a nan sai naga abunda ya turewa buzu naɗi." Aina'u ta faɗin cikin zuciya, amma a
zahiri sai tayi gum. "Tashi muje side ɗin Hajiya." Faɗin Sarah tana miƙewa. Aina'un ma miƙewa tayi tabi
bayan Saran. "Tooo, wannan mai suffar karuwai ɗin kuma daga ina, gashi dai tana ɗan kama da Aunty
Saratu." Faɗin Laure cikin zuciya don jiya basu haɗu ba. Suna haɗa idanu, Aina'u ta sakar mata wani
hararar da ya kaɗa ƴaƴan hanjinta tayi saurin kau da kanta. "Su Aina'u ne, sannunku ku ƙariso mana." Faɗin
Hajiya tana nunawa Aina'un kujeran kusa da ita. Kamar mutuniyar kirki ta duƙa kamar jiya ta gaida Hajiya
da kuma Aunty Maryam ɗin da tayi mata kallo ɗaya ta kau da kai. Laure kuma saurin juyawa tayi ta bar
parlourn don kar ta gaida Aina'un don za su iya zuwa sa'anni ko Laure ta bata shekara guda. Anan suka yi
yininsu, Sarah bazata taɓa iya tuna when last taga Aina'u na sallah ba sai yau da suka kai har la'asar a side
ɗin Hajiya, amma kana ƙarewa sallar kallo zaka fahimci akwai naƙasu a cikinta, don dungure-dungure kawai
take yi. Satin Aina'u guda, amma kullum bayan sun gama hira a side ɗin Hajiya sun dawo bata ƙara saka
Sarah a idanu sai kuma gobe ƙarfe sha ɗaya ko sha biyu idan za tayiwa Khalil rakiya don tunda yayi aure bai
cika fitar sassafen nan ba sai an kira shi emergency kasancewar akwai doctors a asibitin. Yau Aina'u ta
shirya tsiyar da za tayi masu wanda zai hana su bacci, sai da ta bari dare yayi sosai sannan cire ribbon ɗin
kanta ta hargitsa gashin kanta sannan ta kalli kanta sosai a madubi, daga ita sai wata transparent doguwar
rigar bacci ko bra babu sai wani ɗan iskan pant mai igiya, murmushi tayi sannan ta isa wajen ƙofa ta fita ta
nufi sama. Sai da ta isa ɗakin da ta tabbatar da nan ne suke ciki sannan ta riƙe handle ɗin ta soma jijjiga
ƙofar da ƙarfi tana ihu tare da knocking. A wannan lokaci kuma Khalil na duniyar nishaɗi shi da matarsa
suna raya sunna...........
*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_MATAR SAYYADEE_*

*Paid book 08128755583*


[05/10, 11:02 PM] ‫ماي ديا‬: Wani irin yunƙurowa Sarah tayi zata fizge jikinta tana faɗin, "Happiness ana buga
ƙofa." Da hannunsa ya maida ita tare da yin kamar bai ji abunda take cewa ba ya cigaba da birkita
tunaninta da salonsa, tuni ta manta da wani bugun ƙofa da ake yi. Aina'u kuwa jin babu alamun za'a buɗe
Ƙofar kuma ta tabbatar ana ji, sai wani baƙin ciki ya tokare mata wuya ta cigaba bugun ƙofar da dukkan
ƙarfinta. Khalil kuwa bai sararawa Sarah ba sai da ya samu nutsuwa tukun, lokacin har Aina'u ta gaji ta
zauna a bakin ƙofar tare da haɗe kai da guiwa. Khalil kuwa sunkutar matarsa yayi tare da shiga bayi suka yi
wanka sannan suka dawo suka kwanta ya ƙara masu gudun ac tare ja masu barko ya rungume abarsa suka
yi bacci. Aina'u taci kuka kamar ranta zai fita, ba ita ta bar ƙofar ɗakin nan ba sai da taji kiran sallar farko
sannan ta koma ɗakinta ta faɗa kan gado tare da rushewa da kuka. Da asubah Khalil ya tashi ya shiga bayi
ya ɗaura alwala sannan ya fito ya tada Sarah sannan ya wuce masallaci. Kasancewar ranar asabar ce babu
aiki, tun da ya haura sama suka koma bacci shi da matarsa, basu suka sauko ƙasa ba sai sha biyu. Aina'u
kuwa ta leƙo yafi sau ba adadin domin ganin ko sun sauko ƙasan amma wayam sai ta gaji har bacci ya
ɗauke ta kasancewar bata samu bacci ba. Kitchen ya shiga ya ɗauko mata can fanta ɗinta mai sanyi tare
cupcake ya bata kasancewar ta ɗan fara iya cin cake ɗin. Bayan ta gama cin cake da fanta ɗin sai tayi
matashi da cinyarsa tare da cire hular kanta shi kuma ya soma warware all back ɗin da Aunty Maryam tayi
mata guda goma saboda ya fara tsufa, "Mine, idan mace kika haifa ko, sunanki zan mayar, idan kuma
namiji ne...." Tun kamun ya kai ƙarshe tayi saurin faɗin, "Sunanka zaka mayar." Murmushi yayi tare da
faɗin, "Mai yasa kika ce haka?" Juyo da kanta tayi tana facing ɗinsa tare da faɗin, "Saboda soyayyar da
nake maka ne." Hancinta yaja tare da faɗin, "Nima haka love." Dai-dai nan Aina'u ta leƙo, hango Sarah
kwance a kan cinyar Khalil yana yi mata tsifa suna hira cike da nishaɗi, sai taji kamar ta zazzagawa kanta
petur ta cinnawa kanta ashana ta babbake. Komawa tayi cikin ɗakinta tana saƙe-saƙen abunda zata ɓullo
dashi nan gaba. Tun daga wannan rana Aina'u bata ƙara gigin zuwa buga masu ƙofa ba, sai ta tsiri zama a
side ɗin Hajiya da zaran ta tashi daga bacci, bata kuma dawowa side ɗin Sarah sai isha'i. Cikin ƙanƙanin
lokaci Aina'u tayi wani irin mugun shiga jikin Hajiya. Sosai Hajiya ta sakar mata ganin yanda take yi mata
biyayya don har wanki yi mata take yi duk da kuwa akwai mai wanki a gidan. Tun Sarah na mamakin
shaƙuwar Hajiya da Aina'un har ta daina. Babu yanda za ayi Hajiya tayi magana ɗaya biyu bata sako sunan
Aina'u ba. Laure baiwar Allah kuwa, tun da Aina'u ta dawo part ɗin hajiyan ta saka ta gaba da harara da
baƙaƙen maganganu. A gaban Hajiya kuwa sai ta riƙa janta a jiki, ko aiki Hajiya ta saka lauren, sai tayi saurin
tashi tayi tana mai faɗin, "Laure huta, ai wuni kike kina aiki." Laure dai sakin baki kawai take yi tana
kallonta. "Ummin Moon, wallahi yarinyar nan ƙanwar matar Khalil da take shishshigewa Hajiya, sam bata
yi min ba, kama take min da criminal. Akwai alamun rashin gaskiya a ɗabi'un ta. Baki lura da wani abu ba?
Tsoro na take ji, duk lokacin na shiga side ɗin Hajiya da sauri take fita bata kuma dawowa har sai na bar
ɗakin. Don Allah ki saka mata idanu kina kallon moves ɗinta kar taje ta cutar da Hajiya." Ajiyar zuciya Aunty
Maryam ta sauke tare da faɗin, "Wallahi ka riga ni a fili ni kuma na riga ka a zuciya. Laure ta kawo min
ƙorafi ba sai ɗaya ba tasha zaginta tana faɗa mata baƙaƙen maganganu, tabi ta kanannaɗe Hajiya ta shiga
zuciyata sosai ta yanda baza ta yarda da duk abubuwan da zata aikata idan dai ba hujja ta gani mai ƙarfi
ba." Girgiza kai yayi tare da yin kwafa. Bayan kwana uku, gaba ɗaya su Aunty Maryam suna zaune har da
Sarah a parlourn hajiya, babu wanda ya lura da Aina'u lokacin da ta zare jikinta ta shiga ɗakin Hajiya. Bayan
kwana biyu Hajiya ta tara su tana cigiyar gwala-gwalanta na kusan kimanin 175milions, kowa hankalinsa ya
tashi har da Aina'u data zaro idanu tare da dafe ƙirji. Anan dai kowa yayi ta jimami yana tunanin wa zai
sace, Aunty Maryam ta kalli Hajiya tare da faɗin, "Hajiya ko dai kin canza masu wajen ɓoyone kika mance?"
"Maryamu ban taɓa canza masu wajen ɓoyo ba, duk wanda da ɗauki wannan abu yana sane dashi." Faɗin
Hajiya. Karaf Aina'u tace, "Kuma Hajiya kin binciki Laure da kyau? Don naga kaf gudan nan ita kaɗai ke
shiga ɗakinki kai tsaye." Da sauri Laure, Aunty Maryam har da Sarah suka kalli Aina'un jin furucinta, "Hajiya
shekaru bakwai muna tare, idan ina da wannan hali na ɗauke-ɗauke da kin daɗe da sani tun tuni. Wallahi
tun da uwata ta haife ni ban taɓa ɗaukar abun wani ba" faɗin Laure tana mai fashewa da kuka. "A ko wani
irin lokaci ɗan adam ka iya canzawa Laure." Faɗin Aina'u tana hararen Lauren. "Ke Aina'u!" Faɗin Sarah a
tsawace da sauri Hajiya ta ɗagawa Sarah hannu tare da faɗin, "Bana son in ƙara jin komai daga bakin kowa,
ku tashi ku tafi ɗakunan ku. Sarƙa kuma zasu fito domin duk wanda ya ɗauka ba dai ya sayar ba, don duk
inda yake sai an kama shi ko kama ta." Gaba ɗaya kowa ya tashi guiwa sage ya bar ɗakin. Suna shiga ɗaki
Sarah ta ɗaga hannu ta wanke fuskan Aina'u da mari tare da faɗin, "Wallahi baki isa ki kashe min aure ba,
kina hauka ne? Ko baki san Laure ƴar uwarsu bace da har zaki jefeta da wannan mummunar ƙazafin? To
bari kiji, ba zan iya da iskancinki ba, ki shiga ɗaki ki tattaro duk wani abu naki kizo ki wuce gida, ina zaune
cikin rufin asirina kizo ki tada min hankali, to ba zai yiwu ba. Dama ba wani uban abun kike tsinana min ba,
maza tattaro kayanki ga kuɗin mota ki bar min gidana." Hannu akan fuska Aina'u tace, "Ni kika mara Saratu
har kina faɗin in bar maki gidanki? To zan tafi, amma sai kinyi nadama mafi muni a rayuwarki! Baki san
true colour ɗina ba, amma zan fito maki dashi. Ba dai miji kike taƙama dashi ba, mu zuba mu gani, gaki ga
mijin nan." Tana gama faɗin haka ta shige cikin ɗayan parlour ɗin da zai sadata da ɗakinta. Jakarta ta
kinkimo ta fito bayan ta canza kaya ta shafa aboniki a idanunta, nan da nan idanunwan suka kaɗa su kai
jazur kamar taci kuka ta ƙoshi. Bata taras da Sarah a parlourn ba, sai kawai ta saka kai ta fita daga ɗakin.
Sai da ta ajiye akwatinta sannan ta buɗe ta ɗauki wani abu cikin wani ƙatoton box tare da nufa side ɗin
Hajiya, Laure ta taras a parlour sai da ta dungure mata kai sannan ta wuce bedroom ɗin Hajiya tare yin
knocking haɗe da sallama. Daga ciki Hajiya ta bada izinin shiga, tura ƙofar tayi tare da zama a ƙasa tana
kallon tiles ɗin dake shimfiɗe, Hajiya dake tsakiyar gado tana duba wasu kaya ta kalleta tare da faɗin,
"Aina'u lafiya?" Kuka Aina'u ta fashe dashi tare da faɗin, "Hajiya kiyi haƙuri, amma yanda kika ɗauke kika
riƙe ni tamkar ƴarki ya saka ba zan iya bari a haɗa baki dani a cuceki ba, ga sarƙan ki, Saratu ce ta sace tare
da haɗin bakin ƴar aikinki Laure.........."

_Dan Allah kuyi haƙuri bana jin daɗi ne shiyasa kuka jini shuru. Yanzu ma cewa nayi bari nayi naku ko
kaɗan ne yafi babu_

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_MATAR SAYYADEE_*

*Paid book 08128755583*


[11/10, 10:51 AM] Matar Sayyadee: "Yanzu haka Hajiya ta koreni daga gidan nan saboda na faɗa mata
gaskiya abunda take yi bata kyautawa. Yanzu hakan sarƙan nan bata nan na ɗauko shi na kawo maki ba.
Nasan za kiyi mamaki mai yasa na tona mata asiri tana matsayin ƴar uwata, to nayi hakan ne saboda na
tseratar da ita ganin tayi aure gidan mutunci, bana so aurenta ya mutu sanadin abubuwan da take
aikatawa. Shi kansa Khalil ɗin ba jin daɗin zama da ita yake yi ba, a wannan ɗan zaman da nayi na fuskanci
haka, kullum cikin ƙorafi take yi masa akan dole sai ya saya mata gida a wani waje ita bata san zama waje
ɗaya da uwar miji da matar ƙani ko wa, tafi son zama ita kaɗai ta wala. Hajiya baki ga irin ɓarnar kuɗin da
Sarah take yi ba da dukiyar ɗanki, duk abunda tace kamar ta shanye shi, jiki na rawa yake yi mata. Hajiya
sai fa kun tashi tsaye sosai akan Khalil!" Hajiya baki sake take bin Aina'u da kallo tana mamakin ƙaramar
yarinya irin wannan da hassada da kuma iya tsaro zantukan ƙanzon kurege, don tun daga furucinta na
farko ta fuskanci inda ta dosa, babu abunda ke damunta illa tsantsan hassada da mugun hali. "Ina so
tambayarki." Hajiya ta faɗi still tana kallon Aina'un. Gyara zama Aina'u tayi har da matsar hawaye tare da
faɗin, "Ina jinki Hajiya." "Ke da Saratu uwa ɗaya uba ɗaya kuke?" Jinjina kai Aina'u tayi tare da faɗin,
"Uwarmu ɗaya ubanmu ɗaya da ita Hajiya, halin ne kawai ba ɗaya ba." Hajiya tsuke fuska tayi tare da
faɗin, "Tabbas kuwa hali ba ɗaya ba. Amma Allah yayi wadaran naka ya lalace! Yanzu saboda lalacewa da
rashin hankali da tunani, ƴar uwarki ciki ɗaya kike yiwa baƙin ciki da hassada? Duk wani mai hankali idan
yaji wannan magana da kika yi ya san cewa ke munafuka ce kuma baki ƙaunar ƴar uwarki. Ina matsayin
uwar mijinta, shine zaki zo kina faɗamin maganganun ɓatanci akan ƴar uwarki saboda naji haushinta! To ki
sani, na san wacece Saratu, tun lokacin da aka kawota cikin gidan nan nake lura tare da karantarta, yarinya
ce mai natsuwa da hankali. Laure kuma shekaru bakwai kenan muna tare da ita, bata taɓa ɗaukar min ko
mayafi ba balle kuma sarƙa. Bata ma san darajarsa, kuma yanda nasan tarbiyyarta da halinta baza ta taɓa
amincewa a haɗa baki da ita ba domin a cutar dani. Kuma ni tun ɗazu na fahimci ke kika ɗau sarƙoƙin nan
saboda yanda kika riƙa tada jijiyoyin wuya, na rabu dake ne domin inga iya gudun ruwanki don na riga na
san baza su taɓa saiduwar maki ba duk inda za kije don sai kin bata risiti (receipt). Kalle ni da kyau,
mahaifiyarki ma na haifeta, baki isa kiyi min makirci da wayau ba, kuma auren Khalil da uwata Saratu,
mutuwace zata raba shi in Sha Allah. Ba Saratu da take ƴar uwarki ba, Ni kai na mahaifiyar Khalil ban
amince ki ƙara tako ƙafarki cikin gidan nan ba. Kuma kin san dai ina da ƴaƴa hukumomi ko? Tashi ki ɓace
min da gani tun kamun na wanke fuskanki da mari!" Aina'u da baƙin ciki tarkon da ta ɗana bai kama ba ta
miƙe tana yiwa Hajiya wani irin kallo sannan ta juya fuuu ta fita tare da rufo ƙofar da ƙarfi. Laure na zaune
ta zubawa talabijin idanu taji saukar mahaukacin rankwashi a tsakiyar ka sai da ta kwanta flat a ƙasa tsabar
gigicewa. Dawowa tayi daidai kanta tare da faɗin, "Sai na zama ajalinki, shegiya mummuna!" Tana baro
part ɗin ta tsaya tana mamaki domin bata taɓa kawowa a ranta wannan makircin da ta haɗa ba zai yi aiki
ba. "Hajiya kin jawowa kanki bala'i da masifa da tashin hankali! Kin yi kuskure tura hannunki a ramin maciji
kuma wallahi sai ya ɗanɗana maki zafin dafinsa...." Tana gama faɗin haka ta ja akwatinta ta wuce ta bar
gidan. Bayan fitar Aina'u a ɗakin Hajiya, Hajiya ta zabga tagumi tare da faɗin, "Duniya ina zaki damu ne?
Ɗan uwanka ciki ɗaya amma shine ke yi maka hassada da baƙin ciki, kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!
Allah kasa mu cika da imani, Saratu ce dai zama daram dam a gidan nan in Sha Allah!" Wani ajiyar zuciya
Sarah ta saki lokacin da ta tabbatar Aina'u ta bar gidan. Kitchen ta shiga domin haɗawa Khalil abinci don ya
kusa dawowa. Bayan ta kammala girkin ta haura sama ta cancaɗa wanka ta saka wata doguwar rigar
shadda pink colour wanda yasha aiki da baƙin zare, ɗaurin ɗan kwali tayi mai kyau sannan ta fesa turare ta
ƙara kallon fuskanta a madubi ta saki murmushi tare da fita ta sauko ƙasa ta zauna a kan kujera ta ɗaura
ƙafa ɗaya akan ɗaya tana kallon tanƙameman plasma tv ɗinta dake haska film ɗin _Mohabbatain_ a tashar
Bollywood. Da sauri ta miƙe jin ƙarar door bell, buɗe Ƙofar tayi tana kallonsa. Shima kallon nata yake yi
daga sama har ƙasa yana faɗin "Ma sha Allah!" Cikin zuciyarsa. Hannu ta kai ta karɓi jacket ɗin hannunsa
da ya ratayo tare da kai bakinta saitin kumatunsa ta sakar masa kiss tare hura masa fuska tace, "Kar fa a
cinye ni." Hannu ya kai zai cafkota tayi saurin ja baya tana dariya, "Ki tsaya ki gani idan ba'a cinyekin ba."
Gwalo tayi masa tare da faɗin, "Ka kama ni idan zaka iy....." Ko kamun ta rufe baki har ya iso inda take ya
cafki hannunta biyu tare da haɗata da ƙirjinsa yana mai faɗin, "Ni da zan iya haɗiye kin ma da na huta da
kewarki, kullum na fita aiki sai kin hanani sukuni, domin da zarar na bar gida, kece kike min gizo a ko ina."
Hannun ta saka ta rungumosa tare da faɗin, "To ni dai matsalata kar dai garin yi maka gizo kaje kaga wata
macen ka ɗauka nice kawai kace mata, Ina son ki! Tabbas zuciyata zata buga daga nan." Janyeta yayi daga
jikinsa tare da kama hannunta suka nufi sama yana mai faɗin, "Wannan kalmar mai tsada ga macen biyu
kawai nake furtawa, Hajiya da kuma ke, bayan ku, babu macen nan gaskiya." Ƙanƙame hannunsa tayi tare
da faɗin, "Ina son ka, ina sonka sosai." Bakinsa ya kai dai-dai kunnanta tare da faɗin, "Muje ciki a nuna
min!" Tsungulinsa tayi a damtsensa tare da yin dariya. Bayan kwana biyu, Khalil ya fahimci Aina'u bata
gidan, hakan ba ƙaramin daɗi yayi masa ba, amma ko a fuska bai nunawa Sarah ba, kuma bai taɓa yi mata
maganar ya akai baya ganin Aina'un ba, ita ma kuma bata yi masa maganar ba. "Aunty Rose Merry, ina son
don Allah ki kai ni wajen _Hell Ofulafula_ da kike bani labarinsa, amma kar ki bari ko Lami ta sani, ya zama
sirri tsakanin mu kamar yanda muka saba." Aina'u ta faɗi bayan ta kamo hannun Aunty Rose Merry ɗin
bibbiyu. Aunty Rose Merry da kallon mamaki ta bita tare da faɗin, "Lili mai za kije kiyi a wajen _Hell
Ofulafula_? Kin san wanene Hell kuwa? Ko daga jin sunansa kawai ya isa ya firgita ki, ganinsa kuwa, kamar
bala'i ne a wajenki." Aunty Rose Merry ta girgiza kai tare da cigaba da faɗin, "Baza ki iya da Hell ba,
dokokinsa nada tsauri, bazan baki wannan shawarar ba, domin zai saka ki aikata wani mummunar abu mai
girma wanda Yesu Almasihu ba zai yafe maki ba, gwara dai kije wajen _Iya fulowa_, itama ta iya aiki sosai.
Wai ma menene za kiyi? Wa kike so ayi wa wani abun!" Faɗin Aunty Rose Merry. Sake hannunta Aina'u tayi
tare da ɓata rai ta juya baya tana faɗin, "To shikenan! Amma ni duk abunda kika saka ni, ina yi maki kai
tsaye, har babana na cutar saboda ke, amma ni baza ki iya mun ɗan ƙaramin alfarmar nan ba, ashe
soyayyar da kike min na ƙarya ne, saboda ke na koma addinin Christian, na kwana arba'in da biyar a cikin
ɗakin duhu daga Ni sai pastor William yana min wankan zunubi tare da amfani dani, ya aske min gashin
kaina, ya saka na kwanta kamar dabba ina shan nonon kare duk saboda ke, amma shine baza ki iya min
wannan ƙaramin abun ba. Shikenan!" Ta ƙarisa maganar tana mai fashewa da kuka. Jawota Aunty Rose
Merry tayi tare da faɗin, "Kiyi haƙuri Lili, ba dai _Hell Ofulafu_ kike son zuwa ba?" Gyaɗa kai Aina'u tayi
tana share hawayen fuskanta, "To ki kwantar da hankalinki, zan kai ki wajensa, sai dai tafiya ne mai nisa,
don a Abia yake can wani ƙauye mai nisan gaske, kuma shi bai jin yaren Hausa, bai jin English, sai Igbo,
yoruba da ifem." Wani murmushi Aina'u tayi tare da faɗin, "Wannan ba matsala bane Aunty, ba sai kin raka
ni ba, kiyi kwatanci kawai." Shuru Aunty Rose Merry tayi mai tsayi kamun ta saki ajiyar zuciya ta soma
zayyano mata kwatanci tsaf har da yanda zata samu tafintan da zai riƙa faɗa mata abunda Hell yace da
kuma ita abunda zata ce masa. Bayan kwana biyu Aina'u ta shirya kuɗi tsaf tare da ɗaukar hanyar Abia ba
tare da sanin kowa ba idan aka cire aunty Rose Merry, awanni goma sha ɗaya da rabi suka yi a mota kamun
suka isa kuma cikin dare. Aina'u ta zauna, ta mike ta rasa inda zata saka kanta saboda gajiyar zaman mota.
Taji waƙa a wayarta har na Allah ya isa Kasancewar ta tafi da power bank har taji ya fita a cikin ranta. Hotel
ta kama ta kwana, washa gari da sassafe ta nemi wanda Aunty Rose Merry ta Bata number ɗinsa, sai da
suka yi ciniki ta bashi 50k kuma ita za tayi masa kuɗin motar zuwa can sannan suka ɗauki shatar mota
zuwa *_Asaokpuaja_*. Tafiyar awa Shidda ce ta kai su can, nan ma ɗin mai motar jiransu yayi a bakin wani
hanya sabida mota baza ta iya shiga ba, nan ma suka soma cin uban tafiya, sai da suka yi tafiyar awa ɗaya
da rabi sannan suka isa wani ƙatoton baƙin gunki wanda aka yi masa penti da jar kala, da mugun gudu
Aina'u ta koma bayan Ugo ta ɓoye saboda yanda gunkin ya tsoratata da girmansa, "Una no hear wetin I say
before we come here? I tell u say make u no fear if you see anything, because _Hell Ofulafo_ dey look you
through here." Yayi mata nuni da ramin hancin gunkin. Ai sai Aina'u ta ƙara kiɗimewa! Wani sautin mara
daɗi ciki wani harcen yare ya soma magana a kausashe, take Ugo ya kai ƙasa tare da yin sujada sau uku
sannan ya miƙe ya harɗe hannayensa kamar mai neman gafar ya shiga magana cikin yare na kusan sakan
sittin sannan ya yuyo ya kalli Aina'u tare da soma yi mata magana da gurɓataccen turanci, "Hell yace ace
maki idan baki shirya ba, ki koma gida, idan kuma kika ƙara tsorata anan wajen sai ya maida fuskanki tana
kallon ƙeyarki, idan kuma kin shirya kiyi sujada a gaban gunkin nan sau uku." A take Aina'u taji duk wani
tsoron da take ji ya fece musamman da ta tuno korar karen da Sarah tayi mata daga gidanta. Zubewa tayi
tare da yiwa gunkin sujada sau uku, ana ukun ba tare da ta ɗago ba taji wani irin guguwa mai ƙarfi ya taho
ya lulluɓesu, bata kuma buɗe idanunta ba sai a gaban wani garjejen tsohon inyamure jikinsa gaba ɗaya
guraye ne, ya kasance irin zabiyan nan ne, domin idanunsa ma basa tsayuwa waje ɗaya. Gaba ɗaya jikinsa
yayi ƙuda-ƙuda. Kallo ɗaya yayi wa Aina'u ta soma jin wani irin zawo. Wani mummunar dariya ya ɓarke da
ita tare da soma surkulle cikin yaruka daban-daban. Wani ƙatoton tulu ne ya bayyana a gabansa, kallon
Aina'u yayi sannan ya kalli tukun sai ga Aina'u cikin tulun, gaba ɗaya komai ya faru ne cikin daƙiƙu biyu.
Jan zare ya ɗauko tare da jan mayafi ya kulle tulun tare da ɗauresa. Da sauri Ugo ya miƙe tare da yiwa
_Hell Ofulafu_ sujada sannan ya soma tafiya da baya da baya har ya fuce. Sai da Aina'u ta kwana bakwai
cikin tulun nan sannan tulun ya face sai gata a watse a ƙasa daga ita sai ɗaurin ƙirji da baƙin zani da jan ɗan
kwalin da bai rufe tsakiyar kanta ba. Sai da ta kwashi mintuna talatin tana kwance ko motsi bata yi sannan
_Hell Ofulafu_ ya miƙa tare da ɗaga hannu sama sai ga ƙaramin tulu a hannunsa, hannunsa mai tsini ya
caka a jikin tulun, take ya soma tsiyayar da jini mai kauri da wari shi kuma ya shiga zagaye Aina'u da tulun
sau bakwai. A firgice ta farka tana mai buɗe baki tana shan jinin nan dake tsiyayowa daga cikin tulun.
Bayan ya gama wannan ya jawo wata tulun mai ɗauke da wani irin ruwa mai ya ajiye a inda take tare da
saka hannu ya fizge zanin jikinta da ƙarfi. Wani abu ya ɗauko mai kama da kofi sannan ya ɗaga hannunsa
sama sai ga wata murtukekiyar bulala, idan ya tsiyaya mata ruwan sai ya shauɗa mata bulalan sau biyar a
ko ina na jikinta. Sai ruwan nan ya ƙare tas a jikinta, gaba ɗaya jikin nata yayi wani irin ruɗu-ruɗu. Aina'u
tayi suma ya kai goma saboda azaba. Ugo na gefe yana kallon komai, kuma dama ya san sai _Hell Ofulafu_
yayi mata hakan, ta hakane yake cire sauran imanin dake jikin duk wanda ya kawo kansa wajensa. Shi da
kansa ya barbaɗa mata wani magani a jiki tare da kallon Ugo yace masa ya kaita masaukinta idan ta gama
warwarewa sai su dawo ta faɗi buƙatunta. Ugo mai mayar da ita ainahin cikin garin Abia ba saboda nisa,
wani bukka ya kaita suna kwana tare, kuma bai barta haka ba kullum sai ya kwanta da ita. Tana ji kuma
tana gani amma bata da ƙarfin da zata iya dakatar dashi. Sai da ta kwana goma sha biyu kamun ta samu
lafiya. Babu abunda ke huruwa cikin zuciyarta sai wutar ƙiyayyar Sarah da kuma ƙudurin ɗaukar fansa, don
duk abunda ya faru da ita a garin Abia kacokan ta ɗaurawa Sarah laifi. Shikuwa Ugo sai sunne-sunne yake
yi ya ɗauka Aina'u za tayi bala'i akan kwanciya da ya riƙa yi da ita duk da kuwa ba budurwa ya sameta ba,
amma sai ya ga ko kallonsa bata yi ba idan banda ma takura masa da tayi akan su koma wajen _Hell
Ofulafu_. Suna shiga ta taras dashi yayi zaman yoga idanunsa a rufe, zama suka yi suna jiran ya gama
abunda yake yi, sai da ya kwashi awa guda shi ba a ƙasa ba kuma ba'a sama ba. A tsawace yayi magana da
wani yare yana kallon Aina'u da idanunta ke a ƙasa. A kunnanta Ugo ya raɗa mata, "He say make u look his
eyes." Ɗagowa tayi suka haɗa idanu dashi, take taji wani zafi mai tafe da raɗaɗi na shiga idanunta. Cikin
yare _Hell Ugo_ yace cikin yare, "Naga muradinki a cikin idanunki, surukar yayarki, ƴar aikin gidan, da
kuma ita kanta yayar taki, kina so a shiga tsakanin su sannan kuma kina son koma gidan, kuma mahaifiyar
mijin yayarki da kika mutu akansa kike so ta buƙaci dawowarki gidan da kanta." A kunne Ugo ya fassara
mata. Cikin sauri ta shiga jinjina kanta. "Ajiye rabin miliyan ki tafi." _Hell Ofulafu_ ya faɗi yayin da Ugo ya
faɗa mata abunda yace, take ta ajiye masa kuɗin kasancewar tazo dasu. Da hannu ya nuna masu su fita.
Bayan sun fita can bukkar suka koma, a ranar ma sai da Ugo ya kuma amfani da ita, washa gari ɗan taxi
yazo suka koma can cikin garin Abia, kasancewar ta gaji sosai, bai bata bi motar dare ba, a daren ta yanki
tiket ɗin jirgin da zai tashi ƙarfe goma. Yau ya kasance ranar asabar Khalil baya zuwa aiki, zaune suke akan
dinning suna cin lunch wanda Khalil ne ya dafa masu wata taliya mai uban romo wai ita Paraguay fried
superghetti. "Ni dai tunda nake a rayuwata ban taɓa ganin fried superghetti da ruwa a jikinta ba." Faɗin
Sarah bayan ta kalli plate ɗin dake gabanta. "Daɗina dake baki da fahimta wani lokacin. Ance maki sunansa
Paraguay fried superghetti!" Jinjina kai Sarah tayi tare da faɗin, "Eh tabbas nagane!" Yanda tayi maganar da
shaƙiyanci ya saka Khalil ya zaburo ita kuma ta miƙe da sauri suka shiga zagaye dining ɗin. Daga ƙarshe dai
ya kamata tare da cicciɓanta suka yi sama yana faɗin, "Kin ce taliyar babu daɗi amma har da su kashe
kwano." "Nifa bance babu daɗi ba, kawai romon ne yayi yawa." Faɗin Sarah dai-dai lokacin da ya sauke ta
tsakiyar gado tare da faɗin, "A taimakawa likita yaji ɗumin matarsa, kwana biyu ana ta yi min rowa."
Miƙewa tayi tare da faɗin, "Nima ina son jin ɗumin nawa mijin, bari nayi fitsari na dawo." Shafa cikinta da
ya ɗan turo tare da faɗin, "A siyar min da fitsarin" Da sauri ta sauko daga kan gadon tare da faɗin, "Ka san
dai fitsarin mai ciki bai riƙuwa ko?" Ta faɗi hakane tare da saurin shiga bayi, yanda fitsarin ya matseta ya
saka tana shiga ta ɗuka a ƙasa ta soma fitsarin. Wani irin bugawa zuciyarta yayi tare da zaro idanu tana
kallon jajayan mitsi-mitsin ƙananan tsutsotsin dake fitowa daga cikin gabanta, miƙewa tayi tare da kwala
wani uban ƙara ganin tsutsotsin kamar tuttuɗosu ake yi.............

_Alhamdulillah! Na samu lafiya. Nagode sosai da addu'o'ini, my besty (Queen Zarah) thank you Soo much
for the concern. Allah ya barmu tare." 🥰😍😍

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_MATAR SAYYADEE_*

*Paid book 08128755583*


[11/10, 10:51 AM] Matar Sayyadee: Khalil har sai da yayi wani muguwar faɗuwa saboda yanda ya duro
daga kan gadon tsabar rikicewa don duk a tunaninsa faɗuwa Sarah tayi a toilet ɗin. Burum ya faɗa bayin
yana ware idanunsa, ganinta yayi ita bata duƙa gaba ɗaya ba kuma ita bata miƙe ba, ƙafafunta sai rawa
suke yi, "Laf......." Bai ƙarisa cewa lafiyan ba ya waro idanu yana faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!
Sarah menene wannan haka? Daga ina suke fitowa?" Ya faɗi yana mai ɗage skirt ɗinta sama sosai. Da sauri
ya mayar ya sauke gabansa na bugawa saboda yanda yaga tsutsar na fitowa da gudu kamar fitar jini, wasu
ma a dunƙule suke fitowan. "Na shiga uku na, Wayyo Allah shikenan mutuwata ce tazo ta haka!" Faɗin
Sarah tana mai ɗaura hannu a kai. Janyota jikinsa yayi tare da faɗin, "Haba mine, sai kace ba musulma ba!
Menene na ihun da faɗin irin wannan maganar? Idan kika mutu ni kuma inyi yaya? Bafa wani abu bane na
tashin hankali, da yawan mata suna samun irin wannan matsalar. Ki kwantar da hankalinki Allah zai warkar
dake cikin ƙanƙanin lokaci zaki ce na faɗa maki. Kuma ma kin manta mijinki likita ne?" Ya faɗi hakan yana
sakar mata murmushin tare da ɗaukar ƙatuwar butarsu ya taro ruwan zafi sannan ya dawo inda take tana
kuka ya duƙar da ita tare da saka hannunsa ba tare da ko ɗigon kyama ba ya dunga wanko tsutsotsin nan
suna zuba a ƙasa. Sarah kuwa ganin yanda jajayan mitsi-mitsin tsutsotsin ke zubowa yayin da Khalil ke
wanko su dai ta daɗa rikicewa tana kuka sosai tare da damƙe kafaɗunsa. Sai da yaga tsutsotsin sun daina
fitowa sannan yayi mata wanka tare da ɗaukota ya dawo da ita kan gadon don har wani mummunar
zazzaɓi ya saukar mata. Ya juya zai sauka daga kan gadon domin wanke bayin don tsutsotsin na nan a ƙasa
da uban yawa, caraf ta riƙe hannunsa tare da faɗin, "Doctor meke damuna? Zan warke kuwa? Meke kawo
tsutsotsi a gaban mace?" Dariya da wani irin mugun tausayinta ne ya rufe shi jin sunan data kirasa dashi da
kuma irin tambayoyin data jero masa, zama yayi bakin gadon tare da janyota jikinsa gaba ɗaya ya rungume
tare da faɗin, "Ki kwantar da hankalinki Sarah, nace maki wannan ba wani abu bane, ko wata biyu baya da
suka wuce naga irin wannan same problem ɗinnan ga wata tsohuwa. Hakan na iya faruwa when Scratching
the anus or vagina, or wiping them after going to the toilet. This can cause the eggs to stick to your
fingertips or under your fingernails. If you don't wash your hands, the eggs can be transferred to your
mouth or on to food or objects, such as toys and kitchen utensils. Amma akwai maganinsa kuma zaki
warke in Sha Allah." Sarah dai jinsa kawai take yi amma bata cikin duniyar da yake ciki, ta jima da
tsundumawa kogin tunani da tashin hankali. Addu'a ya shiga tofa mata ganin yanda take zabura har bacci
ya ɗauketa sannan ya shimfiɗar da ita ya koma cikin bayin, sai da ya saka handglove ya ɗibi tsutsotsin ya
saka a wani container sannan ya wanke bayin tass yayi wanka. Yana ƙoƙarin saka riga ya soma jin ƙarar
door bell babu ƙaƙƙautawa, da sauri ya ƙarisa saka t-shirt ɗin ya fito daga ɗakin ba tare da ya lura da
zaburar da Sarah tayi ba. Da uku-uku yake tsallake steps ɗin har ya isa ƙofar ɗaki ya buɗe Ƙofar, da Aunty
Maryam yaci karo hankalinta a tashe tana kuka, "Lafiya Aunty Maryam, meke faruwa ne?" Da hannu Aunty
Maryam tayi masa nuni da side ɗin Hajiya tana faɗin, "Khalil, Laure! Laure ce ke ta aman jini guda-guda,
kuma maganarta ya ɗauke." Wani waro idanu yayi tare da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Ya faɗi
hakane tare da nufar side Hajiya da saurinsa, yana zuwa ya kuma taras da gigitacen tashin hankali, "Hajiya
tayi wani irin mugun kumbura kamar fulawar da aka kwaɓa da fulawa, wuyarta yayi wani abu kamar mai
maƙoƙo ya kuma zazzago, haka ma idanunta, naman ƙasan ya zazzago, babu abunda take yi sai jujjuya kai
tana hawaye don ita kaɗai ta san azabar da take ciki. "Maryam ina wayarki, kira mijinki yanzun nan yazo,
kira shi nace maki" Khalil ya ƙarisa maganar a tsawace. Aunty Maryam da gudu ta fita zuwa ɓangarenta
don a can ta bar wayan jikin caji. Khalil sai ya rasa inda zai saka kansa, ga Laure a gefensa na aman jini tana
ƙoƙarin yi masa magana amma babu murya, ga kuma Hajiya na malelekuwa a jikinsa kasancewar ya
rungumeta sai kiran sunansa take yi tana faɗin ya taimaka ya cire mata ciwon dake jikinta. A can ɗaki kuwa
bayan fitar Khalil Sarah ta fara kwararo uban aman jajayan mitsi-mitsin tsutsotsin nan ta baki ta hanci, ga
wani uban tusosi da take saki kamar an buɗe masai tsabar wari, gaba ɗaya ta ɗume ɗakin da wari ga kuma
tsutsotsi ko ta ina, gadon gaba ɗaya ya zama abun kyama. Sarah ta suma fiye da sau biyar tana farfaɗowa.
Cikin abinda bai wuce mintuna sha biyar ba sai ga Ya Abdul-Hakeem a kan bike don gani yayi idan yace zai
yi driving lokaci zai ɓata da yawa, ko kamun ya iso Laure ta fita daga hayyacinta ko motsi bata yi, Hajiya
kuma cikin hukuncin ubangiji kumburin jikin da kansa ya saɓe amma kuma sai ta dawo kamar ƴar yarinya
sannan zazzagowar da idanunta yayi yana nan da wannan abun da ya fito mata a wuya kamar maƙoƙo. Cak
Khalil ya ɗauki Hajiya kamar yarinya ya sakata a bayan mota, ya Abdul-Hakeem kuma ya cicciɓo Laure
wacce bata da maraba da gawa.. Khalil wajen Aunty Maryam ya nufa tare da faɗin, "Maman Moon dan
Allah ki duba min Sarah a ɗaki itama bata da lafiya sosai." Jinjina kai tayi tare da faɗin, "Babu matsala
Khalil, Allah ya basu lafiya dukansu." Da "Ameen" ya amsa tare da saurin shiga cikin motar ya Abdul-
Hakeem yaja motar suka bar gidan. Suna fita Aunty Maryam ta nufi ɗakin Sarah domin dubata, tunda
Sarah tazo gidan bata taɓa shigar mata ko ɗayan parlourn ƙasa ba bare kuma bedroom, yanzu haka ma sai
da tayi tsaam kamun ta haura sama, tun daga last step take jin wani irin unbearable wari mai tada zuciya,
nan da nan wani irin miyau ya soma taruwa a bakinta dama kuma ita sam bata shiri da wari, bama ita ba,
gani take gaba ɗaya zuri'arsu basa ƙaunar wari, haka ma zuri'ar mijinta (Kun san dai mutanan mai duguri
wajen ƙamshi 🤪) musamman ma Khalil mai wanka da turare. Haka dai Aunty Maryam ta dunga ɗauke
numfashi, don tana ƙara kusanta kanta da ɗakin Sarah, mahaukacin wari na ƙaruwa. Hannu ta saka ta
murɗa handle ɗin ƙofar ta shiga ɗakin, da mugun sauri ta dawo baya ta dafe ƙirji tare da faɗin, "Inna lillahi
wa'inna ilaihir raju'un! Allahumma arji'ini fi musibati!! La ila ha'illallahu Muhammadur Rasulullah,
Allahumma la sahala illa maja'altahu sahala!!" Yanda ƙirjinta ke bugawa da sauri-sauri ka ce ƙararrawar
mutuwa aka buga mata, sai kawai ta fashe da kuka tare da komawa ɗakin bayan ta saka hannu ta toshe
hancinta. Babu abunda Sarah keyi sai miƙa mata hannu alamar ta ceceta, Aunty Maryam kuwa ta kasa
ƙarisawa gareta saboda wasu uban tsutsotsin dake mamaye a kan gadon zuwa ƙasa da wuyanta saboda
amansu da ta gama yi yanzu. "Sarah meke damunki? Inna lillahi! Wannan wani irin abu ne kuma?" Faɗin
Aunty Maryam cikin kuka. "Aunty Maryam mutuwa zan yi!" Sarah ta faɗi tana mai sakin wani irin
mahaukacin tusa mai mummunar warin fitar hayyaci tare da wani irin kakarin amai, sai ga aman tsutsotsin
nan na fitowa da uban yawa daga bakin Sarah kamar zata mutu, "Wayyoo, wayyoooo Aunty Maryam,
Wayyo Allah cikina." Da mugun gudu Aunty Maryam ta fita daga ɗakin don tabbas idan ta kuma minti ɗaya
ita ce zata mutun ba Sarah ba, don irin warin da Sarah keyi ba mai misaltuwa bane, tsutsotsin nan banda
ta gabanta har ta duburanta fita suke yi, ba suyi mata ƙaiƙayi kuma basu cizonta, amma kuma ganinsu
kawai abun tsoro da tashin hankali ne mai girma. Aunty Maryam na fita wuce ɗakinta tana wani irin kukan
tausayin halin da Sarah take yi, tunda uwarta ta haifeta bata taɓa ganin kalar wannan cutar ba. Wayarta ta
cire daga caji sannan lalubo number ɗin Khalil ta danna masa kira, lokacin shi kuma suna can kan Laure
suna ƙoƙarin ceto rayuwarta, sun samu sun tsayar da aman jinin, amma kuma maganarta ya ɗauke gaba
ɗaya. Duk irin ihun da za'a yi, ƙarshe ma ko magana aka yi mata a kunne, bata jin komai. Kuma abunda yafi
bawa likitoci mamaki, basu ga musabbabin faruwar haka ba. Hajiya kuma suger kawai suka gani sai kuma
da kidney wanda Khalil ya san dasu, sai suka bar kumburin jikin Hajiya akan ciwon suger ɗin sanadi, ita
kuma Laure babu taƙamaimai musabbabin ciwonta. Haka wayar Khalil dake silent yayi ta ringing yana
yankewa. Cikin lokaci ƙanƙani Nafeesa autarsu Khalil, gata da tsohon ciki sai kuka take yi, lokacin da taga
Hajiya da kuma yanda halittarta ya dawo, yanke jiki tayi ta suma tana farfaɗowa labour yace gani nazo,
dama kuma ashe jiyan kwana tayi da ciwon mara, Kasancewar irin naƙudar Hajiyan suke yi, cikin mintuna
talatin ta haifo ƴarta mace. Hankalin Nafeesa bai ɗan kwanta ba, sai da taga hajiyan ta ɗauki jaririyar da
kanta tana yi mata addu'a, don Hajiyar bata jin komai a jikinta na ciwo sai damuwar halin da Laure take
ciki, yarinya marainiya babu uwa babu uba, dangi sun watsar da ita bata nan bata can kamar wata mota.
Da wannan ya karɓa ya gama mora, sai ya turawa wancen, an mayar da ita uwa jaka, dalilin hakane yasa da
hajiya ta je Maiduguri bayan rasuwar mahaifinsu Khalil da shekara ɗaya sai ta ɗaukota. Da kakan Khalil da
kakan Laure uwarsu ɗaya uba kowa da nashi. "Mu'azzam ka sallame ni na koma gida tunda ni jikina
Alhamdulillah, ga kuma Nafeesa da ta samu ƙaruwa, tana buƙatar kulawa sosai kasan haihuwa ce ta fari,
kuma daga nan idan mijinta ya amince gida muka yi, sannan kuma ina gargaɗinku da babban murya kar ku
sake ku tadawa marmari daga nesa hankali, tunda dai Allah ya ban lafiya ba sai yaji ba, ku bar shi yayi
aikinsa hankali kwance, Ko Musaddiq (Barrister Muhammad Kabir) bance a faɗa masa ba." Da sauri Khalil
yace, "To amma Hajiya....." "Nace bana son su sani idan har na isa! Sannan kuma maza ka amsar min
takardar Sallama mu tafi gida, kuma ina so mu biya ta gidan surukanka zan roƙi alfarmar a bani wannan
ƙanwar tata ta zauna damu na wasu lokaci?" Faɗin Hajiya. Da mamaki Khalil yace, "Hajiya, ba dai Aina'u ba
ko?" A gadarance Hajiya tace, "Ita fa! Ko baza ka kai ni bane?" "Zan kai ki." Faɗin Khalil tare da ficewa daga
ɗakin ya koma office ɗinsa, wayarsa ya fara ɗauka tare da sakawa aljihu ba tare da ya duba ba, gaba ɗaya
hankalinsa ya koma gida, so kawai yake yi ya gansa kusa da Sarah don itama dole ya kawota asibiti ya duba
abunsa. "Ni da kaina zan duba matata babu wani ɗan iskan da zai gane min jikin mata." Ya faɗi a bayyane
tare da fitowa daga office ɗin. Kiciɓis suka yi da ya Abdul-Hakeem, "Yanzu dama wajenka zani, mummyn
Moon ta kira ni tana kuka sosai wai Sarah babu lafiya tana ta aman tsuts........." Ba tare da Khalil ya gama
sauraron ya Abdul-Hakeem ɗin ba ya nufi hanyar waje da bugun sauri, parking lot ya nufa tare da shiga
motar yayi reverse ya bar asibitin a guje. "Ina Khalilullah ɗin? Yazo mu wuce mana!" Faɗin Hajiya wacce ke
kallon yaya Abdul-Hakeem. "Hajiya akwai matsala ya wuce gida, matarsa ce babu lafiya, Maryam tace
aman wasu jajayan mitsi-mitsin tsutsotsin take yi, abun dai babu daɗin ji." "Inna lillahi wa'inna ilaihir
raju'un! Wannan wani annobace ya shigo cikin zuri'a ta? Allah gamu gare ka! Laure babu baki, ni da
maƙoƙo da zazzagowar idanu, surukata kuma da aman tsutsotsi. Kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, Allah
mun tuba." Faɗin hajiya tana mai fashewa da kuka. "Hajiya kiyi haƙuri ki bar kuka, in Sha Allah, zasu samu
sauƙi, ku taso mu tafi gida, to amma wa zai kwana da Laure tunda ba'a bata sallama ba?" Share hawaye
Hajiya tayi tare da faɗin, "Tare da ita zamu tafi tunda itama bayan rashin maganar babu abunda ke
damunta, kuma ba gida muka yi ba kai tsaye, zamu fara biyawa ta gidansu Uwata domin taho da ƙanwarta
ta ɗan zauna damu kaga ni ba ishashshen lafiya ba, Laure kuma babu baki, dole ina neman mai taimako."
"Kuma Hajiya sai a rasa wacce za'a ɗauko domin taimakon ki sai ƙanwar matar Khalil, a'a gaskiya Hajiya,
don ni haka nan yarinyar bata kwanta min a rai ba." Faɗin yaya Abdul-Hakeem. "To ni ta kwanta min, kuma
dole ka kaini gidan na taho da ita." Faɗin Hajiya tana hararensa. Bai kuma cewa komai ba ya juya ya ɗauki
akwatin kayan haihuwar Nafeesa ya fita dashi, ita kuma Nafeesa ta rungumo babynta Hajiya a bayanta
suka fito. Can gidan su Sarah kuwa, Aina'u ta gama shirinta tsaf don tana ganin komai ta tsakiyar tafin
hannunta. Suna parking a ƙofar gidansu ta saki wani murmushi tare da faɗin, "This is the end of you
Saratouh Nuhu!" Fitowa kawai Aina'u tayi da akwati a hannu ta fito waje, kallonta Abdul-Hakeem yayi ta yi
yana mamakin dama ta san da zuwansu ne ganin ba tare da an shiga da sun shiga ciki ba, kuma basu tura
kowa ba har ta fito. Da kanta ta buɗe boat ta saka kayanta a ciki tare da rufewa ta zagayo ta buɗe gidan
baya ta shiga tare da rufe motar tana faɗin, "Hajiya ina wuni, ya kuma ƙarfin jikin?" Ita kanta Hajiyar ba
ƙaramin mamaki tayi ba jin furucin Aina'u, "Ya akai tasan bani da lafiya?" Faɗin Hajiya cikin zuciya. Amma a
fili sai cewa tayi, "Jiki Alhamdulillah Aina'u." Kallon jaririyar hannun Nafeesa tayi tare da faɗin, "An samu
ƙaruwa? To Allah ya raya." Ba tare da tunanin komai ba Nafeesa ta miƙa mata jariyar, hannu biyu Aina'u ta
amshi jinjirar tana mai faɗin, "kyakkyawa da ita!" Daidai nan yarinyar ta tsandara wani mahaukacin ihuu
sai da ya Abdul-Hakeem dake driving ya juyo da sauri yana faɗin, "Lafiya?" Babu wanda ya bashi amsa sai
miƙa hannu da Nafeesa tayi tare da amsar jinjirar, sai kuma tsit kamar an ɗauke ruwan sama. Aina'u kuwa
wani murmushi tayi ganin kurwar ƴar na yawo a saman motar, can kuma sai ga fuskan *_Hell Ofulafula_*
ya wani irin zaro harshe tare da lashe kurwar jinjiran yana mai jinjiwa Aina'un sannan fuskar tasa wanda
Aina'u kaɗai ke gani ya ɓace. Khalil kuwa yana parking da gudu ya nufi side ɗinsu yana tsatstsallake step
uku-uku har ya isa ƙofar ɗakin Sarah, cikinsa ne ya bada wani irin saurin kuuuuuuuuu tsabar wani
dunƙulallan wari da ya shaƙa, amma stil haka ya tura ƙofar ya faɗa ɗakin. Tsalle ɗaya yayi ya isa inda take
tare da rungumota gaba ɗaya a jikinsa.............

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*
*_MATAR SAYYADEE_*
[11/10, 10:51 AM] Matar Sayyadee: "Mutuwa zan yi, mutuwa zan yi Khalil! Wannan ciwon nawa na tafiya
ne. Ni kuma haka nawa ƙaddarar yake! Na shiga uku! Baka jin wani irin wari da ƙarnin da nake yi? Aunty
Maryam ma ta kasa zama dani a ɗakin nan saboda wari da nake yi, na zama abun kyama!" Wasu irin
hawaye ne suka wanke fuskan Khalil amma yayi saurin sharewa saboda baya don zuciyarta ya cigaba da
karaya. "Sarah duk duniya idan sun kyamace ki, ni zan kyamace ki ne? Wallahi babu wannan ciwon aduniya
da za kiyi na kyamace ki! Ba gani nan ba, kina buƙatar kulawar wani ne bayan nawa? Shin na gaza ne??
Sarah nayi alƙawarin muna tare for better for worse, babu abunda zai iya shiga tsakanina dake don wata
lalura ta same ki. Yanzu zan ɗauke ki muje asibiti a duba min jikinki, bari na gyara miki jiki da ɗakin." Ya faɗi
hakane tare da janyeta daga jikinsa ya sauka daga kan gadon, kallon wandon jikinsa yayi sai yaga gaba ɗaya
tsutsotsin ne manne a jikin wandon, sunkuyar da kai Sarah tayi tana mai jin nauyinsa, ta san tabbas yana
ƙaunarta sosai, amma bata taɓa tunanin zai iya yin abunda yake yi mata a yanzu ba, ba tare da kyama ba.
Wandon ya cire ya rage daga shi sai boxer sannan ya cicciɓeta ya kaita bathroom yayi mata wanka, abunda
ya matukar bashi tsoro shine, ganin yanda tsutsotsin suke ɓulɓulowa, ɗazu da ya wanke mata, su daina
fitowa amma kuma yanzu idan yana wankowa kamar ƙara turosu ake yi. "Ya Ilahi!" Shine abunda Khalil ya
furta tare da kinkimarta ya fito da ita ya zaunar akan resting chair sannan ya gyara gadon, yanzu kam Sarah
ba kuka take yi ba, ido kawai take bin Khalil dashi tana jin wani irin ƙaunarsa na ƙara huda tsokar dake
ƙirjinta da ilahirin jikinta har ji take tsigar jikinta na tashi ganin yanda yake nannaɗo zanin gado da
hannunsa duk da kuwa tsutsar na taɓa jikinsa, tana kallon yanda tsokar jikinsa shima yake tashi amma a
fuska baza ka taɓa ganin wani yanayi na kyama a tattare dashi ba. Wayarsa taga ya ɗauko yayi danne-
danne kamun ya kwashi zanin yayin gadon yayi bayi dasu. Ya jima a bayin yana wanke zanin da hannunsa
da ya saka handglove sannan ya sake ɗauraye jikinsa yayi wanka tare da ɗauro alwala don lokacin tuni har
an idar da Sallar la'asar. Hajiya kuwa suna dawowa gida ta buɗe motar tare da kamo hannun Laure tana jin
wani irin mugun tausayinta, da ace tunda ta taso ne bata jin magana da sauƙi da ace lokaci guda kwatsam
ta samu lalurar, "Sannu kinji Laure, Allah ya baki lafiya." Ga mamakin Hajiya sai taga Lauren ta ɗaga kanta
alamar ta amsa sannun hajiyan, "Laure! Laure, kin ji abunda nace kenan? Alhamdulillah jin Laure ya
dawo." Da saurin Nafeesa da ya Abdul-Hakeem suka iso wajen suna faɗin, "Laure kina jin komai yanzu?"
Ƙara gyaɗa kai Lauren tayi hawaye na zubo mata daga idanunta, Aina'u kuwa wani taɓe baki tayi don ita ce
nan tayi magana da _Hell Ofulafu_ ta cikin tafin hannunta, akan ya dawo da jin Lauren ta yanda idan tayi
mata magana za taji, kasancewar ya bata wani abu ta haɗiya idan har tana son wani abu ba sai ta kuma
komawa Abia ba, tana matse hannun ta buɗe zai bayyana ta tsakiyar tafin hannunta. "Laure kiyi magana
mana, ko baza ki iya ba?" Hajiya ta tambayeta tana mai riƙo hannunta biyu. "Girgiza kai Laure tayi alamar
baza ta iya ba." Kuka Hajiya ta fashe dashi tare da faɗin, "Kiyi haƙuri Laure, yanda Allah ya buɗi
kunnuwanki, haka zai buɗe bakinki nan kusa in Sha Allah! Muje ciki." Ta faɗi tare da janta gaba, Aina'u
kuwa boat ta buɗe tare da ɗauko akwatin ta tabi bayan Nafeesa dake gabanta tana kalonta da gawar
babynta dake hannunta tana dariya cikin zuciya. Ya Abdul-Hakeem kuma ɗakin matarsa ya nufa wacce
itama tana can tashin hankali ya saukar mata da zazzafan zazzaɓi. Khalil yana idar da sallar la'asar ya koma
bayan gidan tare da ɗauko buta da baho ya kawo gaban Sarah ya dunga tsiyaya mata ruwan har ta
kammala alwala sannan ya mayar da komai bayin ya fito ya buɗe wardrobe ɗinta ya ɗauko mata hijjab tare
da saka mata yace, "Mine kiyi sallah ki kai wa Allah kukanki, in Sha Allah zai yaye maki wannan cutar. Bari
na sauka ƙasa na karɓo saƙo." Gyaɗa masa kai kawai tayi tare da kabbara sallar bayan ta kalli gabas a
zaunen da take, shi kuma ya fice. Kallon motar ya Abdul-Hakeem yayi tare da faɗin, "Sun dawo kenan!"
Cikin zuciya tare da nufar gate, leda ya karɓa a hannun wani matashin yaro irin masu delivery ɗin nan ya
dawo cikin gidan ya nufi side ɗin Hajiya, gaba ɗaya a parlour ya same su, Hajiya ta zabga tagumi tare da
zubawa Laure idanu. Kallon Laure yayi wacce lokaci guda ta zabge, duk wannan fara'ar da barkwancin sun
tafi, sai kallon kowa take yi a firgice. "Ina wuni ya Khalil." Aina'u ta faɗi tana zuba murmushi don babu
abunda bata gani ta cikin tafin hannunta, har wanka da alwalar da yayiwa Sarah yanzu da kuma fitar da
yayi ya amshi saƙo, bama wannan ba, hatta yanda zuciyarsa ke bugawa da jinin dake zagaye ilahirin jikinsa
tana kallon a yanzu haka. Kallon ɗaya yayiwa inda take ya kau da kai ba tare da ya amsa gaisuwarta ba.
"Mu'azzam ba gaishe ka Ƙanwar matarka take yi ba!" Hajiya ta faɗi tare da ɗan ɓata rai. "Ita ɗin
*_ƘANWAR MATATA_* ce kawai, bayan nan babu abunda muka haɗa Hajiya." Faɗin Khalil cikin zuciya,
amma a zahiri sai cewa yayi, "Lafiya!" A tilastance tare da zama akan kujera yana mai fuskantar Laure yace,
"Ƙawata ya jikin naki? Allah ya baki lafiya kinji! Ina sha Allah komai zai wuce." Ya faɗi hakane duk da yasan
ba zata ji ba, amma ga mamakinsa sai taga ta gyaɗa masa kai tana hawaye. Da sauri ya kalli Hajiya, tun kan
yayi magana hajiyan tace, "Cikin hukuncin ubangiji sai ga jin ya dawo, maganar ma nan kusa in Sha Allah."
Da murmushi ya juya tare da kallonta yace, "Ki kwantar da hankalinki, in Sha Allah komai zai wuce, ji cigaba
da addu'a. Wannan jarabawace daga Ubangijin halitta." Jinjina kai Laure tayi tana mai kallon Aina'u a sace,
karaf sai suka haɗa idanu, wani mugun harara Aina'un ta sakar mata tayi saurin kawar da kai, don wani irin
mugun tsoron Aina'un take yi, duk suka haɗa idanu sai gabanta ya yanke ya faɗi. "Sai kuma naji wani
maganar tashin hankali Mu'azzam, dagaske ne matarka ba lafiya tana aman tsutsotsi?" Hajiya ta faɗi
kamar ta fashe da kuka. Cike da damuwa Khalil yace, "Hakane Hajiya, yanzu ma asibiti zamu tafi da ita." Ko
kamun Hajiya tayi magana Aina'u ta buga wani irin ihu miƙewa ta dafe ƙirji tare da fashewa da kuka tace,
"Wayyoo Allah mun shiga uku, Sarah ce ke aman tsutsotsin?" Wani hararan gefen idanu Khalil yayi mata
tare da faɗin, "As if she care!" A cikin zuciyarsa. Hajiya kuma ƙoƙarin kamo hannun Aina'un tayi amma ta
goce tare da fita da gudu daga ɗakin, taɓe baki Khalil yayi tare da ajiye ledan da ya shigo dashi a gefe ya kai
hannu ya ɗauki babyn Nafeesa akan kujera, tun shigowarsa yake satan kallon babyn, sai yake gani kamar
babu rai a jikinta. Cikin dabara ya kai hannunsa saitin hancin babyn, amma bai ji alamun numfashi ba, taɓa
pulse ɗin yarinyar ya kuma yi nan ma yaji baya harbawa, wani wawan ajiyar zuciya ya sauke tare da kallon
Nafeesa ta gefen idanu, don ba ƙaramin tausayi ta bashi ba. Ba'a mamakin mutuwa, amma yayi mamakin
mutuwar babyn Nafeesa, don ko da Nafeesa ta haifeta, lafiyarta ƙalau kuma akwai kuzari sosai a jikinta da
ƙosashshen lafiya! Rufe babyn yayi har kai tare da shimfiɗar da ita a kan kujeran ba tare da ya kalli Nafeesa
ba. Nafeesa kuwa kallo ɗaya tayiwa babyn da khalil ya ajiye taji zuciyarta ya buga da ƙarfi bata ma san
lokacin da ta buga tsalle ta isa gaban kujeran da ya ajiye babyn ba. "Lafiya Khalilullah ka lulluɓe jaririyar har
ka kamar wata gawa?" Faɗin Hajiya wacce gabanta ke faɗuwa kamar zai faso ƙirjinta ya faɗo don ta san
idan har aka rufe ɗan adam har ka hakan na nufin babu shi. Girgiza kai Khalil yayi yana kallon tiles ɗin dake
shimfiɗe, Hajiya bata san lokacin da ta furta, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Nafeesa kuwa kuka ta
fashe dashi tana mai jijjiga hannun Khalil tana faɗin, "Don Allah kar kace min ta mutu, ka sake dubata da
kyau, lafiya ƙalau muka baro asibiti, Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Na shiga uku!!" Faɗin Nafeesa tana
kallon babyn nata, hannunta kuma yana kan na Khalil dake kallon ƙasa idanunsa sun cika da hawaye.
Hajiya kai hannu tayi ta ɗauki jaririyar tana ƙara dubata, kuka ta fashe dashi bayan tabbatar da yarinyar ta
koma, "Hajiya ƙarfafa mata guiwa za kiyi ba ki karya mata zuciya da kukanki ba, ita nata tayi kyau tunda
bata ɗibi zunubin komai ba, mune abun jin ba ita ba. Allah yasa mai ceto ce. Nafeesa nasan abun da zafi,
amma kiyi haƙuri, Allah da ya karɓe abunsa ya fiki sonta, ki gode masa ta hanyar yin tawakkali, kuma dama
shi da kansa yace ba wai don munce munyi imani ba shikenan ba zai jarabce mu ba. Allah zai baki wata in
Sha Allah, ai ba cewa akai baza ki ƙara haihuwa ba. Ki kwantar da hankalinki kinji, Allah ya baki haƙurin
rashi!" Gyaɗa kai Nafeesa tayi zafafan hawaye suna kwaranyo mata, miƙewa yayi ya ɗauki kasar da ya shigo
da ita ya fita daga ɗakin don zai iya zubar da hawaye idan yana kallonsu, "Allah mun gode maka, Allah kasa
muci wannan jarabawar!" Ya faɗi tare da nufa side ɗin yaya Abdul-Hakeem. Knocking yayi, ba jimawa yaya
Abdul-Hakeem ɗin ya buɗe masa ƙofa, "Lafiya Ibrahim?" Faɗin ya Abdul-Hakeem ɗin ganin yanayin Khalil
ɗin. "Allah ya yiwa ƴar wajen Nafeesa rasuwa yanzu." Da sauri ya Abdul-Hakeem ɗin yace, "Inna lillahi
wa'inna ilaihir raju'un! Ba dai jinjirar ba?" Ko kamun Khalil yace wani abu har Aunty Maryam ta iso wajen
gabanta na wani irin bugawar tsoro da tashin hankali, don duk a tunaninta Sarah ce ta mutu. "Wallahi
kuwa ita, yanzu na shiga ɗakin, su basu ma sani ba sai da na ɗauki yarinyar na duba pulse ɗinta don tun da
na kalleta sau ɗaya na fahimci babu rai a jikinta." "Wacece ta mutu?" Aunty Maryam ta faɗi a firgice. "Ƴar
wajen Nafeesa ce." Ya Abdul-Hakeem ya bata amsa. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Ba yanzu kake faɗa
min ta haihu ba? Mun shiga uku daga wannan sai wannan!" Khalil yace, "Haba Aunty Maryam, Kar kiyi
saɓo mana!" Kuka Aunty Maryam ta fashe dashi daidai lokacin da wayar ya Abdul-Hakeem ɗin yayi ƙara.
"Gama mijinta nan yana kirana." Ya faɗi tare da picking kiran shi kuma Khalil ya juya tare da nufa side
ɗinsa. Aina'u na shiga parlourn Sarah ta fashe da dariya har da kyakyatawa tare da faɗin, "Su Mine da
Happiness kenan, ai yanzu aka soma wasan wallahi, ina nan zuwa gare ka Khalil, wallahi sai na mayar da kai
masarrafin talabijin!" Sama ta hau tare da tura ɗakin Sarah, da gudu ta fito tana mai danne ƙirjinta saboda
wani uban wari daya busota, "Bala'iiiii, gaskiya _Hell Ofulafu_ ka iya aiki, wannan bala'in wari haka, ai ko
Lami da babanmu masoyinta baza su iya jurewa ba balle kuma miji! Taɓ, sunanki sorry Saratu. Aini ko buɗe
Ƙofar ban iya ƙara yi bare in shiga ciki. Allah dai ya ƙara azabar da yafi haka." Aina'u ta faɗi tare da saukowa
ƙasa tana mayar da numfashi. Turo ƙofar Khalil yayi ya shigo, ganin Aina'u zaune akan kujera ya saka shi
sakin wani malalacin murmushi tare da faɗin, "Hmm! Har kin gama ihun tashin hankali akan ƴar uwarki na
aman tsutsotsi? Kin kasa isa wajenta ko? Dama na san baza ki iya ba, wacce ke ciwon da bai kai wannan ba
kin kasa taimakonta sai wannan ne zaki taimaka mata! Nasan wallahi duk ƙaunarki da kuɗi, ko nawa zan
baki, baza ki iya kula da ƴar uwarki ba, ban dai sani ba ko idan kinga tana shashshekar mutuwa za ki iya, to
ina so ki sani, Ni ba zan taɓa gazawa ba da matata, zan mutune matsayin bawa mai hidimta mata! Ki fice
min a ɗaki yanzun nan!! Ke _ƘANWAR MATATA_ ce amma ban san mai yasa ba, baki taɓa burgeni ba, ban
sani ba ko hakan nada nasaba da nuna rashin son ƙulluwar auren mu da Sarah tun farko!" Yana gama faɗin
hakan ya haura sama. Sai da gabansa ya faɗi jin warin ninkuwa yayi a kan nada, ga tsutsotsi ne nan faca-
faca tun daga kan kujeran da take kai har ƙasa, ita kuma kifa kanta kawai tayi akan hannun kujeran tana
shashshekar kuka don kukan yaƙi fitowa. Ajiye ledar yayi a kan gado tare da isa wajenta duk da uban warin
da take yi ya cicciɓeta ya kaita bayi ya ajiye a cikin bathroom tub sannan ya fita cikin sauri ya gyara inda ta
ɓata sannan ya dawo da ita kan gado bayan ya shimfiɗa wani zani gudun kada tsutsotsin su sake ɓata
wajen. Wannan ledan ya ɗauko tare da buɗewa ya zaro pampas ɗin manya guda ɗaya ya saka mata........

_Kuyi haƙuri da wannan Please, in sha gobe zan yi mai yawa_

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*
*_MATAR SAYYADEE_*
[11/10, 4:32 PM] Matar Sayyadee: "Mine, Nafeesa ta samu ƙaruwa ɗazu." Ya faɗi maganar yana mai jan
skirt ɗinta sama ya zage zip ɗin. Out of excitement tace, "Dan Allah! Alhamdulillah Allah ya raya, don Allah
ka ɗauko min picture ɗin babyn in ganta." Kallon fuskanta Khalil yayi, babu abunda yafi kyau da fuskanta
irin fara'arta, sai yaji kamar kar ya faɗa mata babyn ta koma. "Ya naga kayi shuru Happiness?" Faɗin Sarah.
Ajiyar zuciya Khalil ya sauke tare da kau da kansa daga kallonta yace, "Allah ya amshi abunsa, babyn ta
koma." Zaro idanu Sarah tayi tare da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Ina Nafeesan yanzu? Wani
hali take ciki?" Sarah ta faɗi hawaye na zubar mata. Hannunta biyu ya kama tare da faɗin, "Ta ɗauki
dangana, ta san cewar Allah da ya amshi rayuwarta ya fita son yarinyar, ta amshi ƙaddararta ta hanyar
dangana da fauwalawa Allah komai." A hankali Sarah tace, "Allah ya ƙara mata haƙuri da dangana."
Miƙewa yayi tare da faɗin, "Haka ake son duk musulmi da ɗaukar ƙaddara mai kyau da mara kyau idan har
ya yarda shi ɗin cikakken musulmi ne, shiyasa nake so kema ki fauwalawa Allah komai ki daina koke-koken
nan, in Sha Allah zaki samu lafiya. Bari naje zana'idar in dawo sai mu tafi asibitin, kina buƙatar wani abu?"
Girgiza kai Sarah tayi tare da faɗin, "Babu abunda nake buƙata, kayi tafiyarka, Allah yasa mai ceto ce. Nima
zan gwada miƙewa inje can wajen Hajiya yanzu tunda ka saka min pampers tsutsotsin baza su zubo ma."
Kallonta yayi tare da faɗin, "Idan har kin ga baza ki iya ba, kiyi zamanki gaba ɗaya sun san baki da lafiya. Ki
kular min da kanki, sai na dawo." Yana gama faɗin haka ya fita ya bar ɗakin. Hannu Sarah ta ɗaga tare da
faɗin, "Ya Ubangiji ga mijina nan, ka kare min shi daga dukkanin cutuwa, ka ƙara masa so da ƙaunata a cikin
zuciyarsa, ni kuma bani lafiya mai amfani ta yanda zan bauta masa wajen yi masa biyayya har in dawo
gareka. Allah ka bani lafiya alfarmar annabi sallallahu alaihi Wasallam." Ta ƙarisa maganar tare da fashewa
da kuka. Can cikin gida kuwa, har mijin Nafeesa da danginsa sun ƙariso, mahaifiyarsa ita tayiwa babyn
wanka tare da yi mata sutura, shi kuma Qasim mijin Nafeesa sai lallashinta yake yi yana bata haƙuri akan in
Sha Allah zasu samu wani nan kusa. Kamun magrib har sun kai gawan makwancinta sun rufe sun dawo, sai
gidan yayi wani irin tsit kowa da irin jimamin da yake yi, yayin da Laure ke wani irin zabura da firgita idan ta
kasance ita kaɗai a waje, don babu fuskan da take gani sai na Aina'u da _Hell Ofulafu_ suna tsoratata gashi
kuma babu bakin magana. Sarah ta iya fita har side ɗin Hajiya, kallon ɗaya Hajiya tayi mata gabanta ya faɗi
ganin wani mahaukacin rama da tayi, don ko ɗazu da safe sun haɗu kamun faruwar komai, "Wannan wani
irin cuta ce kamar ta iska?" Hajiya ta faɗi a zuciyarta. Sarah kuwa da bata san halin da Hajiyar ta shiga ba,
waro idanu tayi ganin halittarta gaba ɗaya ya canza, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, Hajiya haka kika
koma?" Aunty Maryam ce tayi saurin tarota ganin zata zube a ƙasa, ta zaunar da ita. Rarrafawa tayi ta
ƙarisa wajen Hajiya tare da ɗaura kanta akan ƙafafun Hajiya ta hau rera kuka, hajiya bata iya cewa komai
ba sai shafa bayanta da ta shiga yi tana danne nata hawayen. "Oh Allah! Abu kamar jifa, daga wanda
halittarsa ta canza, sai kuma wacce maganarta ya ɗauke gaba ɗaya, da kuma mai aman tsutsotsi! Gaskiya
wannan abun dubawa ne. Duk mai bin mu da sharri in Sha Allah sai ya koma masa." Faɗin Nafeesa wacce
taci kuka ta ƙoshi, idanun nan sun yi jazur." Wani wawan kallon gefen idanu Aina'u tayiwa Nafeesan a
zuciyarta tana faɗin, "Ashe kema zaki bi ƴarki kenan!" Sarah kuwa ɗagowa tayi ta kalli Nafeesa tare da
faɗin, "Nafeesa wacece kuma maganarta ya ɗauke?" "Laure!" Nafeesa ta bata amsa hawaye na zubowa.
Hajiya ta kalli ɗaya daga cikin yaran dake ɗakin tace, "Namrah kunna rediyon can ki kunna mana karatu
zuciyar kowa tayi sanyi." Da jin haka wuff Aina'u ta miƙe ta fita daga ɗakin ta baya gudun a ganta, don yi
nayi kamar zata shiga toilet ɗin dake parlourn, Aunty Maryam kuwa tunda ta miƙe take lure da ita, don
haka nan taji tana mugun zargin Aina'un, sam tun ranar farko data fara ganinta bata kwanta mata a rai ba.
Da sauri ta zaga ta baya ta tsaya bayan flowers, sai da ta kalli gefe da gefe sannan ta fiddo hannunta tare
danna tsakiyar tafin hannun, cikin second biyar sai ga _Hell Ofulafu_ ya bayyana cikin suffarsa ta tsoro,
gefensa kuma wani gajeren halitta abun tsoro ne mummunan gaske, shi ya daka mata tsawa tare da faɗin,
"Menene buƙatarki ta gaba?" "Nafeesa! Ita nake so tabi jaririyar, ba bada jininta matsayin ruwan da Hell
zai ɗanɗana, sannan ina so a saka mummunar warin da yafi wanda Sarah keyi a jikin mijinta ta yanda zata
riƙa kyamatarsa har hakan ya fusata shi yayi mata wulaƙanci, don na san tabbas idan aka yi haka Khalil zai ji
haushinta tunda shi ya jure bai kyamaceta ba duk da tsutsotsin dake fita a jikinta da kuma warin da take yi.
Sannan na uku, ina so a ɓatar da kokwanto da shakkun da ke zuciyoyin mata da mijin gidan nan a kai na,
ina nufin SS Abdul-Hakeem da matarsa Maryam, sannan Barrister Muhammad Kabir da LTG Abdullah ka
mantar dasu suna da family ka Kaduna, ina so su manta da kowa nasu dake Kaduna, ko da wasa kar su
waiwayi gida! Abdul-Hakeem ma ayi masa abunda zai jawo a koresa daga aiki, don na tsani ƴan sanda
musamman na farin kaya!" Wannan mummunar halittar ya fashe da dariya tare da faɗin, "Aikin ya
kammala, sai dai jinin ƙanwar Mijin yayarki yayi kaɗan, dole sai kin ƙara da jinin yaro ƙaramin kuma
namiji." Shuru Aina'u tayi tana tunanin ta inda zat dea samu jinin yaro ƙaramin, "Rabo ɗan wajen Na'ima!"
Faɗin Aina'u a bayyane tana mai sakin murmushi tare da ƙara faɗin, "Na rage maki wahala Na'ima, a sauka
lafiya Rabo!" Ɓat _Hell Ofulafu_ da wannan halittar suka ɓace daga tafin hannunta don sun gama sauraran
abunda zasu saurara, tun ambaton sunan Rabo da tayi na farko, har _Hell Ofulafu_ ya janyo kurwarsa tare
da haɗiyewa. Aina'u na juyawa suka yi idanu huɗu da Aunty Maryam da ta biyo ta a baya, har fitsarin tsoro
ya gama wanke jikinta, gaba ɗaya jikinta sai kakkarwa yake yi. Aina'u kuwa wani murmushi ta saki ba tare
da ko ɗar ba don Aunty Maryam ɗin taji komai da take tattaunawa da _Hell Ofulafu_. Zagaye Aina'u ta
shiga yi tare da faɗin, "Makanta, kurmanta, rashin yin magana, mutuwa ɓarin jiki, mutuwar gangar jiki
gaba ɗaya, ƙona ki da ranki, wanne kika zaɓa?" Kuka Aunty Maryam ta soma yi tare da faɗin, "Dan girman
Allah Aina'u kiyi haƙuri kar kiyi min ko ɗaya daga cikin abunda kika lissafo, na zaɓi da nayi shuru da baki na,
babu wanda zai ji wannan maganar nan daga ni sai ke!" Wani dariya Aina'u ta kwashe dashi tare da faɗin,
"Kin ga nayi maki kama da wawuya? Ko da yake, ni nayi maki zaɓi, shine barin gidan nan, kuma kin san
wani abu, duk lokacin da bakinki yayi kuskuren buɗewa ya faɗawa wani wannan abun da kika ji, baza ki iya
faɗin komai ba, kuma daga ranar baza ki kuma magana ko kiji ba har ki mutu! Wuce kije ki fara haɗa
kayanki kamun takardar sakinki ya biyo ki!!" Ta ƙarisa maganar a tsawace tana mai nuna mata hanya. Da
sauri Aunty Maryam ta riƙo ƙafafuwanta tare da faɗin, "Na roƙeƙi da girman Allah kar ki raba ni da aurena,
wallahi nayi maki alƙawarin babu mai jin wannan maganar har sai idan Allah ne yayi ikonsa, ina son mijina
da aurena don Allah kar ki raba ni dasu." Wani mugun tsaki ta ja tare da faɗin, "Sai ki zaɓa, rayuwarki,
lafiyar jikinki, ko kuma aurenki?" Shuru Aunty Maryam tayi tana wani irin kukan baƙin ciki. Aina'u ta taɓe
baki tare da faɗin, "Gidan na kowa sai yaji a jikinsa, na rantse da Yesu Almasihu mai ceto!" Da saurin Aunty
Maryam ta kalleta jin abunda ta furta tare da faɗin, "Babu shakka, ashe shiyasa babu ɗigon imani a
zuciyarki, in Sha Allah sai kin girbe abunda kika shuka azzaluma kafurar banza!" A cikin zuciyarta. "Ki wuce
kije ki soma haɗa kaya, don yau gidan mai dattin hula da ɗan kwali za'a kwana!" Tana gama faɗin haka ta
wuce ta bar wajen tana waƙar zumunta. Aunty Maryam kuwa kuka ta dunga rusawa tana tunanin
makomarta, ita da babu uwa, babu uba, rayuwa take yi a wahale a wajen dangin ubanta kamun Allah ya
kawo mata Abdul-Hakeem har suka yi aure, idan ka ganta gidansu gaisuwa taje ko kai masu abun arziki don
suna ba wasu masu arzikin bane, talla tayi su kala-kala irin su kunun gyaɗa da alale, da daddare kuma
burabusko da miyan taushe, kuka da kuɓewa! Har zunɗenta ake yi wai don ta auri ɗan masu kuɗi sai
fankama take yi tana ƙoƙarin manta asalinta. "Shinekan wahalata ta dawo sabuwa fil, masu fatan irin haka
ta faru dani sun samu dama. Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Allahumma arji'ini fi musibati wa aklifni
khairan minha!!" Haka aunty Maryam tayi ta nanatawa har ta isa ɓangarenta. Cak ta tsaya a parlour tana
kallon tanƙameman hotunsu su uku, ita da Abdul-Hakeem da kuma ƴarsu Maimoon. Can gidansu Lami
kuwa, Rabo na zaune kusa da ita da roban abinci a hannunsa yana ci, gaba ɗaya suna tsakar gida suna shan
iska kasancewar garin akwai zafi, kawai sai suka ga Rabo ya fara wani irin jijjiga idanunsa na sama, hatta
robar abincin dake hannunsa jijjiga yake yi, kumfa baƙiƙƙirin ya soma kwaranyowa daga bakinsa, gaba ɗaya
da gudu sukai kansa suna kiran sunansa, Lami kuwa wani tsalle ta buga tare da fasa ƙara ta shiga faɗin,
"Yesu! Yesu!! Yesu gamu gareka mun bar zunubi, duk wani dodo ko maye ko mugun dake son tafiya da
granson ɗina ka tsine masa, a cikin mu'ujizozinka ka cire shaitan ɗin dake kusa da jikana yaaaa Yesu
Almasihu mai ceto!" Tana faɗin maganar ne tana wani irin tuma a ƙasa tare da fasa ihu. Da sauri baba dake
ɗaki ya fito, tuni Na'ima dake riƙe da Rabo tana kuka ta nufi wajen baba tare da miƙa masa shi tana mai
ɗaura hannu a kai tana kuka. Baba kuwa yana amsar Rabo ya fahimci rai yayi halinsa saboda yanda jikinsa
ya sake. Shimfiɗar da shi yayi akan tabarma tare da miƙar masa da hannu sannan ya miƙa hannu ya janyo
zanin dake kan igiya ya lulluɓesa har kai. Wani irin baya Na'ima tayi ta tafi luuuuuu ta faɗi ƙasa sumamma!
Da gudu su Marfu'a suka yi kanta tare da cicciɓanta suka kai ta ɗaki suka shinfiɗe. Lami kuwa sai kururuwa
take yi, hakan ya jawo hankalin maƙota suka cika gidan tam. Baba kuma waya ya ɗaga ya kira abokansa su
baba Sama'ila, har aka gamawa Rabo wanka Na'ima bata farfaɗo ba, sai can har ana tunanin kaisa kawai
sai ta farfaɗo, har ɗaki baba ya shigo yayi mata nasiha tare da ce masa taje tayi masa addu'a, da kyar ta isa
zuwa ta zube guiwowinta a ƙasa kusa da gawar, "Ka yafe min, ka yafe min!" Shine abunda Na'ima tayi ta
maimaitawa tana kuka. "Ba'a kuka gaban gawa Na'ima, haramun ne!" Faɗin baba Sama'ila. Hassana ce ta
kama hannunta suka fita daga ɗakin don har an kawo makara za ayi masa sallah, Gaba ɗayan su babu mai
hijab ko ɗaya, a wajan maƙota suka ara sannan suka iya fita aka yi sallar dasu. Na'ima bata kusa haukacewa
ba, sai da aka saka Rabo cikin mota za'a wuce, sai da aka turata cikin gida aka kullo ƙofar saboda yanda
take wani irin mahaukacin kukan tashin hankali. Baba kuwa babu abunda dake zuwa bakinsa sai Allah yasa
mutuwar nan ta zama sanadin shiryuwar ƴaƴan nasa. Bayan an dawo daga maƙabarta baba yayi ta kiran
layin Khalil domin ya shaida masa mutuwar amma bai samunsa, layin Sarah kuma har ta gama ringin ba'a
ɗauka ba. Can gidansu Khalil kuwa, Aunty Maryam zaune a ƙasa wayarta a hannunta tayi masa ƙuri tana
jiran message daga Abdul-Hakeem akan ya saketa, ɗiririn saƙo ya shigo wayar, gabanta ne ya buga da ƙarfi
don har sai da ta rintse idanu tana addu'a, dakyar ta iya duba saƙon, sai taga ashe daga bank ɗinta ne suna
tayata murnar zagayowar ranar haihuwarta. Wani wawan ajiyar zuciya ta sauke tare da hamdala a
bayyane, daidai nan ya Abdul-Hakeem ɗin ya murɗa handle ɗin ƙofar ya shigo, da wani irin sauri ta miƙe
tana kallonsa gabanta na wani bugawa kamar zai faso ƙirjinta ya faɗo. A hankali ya riƙa takowa ita kuma
tana matsawa har suka dangana ga jikin bago. Goshinsa ya haɗe da nata tare da faɗin, "Maryama, tun da
na aureki tsayin shekaru biyar kenan, baki taɓa yi min wani abun da naji kamar in rabu dake ba, ko wani
aiki nake yi na wahala a wajen aiki, idan na tuna da ke, sai inji farin ciki ya mamaye zuciyata tare da
fuskantar abunda nake yi domin inyi in gama in dawo gida na ganki, ki sani shi aure rai gare shi, idan
lokacinsa yayi, da daɗi da babu daɗi sai an rabu! Kiyi haƙuri Maryam, zan ƙara maimaita maki, baki yi min
komai ba sai alkhairi, kiyi haƙuri da abunda zai fito daga bakina yanzu," sai dai ya ɗan yi jim yana kallonta
sannan ya haɗe hannunta biyu tare da faɗin, "Ki yafe min, na sake ki saki ɗaya Mary......" Bata bari ya kai
ƙarshe ba ta fashe da wani irin kuka tare da gittashi da sauri ta haura sama tare da banko ƙofa, shi kansa
Abdul-Hakeem ɗin wasu zafafan hawaye ne suka kwaranyo masa daga idanunsa, ya rasa wani irin wutane
yake ta ruruwa a zuciyarsa, haka nan ya dunga jin zafi da raɗaɗi, can kuma ya soma jin shi kawai aure ne ya
haƙura dashi, kamar ana ingizashi yaji domin yazo ya saki matarsa da a kullum burinta ta kyautata masa.
Aina'u bata koma ɗakin Hajiya ba saboda ƙira'ar dake tashi, sai ta koma can baya ta inda baza taji sautin
karatun ba ta zauna tana mai jin zafin furucin Nafeesa, "Sai na ɗanɗana maki azababbiyar mutuwa in dai ni
ƴar Elizabeth da Nuhu ce!" Ta faɗi maganar tana sakin kwafa. A ɗakin Hajiya kuwa, Sarah tayi kuka kamar
zata mutu, bata soma jin salama a ranta ba sai da aka kunna ƙira'ar nan. Zuwa anjima can sai ga Khalil ya
shigo ɗakin, shi bai ma ɗauka ta iya zuwa ba nan ɗin ba, sai da ya shiga ɗakinta ya taras bata nan sannan ya
dawo nan, "Ya ƙarin haƙuri Nafeesa?" Luhu-luhun idanunta ta ɗago tare da faɗin, "Alhamdulillah!" Kallon
Sarah Khalil yayi tare da faɗin, "Mine taso mu tafi yamma nayi." "Ina zaku?" Hajiya ta tambaya, "Asibiti
nake so muje na dubata." Gyaɗa kai Hajiya tayi tare da faɗin, "Allah ya ƙara sauƙi, sai kun dawo." Da
ameen Khalil ya amsa, ita kuma Sarah ta miƙe ta fito ya biyo bayanta, abunda ya matuƙar bashi mamaki
shine, lokacin da take cikin ɗakin Hajiya, babu wannan warin da take yi ko kaɗan, amma tana fitowa warin
ya dawo. Bai ce komai ba har suka isa ɗaki, kalonta yayi tare da faɗin, "Za'a canza pampers ɗin ne?" Girgiza
kai tayi. Sai ya nufi wardrobe ya ɗauko hijjab ɗin ta ya saka mata sannan suka fito, a cikin mota ma karatun
ya kunna, yana kallon Sarah yanda ta kwantar da kanta jikin kujera tare da lumshe idanu. Suna isa ya shiga
da ita lab ya ɗibi jininta ya bada ayi gwaje-gwaje sannan suka fito suka nufi X-ray room, nan ma sai da yayi
examining Virgina ɗinta sosai. Kusan test kala goma aka yi mata, basu suka dawo gida ba sai past 10, wasu
tests ɗin sun fito a ranar, wasu kuma sai bayan 8days zasu fito, wanda suka fito a ranar guda huɗu ne,
kuma gama ɗayansu komai normal, guda ɗaya ne ma a ɗan ga yest infection kaɗan shima kuma na ciki ne,
babyn cikinta lafiya ƙalau. Suna dawowa gida ya sake yi mata wanka ya canza mata pampers tayi sallar
isha'i sannan suka ci abincin da ya tsaya ya saya masu a restaurant. Yana son faɗa mata ɗan wajen Na'ima
ya rasu amma bai son hankalinta ya tashi, don sun yi waya da baba daga baya, kuma ya faɗawa baban bata
da lafiya sai dai bai faɗa masa asalin ciwon ba, baban yace masa ba sai tazo ba, tayi zamanta kawai zai faɗa
masu bata da lafiya. Haka suka kwanta ba tare da ya faɗa mata ba. Bai ji kyamarta ba, yanda suka saba
kwana haka suka kwanta kwance a kan ƙirjinsa, can cikin dare ya jisa sharkaf, cikin sauri ya tashi ya kunna
bedside lamp, cike da mamaki yake kallon uban fitsarin da Sarah ta lafta duk da pampers ɗin jikinta ga
kuma tsutsotsin nan sun fara fitowa. Tagumi ya zuba yana kallonta tana bacci peacefully bata ma san mai
ke faruwa ba, hawaye ne suka gangaro masa na tausayinta, ya jima yana kallonta kamun ya sauka daga kan
gadon ya cire boxer ɗin jikinsa don ya jiƙe sharkaf, bayi ya shiga ya wanke jikinsa sannan ya dawo ya soma
tashin ta a hankali, miƙa ta soma yi, sai ji tayi hannunta ya sauka a kan lema, da sauri ta ware idanunta tare
da tashi zaune tana mai faɗin, "Happiness, fitsari kwance nayi? Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Na shiga
uku!!" Tausayi ta bashi sosai, sai kawai ya sunkuceta ya kaita bayin ya ajiye a tub sannan ya fito ya kwashe
zanin gadon ya kai bayin tare da ɗauko wani ƙaramin towel da ruwa da liquid soap ya goge katifar sosai
sannan ya saki fanka tare da kwasar janin gadon ya shigo dashi bayin ya zuba a bucket sannan ya isa
gareta, babu abunda take yi tunda ya ajiyeta sai kuka, "Wallahi tallahi zaki ɓata min rai Sarah! Kanki farau
ko ƙarau? Haba! Baki san kukanki na tada min da hankali ba?" Yana gama faɗin haka ya shiga cire kayan
dake jikinta, sosai yaji tsoro lokacin da ya cire pampers ɗin jikinta gaba wannan jajayan mitsi-mitsin
tsutsotsin sun koma canza colour, wasu sunyi green, wasu yellow-yellow, wasu kuma farare. Bai bari ta gani
ba ya ajiye pampers ɗin sannan ya wasa ruwa ya shiga cuɗa jikinta. Sai da ya gama mata wankan sannan ya
dawo da ita ɗakin ya ajiyeta a kan gado inda babu lema ya saka mata wani pampers ɗin tare da kayan bacci
sannan ya mayar da ita ɗakinsa ya rufeta da bargo ya dawo nata ɗakin ya wanke kayan nan tsaf sannan ya
koma ɗakinsa ya kwanta tare da jawota jikinsa. Aina'u dake ɗakin can side ɗin Hajiya tana kallon komai ta
tsakiyar tafin hannunta, bata san lokacin da ta jefi mirror da wayarta dake gefensa ba, sai ji kake
tatsatsatsatsa! Tafin hannunta ta matsa da ƙarfi, wannan karon _Hell Ofulafu_ bai bayyana ba, wannan
mummunar halittar ne ya bayyana tare da faɗin, "Kina da wutar ciki Aina'u, duk abunda muka ce zamu yi,
za muyi shi, shin bamu cika maki biyu daga ciki bane? Rabo ya mutu, Abdul-Hakeem ya saki Maryam,
yanzu saura warin da za'a turawa Khalil, korar Abdul-Hakeem daga aiki, mutuwar Nafeesa da kuma mantar
da LTD Abdullah da Muhammad Kabiru cewar suna da uwa da ƴan uwa a Kaduna. Kar ki ƙara neman mu
akan wannan buƙatar, sai dai idan wata buƙatar ke gare ki." Yana gama faɗin haka ya ɓace. Ajiyar zuciya
Aina'u ta sauke tare da kwanciya rub da ciki, can kuma ta miƙe ta buɗe zip ɗin jakarta ta ɗauko murɗin
wiwi ta saka a baki tare da kunna lighter ta hau zuƙa, sai da tasha murɗi uku sannan ta kora codine kwalba
ɗaya sannan ta faɗi yarab a kan gadon ta hau bacci. Bayan kwana uku, sam Hajiya bata lura aunty Maryam
bata gidan ba, don tare suka tafi da Moon, ya Abdul-Hakeem kuwa yayi wani irin zugewa, don washa garin
ranar da ya saki aunty Maryam aka dakatar dashi daga aiki, Hajiya kuma ta kasa tambayar ina Aunty
Maryam ɗin duk da kuwa bata ganinta, wani irin mahaukacin tsoron Aina'u take yi, idan ta ganta gabanta
faɗuwa yake yi, Nafeesa ma haka, wannan dalilin ne ya saka ta tattara tabi mijinta duk da dama shima
abunda yake so kenan, don dangi sun taso shi gaba akan ta dawo gidan auranta. Zaune Hajiya tare a kan
kujera ta rasa abunda ke damunta, ga Laure dake gefenta wacce lokaci bayan lokaci take saka bayan hannu
ta share hawayeta, tayi wani irin mugun rama, hatta a fuska sai ƙasusuwa suka fito mata, babu komai a
fuskan dai idanu da haƙora yaƙaƙau! Fitowa Aina'u tayi daga ɗakin da Hajiya ta ware mata tana fito, babu
wanda ya iya ɗago idanu ya kalleta a cikinsu, "Hajiya ko kin san wannan abun dake hannuna?" Faɗin Aina'u
tana mai kai mazaunanta akan kujera, ɗagowa Hajiya tayi ta kalli hannun nata tare da girgiza kai. Sakawa a
baki Aina'u tayi tare da kunna lighter ta kai kan wiwi ɗin tayi masa wani irin zuƙa tare da faɗin, "Wiwi ce!"
Zaro idanu Hajiya tayi tare da yin gum, Laure kuwa babu inda jikinta baya rawa ga warin hayaƙin mara daɗi
mai tada zuciya kuma babu wanda ya isa ya tashi a cikinsu. Sai da tasha murɗi biyu sannan ta kwanta akan
three sitter tare ɗaura ƙafa akan saman kujeran tana kallon Tv, can kuma ta juyo ta kalli Laure tare da faɗin,
"Ke, tashi ki canza min channel zuwa MBC action." Da sauri Laure ta tashi ta nufi wajen TV ɗin daidai
lokacin da Khalil yayi sallama ya shigo ɗakin domin shaidawa Hajiya yana son shi da Sarah su tafi India
domin a duba masa jikinta, don gaba ɗaya result ɗin tasa-tasan da aka yi mata a asibitin bai nuna tana
ɗauke da matsalar komai ba. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, Hajiya! Warin wiwi fa nake ji a ɗakin nan."
Da sauri Laure da hajiyan suka kalli juna sannan suka kalli Aina'u da ta wani irin ɗaure fuska. "Hajiya......."
Tun kamun ya ƙarisa Hajiya tayi saurin faɗin, "Ni dalla ka isheni da magana, to ni nasha wiwin!" Zaro idanu
Khalil yayi, sai kuma ya mayar da dubansa izuwa wajen Aina'u tare da faɗin, "Dan ubanki kece kika sha
wiwin ko?" A watse ta kallesa tare da faɗin, "Hajiya ce tasha, ko baka ji ta baka amsa ba." Wani wawan
mari Khalil ya ɗauke fuskan Aina'un dashi tare da faɗin, "Dan ubanki zo ki bar gidan nan tun da ba gidan
ubanki bane......"

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_MATAR SAYYADEE_*

*Paid book 08128755583*


[12/10, 6:12 PM] Matar Sayyadee: "To sannu ɗan masu gida! Wai kai Khalilullah mai yasa baka da kawaici
ne a rayuwarka? Ƙanwar matarka ce fa! Ai ko don uwata ka raga mata. Gaskiya ka ɗauki hakki, kuma ka
bata haƙuri." Faɗin Hajiya rai a ɓace. Nuna Aina'u dake riƙe da kunci yayi da hannu tare da faɗin, "Wannan
ɗin zan bawa haƙuri? Kiyi haƙuri Hajiya, ban taɓa tsallake umarninki ba, amma yau kam bazan iya abunda
kika umarceni da nayi ba. Hajiya hayaƙi ma ba sonsa kike yi na sani, Laure ko ina da tabbacin bata ma taɓa
ganin wiwi ba bare ta kai bakinta, yarinyar dake fama da kanta ma ina taga lokacin shan wiwi! Nayi imani
da Allah Aina'u ce tasha wiwin nan, kuma a yau ɗin nan kuma ba yanzu ba, sai ta bar gidan nan wallahi!"
Da ƙarfi Hajiya tace, "To kuwa za kayi kaffara don Aina'u babu inda za taje wallahi! Wiwi dai ni nasha gama
sauranta nan." Faɗin Hajiya ta hau waige-waigen inda zata hango saurin da Aina'u ta har a parlourn, da
sauri tace, "Yauwa gashi nan!" A tare suka kai jiki, ita ta kai hannu, shi kuma ya kai ƙafa ya take sauran
guntun wiwin don kada Hajiya ta kai hannu ta ɗauka. "Ai Hajiya da sauri kika yi kika rigasa ɗauka, kin ga
idan kika kunna kika yi zuƙa ɗaya a gabansa wata ƙila yafi gasgata maganarki." Wani irin shaƙa Khalil ya kai
mata tare da faɗin, "Hajiya zan kashe yarinyar nan sai dai nima a kashe ni." Da sauri Hajiya ta taso ta hau
kiciniyar kwace hannun Khalil a wuyan Aina'un da har idanunta sun soma firfitowa, "Wallahi idan baka saki
wuyar yarinyar nan ba zan tsine maka Ibrahim." Wani irin wurgi da ita yayi sai da kanta ya bugu da Centre
table ɗin dake ɗakin ji kake tatsatsatsatsa ya fashe, take jini ya hau tsartuwa a kan Aina'u wacce tuni ta
sulale ta sume, hannu Hajiya ta ɗaura a kai tare da faɗin, "La'ilaha illalah, Muhammadur Rasulullah
Sallallahu alaihi Wasallam, Khalilullah!" Da sauri Khalil ya bar ɗakin a zuciye, don shi ko a jikinsa duk da
uban jinin da yaga Aina'un na zubarwa. Daga nan fita yayi daga gidan gaba ɗaya domin cuku-cukun
passport ɗin Sarah. Hajiya kuwa gaba ɗaya ta ruɗe sai kiran sunan Khalil da ya jima da barin gidan take yi,
Laure dake zaune itama ko motsi bata yi ba, addu'a kawai take yi a zuciya Allah yasa daga suman da tayi ta
wuce barzahu kowa ya huta. Ruwa fridge Hajiya ta ɗauko ta fasa a fuskan Aina'un, a gigice ta farfaɗo tana
zazzaro idanu, can kuma ta tashi da sauri jini na ɗiga ta wuce ɗakin dake mallakinta ta rufo ƙofa, bata
damu da ciwon jikinta ba ta matsa tafin hannunta da ƙarfi sai ga Khalil ya bayyana a immigration office
suna magana da wani, wani irin zaro idanu tayi tare da faɗin, "Barin ƙasar? To ai sai kuyi tafiyar in gani duk
da kuwa na san idan asibitocin duniyar zaku zaga, Sarah baza ta taɓa samun lafiya ba." Tafin hannun ta
kuma matsawa, sai ga wannan mummunar halittar ya bayyana fuska a ɗaure tare da faɗin, "To uwar ƴan
ƙorafi, menene kuma yanzu?" Kallon gefe tayi tare da kai hannu ta ɗauki kwalbar turaren dake kan mirror
ta fasa sannan yanki hannunta na dama tare da tsiyaya jinin a fuskan wannan mummunar halittar sannan
ta ɗuka akan guiwowinta tare da faɗin, "Dan tsarkin tsafin _Hell Ofulafu_ ka taimakeni kamar yanda Khalil
ya zubar min da jini, ina so shima ya ɗanɗana ɗacin da naji wajen yin kuka da idanunsa, ina son a yau ayi
kukan mutuwa a cikin gidan nan, sannan a hana Khalil fita daga ƙasar nan da matarsa, bama ƙasar nan ba,
a kasar masa da tunanin nemawa matarsa magani ko da a wajen Kaduna ne!" Ta ƙarisa maganar ne tare da
tara kanta dake tsiyayar jini a tafin hannunta, yayin da mummunar halittar nan ya saka harshe yana lashe
duk wani jini dake ɗiga a jikinta. Sai da ya gama lashewa sannan ya shiga ɓaɓɓaka mahaukacin dariya tare
da turo hannu ya dafa kanta sannan ya ɓace. Lumshe idanu tayi tare da faɗawa bayi don ta san ɓacewar
yana nufin buƙatarta zai biya. Khalil yana tsaye yaji kamar an kwaɗa masa guduma akai yayi saurin dafe
kan tare da tsugunawa. "Lafiya Khalilullah?" Abokinsa yayi saurin ɗukawa tare da faɗin haka. Bai ce komai
ba, amma ya daɗe yana jin wani irin wuuuu a cikin kansa kamun ya miƙe ba tare da yace komai ba ya nufi
wajen motarsa, "Ibrahim! Ibrahim!!" Abokinsa yayi kiransa yana bin bayansa, amma ko sauraran bai yi ba
ya buɗe motarsa tare da shiga yaja ya bar wajen, sai da yayi nisa da immigration office ɗin sannan ya soma
jin wasai a cikin kansa. Aina'u kuwa canza kaya tayi tare da yiwa kanta dressing sannan ta kunna wiwi tasha
tare codine saboda zuciyarta da yayi zafi, sai da ta zuƙi wiwi ta fesar sannan tace, "Na rantse da girman
Yesu Almasihu, ba don tsananin son da nake maka ba, da wannan marin da fasa kan da kamin ba zai tafi a
banza. Da sai na kashe ka a yau ɗin nan, amma duk da haka, You'll pay for it!" Nafeesa na kitchen tana dafa
pasta, Qasim na parlour yana kallon Tv kwance akan resting chair dake parlourn yana jiranta ta kawo
abuncin, don tun da suka tashi basu ci komai ba, "Honey kin kusa?" Ya faɗi da ƙarfi ta yanda Nafeesan zata
ji daga kitchen ɗin, "Soon in Sha Allah!" Faɗin Nafeesa tana mai saka carot da ta gama wankewa, a gigice ta
saki ludayin dake hannuta tare da buɗe baki za tayi ihu, cak bakin ya tsaya a buɗe ba tare da ihun ya fito
ba, jininta babu inda baya rawa ga fitsarin tsoro dake zirarowo daga jikinta ganin halitta mafi muni a
gabanta, harce ya fiddo kamar na maciji ya caki wuyanta ya shiga tsotse jinin jikinta, sai da ya tsotse kaf
sannan ta faɗi ƙasa yaraf, shi kuma ya kai hannu ya cire pipe ɗin gas ɗin tare da haɗa gobara a kitchen ɗin
sannan ya ɓace ɓat. Da mugun gudu Qasim ya fito daga parlourn jin wani irin warin gas na bala'i, yana tura
ƙofar kitchen gas yayi wani irin uban tsalle ya bugi fuskansa, kan kace kwabo gaba ɗaya gidan ya kama da
wuta, gas ɗin nan kuwa haka ya dunga tsalle yana faɗawa gidan maƙota. Kasancewar layine na masu kuɗi,
tuni har a kira ƴan kwana-kwana na Private, kuma cikin ƙanƙanin lokaci suka iso suka fara aikinsu. Sai da
aka fara cire wutan unguwar gaba ɗaya sannan aka shiga kashe wutan, mutane goma sha shida ne suka yi
mummunar ƙonewa, daga ciki har da Qasim mijin Nafeesa, gaba ɗaya tun daga kai har tafin ƙafa ya ƙone,
ana taɓa jikinsa fata ke biyowa, Nafeesa kuwa tattare dagwargwajajen namanta aka yi, don wasu ma dun
manne a jikin tiles da wuƙa aka kankaro, babu abunda ke tashi unguwar sai koke-koken mutane. Ƴan uwan
Qasim kamar zasu haukace, wasu suka nufi asibitin da aka kai shi, wasu kuma suna tare da
dagwargwajajen naman Nafeesa, ya LTG Abdullah suka kira, sai dai number ɗinsa bai shiga don jiya ya bar
ƙasan zuwa China. Mayar da aƙalan kiran suka yi zuwa ya Abdul-Hakeem, shikuma ya kashe wayarsa gaba
ɗaya saboda tashin hankalin da yake ciki, Khalilullah da driving zai dawo gida wayarsa ta hau ringing, sai da
yayi parking saboda bai ɗaga kira idan yana driving sannan yayi picking, "Inna lillahi wa'inna ilaihir
raju'un!" Shine abunda ya dunga maimaitawa har ya sauke wayar a kunnansa, haɗa kai da steri yayi wasu
zafafan hawaye na zubo masa daga idanunsa, ya jima yana hawaye kamun yayiwa motar key ya nufi can
gidan Qasim ɗin. Tun daga nesa da layin yake hango hayaƙi da ƙauri duk da an samu nasarar kashe wutan,
parking yayi ya nufi inda ƴan uwan Qasim suke, maza huɗu ne da mata biyu, matan sai rusa kuka suke yi,
mazan kuma sunyi jigum-jigum suna kallon naman Nafeesa. Kai tsaye wajen dagwargwajajen naman yayi
tare da duƙawa yana kallo wasu maƙudan hawaye na zirarowa daga idanunsa, jikinsa har rawa yake yi
tsabar tashin hankali, "Allah ya jiƙanki Nafeesa, Allah yasa kina cikin rahamarsa, Annabi yasan da zuwanki."
Yana kawowa nan ya fashe da kuka tare da saka tafin hannunsa ya rufe fuskansa. Sai da Mukhtar wan
Qasim ya ɗagosa tare da janyesa gefe yana bubbuga kafaɗunsa alamar rarrashi. Haɗa kai da bango Khalil
yayi, hawaye sun kasa tsayuwa daga idanunsa, dakyar ya iya controlling kansa ya fiddo wayarsa daga aljihu
tare da dialing number ya Abdullah, wayar bai shiga, sai ya kira layin ya Abdul-Hakeem, shi kuma switchoff,
sai ya mayar da akalar kiran zuwa layin uncle Ameeru, bigu biyu ya ɗaga tare da faɗin, "Tunda naga kiranka
nasan ba alkhairi zaka faɗa min ba, don haka nan baka kira ka gaishe mu, balle kuma yanzu da kayi aure
kana ganin kanmu ɗaya!" "Allah yayiwa Nafeesa rasuwa ta hanyar gobara, yanzu haka ina can gidanta!"
Shine abunda Khalil ya faɗi tare da yanke kiran ba tare da ya bari uncle Ameeru ya dire salatin da ya ɗauko
ba. Uncle Ameeru a gigice ya kira sauran ƴan uwansa a waya ya shaida masu, nan da nan suka haɗu suka
yo gida wajen Hajiya maimakon su wuce can gidan Nafeesan kai tsaye, Hajiya najin sautikan muryansu
yayin tahowarsu taji gabanta ya faɗi don ta san zuwansu ba alkhairi bane, ɗayan biyu ne, ko sun zo neman
kuɗi ko kuma tijarar da suka saba yi mata. Babu sallama suka faɗa ɗakin kasancewar ƙofar buɗe take don
Hajiya bata kulle ƙofa idan dai ba dare bane. "Bilkisu ashe abunda ya faru kenan? Allah ya jiƙan Nafeesa,
oh! Yaushe-yaushe ƴarta ta koma, ashe itama tana tafe." Da sauri Hajiya ta miƙe tana faɗin, "Ban gane ba
mai kuke faɗi ba. Nafeesar ce ta mutu? Nafeesa tawa?" Kallon-kallo aka shiga yi tsakanin su uncle Ameeru,
don sun ɗauka ta san da mutuwar, Uncle Shamsu yace, "Kenan baki sani ba, ɗazun nan Khalil ya kira
Ameeru yake faɗa masa gobara ta kama a gidan duk sun mutu har da mijin." Hannu Hajiya ta ɗaura akai
tare da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Sau uku sannan ta faɗi ƙasa sumamma. Laure a sittin ta
fita ta nufi side ɗin aunty Maryam ta shiga bugawa da ƙarfi, ya Abdul-Hakeem na fitowa ta kamo hannunsa
ta dunga jansa har ɗakin Hajiya, da sauri ya nufi Hajiya yana jijjigata tare da tambayar mai ya faru da ita,
uncle Ameeru ne ya shaida masa abunda ke faruwa, a gigice ya soma karanto Inna lillahi wa'inna ilaihir
raju'un, can kuma ya cicciɓi Hajiyar zuwa mota ya fita daga gidan zuwa asibiti shi da Laure, su uncle
Ameeru kuma suka wuce gidan Nafeesan. A can Asibiti kuwa, jinin Hajiya yayi mugun hawa, ya Abdul-
Hakeem bai bar asibitin ba sai da Hajiya ta farfaɗo aka saka mata drip da kuma alluran bacci, bai samu
sallar gawa ba, domin yayyafawa naman ruwa kawai aka yi saboda yanda tayi dagwargwaje, Khalil ne yace
ba sai Hajiya ta ganta ba, don ganin naman Nafeesa zai iya jefata cikin mummunar hali, ko shi da yake
namiji kuma doctor ba ƙaramin tashin hankali yake ciki ba. Suna dawowa daga maƙabarta da ya halartu
mutane da yawa, don maza da matan unguwan kowa sai bada shaidar alkhairin Nafeesa yake yi. Sosai ta
samu shaida mai kyau daga ƴan unguwa da dangin mijinta, don surukarta har yanzu bata cikin hayyacinta,
wani mugun tashin hankalin suka kuma taraswa, gawar Qasim mijin Nafeesa aka dawo da ita shima ya
amsa kiran Ubangiji domin ba ƙaramin ƙuna yayi ba, ya riga ya dahu sosai. Khalil dai ba ƙaramin tashin
hankali suka gani ba a ranar, yayi wani irin zuru-zuru kamar wanda ya shekara yana ciwo. Haka suka kuma
yiwa Qasim sallah bayan an yayyafa masa ruwa, don shima namar jikinsa sai zagwanyewa yake yi, bayan
sun kai shi makwancinsa sun dawo, sai suka shiga gidansu Qasim ɗin aka yiwa juna gaisuwar mutuwa
sannan shi da Laure da ya Abdul-Hakeem suka wuce asibiti wajen Hajiya duk da ƙanwarta Aunty ya Gana
da Aunty Yaana suna tare da ita. Gaba ɗaya duk wanda ka kalla tsakanin ya Abdul-Hakeem da Khalil ba
wanda bai zama abun tausayi ba. Hajiya kuwa ta farfaɗo amma ko iya ɗago idanu bata yi, harshenta ma
har so yayi ya soma karyewa! Khalil kallo ɗaya yayiwa Hajiyar yaji hawaye sun taru a idanunsa, da sauri
yaju ya bar ɗakin. Aunty Yaana da yare tayi wa Laure magana akan ta zauna ta tsaya a tsaye kamar sanda.
Zama tayi tana kallon Hajiya hawaye na zuba a idanunta. Hannuta Hajiya ta kamo tare da faɗin, "Laure da
gaske Nafeesa ta mutu? Da gaske babu auta Laure?" Sunkuyar da kai Laure tayi tana hawaye, Aunty Yagana
tace, "Haba ya Bilki, kullu nafsin za'ikatul maut! Ki daina saka damuwa aranki, Allah ya fiki son Nafeesa, na
san abun da zafi, amma daurewa za kiyi, addu'ar ki kawai Nafeesa take bukata matsayin ki na uwa. Bp ɗinki
ya hau sosai, idan kina wannan kukan da damuwa ba zai taɓa sauka ba. Dan Allah ya Bilki, kiyi haƙuri ki
sakawa zuciyarki haƙurin rashi." Duk cikin yaren Kanuri tayi mata maganar. Sai kuma ta kalli Laure tare da
faɗin, "Je kira Khalil yazo yayi mata allurar bacci!" Da sauri Hajiya ta ɗaga hannu alamar bata so tare da
danƙe hannun Laure da ɗayan hannunta. Sarah ba ƙaramin wahala taci ba, ga yunwar dake nuƙurƙusan
cikinta amma ko motsi ta kasa, ji take kamar ana hura wuta a jikinta saboda wani irin azabar zafi da take ji,
ta kai gudun ac ɗin ɗakin gaba ɗaya amma bata daina jin zafin ba, ta haɗa da warware fanka zuwa number
ɗin ƙarshe nan ma kamar ƙara hura wutar jikinta ake yi. Ta cire kayan jikinta gaba ɗaya ya rage daga ita sai
bra da pampers ɗin da Khalil ya saka mata nan ma dai bata ji wani salama ba, daga ƙarshe sai da ta cire
komai na jikinta ta kwanta flat a ƙasan tiles amma still babu wani salama sai ma ƙaruwa da zafin yake yi ga
kuma fitsarin da ya zama mara control yana zubo mata, don bata sanin lokacin da take jinsa, zubowarsa
kawai take ji, tsutsotsin nan kuwa sun yi faca-faca a tsakar ɗakin. Da kyar ta rarrafa ta faɗa bayi ta dunga
kwarawa kanta ruwa a jiki, amma da ruwan ya sauka a jikinta sai taji kamar tafasasshen ruwan zafi ta
kwarawa jikinta. Fitowa tayi daga bayin ta zauna daɓar a ƙasa tare da fashewa da kuka tana sosa jikinta
saboda wani mahaukacin ƙaiƙayi da ta soma ji kamar an watsa mata karara. Khalil bashi ya shigo gidan ba
sai gab magrib gabansa na faɗuwa saboda bai ƙaunar yaga Sarah cikin wani hali gashi ya barta ita kaɗai
kuma ya san mahaukaciyar ƙanwarta ba zuwa dubata za tayi ba. Ɗauke numfashi yayi jin wani uban ƙarni,
zarni, hamami, ɗoyi da warin da saman gaba ɗaya ya ɗauka. Haka ya daure ya ƙarisa don yasan shi ɗinne
dai, idan bashi ba babu mai iya jurewa, yana tura ƙofar ɗakin Sarah na sakin wani mahaukacin gyatsa mai
tafe da lafiyayyar tusa mai warin fitar hayyaci, tuni ɗakin yayi wani irin duum akan wanda yake yi. Cikin
sauri ya nufeta ganinta tsirara kuma kwance a ƙasa tana susan jiki, "Mine Lafiya, mai ya faru dake!" Da
hannu bibbiyu ta soma turesa tana faɗin, "Ka bar nan wajen, wari kake yi, warin jikinka zai kashe ni, ka
tashi ka fita nace!" Da mamaki Khalil ya hau shinshina jikinsa yana kallon Sarah, sai kuma yace, "Ɗakin ne
ke wari, bari na gyara miki jikinki na gyara ɗakin zaki daina ji." Faɗin Khalil, Aina'u daka ɗakin Hajiya tana
kallon komai cikin tafin hannunta ta ɗaura ƙafa ɗaya akan ɗaya tana ɓaɓɓaka mahaukacin dariya. Sarah
kuwa duka ta shiga kai masa ta ko ina a jikinsa tana faɗin, "Ka fita nace, wari kake yi, kai abun kyama ne. Ka
fita kabar ɗakin nan." Hannunta ya riƙo biyu tare da faɗin, "Naji zan fita, amma bari na gyara maki ɗakin
tukun da jikinki." Ta jin haka sai tayi wuf ta miƙe ta shiga jifansa da duk abunda taci karo dashi a ɗakin har
tayi sanadin fashe masa goshi. Fita yayi daga ɗakin yana mai matsanaicin jin tausayinta, ya bar gaba ɗaya
abunda tayi masa yanzu matsayin depression ne ya kamata saboda halin da take ciki shi yasa take acting
haka. Ɗakinsa ya koma yayiwa kansa dressing a goshi lokacin ana kwaɗa kiran sallah sai yayi alwala tare da
wucewa masallaci. Sarah kuwa tun sanda aka soma kwaɗa kiran sallah sai taji gaba ɗaya zafin da take ji a
jikinta ya kau, sai wani nannauyen bacci yayi gaba da ita. Lokacin da Khalil ya dawo daga masallaci, haka
kawai ya yaji yana buƙatar jin karatun Alkur'ani, sai ya kunna ƙira'ar minshawi ya saka wayar a gaban
aljihusa, kai tsaye ɗakin Sarah ya nufa, kwance ya sameta a ƙasa, a hankali ya tura ƙofar ya shiga, bai taɓa
ta ba sai da ya gyara ɗakin tsaf sannan ya ajiye wayarsa da har a lokacin tana karatun ya cicciɓi Sarah yayi
bayi da ita, daga can ɗakin hajiya kuwa, tun da Khalil ya kunna karatun nan ta daina ganinsa a tafin
hannunta. Sarah na jinta a hannun Khalil ta buɗe idanunta da sauri tare da zabura, sai kuma ta mayar da
idanu ta rufe, wanka yayi mata sannan ya saka ta ɗaura alwala sannan suka fito ya taimaka mata wajen
saka pampers ya fiddo mata da kaya marasa nauyi ta saka ya bata hijjab ta tada sallah. Bata ƙara jin warin
da Khalil ke yi mata ba saboda karatun da ya kunna, shima kuma bai ji mahaukacin warin ba, sai ya ɗauka
saboda ya gyara ɗakin ne. Shi ya dafa masu indomie da kwai, sai da yaga ta ƙoshi tukun ya daina bata, sai
taga ya jingina da gado yayi shuru, rai babu daɗi ta kallesa tare da faɗin, "Happiness, mai ke damunka?"
Murmushin yaƙe yayi mata don bai ji zai iya faɗa mata Nafeesa ta rasu kuma Hajiya na kwance a asibiti ba,
"Ina tunanin ki ne, Mine. Allah ya baki lafiya kinji!" Ya ƙarisa maganar yana kallonsa. Kallon indomie ɗin da
tashi ta rage tayi tare da ƙarisowa wajensa ta saka hannu cikin plate ɗin ta dunga ɗebowa tana saka mashi
a baki, ba daɗin indomie ɗin yake ji ba ko kaɗan, amma saboda bai son sosa mata rai sai yayi ta amsa har
ya cinye. Kwanciya tayi a jikinsa tare da faɗin, "In Sha Allah zan warke" Ga mamakinta sai taji saukar
hawayensa akan kafaɗanta, da sauri ta kallesa daidai lokacin da wayarsa ya hau ringing ɗin wakar _I miss
You like crazy_, wani irin mahaukacin ihuu Sarah ta saki tare da toshe hancinta tana nuna masa waje
alamar ya fita, da ɗumbin mamaki yake kallonta ita kuwa sai turashi take yi tana faɗin, "Fita nace! Fita daga
ɗakin nan wari kake yi Ibrahim!!" Miƙewa yayi itama ta miƙe ta dunga turashi har waje sannan ta jawo
ƙofar ɗakin ta rufe tare da zamewa jikin ƙofar ta soma wani irin kukan fitar hayyaci, har cikin zuciyarta bata
jin daɗin abunda take masa, amma bata san mai yasa take jin wannan warin da ko ta ƙudurtawa zuciyarta
zata jure sai ta kasa. Khalil ya jima a ƙofar yana mamaki, can kuma ya juya ya koma ɗakinsa. Wani irin
tsallen murna Aina'u tayi daga ɗaki don tana ganin komai tun lokacin da karatun nan ya tsaya. Haka suka
kwashi kwana goma suna yi, da ya shiga ɗakin domin gyarata zata hau ihu tana faɗin ya fita wari yake yi,
tana kuma turashi da ƙarfi. Wani lokacin ƙarfi yake saka mata ya gyara mata jikinta da ɗakin sai ya ajiye
mata abinci ya fita. Wani lokacin kuma sai ya bari sai tayi bacci sai ya shigo ya gyara ko ina don tana iya
gyara jikinta ta canza pampers, zarnin fitsari da ƙarni da warin tsutsotsin naso ya kashe ɗakin don bata bari
Khalil ɗin yayi abunda ya kamata. Kwanan Hajiya ashirin da uku aka sallamota, tunda suke asibitin ko sau
ɗaya Laure bata taɓa sha'awar dawowa gidan ba, haka Aina'u bata taɓa taka ƙafarta taje asibitin ba.
Ɓangaren Sarah sai abunda yayi gaba wajen kyaran Khalil, shi kuwa ko afuska bai taɓa nuna ɓarin rai ko
ƙosawa da ita ba, sai ma wani irin nunkular kulawa da ya ƙara bata don duk tunaninsa depression ke
damunta. Kamar daga sama sai ga Muneeba a gidan Sarah, sosai Khalil yayi murnar ganinta, har bedroom
ɗin Sarah ya kaita, kuma a gaban idanun Muneeban ta yiwa Khalil ɗin koran kare, bayan fitarsa Muneeba
ta hau Sarah da faɗa kamar ta ari baki, sai kawai Sarah ta fashe da kuka tare da faɗin, "To ni ya zanyi
Muneeba, ina zan saka kaina! Ciwo duk yabi ya dame ni, tsutsotsi a gabana, wari da ƙarni gami da hamami
a ɗakina. Mijina kuma duk lokacin da ya kusanto ni, wani irin ƙarni da hamami yake min!" Da idanu kawai
Muneeba take bin Sarah, can kuma sai tace, "Sarah! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!! Wani irin abu nake
ji haka? Shin baba da Lami sun san wannan zancen kuwa? Ai wannan ba cutar da za ayi shuru da baki
bane, dole iyaye suji don cutarki bai yi kala da cutar asibiti ba. Bari ki gani ina zuwa.." Tana gama faɗin haka
ta mike tare da ɗaukar jakarta domin zuwa gida ta faɗawa mahaifiyarta abunda ake ciki domin tayiwa
babanta magana ayi mata treatment na Islamic. Sai dai miƙewarta yayi dai-dai da miƙewar Aina'u da sauri
tare da fitowa ta tsaya bakin gate, Muneeba na fito ta soma tafiya da sauri, sai kawai ji tayi an juyo da ita
da auri tare da taɓa goshinta, "Ki kalli gabas kiyi ta tafiya kar ki ƙara waiwayar nan gidan!" Gyaɗa kai
Muneeba tayi tare da kallon gabas ta hau tafiya ba tare da sanin inda ta nufa ba. Wani irin dariya Aina'u ta
sheƙe dashi tare da faɗin, "Babu mai ja dani ya zauna lafiya, Khalil nawa ne ni ɗaya, don ni aka halicce shi,
duk wacce tayi ƙoƙarin rabani dashi sai na ɗanɗana mata azaba, haka duk wacce tayi ƙoƙarin ceton Sarah
sai na wulaƙanta rayuwarta!" Tana gama faɗin haka ta juyo ta dawo cikin gida. Cikin Sarah ya shiga na wata
bakwai, still babu abunda ya canza, haka kuma Khalil shima bai taɓa canza mata ba. Aina'u ta kai maƙurar
ɓacin rai ganin babu wani canji daga Khalil, sai kawai ta hau shirin tafiya Abia domin samun _Hell Ofulafu_
gaba da gaba domin tayi mai kankat.. Ranar wata asabar ta tafi, wannan karan ma Ugo ne yayi mata jagora
bayan sun gama watsewarsu. Ba ƙaramin tsafi Hell yayi mata ba wannan karan, sannan sai da tayi masa
alƙawarin jinin mutane goma, biyar jarirai, biyar kuma waɗanda suka soma tadawa ƴan shekaru uku zuwa
goma. Sannan ya bata wani kwaɗo ƙarami yace ta haɗiye, idan har ta haɗiye duk wanda ta kalla tace yayi
wani abu babu musu sai yayi, sannan kuma idan har tana son asirin da za ayiwa Khalil ya kama shi, sai ta
kwanta da mahaifinta. "Idan har buƙatata zata biya ko Sarkin maka kace na kwanta dashi zan kwanta
dashi." Shine abunda Aina'u tace. Kwananta uku a Abia ta juyo ta dawo Kaduna, bata sauka a ko ina ba sai
gida lokacin ƙarfe biyu na dare. Banƙare ƙofar gidan tayi sannan ta shiga, ɗakin baba ta nufa kai tsaye tare
da tura ƙofar ta shiga don shi bai saka sakata a ɗaki. A Zaune ta samu baban don tun lokacin da ta tura
ƙofar gida ya farka, hannu ta kai ta kunna switch ɗin ɗakin tare da yin wani irin tsayuwan karuwai tana
mitsi-mitsin da idanu, shi kuwa baba sai yaga gama ɗaya suffarta ta koma ta Lami sak lokacin da take
amarya. Wani irin mugun sha'awa ce ta shiga fuzgar baba har bai san lokacin da ya miƙa mata hannu tare
da faɗin, " _Elizabeth_" ba. Aina'u kuwa wani murmushi ta saki tare da kashe wutan ta nufe shi gadan-
gadan. Cike da rashin imani Aina'u ta bari mahaifin da yayi sanadin kawota duniya ya kusanceta. Sai bayan
komai ya nutsa baba ya sauko daga kan gadon a gigice ya kunna wuta, arba yayi da fuskar ƴarsa kuma
autarsu tana saka brezia, hannu ya kai ya dafe saitin ƙirjinsa tare da soma nunata da hannu yana son yin
magana amma bakinsa ya karkace. Take ya yanke jiki ya faɗi ƙasa rabin jikinsa gaba ɗaya ya mutu. Aina'u
kuwa tana gama saka kaya ta tsallakesa ta bar ɗakin ta koma ɗakinsu. Da sassafe kamun kowa ya tashi ta
bar gidan ta nufi gidansu Khalil. Sarah kuwa tun asuba ta soma jin wani irin mahaukacin ciwon mara
wanda bai misaltuwa don naƙuda ta soma yi gadan-gadan duk da kuwa lokacin haihuwarta bai yi ba don
cikin watansa bakwai, itace har safiya tana abu ɗaya, idan ta kai hannu gabanta tana jin gashi, amma
haihuwa taƙi zuwa sai nuƙurƙusan azaba take yi. Aina'u na fitowa daga gida ta shafa tafin hannunta sai ga
Sarah ta bayyana cikin halin naƙuda. Wani irin nishine ya taho mata, cikin sauri Aina'u ta haɗe yatsanta
biyu ta kame gam, sai Sarah taji kamar an saka igiya an shaƙe wuyarta ga kuma kan ɗa daya soma
turowa............

( _Anya Aina'u ƴar Adam ce kuwa_? 😭)


*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_MATAR SAYYADEE_*

*Paid book 08128755583*


[14/10, 7:45 PM] Matar Sayyadee: Numfashinta ne ya soma ɗauke, idanuwanta kuma suka soma rufewa
ga wani irin azababbiyar azabar da take ji a ƙasanta. Hannu ta kai ƙasanta ta kuma taɓo gashin kan babynta
daya soma turowa, wani irin ƙarfine ya kuma zuwa mata, da ƙarfi ta furta, "La'ilaha illalah Muhammadur
Rasulullah, Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Take taji kamar hannun da ya shaƙi wuyarta an janye shi da
ƙarfi, a wani irin nishi tayi mai ƙarfi daidai lokacin da Khalil ya turo ƙofar, da gudu ya ƙarisa tare da taro
babyn da yayi fut ya fito, idanunta ne ya soma rufewa kuma ga wani kan babyn na ƙoƙarin fitowa amma
kuma ƙarfinta ya soma ƙarewa saboda wahalar da tasha, cinyarta ya soma bugu bayan ya ajiye jaririn dake
tsandara kuka akan gado, cicibarta yayi ya kwantar akan resting chair ɗin dake ɗakin ya soma ƙoƙarin
cetonta, da taimakonsa Sarah ta kuma sunkuto ɗayan jaririn, yana fitowa ita kuwa ta sume. Rasa inda zai
saka kansa yayi, sai ya mance gaba ɗaya taimakon da zai yi mata, da sauri ya fita daga ɗakin ya koma nashi
ɗakin ya dawo hannunsa ɗauke da sabuwar reza ya yanke cibin yaran, basu da muguwar ƙanƙanta kamar
ba bakwainiba, kuma dukansu maza kamar Khalil ɗin yayi kaki. Ruwa ya shafawa Sarah a fuskanta yana
goga tafin ƙafarta har ta farfaɗo, rungumeta yayi tare da faɗin, "Kin gama min komai Sarah, thank you,
thank you Soo much mine, mai kike so a duniyar nan inyi maki shi yanzu nan?" Murmushi tayi tare da
faɗin, "Ka cigaba da sona har bayan raina, kar ka juya min baya a kowani irin hali!" Ta ƙarisa maganar tana
mai shafa fuskansa. Hannu ya kama yayi kissing sannan yace, "Kin riga kin daɗe da samun wannan Sarah,
Khalil naki ne ke ɗaya har abada. Tashi mu tafi asibiti a duba min ke." Aina'u gudu take yi akan titi kamar
mahaukaciya domin Sarah na fara salati hotonta ya ɓace a tafin hannunta na _Hell Ofulafu_ da wannan
mummunar halittar ya bayyana gaba ɗaya fuskansu ɓutu-ɓutu, mummunar halittar nan ya soma magana
da ƙarfi, "Kar ki kuskura ki bari a fita da jariran nan daga gidan nan, idan ba haka ba zaki fuskanci hukunci
har na tsawon shekara ɗaya, Hell ba zai ƙara amsa buƙatunki ba, don idan har suka bar gidan, jinin jariran
bazai shawu ma Hell ba, kasancewar sun shaƙi iskar waje." Yana gama faɗin haka suka ɓace ita kuma ta
hau buga uban sauri, cikin ikon ubangiji duk keken da ta tsayar sai yace mata ba zai je unguwar ba. Kawai
sai ta hau gudu kamar mahaukaciya a kan titi. Khalil fita yayi ya nufi ɗakin Hajiya jikinsa har rawa yake yi
tsabar murna, murɗa handle ɗin yayi don ƙofar a rufe take, tun da Aina'u ta nufi Abi, Hajiya ta tsiri rufe
shashinta, shiga yayi amma babu kowa a parlour, kai tsaye ɗakin hajiyan ya nufa, zaune ya same su ita da
Laure sun yi jigum-jigum. "Hajiya Sarah ta sauka! Kin samu mazaje har biyu!" Out of excitement ya faɗi.
Hajiya ta mance rabon da tayi murna a rayuwarta irin yau, Laure kuwa kuka ta fashe dashi tare da fita da
gudu ta nufi part ɗin Khalil ɗin, so take tayi magana ta nunawa Khalil irin farin cikin da take ciki, amma
kuma babu bakin maganar, Hajiya Kuma ƙasa ta nufa tare da yin sujada sannan ta ɗago tare da fashewa da
kuka tana faɗin, "Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Allah ubangiji ya raya bisa sunnar ma'aiki ya kuma karesu
daga dukkan sharrin mutum da aljan. Muje Mu'azzam inga jikokin nawa!" Ta ƙarisa maganar tana mai
share hawaye. "Hajiya ai ɗauki hijjab ɗinki kawai don daga nan asibiti muka yi. Yaran da uwar suna buƙatar
kulawar likitoci." Juyawa Hajiya tayi ta ɗauki hijjab har da na Laure sannan tabi bayan Khalil, a can ɗaki
kuwa, Laure har ta soma gyara jinin Sarah da ya lalata ɗakin, abun mamaki kuma babu tsutsa ko ɗaya.
Hajiya ɗaukar ƴaƴan tayi duka biyun ta rungume a jikinta tana jin wani irin ƙaunarsu na ratsa jikinta,
"Sannu kinji, Allah yayi maki albarka uwata, sannu da ƙoƙari." Murmushi kawai Sarah tayi tare da sunkuyar
da kai ƙasa. "Ɗauko mata mayafinta mu wuce asibitin." Faɗin Hajiya tana kallon Khalil ɗin, da sauri ya
ɗauko hijjab a cikin wardrobe ya saka mata tare da miƙar da ita tsaye sannan ya ɗauko silipas ya saka mata.
Sai da Hajiya ta saka masu kayan sanyi sannan ta miƙawa Khalil Hassan yayi masa kiran sallah a kunna tare
da yi masa huɗuba da sunansa, (Ibrahim Khalil) Hussaini kuma ya saka masa sunan mahaifin Sarah (Nuhu).
Hajiya riƙe da Hassan, Laure kuma ɗauke da Hussain suka fita daga ɗakin, Khalil ya kama hannun Sarah
suka sauka ƙasa tare da fita daga ɗakin gaba ɗaya suka nufi parking space. A gidan baya ta zauna ita da
Hajiya, shi kuma da Laure a gaba, kamar ance ya kalli ƙasa, sai ya hango kwalin _Mastika gum_ a ƙasa, da
sauri ya kai hannu ya ɗauko tare da ɓare kwalin ya ɗau ɗaya ya jefa a baki yana murmushi don har ya
manta rabon daya kai chewing gum bakinsa. Suna fita daga gidan keke napep ɗin da Aina'u ke ciki ya tsaya,
zuciyarta sai da tayi wani irin tsalle ganin motar Khalil ya fito daga cikin gida, ko kamun ta yunkura motar
Khalil ta kusa bakin titi don gidan yana gaba da titi ne. Haɗa kai tayi da guiwa tare da fashewa da kukan
baƙin ciki. Juyowa mai napep ɗin yayi tare da faɗin, "Lafiya baiwar Allah?" Ba tare da tace komai ba ta fito
daga napep ɗin saboda tsabar rashin imani ta bugi goshinsa da tafin hannunta tare da faɗin, " _Hell_ ga
jinin wannan matsayin sassaucin hukuncinka gareni." Da sauri mai napep ɗin nan yaja kekensa ya bar layin
don ya tsorata da abinda Aina'u tace, sai dai yana zuwa titin bypass, trailer tabi ta kansa. Aina'u kuwa shiga
cikin gidan tayi rai a mugun ɓace ta nufi side ɗin Hajiya. A can asibiti kuwa, jariran a incubator aka saka su
sannan itama uwar aka shiga kula da jikinta, sai dai aka mata ɗinki uku sannan aka saka mata ƙarin ruwa
domin taji ƙarfin jikinta. Hajiya kuwa ta ɗauki waya ta dunga kiran dangi da abokan arziki tana shaida masu
matar Khalil ta samu ƙaruwan ƴan biyu. Khalil kuwa bayan Sarah ta samu barci, sai ya sulale ya fita domin
zuwa can gidansu Sarah ya shaida masu Sarah ta haihu. Wajajen ƙarfe goman Safiya, gaba ɗaya suna zaune
tsakar gida suna karyawa, Na'ima ta kalli Lami tare da faɗin, "Lami baza ki duba baba? Tun safe ban ni
ɗuriyarsa ba, ko wa'azin da ya saba kunnawa banji ya kunna ba." Taɓe baki tayi tare da faɗin, "Yesu ne yayi
min maganinsa! Ai ba ƙaramin addu'a nake yi ba akan Nuhu ya daina kashe mana kunne da wannan karatu
da wa'azin nan da yake saka mana ba, har fata nake Allah yasa Tv ɗin ya lalace ko kuma ya faɗo daga
saman ya fashe." Miƙewa Na'ima tayi tare da nufa ɗakin baban ta ɗaga labule, wani irin ihuu ta saka tare
da faɗin, "Baba ya mutu mun shiga uku!" Ai a sittin daga Lamin har sauran suka nufo ɗakin don ganin halin
da yake ciki. Gashi nan dai kamar me rai kamar kuma gawa! Baki a karkace, hannu a lankwashe, ƙafa ɗaya
da hannu a shanye. "Yes......" Da ƙarfi Hassana tace, "Dalla Lami ki rufe mana baki, baba na cikin wannan
halin shine kike ƙoƙarin kira mana Yesu, Allah dai ya tsinewa wannan addini da kika koma!" Da sauri Lami
tace, "Zan ci ubanki idan kika zagi addinina, ai gwara ni kowa yasan ba addinin sallah nake yi ba, kuma duk
Sunday sai naje Church, ku Kuma fa? Sai dai kullum ayi ta faɗi a baki mu musulmai ne, amma ko sau ɗaya
ba'a yin sallar!" A fusace Marfu'a tace, "Dan Allah Lami ku bar wannan maganar aji da lafiyar baba." Daidai
nan suka jiyo sallamar Khalil a ƙofar gida don tun yana hanya yake kiran layin baba amma ba'a ɗagawa
kasancewar bargo ya rufe wayar shiyasa su Aina'u basu ji ringing ɗin ba. "Kamar muryan mijin Sarah!"
Faɗin Na'ima tare da fitowa daga ɗakin ta nufi kwar gida, "Alhamdulillah!" Faɗin Na'ima bayan taga Khalil
ɗin tsaye a ƙofar gida, "Shigo Khalil, Allah ne ya turo mana kai wallahi. Babane babu lafiya yana can kwance
gaba ɗaya rabin jikinsa ya shanye." Da sauri yace, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Tare da gitta Na'iman
ya wuce ciki da sauri. Hassana da Marfu'a sai sharan hawaye suke yi ganin kamar babu rai a jikin baban,
suna ganin Khalil suka matsa suka bashi hanya. Cicciɓan baba yayi tare da fito dashi daga ɗakin ya nufi
mota, gaba ɗaya suka rufa masa baya har da Lami wacce ko arzikin mayafi babu a jikinta, hatta su Na'iman
ma babu mayafin a jikinsu. Lami, baba Hassana da Marfu'a a baya, Na'ima kuma ta zauna gaba ita da
Nuratu. Sai da suka hau titi sannan Khalil ya ɗan juyo ya kalli Lami tare da faɗin, "Mama, Sarah ta sauka, ta
samu ƴan biyu duk maza yau da safe, dan girman Allah kar a faɗa mata halin da baba yake ciki don itama
tana can asibitin ita da yaran don an saka su a kwalba ne kasancewar basu isa watannin haihuwa ba." Gaba
ɗayansu cike da mamaki da kuma farin ciki suka furta, "Ƴan biyu! Inna lillahi, Hassana ashe Sarah ce zata
riga ki." Na'ima ta ƙarisa da faɗin haka, Lami kuwa cewa tayi, "Yesu Almasihu nagode maka da wannan
kyauta da kai min, a lokacin da ka kwace lafiyan mijina, sai kayi min kyauta da jika har biyu." Tana gama
faɗin haka sai ta hau waƙa, " _Yayi! Yayi!! Yesu yayi!!! Yayi, yayi...._" "Ke dallah Lami ana jimamin halin
baba kin zo kin wani dame mu da zancen banza! Yesun me? Mu Allah ne zai cecemu ba wani yesunki ba!"
Faɗin Marfu'a dake kusa da ita. Lami kuwa sai da ta saka bayan hannu ta bugi Marfu'an sannan tace, " _Ya
Allah mai-iko duka, Uban Ubangijinmu Isa Almasihu, wanda ba ya son mutuwar mai-zunubi ba, amma ya fi
son shi juyo ga barin muguntassa, shi kuma yi rai; Ya bada iko da umurni ga masu-bautansa su furta, su fadi
kuma ga mutanensa da su ke tuba da neman gafarar zunubansu. Allah ke gafartawa, yana kwancewa
dukan masu-tuba da gaskiya, masu-bada gaskiya ga bisharassa mai-tsarki ba da munafunchi ba. Domin mu
roke shi, shi ba mu tuba mai-gaskiya, da Ruhunsa Mai-tsarki, domin abubuwan da mu ke yi yanzu su
gamshe shi; kuma sauran ranmu da ke nan gaba shiyi tsabta da tsarki, domin hakkanan a-karewa mu zo
chikkin farin cikinsa na har abada, ta wurin Isa Almasihu Ubangijinmu. Ubangiji kar kayi duba ga saɓon
yarinyata, ka yafe mata a cikin yafiyarka mai girma! Ka juyo da hankali da tunaninta ta gane gaskiya a cikin
addinin ka ya Yesu Almasihu! Mijina kuma ka bashi lafiya da juriya duk da ya ɓace daga gaskiya, kar kayi
duba da laifinsa, ka samu a cikin aljanna gaba ɗaya, Amin._" Wani irin dariya ne ya kusa kufcewa Khalil jin
yanda surukar tasa ta dage da iya ƙarfinta tana addu'arsu ta kirista, gefe guda kuma yana jimamin rashin
hankali irin na ƴan uwan matan nasa. "Ubangiji ba ya kare mu da komawa addininki Lami! Duk da nasan ba
kullum nake sallah ba, amma bana fatan in mutu a cikin addinin Kirista, ai na taɓa jin wani wa'azi akan duk
wanda yace La'ilaha illalah Muhammadur Rasulullah Sallallahu alaihi, ba zai taɓa dauwama a wuta ba, so
ina da hope ɗin zan shiga ko da kuwa wuta na fara shiga." Faɗin Marfu'a, da sauri Khalil ya juyo kuma
hakan yayi daidai da wani uban burki da ya taka duk sai da suka tsorata, "Ke wacce irin jahila ce? Kina
hauka ne? Kin san mecece wutar ubangiji kuwa? Ƙarya kike yi wallahi, baza ki taɓa iya jurewa azabar Allah
ba, kar ki kuskura ki ƙara faɗin wannan kalmar, kiyi fatan ko hucin wuta kada Allah yasa kiji bare ki shiga ko
da kuwa na daƙiƙa ɗaya ne! Wai tsaya, dukan ku kun taɓa zaman aji na islamiyya kuwa?" Girgiza kai suka yi
gaba ɗaya. Dogon tsaki Khalil yaja tare da faɗin, "Akwai babban matsala!" Yana gama faɗin haka ya kunna
motar tare da cigaba da tafiya ransa a ɓace. Har suka isa asibitinsa babu wanda ya ƙara ko tari, nan da nan
aka shiga da baba emergency, sakamakon gwaje-gwajen da akai masa ya nuna jininsa yayi mugun hawa,
wanda hakan yayi sanadin faɗuwarsa har ya samu mutuwar ɓarin jiki, ga kuma ciwon zuciya da ya kai
matakin stage C. Sosai Khalil ya girgiza da ganin haka, abunda ya kawo ransa shine halin da ƴaƴansa da
kuma matarsa ya kaisa wannan stage ɗin saboda tara abu a zuciya. Aina'u na shiga ɗaki ta soma jin wani
irin kuuwa a kunnanta har sai da ta saka hannu biyu ta toshe kunnan tare da durƙushewa a ƙasa, can ta
soma ji ana ɓarke kayan jikinta, sai da aka mata tsirara sannan aka kwara mata wani irin balaƴenƴen ruwan
sayi mai ƙanƙara-ƙanƙara a jiki sannan aka shiga zubaba mata bulalan doki a jikin, yanda ƙaran dukan ke
fita zaka fahimci ba wai mutum ko aljani ɗaya bane ke dukan, da wannan yace waaap, sai wannan yace
shauuuu! Ba ƙaramin duka taci ba, don tun da ta shiga ciki ake dukanta har wajajan goman Safiya, ta suma
yafi sau a ƙirga, gaba ɗaya jikini yayi ruɗu-ruɗu, sannan kuma aka shafe jikin da gishiri da yaji. Tsabar azaba
Aina'u zawo ta dunga saki a kwance a ƙasan tiles. A can asibiti kuwa, duk wanda ya kalli yanda baba ya
koma lokaci guda sai ka tausaya masa, ido ya juye, hannun da ƙafa na ɓarin dama sun shanye, harce kuma
ya karye, basu Na'ima kaɗai ba, hatta Lami sai da ta fashe da kuka. Khalil jan su Na'iman gefe yayi ya shiga
yi masu nasiha mai ratsa jiki, sannan ya shaida masu abubuwan da suke aikatawa ne ya jefa baba a cikin
halin da yake ciki, sannan yayi masu alƙawarin idan har sun tuba sun komawa Allah duk sun daina yawace-
yawacen da suke yi, shi kuma yayi masu alƙawarin akan su sai inda ƙarfinsa ya ƙare, kuma daga yau in dai
kuɗi suke nema to su tambayesa, sannan ya bawa kowaccen su damar nemo sana'ar da zata riƙa yi
shikuma daga nera ɗaya zuwa miliyan biyu zai bawa kowaccen su ta kama sana'a domin rufawa kai asiri, ya
ƙara da faɗa masu duk wacce ta natsu a cikinsu in Sha Allah tana zaune Allah zai kawo mata mijin
marainiya ya aurenta. Sannan kuma yace dukkansu sai sun koma islamiyya. Lami ma ya kirata gefe yayi ta
rioƙonta akan dan girman Allah ta daina ingiza ƴaƴanta suna yin karuwanci, idan har kuɗi take buƙata tana
da number ɗinsa ta kira ko nawa take da buƙata shi kuma yayi alƙawarin zai bata. Ranar dai kowa jigum-
jigum ya kwana, Lami kuwa lokacin da Khalil ya kaita ɗakin da babies ɗin suke, kamar ta ɗebesu haka taji,
wani irin ƙaunar yaran ya shigeta. Sarah kuwa ganin daga ƴan uwan nata har Lami duk sun koma wani
silent, sai taji wani irin daɗi da natsuwa ya kamata. Babu wanda ya faɗa mata baba na asibitin har sai da ya
kwana goma, Duk yanda suka ɗauka Sarah zata tashi hankalinta, sai suka ga tashin hankali yafi kwatancesu,
kuka kuwa kwana tayi tana yi, yaran kuwa ƙin zuwa tayi ta basu nono saboda haushin Khalil da take ji na
ɓoye mata mutuwa har biyu da kuma rashin lafiyar baban, don mutuwar Rabo ɗan wajen Na'ima da kuma
Nafeesa, duk a ranar aka faɗa mata, tayi kuka kamar ranta zai bar jikinta har sai da jininta ya sake hawa.
Dakyar Hajiya da Khalil suka lallasheta. Lami kuwa hankalinta gaba ɗaya ya koma wajen Aina'u ganin bata
ganta a asibiti ba, rabon da ta saka Aina'un a idanunta ma har ta manta, duk a tunaninta tana wajen
yawace-yawacen banzanta ne, haka nan sai taji hankalinta ya mugun tashi don ko lokacin da su Na'iman
suke tashen yawon bin maza, basu wuce kwana uku ko sati a waje, sannan duk ranar duniya sai sunyi waya
da ita, amma Aina'u kusan watanni uku kenan rabon da ta ganta kuma babu kiran waya, ko Lamin ta kira ta
a waya bata ɗauka. Tagumi Lami ta zabga tana kallon baba da ya koma kamar wani tsumma, a hakan ma
wai don yana Asibitin da ake kula dashi kenan! Ƙara kunnanta tayi zuwa bakin baba ganin magana yake yi
amma bata jin abunda yake furtawa, don harcen ya riga ya karye. Sarah dake kusa dashi don kullum tana
tare dashi, anan kuma take kwana duk da Lami da Na'ima suma suna nan, itama ta kawo nata kunnan
amma bata fahimta ba, fita tayi ta kirawo Khalil domin yazo yaji ko shi zai gane, ko da Khalil yazo ya kara
nashi kunnan, sai yaji kamar yana cewa Aliyu cikin karyewar harce, sai ya ɗago ya kalli Lami tare da faɗin,
"Mama Ni dai ji nayi kamar yana faɗin Aliyu, kuna da wani ne mai suna haka?" Girgiza kai tayi tare da
faɗin, "Gaskiya babu, da dai ma Lukman yace, sai ince ɗansa namiji yake nema." Da mamaki Khalil ya kalli
Lami tare da faɗin, "Mama dama kina da ɗa namiji?" Gyaɗa kai tayi tare da share guntun hawaye tana
kuma jin tsoron da kunyar faɗin Lukman ya mutu da kuma sanadin mutuwar tasa don ko ƴan uwansa basu
sani ba, daga ita sai ƙawarta Aunty Rose Merry suka san komai, su Na'ima kuwa sun ɗauka yana can yawon
banza da sace-sacen da ya saba. Khalil bai ƙara cewa komai ba sai juyawa da yayi ya kalli baba dake ta
ƙoƙarin magana amma babu baki, kuma ba kowa yake kira ba sai Aina'u yana faɗin, "Allah ya isa tsakanina
da Aina'u" su Khalil kuma Aina'un kawai suke ji shima kuma cikin karyewar harce sai kalmar yake yi masu
kamar Aliyu. Bayan fitan Khalil daga ɗakin sai Lami ta juyo ta kalli Sarah tare da faɗin, "Sarah, kin san kuwa
har yanzu babu wanda yasan inda Aina'u take! Yau watanni uku kenan rabon da na saka ta a idanu." Da
sauri Sarah ta kalli Lami tare da faɗin, "Wai dama baku san tana gidana ba? Ai tana can wajen Hajiya,
Maman Khalil." Da mamaki Lami tace, "Gidanki? Tun yaushe?" Sarah tace, "Ai ta jima, zata kai kusan
watanni ukun da kwanaki, duk da nima sai in haɗa sati biyu ban ganta ba." Riƙe haɓa Lami tayi tare da
faɗin, "Lallai Aina'u! Yanzu kuma ta san babanku ba lafiya amma ta rasa zuwa duba shi." Watsa hannu
Sarah tayi tare da faɗin, "Ohooo! Ta damu dashi ne? Ni wallahi Lami, wani lokacin Aina'u tsoro take bani.
Tana da mugun hali." Wani irin jijjiga baba ya fara yi yana watsa hannunsa na dama alamar dai magana
yake yi amma babu mai gane abunda yake cewa, kuma Sarah yake kallo yana watsa hannun. Fadi yake
Sarah ta kori Aina'u a gidanta, amma kuma bata gane ba sai kukan da take yi ganin yanda ya burkice, fita
tayi da gudu tayi office ɗin Khalil, yana ciki yana duba wata petient ta afka tare da kamo hannunsa zuwa
ɗakin baban. Allurar bacci yayi masa, nan da nan baccin ya kwashesa, sannan Khalil yace duk su fita daga
ɗakin su bar shi ya huta. Aina'u kuwa kwananta goma a ɗakin Hajiya babu ci babu sha sai ƙarban azaba
daga hannun _Hell Ofulafu_ take yi babu ƙaƙƙautawa. Dukan safe daban, na rana da ban, haka na dare.
Kuma har wannan lokacin Hajiya bata san da dawowarta ba, ba ƙaramin alwashi da mugun nufi Aina'u take
yi ba a zuciyarta duk lokacin da ta samu sassauci da yafiyar Hell, wani irin tsanar Sarah ta kuma ji ya ninku
a zuciyarta. Watan su Sarah ɗaya a asibiti aka sallame su, idan kaga twins baza ka taɓa cewa bakwaini
bane, sun yi ƙiba abunsu, haka ma Sarah ta ƙara cika tayi kyau, baba ma an sallame shi duk da jikin na nan
dai jiya i yau, sai dai Khalil yace zai riƙa zuwa har gida yana yi masa gashi wanda in Sha Allah zai taimakawa
jikin nasa. Satin na zagayo da sallamar su aka yi wani gagarumin taron sunan twins, _Sam'an_ da
_Sauban_. Irin kyaututtukan da Sarah ta samu faɗi ɓata baki, a gaban idanun Aina'u akai komai, don ta
samu sassaucin azabar, sai jinya jikinta da take yi yanzu, tayi wani irin rama da baƙi, haushi da tsanar kowa
take yi a gidan, hotunan Khalilullah dake wayanta kawai take kallo taji sanyi azuciya. Khalil ya maida komai
nasa da sunan Sam'an da Sauban, wani irin mahaukacin soyayya yake gwadawa Sarah da ƴaƴanta. Khalil ya
bawa su Na'ima miliyan biyu-biyu kowaccen su har da Lami, sannan ya saya masu wani four bedroom flat a
Jama'a road, tare da saka dukkansu a islamiyya kuma Alhamdulillah duk sun fara zuwa kuma natsuwa ta
soma shiga jikinsu. Hajiya damuwarta ɗaya, ta rasa abunda ke mata daɗi a duniya, wani irin abu take ji ya
tsaya mata a zuciya amma ta rasa menene wannan abun, sai ta zauna shuru tana tunani, duk tabi ta rame
ita da ya Abdul-Hakeem. Kuma har yanzu ta kasa tambayarsa akan matarsa da kuma zaman gida da yake yi
babu aiki. Aina'u kuwa ta warke garas, sai dai tsafinta ba zai taɓa ƙara amfani ba sai nan da shekara ɗaya,
haka Hell ya faɗa mata. Baiwar Allah Sarah kuwa, yanzu bata da damuwar komai, ta warke garas kamar
bata taɓa ciwo ba, tun da ta haihu bata ƙara ganin tsutsotsin nan ko guda ɗaya daga jikinta ba, sannan
wannan warin da mijinta yake yi mata duk babu. Wani irin soyayya suke shimfiɗawa wanda ko lokacin da
take amarya basu yi ba. Twins sun shiga wata shidda da haihuwa, yara tubarkalla don har tsayuwa suna yi
idan suka kama abu, kamanninsu ya ƙara fitowa sosai da Khalil, ga wayau. Sun san Laure sosai don itace
mai taya Sarah raino, amma kuma abunda ke matukar bawa Sarah mamaki shine, ko muryan Aina'u suka ji
gaba ɗaya rikicewa suke yi suna kuka, Sam'an shi har wani kakkafewa yake yi..........

_Asha weekend lafiya 🤩_

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_MATAR SAYYADEE_*

*Paid book 08128755583*


[16/10, 8:26 PM] Matar Sayyadee: Tsaye take a tsakiyar ɗakin tana wani irin dariya mai tafe da hawaye
baƙin ciki da kuma farin ciki lokaci guda, domin bayan tsawon shekara ɗaya har da wata uku, jiya da
daddare _Hell Ofulafu_ ya dawo mata da makamanta, yanzu tana iya ganin komai ta tsakiyar tafin
hannunta, sannan tana iya magana da _Hell_ da wannan mummunar halittar duk ta tafin hannun nata.
Tsafinta ya ninku yanzu ta yanda tana iya ganin mutum idan taso har a jikin bango, sannan ta jikin bangon
zata iya yi masa duk abunda taga dama, yanzu haka ma, tana kallon Sam'an da Sauban dake tsere a
parlour, pampers ne kawai a jikinsu, tuntuni Sarah ke so tayi masu wanka amma da wannan yayi can, sai
wancen ya zille yayi can, Khalil na zaune kan kujera sai dariya yake yi mata kuma yaƙi tashi ya taimaka ya
kamo mata su, shekaransu ɗaya da wata uku cif, amma wayansu ya zarce tunanin mai karatu, ga magana a
bakinsu kamar uwar aku. Idan Sarah ko Khalil suna so su tantancesu, sai su kira suna, misali sai suce
Sam'an! To Sam'an ɗin ne zai juyo Sauban kuma harkan gabansa zai cigaba dayi kasancewar ko ita kanta
Sarah sai tayi dagaske take bambance su, daga baya kamar sun gane, idan aka ce Sauban ko Sam'an, sai
gaba ɗaya su juyo. Khalil ruɗewa yake yi sai ya shiga tambayar Sarah, "Dan Allah wanene Sam'an, wanene
Sauban a cikinsu?" Taɓe baki take yi tare da faɗin, "Ka gano da kanka ai kai babansu ne, idan a waje aka
tambaye ka yaya za kayi?" Sai Khalil yace, "To ai shiyasa nake son ki bambance min tunda ke kina gane su
gudun kar inji kunya watarana!" Idan ya faɗi hakan sai ta nuna su ɗaya bayan ɗaya, ita kanta tana ganesu
ne da ɗabi'unsu, Sauban yana da faram-faram kuma yana da dogon fuska, Sam'an kuma bai cika faram-
faram ba, kuma fuskansa bata kai ta Sauban ɗin tsayi ba duk da shima dogon fuskan garesa, babu abunda
suka ɗauko na Sarah idan ka cire dimple, amma bayan haka kaf kamannin Khalil suka yo. Wani kalan
murtuke fuska Aina'u tayi ganin yanda Sarah da Khalil suke wasa suna zagaye parlourn su da ƴan biyun
nasu. "Wannan shine ƙarshe farin cikinki a cikin gidan nan, ni Aina'u sai na baƙanta maki fiye da yanda kika
baƙanta min, sai na wulaƙanta rayuwarki, sai na saka ki hawayen jini, sai na ruguza zuciyarki, sai na
ɓalɓalta rayuwarki dana ƴaƴanki, sai na kashe ki da baƙin ciki, sai nayi kwanciyar aure da mijinki a gaban
idanunki, sai na zama kishiyarki, na kuma ƙasƙantar dake. Babu aure tsakanina da mijinki, amma na rantse
da Ubangijin mu Yesu Almasihu mai ceto, sai nayi tarayya da mijinki kuma a cikin gidan nan a gaban uban
kowa, kuma duk wanda yace zai kawo mi shamaƙi ko shishshigi, sai na kashe shi!" Tana gama faɗin haka ta
ɗauko wani icce wanda aka ɗaɗɗaure shi kamar ƴar tsana sannan ta jawo wani tulu daga ƙasan gado mai
ɗauke da wani irin baƙin ruwa mai kauri sannan ta ambaci sunan Khalil sau uku sannan ta tsunduma iccen
nan har sai da guiwar hannunta ya shige ciki sannan ta fiddo hannun, wani mugun murmushi ta saki tare
da saka ɗayan hannunta ta fizgi gashin kanta sannan ta tura a cikin ramin idanun wannan iccen da ya koma
ƴar tsana amma bana itace ba, sannan ta tsaki saitin zuciyar ƴar tsanar nan har sai da hannunta ya lume
tare da ambatan sunanta sau uku sannan ta saki ƴar tsanan cikin tulun ya bata sautin 'tsumbul', sai ta
mayar da tulun ƙarkashin gado tare da duƙawa ƙasan guiwowinta ta leƙa ƙarƙashin gadon ta jawo wasu
ƴan tsanar guda biyar, ɗaya bayan ɗaya ta riƙa tsaka wani abu mai tsini a ƙahon zuciyarsu sannan ta jefa
cikin tulun nan ta miƙe tana jin wani irin matsanaicin farin ciki ganin gaba ɗaya ɗakin ya turniƙe da hayaƙi
da kuma wani irin duhu, can kuma bayan mintuna talatin komai ya washe, kuma dama _Hell_ yace idan
har hakan ta faru bayan kammala aikinta, to hakan na nufin aikinta yayi! Khalil ya kai hannu zai cafki Sarah
dake ƙoƙarin kama Sam'an yaji wani irin abu kamar mashi ya soki zuciyarsa da ƙarfi, wani irin baya yayi zai
faɗi Sarah ta kai hannu ta riƙosa amma duk da haka sai da suka kai ƙasa saboda gaba ɗaya jikinsa ne ya
saki. A ruɗe ta shiga kiran sunansa tana jijjigasa har hawaye ya wanke fuskanta, ƴan biyu kamar sun san
abinda ke faruwa sai suma suka zagaye Khalil ɗin suna jijjiga cikinsa, shi kuwa duk yana jinsu, amma sai ya
rasa shin a wani duniya yake, a hankali yaji zafin zuciyar na raguwa, can kuma sai ya soma jin wani baƙon
al'amari na shiga zuciyarsa, kuma ya rasa shin farin ciki yake yi ko akasin haka. Zuwa can sai ya miƙe da
sauri yana mai riƙe kansa, "Happy lafiya? Mai ke damunka?" Sarah ta faɗi tana mai kai hannu goshinsa,
twins ma da gwarancinsu suka haɗa baki suka ce, "apy yafila? (Happy lafiya?)" Murmushi Khalil yayi tare
da dungure masu kai yana faɗin, "Dan gidanku, daddy ba apy ba." Murmushi ƙarfin hali Sarah tayi don
gaba ɗaya hankalinta bai jikinta, duniya bata ƙaunar Khalil yayi ciwo don bai iya ciwo ba. Kamun yayi yana
jimawa, amma kuma idan ya tashi yi, kamar ba zai yi raiba haka yake. Tashi yayi tare da faɗin, "Kaina ne ya
ɗan sara min, amma nasan ina shan magani zai tafi, bari naje na ɗan huta kamun lokacin sallah yayi."
Gyaɗa masa kai kawai Sarah tayi jiki duk sake. Kumatunta ya kama tare da faɗin, "Smile now! Ba mutuwa
zanyi ba, muna nan tare mutuwar ma baza ta raba mu ba, tare zata ɗauke mu." Duk da haka yaƙe kawai
tayi, shi kuma ya hau sama ya barsu nan parlour. Jiki a sanyaye Sarah ta wuni, aikin ma dai kawai yinsa take
yi. Shi kuwa Khalil, koda ya koma ɗakinsa, bai iya baccin ba, tunani kawai ya riƙa yi, can kuma ya sauko don
haka nan yaji yana son zuwa side ɗin Hajiya. Saukowa yayi lokacin Sarah na ɗaya parlourn ita da yara, ba
tare da ya neme su ba ya fice abunda bai taɓa yi ba. Ita kuwa Sarah bata san da fitarsa ba, ta ɗauka har a
wannan lokacin yana sama a ɗakinsa. Aina'u kuma tana fitowa daga ɗakita, kai tsaye ɗakin Hajiya tayi
hannunta riƙe da wani baƙin padlock, ba tare da knocking ba ta murɗa handle ɗin ƙofar da ƙarfi tare da
faɗin, "Hajiya!" A razane kasancewar ita nata sihirin _Hell_ yace sai ta firgita tukun zai kamata. A razane
Hajiyar ta juyo, cikin sauri Aina'u ta ɗaga padlock ɗin tare da datse shi tana dariyar samun nasara. "Aina'u
kina buƙatar wani abu ne?" Hajiyan ta samu kanta da faɗin haka. Aina'u kuwa domin tabbatarwa sai cewa
tayi, "Buɗe bakinki ki tsaya a haka." Nan take Hajiyar tayi kamar yanda Aina'un tace. Wani irin dariya
Aina'u ta saki tare da faɗin, "To rufe bakin." Tuf Hajiya ta rufe tana mai bin Aina'u da idanu. Zaro mata
idanu Aina'u tayi tare da faɗin, "Bar kallo na!" Da sauri Hajiya ta sunkuyar da kai ita kuma Aina'u ta maka
mata harara tare da faɗin, "Da ace lokacin da na kira ki a waya domin ki dakatar da ɗanki ga auren yayata,
kin dakatar, da yanzu kina zaune cikin lumana babu tashin hankali, amma tunda baki yi hakan ba, yanzu
aka soma wasan!" Tana gama faɗin haka ta fice daga ɗakin tare da fitowa parlour dai-dai lokacin da Khalil
ya turo ƙofa ya shigo, idanu huɗu suka yi da juna, wani irin ajiyar zuciya Khalil ya sauke tare da sakarwa
Aina'u wani irin murmushi wanda ya kusa sumar da ita. "Aina'u!" Ya kira sunansa cikin wani irin salo,
"Na'am Khalilullah mijin Saratu!" Ajiyar zuciya ya kuma saki for the second time sannan ya zauna tare da
faɗin, "Zauna mana Ai'n." Yanda ya gajerta sunanta sai taji kamar duk duniya babu wanda ya iya kiran
sunan kamarsa, zama tayi daf dashi kasancewar a 2sitter ya zauna, fuskantar yayi tare da faɗin, "Oh, Ai'n
kamar ba cikin gidan nan kike ba, ko zuwa wajen ƴar uwarki bakya yi balle a haɗu a gaisa." Wani farrrrr da
idanu tayi tare da faɗin, "To ai ku ɗinne love bird, sam baku buƙatar irin mu masu hana ruwa gudu kusa
daku, kullum kafi son ganinka naniƙe jikin matarka." Kau da maganar yayi tare da faɗin, "To yanzu dai
muna gayyatarki shashinmu domin taya mu hira." "As you wish, your excellency!" Dariya Khalil yayi tare da
faɗin, "Sai kace wani gomna. Mu dai muna jiranki, na miƙa maki katin gayyata kullum da daddare kike
zuwa kina taya mu hira!" Faɗin Khalil. "An gama ranka ya daɗe." Faɗin Aina'u. Daga nan Aina'u ta riƙa jansa
da hira, sai ga Khalil har da kyakyatawa. Kamar yanda Khalil ya buƙata, da daddare sai ga Aina'u cikin wani
irin mahaukacin kwalliyar ɗaukar hankali, gaba ɗaya suka kan dinning suna cin abinci ta murɗa handle ta
shigo, Khalil ne ya fara juyawa fuskansa ɗauke da murmushi yana mai faɗin, "Ƙariso nan Aina'u ayi dinner
ɗin dake. Sauban na riƙe a wajensa, jin muryan Aina'u duk sai ya rikice yana neman guduwa wajen uwarsa,
Sam'an dake wajenta riƙe hannunta yayi gaam jikinsa na rawa. Sarah kuwa murmushi tayi tare da faɗin,
"Aina'u kenan, kamar ba gida ɗaya muke ba! Ko kin koma gida ne?" Taɓe baki Aina'un tayi tare da faɗin,
"Baki so gani na bane kawai." Ta faɗi hakane tare da jawo kujeran kusa da Khalil ta zauna a kai tare da
kallon Khalil ɗin tare da narke fuska. tana mai faɗin, "To ayi serving ɗina mana, ko da kaina zanyi." Cikin
sauri Khalil ya miƙe tare da ajiye Sauban, shi kuwa dama abunda yake jira kenan da gudu ya nufi gun
mamarsa yana kuka, ita kuwa Sarah wani irin maɗaukakin mamaki ne ya rufeta ganin yanda jikin Khalil
yake rawa don kawai zai zubawa Aina'u da basu taɓa ga macijiba abinci. Sai kawai ta zuba idanu tana
kallon ikon Allah. "Ai'n ga couscous, ga jellof rice, wanne za'a zuba maki?" Ɗaga idanu sama tayi tare da
faɗin, "Wanda kake ci shi zaka zuba min." Jellof rice ɗin ya zuba mata tare da kaza sannan ya ki plate ɗin
har gabanta tare da faɗin, "Gashi _Ƙanwar matata_" wani irin ƙululun baƙin cikine ya mamaye zuciyar
Aina'u jin sunan da ya kira ta dashi wai _Ƙanwar matata_! "Nafi gaban haka wallahi!" Aina'u ta faɗi cikin
zuciya, amma a zahiri sai tayi wani irin murmushi tare da kallon yanayin Sarah ta gefen idanu, abun yayi wa
Aina'u daɗi ganin confusion a idanun Saran. Spoon ta saka ta ɗebo abincin tare da sakawa a baki, lunshe
idanu tayi jin wani daɗi da ya mamaye kunnuwanta don Sarah gwana ce wajen iya girki duk da ba yi suke yi
a gida ba. Aina'u na cin abinci a lokaci guda kuma tana jan Khalil da hira, shi kuma kamar wani wawa ya
saki baki sai ɓaɓɓaka dariya yake yi. Sarah miƙewa tayi ta bar wajen zuciyarta na susa, duk da tasan babu
aure tsakanin Aina'un da Khalil ɗin idan dai har ba mutuwa tayi ba, sai taji wani irin matsanaicin kishi da
damuwa yanda Khalil ɗin ya manta tana wajen, da dane, Aina'u bata ma isa ta ƙariso inda suke ba balle har
ta zauna kusa dashi, da bata jin daɗin yanda Khalil ɗin yake ɗaurewa Aina'un fuska ganin su Na'ima yanzu
har wani respect yake basu matsayin yayyin matansa, amma kuma ya kasa sabawa da Aina'u, sai ta bar
hakan matsayin rashin haɗuwar jini, amma yanzu lokaci guda da taga wannan sauyin duk sai taji
matsanaicin damuwa ya kamata. Bayan ta hau sama sai ta canzawa twins pampers tare da saka masu
kayan baccinsu sannan ta sayar dasu har bacci ya ɗauke su lokacin ƙarfe tara da mintuna biyar amma har
yanzu Khalil bai dawo ba, kwanciya tayi tare da rufe idanu amma sai taji gaba ɗaya baccin yaƙi zuwa, tashi
tayi ta sauka a kan gadon tare da fitowa ta tsaya daga nan sama tana hangen Khalil kusa da Aina'u kamar
zasu shigewa juna yana nuna mata abu a waya suna dariya. Da sauri ta juya ta bar wajen saboda bata son
kawo zargi a zaman aurenta dashi. Ko da ta koma ɗaki, sam bacci ya kasa zuwan mata sai juyi take yi tana
saƙe-saƙe a zuciya tare da duba agogo a wayarta, sai da agogo ya buga ƙarfe ɗaya sannan taji buɗe ƙofar
Khalil ya shigo ɗakin, tana jinsa ya shiga toilet yayi wanka kasancewar kullum zai kwanta sai yayi wanka,
kayan bacci ya saka sannan ya hayo gadon tare da gyarawa twins kwanciya ya mayar dasu ƙarshen gadon
ahankali gudun kar su tashi sannan ya jawo Sarah jikinsa ya rungume, duk tana jinsa sai tayi kamar bacci
take yi har ta soma jin saukar numfashinsa alamar baccin ya ɗaukesa. Ajiyar zuciya ta sauke domin ta rasa
wani irin tunani za tayi, sai wajajen ukun dare bacci yayi gaba da ita. Washa gari da sassafe bata nuna masa
komai ba ta haɗa masa breakfast da duk abunda zai buƙata, haka kayan da zai saka bayan ya fito daga
wanka. Ita ta taimaka masa ya saka kayan sannan yayiwa twins kiss a kumatu kasancewar basu farka ba
sannan suka sauko ƙasa tayi serving ɗinsa ya karya. Sun rabu kamar kullum bayan yayi hugging ɗinta tare
da yi mata kiss ita kuma tayi masa addu'ar Allah ya tsare sannan ya tafi. Da sauri Aina'u dake kallon komai
a bangon ɗakinta dake shashin Hajiya ta fito cikin uban kwalliya tare da isa inda yake yana ƙoƙarin buɗe
mota, "Manyan gari kenan, har za'a fita ba tare da an ganni ba!" Da sauri Khalil ya kalleta tare da faɗin,
"I'm so sorry Ai'n, na kusa nayi latti ne shine nake sauri, kin san jiya mun sha hira, abunda ya makarar dani
kenan." "Kar inzo yau kenan?" Faɗin Aina'u tana wani kashe idanu. Waro idanu Khalil yayi tare da faɗin,
"Wa! Ai ko da har ɗakin Hajiya zan biyo ki, baki san yanda hira dake yake matuƙar sani nishaɗi ba ko? Kar
ma ki fara min wannan wasan." Wani shu'umin dariya Aina'u tayi tare da faɗin, "Hakane! To mu fita tare ka
ɗan rage min hanya nima dama fitan zan yi." Da sauri ya buɗe mata gaban mota sannan ya zagaya ya shiga
mazaunin driver yaja motar suka bar gidan. Sakin labule Sarah tayi tare da jinginar da bayanta jikin window
ɗin tana faɗin, "Ya Allah ka tausaya min kasa ba abunda nake tunani bane akan mijina da ƙanwata. Wunin
ranar sukuku tayi sa, ƙarfe shida Khalilullah ya dawo kamar yanda ya saba, sai dai kuma tare suka dawo da
Aina'u kamar yanda suka fita tare, kasancewar Sarah na ɗakinsa tana fesa airfreshner, sai tayi saurin ɗaga
labulan window jin ƙarar motarsa, gabanta ne ya buga da ƙarfi ganin Aina'u ta fito daga motar hannunta
ɗauke da wata ƙatuwar leda bakinnan kamar zai yage tsabar washesa da take yi. Sakin labulan tayi tare da
saukowa ƙasa sauri, buɗe ƙofar Khalil yayi ya shigo fuska ɗauke da fara'a, ganin yanayin matar tata duk sai
jikinsa yayi sanyi, gashi tayi bala'in kyau cikin wani Indian material da tayi ɗinkin straight gown dashi,
gashin kanta kuma ta kama shi in a middle ponytail, jelar gar dokin wuyanta, fuskanta yaci makeup mai
ɗaukar idanu, "Wife, lafiya naga fuskanki haka?" Maimakon ta bashi amsar tambayarsa, sai cewa tayi, "Ina
kuka je kai da Aina'u? You left this house together and you also came back together." Murmushi yayi tare
da faɗin, "Wai Aina'u? Rage mata hanya nayi wai zata wajen ƙawarta, luckily kuma sai muka sake haɗuwa
shiyasa muka dawo tare." Sarah bata iya cewa komai ba sai kallonsa da ta riƙa yi, "Come on, smile!" Ya faɗi
yana mai bata side hug. Yau ma dai irin na jiya aka kuma, Aina'u ta kuma zuwa kuma still sai 1am Khalil ya
dawo ɗakin, abun na matuƙar damun Sarah a zuciya, sam bata samun kulawar Khalil yanzu, ya kai yanzu ko
kwalliya tayi bai kallo bare ya yaba, girki kuma Aina'u ta koma yi masa, idan Sarah ta zuba masa abinci, sai
yace mata Aina'u zata kawo masa, tun Sarah na daurewa kusan sati Uku, har ta zuciya wata rana taje har
side ɗin Hajiya ta samu Aina'u a ɗaki bayan Khalil ya wuce asibiti, zaune take tana kallon tafin hannunta, ba
kowa bane a ciki sai Khalil dake zaune yana duba petient, bata san da zuwan Sarah ba kasancewar ba ita
take kallo ba a wannan lokacin, turo ƙofar da Sarah tayi ne ya dawo da ita cikin hayyacinta tayi saurin
kallon ƙofar don tasan Hajiya da Laure ko giyan wake suka sha baza su shigo mata ɗaki ba, wani kallon
banza ta watsawa Sarah da taga itace a ƙofar ɗakin, a zuciye Sarah ta ƙarisa ɗakin tare da ɗauke Aina'u da
mari sannan ta nunata da yatsa tare da faɗin, "Dan ubanki ki tattara kayanki ki bar gidan nan, idan ba haka
ba, sai na kakkaryaki, shegiya ƴar iska, na gama gane take-taken ki, so kike ki ɗauke min hankalin miji ko?
Don baki da kunya mijina kike so? To wallahi ahir ɗinki! In the first place ma na kasa gane uban da kike yi
cikin gidan nan tunda ba gidan ubanki bane, to ki saurareni da kyau, ki tattara ki bar gidan nan tun kan inyi
maki watsi da kayanki wallahi. Wawuya shashasha!" Tun da Sarah ta fara magana har ta dire Aina'u ko tari
bata yi ba sai ma wani murmushi da take yi, amma deep down ita kaɗai tasan mai take shiryawa cikin
zuciyarta. Sarah kuwa fita tayi tare da banging ƙofar. Har akai kwana uku Sarah bata kuma ganin Aina'u ba,
sai tayi tunanin ko taji abinda ta faɗa mata ne ta bar gidan, sai dai kuma gaba ɗaya ta kasa gane kan Khalil,
don wani lokacin har mancewa yake yi idan zai kirata sai yace, "Aina'u." Sarah gaba ɗaya hankalinta ya
tashi ta soma tunanin mai Aina'u tayiwa Khalil haka. A ran kwana na huɗu, kawai sai ganin Khalil tayi ɗauke
da akwatin kaya, Aina'u a bayansa shikuma ransa a mugun ɓace, a nan gaban Aina'u ya hau Sarah da faɗa
abunda bai taɓa yi ba, "Wannan wani irin haukane da jahilci! Ƙanwar taki kika kora a gidan nan saboda
selfishness ɗinkin? Kin bani mamaki Saratu! To yanzu na dawo da ita da kaina, she will stay here with us."
Yana gama faɗin haka ya ɗauki akwatin tare da kallon Aina'u yace, "Ai'n, follow me." Da sauri Sarah tasha
gabansa tare da faɗin, "Aina'u bata da ɗaki a sama." "Let go of my way Sarah Nuhu! Kar ki ja inyi maki
abunda ban taɓa yi maki shi ba a daran nan." Baki sake Sarah ke kallonsa, yayin da Aina'u ke wani irin
shu'umin murmushi. A gaban idanunta Aina'u ta bi bayan Khalil suka haura sama. Da daddare bayan Khalil
ya dawo ɗakin Sara, don yau sun kai kusan 2am suna hira da Ai'n kamun ya dawo ɗakin Sarah. Sai da ya
gama komai ya hawo kan gadon sannan Sarah ta miƙe ta zauna tare da kunna bedside lamp tare da faɗin,
"Ka tashi za muyi magana Please!" A raunane tayi maganar yanda zai ji tausayinta, amma ko juyowa bai yi
ba don juya mata baya yayi abunda bai taɓa faruwa ba tunda suka yi aure. Ƙara maimaita abunda tace tayi
a karo na biyu, a fusace ya juyo tare da faɗin, "Baccin baza ki bari inyi cikin salama ba? Wato kin ɗauko
wani hali da ba naki ba kin ɗaurawa kanki ba? Saboda tsabar kishi da rashin sanin ya kamata, shine za ki
riƙa kishi da ƙanwarki ciki ɗaya, Aina'u fa ƙanwarki ce, _Ƙanwar matata!_ kin taɓa jin inda miji ya auri
ƙanwar matarsa uwa ɗaya uba ɗaya kuma ba mutuwa tayi ba? Ni dalla malama kin isheni!" Yana gama
faɗin haka ya fita daga ɗakin tare da bugo mata ƙofar da ƙarfi sai da twins suka firgita tare da tsala ihu.
Aina'u kuwa daga ɗakinsa tana kallon komai, daga ita sai wata ƴar iskan rigar bacci da babu komai a ciki ta
fito ta tsaya a bakin ƙofa, Khalil na zuwa wajen ta jawo hannunsa tare da shigo dashi ɗakin sannan ta
murza key. Narai-narai tayi da fuska tare da shafa fuskansa zuwa ƙirjinsa ta shiga faɗin, "Kayi haƙuri ta
hanaka bacci ko? Kar ka damu idan ita bata sonka, Ni ina sonka kuma zan kula da kai." Wani irin babu daɗi
Khalil ya dunga ji amma bai san mai yasa ba ya kasa hanata abunda take yi, hannunsa ta kamo ta zaunar
dashi a bakin gado tare da zama akan cinyarsa ta kamo ƙeyarsa tare da haɗe bakinsu waje ɗaya. Da sauri
Khalil ya rufe idanu gabansa na faɗuwa da ƙarfi, can kuma ta ɗaga shi tare da turasa ya kwanta flat sannan
ta hau kanshi ta shiga kissing ɗinsa, shi kuwa Khalil bai son lokacin da ya biye mata ba..........

_Na san yau zan sha caccaka, wallahi har gabana faɗuwa yake wajen rubuta page ɗin nan saboda nasan
akwai wanda zasu tsine min tabbas, amma don Allah abunda nake so daku, kar ku kalli wannan page ɗin a
wani mahanga ta daban, wallahi ko Khalil da Sarah + Hajiya suna addu'a da sauke Qur'ani kullum, abunda
Allah ya rubuta sai ya faru, mutum bai taɓa wuce ƙaddararsa, Fiyayyan mahalicci ma asiri ya kamasa balle
wani kashi Khalil_

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_MATAR SAYYADEE_*

*Paid book 08128755583*


[17/10, 6:09 PM] Matar Sayyadee: Gaba ɗaya Khalil ya rasa control ɗinsa, Aina'u ta juye masa kamar
Sarah, yunƙurawa yayi tare da juyata ya koma kanta tare da birkice mata, sai sararaba sai da ya samu
natsuwa sannan ya koma gefe, Aina'u kuwa cikin zuciyarta cewa tayi, "Na rantse da Yesu Almasihu babu
uban da ya isa ya rabamu tunda na ɗanɗani zumanka, shegiya ƴar iska ashe ta san daɗin da take kwasa
shiyasa kullum tana naniƙe da kai babu dare babu rana." Da sauri ta tashi zaune tana kallon Khalil da yaja
zanin gado ya rufe jikinsa yana shashshekar kuka kamar wani ƙaramin yaro, "Heart, mai ya faru kake
kuka?" Ta faɗi tana mai kai hannu jikinsa, wani irin tureta yayi da hannunsa ba tare da ya juyo ba yana mai
jin baƙin ciki da dana sani har da na haihuwarsa da Hajiya tayi kasancewar ya kusanci Ƙanwar Matarsa
wanda har ga Allah shi bai san yanda aka yi hakan ta faru ba, don gaba ɗaya Aina'u koma masa Sarah tayi,
sai tunaninsa gaba ɗaya ya gushe, kuma bai dawo cikin hayyacinsa ba har sai da ya biya buƙatarsa da ita.
Wani irin durowa Aina'u tayi tare da duƙawa ƙarƙashin gadon da suke kai, sai taga still tukunyar tsafinta
nasan kuma bai canza kala ba, ɗagowa tayi ta kalli Khalil ɗin da har wannan lokacin shashshekar kukan
yake yi yayi ruf da ciki, a hankali ta kuma duƙawa ta tura hannunta cikin tukunyar har sa da tsintsiyar
hannunta ya shige sannan ta ɗago tare da hawa gadon, tun daga kan ƙeyarsa take shafa masa hannunta
har zuwa kan ƙirjinsa, nan take ya mirgino tare da zuba mata idanu, still sai ta kuma rikiɗemasa zuwa
Sarah, "Ina matuƙar ƙaunarki, sosai fa!" Ya faɗi yana mai kai hannu ya shafo fuskanta, caraf ta riƙe hannun
tana mai jin wani irin sanyi a cikin zuciyarta don da tayi tunanin tsafin da tayi masa ya lalatace, ɗaura kansa
tayi a ƙirjinsa tana yi masa tafiyar tsutsa a cikin kunne zuwa bayan kunnansa har bacci ya ɗaukesa, tana
ganin haka ta ajiye kansa a kan pillow a hankali tare da sauka daga kan gadon ta kunna hasken ɗakin
sannan ta jawo wannan tukunyar dake ƙarƙashin gado ta fito dashi tare da tsoma hannu ta ɗauko wannan
mutum-mutumin itacen nan ta hau kan gadon tare da kaisa saitin ƙirjin Khalil, wannan baƙin ruwan ya riƙa
ɗiga akai, sai da ruwan ya mamaye ƙirjin sannan Aina'u ta zaro wani abu mai kama da mashi ta ɗaga tare
da cakawa da ƙarfi a ƙirjin wannan mutum-mutumin sai da Khalil dake bacci yayi wani irin zabura tare da
dafe ƙirji, amma yana arba da fuskan Aina'u sai ya sakar mata murmushin tare da miƙa mata hannu alamar
tazo garesa duk da yana kallon abinda ke hannunta amma bai iya ko ƙare masa kallo ba balle ya tanka.
Sauka tayi ba tare da ta isa wajensa ba ta mayar da komai cikin ƙarƙashin gadon sannan ta kashe wutan
ɗakin ta hau kan gadon ta shige jikinsa, a cikin daren nan sai da ta ƙara naiman Khalil sau uku sannan tayi
bacci. Ɓangaren Sarah kuwa, raya darenta tayi da kuka, don yanda taga rana haka taga dare, idanunta yayi
luhu-luhu, ji tayi sam baza ta iya jure rashin Khalil a kusa da ita ba, ta riga ta gama yanke shawarar zata
cewa Khalil ko ita ko Aina'u, kuma ta san a irin ƙaunar da yake yi mata, itan zai zaɓa. A kunnanta akai kiran
sallah, saukowa tayi daga kan gadon ta nufi bayi ta ɗauro alwala tare da tada sallah, bayan ta idar da sallar,
sai ta miƙe ta hau gado saboda wani irin bacci dake fuzgar kasancewar bata samu bacci ba. Tana kwanciya
baccin yayi gaba da ita. Can cikin baccinta taji ihun kukan Sam'an, da sauri ta tashi zaune tare da jawosa
jikinta ta hau shayar dashi, shima Sauban kamar an tsikaresa sai ya tashi. Ko data gama shayar dasu,
wayarta ta jawo ta kunna, da sauri ta diro daga kan gadon ganin bakwai da mintuna arba'in tare da faɗin,
"Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Breakfast ɗin Happiness." Tana gama faɗin haka ta fice ko sauraran su
twins dake kuka saboda ta fita bata yi ba, jawo ƙofar tayi tare da soma saukowa daga steirs ɗin da sauri,
saura steps huɗu ta sauko gaba ɗaya ta tsaya turus tana kallon ikon Allah, zaune Khalil yake a kan dinning,
Aina'u kuma cikin wani irin shigar ɗaukar hankali tsaye a bayansa ta turo hannayenta ta saman kafaɗansa
tana saka masa Irish a plate, daga nesa ma zaka ɗauka rungumesa tayi. Sarah har wani jiri taji yana neman
yar da ita tayi saurin riƙe ƙarfen dake gefenta tana maimaita, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Cikin
zuciyarta. "Ka cinye tass, ban so ka fita da yunwa." Faɗin Aina'u cikin kunnen Khalil ɗin har da ɗan cizon
fatar saman kunnensa, shi kuma Khalil wani irin yaji yaja tare da cafko hannun Aina'un ya zagayo da ita
tare da jan kujeran baya ya ɗaurata a kan cinyarsa sannan ya zagayo hannunsa ya rungumeta tare da faɗin,
"Abincin kike so inci kuwa? Bari dai in baki tukwuicin daɗin da kika bani jiya!" A firgice suka juya gaba ɗaya
suna kallon Sarah data kwatsatsa wani irin ihuuu tare da gungurowa saboda ƙafarta da ya kasa riƙeta
sakamakon abunda taji ta kuma gani. Da sauri Khalil ya ture Aina'u dake jikinsa tare da ƙarisawa wajen
Sarah har da haɗawa da gudu, jijjigata ya soma yi yana kiran sunanta da ƙarfi, Aina'u kuwa folding
hannunta tayi tana kallonsu takaicin na neman kasheta, "Wato kai kana da taurin kai ko? Har yanzu tana
maƙale a zuciyarka kenan! To zanyi maganin ka tabbas." Faɗin Aina'u cikin zuciya. Sarah kuwa tunda ta
faɗo ƙasa ta fita daga hayyacinta, taimakon gaggawa Khalil ya soma bata ta hanyar bata numfashin bakinsa
bayan ya toshe hancinta, wani irin numfashi taja tare da wawware idanunta, sai da ta kwashi second
ashirin kamun ta saki wani ajiyar zuciya ta kuma zubawa Khalil idanu ko kyaftawa bata yi, "Mine!" Ya kirayi
sunanta a hankali, caraf ta riƙe hannunsa tare da ƙanƙamesa ta shiga faɗin, "Mafarki Happiness! Mafarki
nayi wai Aina'u tazo gidan nan tana neman shiga tsakaninmu. Ba gaskiya bane ko Happy?" Sarah ta faɗi
tana fatan Allah yasa abunda taji ta kuma gani duk a mafarki ne. Aina'u najin haka ta ƙariso wajen tare da
faɗin, "Na'am, mai kike cewa Aunty Sarah! Naji kamar kina kiran sunana." A firgice Sarah ta ɗago daga kan
ƙirjin Khalil tana kallon Aina'un, can kuma ta miƙe da sauri tana kallon Khalil ɗin dake ɗuke ya kasa ko ɗago
idanu balle ya kalleta saboda wani irin kunyanta da yake ji. Wasu irin ruwan hawaye Sarah ta shiga
zubarwa tare da duƙawa akan guiwowinta ta shiga faɗin, "Happy, mai na rageka dashi a cikin gidan nan? Ta
ina na gaza? Shin ka taɓa nemana a shimfiɗa na ƙaurace maka? Ƙanwata Khalil! Ƙanwata uwa ɗaya uba
ɗaya kake nema Khalil!! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!!! Ka cuce ni ka cuci rayuwarka, da iliminka, da
matarka da ƴaƴanka da komai kake aikata zina! Wallahi tallahi baka yi min adalci ba." Ta ƙarisa maganar
tana mai rushewa da kukan baƙin ciki, can kuma ta ɗago ta kalli Aina'u tare da faɗin, "Ke kuma asararriya
wulaƙantacciya, watsatstsiya azzaluma muguwa mai shiga tsakanin mata da miji, anya kuwa ke jini nace
Aina'u? Anya kuwa ba canje akai wa Lami a asibiti ba? Zo ki fice ki bar gidan nan ko wallahi inyi ajalinki,
bazan taɓa bari kici galaba akan mijina ba!" Sarah na gama faɗin haka ta kwasa da gudu ta nufi kitchen
tare da ɗauko wuƙa ta fito da gudu tayo kan Aina'u tana faɗin, "Fita ko in kashe ki sai dai nima a kashe ni!"
Da sauri Khalil ya shiga tsakani tare da kwace wuƙar a hannun Sarah yana faɗin, "Baki da hankali ne
Mine?" A zafafe tace, "Eh bani da shi! Tun ranar da ka fara naniƙewa Aina'u na rasa hankalina, kuma bazan
taɓa dawowa cikin hankalina ba sai ranar da ka rabu da ita." Hannu biyu yasa ya riƙo damatsanta tare da
faɗin, "Ki dawo cikin tunaninki Sarah, ni da Aina'u babu abunda ke tsakanin mu sai wa da ƙanwa, ita ɗin fa
ƙanwarki ce, Aina'u Ƙanwar matata ce kawai." "Ƙarya ne, ni ba ƙanwar matarka bace kawai, ka faɗa mata
gaskiya kawai tunda yanzu ta san komai, idan zata iya haƙuri, to! Idan kuma baza ta iya ba, hanya a buɗe
take, amma maganar ni ƙanwar matarka ce kawai wannan ba haka yake ba, ka gama kwanciya dani a ɗaki
jiya kana min ihun daɗi da sambatu, har kana faɗin baka taɓa samun natsuwa a jikin Maman twins ba
kamar yanda jiyan ka samu a jikina, ohh duk ka manta da wannan kenan?" Zaro idanu Khalil yayi don ya
san wallahi shi bai ce haka ba. Itama Aina'un zaro masa idanun tayi tare da faɗin, "Ko ba haka bane!" "Ya
ke Kuma anan son kashe wuta kina ƙara rurawa!" Ko kamun su ankara Sarah tayi kukan kura ta wanke
fuskan Aina'u da maruka hagu da dama tare da shaƙar mata wuya tana faɗin, "Sai na kashe ki yau a cikin
gidan nan!" Da kyar Khalil ya janye Sarah a jikin Aina'u sai aika mata da maruka da naushi take yi, Aina'u
kuwa wani irin zuciya ne ya yunƙurota, take ta danna yatsarta tsakiyar tafin hannunta sannan ta murza da
ƙarfi. Nan take wani zuciya ya yunƙurowa Khalil ya ɗaga hannu tare da wanke fuskan Sarah hagu da dama
sai da tayi taga-taga zata faɗi, da mugun mamaki take kallonsa hannunta dafe da kunci hawaye na tsiyaya.
Khalil kuwa jawo Aina'u yayi ya rungume har da jijjigata kamar baby yana faɗin, "Akwai inda ke yi maki
ciwo muje asibiti?" Girgiza kai Aina'u tayi tana wani narkewa tare da faɗin, "Ka ɗaukeni muje ɗakinka,
tsoro nake ji kar ka fita ta nemi kashe ni, muje ɗaki kar ka fita ko ƙofa yau!" Cak ya ɗauketa tare da saɓata a
kafaɗa ya gitta Sarah da tayi mutuwar tsaye. Aina'u kuwa wani irin gwalo rayiwa Sarah mai tsayawa a
zuciya sannan taja hannunta wajen wuyanta alamar zan kashe ki sannan ta shiga nunata da ɗan yatsa tana
jijjigawa alamar gargaɗi. Zubewa Sarah tayi a ƙasa tama kasa kuka sai kalle-kalle kawai take yi a ɗakin, can
kuma ta girgiza kai tare da faɗin, "Tabbas wannan ba Khalil ɗina bane, Khalil ɗina bai son ganin ɓacin raina
kuma bai son damuwata, dole akwai abunda Aina'u tayi masa, haka nan Khalil ba zai taɓa canza min ba.
Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!!!"
Haka Sarah ta dunga maimaitawa har kuka ya kufce mata. Tafi ƙarfin awa guda a wajen kamun ta tashi ta
haura sama, daidai ɗakin Khalil ta jiyo saurin da ya kusa tsayar da numfashinta, "Ohh my God! Aina'u
you're soooo sweet, wallahi kinfi zuma daɗi!! Na baki kaina ki cinyeni tasssss, show me Ai'n, show me that
you love me, do it properly, ohhh myyyyyyy.........." Da mugun gudu Sarah ta bar wajen tare da faɗawa
ɗakinta, ko kula su Sauban dake kuka bata yi ba ta shiga rera nata kukan, bata gansu ba, amma idanunta ya
gama hasaso mata hotonsu gaba ɗaya a idanunta, data kulle idanu abunda take gani kenan, nan da nan
jikinta ya ɗauki wani irin zafi mai tsanani tare da ciwon kai. Sauban ne ya tako ya iso wajen gadon tare da
kama rigar baccinta ya shiga ja yana faɗin, "momiiii." Shima Sam'an sai ya taho shima yana kukan, da kyar
ta iya kai hannun ta ɗauko su duka ta rungume a jikinta ta kuma fashewa da kuka, kamar wanda suka san
kukan da take yi, suma sai suka ƙara fashewa da kukan. A haka ta shayar dasu hawayeta na ɗiga a jikinsu
har suka ƙoshi sannan ta miƙe da kyar ta cire masu pampers sannan ta kaisu bayi tayi masu wanka ta
shiryasu duk tana kukan sannan itama tayi wankan ta fito ko mai bata shafa ba ta zura doguwar riga tare
da haɗa kayanta da na twins ɗin a cikin akwati ta goya Sam'an ta riƙe Sauban a ɗaya hannun ɗayan Kuma
ta shiga jan akwatin, tana fitowa Aina'u na fitowa daga ɗakin Khalil don bayan sun gama abunda suka yi da
Khalil ɗin sai ta shafa hannunta ta shiga hango Sarah daga ɗakinta tana ɓaɓɓaka dariya, don ba ƙaramin
daɗin ganin halin da Sarah take ciki take yi ba. Ko kallonta Sarah bata yi ba duk da kuwa tana fitowa ta
ganta, amma sai tayi kamar bata ganta ba don zuciya zai iya sakawa ta caki maƙogwaranta ta faɗi ta mutu.
"Ke dawo nan!" Aina'u ta faɗi bayan ta murza tafin hannunta. Babu musu Sarah ta juyo ta dawo inda
Aina'un take, "Menene a cikin akwatin nan kuma ina zaki?" Faɗin Aina'u. "Kaya twins ne da nawa, kuma
gida zani." Sarah ta bata amsa cikin zuciyarta tana mamakin yanda akai take sauraran Aina'un. "To ki koma,
babu inda zaki, ai baki fara ganin komai ba tukun, so nake zuciyarki ta buga ki mutu saboda baƙin ciki
kamar yanda nima kika ɗanɗanamin baƙin ciki. Maza koma ɗaki yanzun nan!" Aina'u ta ƙarisa maganar da
ƙarfi, "My love meke faruwa?" Faɗin Khalil daga ciki jin ihun Aina'un. "No, babu komai yi kwanciyarka."
Komawa yayi ya kwanta don dama a kwancen yake, ita kuma tabi bayan Sara dake ƙoƙarin buɗe ɗakinta da
harara. Tun daga wannan ranar Sarah ta koma hoto a cikin gidan ita da yaranta, don sai ta kwana bakwai
bata saka Khalil a cikin idanunta ba, tayi wani irin mugun rama kamar mai ciwon ƙanjamau, ga wani irin
mugun tsoron Aina'un da take yi, don har ɗaki Aina'u ke biyota tana bata command, ita ke masu girki tayi
serving ɗinsu, sannan idan sun gama taje ta kwashe kayan ta kai kitchen ta wanke, da daddare kuma su
dame ta da ihu ita da Khalil ɗin, kwana take yi bata bacci, amma duk da haka bata taɓa tunanin ta tashi ta
raya daren ba ko da da raka'a biyu ta kai kukanta wajen Allah, babu abunda take yi sai kuka, sallolin nan
biyar dai basu wuce ta, amma bata san tayi azkar ɗin safe dana maraice ba, ko kuma ta buɗe Qur'ani ta
karanta ba. Sai dai ta zauna tsakiyar gado tayi ta kuka. Ɓangaren Khalil kuwa, yafi Aina'u rama, a fuskane
kawai kamar yana farin ciki, amma deepdown zuciyarsa ciwo take masa, duk lokacin da zai sadu da Aina'u,
koma masa take yi Sarah, sai bayan ya kammala sai ta rikiɗe ta dawo masa Aina'u, haka shima zai ta kuka
har gari ya waye, yanzu sallar ma ya daina zuwa masallaci kwata-kwata, a nan ɗaki yake yi, kamun Aina'u
ta soma korashi parlourn don _Hell_ yayi mata warning akan idan har yana Sallah a inda kayan tsafinta
yake, komai zai lalace. Yauma Sarah na zaune akan gado tana sana'arta, sai ji tayi an bugo ƙofar da ƙarfi, da
sauri ta ɗago jikinta na rawa ganin Aina'u ce, su Sauban kuwa dake wasa a ƙasa har sun yo kan Aina'u sun
ƙanƙame, "Ki tattara kayanki tsaf ki koma ɗakin ƙasa da zama, ko da wasa kar in ƙara ganin ƙafarki a saman
nan." Aina'u na gama faɗin haka ta fice daga ɗakin, don yau kama Khalil tayi a bakin window ɗin Sarah
yana kallonsu ita da ƴaƴanta kasancewar akwai haske a barandar, ita kuma Aina'u ta tashi fitsari taga bai
ɗakin shine ta fito ta gansa jikin window ɗin yana hawaye. Yana jin motsinta ya share hawaye da sauri tare
da soma kame-kame. Ɗaki ta nuna masa da hannu, suf-suf-suf ya wuce ita kuma tabi window ɗin da
harara tare da yin kwafa ta bishi ɗakin. Wannan dalilin ne ya saka ita kuma ta kori Sarah daga saman gaba
ɗaya. Ita Sarah har cikin ranta ta san Aina'u bata bar Khalil haka ba, amma rashin dabara da hankali ya saka
ta kasa kai kukanta zuwa ga Allah. Watan Sarah Shidda a cikin wannan bala'in amma ko sau ɗaya bata taɓa
jaraba kai kukanta ga mahalicci ba, sai dai kuka wani lokacin kuma tace Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un,
tuni ta yaye su twins don daga ita har Khalil ɗin duk sun zama abun tausayi da tsoro don ba ƙaramin rama
suka yi ba, shi kuwa Khalil duk ranar da yaje asibiti, don asibitin ma ba kullum take bari yake zuwa ba, sai
couligue ɗinsa sun yi masa caaaa akan mai ke damunsa duk ya rame, wasu kuwa sun fara zargin halin da
yake ciki na neman ƙanwar matarsa, don Aina'u kullum sai ta saka shi a gaba sun fita zuwa wajajen
shaƙatawa tare, suyi hotuna wani lokacin ma a hotel suke kwana. Yau ya kasance Sunday babu inda Khalil
yake zuwa, sai dai sau da yawa basa wuni a gida shi da Aina'un, don yana daga cikin ranakun fita yawonsu,
zaune yake a parlour daga shi sai gajeran wando, Aina'u kuwa ta ɗaura kanta a kan cinyarsa tana danna
waya, can wata ƙawarta ta turo mata da bp sai da ta gama kallo sannan ta nunawa Khalil tare da faɗin, "My
love yau wannan style ɗin za muyi!" Ƙarban wayar yayi ya kalla da kyau sannan yace, "Kuma fa zai yi
suger." Tashi Aina'u tayi tare da faɗin, "Bari ma ka gani dama bamu taɓa yi a parlour ba." Tana faɗin hakan
ta kai hannu zata zame boxer ɗinsa, da sauri ya riƙe tare da faɗin, "Sarah might come out ita da yara, muje
ciki kawai." "Ni kuma anan nake son muyi!" Tana gama faɗin hakan ta sutale masa wando tare da soma yi
masa blowjob, tuni ya manta da batun su Sarah zasu iya fitowa ya hau moaning, gaba ɗaya ya fice daga
hankalinsa kuma dama abunda Aina'un take so kenan, nan da nan ta cire ƴar iskar doguwar rigar dake
jikinta ta yar ta hau kan Khalil ɗin daidai lokacin da twins suka fito parlourn kamar an jeho su. Da gudu
Sarah ta fito daga ɗayan parlourn jin ihun su Khalil ɗin a parlour kuma taga lokacin da twins suka fita, "Inna
lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Sarah ta faɗi da ƙarfi tare da kai hannu ta rufe idanun twins tana wani irin
kuka, don ko da suka fito suka ga abunda Khalil ɗin suke yi, cak suka tsaya sunata kallo. Shi kuwa Khalil
wani irin tsalle yayi tare da ture Aina'u yana kare jikinsa yana mai jin kamar ƙasa ta tsage ya shige ganin
yaransa sun ga abunda yake yi. Hannunsu Sarah ta kama tana kuka tare da shigewa ɗayan parlourn. Da
sauri Khalil ya saka wandonsa ba tare da ya kalli Aina'u ya wuce sama. Aina'u kuma tsaki tayi tare da
ɗaukar rigarta ta saka ta zauna tana kaɗa ƙafa. Bayan mintuna talatin Sarah ta fito ta samu Aina'u a inda
take, zubewa tayi kan guiwowinta tana kuka sosai tare da faɗin, "Aina'u dan girman Allah, dan ƙaunar da
Allah yakewa Manzonsa s a w, idan kina ƙaunar ki shiga aljanna kiyi haƙuri ki koma gida ki fita daga
rayuwar mijina ki warware koma menene ki kai masa don na san duk abunda yake yi ba cikin hayyacinsa
yake ba." faɗin Sarah don ta mance Aina'un ma da daɗe da barin musulunci. Wani irin dariya Aina'u ta
fashe dashi tare da faɗin, "Wallahi babu uban da ya isa ya raba ni da Khalil, kuma da gaske mijinki ba a
hayyacinsa yake ba, amma kuma har ya mutu babu wanda ya isa ya warware abunda nayi." Faɗin Aina'u
tare da miƙewa ta hau sama. Sarah ta jima tana kallonta kamun ta koma ta kamo hannun twins ɗin suka
fita daga ɗakin don ta gama yanke hukuncin mayar dasu side ɗin Hajiya za tayi saboda gudun gurɓacewar
tarbiyansu. Tana shiga ɗakin Hajiya ta idda Laure bisa darduma ta kai kanta ƙasa sa shashsheƙar kuka take
yi tana ganawa da ubangijinta. Turus ta tsaya tana auna hauka da rashin hankalin ta, "Idan dai har Laure
zata yi sujjada tana kuka domin buƙatarta wajen ubangiji, to ni mai na tsaya yi kenan? Tabbas babu
maganin da Ubangiji bai dashi.........."
*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_MATAR SAYYADEE_*

*Paid book 08128755583*


[19/10, 6:17 PM] Matar Sayyadee: Koda Laure ta ɗago fuskanta, jaga-jaga yayi da hawaye saboda kukan da
tayi, zama Sarah tayi akan kujera hannunta riƙe dana twins tana ta kallonta har ta idar da sallar. Bayan ta
shafa addu'a sai tayiwa Sarah murmushi tana mai miƙawa twins hannu, gaba ɗaya sai suka tafi wajenta,
Sarah miƙewa tayi ta nufi ɗakin Hajiya, sai da ta Kwankwasa sannan ta murɗa ta shiga, zaune ta samu
Hajiya ta zabga uban tagumi, duk da irin ramar da Sarah tayi, ba ƙaramin tsoro da tausayi Hajiya ta bata ba
saboda yanda ta koma ta yanƙwane, "Hajiya ina wuni?" A ɗan tsorace Hajiya ta ɗago tana kallon Sarah don
bata ji shigowarta ba. "Lafiya ƙalau Sarah, zauna mana, ina ƴan biyu kyautar Allah?" "Suna parlour wajen
Laure." Sarah ta bata amsa hawaye na ciccikowa daga idanunta. Wani ajiyar zuciya Hajiya ta sauke tare da
kallon Sarah tace, "Sarah ban san mai ke faruwa a cikin gidan nan ba, komai ya tsaya cak, babu walwala da
farin ciki, zukatu cunkushe suke da baƙin ciki, hasken dake gidan nan gaba ɗaya ya dusashe, ƴaƴana sun
manta dani, Marmari bai taɓa yini bai kirani a waya ba, Muhammad Kabir shima bai taɓa kwana ba tare da
yaji muryata ba, amma yanzu tsayin shekara ɗaya har da watanni biyar rabon da naji muryansu, ko balle
kuma su tako suzo inda nake, na rasa wannan wani irin al'amari ne wannan, uwata!" Hajiya ta ƙarisa
maganar hawaye na zubo mata. Gaba ɗaya sai jikin Sarah yayi mugun sanyi ganin tsohuwa na hawaye.
Hannunta Sarah ta dafa tare da faɗin, "Hajiya kiyi haƙuri, amma ni a tunanina ba hakannan ba su ya
Abdallah zasu ƙaurace maki har na tsawon shekara ɗaya da watanni! Hajiya addu'a da roƙon Allah har da
sadaka zaki fara daga yau akan Allah ya karkato maki da dukkan hankalinsu a kanki, in Sha idan muka
miƙawa Allah lamuranmu da kyakkyawar yaƙini, in Sha Allah zai yaye mana damuwarmu, Hajiya gaba ɗaya
mun mance da Allah shiyasa shima ya mance damu, kuma na tabbata idan muka koma garesa zai amshi
buƙatunmu da hannu bibbiyu. Hajiya ban san cewar duk tsawon shekarun nan aikin banza nake yi ba
wajen raya darena da kuka ba sai yau da na shigo ɓangaren nan na tarar da Laure na ganawa da
ubangijinta tare da ƙasƙantar da kanta tana kuka. Hajiya muyi koyi da Laure in Sha Allah duk matsalolinmu
zasu gushe!" Shuru Hajiya tayi tana sauraren Sarah cike da jin kunya da kuma dana sani akan rashin kai
kukanta tuntuni zuwa ga mahalicci, sai hakan ya tuno mata da marigayi (Nuruddeen Muhammad)
mahaifinsu Khalil, da wani abu ya shige masa duhu ko kuma yana fuskantar matsaloli, nan da nan yake
ƙara nau'ikan ibadu akan wanda yake yi, dama kuma azumin litinin da Alhamis ya zame masa jiki da kuma
sallar dare, sai ya ƙara ninkawa, almajirai yake tarawa fiye da ɗari kuma ya shiga cikinsu su sauke ƙur'ani
sau goma a cikin sati guda, sannan ya shiga sadaka a masallatai tare da gidajen maru, maƙowa kuwa
kyautatawarsu daban take, hakan ne ya saka duk tuggun da ƴan uwansa suke binsa dashi yake koma masu.
Kuma ƙa'ida ne lokaci da yake raye, tun su Khalil na ƙanana sai ya haɗa kansu har matan sun sauke ƙur'ani
duk bayan kwana goma, bayan rasuwarsa da kuma yanayin aikinsu gami da mai da hankali kan tsantsan
boko ya saka suka watsar da komi, kuma Lokacin da yake da rai, kullum gidan cikin sauraren karatun
Alƙur'ani ake. Ajiyar zuciya Hajiya ta sauke tare da kallon Sarah tace, "Tabbas Saratu duk abunda kika faɗi
hakane. Wato lokacin da mahaifinsu Khalil yake da rai, wallahi kullum cikin gidan nan karatun Alƙur'ani ake
saurare, sannan duk bayan wani lokaci, Alai sai ya tara almajirai anyi saukar ƙur'ani da sadaka, bayan
rasuwarsa ne komai ya watse!" "Hajiya a shawarce, ya kamata komai da ake yi cikin gidan nan ya dawo har
abada." Faɗin Sarah. "In Sha Allah, uwata. Nagode maki sosai da tunatarwarki uwata, Allah yayi maki
albarka." Faɗin Hajiya. Sarah ta amsa da ameen tare da miƙewa ta fita daga ɗakin, a parlour, su twins na
ganin mahaifiyarsu sai suka bar jikin Laure da sauri tare da ƙarisowa wajenta, Sarah tayi-tayi su koma a
atafau suka ƙi, haka nan ta koma side ɗinta dasu, babu kowa a parlour sai tayi saurin shigewa ɗaki don
kallo kujeran dake parlourn zai iya saka ta faɗi ta mutu, don gaba ɗaya hoton Khalil da Sarah take gani
tsirara a kan kujerar. Aina'u kuwa duk abubuwan da Sarah ta tattauna da Hajiya tana kallon komai daga
ɗaki, wani ƙuƙulun takaici ne ya tokare mata waya ganin Sarah tun ba'a je ko ina ba tana son lalata mata
shirinta. Tashi tayi ta kullo ƙofar kasancewar ko da Khalil ya bar parlourn ɗazu, ɗakin Sarah ya shige ya kulle
kansa, sai ta ɗuka ta fiddo wannan tukunyar tare da tura hannun ciki ta ɗauko wannan mutum-mutumin
na itace ta matse saitin zuciyarsa da ƙarfi tare da tsundumawa cikin tulun sannan ta kuma cirowa ta ƙara
danna ƙirjinsa sannan ta saki daga sama ya faɗa tsumbul a cikin tulun tare da mayar da tulun ƙasan gado
sannan ta shafa tsakiyar tafin hannunta sai ga hoton fadwa ƴar wajen Marfu'a, Bobo da Nana ƴan wajen
Hassana, mimi ƴa guda da ta ragewa Na'ima, Sai Sultee da haidar ƴaƴan Nuratu. Wani murmushi tayi tare
da zana maciji a hannunta, nan take macijin ya soma motsi tare da tafiya da sauri-sauri, ɗaya bayan ɗaya
macijn nan ya dunga saransu suna zuba ihu kasancewar gaba daya suna wasa ne a tsakar gidan, yayin da
iyayensu suke makarantar dake gaban gidan kaɗan, Na'ima ce kawai bata je saboda fama da ciwon kai da
take yi kwana biyu, Lami kuma tana ɗaki ta saki ac tana sharar barci don bata jima da dawowa gidan ba
daga gidan Aunty Rose Merry. Da gudu Na'ima ta fito jin wani irin mahaukacin ihu da Mimi ta saki
sakamakon saran maciji, dai-dai nan Lami itama ta fito da sauri, a kan idanunsu macijin ya sulale yabi
bayan flowers ya ɓace amma su basu ga ɓacewar nasa ba. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" "Lord of
Jesus!" A tare Lami da Na'ima suka faɗi haka sannan suka yi kan ƴaƴan da gudu suna jijjigasu, cikin
ƙanƙanin lokaci har fatan jikinsu ta sauya kala ta koma green yayin da baƙin kumfa ke fita daga bakunansu
suna wani irin jijjiga, kuka Na'ima ta fashe dashi tare da ɗaura hannu a kai, can kuma ta nufi gate da gudu
ta fita ko mayafi babu tana kuka tana faɗin a taimaka mata, tare suka dawo da maza biyar cikin gida, inda
yaran suke ta kaisu tana kuka, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Mai ya same su?" Gaba ɗaya suka faɗi
suna mai isa kusa da yaran tare da taɓa su. "Macijine ya sare su, nima ihunsu naji na fito sai naga macijin
da sauri yabi bayan flowers ɗin na." Ɗaya daga cikin su ya nufi bayan flowers ɗin yana dubawa, "Tabbas
kuwa! Ga saɓarshi nan a nan wajen!" Ya faɗi yana mai ɗago saɓar macijin. Huɗun da suke kan yaran suka
kalli juna bayan tabbatar da babu sauran numfashi a jikin yara, "Yaro yi min bayani, sun mutu ko?" Faɗin
Lami tana mai duƙowa tare da taɓa wuyan Mimi dake daf da ita. "Iya sai dai haƙuri, Allah ya riga ya ɗauki
rayuwar waɗannan ƴaƴan." "Yesuuuuuu! Wannan azaba da jarabawar ya isa haka! Muna yabonka Ya Allah:
mun dauki cewa kai ne Ubangiji. Dukan duniya tana yi maka sujadda, Uba Ma-dauwami. Agareka Malaïku
duka suna tada murya, da Sammai da Ikoki duka da ke cikinsu. A gareka Charubin da Sarafin kullayomi
suna tada muriya. Mai-tsarki, Mai-tsarki, Mai-tsarki: Ubangiji Allah Mai-runduna. Samma da kasa cike su
ke da Sarautar darajarka. Jama’a masu daraja ta zamaninka tana yabonka. Managarcin zumunta ta
Annabawa tana yabonka. Jama’a mai-daraja ta Masu-shahada suna yabonka. Ekklisiya mai-tsarki cikin
dukan iyakar duniya tana shaidanka: Ya Uba mai-sarauta mara-iyaka: Danka kuma mai-girma, mai-gaskiya,
ma-kadaici: Ruhu Mai-tsarki kuma Mai-taimako. Kai ne Sarkin Daraja: Ya Almasihu. Kai ne Da matabaci na
Uba. Sa’anda ka dauka ma kanka ka ceci mutane, ba ka yi kyamar cikin buduruwa ba. Sa’anda ka yi nasara
da zafin mutuwa, ka budi Mulkin Samma ga masu-bada gaskiya duka. Kana zaune ga hanun damar Allah
(Astagfutullah) a cikin darajar Uba. Muna bada gaskiya za ka zo ka zama mai-shari’anmu. Muna rokonka fa,
ka taimaki bayinka: wandanda ka fanshe su da jininka mai-daraja: Ka maishe su a-cikin lissafin tsarkakanka,
a-cikin daraja ta har abada. Ya Ubangiji ka ceci jama’arka, ka sa ma gadonka albarka. Ka malke su: ka
ɗaɗɗaga su har abada. Yo da gobe muna girmama ka; Muna sujadda ga sunanka kuma kullum ba matuka.
Ya Ubangiji da yardarka ka tsare mu kar mu mutu da zunubi. Ya Ubangiji ka yi mana jinkai: ka yi mana
jinkai. Ya Ubangiji ka bar jinkanka shi rufto mana: da shike ban gaskiyarmu tana gareka. Ya Ubangiji, a-
gareka na bada gaskiya, kada ka bar ni na rude har abada. Wannan yara da suka koma izuwa gareka a yau,
ka hura ruhinsu a cikin tsarkinka, ka yafesu a cikin irin yafiya naka, mu kuma ka karemu kar muyi mutuwa
irin nasu, Yaaa Yesu Almasihu uba!" Kallon-kallo mutanan nan suka shiga yi, don duk a tunaninsu Lami
musulmace duk ganin da suke yi mata, sai yaji da suka ji uban yabo da ta kwararo suka fahimta, "Ashe
aljihun baya ce!" Ɗayan ya kalli ƴan uwansa ya faɗi, shi kuma mai riƙe da fatar maciji yace, "To Allah ya
ƙara nauyin ƙasa!" A fusace Na'ima tace, "To ba amin ba! Wannan wani irin Magana ce haka kuke yi? Ai ko
da ace a cikin addinin Kirista aka haifi su Mimi bai kamata kuce haka ba tunda dai basu san komai ba, kuma
ko yanzu a makarantar Annabi Ibrahim zasu tashi in Sha Allah! Balle kuma Ni uwarsu acikin musulunci aka
haife ni kuma, na furta kalmar Ashhadu Allah ilaha Illallah, Wa Ashhadu anna Muhammadan abduhu wa
rasuluhu!" Da sauri mutumin yace, "Allah ya baki haƙuri, kiyi haƙuri dan Allah!" Na'ima bata kuma cewa
komai ba sai kukan da take yi. Ita ta riƙa ɗaukar ƴaƴan tana kaisu ɗaki tare da rufesu har kai, bata yarda ko
gawa ɗaya Lami ta taɓa ba, sai da ta kulle ɗakin sannan ta fito sanye da hijjab tana kuka ta nufi
makarantarsu, shugabar makarantar ta sanarwar komai tare da roƙonta akan tazo tayiwa yaran wanka ta
shiryasu. Sosai shugaban makarantar mai suna Malama Nusaiba ta tausaya mata tare da lallashinta ta
kuma bata baki sannan ta kira su Nuratu don saura mintuna goma a tashi a islamiyar, suma sai da tayi
masu nasiha mai ratsa jiki sannan ta shaida masu abunda ke faruwa, kuka suka fashe dashi duka, bata
hanasu ba kasancewar ba kururuwa suke yi ba. Tare suka koma gidan har da Malama, kuma kamar yanda
Na'ima ta buƙata, malamar ce tayi masu wanka sannan ta suturtasu da kikkafani. Khalil na kwance yayi ruf
da ciki akan gado, ya rasa duniya mai ke yi masa daɗi, gaba ɗaya ji yake ya tsani kansa gaba, "Why am I
even alive?" Be san sanda ya faɗi hakan ba yana mai kaiwa katifa nausuka kamar zararre! Burum Aina'u ta
faɗo ɗakin tare da kama ƙugu tana kallonsa idanu a ƙanƙance, da sauri ya miƙe zaune yana kallonta
gabansa na faɗuwa don duk lokacin da ta zuba masa idanu haka, matsanaicin tsoronta yake ji har gabansa
na bugawa da sauri-sauri. Nuna kanta tayi tare da faɗin, "Ni! Ni zaka wulaƙanta Khalil saboda kaga matarka
da ƴaƴanka? Wato idan mutuwa zanyi sai dai in mutu ko? Ka san cewar ban kawo ba, amma saboda tsabar
iskanci da wulaƙanci shine ka sauka ka barni da wahala ko?" Ko mai Khalil bai iya ce mata ba, ji yake
ƙirjinsa yayi masa wani irin zafi da ƙunci, hawaye ne yaji suna neman zubowa amma bai basu sararin haka
ba, yana jin mugun tsanar Aina'u kamar ya kasheta, amma yana jin sam ko afuska ba zai iya nuna mata
hakan ba, duk haushi da tsanar da yake yi mata, idan har suka haɗa idanu sai yaji komai ya washe. "Ina
magana ka min shuru! Mahaukaciya ka mayar dani ko kuma me?" Ta faɗi a tsawace. Sam Khalil bai tsorata
da tsawarta ba, amma yana ɗagowa suka haɗa idanu da Aina'u be san lokacin da ya furta, "Kiyi haƙuri dan
Allah" ba. Harararsa tayi tare da faɗin, "Idan kana so inyi haƙuri in yafe maka, ka tashi yanzu ka sauka ƙasa
ka samu ruɓaɓɓiyar matarsa ka koreta ita da ƴaƴanta, idan ba haka ba kuma...." Ta ƙarisa maganar tare da
jan ɗan yatsarta akan kuyanta. Ƙura mata idanu Khalil yayi ko kyaftawa bai yi ba, wani uban tsawar ta kuma
daka masa tare da faɗin, "Ko baka ji bane?" Da sauri ya miƙe tare da faɗin, "As you wish Ai'n!" Yana gama
faɗin haka ya gittata ya fita daga ɗakin. Wani irin tsalle Aina'u ta daka tare da faɗin, "Yyyesss!" Khalil na fita
daga ɗakin wasu zafafan hawaye suka shiga zubowa daga idanunsa har zuwa kan ƙirjinsa, kamar kwai ya
fashe a cikinsa haka ya riƙa takawa har zuwa ƙofar ɗakin Sarah. Ya jima tsaye kamun ya saka hannu ya
murɗa handle ɗin ƙofar ya shiga, duƙe take a bakin gado tana sakawa Sam'an wando, da farin ciki gami da
ihu yace, "Daddy!" Yana mai nuna shi da hannu. Da sauri Sarah ta waiga tana kallon Khalil ɗin dake bakin
ƙofa yana kallon ƙasa hawaye na tsiyayo masa har yana ɗiga a ƙasa. Kallon su Sam'an tayi tare da faɗin,
"You two should go and play in the parlour, will meet you there in the next two minutes!" Da sauri Sauban
yace, "With daddy?" Ya faɗi hakane yana mai nunasa da hannu. Ɗaga masa kai tayi tare da sauko dashi
daga kan gado, dukkansu sai da suka yi shaking hannun daddynsu, har zasu wucesa sai ya dawo dasu baya
ya rungume a jikinsa tare da fashewa da kuka yana mai shafa fuskansu. Sarah ce ta ƙariso wajen itama
kukan take yi sosai tare da kama hannunsu ta fitar dasu sannan ta jawo ƙofar ta rufe. Kallonsa ta riƙa yi
hawaye na zubar mata, shi kuma kansa a ƙasa yana zubda hawaye kuma ya kasa ɗagowa ya kalleta,
"Happiness!" Ta kira sunansa a hankali. Da wani irin ƙarfi ya jawota jikinsa ya rungume ƙas tare da sakin
kuka kamar yaro, irin ruƙon da yayi mata sai da taji kamar haƙarƙarinta zai ɓaɓɓalle, "Ɗan sassauta kaɗan."
Sarah ta faɗi muryanta na rawa don wani irin shauƙi da missing ɗin mijinta ne ya dirar mata, "Saraaah!" Ya
kirayi sunanta cikin wani irin raunataccen murya tare da riƙeta gam-gam yana jin wani irin natsuwa na
mamayesa, don ba zai iya tuna when last ya riƙeta haka ba. "Sarah meke faruwa damu! Sarah na haukace,
ban cikin hayyacina, ban san meke faruwa dani ba, ina jin kamar an ɗauke Khalil ɗin dake cikin jikina,
Saratuuuuuu." Ya ƙarasa kiran sunansa tare da fashewa da kuka jikinsa na rawa. Wani irin tausayinsa ne ya
mamaye zuciyarta, soyayya da ƙaunarsa na kuma ruruwa a zuciyarta, a lokaci guda kuma tana aikawa
Aina'u da kwandon tsinuwa na raba tsakaninsu da tayi. Don Sarah duk wannan abubuwan dake faruwa har
ganinsa turmi da taɓaryan da tayi da Aina'u, bai taɓa sakawa taji ta tsaneshi ba, saboda tayi imani duk
abunda yake yi ba'a cikin hayyacinsa yake ba, sai dai baƙin ciki da takaici kam ta ɗebe shi iya ɗiba, don ta
tabbata da za'a gwada zuciyarta, za'a tabbatar ta samu matsala, Hassan jini kuwa idan yana kaiwa million,
to nata sai ya wuce, don babu ranar da bata kwana ta kuma tashi da ciwon kai mai tsanani. "Addu'a itace
makamin mumini daddyn twins, ka tashi tsaye ka kai kukanka gaban Ubangiji! Ka rage bacci ka raya
darenka wajen roƙon ubangiji, ka yawaita saurarar karatun Alƙur'ani in Sha Allah duk wani abun da yake
damunka a zuciyarka zai yaye kuma zaka samu sauƙi. Mun samu jin daɗin duniya, mun bar ubangiji shiyasa
Allah ya barmu, amma idan muka miƙa wuya zuwa ga mahalicci, komai zai wuce kamar ba'a yi ba." Ƙara
rungumeta yayi tare da faɗin, "Hakane! Hakane!! Maganar ki haka take Mine." Sun kusa mintuna biyar a
haka suna jin bugun zuciyar juna kumun zuwa can yayi saurin janyeta a jikinsa ya nufi wardrobe tare da
soma zubo da kayan sawanta dana su twins a kan gado kuma a lokaci guda yana kuka. Da sauri ta nufesa
tare da kamo hannunsa tana faɗin, "Haolii menene haka? Mai yasa kake fiddo mana da kayan sawarmu?"
Fincike hannunsa tayi ba tare da yace mata komai ba ya cigaba da fito da kayan kuma yana hawaye. Ƙara
kamo hannun nasa tayi tare da faɗin, "Menene haka Khalil!" Da ƙarfi yace,"Ki sake ni Mine, ki sake ni dan
Allah!" Ya faɗi tare da sakin rigar da ya ɗauko ya zauna a bakin gadon tare da riƙe kansa yana kuka. Duƙawa
tayi a gabansa itama tana kukan tare da soma faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir!" Tun tana maimaitawa ita
kaɗai har shima Khalil ɗin ya ɗauka, duk sai suka cika ɗakin da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un."
Aina'u dake ɗaki tana kallon komai a tafin hannunta ta kwaso da uban gudu har tana a dungure a steirs, ko
kamun ta ida dungurowa ta saka yatsa ta caki tafin hannunta da ƙarfi, a take Khalil dake zaune ya zabura da
ƙarfi tare da ture Sarah ya shiga faɗin, "Tashi! Ki tashi ki kwashi duka kayanki ku bar min gida ke da yaranki
sai na neme ki!! Ki tashi nace!!!" A kiɗime Sarah ta tashi don ba ƙaramin ruɗewa tayi ba da jin wawan
tsawar da ya buga mata. Ƙaton akwatinta ya jawo tare da soma loda kayanta dana yaran a ciki dai-dai
lokacin da Aina'u ta banko ƙofar ɗakin ta shigo tana huci, "Wato kai kake haɗa mata kayan ko? To zo ka fice
ta haɗa da hannunta." Idanu jazir Sarah ta kalli Aina'u tare da faɗin, "Aina'u ke ƴar wuta ce babu tantama!
Baza ki taɓa gamawa da duniya lafiya. Fir'auna Kina samanki yake Aina'u. Uwa da uba ɗaya suka haife mu,
amma wallahi tallahi billahil azeem bazan taɓa yafe maki ba ko da zanga kabarinki naci da wuta! Kin shiga
tsakani na da mijina, kin shiga tsakani uwa da ƴaƴanta, Aina'u mutuwarki abun tsoro ce wallahi." Wani irin
shu'umin murmushi Aina'u tayi tare da kallon Khalil tace, "Kana jin abunda take faɗi baza ka ɗau mataki
ba?" Khalil dai bai ce komai ba, Sarah kuma a zuciye ta ƙarisa wajen Aina'u tare da wanke fuskanta da mari
hagu da dama tare da fashewa da kuka tana faɗin, "Allah ya tsine maki Aina'u, Allah ya tsine maki albarka
muguwa azzaluma, mara imani! A kafuran ma ke dutse ce, makamashin wutan jahannama! Yanzu baki ji
komai ba Aina'u? Ki kwanta da mijina agaba da ƴaƴana Aina'u! Mijin yarki Aina'u!! Anya akwai tsoka a
ƙirjinki kuwa? Aina'u ke ƴar wuta ce!" Wani kallo Aina'u tayiwa Khalil tare da faɗin, "Kamar yanda ta ɗaga
hannu ta wanke fuskata da mari, haka nake so ka ɗaga naka hannun ka wanke fuskanta da mari, ka nuna
mata babu wanda ya isa ya taɓa ni a gabanka ya zauna lafiya ko uban wanene kuwa!" Da sauri Khalil ya ce,
"Aina'u......" "Don as I said!" Ta katse shi da ƙarfi. Juyawa yayi ya kalli Sarah tare da nuna mata ƙofa yace,
"Get out of this house right now, and don't forget to go with your kids!" Hawaye kawai Sarah keyi tana
kallonsa, irin kallon kar kayi min haka. Juya baya yayi yana hawaye gabansa na wani irin faɗuwa. Sarah
kuwa wani irin kuka ne ya kufce mata, da sauri ta ƙarisa kusa dashi ta ɗuka tare da riƙe ƙafafunsa ta shiga
faɗin, "Happiness, Kar Kayi min haka, ka manta alƙawarin da kayi min? Ka manta kace min zamu kasance
tare, for better for worse, ka mance kace baza ka taɓa bari nayi hawayen baƙin ciki ba, ka manta kace an
halicceni ne domin ka, kai ma Kuma an halicce ka ne domin ni? Ka dubi girman Allah ko don Sam'an da
Sauban ka barni a ɗakin mijina." Da ƙarfi Aina'u tace, "Capital NO! You're more welcome. Park your things
and get lost!" "Da mijina nake magana ba dake ba Aina'u!" Sarah ta faɗi da ƙarfi. Wani shu'umin murmushi
Aina'u tayi tare da faɗin, "To ai shi kansa mijin da umarnina yake amfani. Ko baki san ni nace ya kore ki
ba?" Sarah bata bata amsa ba ta cigaba da yiwa Khalil magiya. Tureta Khalil yayi tare da faɗin, "Please
Sarah, don't make things worse, just do as I said." Yana gama faɗin haka ya tashi ya fita. Aina'u sai da tayi
mata gwalo sannan ta fice daga ɗakin, "Sarah ki tashi kawai ki tafi kar ƴar iskan nan ta saka Khalil ya yanke
igiyoyin aurenki dake kansa." Wata zuciyar ta faɗa mata haka. Da sauri ta tattare kayan ta zuba a akwati ta
zuge zip tare da saka hijjab sannan ta jawo akwatin zuwa parlour ta ɗauki Sam'an ta riƙe Sauban kuma ta
goya shi, sai da ta ƙarewa parlourn kallo sannan ta murɗa handle ta fita tana kuka, tana zuwan wajen gate,
kamar ance ta juyo, sai ta ganshi a bayanta yana hawaye, buɗe hannunta yayi tare da saka mata Atm card
ɗinsa tare da faɗin, "Current account, date of birth ɗinki ne pin ɗin. Ki kular min da kanki da yaranmu."
Caraf Sarah ta rike hannun tana kuka tana girgiza masa kai, shima hawayen yake yi tare da ƙoƙarin kwatar
hannunsa, da kyar ya zame hannun tare da yiwa Sam'an kiss a goshi yace, "I'm going to miss you son, ku
tayani neman gafarar mummynku." Yana gama faɗin haka ya juya da sauri. Kuka sosai Sarah tayi ta rusawa
kamun ta juya tare da jan akwatin suka fice daga gidan..........

( _Wannan scene ɗin ya taɓa min Heart 😭 da gaskiyar Sarah da tace Aina'u ƴar wuta ce_)

*Kuyi haƙuri da rashin ganin update jiya, transformer ɗin mu ce ta buga*

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_MATAR SAYYADEE_*

*Paid book 08128755583*


Sai da ta juyo ta kuma ƙarewa gidan kallo sannan ta soma tafiya tana hawaye, kasancewar gidan babu nisa
da bakin titi nan da nan ta iso bakin titin tana nishi don ba ƙaramin kaya bane a cikin akwatin har da
atamfofinta na lefe kusan kala ashirin a ciki wanda ba'a ɗinka ba, don ta kwashe wasu ta saka cikin
wardrobe da kuma wasu akwatinan don da maƙil yake da kaya, yanzu kuma ga kayanta dana su Sauban a
ciki sannan kuma ga goyo ga kuma Sam'an dake hannu. Tsaye tayi a bakin titin tana tunanin inda zata, don
ji tayi gaba ɗaya bata ƙaunar komawa gidansu, gashi kuma babu wani wajen da take dashi da zata je.
"Lafiya state!" Ta faɗi a bayyane tare da saurin nufa wani shagon pos dake bakin titin ta ciri dubu hamsin
tana yin hamdala a zuciya saboda taimakonta da Allah yayi wajen sa Khalil ɗin ya kawo mata ATMcard
ɗinsa da yanzu bata san yanda za tayi ba don ita bata samu sararin da ta ɗauko nata ATM ɗin ba da kuma
kuɗinta da take ajiye a ɗakin duk lokacin da Khalil ɗin yayi mata kyauta. Napep ta tsayar tace masa tashar
kawo ze kaita, shi dakansa ya fito ya saka mata akwatin a ciki sannan ta shiga, har cikin tashar ya kaita tare
da fiddo mata da kayanta sannan ta biya shi hakkinsa ta ja akwatin ta soma tafiya, nan da nan aka soma
tambayarta inda zata, "Nasarawa zani!" Da sauri wani tsoho a ciki yace, "Taho nan muje dama ke kawai
muke jira motar ta cika." Hamdala tayi cikin zuciyarta jin saura mutun ɗaya, don ta bala'in ƙosawa ta bar
kaduna. Bayan kowa ya bada kuɗin mota tare da rubuta address da number waya da suna sannan driver
yaja motar suka ɗau hanya. Sai da suka hau hanya sosai sannan gabanta ya hau faɗuwa kasancewar bata
taɓa zuwa ba, sunan garin da unguwan kawai take ji a bakin baba, ga kuma ƴan biyu da suke ta yi mata
kuka a cikin motar, sai wajajen ƙarfe biyar suka isa, daga nan ta roƙi mai motar akan y taimaka mata wanba
zata kuma bata san garin ba, nan ya sakata a motar wamba, ko da suka isa wamba, da tambaya aka kawota
layin abakwa da take ji baba Nuhu na yawan ambata matsayin layinsu. Kalle-kalle kawai take yi ta rasa inda
zata nufa, gashi isha'i ake neman yi don garin ya soma duhu, wajen wani gindin bishiya ta nufa inda ta
hango dattijai su bakwai a zaune a kan tabarma, da kyar take tafiya, Sauban yayi bacci a bayanta, Sam'an
shima haka sagale a kafaɗanta, ga kuma ƙatuwar akwati tana ja. Har ƙasa ta ɗuka bayan tayi sallama sun
amsa mata, sai duk suka zuba mata idanu suna kallonta da mamaki, gashi dai bata yi kama da mabaraciya
ba balle suyi tunanin bara tazo yi. "Sannunku da hutawa baba, Ina wuni?" Faɗin Sarah, sai gaba ɗaya suka
amsa mata da "Lafiya ƙalau." Cikin gurɓatacciyar hausarsu. "Baba dan Allah tambaya nake yi, ina neman
gidan wani ana ce masa Nuhu, amma ya jima da barin garin nan." Kallo-kallo suka shiga yi, can kuma ɗaya
daga ciki yayi wa na kusa dashi magana a kunne, sai wanda aka yiwa maganar a kunne yace, "Nuhu?
Shekarunsa nawa da barin nan, kuma kin tabbata ɗan nan ɗin ne?" Shuru Sarah tayi na ƴan wasu daƙiƙu
kamun tace, "Eh to, a yanda dai yake bamu labari ya tabbatar mana dashi haifaffan nan ne, kuma yace
sunan unguwarmu layin abakwa, sunan mahaifinsa Murtala, mahaifiyarsa kuma Zainabu! Sannan kuma ya
bar garin nan shekaru talatin da huɗu kenan, ya bar garin ne saboda ƴan uwansa basu so ya auri budurwar
da yake so kasancewar ta kirista mai suna Elizabeth ana yi mata inkiya da (Lami)." Gaba ɗaya wajen suka
ɗauka da faɗin, "La'ilaha illalah Muhammadur Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallama! Wannan ai Nuhu na
wajen mu take magana a kai!" Ɗaya daga cikinsu ya ƙarisa maganar da faɗin haka. "Ke yarinya ya kuke
dashi?" Tun kamun tayi magana wanda ke ɗan gab da ita yace, "Tun da yarinyar ta ɗuka anan nake kallon
fuskanta, babu hoton wanda na gani a kwance a fuskanta sai na ɗan uwana Nuhu." Ya ƙarisa maganar yana
share guntun hawaye. "Ƴarsa ce ni!" Sarah ta faɗi muryanta na cracking. Su uku dake wajen suka miƙe a
tare tare da faɗin, "Taso yarinya, gida kika zo, duk nan iyayenki ne." Wani irin sanyi da salama Sarah taji
yana shiga jikinta. Miƙewa tayi ta soma bin bayansu kasancewar ɗayan ya ɗauki akwatin yayi gaba, sai ya
kasance yaran ne kawai a hannunta da ƙaramin handbag ɗin da ta saya a lokacin da suka sauka. Ƙatoton
gidane irin na da ɗin nan wanda aka yi sa da ginin ƙasa, sai dai yasha gyara da abubuwan zamani, kuma
akwai wasu gina-gine guda biyu a tsakiyar gidan da aka yi su da cement blocks. Ɗaya daga cikin ginin bulo
suka nufa mai kyau dashi, Sarah sai kalle-kalle take yi hannunta dafe da bayan Sam'an dake kwance a
kafaɗanta. Hannu ya saka ya murɗa handle ɗin ƙofar tare da yin sallama sannan ya shiga. Babu kowa a
parlourn sai fankar sama dake gudu sosai. "Zauna mana, suna cikine, bari na kira su." Ya faɗi hakan yana
mai nuna mata kujera sannan ya bi wani ɗan dogon hanya a parlourn. Sarah kuwa kamun ta zauna sai da
ta gama ƙarewa tsaftaccen parlourn mai ɗauke da set ɗin kujeru da kuma Tv bango 32 inches da idanu
sannan ta shimfiɗar da Sam'an a kan 3sitter tare da kwanto Sauban sannan ta zauna ta rungumesa tana
cigaba da ƙarewa parlourn kallo har idanunta suka sauka akan wani ƙatoton hoto a jikin bangon ɗaki ta
bangon arewa, ƙurawa hoton idanun tayi duk da kuwa irin Black and White ɗin nan ne, su huɗu ne reras a
jikin hoton, waro idanu tayi sosai tana ƙara kallon hoton da kyau, baba Nuhu ne zaune a kan wata farar
kujeran ƙarfe shigen irin ta sarauta, sai wani ta gefen hagunsa mai irin kamanninsa babu bambanci yana
murmushi sannan ya dafa mai kama dashi sak ɗin nan dake zaune a kan kujera, sai wannan mutumin da ya
kawota cikin ɗakin da take yanzu a ta gefen wanda ya dafa baba Nuhu ya ɗan leƙo shima yana murmushi,
sai shima mai kama dashi sak ta hannun damar wanda ke zaune a kan kujera ya turo hulan kansa gaba
tulun gashin da ya tara ya fito ta baya da kuma gefe-gefe kansa stil shima yana murmushi, "Inna lillahi
wa'inna ilaihir raju'un, kaii! Kenan da baba da wannan mai kama dashi ɗin ƴan biyu ne, shima kuma
wannan da ya kawo ni nan shima ɗin ƴan biyune kenan? Kenan anan nayi gadon ƴan biyu, ikon Allah!" Cike
da tsantsan mamaki tayi maganar a bayyane. Daga ƙarshe sai ta tashi ta isa wajen hoton tana kallo daga
tsaye. Da wani irin ihuu da murna taji an rungumeta ta baya, da sauri ta waigo tana mai cin karo da fuskan
wata kyakkyawar yarinya mai kama da ita, gaba ɗayansu waro idanu suka yi suna mai shafa fuskansu suna
kuma dariya at the same time, "Sunana Suhana, yarinyar wannan dake zaune a hotonan!" Suhana ta faɗi
tana mai nuna hoton wanda ke zaune, don ita Sarah a tunaninta ma shine baba Nuhu, sai Suhana ta nuna
shi matsayin mahaifinta, sai ta fahimci baba Nuhu shine na tsayan. "Abbana da Abbanki are twins!"
Suhana ta kuma faɗi tana dariya tare da kamo hannun Sarah wacce ke ta kallon fuskar Suhana kuma
murmushi yaƙi barin fuskanta. "Uwar surutu, kin tsareta da surutun ko? Ai sai ki wuce ki haɗa mata ruwan
zafi a bayi tayi wanka taji daɗin jikinta sai taci abinci." Faɗin wannan da ya kawo ta cikin gidan cikin yaren
_Nindire_, bayansa kuma wata kyakkyawar mata ce mai fara'a sosai, haƙorinta guda ɗaya na gefen dama
na Makka ne sai kyalli yake yi. "Wallahi ga kama nan, ai surprise zamu bawa su Ya Hassan da Nnanne, sai
da safe tukun duk zasu ganta." Faɗin matar tana kallon Suhana tare da faɗin, "Saura kuma kije ki faɗa
masu, don na sanki da tsinannan surutu!" Turo baki Suhan tayi tare da faɗin, "kaji ta ko Ba Lukman!" Da
sauri Sarah ta kalli wanda Suhan ɗin ta kira da Ba Lukman tana murmushi gano ashe wanta Lukman sunan
wannan ɗin baba ya saka masa. "Baki faɗa mana sunanki ba yarinya!" Faɗin Ba Lukman. Sunkuyar da kai
Sarah tayi tare da faɗin, "Sunana Saratu!" Da sauri ba Lukman yace, "Kai! Kai!! Kai!!! Suna mai girma da
daraja Nuhu ya saka maki, ai sunan wacce ta riƙe mu duka kenan har shi bayan mutuwar mahaifiyarmu,
kuma ita ɗin ƙanwace ga mahaifiyarmu uwa ɗaya uba ɗaya." Murmushi Sarah tayi yayin da matar Ba
Lukman ta nufi inda twins suke tana kallonsu, "Tubarkalla ma sha Allah! Kaga ƴaƴa kyawawa kamar su suka
yi kansu, ni wannan ma ai sun fiku nuna kamanni, taɓ! Zan iya bambance su kuwa?" Ta faɗi cikin yare,
Sarah da bata jin ko zo in kashe ka, sai binsu da idanu take yi. Ba Lukman ma ƙarisawa kusa dasu yayi yana
kallonsu cike da ƙaunarsu daidai lokacin da Sauban ya farka yana mai furta, "Mummyyyy, I want to piii." Ko
kamun tayi wani motsi har Suhana ta isa wajen tare da sunkutoshi, shi kuwa bai mata ƙiwa ba, don suna
matukar kama da Sarah shiyasa bai gane ba Sarah bace ta ɗauke shi, po ta ɗauko wankakke tas kamar ba'a
komai a ciki ta ɗaurasa a kai, tana kallon fuskansa, "Momma, har da pupu zan yi!" Dariya Suhana tayi tare
da faɗin, "To kayi!" Kallonta Sauban yayi ta yi kamar yana so ya gano ba mummynsa bace, sai da ya gama
kashin ta wanke masa, wajen mayar masa da wando suka soma faɗa don yaƙi sam ya mayar da wandon,
daga ƙarshe sai ya lankwashe ƙafar yana kuka, leƙowa Suhana tayi tare da faɗin, "Yaƙi yarda in mayar masa
da wando." Sarah nufar akwatinsu tayi ta kwantar tare da fiddo masa wani wandon ta miƙawa Suhan tana
mai faɗin, "Ai su haka suke, idan suka yi pupu basu taɓa yarda su mayar da wandon jikinsu sai dai wani."
"Yaran nawa ashe ƴan gayu ne!" Faɗin Suhana bayan ta karɓi wandon. "Saratu ki shiga wancen bayin kiyi
wanka sai kizo kici abinci." Kai sunkuye Sarah tace, "To Baba!" Ta ƙarisa maganar tare da cire hijjab ɗin
jikinta ta ninke ta ajiye a hannun kujera sannan ta nufi bayi. Suhana na dawowa parlourn Sam'an shima ya
tashi, sai ta haɗa su ta rungume duka a jikinta. Bayan Sarah ta fito daga wanka, sai Suhana ta nuna mata
ɗakin da zata shiga domin tayi shiri ita kuma ta nufi bayi da twins domin yi masu wanka. Sarah tana shiga
ɗakin, ko mai bata shafa ba, riga kawai ta zura tare shimfiɗa dardumar da ta gani a gefen gado tare
shimfiɗawa ta saka hijjab ta tada sallah, sai da tayi na magrib da isha sannan ta kuma tada sallah tayi
raka'a biyu, a sujadarta na ƙarshe ta shiga kwararo bukatun tana kuka sosai. Ta jima a sujada tana kai
kukanta ga mahaliccinta......

_Anticipate a long page tomorrow, wallahi har yanzu ban jin daɗi, Wannan ma dakyar nayi_

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
Bayan ta idar da sallar, sai ta jingina da gado tana tunanin Khalil hawaye na zubo mata, hannu ta ɗaga
sama tare da faɗin, "Ubangiji mahaliccin sammai da ƙassai, mai kowa mai kome, ga bawanka nan Ibrahim,
ka kiyaye shi daga sharri da tsafin Aina'u, ga kwato shi daga hannun azzaluma mara imani Aina'u, ya Hayyu
ya Ƙayyumu, alfarman soyayyar dake tsakaninka da mafificin halitta, Muhammadur Rasulullah (SAW) ka
ceto mijina daga halakar Aina'u ya rabbis samawati al'ardi." Ta ƙarisa maganar tare da fashewa da kuka.
Juyawa tayi ta kai hannu kan handbag ɗinta dake kan gado tare da buɗe zip domin ta ɗauko wayarta, a
firgice ta soma zazzage jakarta tana neman wayarta mai tsada da Khalil ya canza mata ranar da suka yi
celebrating first anniversary ɗinsu bayan haihuwar twins. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Wallahi to duk
yanda aka yi a tasha aka sace wayar nan, shikenan I missed everything including our history pictures!!"
Faɗin Sarah tana mai fashewa da kuka, don sam ba satar wayar bane yafi tsaya mata a rai, hotuna da
videos ɗin dake cikin wayar ne wanda dawowarsu zai yi matuƙar wuya ke mugun bata takaici. Jin alamar
ana nufo ɗakin sai tayi saurin goge hawayenta tana mai ƙirƙirar smiling face tana ɗaurawa a nata fuskan.
"Assalamu alaikum, Maman twins kin idar?" Faɗin Suhana, ganin Sarah a zaune sai ta juya ta koma
parlourn, can sai gata da abincin a rufe a plate, murmushi Sarah tayi mata tare da faɗin, "Nagode Suhan."
Murmushin itama Suhan ɗin tayi mata tare da faɗin, "Bari naje parlour wajen su twins, don har yanzu basu
gane bake bace ba." Ta faɗi hakane tare da miƙewa ta fita. Bayan fitan ta, Sarah sai ta buɗe plate ɗin,
alalen gwangwani ne yaji miyan source da hanta. Guda ɗaya kawai Sarah ta iya ci ta rufe, don da kyar take
haɗiyewa saboda damuwar dake cinta a rai, data rufe idanunta, Khalil kawai take gani yana yi mata gizo,
idan ta tuna lokacin da suke farin ciki kamun zuwan Aina'u, sai taji daɗi har sai hakan ya bayyana a
fuskanta, idan kuma ta tuna baƙin cikin da Aina'u ta ƙunsa mata, sai taji hawaye na wanke fuskanta. Wani
ƙaramin ƙur'ani ta gani irin mai zip ɗin nan a side drawer, hannu ta kai ta ɗauko tare da zuge zip ɗin ƙasa,
ajiyar zuciya ta saki tana mai ƙoƙarin tuna when last ta riƙe ƙur'ani a hannunta ta karanta, kuka ta fashe
dashi ganin ta kasa tuna wani lokaci ne na ƙarshe data ɗauki Qur'ani domin karatu, ko a can gida sai dai
idan zata goge ta saka masa turare take ɗauka, amma bayan haka kam, bata ɗauka domin niyyar karatu,
har akai azumi guda biyun da tayi a gidan Khalil, bata taɓa karatun ƙur'ani ba, sai dai ana yin asham wani
lokacin har da tahajjut kasancewar masallacin a cikin gidansu Khalil ɗin yake, "Dole ko mai aka yi mana ya
kama mu tunda mun saki Allah mun kama Duniya!" Faɗin Sarah cikin zuciya. Suratul Yusuf ta buɗe ta soma
karantawa don surar na ɗaya daga cikin surorin da take matuƙar so a cikin Alqur'ani don sai da ta haddace
tsaf amma rashin muraji'a yasa duk ya zube, suratul Ma'ida, Maryam, Buruj da Nisa'i, don Nisa'i ma gaba
ɗaya surar ta haddace ita da Kahfi, don lokacin da suke tashin ƙawance da Muneeba, duk juma'a sai sun
sauketa don musaffa suke yi. Sarah bata iya baccin kirki ba, Allah yaso ma Suhan tazo tayi mata sallama a
kan tare zasu kwana a ɗayan ɗakin ita da ƴan biyu, ita kuma Sarah anan ta kwana ita kaɗai, sai dai rabi da
kwata na cikin daren, raya shi tayi da tsayuwan dare saboda ta kasa baccin. A idanunta akai sallar asubah,
abunda yayi matuƙar burgeta a gidan shine, tun bayan saukowar masallaci take jin sautukan ƙira'a
mabanbanta na Alkur'ani cikin muryoyin maza da mata ya ɗume gidan, sai kawai itama ta hau karatu da
wannan ƙur'anin data gani a ɗakin. Sai ƙarfe takwas daidai taji gidan ya ɗauki tsit, sai itama ta saka aya
sannan ta rufe ƙur'anin tana mai yin sujada ɗon ta tsaya ne a kan ayar da ake sujada. Suhan ce ta shigo ita
da twins har anyi masu wanka amma sun ƙi yarda ko wando ta saka masu, akwatin kayansu Sarah ta buɗe
tare da fiddo kayansu ta mikawa Suhan ɗin tare da rufe akwatin ta miƙe tsaye tana nannaɗe dardumar,
"Maman twins ki fito za muje muyi breakfast, you will be shock idan muka shiga side ɗin Nnanne." Ba tare
da ta cire hijjab tabi bayan Suhan data rigata fita, Sarah tayi mamaki ganin duk da twins sun ganeta amma
basu ƙoƙarin gudu daga wajen Suhan ba duk ƙiwarsu. Bata taras da kowa ba a parlourn, duk sun hallara
ɗakin Nnanne, "Ina su Ba Lukman?" Faɗin Sarah, "Suna can ɗakin Nnanne." Suhan ta bata amsa tare da
fita both hannunta na ɗauke da twins. "Da kin ajiyesu su taka da ƙafursu, sai baki wahala suke yi." Faɗin
Sarah, su kuwa twins najin haka suka ƙare lafewa a jikin Suhan, Suhan Kuma cewa tayi, "Ai wallahi ban
sauke su." Dariya kawai Sarah tayi don ta lura Suhan ɗin na matuƙar ƙaunar twins, itama sai taji tana
ƙaunar Suhan ɗin. Sun ɗan yi tafiya kamun suka iso sashen Nnanne da yake da girman ban mamaki, ga
uban uban takalma birjik a ƙofar ɗakin na maza da kuma na mata. Sallama su Sarah suka yi kamun suka
shiga ciki, da maɗaukakin mamaki Sarah ta take kallon jama'ar dake ɗakin suna zazzaune akan ƙatuwar
carpet ɗin dake shimfiɗe a ɗakin sun zagaye wata farar tsohuwa mai mugun kwarjini da kuma kamala
kasancewar mai riko da ibada, ta tsufa sosai, amma babu ruɗewa a tattare da ita saboda zuciya da gangan
jikinta sun ginu ne akan Addinin Allah cikin tafarkin _SUNNAR MA'AIKI SAW_. Suna shigowa gaba ɗaya
idanu ya koma kan Sarah da kuma ƴan biyu dake hannun Suhan, gyaran muryan Nnanne tayi, sai koma ya
dawo cikin nutsuwarsa don sun san dokar, babu mai magana har sai an kammala cin abinci kamun nan ake
gabatar da meeting na tsawon awanni biyu rak, a dunƙule Sarah ta gaishe da duk manyan wajen, cike
kuma da sakin fuska suka amsa mata gaisuwarta sannan suka nemi waje suka zauna, daga nan ƴan aikin
gidan wanda a ƙalla sun kai ashirin suka gabatar da abinci, daga kowa yayi serving kansa, tunda aka fara cin
abinci babu wanda ya ƙara ko kwakwkwarar motsi har suka kammala sannan ƴan aiki suka ƙara zuwa suka
kwashe komai. Nnanne kuwa tun da takai lomar abinci ɗaya baki take kallon Sarah har ta kammala baya yi
cokali biyar kwarara ba. Shuru gaba ɗaya ɗakin yayi ana jiran Nnanne ta soma yin magana don hakane zai
bawa Kowa damar yin magana, ita kuwa Nnanne taƙi magana sai kallon Sarah da take yi kawai babu
kyaftawa, "Yarinya!" Ta faɗi slowly still tana kallon Sarah. A hankali Sarah ta ɗago tana kallon Nnanne, nan
take taji wasu irin ruwan hawaye na kwaranyo mata akan fuskanta ganin gaba ɗaya ɗakin nan da take duk
yawansu ƴan uwan mahaifinta ne. "Yarinya daga ina, kuma ke wacece?" Nnanne ta kuma jeho mata wata
tambayar, Sai da Sarah taja majina kamun tace, "Sunana Sarah, mahaifina kuma sunansa Nuhu kuma a nan
gidan aka haifesa." Ta faɗi hakan tana mai nuna Ba Nura (Mai kama da Baba Nuhu) tare da cigaba da faɗin,
"Sak haka Babana yake" ta ƙarisa maganar tare da rushewa da kuka tuno halin da Baba yake ciki na
mutum-gawa. Wani irin ajiyar zuciya Nnanne tayi tare da soma goge hawayen da yake shirin zubowa,
matan ɗakin masu raunin zuciya har sun soma kuka, Nnanne miƙawa Sarah hannu tayi alamar ta taho kusa
da ita, da rarrafe Sarah ta ƙarisa tare da rungumeta ta fashe da tsumamman kuka wanda ya taɓa zuciyar
mutane da dama dake ɗakin. "Ina ɗana? Ina kika baro min Hussaini na!" Faɗin Nnanne cikin kuka. Ƙara
kwakwuneta Sarah tayi tare da faɗin, "Ina can Kaduna, Yana can Nnanne kullum bashi da magana sai taku,
duk lokacin da zai bani labarinku, cemin yake yi ba zai iya haɗa idanu daku ba saboda abunda ya aikata
maku. Nnanne baba yana can kwance kamar gawa, ba magana babu motsi!" Sarah na kowa nan sai ta
kuma fashewa da kuka sosai har tana ƙanƙame jikinta duk kukan gaba ɗaya da biyu take yinsa, tunowa
take da halin da Baba yake ciki da kuma halin da take ciki yanzu, sai kukan ya zama biyu. Kuka Nnanne ta
fashe dashi wanda ya tada hankalin dattijan dake ɗakin sai duk suka taso suka zagayeta suna bata baki. "Na
janye dokar da na saka akan Hussaini, na janye wallahi. Kuje ku taho da ɗan uwanku, kuje Hassan ku taho
dashi. Ina son ganinsa kamun na koma ga Allah. Na yafe masa har abada, na yafe maka Nuhuna." Ko
wannensu sai da ya share guntun hawaye. Ba Lukman kuwa wani irin farin cikine ya lulluɓesa yana mai jin
daɗin saukowar Nnanne, domin ba dadun ita ba, da tuni sun nemi Baba Nuhu a duk inda yake." Hannun
Nnanne a kan Sarah tare da faɗin, "Jikanta kuma takwarata, bani labarin ɗana Nuhu!" Gyara zama Sarah
tayi tare da faɗin, "Nnanne idan har kina da ƙarfin zuciyar ji, to ki saurareni sai dai labarin Babana ko kuma
ince maki dukkanmu, ba labari bane mai daɗin ji!" Gaba ɗaya ɗakin wani irin tsit yayi na wasu daƙiƙu
kamun Sarah taja wani numfashi tare da soma faɗin...., "Tun da nake ban taɓa ganin mutum mai haƙuri da
sauƙin kai kamar mahaifina ba, mu shidda ya haifa mata sai namiji ɗaya, Na'ima, Nuratu, Hassana, Lukman
(Tana faɗin sunan Lukman, Ba Lukman ya ɗago don ya san tabbas shi akai wa takwara) Marfu'a, Ni Saratu
da kuma autarmu Aina'u......." Tun daga karayar arzikin baba, taɓarɓarewar tarbiyansu Na'ima da irin
karuwancin da suka zuba sanadin huɗubar Lami, lalacewar Lukman, sanadin shiga islamiyarta, aikin da tayi
a restaurant wanda shine sanadin haɗuwarta da Khalil, cikin da yayi mata zuwa zubewarsa,
gwagwarmayar da aka yi kamun auran da kuma auren, farin cikin da ta samu a gidan zuwa ciwon da tayi na
tsutsa da irin kulawar da Khalil ɗin ya bata har zuwan Aina'u gidan, haihuwarta, ciwon Baba (duk da bata
faɗa masu sanadi ba don itama bata sani ba) da kuma iskanci da mulkin da Aina'u ta zuba har izuwa
sanadin barowarta kaduna duk sai da ta zayyane masu tana kukan fitar hayyaci. Ba ita kaɗai ba, gaba ɗaya
ɗakin yara da manya kuka suke yi, "Haka Nuhu yaga rayuwa? Yanzu ƴaƴan Nuhu ne suka yi karuwanci har
da ƴaƴan shegu! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!!" Faɗin Nnanne tana mai dafe saitin zuciyarta, ɗaya
hannunta kuma yana riƙe da hannun Sarah dake kuka. Gaba ɗaya ɗakin babu wanda bai ji mugun tausayi
Sarah ba jin halin bala'in data shiga sanadin ƙanwarta ciki ɗaya! "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!
Nnanne!!" Ba Lukman ya faɗi da ƙarfi ganin Nnanne zata dungura don suma tayi. Nan da nan suka kwashe
ta zuwa asibiti. Sai da Hajiya tayi sati tana jinya kamun aka sallame don jininta ne ya hau sosai, Sarah kuwa
taga ƙaryar wani abu wai shi dangi, don kuwa irin jama'ar dake tururuwar zuwa ganinta sunfi ƙarfin a ƙirga,
wannnan ya jata riiii zuwa gidansa, sai wancen ma yaja. Ɓangaren Hajiya kuwa, tun bayan tafiyar Sarah da
kwana biyu wanda bata ma san bata gidan ba ta tashi tsaye sosai akan roƙon Allah, waya ta buga
Maiduguri tare da faɗin buƙatunta wajen wani babban malamin musulunci tace a haɗa almajirai suyi mata
sauka zata turo da abun sadaka ta waya, sannan ta kira malamin da yake masu saukar Qur'ani tun lokacin
da Alai yake da rai, ta faɗa masa buƙatunta, kasancewar girma yà kama shi sosai, sai ya saka ƴaƴansa da
almajirasa suka cika gidan Hajiya da karatu, ranar ba'a gidan Aina'u da Khalil suka kwana ba, ihu ta riƙa
masa a kan su bar gidan, sai da aka haɗa kwanki goma ana sauka a gidan tare da buɗe gidan da hayaƙin
shaiɗanu. A rana ta goma sha huɗu, Aina'u ta taso Khalil suka dawo gidan, kai tsaye ɗakin Hajiya ta nufa
tana kwala kiran, "Bilkisu! Bilkisu!! Ki fito nan tsohuwar munafuka annaminiya" tana tafiya hannunta riƙe
dana Khalil har parlourn Hajiya, da sauri Hajiya ta fito tana ƙarewa Aina'u dake riƙe da hannun Khalil kallo,
"Menene haka nake gani Khalilullah!" Hajiya ta nuna hannun Aina'u dake riƙe dana Khalil fuskanta ɗauke
da mamaki, " _ƙanwar matarka_ ce fa Ibrahim!" Wani wawan harara Aina'u ta jefi Hajiya dashi tare da yin
wani irin dariyar ƴan iska sannan wani janyo Khalil ɗin tare da riƙo kansa ta haɗe bakinsu waje ɗaya. Da
sauri Hajiya ta rintse idanunta gabanta na wani irin bugawa tana istigfari cikin zuciya. "Wallahi kika ƙara yin
magana akan alaƙata da ɗanki, yanzu gabanki zan sutale masa wando kuma kina kallo zai yi amfani dani,
wata ƙila na har rabo ya shiga tsakani!" Wasu irin zafafan hawayene suka shiga kwaranyo daga idanun
Hajiya har tsikar jikinta na tashi, "Na taso maki da sha'awar shekaru ko? Kar ki damu idan ƙaiƙayi yake
maki, inada mutane dai-dai dake da zasu iya biya maki buƙata." Wani irin kuka Hajiya ta fashe dashi mai
ƙarfi kuma har wannan lokacin idanunta a rufe suke, "Ibrahim a gabanka, a gabanka _Ƙanwar matarka_
take faɗa min irin wannan maganar amma ka kasa ko tari mai ƙarfi, a gabanka Mu'azzam!!" Hajiya ta faɗi
tana kuka. Khalil kuwa tunda ya sunkuyar da kanshi a ƙasa hawaye masu uban gudu suke sauka a akan
tiles, ya kasa ko ɗagowa, jikinsa ne kawai ke karkarwa. "Ba kukanki nazo inji a nan ba, zuwa nayi inyi maki
kashedi akan kar ki kuskura ki kuma kiran wasu ƴan iska gidan nan suzo suna yin tsaface-tsaface, kinji ko
baki ji ba?" Wani irin haske ne ya gilma a fuskan Aina'u har sai da taji shock, Hajiya ta nuna mata ƙofar fita
tare da faɗin, "Wa ya haifi ubanki da har zaki shigo cikin gidan ChiefJustice Nurudden kice zaki bawa
matarsa order, fita kamun na saka a ƙarar da zuri'ar ku!" Hajiya ta faɗi a tsawace. Baya Hajiya tayi zata faɗi
saboda wani gigitacen mari da Aina'u ta ɗauketa dashi tare da faɗin, "Kul! Kika ƙara ɗaga hannunki a jikina.
In kwanta da ɗan naki in bashi natsuwa har sai da ya manta sunanki, shine zaki saka min da mari, ƙarya
kike yi wallahi!" Hannu dafe da kunci Hajiya ta kalli Khalil da ya tarota tare da zaunar da ita a kan kujera,
"Khalil har lalacewaka ta kai haka? A gaban idanunka _Ƙanwar matarka_ ta ɗaga hannu ta mare Ni." Jikin
Khalil wani irin rawa yake yi har naman jikinsa na ɗagawa haƙorinsa na haɗuwa dana juna a lokacin guda
gashin dake kwance a jikinsa suna wani irin mimmiƙewa, idanunsa kuwa sun koma wani irin abun tsoro
saboda yanda suka kaɗa sukai jazur............

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[29/10, 12:57 PM] Rahamanatu: Ganin yanda gaba ɗaya yanayinsa ya canza, sai ta soma ja da baya kaɗan-
kaɗan tana kuma murza tafin hannunta a lokaci guda, sai dai gabanta ne ya yanke ya faɗi da ƙarfin tsiya jin
bata ji wannan sanyin da ta saba ji ba a duk lokacin da ta murza tafin hannun, da saurin ta fiddo tafin
hannun tana kallo gabanta na wani irin zullon tashin hankali, "Na shiga uku tafin hannuna yayi baƙi!" Ta
faɗi da ƙarfi ganin har hayaƙi yake yi, a dai-dai wannan lokacin ne kuma Khalil ya wani irin shaƙo wuyanta
tare da ɗagata ya buga a ƙasa dai-dai lokacin da Laure ta shigo parlourn da gudu tana faɗin, "Inna lillahi
wa'inna ilaihir raju'un! Hajiya hayaƙi a ɗakinki." Cak ta tsaya tana mai kai hannu kan maƙogwaronta tare da
kallon Hajiya da itama take kallonta cikin tsantsan mamaki da kuma farin ciki. Laure nuna bakinta tayi
sannan ta nuna Hajiya cikin mamaki, hajiyan sai ta gyaɗa mata kai alamar eh tabbas taji fitar muryanta.
Kuka Laure ta fashe dashi tare da kai goshinta ƙasa tayi sujada. Khalil kuwa wani irin kwallon tashin hankali
ya riƙa yi da Aina'u tana buguwa da edge ɗin bangon ɗakin yana faɗin, "Mahaifiyata kika ɗaga hannu kika
mara? Mahaifiyar tawa!!" Baki, kai da hancin Aina'u sai tsiyayar da jini yake yi tsabar naushi da Khalil ke
aza mata, da sauri Hajiya ta nufi Khalil tare da faɗin, "Mu'azzam ka sake kyaketa haka, ka kyaleta nace!"
Faɗin Hajiya da ƙarfi, shi kuwa Khalil bai saurareta ba ya cigaba da naushin Aina'u a duk inda ya samu a
jikinta, fuska, baki, ciki da ƙirjinta duk sun nausu, sai da Hajiya ta shiga tsakiya tukunna Khalil ya dakata da
dukanta, ita kuwa Aina'u sai tsiyayar da jini take yi, tafin hannunta kuwa ta murza yafi sau shurin masaƙi.
Ganin Hajiya a tsakiyarsu, da sauri ta rarrafa ta fice daga ɗakin ta nufi ɓangaren Sarah riƙe da cikinta. Tana
shiga sama ta haura zuwa ɗakin Khalil ɗin tare da duƙawa ta janyo tukunyar tsafinta, sai dai tana gama
fuddoshi ya bada sautin fuuus ya watse a ɗakin, nan da nan ɗakin ya ɗauki wani irin ɗoyi, kuma hayan yayi
daidai da wani irin murɗawa da cikin Aina'un yayi, ƙafafuwanta su hau wani irin rawa, idanunta na wani
irin far-far-far kamar wacce kwayar idanunta zasu faɗo ƙasa, nan da nan wani irin guguwa ya tashi a
tsakiyar ɗakin na kusan tsayin mintuna biyar kamun _Hell Ofulafu_ ya bayyana a tsakiyar ɗakin rabin
fuskansa a ƙone, shi kuwa mummunar halittar nan gaba ɗaya jikinsa a ƙone yake. Wata shimfiɗeɗiyar
bulalace a hannun Hell Wanda gefe-gefe bulalan wasu irin manya-manyan ƙayoyi ne masu matukar tsini da
kaifi, jikin Aina'u wani irin rawa ya ɗauka ganin Hell da wannan bulala. Ɗaga bulalan yayi tare da shimfiɗa
mata sai da ya zagaye jikinta har zuwa kan fuskanta, wani irin ihuu ta saki wanda ya ɗauki gidan gaba ɗaya,
nan da nan jikinta ya hau tsirtuwar jini har zuwa fuskan, don bulalan yana sauka a kan fatan jikinta ya taho
da fatarta, haka ya dunga zubaba mata bulalan tana ihu tana birgima, bayan ya gama farfashe jikinta
sannan ya zaro wata doguwar ƙarfe wanda kallo ɗaya zaka yiwa Ƙarfen zaka tabbatar ya ɗauki awanni a
cikin wuta saboda irin jan da yayi. Ba tare da tausayi ba ya dunga ɗaura wannan ƙarfen a ko'ina na fatar
jikinta, Aina'u tsabar azaba ko kuka ta kasa yi sai wani jan numfashi da ta riƙa yi. Hello bai haƙura ba sai da
ya banƙare Aina'u sannan ya fiddo da wani abu kamar kwaɗo mai matukar muni da azababben wari ya
tura cikin gabanta sai har sai da tsintsiyar hannunsa ya shige ciki. Aina'u wani mahaukacin gurnani ta saki
wanda ya taho da wani mulmulallan jini da bakinta, Hell na ciro hannunsa a gabanta jini ya biyo baya
baƙiƙƙirin mai masifaffan wari. Wani irin dariya ya shiga ɓaɓɓakawa kamun ya dafa mummunar halittar
nan suka ɓace, Aina'u kuwa sai wani irin birgima da buga kanta a ƙasa take yi saboda mummunar azabar
da take yi mai wuyar fasaltuwa, bayan jinin dake biyu jikinta da gabanta, wani manya-manyan tsutsotsi da
ƙananan baƙaƙen kunamu suka shiga fitowa ta gabanta kuma masu cizo da tsungulin, Aina'u sai zaro harce
take yi tana wani irin surutan gigin azabar da take ji a cikin jikinta. Wani irin ɗaukar zafi jikinta ya soma yi
kamar ana dafa mata jikin, da kyar ta iya cire komai na jikinta tana wani irin gurnanin azaba, kuka ta fashe
dashi gani yanda tsokar naman jikinta ke yankowa yana faɗowa kuma duk tsokar data faɗo, wasu fararan
tsutsotsi ne ke mamaye wajen suna tsungulin jikinta. Hatta naman dake wuyanta zazzagowa yayi ya faɗo
kana ganin tafiyar maƙogwaronta, idanunta sunyi wani irin ɓulu-ɓulu sun zama abun tsoro, cikin ƴan wasu
mintuna gaba ɗaya kamannin Aina'u ya sauya ta koma wata abun tsoro, fuskansa ya mokaɗe, bakinta ya
turo yayi tsini kamar na kare, haƙoranta sun turo sunyi cirko-cirko a baki. Ɓangaren Hajiya kuwa, Khalil na
tsaye ya yanke jiki ya faɗi yana wani irin jijjiga kamar mai farfaɗiya, ruɗewa Hajiya tayi tana faɗin, "Inna
lillahi wa'inna ilaihir raju'un, Laure! Laure!! Laure na shiga uku ki taimaka min ya zanyi." Daidai nan aka
murɗo ƙofar aka shigo, ya Abdul-Hakeem ne da Aunty Maryam ce wacce tayi wani irin mahaukacin rama
kamar wacce ta tashi daga ciwo, "Alhamdulillah, Abdul-Hakeem taimaka min mu kaita asibiti dan Allah!" A
raunane Aunty Maryam tace, "Hajiya ba asibiti za'a kai shi ba, daddyn moon ɗauke shi ka mayar dashi kan
kujera ka bashi wannan maganin mu gani." Ta ƙarisa maganar tana mai fiddo wani goran magani a cikin
jakarta. Cicciɓarsa ya Abdul-Hakeem yayi tare da mayar dashi kan kujera sannan ya karɓi goran hannun
Aunty Maryam ya bude tare da buɗe bakin Khalil yayi bismillah ya zuba masa har sau uku. Cikin minti ɗaya
ya miƙe da sauri yana faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Ya faɗi hakane tare da ɗaura hannunsa
biyu a kai yana girgiza kai. "Hajiya meke damuwa? 'Hajiya mafarki nayi ko? Ba gaskiya bane duk abunda na
gani ko? _Ƙanwar matata_ bata zo cikin gidan nan ta raba ni da matata ba ko? Hajiya Sarah tana ɗakinta
ko?" Dafa shi Hajiya tayi tare da faɗin, "Kwantar da hankalinka Khalil, dawo cikin na tsuwarka." Da sauri
Khalil yace, "Hajiya natsuwata baza ta taɓa dawowa ba har sai kun faɗa min duk abunda nake tunanin ya
faru bai faru ba. Hajiya kinsan abunda ke min gizo a idanuna kuwa? Hajiya kin san bala'in da nake gani
kuwa!" Da wani irin ihu yake maganar domin kwanciyar da yayi da Aina'u agaban twins da Sarah kawai
yake dawo masa cikin idanunsa. "Khalil ba mafarki kake yi ba!" Faɗin ya Abdul-Hakeem. Wani irin duum
Khalil ɗin yaji a cikin kansa, "Dagaske ne na koreta, dagaske ne da kaina na kori matata, dagaske na kwanta
da _ƙanwar matata_ agaban matata da ƴaƴana. Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Wai meke faruwa dani
ne, ku faɗa min!" Ihun da yayi sai da ya razana kowa a cikin ɗakin. Ya Abdul-Hakeem ya kalli Aunty Maryam
tare da faɗin, "Mommyn moon yi masu bayanin da kika min!" Hawaye na kwaranyo a idanun Aunty
Maryam ta soma faɗin, "Hajiya tun da uwata ta haife ni, ban taɓa ganin azzaluma kuma mushrika irin
Aina'u ba, duk wani bala'in dake faruwa a cikin gidan nan sanadinta ne, Aina'u itace sanadin kurmancewar
Laure, rashin lafiyar da kika yi har ya zazzago da idanunki, rashin kiranki da ya LTG da ya barrister, domin ita
ta karkatar da hankalinsu da barin nemanki, mutuwar jinjirar Nafeesa da kuma korata da daddyn moon
yayi har da dakatar dashi da akai a wajen aiki. Aina'u matsafiyace ta gaske, domin bokanta a tare da ita
yake koda yaushe, tana matsa tafin hannunta yake bayyana a ciki, sannan kuma tana kallon komai da kowa
dake cikin gidan nan ta cikin tafin hannun, har kisa tana iya aikatawa ta hakan. A ranar da na kamata tana
magana da bokan, a ranar ta saka ya Abdul-Hakeem ya sake ni, sannan tayi min kashedi akan idan har na
faɗawa wani abunda naga tana yi, sai tayi min irin abunda tayiwa Laure. Tun da na bar gidan nan, kullum a
firgice nake kwana har na tsawon shekara ɗaya da rabi duk da cewar wata na biyu a gida baban moon ya
turo min da text akan ya mayar dani sai dai kuma inyi haƙuri ba zai iya dawo dani cikin nan gidan ba, a
hakan nayi ta hakuri ina kai wa Allah kukana babu dare babu rana, ban taɓa tunkarar kowa da Maganar ba,
sai ranar da naje taron wani wa'azi a makarantar da nayi sauka, sai nayi katari malamin yana ta wa'azi akan
harkan bin boka har da kuma addu'o'in da mutum zai lazimci yi domin kariya, tun da na fara wannan
addu'o'in babu dare babu rana ina roƙon Allah ya karya alkadarin Aina'u da tsinannun matsafanta, cikin
ƙanƙanin lokaci tsoran Aina'u ya fita daga cikin zuciyata har na nemi mijina na bashi addu'o'in shima da
kuma magungunar da zai riƙa sha da kuma turare gidan, to sai kuma kwanakin baya yazo ya faɗa min kin
kawo almajirai sunata sauke alƙur'ani, sosai hakan yayi min daɗi ganin zamu haɗa hannu mu yaƙi azzaluma
Aina'u. Khalil kayi haƙuri, Allah zai saka mana kai da matarka, domin ta cutar da kowa na cikin gidan. Kuma
Allah ba azzalumin bawansa bane, baya taɓa kama mutum da laifin da ya aikata ba da gangan ba, kayi
komai ne bisa tsafi da makirci irin na shaiɗaniya kuma annoba Aina'u." Da wani irin speed Khalil ya bar
ɗakin ya nufi nashi side ɗin, Hajiya da ya Abdul-Hakeem har da Aunty Maryam da Laure suka bi bayansa.
Khalil bai tsaya murɗa handle ɗin ƙofar ba, kafaɗa ya saka ya bugi ƙofar da wani irin mahaukacin ƙarfi sai
ga ƙofar a ɓalle, faɗawa ɗakin yayi idanunsa a rufe tsabar zafin zuciya da fusata, dai-dai nan ya Abdul-
Hakeem ya faɗo ɗakin shima, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Faɗin ya Abdul-Hakeem da ƙarfi saboda
ganin wani mummunar halitta mai ban tsoro a nannane kuma fatar jiki na zagwanyewa sannan tsutsotsi na
fita, ga kuma ƙananan kunamu baƙaƙe masu cizo dake fitowa daga gaban Aina'u, gaba ɗaya tayi watsi da
kayan dake jikinta. Rintse idanu yayi tare da faɗin, "Allahumma arji'ini fi musibati wa aklifni khairan minha,
wannan wacece haka? Hajiya kar ki shigo don Allah!" Ya fadi don baya son Hajiyar ta razana. Amma tuni
Hajiyar ta sako kai ta shigo ɗakin, zuuu ta tafi zata faɗi saboda razanar da tayi ganin Aina'un. "Nice Aina'u,
ku taimaka min ku kaini asibiti, wallahi mutuwa zan yi, ku taimaka min!" Faɗin Aina'u, wanda bai san
abinda ta aikata ba, dole yaji tausayin halin da take ciki. Maƙogwaro a waje, tsokar fata sai yankowa take
tana faduwa tsutsa na cin ramin wajen da tsokar ta faɗo, ga tsutsotsi da baƙaƙen ƙananan kunamun dake
fitowa daga gabanta masu azabar harbi da ciwo, idanu sun zazzago, baki ya turo uwa na kare, ga kuma zafi
da mummunar wari da jikinta yake yi, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Faɗin Hajiya tare da fashewa da
kuka tana faɗin, "Aina'u, kece kika dawo haka? La haula wala quwata illah Billah! Aina'u kin ga ƙarshen
aikata sharri ko!" Hajiya na ida zancenta Aina'u ta ɗuka kamar kare ta hau kukan jaki kamar zata fasa ɗakin,
can kuma kamar an tambayeta ta soma confessing abubuwan data aikata, "Abia naje nayi mummunar tsafi
domin in samu zuciyar Khalil, ban san sau nawa wani inyamuri mai suna Ugo yayi amfani dani ba, nayi
kwanaki cikin tukunyar tsafi, sannan na kashe mutane babu adadi, daga cikin akwai jikanki ƴar wajen
Nafeesa, ni na sadaukar da jininta wa Hell, sannan nice na kashe Nafeesa da mijinta ta hanyar tura aljani ya
tsotse jininta sannan ya bude tukunyar gas wanda hakan yayi sanadin rayuka da dama. Nice na kashe
ƴaƴan ƴan uwana duka ta hanyar tura aljani ta suffar maciji ya sare shi, nice na kashe ɗan adaidaita sahu
saboda rashin tafiya da sauri da yayi har na rasa damar kashe ƴan biyun Sarah tun suna jarirai, Ni ce na
tura Muneeba cikin duniya wanda har yanzu tana ta tafiya bata san inda kanta yake ba, nice nayi wa Khalil
mummunar tsafi yayi ta amfani dani ba cikin hayyacinsa ba, sannan nice na tura na saka Hell ya tura aljami
mantau cikin kwakwalwar Ya Abdullah da ya barrister domin su manta dake Hajiya har abada, nice nayi
asiri Abdul-Hakeem ya saki matarsa domin ta gano sirina, sannan na saka aka dakatar dashi daga wajen
aiki, kuma duk na samu ƙarfin tsafin nan ne ta silar kwanciyar aure da nayi da mahaifin da yayi sanadin
zuwana duniya domin hakan shine cikar tsafina, na samu nasarar kwanciya dashi ne ta sanadin tsafin da
nayi masa sannan na juye masa sak Lami, sai bayan ya gama amfani dani sannan hankalinsa ya dawo
jikinsa, baƙin cikin haka ya saka ya yanke jiki ya faɗi, dalilin faɗuwar da yayi shine silar ciwon da yake fama
dashi yanzu na shanyewar ɓarin jiki." Tsabar zuciyar Hajiya ta kasa ɗaukar abunda taji daga bakin Aina'u,
faɗuwa ƙasa tayi a sume. Khalil kuma yayi kan Aina'u da dukan fitar rai. Sai Abdul-Hakeem ya rasa wa zai
riƙe a cikinsu, daka ƙarshe dai ya bawa Hajiya taimakon gaggawa ta hanyar fitar da ita daga ɗakin ya
yayyafa mata ruwa, sai da ta farfaɗo tukun ya koma ɗakin ya riƙe Khalil dake neman kashe Aina'u, "Baka da
hankali ne Khalil? Mai yasa zaka kashe gawar da ba taka ba? Ai wannan yarinyar bata buƙatar komai na
hukunci daga gare mu, hukuncin da Allah ma yayi mata tun a nan duniyar ya isheta wallahi." "Ka barni na
kasheta dan girman Allah Ya Abdul-Hakeem!" Fadin Khalil yana kuka sosai. "Wallahi ba zan bari ka rage
mata nauyi ba. Ɗan yatsarka ɗaya ma ba zan bari ya kuma taɓata ba." Ya faɗi tare da kama hannunsa ya
fito da shi daga ɗakin sannan ya jawo karyayyan ƙofar ya rufe. Ƙasa suka sauka inda Hajiya take tana kuka
sosai, idanunta sun kaɗa sunyi jajur tuno autarta Nafeesa. Kallon Khalil Hajiya tayi tare da faɗin, "Kaga
sakamakon rashin ji ko Khalil? Da ace baka ɗurawa ƴar mutane ciki ba, yaushe har wannan bala'in zai shigo
cikin gidan mu. Ka kwaso mana dangin matsafa, dangin masifa da bala'i cikin gidanmu muna zaune lafiya!
Me za ayi da irin wannan tsinannen zuri'a, wallahi haɗa zuri'a da irin yarinyar nan mafisa ce babba rayuwa,
ina jin dama ace ban haifeka ba Khalil, da duk haka bai faru damu ba. Sanadinka rayuka da dama sun
salwanta, ƴata, autata Nafeesa ta kashe min ita, ta ashe ƴarta wacce idan ina ganinta zanji sanyi, ta kashe
mijin, ta kashe kowa! Allah ya isa tsakani na da wannan ƴar iskan yarinyar. Ibrahim, aurenka da Saratu bai
amfane mu da komai ba sai bala'i da masifa, kuma ka rubuta ka ajiye, idan har nice nayi naƙuda sannan na
tsuguna na haifeka, ba amince maka ka dawo da Saratu cikin gidan nan ba, ƴaƴa kuma a dawo dasu zan
riƙe!"

_Wacece take ganin Hajiya bata kyauta ba? Ni dai na fahimci ciwon da take ji_ 😬🤐

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[29/10, 12:57 PM] Rahamanatu: Bayan ta idar da sallar, sai ta jingina da gado tana tunanin Khalil hawaye
na zubo mata, hannu ta ɗaga sama tare da faɗin, "Ubangiji mahaliccin sammai da ƙassai, mai kowa mai
kome, ga bawanka nan Ibrahim, ka kiyaye shi daga sharri da tsafin Aina'u, ga kwato shi daga hannun
azzaluma mara imani Aina'u, ya Hayyu ya Ƙayyumu, alfarman soyayyar dake tsakaninka da mafificin halitta,
Muhammadur Rasulullah (SAW) ka ceto mijina daga halakar Aina'u ya rabbis samawati al'ardi." Ta ƙarisa
maganar tare da fashewa da kuka. Juyawa tayi ta kai hannu kan handbag ɗinta dake kan gado tare da buɗe
zip domin ta ɗauko wayarta, a firgice ta soma zazzage jakarta tana neman wayarta mai tsada da Khalil ya
canza mata ranar da suka yi celebrating first anniversary ɗinsu bayan haihuwar twins. "Inna lillahi wa'inna
ilaihir raju'un! Wallahi to duk yanda aka yi a tasha aka sace wayar nan, shikenan I missed everything
including our history pictures!!" Faɗin Sarah tana mai fashewa da kuka, don sam ba satar wayar bane yafi
tsaya mata a rai, hotuna da videos ɗin dake cikin wayar ne wanda dawowarsu zai yi matuƙar wuya ke
mugun bata takaici. Jin alamar ana nufo ɗakin sai tayi saurin goge hawayenta tana mai ƙirƙirar smiling face
tana ɗaurawa a nata fuskan. "Assalamu alaikum, Maman twins kin idar?" Faɗin Suhana, ganin Sarah a
zaune sai ta juya ta koma parlourn, can sai gata da abincin a rufe a plate, murmushi Sarah tayi mata tare da
faɗin, "Nagode Suhan." Murmushin itama Suhan ɗin tayi mata tare da faɗin, "Bari naje parlour wajen su
twins, don har yanzu basu gane bake bace ba." Ta faɗi hakane tare da miƙewa ta fita. Bayan fitan ta, Sarah
sai ta buɗe plate ɗin, alalen gwangwani ne yaji miyan source da hanta. Guda ɗaya kawai Sarah ta iya ci ta
rufe, don da kyar take haɗiyewa saboda damuwar dake cinta a rai, data rufe idanunta, Khalil kawai take
gani yana yi mata gizo, idan ta tuna lokacin da suke farin ciki kamun zuwan Aina'u, sai taji daɗi har sai
hakan ya bayyana a fuskanta, idan kuma ta tuna baƙin cikin da Aina'u ta ƙunsa mata, sai taji hawaye na
wanke fuskanta. Wani ƙaramin ƙur'ani ta gani irin mai zip ɗin nan a side drawer, hannu ta kai ta ɗauko tare
da zuge zip ɗin ƙasa, ajiyar zuciya ta saki tana mai ƙoƙarin tuna when last ta riƙe ƙur'ani a hannunta ta
karanta, kuka ta fashe dashi ganin ta kasa tuna wani lokaci ne na ƙarshe data ɗauki Qur'ani domin karatu,
ko a can gida sai dai idan zata goge ta saka masa turare take ɗauka, amma bayan haka kam, bata ɗauka
domin niyyar karatu, har akai azumi guda biyun da tayi a gidan Khalil, bata taɓa karatun ƙur'ani ba, sai dai
ana yin asham wani lokacin har da tahajjut kasancewar masallacin a cikin gidansu Khalil ɗin yake, "Dole ko
mai aka yi mana ya kama mu tunda mun saki Allah mun kama Duniya!" Faɗin Sarah cikin zuciya. Suratul
Yusuf ta buɗe ta soma karantawa don surar na ɗaya daga cikin surorin da take matuƙar so a cikin Alqur'ani
don sai da ta haddace tsaf amma rashin muraji'a yasa duk ya zube, suratul Ma'ida, Maryam, Buruj da
Nisa'i, don Nisa'i ma gaba ɗaya surar ta haddace ita da Kahfi, don lokacin da suke tashin ƙawance da
Muneeba, duk juma'a sai sun sauketa don musaffa suke yi. Sarah bata iya baccin kirki ba, Allah yaso ma
Suhan tazo tayi mata sallama a kan tare zasu kwana a ɗayan ɗakin ita da ƴan biyu, ita kuma Sarah anan ta
kwana ita kaɗai, sai dai rabi da kwata na cikin daren, raya shi tayi da tsayuwan dare saboda ta kasa baccin.
A idanunta akai sallar asubah, abunda yayi matuƙar burgeta a gidan shine, tun bayan saukowar masallaci
take jin sautukan ƙira'a mabanbanta na Alkur'ani cikin muryoyin maza da mata ya ɗume gidan, sai kawai
itama ta hau karatu da wannan ƙur'anin data gani a ɗakin. Sai ƙarfe takwas daidai taji gidan ya ɗauki tsit,
sai itama ta saka aya sannan ta rufe ƙur'anin tana mai yin sujada ɗon ta tsaya ne a kan ayar da ake sujada.
Suhan ce ta shigo ita da twins har anyi masu wanka amma sun ƙi yarda ko wando ta saka masu, akwatin
kayansu Sarah ta buɗe tare da fiddo kayansu ta mikawa Suhan ɗin tare da rufe akwatin ta miƙe tsaye tana
nannaɗe dardumar, "Maman twins ki fito za muje muyi breakfast, you will be shock idan muka shiga side
ɗin Nnanne." Ba tare da ta cire hijjab tabi bayan Suhan data rigata fita, Sarah tayi mamaki ganin duk da
twins sun ganeta amma basu ƙoƙarin gudu daga wajen Suhan ba duk ƙiwarsu. Bata taras da kowa ba a
parlourn, duk sun hallara ɗakin Nnanne, "Ina su Ba Lukman?" Faɗin Sarah, "Suna can ɗakin Nnanne."
Suhan ta bata amsa tare da fita both hannunta na ɗauke da twins. "Da kin ajiyesu su taka da ƙafursu, sai
baki wahala suke yi." Faɗin Sarah, su kuwa twins najin haka suka ƙare lafewa a jikin Suhan, Suhan Kuma
cewa tayi, "Ai wallahi ban sauke su." Dariya kawai Sarah tayi don ta lura Suhan ɗin na matuƙar ƙaunar
twins, itama sai taji tana ƙaunar Suhan ɗin. Sun ɗan yi tafiya kamun suka iso sashen Nnanne da yake da
girman ban mamaki, ga uban uban takalma birjik a ƙofar ɗakin na maza da kuma na mata. Sallama su
Sarah suka yi kamun suka shiga ciki, da maɗaukakin mamaki Sarah ta take kallon jama'ar dake ɗakin suna
zazzaune akan ƙatuwar carpet ɗin dake shimfiɗe a ɗakin sun zagaye wata farar tsohuwa mai mugun
kwarjini da kuma kamala kasancewar mai riko da ibada, ta tsufa sosai, amma babu ruɗewa a tattare da ita
saboda zuciya da gangan jikinta sun ginu ne akan Addinin Allah cikin tafarkin _SUNNAR MA'AIKI SAW_.
Suna shigowa gaba ɗaya idanu ya koma kan Sarah da kuma ƴan biyu dake hannun Suhan, gyaran muryan
Nnanne tayi, sai koma ya dawo cikin nutsuwarsa don sun san dokar, babu mai magana har sai an kammala
cin abinci kamun nan ake gabatar da meeting na tsawon awanni biyu rak, a dunƙule Sarah ta gaishe da duk
manyan wajen, cike kuma da sakin fuska suka amsa mata gaisuwarta sannan suka nemi waje suka zauna,
daga nan ƴan aikin gidan wanda a ƙalla sun kai ashirin suka gabatar da abinci, daga kowa yayi serving
kansa, tunda aka fara cin abinci babu wanda ya ƙara ko kwakwkwarar motsi har suka kammala sannan ƴan
aiki suka ƙara zuwa suka kwashe komai. Nnanne kuwa tun da takai lomar abinci ɗaya baki take kallon Sarah
har ta kammala baya yi cokali biyar kwarara ba. Shuru gaba ɗaya ɗakin yayi ana jiran Nnanne ta soma yin
magana don hakane zai bawa Kowa damar yin magana, ita kuwa Nnanne taƙi magana sai kallon Sarah da
take yi kawai babu kyaftawa, "Yarinya!" Ta faɗi slowly still tana kallon Sarah. A hankali Sarah ta ɗago tana
kallon Nnanne, nan take taji wasu irin ruwan hawaye na kwaranyo mata akan fuskanta ganin gaba ɗaya
ɗakin nan da take duk yawansu ƴan uwan mahaifinta ne. "Yarinya daga ina, kuma ke wacece?" Nnanne ta
kuma jeho mata wata tambayar, Sai da Sarah taja majina kamun tace, "Sunana Sarah, mahaifina kuma
sunansa Nuhu kuma a nan gidan aka haifesa." Ta faɗi hakan tana mai nuna Ba Nura (Mai kama da Baba
Nuhu) tare da cigaba da faɗin, "Sak haka Babana yake" ta ƙarisa maganar tare da rushewa da kuka tuno
halin da Baba yake ciki na mutum-gawa. Wani irin ajiyar zuciya Nnanne tayi tare da soma goge hawayen da
yake shirin zubowa, matan ɗakin masu raunin zuciya har sun soma kuka, Nnanne miƙawa Sarah hannu tayi
alamar ta taho kusa da ita, da rarrafe Sarah ta ƙarisa tare da rungumeta ta fashe da tsumamman kuka
wanda ya taɓa zuciyar mutane da dama dake ɗakin. "Ina ɗana? Ina kika baro min Hussaini na!" Faɗin
Nnanne cikin kuka. Ƙara kwakwuneta Sarah tayi tare da faɗin, "Ina can Kaduna, Yana can Nnanne kullum
bashi da magana sai taku, duk lokacin da zai bani labarinku, cemin yake yi ba zai iya haɗa idanu daku ba
saboda abunda ya aikata maku. Nnanne baba yana can kwance kamar gawa, ba magana babu motsi!"
Sarah na kowa nan sai ta kuma fashewa da kuka sosai har tana ƙanƙame jikinta duk kukan gaba ɗaya da
biyu take yinsa, tunowa take da halin da Baba yake ciki da kuma halin da take ciki yanzu, sai kukan ya zama
biyu. Kuka Nnanne ta fashe dashi wanda ya tada hankalin dattijan dake ɗakin sai duk suka taso suka
zagayeta suna bata baki. "Na janye dokar da na saka akan Hussaini, na janye wallahi. Kuje ku taho da ɗan
uwanku, kuje Hassan ku taho dashi. Ina son ganinsa kamun na koma ga Allah. Na yafe masa har abada, na
yafe maka Nuhuna." Ko wannensu sai da ya share guntun hawaye. Ba Lukman kuwa wani irin farin cikine
ya lulluɓesa yana mai jin daɗin saukowar Nnanne, domin ba dadun ita ba, da tuni sun nemi Baba Nuhu a
duk inda yake." Hannun Nnanne a kan Sarah tare da faɗin, "Jikanta kuma takwarata, bani labarin ɗana
Nuhu!" Gyara zama Sarah tayi tare da faɗin, "Nnanne idan har kina da ƙarfin zuciyar ji, to ki saurareni sai
dai labarin Babana ko kuma ince maki dukkanmu, ba labari bane mai daɗin ji!" Gaba ɗaya ɗakin wani irin
tsit yayi na wasu daƙiƙu kamun Sarah taja wani numfashi tare da soma faɗin...., "Tun da nake ban taɓa
ganin mutum mai haƙuri da sauƙin kai kamar mahaifina ba, mu shidda ya haifa mata sai namiji ɗaya,
Na'ima, Nuratu, Hassana, Lukman (Tana faɗin sunan Lukman, Ba Lukman ya ɗago don ya san tabbas shi
akai wa takwara) Marfu'a, Ni Saratu da kuma autarmu Aina'u......." Tun daga karayar arzikin baba,
taɓarɓarewar tarbiyansu Na'ima da irin karuwancin da suka zuba sanadin huɗubar Lami, lalacewar
Lukman, sanadin shiga islamiyarta, aikin da tayi a restaurant wanda shine sanadin haɗuwarta da Khalil,
cikin da yayi mata zuwa zubewarsa, gwagwarmayar da aka yi kamun auran da kuma auren, farin cikin da
ta samu a gidan zuwa ciwon da tayi na tsutsa da irin kulawar da Khalil ɗin ya bata har zuwan Aina'u gidan,
haihuwarta, ciwon Baba (duk da bata faɗa masu sanadi ba don itama bata sani ba) da kuma iskanci da
mulkin da Aina'u ta zuba har izuwa sanadin barowarta kaduna duk sai da ta zayyane masu tana kukan fitar
hayyaci. Ba ita kaɗai ba, gaba ɗaya ɗakin yara da manya kuka suke yi, "Haka Nuhu yaga rayuwa? Yanzu
ƴaƴan Nuhu ne suka yi karuwanci har da ƴaƴan shegu! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!!" Faɗin Nnanne
tana mai dafe saitin zuciyarta, ɗaya hannunta kuma yana riƙe da hannun Sarah dake kuka. Gaba ɗaya ɗakin
babu wanda bai ji mugun tausayi Sarah ba jin halin bala'in data shiga sanadin ƙanwarta ciki ɗaya! "Inna
lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Nnanne!!" Ba Lukman ya faɗi da ƙarfi ganin Nnanne zata dungura don suma
tayi. Nan da nan suka kwashe ta zuwa asibiti. Sai da Hajiya tayi sati tana jinya kamun aka sallame don
jininta ne ya hau sosai, Sarah kuwa taga ƙaryar wani abu wai shi dangi, don kuwa irin jama'ar dake
tururuwar zuwa ganinta sunfi ƙarfin a ƙirga, wannnan ya jata riiii zuwa gidansa, sai wancen ma yaja.
Ɓangaren Hajiya kuwa, tun bayan tafiyar Sarah da kwana biyu wanda bata ma san bata gidan ba ta tashi
tsaye sosai akan roƙon Allah, waya ta buga Maiduguri tare da faɗin buƙatunta wajen wani babban malamin
musulunci tace a haɗa almajirai suyi mata sauka zata turo da abun sadaka ta waya, sannan ta kira malamin
da yake masu saukar Qur'ani tun lokacin da Alai yake da rai, ta faɗa masa buƙatunta, kasancewar girma yà
kama shi sosai, sai ya saka ƴaƴansa da almajirasa suka cika gidan Hajiya da karatu, ranar ba'a gidan Aina'u
da Khalil suka kwana ba, ihu ta riƙa masa a kan su bar gidan, sai da aka haɗa kwanki goma ana sauka a
gidan tare da buɗe gidan da hayaƙin shaiɗanu. A rana ta goma sha huɗu, Aina'u ta taso Khalil suka dawo
gidan, kai tsaye ɗakin Hajiya ta nufa tana kwala kiran, "Bilkisu! Bilkisu!! Ki fito nan tsohuwar munafuka
annaminiya" tana tafiya hannunta riƙe dana Khalil har parlourn Hajiya, da sauri Hajiya ta fito tana ƙarewa
Aina'u dake riƙe da hannun Khalil kallo, "Menene haka nake gani Khalilullah!" Hajiya ta nuna hannun
Aina'u dake riƙe dana Khalil fuskanta ɗauke da mamaki, " _ƙanwar matarka_ ce fa Ibrahim!" Wani wawan
harara Aina'u ta jefi Hajiya dashi tare da yin wani irin dariyar ƴan iska sannan wani janyo Khalil ɗin tare da
riƙo kansa ta haɗe bakinsu waje ɗaya. Da sauri Hajiya ta rintse idanunta gabanta na wani irin bugawa tana
istigfari cikin zuciya. "Wallahi kika ƙara yin magana akan alaƙata da ɗanki, yanzu gabanki zan sutale masa
wando kuma kina kallo zai yi amfani dani, wata ƙila na har rabo ya shiga tsakani!" Wasu irin zafafan
hawayene suka shiga kwaranyo daga idanun Hajiya har tsikar jikinta na tashi, "Na taso maki da sha'awar
shekaru ko? Kar ki damu idan ƙaiƙayi yake maki, inada mutane dai-dai dake da zasu iya biya maki buƙata."
Wani irin kuka Hajiya ta fashe dashi mai ƙarfi kuma har wannan lokacin idanunta a rufe suke, "Ibrahim a
gabanka, a gabanka _Ƙanwar matarka_ take faɗa min irin wannan maganar amma ka kasa ko tari mai ƙarfi,
a gabanka Mu'azzam!!" Hajiya ta faɗi tana kuka. Khalil kuwa tunda ya sunkuyar da kanshi a ƙasa hawaye
masu uban gudu suke sauka a akan tiles, ya kasa ko ɗagowa, jikinsa ne kawai ke karkarwa. "Ba kukanki
nazo inji a nan ba, zuwa nayi inyi maki kashedi akan kar ki kuskura ki kuma kiran wasu ƴan iska gidan nan
suzo suna yin tsaface-tsaface, kinji ko baki ji ba?" Wani irin haske ne ya gilma a fuskan Aina'u har sai da taji
shock, Hajiya ta nuna mata ƙofar fita tare da faɗin, "Wa ya haifi ubanki da har zaki shigo cikin gidan
ChiefJustice Nurudden kice zaki bawa matarsa order, fita kamun na saka a ƙarar da zuri'ar ku!" Hajiya ta
faɗi a tsawace. Baya Hajiya tayi zata faɗi saboda wani gigitacen mari da Aina'u ta ɗauketa dashi tare da
faɗin, "Kul! Kika ƙara ɗaga hannunki a jikina. In kwanta da ɗan naki in bashi natsuwa har sai da ya manta
sunanki, shine zaki saka min da mari, ƙarya kike yi wallahi!" Hannu dafe da kunci Hajiya ta kalli Khalil da ya
tarota tare da zaunar da ita a kan kujera, "Khalil har lalacewaka ta kai haka? A gaban idanunka _Ƙanwar
matarka_ ta ɗaga hannu ta mare Ni." Jikin Khalil wani irin rawa yake yi har naman jikinsa na ɗagawa
haƙorinsa na haɗuwa dana juna a lokacin guda gashin dake kwance a jikinsa suna wani irin mimmiƙewa,
idanunsa kuwa sun koma wani irin abun tsoro saboda yanda suka kaɗa sukai jazur............

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[29/10, 12:57 PM] Rahamanatu: Hajiya na gama faɗin haka ta miƙe ta fita fuuu tana sharar hawaye. Khalil
kuwa mutuwar tsaye yayi a wajen yana jin wani irin matsanaicin bugun zuciya kamar zata faso ƙirjinsa ta
fito, Abdul-Hakeem kallonsa yayi tare da ɗaga hannunsa yana shafa ƙirjinsa alamar he should calm down
sannan ya fita ya bi bayan Hajiya. Aunty Maryam ƙarisowa tayi kusa da Khalil tare da faɗin, "Khalil ka
kwantar da hankalinka, in Sha Allah Hajiya zata sauko. Maganar laifi kuma, ba laifin Sarah bane, Sarah bata
da laifi akan abinda Aina'u ta aikata, ita kanta Sarah ai Aina'un ta cutar da ita, don wannan tsutsotsin da ta
riƙa fitarwa warin nan ai babbar cutarwa ce! In Sha Allah hajiya zata sauko, don tabbas babu laifin Sarah a
cikin abinda Aina'u ta aikata, kuma wallahi ko da ba Sarah ka aura ba, Aina'u sai ta shigo cikin gidan nan ta
wata hanya daban ta cutar damu don hakan rubutacce ne a cikin ƙaddarar mu, kuma muma duk muna da
namu laifin na sake da muka yi da Allah muka kama jin daɗin duniya, mun manta da azkar da karatun
Alƙur'ani wanda Alai ya gina a cikin gidan nan, mun ɗauka kawai salloli biyar da azumin watan Ramadan
ɗin da muka riƙe kawai sune dolen mu. Wannan izinace a gare mu dukanmu. Amma tabbas Sarah bata da
laifin komai, kuma ina ji a jikina zata sauko nan kusa, yanzu dai shawarar da zan baka itace, tunda har
Hajiya tayi fushi haka har ta furta waɗannan kalamai, ka kyaleta na wasu lokaci, kar ka kuskura ka
tunkareta da maganar, ka bari har ta huce tukun." Gyaɗa kai Khalil yayi tare da faɗin, "Shikenan, Nagode
Aunty Maryam!" Yana faɗin haka ya fita ya bar ɗakin, side ɗin Hajiya ya koma ya nufi ainahin ɗakinsa dake
sashen, buɗe Ƙofar yayi ya shiga ciki, ɗakin nan kamar yanda yake, bayi ya nufa ya dunga cuɗa kansa kamar
zai yage fatar dake jikinsa saboda tuna ya haɗa jiki da Aina'u. Ya jima kamun ya fito daga wanka, wajen
mirror ya nufa yana ƙarewa kansa kallo ganin yanda ya koma kamar mahaukaci, gashin kansa yayi buzu-
buzu babu gyara. Hawaye zafafa yaji suna biyo ƙirjinsa sakamakon tuno duk abubuwan da yayiwa Sarah,
"Hajiya ki taimakeni kar ki raba ni da uwar ƴaƴata!" Ya faɗi yana mai zama a kan kujerar dake gaban mirror
ɗin tare da ɗaura kai a kan drawer. Ya jima a haka kamun ya tashi ya saka don ko shafa mai bai yi ba.
Fitowa yayi daga ɗakin, kiciɓis suka yi da Laure a ƙofar ɗakinsa, kanta a ƙasa don kuka take yi tace, "Ya kalif
kaje inji Hajiya!" Ba tare da yace komai ba ya gittata ya wuce. Ɗakin hajiyan ya nufa, sai da ya Kwankwasa
sannan ya shiga ciki, zaune ya same tana waya kamar zata taune harshe don masifa, "To shikenan sai kazo
goben, don wasu abubuwan ma baza su faɗu ba har sai ka iso, ku taho kai da Ayshan." Faɗin Hajiya. Tun da
tace ku taho kai da Ayshan, Khalil ya fahimci da Ya Abdullahi take magana. Ajiye wayar tayi tare da kallonsa
tace, "Khalilullah, ka dai ji abunda na faɗa maka ko? Tom! Yanzu abunda nake so da kai, kayi maza ka tashi
ka tafi gidansu yarinyar nan ka taho min da jikokina, sannan ka tabbatar kamun ka dawo cikin gidan nan ka
tsinke igiyar dake tsakaninka da ita, sannan gobe in Sha Allah idan Marmari daga nesa ya iso yaga wannan
la'ananniyar yarinyar data tarwatsamin gida, zaka nemo akori kura a kwasheta a kai ta gidan iyayenta can
susan yanda za suyi da ita, mu baza mu yafe mata ba, amma kuma baza muyi mata komai ba domin Allah
ya riga ya soma nuna mata iyakarta tun a nan gidan duniya! Sauran kuma sai mun je can. Don haka ka tashi
maza ka bar gidan nan kayi abunda na umarce ka da kayi." Ta ƙarisa maganar tana mai nuna masa hanya.
Ya kwashi kusan mintuna biyu jikinsa na rawa kamun ya miƙe ya fita daga ɗakin. Kai tsaye parking lot ya
nufa ya buɗe mota ya shiga yayi reverse ya bar gidan, a hanya babu abunda yake yi sai goge zufa kuma a
lokaci guda gabansa na wani irin bugawa da ƙarfin tsiya, kuma hakan ƙara faruwa ne idan ya ƙara kusa da
unguwarsu Sarah. A ƙofar gidan yayi parking sannan ya fito daga cikin motar, glasses ɗinsa ya fiddo ya saka
saboda yanda idanunsa suka yi jazur. Kallon layin ya riƙa yi, domin tunda ya saya masu gidan zai iya irga
zuwansa unguwar. Gaban gate ɗin gidan ya tsaya tare da kai hannu ya Kwankwasa gidan sau uku, jin
alamar ana cire jamlock sai ya ɗan matsa baya kaɗan yana jiran a buɗe Ƙofar. Murmushi ta sakar masa tare
da faɗin, "Ah Khalil kai ne a gidan namu yau? Wallahi yanzu muka gama magana da mama (Lami,
kasancewar malamar mu ta hana su kiran sunanta kai tsaye. Tace masu hakan rashin tarbiyya ne da nuna
rashin ɗa'a ga mahaifiya )" Faɗin Na'ima wacce gaba ɗaya ta rame kamar ba Na'ima ƴar gayu ba.
Murmushin kawai ya iya mata, "Shigo mana ka tsaya a tsaye." Ta faɗi tare da matsa masa, shigowa yayi
yana mai ƙara gyara zaman glasses ɗin fuskansa, a tsakar gidan ya taras da Lami da sauraran ƴaƴanta, sai
dai yaji gidan tsit ba kamar yanda ya saba jin hayaniyar yaransu ba aduk sanda ya leƙo, kasancewar yana
zuwa masu da abun motsa baki, suna jin muryansa ko da basu tsakar gidan suke fitowa da gudu suna masa
oyoyo. Har ƙasa Khalil ya tsuguna tare da faɗin, "Mama ina wuni, na same ku lafiya?" Sai da Lami ta ƙura
masa idanu na kusan tsayin mintuna biyu kamun tace, "Lafiya Khalil? Shin kayi dogon jinya ne? Amma
Saratu bata kyauta ba da bata zo ta faɗa ba, ashe shiyasa kenan babu ganta wajen zaman makoki ba!"
Faɗin Lami cikin jimami. Gaban Khalil ne ya buga da wani irin ƙarfi jin abunda Lami tace, amma kuma sai
yayi saurin kawar da hakan cikin ransa tare da furta, "Mama wanene ya mutu har akai zaman makoki bamu
sani ba?" Nuna su Na'ima tayi tare da faɗin, "Gaba ƴaƴansu ne suka mutu sakamakon saran maciji!"
Na'ima har idanunta sun cicciko da hawaye sakamakon tado mata da mikin da Lami tayi. Khalil kuma sai
yanzu ya tuna abunda Aina'u tace lokacin da take confessing, cewar ta tura maciji ya sari duka ƴaƴan gidan
ta bawa bokanta jininsu. "Wannan yarinyar tsinanniya ce ta ƙarshe!" Faɗin Khalil cikin zuciya. Shuru yayi na
wasu lokaci kamun yace, "Mama idan babu damuwa ina son magana da dukkan ku dan Allah, amma
kamun nan bari na duba Baba tukun." Jinjina kai Lami tayi, yayin da shikuma ya miƙe ya nufi ɗakin baba
wanda har yau yana nan kwance kamar gawa. Sallama yayi tare da saka hannu ya cire takalmin ƙafarsa sau
ciki sannan ya shiga, baba na nan kwance a kan gadon, Sai dai cikin tsafta yake don ba ƙaramin ƙoƙari su
Na'ima suke yi ba wajen kula da tsaftar baban kasancewar anan yake bowali da bahaya! Har gaban gadon
Khalil ya jawo kujera tare da zama sannan ya kamo hannun baba dake bacci tare da soma faɗin, "Baba kayi
haƙuri duk da nasan cewar kalmar ciwo zata ƙara saka maka cikin zuciya! Tabbas ko da ban san ainahin
ciwon da kake ji ba matsayin ka na uba, amma zan iya ɗan kwatanta ko da kaɗan ne. Kayi haƙuri, shine
kawai abunda zan iya ce maka. Sannan in Sha Allah baba bazan taɓa bari rayuwar Sarah dana sauran
ƴaƴanka ya taɓarɓare ba kamar na Aina'u, nayi maka wannan alƙawarin, zan tsaya tsayin daka a kansu, Ni
ba sirikinka bane kawai, Ni ɗane a wajenka kuma yayyinsu Na'ima. Kai kuma Baba in Sha Allah zaka warke
kuma ka cigaba da harkokinka kamar da. Kayi haƙuri baba!" Abunda ya matuƙar bawa Khalil mamaki jin
Baba ya ɗamki hannunsa ya riƙe gam-gam kuma a lokaci guda hawaye na zirarowa daga kwarmin idanunsa
har suna shiga kunnensa. Khalil ɗaura ɗayen hannunsa yayi a kan na Baba tare da riƙe hannun da ƙarfi
yana kallon fuskan baban dake a rufe kuma yana zubar da hawaye. "Kayi haƙuri baba, in Sha Allah zaka
samu cikakken lafiya." Baba magana yake so yayi, amma babu damar haka, a zuciyarsa kuwa cewa yake,
"Dan girman Allah Ibrahim kar ka nema min lafiya, ka barni a haka, ni fatana ɗaya in koma ga Allah cikin
gaggawa kuma tare da imani, don baƙin cikin dake cin zuciyata ni kaɗai na san shi. Dan Allah Khalil ka barni
a haka." Da kyar Khalil ya iya zame hannun Baba a cikin nashi sannan ya fita daga ɗakin, dama kuma
Na'ima na jiransa domin tayi masa jagora zuwa parlourn Lami, yana fitowa tayi gaba, shi kuma ya bita a
baya har cikin ɗakin Lamin. Be zauna a kan kujera ba, a ƙasa ya zauna tare da zare glasses ɗin dake maƙale
a idanunsa ya ajiye a gefe yana kallon mutanan dake ɗakin cikin dabara, amma har ya gama kallosu bai
hango fuskan annurin zuciyar tasa ba a cikinsu. Kai a sunkuye ya kuma gaida Lami a karo na biyu tare da yi
mata ta'aziyar jikokinta ƴan gaba da fatiha sannan ya ɗaura da faɗin, "Haƙiƙa na taho maku da labari mai
girgizarwa da tashin hankali gami da baƙin ciki!" Yana kaiwa nan ya ɗan dakata na wasu daƙiƙu, yayin da
Na'ima ta shiga nanata "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Kasancewar malamar su ta faɗa masu duk
ɗayansu da ya faɗa cikin wata masifa to ya karantata. Lami kuwa da ƙarfi ta faɗi, "Yesu Almasihu mai ceto,
ka kawo ɗauki da sassauci, ka sanyaya zuciyarmu da ruwa mai tsarki." Khalil kuwa bayan dogon ajiyar
zuciya sai ya soma basu labari tiryan-tiryan, bai rage komai a cikin abubuwan da Aina'u ta aikata ba, har
kwanciyar aure da yayi da ita sai da ya faɗa masu, kashe-kashen da tayi har zuwa koran da ta saka yayi wa
Sarah da kuma halin da Aina'un take ciki yanzu na girban abubuwan data shuka. Kif! Lami ta faɗo daga kan
kujera ta sume, yayin da su Na'ima suka fashe da kuka jikinsu na rawa jin abubuwan da Aina'u ta aikata
daga ciki har da kwanciyar aure da tayi da mahaifinsu. Hassana ce tayi kan Lami tare da yayyafa mata ruwa
ta farfaɗo, wani irin kuka Lami ta fashe dashi tare da faɗin, "Ubanmu wanda ke cikin Sama, na tsarkake
sunanka, mulkinka shi zo akan abin da ka ke so ayi shi cikin duniyar nan kammar yada ake yinsa cikin sama.
Ka gafarta mana laifinmu, kamar yarda muna gafarta ma waɗanda su ke yi mamu laifi. Kada ka kai mu
wurin jaraba, amma ka cece mu daga Shaiɗan. Duka mulki, da iko da girma naka ne, har abada. Kada ka
kama ni da laifin haihuwar Aina'u ya Yesu Almasihu! Na san ita mai saɓo ce mummana a gareka, saɓo mafi
muni shine kwanciya da mahaifin daya haife ka, ya Yesu amintace, bani da laifi akan abinda ƴata ta aikata,
kayi mata hukunci amma ka cire mu Ni da sauran ƴaƴana. Mai girma Yesu Almasihu, na duƙa da duka
guiwowina a ƙasa ina neman yafiya da yafiyarka, ka amsa min, Amin." Khalil duƙar da kai kawai yayi yana
jiran ace masa ga inda matarsa take. Na'ima da su Hassana kuwa kamar zuciyarsu zai fito saboda irin kukan
da suke yi, "Mama dan girman Allah Aina'u ƴarki ce? Anya kuwa ba canje aka yi maki a asibiti ba? Ina ina
ganin babanmu bashi ya haifi Aina'u ba, ɗan halak ba zai taɓa yin tarayya da mahaifinsa ba." Faɗin
Na'iman. Sai da Lami ta fyace majina sannan tace, "Na rantse da girman Yesu Almasihu mai ceto, Ni da
mahaifinku Nuhu muka haifi Aina'u, Aina'u ƴata ce, kuma ƴar Nuhu ce, Ni ina ganin baƙin da Mahaifiyata
pasto Emanuella tayi min ne yake bina, don ta taɓa tsine min lokacin da zan auri mahaifinku Nuhu. To ni
babban tashin hankalina shine, kai Khalil kace ka kori Sarah, to tun yaushe? Don Sarah dai bata zo gidan
nan ba." Da sauri Khalil ya ɗago tare da faɗin, "What! Bata zo nan gidan ba? To ina zata je daya wuce nan
ɗin." Duk a gigice yayi maganar kuma ya miƙe tsaye. "Gaskiya Saratu bata zo gidan nan ba!" Lami ta kuma
faɗi tare da kallon su Na'iman dake kuka tace, "Ko ku kun ganta?" Girgiza kai suka yi dukansu, Khalil yace,
"Wallahi yau kimanin kwanaki goma sha bakwai kenan da barin ta gidana, to idan bata zo nan ba, ina zata
kenan? Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!! Allah ka tsare min matata da
ƴaƴana a duk inda suke." Lami hannu ta ɗauka akai tare da soma kwarara ihu har da kwance zani tana
faɗuwa a ƙasa tare da faɗin, "ƴata kina ina, ina kika je kika ɓuya? Yesu Almasihu ka nuna min hanya cikin
sauƙi!" Khalilullah fita yayi da sauri tare da barin gidan hankalinsa a bugun tashe, buɗe mota yayi tare da
shiga ya ɗaura kansa akan steri yana tunanin hanyar da zai fara neman Sarah. Kwankwasa masa glass yaji
ana yi, a hankali ya ɗago tare da sauke glass ɗin motar Kasancewarta tinted, "Muneeba!" Ya kira sunanta
da mamaki don rabon da ya sakata a idanunsa tun lokacin data kawo masu ziyara lokacin Sarah na fama da
cutar tsutsotsin nan, don shi bai ma san tafiyarta ba, kuma tun daga ranar bai Kum samun labarinta ba.
Buɗe mata murfin motar yayi tare da faɗin, "Naji daɗin ganinki, shigo ciki Please." Girgiza kai tayi tare da
faɗin, "Kayi haƙuri ba zan iya shigowa ba, domin a yanzu haka maganar da nake faɗa maka idan har
Babana ya samu labarin to tabbas zan fuskanci mummunar hukunci mai tsanani don ya haramta min nufa
inda kuke ko yin magana da ɗayanku. Kaga wancen makarantar, acan nake koyarwa, fitowata kenan na
ganka ka fito daga gidan nan shine nace bari na ƙariso mu gaisa." Shuru yayi na wasu ƴan daƙiƙu sannan
yace, "Mai ke faruwa ne Muneeba?" Dafa glass ɗin motar tayi tare da faɗin, "Abunda ya wuce ya wuce,
amma dai bari na tsungulo maka kaɗan daga halin da na shiga sanadin zuwa gidan ka wancen ranar. Bayan
naga halin da ƙawata take ciki, sai na tashi da sauri domin zuwa wajen iyayena su taimaka mata da
magungunan karya sammu da kuma addu'o'in da zata riƙe ya zama makaminta don its obvious matarka
sammu ne a jikinta. To ina fitowa kawai naji an taɓa ni ta baya, juyowar da zanyi sai muka yi idanu huɗu da
ƙanwar matarka, sai ta daki goshina tare da cewa in kalli gabas inyi tafiya kar in kuma dawowa gidan! To
tun daga wannan lokacin ban kuma sanin inda kai na yake ba sai tafiya kawai nake ta yi, amma kasancewar
iyayena ma'abota ambaton Allah ne haka nima kuma na tashi da wannan ɗabi'a shiyasa Allah ya sauƙaƙa
min wahala ban jima ina garari ba aka gano inda nake aka dawo dani gida, sai dai na sha jinya mai tsayi
kamun na samu kaina, bayan na dawo cikin hayyacina ne na shaidawa iyayena abunda ya faru, to daga nan
ne sukai min iyaka daku, sannan suka ce in dai addu'a ce aduk inda aka yi to da cikin ƙarƙashin ƙasa ne zata
karɓu indai anyi ta cikin yaƙini, saboda haka zasu riƙa bin ku da addu'a daga nan inda suke ba sai na kuma
takawa inda kuke ba, sannan Babana ya saka min doka mai tsauri akan kar in kuskura ko hanyar gidanku na
ƙara bi ta wajen." Shuru Khalil yayi yana mamakin irin mugun hali da rashin imanin Aina'u. "Allah ya saka
maki Muneeba, muma Aina'u tayi mana muguwar cutarwa da tafi wanda tayi mai, sai dai kawai Allah yayi
mana sakayya!" Rausayar da kai Muneeba tayi tare da faɗin, "Ameen, a gaida Saran, sai anjima." Tana
gama faɗin haka ta ɗaga masa hannu sannan ta wuce. Ɗaga glass ɗin sama yayi tare da kunna motar ya
bar wajen, a kan hanya sai saƙe-saƙe yake yi ta inda zai fara neman Sarah, ɗilin! Yaji saƙo ya shigo cikin
wayarsa, kamar ba zai duba ba, sai kuma ya mika hannu ya ɗauko wayar dake kan seat ɗin gefensa, ganin
debit alert daga GTbank sai yayi tsaki ya ajiye wayar, can kuma ya taka wani mahaukacin burki a tsakiyar
titi, Allah yaso babu wanda ke binsa a baya, hannunsa na rawa ya ɗauko wayar ya shiga cire key da sauri,
'wrong pin' ya nuna masa kasancewar da sauri yake danna code ɗin. Khalil bai taɓa dana sanin saka pin a
rayuwarsa ba sai yau don ƙosawa yayi ya buɗe wayar, ƙara sakawa yayi stil cikin sauri, wannan karan ya
bude, shiga message ɗin yayi ya shiga karantawa da sauri, wani irin sanyin Ni'ima ce ta shiga bin saƙo da
lungu jikinsa, "Allah Ubangijin mai kowa mai kowai, mai sauƙaƙawa bawa a cikin matsala, Allah Nagode da
a wancen lokacin ka bani courage ɗin bata ATMcard ɗina." Faɗin Khalil sakamakon ganin debit alert daga
Nasarawa, Lafiya state. "Wamba, unguwar abakwa!" Ya kuma faɗi a bayyane tuno lokacin da yake tambaye
Sarah a kan wani yare su har ta faɗa masa sunan garinsu har da unguwar. "Alhamdulillah!" Ya kuma faɗi
daidai da lokacin da wayarsa tayi ƙara, ganin Hajiya ke kiran wayar sai da gabansa ya faɗi. Jiki a sanyaye ya
ɗaga wayar, "Ka dawo gida tunda ba'a can aka haife ka ba, kuma Marmari ya biyo jirgin sojoji yazo,
isowarsa kenan shi da Ayshan. Abu na gaba kuma, kar ka kuskura ka shigo cikin gidan nan idan har ka san
akwai igiyar aurenka aka ƴar dangin matsafan nan!"

_Wai me Hajiya take nufi damu ne_😞

_Kuyi haƙuri dan Allah da rashin ganin update jiya, wani ɗan matsala aka samu_

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[29/10, 12:57 PM] Rahamanatu: "Hajiya dan........." Ko kamu ya ƙarisa abun da yake shirin faɗa har Hajiya
ta yanke wayarta. Hannu ya kai ya daki steari da ƙarfi tare da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!
Haba Hajiya!! Habaaa!!!" Ya jima kamun ya kunna motar ya sau hanya, "Wannan shi ake kira ga ƙoshi ga
kwanan yunwa!" Ya faɗi bayyane, can kuma ya kuma ɗaukar wayar ya sake dailing number ɗin Sarah, "
_The number you're trying to call is currently switched off, please try again later. Thank you_." Tsaki yayi
tare da ajiye wayar a gefe ya nufi gida don bai san dame Ya Abdullah yazo ba. Tafiyar da zai yi ta mintuna
sha biyar, amma saboda tsoro da tashin hankali cikin mintuna talatin da biyar ya iso layinsu. Tun da ya
hango uban sojoji uwa saƙago sun tsatstsaya ya kuma tabbatarwa kansa ya LTG ya iso gidan. Horn yayi, mai
gadi ya wangale gate shi kuma ya shiga tare da parking sannan ya fito yana tafiya sumimi-sumumi kamar
an tsoma jaba a cikin koko. Tun da ya doshi ɗakin Hajiya yake jin koke-koken mata na fitowa daga ɗakin.
Shahada yayi tare da ɗaga labule ya shiga. Turus ya tsaya yana kallon matan dake ɗakin tare da mamakin
yaushe suka iso all the way from Maiduguri. Duƙawa yayi har ƙasa tare da soma gaishe su, yayin da kansa a
ƙasa ya shiga gaida ya Abdullahi da tun shigowarsa kallo ɗaya kawai yayi masa ya kau da kai. "Wallahi,
tallahi Hajiya baza mu taɓa yarda ba, sai an ɗauki mataki akan wannan abu da ƙanwar matar ya Khalil tayi
masa, ta cuce mu ta raba mu da ƴar uwarmu, kema kuma tayi ƙoƙarin raba mu dake, baza mu yafe mata ba
akan wannan abu da tayi mana. Hajiya ko gawan Nafeesa ban gani ba!" Ta ƙarisa maganar tare da fashewa
da kuka mai ciwo. "Har da jaririyar da bata ji ba bata gani ba, yarinyar da bata jima da shaƙar iskar duniyar
ba, wannan wani irin rashin imani ne haka!!" Aysha ta sake faɗi tana mai kwanciya akan cinyar Aunty
Yagana, ƙanwar Hajiya. Shafa kanta Aunty Yaganar tayi tare da faɗin, "Aysha duk wacce imaninta zai bar
jikinta har ta iya kwanciyar aure da mahaifinta, to wallahi babu abunda baza ta iya aikatawa ba, da a
zamanin annabawa tazo, to tana ɗaya daga cikin wacce zata iya yunƙurin kashe Annabi! Wallahi Hajiya ina
bayanki ɗari bisa ɗari, kar ki sake ki yarda matar Khalil ta dawo cikin gidan nan, mai za ayi da zuri'a irin
tasu, zuri'ar matsafa, zuri'a karuwai ƴan dangi Arna!! Ai wallahi don dai kisa haramun ne, da ko ƴaƴan da
Khalil suka haifa tare, shaƙe wuyansu kawai za ayi su mutu kowa ya huta. To sun tsotsi nonon tsiya!" Faɗin
Aunty Yagana a mugun zuciye, don har ta kusan fin Hajiya ɗaukar zafi. Khalil lokacin guda yaji haushin
Aunty Yagana ya rufesa jin abunda tace akan ƴaƴasa, nan da nan ya ɗaure fuska tamau. "Kayi abunda na
umarce ka dashi ko kuwa???" Faɗin Hajiya tana watsawa Khalil harara. Ko kamun yayi wani yunƙurin yin
magana tuni Aunty Falmata mai bin Aunty Yagana tace, "Ba magana ake yi maka ba don ubanka? Ko sai na
taso ba na shaƙi wuyarka!" Ta ƙarisa da ƙarfi har sai da Khalil ya razana, "Hajiya wallahi, tallahi daga gidan
nake, su kansu iyayenta basu san bata gidana ba, ashe dana koreta ba gida tayi ba, can dangin babanta ta
nufa." Ya ƙarisa maganar a tausaye. "Dubi yanda yake wani rausayar da kai kamar maraya, to ubanka zaka
ci, kuma dole ka rabu da yarinyar nan tun da ba tare aka haife ku ba. Yaro duk kabi ka zama wawa a kan
mace!" Faɗin Aunty Yagana. "Uhm! Baku ji wata maganar banza da yake yi ba, wai ta tafi dangin
mahaifinta. Ina ce nan Marmari yayi bincike lokacin auren naku, kowa cewa yake bai san asalin mahaifinta
ba, su dai kawai tarewarsu suka gani a unguwar, kuma babu wanda ya taɓa ganin wani ko wata daga cikin
ƴan uwansu yazo gidan, kaii Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'una, wannan fitina haka!" Hajiya ta faɗi har da
buga cinya. Tun da suka fara magana ko tari ya Abdullahi bai yi ba yanzu da yayi gyaran murya tare da
faɗin, "Hajiya, tun farko irin haka na guda shiyasa naƙi auren don zuciyata bai kwanta da ahalin ba, amma
Hajiya kece ki kai ta tausata akan inyi haƙuri ayi auren tunda dai mutane huɗu sun bata shaida a kan ita
matar Khalil ɗin, sannan kika ƙara da faɗin, laifin wani bai shafan wani. To Hajiya yanzu hakan ma haƙuri za
kiyi tunda dai an riga an haɗa zuri'ar nan kuma laifi bana matar Khalil bane, na ƙanwar matarsa ce, kuma
laifin ƙanwar matarsa babu yanda za ayi ya shafi matarsa, tunda ke shaida ce hatta ita kanta matar tasa ba
barinta tayi ba. A bar abunda ya wuce ya wuce, sai a tari gaba kawai." Tsabar zuciyar Hajiya na tuƙuƙi, ta
buɗe baki za tayi magana ta shaƙe da miyau, take ta hau wani irin mugun tari, idanunta na zubar da
hawaye. Da sauri Laure ta nufi kitchen ta ɗauko bottle wata ta buɗe tare da kawowa Hajiyar, da sauri
Hajiya ta karɓa ta kafa kai, sai da tasha rabi sannan ta ajiye goran tana mai da numfashin. Babu abunda
kake ji a ɗakin sai "Sannu Hajiya!" Sai da ta lafa sosai sannan ta shiga faɗin, "Marmari idan har ka san ba
zuwa kayi ka taimaka min muyi wannan yaƙin tare ba, to ka tashi ka koma tun yamma bata yi maka ba, don
ka san wallahi, ba zan taɓa yarda Saratu ta kuma zama da Khalil ba in har nice na haifesa, idan kuma zai yi
mani musu da gardama, sai in sallawa duniya shi!" "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, Hajiya!" Khalil ya faɗi
da ƙarfi har da dafe ƙirji yana zaro idanu. "Haba Ya Bilki, ai wannan furucin bai kamata ya fito daga bakinki
ba matsayinki na uwa, idan ki kai haka ai sun ci riba. Hakan ma ba zata faru ba, Khalil ai me biyayya ne, ko
ba haka ba Ibrahim, mai sunan ɗan gatan Allah!" Faɗin Aunty Yagana har da dariya. Sunkuyar da kai yayi
tare da gyaɗa kan alamar eh. Aunty Falmata kuwa cewa tayi, "Yauwa Khalil, ko kai fa! Yanzu abunda za ayi,
dubawa za kayi cikin dangi na nan ko na can Maiduguri, a kwai ƴan mata tsala-tsala, na san dai ba zai wuce
kyal-kyal banzar matar nan taka bace kake ganin baza ka samu sama da ita ba kasancewar jajur kuma
kyakkyawa, to akwai waɗanda suka fita komai a cikin dangin ubaka dana uwarka. Dangin ubanka akwai irin
su, Ajaja, Gona, Am'an, yaba, yakaruu duk kyawawane duk da kuwa baƙaƙe ne, idan kuma basu yi maka
ba, sai ka tafi dangin uwarka, ka san dai Shuwa ba baya ba wajen kyau, gasu Hindatu, Rakiya, Raliya dasu
Aysha da Ameena, kai nayi tuya na mance da albasa, ga wannan ƴa ƴar wajen Mariya, _Habbooba_! Kai ita
ma na zaɓa maka, Yarinya kamar India, yanda kasan ita tayi kanta tsabar kyau, ga gashi don san yana ɗaya
daga cikin abubuwan dake tsole maku idanu ku maza." Caraf Hajiya tace, "Wallahi ni Habbooban ma tafi
kwanciya min a rai, kawai ayi magana da iyayenta, idan sun amince sai ayi magana. So nake ayi komai cikin
gaggawa, kuma ni wallahi na haƙura da zamansa a nan Nigeria kuma dama ni na matsa a kan ya dawo nan
ɗin, to yanzu na haƙura, ana ɗaura auren sai ya tattara matarsa su koma cen _Las Vegas_ ɗinsa da zama."
Da gefen idanu Ya Abdullahi ya kalli Hajiya tare da ɗan yin murmushin gefen baki tare da miƙewa yace,
"Muje can side ɗin naka naga yarinyar!" Yana gama faɗin haka ya fice, da sauri gaba ɗaya mutanen ɗakin
suka miƙe suka fito don suma duk abunda ake yin basu ga Aina'u ba. Jiki a sanyaye Khalil ya miƙe yabi
bayan ya Abdullah zuwa side ɗinsa, shi ya saka key ya buɗe sannan ya shiga, ya Abdullahi yabi bayansa, su
Hajiya kuma suka bi bayan ya Abdallah. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Kuna jin warin da nake ji kuwa a
cikin ɗakin nan kamar gawa ta ruɓe?" Faɗin Nafeesa tana mai toshi hancinta. Gaba ɗaya sauran ma toshe
hancinsu suka yi, "Allah yasa ba wannan shaiɗaniyar bace ta mutu a cikin gidan mu!" Hajiya ta faɗi. Cikin
sauri Khalil ya nufi sama yana tsallake step bibbiyu. Ƙafa ya saka ya daki ƙofar ta bulle da ƙarfi, da wani
uban sauri ya koma baya yana toshe hanci tare da zaro idanu, "Wa'innahu Sulaimanu!" Faɗin Aunty Yagana
da aunty Falmata. "Ibrahim menene wannan ka ajiye a ɗakin ka." Ɗagowa Aina'u tayi cikin wa.i irin mugun
azaba tare da faɗin, "Ku taimaka min, ku taimakeni Aina'u ce!" Kuka Hajiya ta fashe dashi tare da faɗin,
"Wallahi tallahi jama'a mu kiyaye ALLAH! Mu kiyaye ALLAH jama'a!! Yanzu wannan yarinya Aina'u ce ta
koma haka?" Kallonta Nafeesa take tayi cikin tsoro, ganin da tayi mata na ƙarshe shine ranar da tazo washa
garin auren su Khalil. Yanzu kam ta lalace, tsirara take a cikin ɗakin, maƙogwaronta a waje, idanunta ya
zazzago, ko ina a jikinta babu inda babu rami zuƙuƙu, duk inda tsokar ta yanko ta faɗo, tsutsotsi ke
cunkusuwa a wajen suna cin sauran naman dake wajen. Gaba ɗaya Aina'u ta fice daga hayyacinta, gashin
kanta duk ta gama fuzgar shi, haƙoranta duk jini ta gama tattaune leɓenta. Sai wani irin miƙewa take yi
tana zabura sannan sai ta fasa ihu tare da kai hannu gabanta ta kwakwulo kunamu ta watsar a tsakar ɗakin
sannan ta hau burgima tana buga kanta da bango. "Hajiya a fitar da yarinyar daga gidan nan, ta koma can
gidan iyayenta dan Allah!" Fadin Nafeesa jikinta na wani irin rawar tashin hankalin ganin halin da Aina'u
take ciki. Ya Abdallah kuwa girgiza kai yayi tare da saurin barin waje yana mai faɗin, "Hajiya yanzu yarinyar
nan zata bar gidan nan, ku fito mu fita." Gaba ɗaya suka bi bayansa, Khalil kuwa sai da ya kalli Aina'u
sannan yace, "Ban taɓa jin ɗigon tausayinki ba Aina'u, domin kuwa kin cutar dani matuƙa, Kuma idan har
Hajiya tayi nasarar rabani da matata, hmmm!" Yana gama faɗin haka ya fice daga ɗakin da sauri hawaye na
zubar masa. Cikin ƙanƙanin lokaci ya Abdallah ya kirawo wani mai akori kura ya bashi 50k ya toshe hanci
tare da saka glove, bayan lulluɓe jikin Aina'u ya kinkimeta ya saka a bayan akori kuran ya tada mota ya nufi
jama'a road can gidansu Lami. Lokacin da aka shigo da Aina'u gidan, ihu Lami ta riƙa yi tana tuma a ƙasa,
su Na'ima kuwa tsoron Allah ne ya ƙara huda zukatansu, duk da halin Aina'u sai da ta ɗan basu tausayi.
Saboda tsananin warin da take yi, ɗaki ɗaya da akai masu ƙatoto saboda kiwo suka share sannan suka ajiye
ta a ciki, babu abunda take yi sai tone-tonen abubuwan da tayi. Lami na jin sunan _Hell Ofulafu_ gabanta
ya buga da ƙarfi ta fito daga ɗakin tana faɗin, "Rose Merry! Rose Merry ce kawai zata iya kai Aina'u wajen
Hell! Yesu Almasihu ka kawo ƙarshe Rose a wannan rana mai albarka ta Sunday." Faɗin Lami tare da fizgar
zanin dake kan igiya ta fita fuuuuuuuu. Saboda tsabar tashin hankali Lami ko abun hawa bai hau bata hau
ba, haka tayi ta tafiya a ƙafa har ta isa gidan Rose Merry. Knocking ta hau yi a ƙofar gidan kamar zata ƙarya
duk da kuwa akwai kwaɗo dake nuna alamun mutanan gidan basa nan, don anty Rose Merry idan ta tafi
church duk Sunday bata dawowa sai bayan la'asar ko kuma gab la'asar. "Madam ai gidan a kulle yake, kalli
padlock ɗin mana." Faɗin wata bayarabiyar mata mai ɗauke da ƙaton bawon gorunan magani a kai, sai a
sannan ta kalli kwaɗon tare da kai hannu ta taɓa, zamewa tayi ta zauna akan dakalin gidan, don ji take ba
zata iya taɓa tafiya ba tare da tayi ido huɗu da Rose Merry ba. Ta kusan awa ɗaya a wajen kamun Aunty
Rose Merry ta ƙariso wajen cikin shigar farar atamfa mai ratsin sky blue, sai farar rigar less da kuma sky
blue ɗin gwaggwaro. Tana ganin Lami ta washe baki tare da faɗin, "Elizabeth Akanchewa Uchendo, ƙawata,
my childhood friend." "Stop that nonesense Rose Merry David Anthony! I came here to ask of what you
did to my daughter! You've poisoned my daughter's heart Merry, Yesu Almasihu ya tsine maki, Ƙawancena
dake babu alheri a ciki, ke guba ce, ke shaiɗaniya ce, kin kai min ƴata wajen azzalumin nan _Hell Ofulafu_,
tun ranar farko da kika fara kai ni Abia na san wannan mugun mutum ne mara imani, duk tsafin da ake yi a
gidanmu, baza su iya rashin imanin da Hell yake yi ba, yanzu na ƙara tabbatar da cewa kece kika kashe min
ɗana Lukman, kuma ki sani, na rantse da tsafin Babana, You will pay for what you did!" Lami na gama faɗin
haka ta juya zata bar wajen, da hannu ɗaya Aunty Rose ta jawo kafaɗanta tana wani irin murmushin
mugunta, sai da ta juyo da Lami gaba ɗaya sannan ta kyasta babban yatsarta da kuma manuniya tare da
faɗin, "Hey Elizabeth, do you think I came all the way from Nassarawa state to Kaduna, just because of our
friendship? You're a fool, a big fool Elizabeth! Nazo Kaduna ne domin mijinki, don mijinki Elizabeth! Tun
ranar da na fara ganin Nuhu, naji ina matuƙar ƙaunarsa, amma kuma sai kika min shigar sauri, sannan
kuma kin tuna abunda Akanchewa Uchendo ina nufin mahaifinki yayi wa Babana, yayi masa asiri ya raba
shi da mamana, ya raba shi da duka arzikinsa sannan ya mayar dashi makaho, Ni kuma gani har yanzu ban
taɓa aure ba. Kina tunanin sai ni kuma in zuba maki idanu ki auri ɗan gidan malaman can, sannan kuma in
barku kuyi zaman lafiya?" Sai ta girgiza kai tare da ɗaukar ƙafa ɗaya a kan dakali sannan tace, "Bari na faɗa
maki abunda baki sani ba Elizabeth, nice sanadin lalacewar duka ƴaƴanki, Ni na kai sunanki wajen Hell,
nayi amfani da kwaɗayin duniyarki, na saka Hell ya sakaki kika kai ƴaƴanki ga halaka, sannan ɗan ki tilo
namiji na saka masa cutar sata da kuma shaye-shaye, ƴa ɗaya ce ta gagare ni, ita ce Saratu, Ni na saka Hell
ya saka maki tsanar mijinki da jin haushinsa da kuma rashin ganin ƙimarsa, sannan Ni nasanwa mijinki
karayar arziki bayan na nakasta ƙafarki, ƴarki kuma Aina'u, banyi mata komai ba, jinin mahaifinki ne ke
yawo a jikinta, don ita ce tayo gadon ubanki gaba ɗaya har ta damesa ta shanye. Kuma Lami yanzu aka fara
wasan a tsakanin mu. Ban san mai Aina'u tayi ba, amma tun da tace min tana so in haɗata da Hell na
tabbatar Aina'u ɗiyarki ce, domin bata yada halinki dana mahaifinki ba. Mu zuba ni da ke Elizabeth!" Tana
gama faɗin haka tayi wani murmushi tare da kaucewa ta nufi wajen ƙofa ta buɗe tare da shiga ta bugo
ƙofa. Lami ta jima a tsaye tana jujjuya maganganun Rose Merry kamun taja jiki a sanyaye ta nufi gida. "Ai
da zafi-zafi akan daki ƙarfe Hajiya Mariya, Ni dai idan har ba'a tsayarwa Habbooba miji ba, nayi wa Khalil
kamu!" Faɗin Hajiya tana murmushi..............

_Kar ku damu, zamu haɗu gobe in Sha Allah. Na san nayi laifi kam_ 😬

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[29/10, 12:57 PM] Rahamanatu: Cike da farin ciki Hajiya Mariya tace, "Hajiya Bilki wanene zai ƙi son haɗa
jini dake? Ai wallahi ko an tsayarwa Habbooba miji, haƙuri za'a bashi, gida bai ƙoshi ba ba'a baiwa na dawa
ba, balle kuma Habbooba bata da wani tsayayye miji. Ba'a jima da kammala degree ɗinta ba. Yanzu ne ta
ɗan soma kula samarin ma." Wani ajiyar zuciyar farin ciki Hajiya ta sauke tare da faɗin, "Alhamdulillah!
Alhamdulillah!! Shikenan tuwona maina, yanzu abunda za'a yi, ki ɗan fara Kwankwasawa Alhj Mutallab da
maganar kamun daga nan su Marmari su zo tambayar aure, don so nake kawai da sun zo, har lokacin biki a
tsayar. Allah yasa dai kar Habbooba ta bamu matsala!" "Hajiya baki da matsala, Habbooba kuma babu
matsala daga wajenta in Sha Allah." Layla dake gefen Hajiya Mariya sai jan gyalen lifayan data naɗe jikinta
take yi tana faɗin, "Umm! Umm!!" Ita kuma haj Mariya sai kai mata duka take yi tana bige hannunta, sai da
ta gama wayar sannan ta kalleta a fusace tare da soma magana cikin yaren Shuwa, "Mai yasa baki da
hankali ne Layla? Kin san da wacce nake magana amma sai takura ni kike yi, baki bari in gama wayar tukun
sannan kiyi min duk maganar da zaki yi min!" Turo baki kyakkyawar farar yarinyar tayi tare da faɗin, "Haba
Umm, why always Habbooba? Komai Habbooba, duk abunda kika samu, Habbooba, idan kyauta za kiyi,
Habbooba is the first person to received before everyone, haba Umm!" Layla ta ƙarisa maganar cikin ɗacin
zuciya. "To yanzu kuma me nayi Layla?" Faɗin Hajiya Mariya tana mai zama kusa da Laylan. "Naji lokacin da
kuke magana da Aunty Yagana a parlour, shine kika yi sauri kika dawo bedroom ɗinki, and then yanzu
kuma kina magana da aunty Bilkin Kaduna, kuma i heard anything you were saying, it all about uniting
Habbooba and that son of her's!" Janyota jikinta tayi tare da faɗin, "Haba Layla, ba wai nafi son Habbooba
bane a kanki, kin ga you're just 18years, amma ita she's 27years, kin ga dole ita zan so na fara kawaswa a
nan gidan tafi gidan nata mijin kamun ke. Be petient, in Sha Allah kema mijinki na nan zuwa soon!" Shuru
Layla tayi bata ƙara cewa komai ba. Tayi haj Mariya tayi tare da fita daga bedroom ɗinta ta nufi na
Habbooba, tun daga corridor ɗin da zai sadata da ɗakinta take jiyo sautin wakar _Allela Belela_ kamar zai
fasa dodon kunnenta, sai data toshe kunnen sannan ta iya ƙarisawa har cikin ɗakin Habbooban sannan ta
kai hannu ta zare socket ɗin radion ta jefar. Wata fara tass ɗin budurwa ce kwance a kan gado daga ita sai
wani Short kalar baby pink wanda ya tsaya mata iya cinya, sai rigar short ɗin ta kamfanin Armani da ya
kawo dai-dai inda short ɗin ya tsaya mata, gashinta baƙi siɗik mai uban tsayi daya barbazu akan gagon,
rubutu take yi a kan wani jotter kuma a lokaci guda tana kallon screen ɗin iPhone X ɗinta, jin waƙar da take
sauraro ya tsaya cak sai tayi saurin juyowa da sauri, kyakkyawa ce ta bugawa a jarida, gashinta ya watsu
baya, wasu kuma suka rufe gefen fuskanta, hannu ta saka ta mayar da gashin baya tare da turo baki ganin
mahaifiyarta ce da wannan aikin. "Habbooba." Mahaifiyar ta kira sunanta a hankali tare da zama a bakin
gadon, cikin sauri Habbooba ta kawo kanta ta ɗaura a kan cinyar maman tata, "Ya Rasulullahi, Habbooba
na hana ki ƙure sauti a ɗakinki, idan za kiji waka, ki riƙa saka sautin daidai kunnanki dan Allah!" "Umm,
idan ban saka volume dayawa ba, waƙar bai min daɗi sosai." Faɗin Habbooba. Ajiyar zuciya Umm tayi tare
da faɗin, "Habbooba!" Ɗagowa tayi ta kalli Umm ɗin jin yanda ta kira ta with seriousness, "Na'am, Umm!"
"Kin san wannan?" Umm ta faɗi tare da nuna mata hoton Khalil lokacin yana _Las Vegas_, tsaye jikin wani
ƙarfe hannunsa biyu sanye cikin aljihun wandonsa yana sanye cikin wata navy blue ɗin bodyhug irin
highneck ɗin nan, murmushin kwance a fuskansa wanda ya bayyanar da 2dimples ɗinsa, ba ƙaramin kyau
yayi ba. Ƙarɓan wayar tayi a hannun Umm tare da zoomin picture ɗin sosai tana faɗin, "Wow! He look
familiar, amma na rasa inda na taɓa ganinsa. Yana da kyau sosai Umm." Wani murmushin jin daɗi Umm
tayi tare da karɓan wayar sannan tace, "Future husband ɗinki ne!" Waro idanu Habbooba tayi tare da tashi
zaune tace, "Umm, are you for real? Like da gaske kike Umm?" Dariya Umm tayi tare da faɗin, "Ni na taɓa
yi maki ƙarya ne? Mahaifiyarsa ce ta buƙaci ya ƙara aure saboda bata son first wife ɗinsa da yake zaune da
ita, shine ta zaɓe ki a matsayin matar da zai aura, kuma kin san ko shi ɗin ɗan wanene?" Girgiza kai
Habbooba tayi gabanta na faɗuwa jin yana da mata, don it's obvious Shuwa basu ƙaunar kishiya! "Ɗan
_late CJN Nurudden Muhammad_ ne, kuma kin san dai CJN Nurudden Muhammad mijin cousin ɗita ce,
don da mahaifin haj Bilki, da Mahaifiyata, ubansu ɗaya, uwa ce kowa da tasa." Jinjina kai Habbooba tayi
tare da faɗin, "Na tuna, na tuna inda na taɓa ganinsa, lokacin da muka je ta'aziyar mahaifinsa ne na taɓa
ganinsa, he's a medical doctor ko?" Jinjina kai Umm tayi tare da faɗin, "Tabbas shine, kin gane sa." A
sanyaye Habbooba tace, "Umm I love him, but yana da mata kika ce." Ta ƙarisa maganar cike da rauni.
Kamo hannunta Umm tayi tare da faɗin, "Come on, sai kace ba Shuwa ba, Kar ki bani kunya mana, Shuwa
ba'a san mu da tsoran kishiya ba, kishiya ko wacece ita bata bamu tsoro. Ni dama kuma amincewarki nake
so, kuma baki san wani abu ba, ita matar tasa ma, sakinta za ayi don ita mahaifiyar tasa cewa tayi dole ya
saki first wife ɗinsa, kuma da zarar anyi auren, _Las Vegas_ zaku wuce acan za kuyi zaman ku." Wani irin
runguma Habbooba tayi wa Umm tare da faɗin, "Na amince Umm, zan aure shi kuma ni dama tun ganin
da nayi masa na farko naji ina matuƙar sonsa." Shafa kanta Umm tayi tare da miƙewa fuskanta cike da
murmushi ta bar ɗakin. Bayan kwana biyu! "Khalil ka san mai yasa nayi kiranka a gaban ƴan uwanka gasu
gaba ɗaya?" Faɗin Hajiya tana yin nuna gasu, ya Abdullah, ya Abdul-Hakeem, ya Barrister, da kuma Aysha.
Girgiza kai Khalil yayi, don shi da badan ritsa shi da aka yi ba, da yanzu haka yana hanyar Nassarawa wajen
matarsa, "Yauwa, to na kiraka ne in kuma jaddada maka maganata akan sakin matarka, Ibrahim wallahi
dole ne ka saki yarinyar nan, ƴaƴa kuma ni da kai na zan aika har Nassarawar a ɗauko min su, kar ka damu
ba zan barka babu mace ba tunda ka riga ka saba da mata, na zaɓo maka cikin dangi, ba kuma ƴar kowa
bace sai ƴar ƙanwata Habbooba, yarinya fara tas kyakkyawa da ita. Don haka idan ba so kake na ɗaga maka
nono ba, dole ne ka saki yarinyar nan, ehe. Aure kowa ya san ba dole bane, shikuwa saki surah sukutum
aka saukar a kansa, Allah da kansa shi ya halatta sakin aure! Kuma na riga nayi rantsuwa sai ka saki
Saratu!" Kan Khalil a ƙasa babu abunda yake zubarwa face hawaye. Ya Abdullah gyaran murya yayi tare da
faɗin, "Hajiya, Ta yiwu ɗaya daga cikin dalilan da ya sa ake kiran wannan sura da sunan surar saki (Ɗalak)
shi ne irin hukunce hukuncen sakin da suke ƙunshe a cikinta makil, wanda wannan yana nuna mana irin
la'akarin da shari'ar musulunci ta yi dangane da al'amarin saki, saboda irin hatsarin da yake da shi, domin
abu ne wanda in har ba'a yi da gaske ba, kuma ba'a yi shi yanda musuluci ya zo da shi ba, sai ka samu ya
taimaka wajen wargaza al'umma da tarbiyyar iyali, kana da haifar da gaba da kiyayya a tsakanin dangi.
Kamar yanda rashin kiyaye hukuncin sakin ke iya haifar da aure kan aure, wanda daga karshe a dinga haife
'ya'ya marasa tabbas ɗin iyaye. Kamar yanda kuma, shi saki ba wani abu ne wanda shari'a ke ƙarfafa
gudanar da shi ba, bil hasali ma shi ne halas wanda Allah ya fi ƙi, kamar yanda ya zo a mashahuriyar
ruwaya daga Ma'asumai (A.S.) "Babu wani abu da Allah ya halatta kuma yake fushi da shi fiye da saki.
Wannan ruwayar ta zo cikin Wasa'ilus shi'ah juzu'i na 15 shafi na 266. Sai dai kuma wani abin tambaya a
nan shi ne, mene ne ya sa shari'a ta halatta yin saki ? Amsa a nan ita ce a irin hali na zaman yau da gobe na
ma'aurata a wasu lokuta za ka samu cewa akwai wasu halaye waɗanda suke faruwa marasa daɗi wanda in
da za'a tilasta ci gaba da zama da juna a tare da waɗannan halayen, sai mu samu rayuwa za ta yi ma wanda
yake cutuwa, tsanani da kunci wanda zai iya kaiwa ga halaka da abin da ya yi kama da haka. To saboda
Allah ne mahaliccin kowa da komai, kuma asanin abin da zai kai ya kawo, don haka ya kawo magani da
mafita a duk lokacin da irin waɗannan matsaloli suka bijiro a tsakanin ma'aurata, wanda wannan magani
shi ne saki, duk da cewa ba'a son al'amarin ya kai ga haka, sai ya zama dole. Musulunci addini ne da ya
ƙunshi komai da komai don inganta rayuwar ɗan Adam a duniya da Lahira. Bai bar ɗan Adam ya yi amfani
da hankali da tunaninsa kawai don tsara wa kansa makoma ba, saboda shi ɗan Adam mai rauni ne, mai son
zuciya ne, mai haɗakma ne, mai rowa ne, kai ƙarewa ma mai butulci ne ga wanda Ya halicce shi. To in har
zai yi butulci ga Mahaliccinsa, ta yaya zai tsara rayuwar da sauran abokan zamansa za su ji daɗi? Aure daya
ne daga cikin ginshiƙan rayuwar al’umma, wannan ya sa Musulunci bai bar shi sasakai ba ƙa’idoji da dokoki
ba. Kuma baya ga ƙa’idojin zamantakewa a tsakanin ma’auratan, duk da ba a fata, amma ya tsara yadda za
a rabu idan aka kasa samun jituwa ko maslaha a tsakanin miji da matar. Saki a matsayin zaɓi na ƙarshe:
Ko da yake an halasta saki a Musulunci alama ce ta sassauci da aiki da tsarin shari'ar Musulunci, kiyaye
haɗin kai na iyali yana ɗaukar fifiko don kare yara. Saboda wannan dalili, saki a koda yaushe zabin karshe
ne, bayan gajiyar dukkan hanyoyin sulhu. Misali, Allah yana magana da maza yana tambayar su da su yi
ƙoƙari don kiyaye auren, koda sun ƙi matansu: Ku zauna da su bisa tushen kyautatawa da adalci. To, idan
kun ƙi su, akwai tsammãnin ku, ku ƙi wani abu, kuma Allah ya sanya albarka a cikinta. Surah 4 Aya 19
Haka nan ayar nan tana magana ne ga mata suna tambayarsu irin wannan: Idan mace ta ji tsoron zalunta
ko tawaya daga bangaren mijinta, Bãbu laifi a kansu idan suka yi sulhu a tsakãninsu, Surah 4 Aya 128,
wannan ayar tana magana ne ga dangi ko kuma al'umma don wannan manufa ta kubutar da wannan alaka,
wanda Allah bai sauwake wa karya ba: Idan kun ji tsõron sãɓa a tsakãninsu, (biyu) masu sasantawa, daya
daga danginsa, da sauran daga nata; idan suna fatan zaman lafiya, Allah zai daidaita su: Kuma Allah Masani
ne, kuma Masani ne ga dukkan komai. Surah 4 Aya 35, Amma, idan bayan gajiyar dukkan hanyoyin sulhu,
Ƙiyayyar da ke tsakanin miji da mata har yanzu ta fi haƙuri, sannan saki ya zama babu makawa. Ga kuma
hazakar shari’ar Musulunci, wanda ke da amfani, maimakon hanyoyin da ba su dace ba, zuwa ga haƙiƙanin
yanayi. Maƙasudin aure, da kuma duk wani ɓangare na rayuwar dan Adam, su ne don cimma farin ciki da
nagarta. Don haka, lokacin da aka hana mutane hakkinsu na kashe auren da ba a yi daɗi ba, waɗannan
biyun an keta su sosai. Wannan shine, kamar yadda ma'aurata za su rayu cikin wahala, wanda zai iya kai su
ga rashin imani a aure. Don haka saki a cikin wannan yanayin - idan an auna har zuwa bala'in rarrabuwar
iyali – zai zama ƙasa da bala'i.
Maza suna da hakkin saki. Idan mutum baya son kiyaye aurensa saboda wani dalili, sai ya saki matarsa
kuma ya biya mata kudi ta hanyar biyan ta abin da ake ce wa mut’a. Wannan kari ne akan abin da ake yi
mata na kudi akai-akai, idan har tana da hakkin 'ya'yansu.
Saki ya fara aiki da zarar miji ya furta ko ya rubuta duk wata ka'idojin saki na shari'a kamar: ‘Na sake ki’ ko
‘kin sakeki’...da sauransu. Miji na iya yin wadannan ko dai da kansa ko kuma ta hanyar manzo (Ɗan
aike).Idan har sha'awar mace ce ta yanke auren, lamarin ya zama daban. Dalilinta na iya zama cewa ta
sami rashin lafiya, miji baya iya ciyar da ita kudi ko kuma ba ya da karfin jima'i. Za ta iya tabbatar da
wadannan aibu a gaban alkali, sai alkali ya ba ta saki tare da samun cikakkiyar damar samun dukkan
hakkokinta na kudi.
Hakanan, idan mijin ya kyautata mata amma ba ta son ci gaba saboda wani dalili na zuci, sai ta tambaya
me ake ce masa khul’. Wannan yana nufin a ba da saki amma ba tare da samun dama ga haƙƙin kuɗi ba, da
kuma biyawa mijin sadakin da ya riga ya biya akan aurenta. Hajiya, duk na kori maki wannan jawaban ne
saboda kisan cewa shi fa kalmar saki ba abun da za ayi wasa dashi bane, A wasu lokuta, furta kalmar saki
ya zama mara amfani. Daga cikin wadannan har da lokacin da miji yake:1.) Buguwa. 2.) Wani ya tilasta
musu furta su. 3.) Cikin tsananin bacin rai har bai san abinda yake fada ba. 4.) A cikin yanayi mara kyau na
hankali, kamar hauka na wucin gadi, farfadiya ko a cikin suma. A irin wadannan lokuta, saki banza ne. Kin
ga kuma Khalil na ƙaunar matarsa, kece kawai kike son tilasta masa ya sake ta. Hajiya bari nayi maki wani
tambaya dan Allah, shin a zaman da kika yi da matar Khalil na kimanin shekaru biyu da ɗoriya, shin kin
taɓa ganin wani mummunar hali da take dashi? Shin ta taɓa zaginki? Ta taɓa dukanki? Ta taɓa hana ɗanki
zuwa gareki ko kuma yi maki wani alkhairin? Bin bata girmamaki da yi maki biyayya?" Shuru Hajiya tayi,
can kuma ta girgiza kai tare da faɗin, "Ko ɗaya, Saratu bata taɓa yi min ɗaya daga cikin abubuwan daka
lissafo ba." "To kin gani Hajiya! Hakan na nufin baiwar Allahn nan bata yi maki komai ba, kawai laifin ƴar
uwarta ne yake son shafarta. Hajiya dan girman ubangijin halitta, ki sassautawa zuciyarki ki bar maganar
Khalil ya saki matarsa, wallahi Allah zai yi fushi dake idan har kika tilasta masa rabuwa da matarsa, don
wallahi zaki iya haddasa ɓanna a bayan ƙasa, zata iya yuwuwa, ki tsinke igiyar dake tsakaninsu, amma
kuma suje suna bibiyar juna a waje bayan babu aure tsakanin su, kuma kin ga idan har haka ta faru, wallahi
kina da babban kamasho! Hajiya ina roƙon wannan Alfarmar, ki sassautawa Ibrahim kar ki raba shi da
matarsa dan Allah!" Ya Abdallah ya ƙarisa maganar a tausashe. "Uhm! Naji bayanka Marmari, kuma na
gamsu, sai dai nima ina da nawa sharuɗɗan." Gyara zama Ya Abdullahi yayi, Khalil wani sanyin rahama ne
ya shiga ziyartar lungu da saƙon jikinsa jin Hajiya ta janye ƙudurin saki, he is willing to accept all her
sharuɗɗa in har zata amince ya cigaba da zama da his light. "Na farko dai dole ne ya auri Habbooba, na
biyu, kar ya kuskura ya wulaƙanta min ƴa saboda matarsa kuma kar ya bawa matarsa fuskan da zata
wulaƙantamin ƴa saboda tana taƙamar ita ce matar so, na uku, yayi takakkiya har Maiduguri yaje ya nemo
soyayyar Habbooba, don ita ba _matar shige_ bace, idan har ya cika duk wannan, na amince ya cigaba da
zama da matarsa, zan yi azumi uku na rantsuwar da nayi." Faɗin Hajiya, "To kai kaji Khalil, shin ka amince
na abunda Hajiya tace." Gabansa na bugun tara-tara ya ɗago ya kalli ya Abdallah, sannan ya kalli Hajiya
tare da sunkuyar da kai ya furta, "Na amince da duk abunda kika ce Hajiya. Zan je Nassarawa na dawo da
Sarah, bayan na dawo sai in tafi Maidugurin!"

( _Ni kuwa nace Uhmmm! To me zance ni Matar Sayyadeen banda uhm ɗin? Dan-dan-dan-dan-dan-dan!
Akafta_ 🙆)

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[14/11, 12:31 PM] Matar Sayyadee: Taɓe baki Hajiya tayi, don gaba ɗaya Sarah ta gama ficewa daga
zuciyarta. "Allah ya kiyaye hanya! Yaushe zaka wuce?" Ɗan shuru yayi, sai kuma can yace, "Hajiya, idan so
samu ne in tafi tun yau!" Ya ƙarisa maganar a raunane. Wannan karon ma taɓe bakin tayi tare da faɗin,
"Allah ya jiyaye hanya, ka dai tabbatar kana tafiya kana sauraran karatun Alkur'ani, sannan kana isa ka
kuma tabbatarwa da Li'ilafi a bakinka, atoh! Na dai faɗa maka." Murmushi ya Abdallah da ya Abdul-
Hakeem suka yi a lokaci guda, yayin da Khalil yace, "In Sha Allah Hajiya." Yana gama faɗin haka ya miƙe
jikinsa har rawa yake yi ya fice, ya ƙosa yaje yaga halin da matarsa take ciki. "Uhm, dubi yanda jikinsa ke
rawa akan mace kamar wawa, Allah dai ya kyauta!" Faɗin Hajiya tana wani rausayar da kai. Wannan karon
ya Barrister ne yayi dariyar yana mai sunkuyar da kai don yanda Hajiyar ta rausayar da kai ba ƙaramin
dariya ta bashi ba. Khalil kuwa wuta-wuta ya tafi ya ɗauko ɗayan ATMcard ɗinsa da kuma 200k da yake
dashi cash a ƙasa sannan ya canza kaya sharp-sharp ya fito ya ɗago ɗakin Hajiya, kallo ɗaya Hajiya tayi
masa tace, "Uhm" tare da kawar da kai. Har gabanta ya isa tare da faɗin, "Hajiya kiyi addu'a zan tafi."
"Allah ya tsare ya kiyaye hanya." Shine abunda tace kanta a juye. Miƙewa yayi tare da kallon yayyin nasa
tare da faɗin, "Zan wuce, a saka ni cikin addu'a yaya." Gaba ɗaya suka haɗa baki wajen faɗin, "Allah ya
kiyaye hanya Ibrahim." Ya Abdallah ya ƙara da faɗin, "A gaida iyayen matar naka, kar kuma ka manta ka tafi
hannu rabbana, kayi masu tsaraba a hanya." Da "In Sha Allah." Khalil ya amsa. "Allah ya kiyaye hanya yaya
Khalif, a gaida Aunty Sarah da ƴan biyu, a faɗa masu nayi kewarsu." Faɗin Laure. "Ameen Laure, in Sha
Allah zasu ji." "Ƙarshen kewa, je kwaso kayanki ki bishi ku tafi." Faɗin Hajiya tana mai zabgawa Laure
harara. Shi kansa Khalil ɗin sai da ya murmusa kamun ya fice daga ɗakin. Kai tsaye wajen mota ya nufa tare
da shiga ya tada ya bar gidan ya ɗau hanya. A can Nassarawa kuwa, Nnanne ce a ɗaki daga ita sai Sarah
wacce ke zaune a wajen ƙafafunta. "Takwarata, zan baki labarin wanene mahaifinki da kuma mahaifiyarki.
Kin ganni nan, bani ce na haifi ubanki ba, amma yanda nake sonsa da ƙaunarsa, ko mahaifiyarsa sai da ta
nuna min ta jikinta ya hudo yazo duniya. Ni da mahaifiyar Nuhu, uwarmu ɗaya, uban kowa da dashi. Don
bayan mutuwar mahaifin ya Rahmatu, shine Mahaifiyarmu ta auri babana. Ita tasha mama ta sakarmun,
gaba da bayan mahaifiyarmu, Nindire ne, kuma anan cikin wamba aka haifi mamanmu, gadon gidanmu
shine ilimi, don sunan gidanmu, gidan malamai. Ubansu Nuhu, da Mahaifiyarmu ni da mahaifiyar Nuhu,
uwa ɗaya uba ɗaya suka haifesu, kin ga kenan auren zumunci akai wa mahaifiyar Nuhu da mahaifinsa.
Mahaifiyarsu Nuhu, kakarki kenan, macece mai haƙurin gaske, da wuya mutun yaga ɓacin ranta, ko shi
mahaifinsu Nuhun, yace har ta koma ga Allah bai taɓa ganin ɓacin ranta ba, ga biyayyar aure! Bayan
rasuwarsa ne mahaifinmu ya bashi ni, don ya Rahmatu tana haihuwarsu Nuhu da Nura jini ya ɓalle ta amsa
kiran Ubangiji. Bata taɓa haihuwar ɗa ɗaya ba, baban ku Lukman da Kamal sune ƴaƴanta na fari, bayan ta
yaye su ne ta haifi su mahaifinki, ina tunanin ita kika gado. A wannan lokacin ni kuma mijina zaman mu ya
ƙare, haihuwar mu ɗaya dashi, Ruƙayyatu, gaba ɗaya dai zaman namu dashi na shekara ɗaya ne auren ya
mutu, kuma ban kuma wani auren ba, ashe rabon Alyasa'a ne. Bayan arba'in ɗin yayata Rahmatu, aka
ɗaura aure na da Alyasa'a, ni na cigaba da shayar dasu ƴan biyu tare da rainon su Lukman da Kamal.
Yarane masu matuƙar tarbiyya, tun sun Lukman nada shekaru goma sha ɗaya suka haddace Alkur'ani, don
yaro ma ba'a saka shi boko sai ya haɗa izu goma. Na haifi ƴaƴa hudu a nan gidan, Raliya, Zainabu, Khadijah
da Usman. Duk a cikin ƴaƴana nafi ƙaunar Nuhu, don yarone mai sanyin hali da biyayya, duk da sauran ma
suna da biyayya, amma Nuhu daban ne, abunda yasa ake saurin bambamce su kenan da tagwaininsa, don
Nura sak nine, yana da zafin rai da kuma riƙo. Lokacin da suka kammala secondary School, basu cigaba da
makarantar gaba ba, sai kowanne ya cigaba da sana'ar da yake yi, Lukman harkar noma yake yi, Kamal
kuma sana'ar fata, Nura kuma harkan kayan mata yake yi, wanda kuke kira konsimetis (Cosmetics), shi
kuma Nuhu sai ya zaɓi harkar tafiye-tafiye a mota yana tuƙa irin manyan motocin nan. Duk abunda nace
wa Nuhu ina so, sai dai idan bai da shi, sannan idan nace masa bani son abu kaza, har abada ya bar abun
nan duk son da yake masa. A can ƙasan layin nan, idan kika yi kwana daga hannu dama, layine na wasu
mutane wanda basa addinin musulunci, ɓangare ɗaya, addinin kakanni suke yi, bautar gumaka (Traditional
religion), ɗayan ɓangaren kuma, kiristoci ne, (Christianity religion), sam waɗannan addinai biyu, basa shiri
da juna, kuma basa ga maciji. Pasto Emmanuelle, wasu kuma suna kiranta Debora, itace mahaifiyar
mahaifiyarki, ita ta kasance cikakkiyar kirista ta Catholic, irin masu zafin nan ne su, kamun zamanta pasto,
ko kuma ince maki kamun ta girma izuwa pasto, sun ƙulla soyayya da mahaifin Debora (Mahaifiyarki),
kuma shi mahaifin Debora yana bin addinin kakanni ne wanda kiristoci basu yarda dashi ba, kuma suna
ganin addinin da suke yi bana gaskiya bane, sannan dangin Samuel (Akanchewa Uchendo), sun ƙasance
ƙasurgumamun matsafa ne na bugawa a jarida. An kai ruwa rana sosai kamun dangin biyun nan suka
amince da aurensu wanda sai da Samuel yayi mata ƙaryar ya koma addininta na kiristanci sannan akai
auren wanda kuma a zahirin gaskiya bai koma addininta ba, yana nan yana tsafinsa. Bayan haifuwar
Elizabeth, mahaifiyarki Kenan, sai a lokacin Debora ta gano cewar Samuel bai bar addininsa ba, yana nan
kuma yana tsafinsa, dalilin haka ta kaisa kotu suka rabu tare da goyon bayan iyayenta sannan kuma ta
kwace Elizabeth ta mayar da ita hannunta. Su kuma iyayen Samuel sun ji haushin haka sosai, sai suka yi
wani mummunar tsafin da yayi sanadin rayuwar iyayen Debora ta hanyar dogon jinya da kuma aman jini.
Bayan mutuwarsu, hakan ya ƙara tsananta wutar gaban dake tsakanin two families ɗin sosai har ta kai ga
sai da hukuma ta shiga tsakanin su. Samuel baya zuwa ganin Elizabeth, haka itama Elizabeth bata zuwa
ganin Samuel kamar ba mahaifinta ba, don mahaifiyarta ta nuna mata cewar ai dangin Samuel gaba ɗaya
ƴan wuta ne. Duk lokacin da Nuhu yazo Nassarawa, yana yawan zuwa can unguwarsu Elizabeth
kasancewar yana da abokin da suke aikin mota tare, duk da Chidebere ba musulmi bane, amma yarone
yaron kirki don na jima ina masa fatan hasken musulunci. To a wannan unguwar Nuhu yaga ƙawar
Elizabeth (Lami) kuma yaji yana sonta. A yanda labari yazo min, ita Elizabeth ɗin ya samu da zancen
kasancewarta babbar ƙawarta domin ta shawo masa kan ita Merry ɗin. Amma bayan wasu kwanaki
Kwatsam, sai Nuhu yazo ya same ni da zancen yana son wata yarinyar ƴar unguwar wai ita Elizabeth, koda
yazo min da wannan zancen, koren kare nayi masa tare da faɗa masa in har nice mahaifiyarsa, to ban
yarda ya ƙara kallon unguwar ba balle ma ya ƙara zuwa wajen yarinyar. Tun daga wannan rana kuwa, ban
kuma jin makamancin labarin ba, sai na ɗauka ya watsar da zancen. Amme me, bayan wasu watanni, sai ga
motocin ƴan sanda har biyu a ƙofar gidan nan, lokacin mahaifinsu Nuhu na fama da cutar ciwon ciki na
ajali, sai ga sallama wai ana neman mu a police station, duk da Alyasa'a bai jin daɗi haka ya kwashi jiki shi
dasu Lukman da shi kansa Nuhun suka tafi caji ofis, acan caji ofis sai da akai masu tijara sannan aka rubuta
yarjejeniya akan babu Nuhu babu kula Elizabeth, Wai a cewarsu zai ɓata mata tarbiya kuma ya hure mata
kunne. Sosai wulaƙancin da akai masu a caji ofis ya tsayawa Alyasa'a a zuciya har yayiwa Nuhu furucin idan
har ya sake ya ƙara kula masu ƴa to bai yafe masa ba. Ni kai na kamar zan ari baki wajen faɗa. Ashe a can
gidansu Elizabeth kuma, tana can tana ta ihu da kuma akan ita tana son Nuhu a haka, kuma idan aka
rabata dashi zata kashe kanta. Ance har coci-coci aka kaita ana mata addu'a akan ta dawo cikin hayyacinta,
amma tana nan kan bakanta. Wata rana da daddare ta haɗa kayanta ta gudu gidan babanta, a wannan
ranar sai da Samuel yayi shagali ana ta yanke-yanken dabbobi, saboda ya ƙuntatawa Pasto Emanuella
Debora rai, sai yayi alƙawarin sai ya cika mata burinta na auren Nuhu. Ranar da farin ciki Elizabeth ta
kwana. A can gidan pasto Deborah kuwa, ba ƙaramin tashin hankali ta samu ba, don ta san idan har haka
ta kasance, sosai zata samu koma baya daga mabiyanta. Don da yawan mutane zasu daina zuwa cocinta
balle su saurareta. Har gida taje ta samu Samuel akan ya bata ƴarta, amma ya nuna mata sam bai san
wannan maganar ba, ƴarshi ita ta zaɓi dawowa ƙarƙashinsa, amma kuma ga Elizabeth nan, idan ta yarda
zata bita, to ta kama hannunta su wuce. Amma ƙememe Elizabeth ta nuna baza tabi Pasto Debora ba.
Debora a zuciye ta fice daga gidan, in taƙaice maki dai magana har kotu, kuma Samuel ne da nasara, don
Elizabeth ta nunawa alƙali cewar bada ƙarfi mahaifinta ya mayar da ita gidansa ba, itace taji tana son
komawa da zama wajen mahaifinta. Ana fitowa daga kotu pasto Emanuella ta kira taron ƴan jarida ta
shaidawa duniya ta tsinewa Elizabeth, yanzu ba ƴarta bace ba har sai lokacin da ta dawo wajenta gaba
ɗaya ta kuma bata haƙuri tare da fita harkan Musulmin saurayin da take so gaba ɗaya. Duk wannan bala'in
da ake yi, ashe kullum idan har Nuhu na gari yana gidan matsafan nan wajen ɗiyar Debora, a can yake cin
abinci. Lokacin da mahaifinsa ya samu wannan labarin a cikin gari, kusan faɗuwa ya kusa yi kuma dama
gashi ba isasshen lafiya ba, nan muka tara Nuhu muna masa faɗa sosai. Wani ihu daya kwatsatsamin bani
ba, hatta mahaifinsa sai da ya firgita, Nuhu babu kunya ya shiga cemin, 'Ke ba Mahaifiyata bace, baki isa ki
yankewa gobena hukunci ba, don haka babu wani banzan da ya isa ya hanani auren Elizabeth Lami'. Dafe
ƙirji Alyasa'a yayi tare da faɗin, har dani kake faɗawa haka Nuhu?' Nuhu sai ya riƙe ƙugu ya ɗage kai yana
hura hanci. Zamewa ƙasa Alyasa'a yayi tare da kallona na buɗe baki zanji magana kenan yace, 'Bar shi
Saratu, bar shi! Yaje duniya zata koya masa hankali. Ban amincewa ɗan da na haifa ya ƙara yi masa magana
ba, sannan ban yarda ya ƙara zama min a cikin gida ba, sannan duk wani abu da yasan nawane, ya ajiye ya
tafi!" Yana gama faɗin haka ya juya ya shige ɗaki. Ina kallon lokacin da yake share hawaye. Shi kuwa Nuhu
kaɗa kai yayi ya fice yan faɗin 'To se me don an kore ni, duniya ai faɗi ce da ita.' wannan rana ita ce ranar
da na saka Nuhu a idanuna na ƙarshe. Daga ƙarshe muka samu labarin wai ya musuluntar da Elizabeth har
sunyi aure sun bar garin. Basu fi wata biyar da barin garin ba, Alyasa'a ya amsa kiran Ubangiji, amma kin
san wani abu, tsakanin ɗa da mahaifa, kamun Alyasa'a ya cika sai da ya furta kalmar yafiya ga mahaifinki.
Wannan shine labarin sanadin barin gida da mahaifinki yayi." Sosai Sarah ke kuka kamar ranta zai bar jiinta.
"Nnanne ina ji a jikina Babana ba'a cikin hayyacinsa yayi maku duk abinda yayi maku ba, ke da kanki kin ce
baban mamana matsafine, kuma yayi alƙawarin cikawa mamana burinta domin ya baƙantawa mahaifiyar
mamana, to wallahi zai iya komai daga ciki har da juya kwakwalwar mamana. Kuma jikina ya bani, shi ya
mayar da soyayyar da Babana kewa Aunty Rose Merry izuwa kan mamana domin ya samu cikar burinsa,
tunda tun farko ai Aunty Rose Merry ɗin Baba ke so ba Mamana ba. Nnanne akwai alamar tambaya akan
wannan batu!" Shuru Nnanne tayi na wasu daƙiƙu tare da faɗin, "To, Allah masanin gaibu Saratu. Mahaifin
mamanki ne kawai zai iya warware wannan ƙullin, idan shi sanadi ko bashi bane." Da sauri Sarah ta kalleta
tare da faɗin, "Yana nan a raye ne?" Jinjina kai Nnanne tayi tare da faɗin, "daga Samuel har pasto
Emanuella Debora suna nan a raye!" Dafa Nnanne tayi tare da faɗin, "Nnanne idan kinyi min lamuni, zan je
gidan domin na gana dashi mahaifin maman nawa." Murmushi Nnanne tayi tare da faɗin, "Bashi kaɗai ba,
har ita pasto ɗin zan so ki kai mata ziyara. Idan kin nutsu zuwa gobe, zan saka a kai ki. Idan zaki tafi, zan
baki kuɗi sai ƴar wajen Lukman ta raka yi." Da sauri Sarah tace, "Nnanne Ina da isassun kuɗi, Khalil ya bani
ATMCARD ɗinsa domin nayi amfani da kuɗin ciki idan buƙatar haka ta taso." "To ma sha Allah!" Faɗin
Nnanne. Sarah kuma tashi tayi tare da faɗin, "Nnanne zan fita na ciro kuɗin yanzu nayi sayayyar, kin ga
goben sai dai kawai mu wuce." Gyaɗa mata kai Nnanne tayi. A nan gaban ƙofar gidansu ta ciri dubu
hamsin. Kuma a wannan lokacin ne Khalil yaga alert ɗin kuɗi ya shigo wayarsa wanda hakan ya nuna masa
inda Sarah take. Washa gari tun ƙarfe goma Sarah ta saka Suhana a gaba akan ta tashi su tafi gidan Samuel.
"Wai ke baki da kunya ko? Kakanki ne kike kiran sunansa gatsau haka? Kaka Samuel zaki ce!" Harara Sarah
ta maka mata tare da faɗin, "Anƙi ace kakan, kako ba kaka. Kaji wani suna wai Samuel!" Ta ƙarisa maganar
tare da bushewa da dariya. "Baki da kirki maman twins!" Faɗin Suhana tana ƙarisa sakawa Sam'an takalmi.
"Wai auntyn Sam'an, dasu za muje?" Faɗin Sarah. Hannun Sam'an ɗin ta kama tare da faɗin, "Kwarai
kuwa! Sauban muje kaji." Ta faɗi tana riƙe hannayensu. Komai Sarah bata ce ba har suka fito parlourn,
matar ba Lukman suka samu a parlour, "Aunty zamu wuce!" Faɗin Sarah. "To Sarah, Kar dai a manta ayi
addu'a, sannan idan sun baku nama, kar kuci." Da "To" suka amsa sannan suka fita daga ɗakin, sai da suka
ƙara zuwa wajen Nnanne suka yi mata sallama sannan suka fito. Kasancewar babu nisa, a ƙafa suka yi ta
takawa har suka gangara, sun zo wajen ƙofar gidan wani makeken gida wanda gaba ɗaya wanda shi ya
haska unguwar, sai Suhana ta taɓo Sarah tare da faɗin, "Sis ga gidan kakarki, pasto Emanuella Debora."
Ɗaga kai Sarah tayi, babu abunda idanunta suka fara ganin sai tafkeken sunanta a jikin saman gidan,
_Pasto Emanuella Debora Gabriel House_. "Lallai matarnan taji kuɗi, duk wannan uban gidan nata ne?"
Gyaɗa mata kai Suhana tayi tare da faɗin, "Kuma ƴata rak kawai gareta, Mahaifiyarki!" Taɓe baki Sarah tayi
suka cigaba da tafiya har zuwa wani ƙaton ginin ƙasa, rabin katangar ta zube kana iya hango mutanan dake
ciki, ga manya-manyan tukwane nan a kan murhun duwatsu har huɗu, gefe kuma ƴan matane su kusan
bakwai da ɗaurin ƙirji, wasu kuma ɗan siketi ni iya ƙauri sai riga da bata gama rufe cibiya ba da uban kitson
attachment har baya, farcen hannu zaƙo-zaƙo da ƙumba. Wasu tsoffi kuma zagaye a akan wani banci suna
wani abun da su Sarah basu sani ba don basu iya hangowa. Can gefe kuma samarine da manyansu suna
shan wani abu a kofi, wasu kuma suna buɗe wannan tukunyar suna ɗeban abun ciki suna sha. "Kin ga
wancen abun da suke sha a kofi, sunansa burkutu." Faɗin Suhana. "Burkutu dai!" Sarah ta faɗi tana kallon
Suhana, jinjina mata kai tayi daidai lokacin da suka iso ƙofar gidan. "Gafaranku dai!" Faɗin Suhana. Gaba
ɗaya mutanan gidan suka zuba masu idanu, "Lafiya?" Wata budurwa mai ɗaurin ƙirji ta faɗi. "Mun zo
wajen baba Samuel ne." Faɗin Suhana. Da hannu suka yi masu nuni da ɗakin, domin idan da sabo sun saba
ganin musulmai suna zuwa gidan wajen baba Samuel domin yayi masu aikin asiri kasancewarsa
shahararren matsafi. Daga asabarin dake ƙofar suka yi sannan suka shiga. Ɗagowa wani tsamurarren tsoho
yayi tare da kallonsu, wani murmushi ya saki sannan ya nuna masu wajen zama tare da kallon Sarah yace
mata, "Jikata, ƴa ga Elizabeth! Kin zo nan ne domin son sanin mahaifinki Nuhu yana cikin hayyacinsa ya ƙi
bin umarnin Mahaifansa ya auri Elizabeth ko?" Da mugun mamaki Sarah ta kalli Suhan sannan ta mayar da
kallonta izuwa ga Baba Samuel. Murmushi yayi tare da nuna mata tukunyar tsafin dake gabansa, sannan
yace, "Duk wanda ya iso ƙofar gidana tukunyar tsafina take faɗa min zuwansa da kuma abunda ya kawosa
gare ni. Ina ƴata Elizabeth?" Shuri Sarah tayi tana kallonsa, babu ta inda ta hango kamannin mamanta a
jikin wannan yamutsatstsan tsohon, sai dai tabbas taga wani baƙin halitta dake cikin kwayan idanunsa
wanda akwai shi sak a idanun Lami. Dariya Baba Samuel yayi mai sauti wanda ya saka Sarah saurin kallonsa
ita da Suhana. "Tabbas hasashenki gaskiya ne! Ni na juya tunanin mahaifinki, sannan ni na sanya soyayyar
ƙawar mahaifiyarki ya juye na mahaifiyarki a zuciyar babanki, Elizabeth bata taɓa son Nuhu ba, haka Nuhu
bai taɓa son Elizabeth ba, nayi amfani da dutse ɗaya ne na jefi tsuntsu biyu, na haɗa wannan soyayyar ne
domin in wulaƙanta tsohuwar matata pasto Emanuella Debora Gabriel, na biyu kuma domin in rama
abunda mahaifin Rose Merry yayi min, kuma naji daɗi sosai saboda na rama komai cikin sauƙi." Ya ƙarisa
maganar yana dariyar jin daɗi. Miƙewa Sarah tayi tare da kama hannun Suhan tace, "Tashi mu tafi Suhan,
tsoro tsohon nan yake bani!" "Mijinki yana hanya, yanzu haka yana cikin unguwar nan yana cigiyar
gidanku, sannan nan da wasu kwanaki masu zuwa, mijinki zai sake auren wata ƴarinya kyakkyawa wacce za
tayi yunƙurin kwace maki fada a cikin gidanki, baza ku taɓa jituwa da ita ba, yarinya ce mai tsananin kishi,
sannan uwar mijinki bata sonki yanzu, kuma akwai wani abun mamaki da zai faru kuma zai girgiza uwar
miji kuma sannan........." "Muje Suhan!" Sarah ta faɗi da ƙarfi jikinta na rawa. Da sauri Suhan ɗin tayi gaba,
yayin da Baba Samuel ya ɗaga murya tare da faɗin, "Idan kina neman wani taimako, kiyi gaggawan zuwa
nan, cikin ƴan daƙiƙu zan gyara maki komai."

( _Mu haɗe tomorrow, walleh na gaji_)

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[14/11, 12:31 PM] Matar Sayyadee: "Suhan kina jin abunda wannan kafurin bawan yake faɗi?" Dariya
Suhana tayi tare da faɗin, "Matsafi menene ba zai iya kintata ya faɗa maki ba! Kar ki yarda ki saka
maganarsa cikin zuciyarki, don ƙarya yake faɗa maki. Ko da wasa kar kiyi imani da abunda ya faɗa maki."
Ajjyar zuciya Sarah ta saki tare da faɗin, "Uhm, dama wanene zai yarda da zancen mushiriki? Sai mushiriki
irinsa, Allah ka tsare mana imanin mu." Da ameen Suhana ta amsa suka cigaba da tafiya, amma kuma ƙirjin
Sarah bai dena bugawa da sauri-sauri ba. "Ya, zamu shiga ne?" Faɗin Suhana tana kallon gidan _Pastor
Emanuella Debora Gabriel_. Girgiza kai Sarah tayi tare da faɗin, "A'a muje gida kawai, ba yau ba. Wani
lokacin mazo." Ɗaga kafaɗa Suhana tayi suka cigaba da tafiya. "Ƴan mata, dan Allah ji mana!" Daga Sarah
har Suhana babu wanda ya kalli gefensa, cigaba da tafiya suka yi. "Baiwar Allah dan girman ubangiji ki
tsaya ki saurareni!" Ya faɗi bayan yasha gaban Sarah tare da haɗe hannunsa biyu. "Bawan Allah gafara min
a hanya ni matar aure ce, kar ka ketahaƙƙin aure Please!" Tana gama faɗin haka ta gittasa ta wuce. Da
sauri ya kuma bin su ya tsaya ta gefen Sarah suna tafiya a jere, daga nesa idan ka gansu zaka rantse tafiya
suke suna hira. "Malam baka da hankali ne, tace maka matar aure ce, ko baka gani ne? Duba nan
waɗannan da kake gani, yaranta ne!" Suhana ta faɗi a kausashe. "Nima mijin aure ne Malama!" Saurayin
ya faɗi yana dariya. Babu wanda ya ƙara tankasa tsakanin Sarah da Suhan, shi kuma mayen sai binsu yake
yi yana zuba zance, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Sarah ta faɗi tare da soma rage tafiyarta ganin
motar Khalil a ƙofar gida, shi kuma jingine a jikin motar yana danna waya, kamar ance ya juyo, sai suka yi
idanu huɗu dashi, da sauri Sauban da Sam'an suka fizge daga hannun Suhan suka nufi Khalil suna faɗin,
"Daddy!" Shi kuma Khalil gaba ɗaya hankalinsa yana kan Sarah da saurayin dake gefenta, nan da nan wani
mahaukacin kishi ya turniƙe masa zuciya, ransa yayi mummunar ɓaci kamar zai yi bindiga ya fashe,
idanunsa har ƙanƙancewa suka yi tsabar bala'in dake cinsa, duk farin cikin da ya taho dashi sai yaji gaba
ɗaya yana neman rushewa. Hannu twins ya kama ya saka a jikinsa ba tare da ya cire idanunsa akan Sarah
da saurayin ba. "Shine babansu twins?" Faɗin Suhana a kunnan Sarah. Jinjina mata kai Sarah tayi tare da
saurin yin gaba ta wuce wannan saurayin kaɗan ganin irin kallon da yake binsu dashi. Da tsaurin idanu da
kuma rashi hankali tare da rabon shan duka wannan saurayin ya kai hannu tare da janyo gyalen Sarah yana
mai faɗin, "Haba ƴan mata, tun ɗazu nake ta yi maki magana kinƙi kulani. Wani mummanar ɓarin
makauniya Khalil ya sauke masa a both chics ɗinsa tare da kuma sauke masa naushi a karan hancinsa, nan
take jini ya ɓalle. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Sarah ta faɗi da ƙarfi, yayin da Suhana ta faɗa cikin
gida da gudu ganin Khalil ya shaƙi wuyan saurayin nan yana ta kai masa naushi a baki da hanci, don riƙo
yayi masa ba ƙarami ba. Sarah kuwa babu abinda take yi sai salati da kuka tana faɗin, "Dan girman Allah
Happiness ka sake shi kar ya mutu!" "Bar nan wajen yanzu! Zan dawo kanki idan na nagama dashi." Ya faɗi
a mugun tsawace sai da Sarah taja baya ganin yanda idanunsa suka canza launi, "Yau sai na koya maka
hankali ta yanda ko macen Akuya ka gani baza ka mata kallo biyu ba balle kuma matar wani!" Khalil ya faɗi
yana ƙara kai masa duka. Da sauri Sarah ta kamo twins ta rungume a jikinta tana kuka. Ba Lukman ne cikin
sauri tare da Suhana dake biye dashi a baya, riƙe hannun Khalil yayi cikin sauri tare da faɗin, "Yi haƙuri ka
sake shi dan girman Allah!" A hankali Khalil ya saki wuyar rigar saurayin yana mai jifansa da harara. Kallon
saurayin ba lukman yayi tare da faɗin, "Ya akai haka samari? Da hankalinka zaka bi matar aure bayan ta
shaida maka ita matar aure ce?" Saurayin da hannu biyu a sama ya soma faɗin, "Rabon shan duka ne ya
kawoni layin nan Wallahi, amma ba layin bina bane, kuma wallahi tabbas ta faɗa min ita matar aure ce,
amma na ɗauka wasa take yi don haka wasu ƴan matan ke faɗi." Wani naushin Khalil ya kuma kai masa, da
sauri Ba Lukman ya tare tare da faɗin, "Haba bawan Allah, kayi haƙuri mana." Sai ya juya ya kalli saurayin
tare da faɗin, "Daga yau idan halinka ne ka kuma, ko da ace ita ɗin ba matar aure bace, ai be kamata tunda
har ta furta maka kalmar tana da miji sai ka haƙura ka kyaleta, to ai gashi nan taurin kai ya jawo maka
bugu." "Ayi man afuwa, wallahi na daku in sha Allah ba zan ƙara wannan kuskuren ba." "Kama ƙara!" Khalil
ya faɗi yana mai jifansa da harara. Da sauri saurayin ya bar wajen jini na ɗiga daga hancinsa. Ba Lukman
kuwa cikin zuciyarsa cewa yayi, "Haka ake son kowani namiji ya kasance mai kishin matarsa." Amma a
zahiri sai cewa yayi, "Ko kai ne wanda aka ce yana sallama dani a waje?" Sunkuyar da kai Khalilullah yayi
yana gyara zaman rigarsa tare da faɗin, "Eh, nine baba." Sai kuma ya ɗan rage tsayinsa tare da faɗin, "Baba
ina wuni?" Murmushi ba Lukman yayi tare da faɗin, "lafiya ƙalau, shigo daga ciki mana." Faɗin ba Lukman
tare da yin gaba, hanya Khalil ya nunawa Sarah alamar tayi gaba, hannun ƴan biyu ta kama suka shiga
gidan Suhan a bayansu sannan shima yabi bayansu. Gaba ɗaya ɗakin Nnanne suka nufa, ba Lukman ne ya
soma shiga sannan su Sarah, "Shigo mana!" Ba Lukman ya faɗa yana mai ɗaga labule. "Wanene?" Daga ciki
Nnanne ta faɗi. Juyawa Ba Lukman yayi tare da faɗin, "Mijinta ne." Ya faɗi maganar yana nuna Sarah.
Duƙawa Khalil yayi tare da cire cover shoe ɗin ƙafarsa, kyakkyawar ƙafarsa cikin safa ta bayyana. Sai da yayi
Sallama sannan ya kutsa kai ya shiga parlourn Nnanne. Bai zauna a kan kujera, a ƙasa ya ɗuka, da sauri
Nnanne tace, "Tashi, maza tashi ka hau kan kujera ka zauna." Sai ta juya ta kalli ba Lukman tare da soma
magana cikin yare. Da sauri ba Lukman ɗin ya fita bayan ya kuma nunawa Khalil wajen zama alamar ya
koma kan kujera ya zauna. Khalil bai zauna ba sai da gaida Nnanne tukun ya zauna, yana zama twins suka
tafi wajensa ya ɗaura su a jikinsa. "Sannu da zuwa, na sha hanya! Yasu wajen iyayen naka?" Kai a ƙasa
Khalil yace, "Alhamdulillah, duk suna gaishe ku!" "To madallah!" Faɗin Nnanne dai-dai shigowar matar Ba
Lukman ɗauke da faranti a hannunta. A gaban Khalil ta dire faranti tare da faɗin, "Barka da zuwa!" Kai a
ƙasa ya gaisheta. Ta jikin bango Sarah tayi ta matsawa a hankali har ta fice daga ɗakin, duk Khalil na
kallonta har ta fice, kuma tun da ta bar ɗakin bata kuma ko leƙa tsakar gida ba. "Maman twins gaskiya kin
yi mugun sa'ar miji, wannan kyakkyawa haka ga gayu, sannan uwa uba irin wannan so da kishin ki da yake
haka! Wallahi kice Alhamdulillah!" Murmushi Sarah tayi tare da faɗin, "To Alhamdulillah!" A can ɗakin
Nnanne kuwa, bayan takurawa Khalil da Nnanne tayi sai da yaci kusan rabin abincin nan, sannan ta kira
duka ƴaƴanta maza ta riƙa introducing ɗin su ga khalil, lokacin da Khalil yayi arba da Ba Nura, sai da
mamakinsa ya bayyana a fili, Nnanne na Lure dashi, murmushi tayi tare da faɗin, "Tagwainin sirikinka ne,
sunansa Nura, tare da aka haife su da Nuhu, wannan kuma (Tayi nuni ga Baba kamal) ga tagwaininsa nan,
Lukman." Cike da sha'awa Khalil ya kallesu tare da ƙara gaidasu. Amsa masa suka yi suma cikin sakin fuska.
Nnanne tayi gyaran murya tare da faɗin, "Ibrahim, mun ji labarin komai daga matarka, sai dai kuma yanzu
muna son jin ta bakinka domin mu san ta yanda zamu ɓullowa lamarin." Shuru Khalil yayi na wasu daƙiƙu
kamun ya soma bada labari kamar yanda Sarah ta bada, har ma da wanda bata sani ba, lokacin da yake
bada labarin abunda Aina'u tayiwa Baba Nuhu, fashewa da kuka yayi, don duk lokacin da ya tuno ƙunar
dake ransa na abunda Aina'u tayi masa, sai kuma Baba ya faɗo masa rai, don idan har shi da yake Mijin
yayarta yaji wannan ƙunar, to ya baba da yake mahaifinta zai ji. Sai da ya fyeɗe masu kaf amma kuma ya
ɓoye masu ƙiyayyar da Hajiya take yiwa Sarah yanzu ba da kuma zancen auren da zai yi. Gaba ɗaya ɗakin
suma kukan suka saka, Nnanne kuwa har da shashsheka. "Nannan wannan Aina'u ta tabbatar ita ɗin jikar
matsafi Samuel ce! Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, duniyar nan ina zaki damu ne!! Ace ƴa tayi kwanciyar
aure da mahaifinta." Faɗin Nnanne tana fyatar majina. Shuru ɗakin ya ɗauka na wasu daƙiƙu. Can Nnanne
tace, "Tabbas Ibrahim kun bar Allah a lamuranku, kun fifita boko akan ilimin addini shiyasa Allah ya barku
da iyayenku, shi kuma Nuhu, zan iya cewa hakan yana cikin ƙaddararsa ce. Allah Sarki Nuhu ko gawan
ubansa bai gani ba." Ta ƙarisa maganar tare da fashewa da kuka. Wani irin shuru ɗakin ya ɗauka, can kuma
Nnanne ta kalli Khalil tare da faɗin, "Kai Ibrahim, ƙafata ƙafarka zuwa Kaduna, mutuwa ce kawai zata
hanani zuwa Kaduna." "Ai Nnanne ba ke ɗaya ba, har da mu!" Faɗin ba Lukman. Khalil kallon Nnanne yayi
tare da faɗin, "Nnanne dama zuwa nayi na tafi da Saratu. Dan Allah kuyi haƙuri da abunda ya faru kar ku
hanani tafiya da ita, wallahi ba cika hayyacina nake ba duk abubuwan da suka faru!" Da sauri Nnanne tace,
"Kaji wata magana! Kai Ibrahim ai mune zamu roƙi wannan alfarmar ba kai ba, don jininmu ce tayi maku
laifi. Aina'u ita ce silan komai, kar ka manta har kashe maka ƴar uwa tayi tare mijinata da kuma jinjiranta
da gama shaƙar iskar duniyar bata yi ba. Wallahi kai zamu baiwa haƙuri. Ai mu ka nuna mana so da ƙauna,
idan da wani namijin ne, duk soyayya da ƙaunar da yake wa Sarah, kai ko da duniya suka haifa tare, ba zai
ƙara zaman aure da ita ba. Mun gode Ibrahim, mun gode Allah ya saka maka da alkhairi, Allah ya dubi
zuri'ar ka, ya kare ku daga sharrin maƙiya na kusa dana nesa, ya kuma shirya maka zuri'a ya ƙara buɗi." Da
Ameen Khalil ya amsa yana jin sanyi a ransa. "Nagode sosai Nnanne, goben sai mu tafi tare, motar zata
ɗauke mu duka in Sha Allah!" "Ai ko bata ɗauke mu ba, akwai ta gida sai babban ɗan Lukman Hamisu yaja
motar." Faɗin Nnanne. "Haka ma za ayi!" Faɗin ba Nura. "Allah ya kai mu goben! Ku nuna masa masauki,
basu gaisa da matar tasa ba" Fadin Nnanne. Miƙewa Khalil yayi yabi bayan ba Nura tagwainin Baba Nuhu.
Can farkon gidan suka nufa, ba Nura ya saka key ya buɗe ɗakin tare da faɗin, "Shiga a share yake tass!"
"Nagode baba." Khalil ya faɗi yana mai kutsa kai cikin ɗakin. Ƙatuwar katifar ƙasa a ɗakin an lailayeta da
zanin gado sai bayi. Zama yayi a gefen katifar yana kallon ɗakin. Wayarsa ce tayi ƙara, yana jin ringing ɗin
yasan cewa Hajiya ce saboda special tone ɗin da ya saka mata, katse kiran yayi sannan ya kirata. Ringing
biyu ta ɗauka tare da faɗin, "Assalamu alaikum, Ibrahim ka sauka kuwa?" Faɗin Hajiya, "Ameen
wa'alaikissalam, na sauka Hajiya, yanzu haka ma gani cikin gidan." Daga can Hajiya ta hau faɗa, "Ka sauka
shine baza ka iya kira ka faɗa min ba, ni ina nan tun ɗazu bisa kan darduma ina addu'a Allah ya sauke ka
lafiya ya kare ka daga sharrin aljnan, mutum da kuma matsafa, ashe kai share gindi kayi ka zauna ko
tunawa baka yi ba kirani ka faɗa min ka sauka saboda kana cikin dangin ubanka ko?" "Kiyi haƙuri Hajiya,
ban jima da sauka bane, kuma yanzu nake shirin kiranki dama!" Faɗin Khalil yana murmushin rigimar da
Hajiya ta ɗauko yanzu. "Na dai faɗa maka Li'ilafi ya kama bakin ka a cikin gidan nan da kake wallahi!"
Hajiya ta kuma faɗi har da zuba kwafa. "Hajiya wallahi gidan malamai ne nan, ba yanda kike tunani bane."
Faɗin Khalil. Taɓe baki Hajiya tare da kawar da maganar wajen faɗin, "Kaga number ɗin da Maryamu ta
turo maka ko?" "Eh, nagani Hajiya." Khalil ya faɗi yana mai yin wani iri da fuska ganin Hajiya sai ƙoƙarin
tura abu gaba take yi. "To Number ɗin Habbooba ne, ka soma kiranta tun yanzu ka fara neman soyayyarta
ta cikin waya, kuma wallahi umarni nane hakan idan har baka ƙaunar ɓacin raina." "Zan kira in Sha Allah
Hajiya!" "Allah ya yarda!" Faɗin Hajiya tare da yanke wayar. Ajiye wayar yayi a gefe yana jin farin cikin
kasancewarsa cikin wannan gida, don ya yaba sosai da tsari da kuma addinin gidan. Wayarsa ce ta ƙara yin
ƙara, "Hajiya again!" Ya faɗi tare da kai hannu ya ɗauki wayar yayi picking ya kai kunnensa, "Eh, lallai! Kana
gidan mushirikan dangin matarka dole ka ɗaga min kira ai!" "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Khalil ya
faɗi cikin zuciya, don har ga Allah ya mance ita ta kira wayar. "Kiyi haƙuri Hajiya bari na kira ki." Faɗin
Khalil. "Kar ka kuskura ka yanke min waya! Saurare ni kawai, kar ka yarda bayan na katse wayata baka ɗaga
wayarka ka kira Habbooba ba! Ka dai ji na faɗa maka!" Tana gama faɗin haka ta yanke wayar. "Hajiya zata
saka ni a matsala wallahi! Ni mai zan yi da wata Habbooba!!" Ya faɗi yana scrolling messages ɗin wayarsa
har yazo kan na Aunty Maryam data turo masa Number. Dialing number yayi ba tare da ajiye wayar akan
katifa ya saka a handsfree sannan ya hau cire safar ƙafarsa. Ringing ɗin ya kusa katsewa sannan Habbooba
tayi picking wayar tana mai faɗin, "Assalamu alaikum!" Kana jin muryan zaka san cewar either Shuwa ce
ko balarabiya ke magana. Ciki-ciki Khalil ya amsa da, "Ameen wa'alaikissalam!" Sannan yayi shuru, itama
daga can ɓangaren tayi shuru. Sun kwashi tsayin mintuna biyar babu wanda yayi ko tari, shi Khalil kwanciya
ma yayi flat yana kallon ceilin ɗin ɗakin har ya mance ya kira wata a waya, saurin muryanta ya jiyo tana
faɗin, " _Manil lazhi yatakallam_? (Wa ke magana?" Khalil yana jinta yayi shuru, kuma ba wai don bai ji
abunda tace ba. " _Hello, Iza lam tatakallam, Igilaƙil mahmulah! (Idan baza kai maganar ba, ka kashe
wayar)_" Da ƙarfi ta ƙarisa maganar saboda haushin da taji na rashin maganar da mai kiran yaƙi yi. "Iglaƙi
mahmulatiki! (Ki kashe taki wayar)" Khalil ya bata amsa a karon farko. Wani irin shuruu ta ɗauka jin yanda
yayi maganar a kashe, a kuma daidai wannan lokacin Sarah tayi sallama a ƙofar ɗakin, ba tare da Khalil ya
kashe wayar ba ya amsa sallamar tare da bada izinin shigowa. A hankali ta buɗe labulen ta shigo ɗakin,
sanye take da dogon hijjab navyblue har ƙasa. Harara ya maka mata tare da faɗin, "Menene haka zaki wani
shigo min da hijjab har ƙasa, sallah za kiyi?" Bata ce komai ba ta nemi gefen katifar ta zauna tare da faɗin,
"Ina wuni? Ka iso lafiya?" "Ba lau ba, kin fi kowa sanin haka!" Khalil ya faɗi yana kallonta kamar zai cinyeta.
"Haba maman twins, da wayanki zaki saka ƙaramin hijjab ki fita, kin kuma san cewar Allah ya halicceki ma
sha Allah! Yanzu wanene zai ganki yace kin haifi ƴan biyu a cikinki?" "Kayi haƙuri hakan ba zai sake faruwa
ba!" Faɗin Sarah idanunta na ciccikowa da hawaye. Hannu ya kai ya jawota tare da faɗin, "Cire hijab ɗin
nan Mine, cire in ganki da kyau matata, nayi matuƙar, matuƙar kewarki! I really miss you sooo much my
endless bliss!" Ya faɗi hakan yana mai kwantota jikinsa bayan ya cire hijjab ɗin ya ajiye agefe. "Allah ya isa!
Ban yafe ba shiga tsakanina da akai da farin cikina!" Wani irin kuka Sarah ta fashe dashi daman kuma jiran
haka take yi, Khalil bai dakatar da ita ba, sai ma rungumetan da yayi sosai yana shafa bayanta, "Ki yafe min
mine, Sarah ki yafe min duk abunda nayi maki. Ina cikin hayyacina ba zan taɓa aikata abunda ya faru ba ba
Sarah. Sarah a raised this hand on your face! Oh Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!! Sarah ji nake kamar na
yi ta rusa ihu, addu'a nake yi tun da na dawo cikin hayyacina, Allah yasa duk abunda ya faru damu mafarki
ne. Mine na slept with your sister a gaban idanunki da ƴaƴa......" Bata bari ya ƙarisa ba ta rufe masa baki da
tafin hannunta tana girgiza masa kai tare da faɗin, "Let bygones be gone please, we shouldn't have to
remember the past. Bana so na tuna komai da ya faru tsakanin mu mara daɗi, I'm glad ka dawo cikin
hayyacinka, hakan yafi min komai daɗi Happiness. Let create a new life!" Hannunta ya riƙo duka biyun tare
da ɗaurawa a kan ƙirjinsa sannan ya haɗe goshinsu waje ɗaya yana kallon cikin idanunta tare da faɗin,
"Smile" wani murmushi ta saki da ya ƙara fitar da kyawunta. Miƙewa tsaye yayi sannan itama ya miƙar da
ita. Kallonta ya riƙa yi from head to toes ganin wani fitinanniyar purple crazy gown dake jikinta, gefen
cikinta zuwa bayanta gaba ɗaya a buɗe suke, wani ɗan hook ne irin na bra ya riƙe rigar ta gaba, gaban rigar
mai irin bra ɗin nanne yaji flowers manya, hatta ramin cibiyarta a buɗe take, gashin kanta kuma tayi
parking ɗinsa a can gaban kai irin yanda yake so. Ita Sarah sam bata so yin wannan shigar ba, Suhana ce ta
tilasta mata sai da tayi har da yi mata simple make up. "Oh my God, zaki kashe ni da wannan kwalliyar
Sarah, Kar fa ki saka inyi abun kunya a gidan surukai!" Ya ƙarisa maganar yana jawota gaba ɗaya jikinsa tare
da tura hannunsa cikin tsakankanin rigar tata. Lumshe idanu Sarah tayi hawaye na zubar mata jin yanayin
da ta jima bata jisa ba a jikinta. Hannu ta saka ta ƙanƙamesa tana sakin siririn kuka. Da baya da baya yayi ta
tafiya da ita har wajen ƙofa ya miƙa hannu ya saka sakata sannan ya sunkuceta suka faɗa kan katifar, ba
tare da wani jinkiri ba ya hau kasheta da hot romance da ya kusa gigita tunaninta, daga ita har shi sun
mance a inda suke, har sai da nutsuwa ta saukar masu tukun. Tare suka yi wanka a cikin bayin ɗakin. Sai
bayan sun gama kimtsawa sannan Khalil ya kuma jawota jikinsa suka shiga labari. "Nnanne tace in faɗa
maka anjima za muje gidan maman Lami da babanta ka gansu." Hannu ya saka ya ɗane mata baki tare da
faɗin, "Mama, ba Lami ba........." Ƙarfe biyar suka kintsa, wannan karan daga ita sai Khalil suka nufi gidan
baba Samuel, har ga Allah tsoran tsohon nan Sarah take yi, bata so sam imaninta ya raunana shiyasa taki
kawo hasashensa na ɗazu cikin zuciyarta. Wannan karan tun suna ƙofar ɗakin suka fara jin dariyar baba
Samuel. Ɗaga asabarin Sarah tayi tare da shiga Khalil a bayanta. Tunda Khalil ya shigo Baba Samuel yake
kallonsa, yana zama baba Samuel ya cafki hannunsa tare da ware tafin hannunsa ya kalla sannan ya kalli
kwayar idanunsa tare da faɗin, "Mata uku zasu haihu maka a shekara ɗaya kuma duka ƴaƴa mata zasu
haifa, biyu daga ciki matanka ne wanda ka biya sadaki, ɗaya kuma ba matarka bace amma kai ne uban
cikin! Na gani a kwayar idanunka, kuma na gani ta tafin hannunka, wacce ta kasance babu sadaki a
tsakaninku, zata mutu kuma rainon ƴar da ta haifa hannu wannan matar taka kuma jikata zai koma. Akwai
ƙalubale masu dama da wannan ƴa zata fuskata, domin za'a haifeta ne da cutar makanta, kuma
yarinyar......." "Enough baba Samuel!" Sarah ta faɗi da ƙarfi jikinta na rawa gabanta kuma na faɗuwa yayin
da Khalil kuma ya fizgi hannunsa da Baba Samuel ya riƙe da ƙarfi ya taro Sarah dake ƙoƙarin zubewa a
ƙasa......

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[14/11, 12:31 PM] Matar Sayyadee: "Happiness wannan mutumin mushiriki ne, zuwa wajensa bala'i ne.
Allah yaga zuciyarmu ba zuwa nan muka yi domin yayi mana duba ba, let get out of here please!" Sarah ta
faɗi tana mai damƙe gefen rigarsa. Wani irin murmushin baba sameul yayi tare da faɗin, "Naga irinki da
yawa my grand-daughter, wasu sun dawo sunyi da mamaki anan inda kike kuma suka bani haƙuri, kuma
har yanzu muna tare da wasunsu ina yi masu duba. You're my grand-daughter shiyasa nake faɗa maki duk
wannan, wasu da yawa da kuɗi suke nema in yi masu irin wannan duban amma ban yi, you're very special
to me shiyasa. Amma time shall tell! Idan kun tafi Kaduna gobe, kice wa Elizabeth I love her Soo much and
I miss her, sannan idan kun isa gidan _Pastor Emanuella Debora Gabriel_, kuce mata Samuel na gaishe ta!
Sannan ku faɗa mata ta guji zaman aure dani saboda addinina, to gashi nan ta haɗa jini da Addinin da tafi
tsana har da ƴaƴan jikoki, sannan idan kun isa Kaduna kije wajen ƴar uwarki, ku faɗa mata cewar nayi
alƙawarin da rantsuwa daOgun, Shango, Eshu, Ọrunmila sai na kashe _Ofulafu_ saboda abunda ya aikata
mata!" A ruɗe Sarah ta kalli Khalil tare da faɗin, "Mai ya samu Aina'u?" Hannunta ya kama tare da faɗin,
"Tana can tana girbe abunda ta shuka. Ƙaiƙayine ya koma kan masheƙiya!" Wani dariya Baba Samuel yayi
tare da faɗin, "Noma da ban ruwan da kake tayi a gonar daba taka ba ta fidda fure, kai wani irin halittar
ubangijine wanda da wuya yayi mu'amala da mace bata samu ciki ba, yanzu haka ina kallon yanda kwan
halittar dake jikinsa Sarah wanda ka zuba ɗazu yana yawon neman hanyar shiga mahaifarta, yanzu saura
mace ɗaya tak!" Yana gama faɗin haka ya bushe da dariya har da tuntsirawa, cak Sarah da Khalil suka tsaya
suna kallonsa cike da mamaki furucinsa. Kallon juna suka yi sannan suka kuma kallon Baba Sameul,
"Happiness mu fita dan Allah, wallahi wannan maye ne, yana ganin har kayan cikinmu." Damƙe hannunta
Khalil yayi suka fita daga ɗakin suna yin addu'a cikin zuciyoyinsu. Wani irin abune ya tsirga tun daga
kwakwalwar Khalil har zuwa tsakiyar tafin ƙafarsa. Haɗa kai yayi da ginin ƙofar gidan tare da faɗin, "What if
dagaske ne abinda tsohon nan ya faɗi? Ina ji a jikina _ƙanwar matata_ na ɗauke da cikina. Sarah in tsoran
Kar dagaske ne ai Aina'u na ɗauke da ciki!" Ya ƙarisa maganar a matuƙar raunane. Girgiza kai Sarah tayi
tare da faɗin, "A'a Happiness, Aina'u baza ta taɓa samun cikinka ba jinin ubangiji. Aina'u bata da ciki Mine,
Aina'u baza ta haihu da kai ba, Ni kaɗai zan haifo maka ƴaƴa sai kuma matar da zaka aura nan gaba. Amma
in sha Allah bayan haka baza ka taɓa haihuwar shege ko shegiya ba!" A hankali ya juyo tare da faɗin, "Ina
fatan haka Sarah, sai dai ina jin tsoro sosai." "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un. Kayi ta maimaita hakan, in
Sha Allah zaka samu sauƙi a zuciyarka." Jinjina mata kai yayi sannan suka cigaba da tafiya kowa da saƙe-
saƙen da yake yi a zuciya. A ƙofar gidan pastor _Emmanuella Debora Gabriel_ suka tsaya, Sarah ce tayi
knocking, cikin ƴan daƙiƙu gateman ya buɗe mata ƙofar tare da faɗin, "From where? Who are you looking
for?" Kai tsaye Sarah tace, " _Pastor Emmanuelle Deborah Gabriel_" Kallo sama da ƙasa yayi masu, ganin
basu yi kama da matsiyata ba, sai yace, "Tana cirewa wata mata evil spirit a sama, can you wait for her?"
Wannan karon Khalilullah ne yayi maganar, "show us the waiting room, we'll wait for her." Da hannu gate
man ya nuna masu wajen zama sannan ya matsa suka shiga ciki. Mintuna goma sai ga mutane su bakwai
sun fito a hannunsu riƙe da wata ƴar budurwa suka saka ta cikin mota sannan suka koma ciki, muryan
pastor Debora suka jiyo da ƙarfi kamar zata tsaga gidan tana faɗin, "Dear Lord Jesus: Father God, in the
name of Jesus Christ , I take authority and dominion over my home. I command every demonic entity that
has entered into my house has to bow its knee. I come to you in the name of Jesus Christ , and I am asking
for forgiveness of my sins. I’m repenting for disobeying to my parents, abondoned my daughter. Father
God, I also repent if I have any bitterness towards anyone and forgive them for hurting me, and I give them
over to you. Father God, I repent and I renounce my involvement with anything that was not of you. I also
repent and renounce for bringing anything into my house that was not of you such as idols, other gods,
other religions, and so on. Father God, by the blood of Jesus Christ, I break any assignment of every evil
spirit to this space. I bind every evil spirit that is in this room and command them to go where the Lord
Jesus Christ has ready for them. Father God, in the name of Jesus Christ , I renounce and reject any inch of
this room, this house and this property that has been yielded or surrendered unto Satan and by faith I take
it back and surrender it to the Lord Jesus Christ. Father God, in the name of Jesus Christ , by faith, I claim
that this room is covered under the blood of the Lord Jesus Christ and no evil spirit can enter it. I
command everything must leave this house now. I decree that every legal right has been broken. I call on
the Lord to blow and remove every demonic spirit out now to never return, in the name of Jesus Christ .
Amen." Kallon Sarah yayi tare da faɗin, "Wannan kwakwazo haka, saura kaɗan na zura da gudu ai!" Dariya
Sarah ta kyalkyale dashi tare da faɗin, "Ai su akwai kwakwazo kamar za ayi faɗa!" Wannan karon tare suka
fito har da ita Debora ɗin da kuma wasu ƴan mata uku da maza biyu, suma a cikin motar aka saka su
sannan mutanan nan suka duƙa suna godiya ga paston, ita kuma sai albarka take saka masu. Motar suka
shiga suka tada. Tun da Pastor ta fito Sarah ke kallonta, "without doubt wannan ita ta haifi mamana, duk
da ta tsufa, amma ga kamannin mamana nan gaba ɗaya a tare da ita." "Nima abunda nake cewa kenan a
zuciyata." Khalil ya faɗi yana mai miƙewa, pasto Emanuella kuwa ganin mutanan da bata sani ba suna
nufota, sai ta tsaya cak tana jiransu. Bayan sun iso sai gaba ɗaya suka ɗan duƙa suka gaisheta, amma masu
tayi cikin fara'a tare da faɗin, "Amma ban gane ku ba!" Sarah tace, "Sunana Saratu Nuhu, yarinyar ƴarki
Elizabeth!" Wani irin waro idanu Pastor tayi tana kallon Sarah, can kuma ta kai hannu ta riƙo ta tare da
faɗin, "Ke ƴar Elizabeth ce? Dukkan ku?" Ta ƙarisa maganar tare da nuna Khalil. Girgiza kai tayi tare da
faɗin, "Wannan mijina ne!" Shima kamo hannunsa tayi tare da faɗin, "Thank you Jesus, thank you for
everything!" Sannan ta riƙe hannunsu duka tare da jansu zuwa cikin gida. A ƙaton main parlour ɗinta ta
ajiye su, cikin ƙanƙanin lokaci sai ga house help ɗinta sun cika gabansu Khalil da kayan motsa baki dasu
drinks, kan ka kuma cewa kobo sai ga ƴan uwan Pastor suna shigowa, nan da nan har sun cika parlour ɗin,
masu kuka nayi, masu ihun addu'ar nan nayi, masu rungume Sarah har da Khalil ɗin maza da mata nayi.
Khalil sai taka ƙafar Sarah yake yi ganin garadan arna na kama masa mata, da an nuna wani ance, "Sarah
wannan uncle ɗinkin ne." Take zai taso ya bata side hug yana saka mata albarka. Dangin Lami suma suna
da yawa sosai. Kowa sai tambayanta in Elizabeth, ƴaƴanta nawa. Duk tambayar da suka yi mata ta basu
amsa, sai dai bata basu labarin komai ba game da abunda ke faruwa. Jin gobe zasu tafi Kaduna, Pastor
Emmanuelle ta daka tsalle take ba zai yiwu ba, sai sun kwana a gidanta, hakan ya kusa haifar da rikici don
Nnanne itama cewa tayi dole sai sun tafi gobe domin taga ɗanta. Daga ƙarshe dai gaba ɗaya suka yanke
hukuncin zasu tafi Kaduna har da Pastor Emanuella itama da tata tawagar, amma duk da haka Sarah da
Khalil a gidan Pastor Emmanuelle Deborah suka kwana, har twins sai da aka kawo su Pastor ta gansu.
Yanda akai ta kwaɗa masu ihu a kunne da sunan addu'a, sai da Khalil yaji kamar ya fizgo ƴaƴansa,
"Abraham, zaka bani twins su zauna a wajena ko?" Pastor Emmanuelle Deborah ta faɗi tana yiwa Sam'an
da Sauban kiss a goshi. "Har ma na baki! To ko shure-shuren mutuwa kike ba zan iya baki su suyi koda
kwana biyu. Haka nan yarana su koma cewa _In the name of Jesus, Hallelulaya_" amma a zahiri sai cewa
yayi, "Eh grandma!" Washa gari ƙarfe tara, kowa ya gama shiryawa, Khalil, Sarah da Suhan a mota ɗaya, su
Nnanne, ba Lukman, ba Nura da ba Kamal a mota ɗaya, sai _Pastor Emmanuelle Deborah da tawagarta a
mota ɗaya. Ƙarfe biyu daidai suka shigo Kaduna, kai tsaye jama'a road suka nufa. A ƙofar gate sukai
parking, Sarah ce ta soma fitowa tayi cikin gidan da sauri tana mai jin farin cikin dalilinta Baba Nuhu zai yi
reuniting da iyayensa. A tsakar gida ta samu Lami tana shanya, duk ta rame ta ƙara duhu, Lami na ganinta
ta rungumeta tare da faɗin, "Sarah were have you been all this day? Muna na nemanki, mijinki was here
6days ago yana nemanki." "Mama, I have a surprise for you!" Da mamaki Lami take kallon Sarah kamun ta
jiyo sallamar su Nnanne suna shigowa, Lami bata gane Nnanne ba, don bata taɓa ganinta bama, amma
tana ganin ba Nura jikinta ya fara rawa don shi ta sansa don tasan Baba Nuhu twins ne kuma ta taɓa ganin
har su baba Lukman. "Mother!" Faɗin Lami da ƙarfi wanda ya saka gaba ɗaya su Na'ima suka fito daga
ɗakin suna faɗin, "Mama lafi..." Ba tare da sun ƙarisa maganar ba suka kuma haɗa baki tare da nuna Baba
Nura suka furta, "Baba!" Da ƙarfi. "Uncle John, uncle Uche, uncle Joshua, aunty Grace, aunty Delilah, aunty
Roth!" Faɗin Lami tare da fashewa da kuka ganin ƙannnai mamanta maza da mata. Ɗaya bayan ɗaya ta
bisu ta shiga rungumesu kamun ta dawo gaban Pastor Emmanuelle Deborah ta zube guiwowinta a ƙasa ta
kama ƙafarta tana kuka sosai while asking for forgiveness. Ɗagota Pastor Emmanuelle Deborah tayi tare da
faɗin, "I forgive you my dear daughter. Na yafeki! Ba lefinki bane adukkan komai da kika aikata, laifin
ubanki taɓaɓɓe kuma mara rabo a duniya da kuma can sama, Allah shine yake sonki da ya karkato
hankalinki kika koma addininki na gaskiya." Wawan tsaki Nnanne ta saki tare da faɗin, "Allah tsine! Ke
Saratu, duk waɗannan ƴan uwanki ne? Sune yayyinki ƴaƴan Nuhu?" Gyaɗa kai Sarah tayi tana hawaye. Su
Na'ima ma kukan suka fara yi don sun fuskanci abunda ke faruwa, dangin Lami ne da kuma dangin Baba.
"Wannan ƙanin babanku ne, tagwaininsa ne, a mahaifa ɗaya suka zauna da mahaifinku, wannan kuma
yayyin mahaifinku ne, suma ƴan biyu duk da ga zahiri nan kun gani. Ni kuma, ciki ɗaya muka zauna da
mahaifiyar Nuhu, ita ta saki Nono ta bar min, amma uba kowa da nasa. Gaba ɗaya su Na'ima sai suka
ƙarisa gareta suka rungumeta suna kuka. "Muje ku kai ni wajen ɗana, muje!" Nnanne ta faɗi. Hannunta
Na'ima ta kama har ɗakin Baba dake kwance kamar gawa. Da sallama suka shiga ɗakin gaba ɗayansu.
"Nuhu, Nuhuna, kai ne ka koma haka!" A razane Baba ya buɗe idanunsa tare da motsa hannu da ƙafarsa
abunda tunda ya kwanta bai taɓa yi ba, don sosai ya motsa. Yana ido huɗu da ƴan uwansa ya soma wani
irin jijjiga yana son gungurowa daga kan gado kuma yana hawaye da kuka. Suma gaba ɗaya kukan suka
saka tare da matsawa kusa dashi.

_Kuyi haƙuri da wannan, wallahi jinya nike yi_

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[14/11, 12:31 PM] Matar Sayyadee: _In sha Allah saura 5pages mu ƙarƙare_

Hannu Nnanne ta miƙa ta riƙo hannunsa tana mai zubar da hawaye, "Haka ka koma Nuhu? Nuhu haka
Allah yayi da kai? Ashe zan sake ganinka amma a irin wannan hali Nuhu! Nuhu Allah ya baka lafiya." Baba
Nuhu kuka yake yi sosai ƴaƴansa da ƴan uwansa na taya shi. Daga wajen kuma, ihun su Lami da nata
tawagar kawai kake ji sun zagaye suna ta addu'a suna faɗin, _In the name of Jesus!_, suma dai kukan suke
yi. Khalil kuwa yana sauke su ya juya kan motar shi da twins zuwa gida. A hankali yayi ta tafiya gabansa
kuma na faɗuwa domin ya san yana isa gida maganar da Hajiya zata fara yi masa shine zuwa Maiduguri.
Horn yayi, mai gadi ya wangale masa gate shikuma ya tura hancin motarsa ciki ya naimi waje yayi parking
sannan ya fito ya zagaya ya buɗewa ƙofa ya fiddo su twins sannan ya rufe motar tare da kama hannunsu
suka nufi sashen Hajiya. Sallama yayi sannan ya murɗa handle ɗin ƙofar ya kutsa kai, Hajiya ce a parlourn
ita da Aysha, Laure da su aunty Yagana don basu tafi ba suna nan. Da sauri Laure ta miƙe tare da kamo su
twins tana yi masu oyoyo. Waje Khalil ya samu ya zauna sannan ya shiga gaida su Hajiya, su aunty Yagana
ne kawai suka amsa, Hajiya kuwa wata uwar harara ta galla masa tare da zabga uban kwafa tana girgiza
ƙafa. "Sannu da zuwa ya Khalil, ya hanyar?" Faɗin ƙanwarsa Aysha. "Lafiya ƙalau Aysha, ashe kina nan baki
koma ba." Aysha tace, "Ai ina nan har sai an gama biki tukun." Da sauri Khalil yace, "Wani biki kenan?"
Kallon Hajiya Aysha tayi kamin ta dawo da kallonta izuwa ga Khalil tare da faɗin, "Bikinka mana! Yau su
Uncle Shamsu da ya Abdallah suka tafi Maiduguri kai kuɗin aurenka." Wani irin zufa da yanko daga goshi
Khalil ya share tare da haɗiye miyau maƙot sannan ya kalli Hajiya, Hajiya kuma dama jira take yi, sai ta hau
faɗa kamar ta ari baki, "Saboda ka tafi garin matsafan iyayen matarka, shine zaka wulaƙanta min ƴa ko?
Tun kamun ayi auren har ka soma wulaƙanta yarinyar mutane ko? Saboda iskanci da rashin mutunci don
nace ka kira yarinya ka fara neman soyayyarta a waya shine zaka bawa matarka waya ta gaggaya mata
magana ko!" Da mugun mamaki Khalil ke kallon Hajiya, can kuma yace, "Hajiya ita yarinyar ce tace na
kirata na bawa Sarah waya ta zazzageta? Wallahi tallahi ƙarya take yi Sarah ko labarinta bata sani ba balle
har ta ɗau wayata ta zageta." "Nice maƙaryaciyar kenan dana faɗa maka? Kana nufin haka kawai sai
Habbooba ta zabga maka ƙarya ba tare da kayi ba? To bari kaji, yaran Mariya yara ne masu tarbiyya, ba'a
rainesu da yin ƙarya ba. Kuma wallahi, ku zama sheda Yagana, idan yaron nan yace zai ɓata min rai ko
kuma ya nemi ɓata zumuncin dake tsakanina da Mariya, to abunda zai fito daga bakina na furta ba mai
daɗi bane. Kuma wallahi kwana biyar kawai ba bashi, ya tattara ya tafi Maiduguri wajen yarinyar nan tun
da dai ya dawo da ƴar dangin matsafan." Faɗin Hajiya tare da kallon Laure tace, "Lauratu maza yi ɗaki da
yaran nan kiyi masu wanka da ruwan maganin nan sannan ki tofe su da Li'ilafi da sauran addu'o'i don
bamu san irin tsaface-tsafacen da aka yi masu ba. Don babu mamaki kiji yara sun koma faɗin _Jesus Chris_,
sannan ki duba wuyarsu da kyau yanzu haka ba abun mamaki bane ki gansu rataye da sarƙar cross a
wuya." Khalil bai iya ko tari ba, mamaki kawai yake yi wai Sarah ta kira Habbooba a waya. "Habiba take ko
Mahbuba, wannan yarinyar tun kamun na aurota har ta soma ƙoƙarin haɗani faɗa da Mahaifiyata, wannan
yarinya daga ji ba matar rufin asiri bace. Yaushe ma Sarah ta san da ita balle ta kirata a waya?" Faɗin Khalil
cikin zuciya tare da yin shiru. Can kuma ya tuna, lokacin da ya kira ta a waya bai kashe ba har Sarah ta
shigo ɗakin, shi kuma ya manta ma ya kiratan, "Maybe taji maganarmu da Sarah ne shiyasa ta haɗa min
wannan ƙullin, lallai ma yarinyar nan!" Faɗin Khalil cikin zuciya. "Hajiya bari naje nayi wanka na canza
kaya!" Ya faɗi kansa a ƙasa. "Ban riƙe ka ba ai." Faɗin Hajiya tare da mayar da dubanta ga Tv. Miƙewa Khalil
yayi tare da nufar hanyar ɗakinsa dake nan side ɗin Hajiya. A can Maiduguri kuwa, haj Mariya ta riga ta
bawa Habbooba number ɗin Khalil kuma tayi saving a wayarta tun kan Khalil ya kira ta, sai bata yi yunƙurin
kira ba har sai lokacin da shi ya kira da kansa don haj Mariya ta faɗa mata taja ajinta kar ta nuna son da
take masa har ya fahimta. Tana kwance a ɗaki tana sauraran waƙar Naada wayarta ta soma ringing, bata
lura ba saboda ƙarar da ta cika a ɗakin, kamar ance ta juya ta hangi wayar na haske, hannu ta kai ta jawo
wayar lokacin tana gab da tsinkewa tayi sauri picking ganin wanda ke kiran tare da karawa a kunne amma
sai ta nuna kamar bata san dawa take magana ba kuma dama Habbooba akwai girman kai. Shi kuma Khalil
sai ya nuna mata gidan tazo. Habbooba tana jin lokacin da Sarah ta shigo ɗakin har da maganganun da
suka yi duka, zuciyarta ne ya soma bugawa da ƙarfi hankalinta yayi mugun tashi lokacin data fahimci
abinda yake yi da matarsa a wannan lokaci, don Khalil irin masu sakin maganganun nan ne, sam basu ɓoye
abunda suke ji. Kashe wayar Habbooba tayi da sauri tare da fashewa da kuka mai sauti ta diro daga kan
gadon tare da fita ta faɗa ɗakin mahaifiyarta tana kuka sosai, tafi ƙarfin 30mins tana kuka kamun nan
tayiwa mahaifiyarta bayanin abunda ke faruwa ta haɗa har da ƙaryar cewa matar Khalil ɗin ce ta kirata a
waya tana ta zaginta kuma Khalil ɗin ne ya bata wayar. Ran haj Mariya yayi mugun ɓaci don ta kasance irin
iyayen nan ne masu matuƙar ƙaunar ƴaƴansu. Nan da nan ta ɗaga waya ta kira Hajiya har da kukan
munafunci tana faɗin a fasa wannan haɗin kai tunda ba zai yiwu ba, kuma dama Habbooba ba rasa
masoya tayi ba, nan hankalin Hajiya yayi mugun tashi ta shiga bawa haj Mariya haƙuri tare da faɗin, in Sha
Allah gobe-gobe za'a zo kawo kuɗin auren Habbooban saboda su san da gaske take yi, ta kuma ƙara da yi
mata ƙarin bayani akan dawowa da matar Khalil ɗin za tayi wanda a cewar Hajiya ba'a son ran Khalil ɗin
bane. Sun kai kusan awa suna magana sannan Hajiyar tace a bawa Habbooba, nan ma tayi ta lallashin
Habbooban tana bata baki tare da bata assurance ɗin ita ce ta gaban goshin Khalil ɗin. Wannan abun ne ya
fusata Hajiya tayi ta wa Khalil bala'i. Gidan Lami kuwa, cikin ƙanƙanin lokaci ya cika, domin mabiyan Pastor
Emmanuelle Deborah na nan Kaduna, suna samun labarin zuwanta suka dunga cincirindon zuwa domin
samun albarka, gidan gaba ɗaya sai ya ruɗe da hayaniya kamar coci, wasu mutanan da basu samu damar
shigowa ciki ba, a ƙofar gida suka tsaya da uban gangunarsu na coci sunata busa da kuɗi. Canopies huɗu
aka saka a cikin gidan da uban kujeru, kuma gaba ɗaya mutane sai da suka cika wajen wasu ma a tsaye don
ma gida nada ɗan girma, abinci kuwa da drinks da snacks ko ta ina. A cikin ɗakin Baba Nuhu kuma, tagumi
suka zuba saboda hayaniyar ta ishe su da waƙe-waƙen coci ga kuma mara lafiya. Babu suka samu sauƙin
iface-ifacen nan ba sai wajajen ƙarfe biyar na yamma sannan su kai ta watsewa. Sai kuma a wannan lokacin
Lami ta samu damar zuwa ta gaida su Nnanne, babu yabo babu fallasa Nnanne ta amsa bata haka su ba
Lukman ma. Da misalin karfe bakwai na yamma, su uncle John ƙannan Pastor suka fita suka kama hotel a
can farkon layin kasancewar gidan yayi masu kaɗan, Aunty Ruth, aunty Grace da aunty Delilah a ɗakin Lami
zasu kwana har da Pastor Emmanuelle. A ɗakin su Na'ima da Sarah da Suhana zasu kwana har da Nnanne,
su ba Lukman kuma a ɗakin Baba Nuhu. Sai da dare ya raba sannan gaba ɗaya suka baro ɗakin Baba Nuhu
kasancewar hira suka riƙa yi ana bawa su Na'ima labarin da basu sani ba. Gaba ɗaya sun manta da wata
Aina'u ko abincin da suka saba tura mata ta ƙasan ɗaki basu kai ba. Tana can cikin mugun mawuyacin hali a
ɗaki ita kaɗai babu abunda take kira sai "Ruwaaa!" Ƙananan fararan tsutsotsi sai yawo suke a jikinta suna
cin jikinta inda yayi rami. Kanta ya suɗe tass, kuma har yanzu ƙananun kunamun suna fitowa daga jikinta.
Ga wani uban wari mai tashin hankali dake fitowa daga jikinta kamar mushe, idanunta sun zazzago, ga
bakinta daya turo kamar na kare. Yanzu ya kai ga kamun Aina'u tayi magana sai tayi haushin kare tukun.
Washe gari bayan an gama karyawane Nnanne tace, "Wai ni ina ɗayar jikar Samuel ɗin ce mai yunƙurin
kashe aure?" Da sauri Na'ima tace, "Inna lillahi! Jiya ma ba'a kai mata abinci ba." Ta faɗi tana miƙewa
tsaye. Hannunta Nnanne ta riƙo tare da faɗin, "Ana hirar mutunci yaushe za'a tuna da mushirika mai
kashe-kashen mutane da yunƙurin kashe aure! Muje ƙafata-ƙafarki domin in ganta." "Wallahi Nnanne idan
kika yi arba da Aina'u duk abunda ke zuciyarki sai ya ragu, duk mai imani sai ya tausaya mata, kashe mana
ƴaƴa tayi, amma wallahi ina jin tausayinta, muje gani ya kori ji!" Faɗin Na'ima tana mai yin gaba Nnanne
biye da ita, gaba ɗaya sauran ma suka miƙe har dasu ba Lukman, tun da suka doshi ɗakin suke jin wani irin
mahaukacin ɗoyi na tasowa daga ɗakin. Na'ima ce ta tura ƙofar, ai kamar ƙara buso warin aka yi duk suka
toshi hanci. Haushin kara suka soma ji daga ciki, da sauri Nnanne tace, "Kare kuka haɗata da shi a ciki?"
Girgiza kai Na'ima tayi tare da faɗin, "Ita ce take yin haushin, idan za tayi magana sai ta fara wannan
haushin karen tukun." Daidai nan Nnanne ta hango Aina'u kamar angulu ta duƙa. "Inna lillahi wa'inna
ilaihir raju'un! Wannan ita ce Aina'u?" Ta ƙarisa maganar tare da fashewa da kuka. Da saurin Sarah ta
ƙarisa shiga cikin ɗakin tana wani irin kuka tare da duƙawa a gaban Aina'un tace, "Aina'u kece haka? Haka
kika koma? Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Aina'u ɗaga hannu tayi da sauri ta cafki hannun Sarah tare
da faɗin, "Saratu, Sarah! Ashe za kiji tausayina duk da abunda nayi ta yi maki? Sarah ki yafe min dan Allah!!
Dubi yanda Allah ya mayar dani. Na ɗauka zan yi rayuwa mai tsayi inyi ta shuka tsiya ina abunda naga
dama, ashe ba haka bane, ƙarshena ba mai kyau bane. Ni na san wuta zan shiga saboda abubuwan da nayi
ta aikatawa. Na bar addinin gaskiya na koma ba ɓata duk dan in samu duniya, gashi duniyar bata samu ba
sai ma koya min hankali da take yi. Kaicona! Kaicona ni Aina'u!! Ta ina ma zan fara neman gafarar abunda
na shuka? Ta ina zan nemi gafarar wanda suka mutu, ƙananan yaran da basu ji ba kuma basu gani ba, mai
keken napep ɗin ba sai san komai ba sai ƙoƙarin naiman na halas ɗinsa, jaririyar Nafeesa da bata san komai
ba, duniyar ma shigowarta kenan, Nafeesa da mijinta da basu aikata mun komai ba da kuma maƙotansu,
Sarah na azabtar dake ta hanyar sanya maki cuta a jikinki, na nesan taki da mijinki sannan na dulmiyar da
mijinki ta hanyar asiri, na sanya shi yana ta amfani dani ba tare da son ransa ba, na saka ya dake ki da
hannunsa, na saka ya ƙaurace maki, na sanyawa mahaifiyarsa ciwo, na saka ɗanta ya saki matarsa, na raba
Hajiya da ƴaƴanta na tsayin shekaru biyu, na rufe bakin Laure baiwar Allahn da bata yi min komai ba, mafi
muni, nayi kwanciyar aure da mahaifin da yayi sanadin zuwana duniya wanda sanadin haka har yanzu yana
kwance shi ba gawa ba shi ba mai rai ba. Gashi yanzu ina girbe abunda na shuka. Kaicona!!" Kowa a ɗakin
kuka yake yi. Wani irin mugun tari Aina'u tayi, sai ga jini ya feso ta bakinta, gaba ɗaya sai suka yo kanta,
hannu ta ɗaga masu da sauri tare da faɗin, "Ku barni kawai, babu abunda zaku iya min a yanzu, ku bar ni,
ni na san mutuwa zan yi." Ta faɗa tana yin wani irin yunƙuri mai ƙarfi sai ga mitsi-mitsin tsutsotsin nan na
fitowa ta duburanta a lokaci guda kuma naman ƙirjinta ya zagwanyo ya faɗo ƙasa. Luuuuuu Nnanne ta tafi
a sume, da sauri ba Nura dake bayanta ya riƙota tare da fito da ita daga ɗakin. Sarah da su Na'ima kuwa
zagaye Aina'un suka yi suna kuka sosai tare da tofa mata duk addu'ar da tazo bakinsu. "Wallahi tallahi na
yafe maki Aina'u, wannan halin da kike ciki kawai ya ishi mutum ishara. Ni dai nawa laifin da kika min
wallahi na yafe maki. Rintse idanu Aina'u tayi hawaye na kwaranyo mata daga idanunta tana ƙara damƙe
hannun Sarah kamun nan ta ɗaura hannunta a ƙasan cikinta tace, "Bana son yasan ko tasan nice
mahaifiyarta ko mahaifiyarsa, na baki har abada, ke nake so ki raini abunda ke ciki idan har Allah yayi zai
haife. Khalil shine uban abunda ke cikina, ke mahaifiyar abunda ke cikina ne ta kowani ɓangare, kada ta
ɗauki halina ko ɗaya dan girman Allah. Ina so ta kasance ko ya kasance mahaddatan Alkur'ani. Kar a bashi
ko a bata labari dan Allah. Wannan sune wasiyyata a gare ki dan Allah. Na san nayi maki mummunar laifin
da ban cancanci ki tausaya min ko ki riƙe abunda na haifa, amma na san za kiyi ko don Khalil masoyinki. Na
san baza ki taɓa wulaƙanta ɗansa ko ƴarsa ba. Kiyi min wannan alfarmar Saratu!" Ta ƙarisa maganar tana
wani irin jijjiga can kuma ta sume. Hankalin su Sarah ya tashi, da sauri Na'iman ta fita ta ɗebo ruwa saboda
ruɗewa ta sheƙa mata a fuska. Wani irin ajiyar zuciya ta sauke tana kallon ƴan uwanta ɗaiɗai. "Ku faɗawa
Lami taje ta amso ɗanta a wajen Aunty Rose Merry, Lukman na nan da ransa, bai mutu ba, ƙarya Rose
Merry take mata, za tayi amfani dashi ne domin cusawa Lami baƙin ciki. Yanzu haka Lukman yana wajen
Pastor William ta saka anyi masa wankan zunubi, kuma Pastor William yana amfani dashi ne ta duburansa,
yanzu haka cinikinsa za ayi da wani bature domin sayar dashi a tura shi ƙasan waje ana amfani dashi ta
dubura. Kuje maza da sauri ku dawo da ɗan uwanku!" A kunne Lami Aina'u tayi maganar domin suna bakin
ƙofa ita dasu Pastor Emmanuelle Deborah da kuma ƙannanta. "Jeeeesus Chris!" Pastor Emmanuelle
Deborah ta faɗi da ƙarfi lokacin da tayi arba da Aina'u. Su uncle Uche da uncle Joshua da gudu suka yi baya
suna faɗin, "In the name of Jeeeesus!" Uncle John ne kawai ya iya ƙarfin halin tsayawa shima baya-baya.
Lami kuwa wani irin ihuu ta zunduma tana mai faɗin, "Yesu Almasihu ka tsinewa Rose albarka, ka ajiyeta a
cikin wutan mai zafi da ƙuna, ka saka ta a cikin wutan iblis shaithan abun ƙi!" Ta ƙarisa maganar tare da
ɗaura kanta a kafaɗar Pastor Emmanuelle tana mai cigaba da faɗin, "Rose Merry ya ce sanadin lalacewar
Aina'u, da bata nuna mata hanya taje wajen _Hell Ofulafu_ ba, da yanzu yarinya na tana cikin hasken Yesu
Almasihu, gashi yanzu tana ƙoƙarin lalata min rayuwar ɗana, bayan tare da ita muka kai Lukman wajen
Pastor William yayi masa wankan zunubi domin ya daina sata da shaye-shaye, kwanansa goma sha huɗu a
can aka aiko min wai Yesu Almasihu ya tsine masa saboda mugayen zunubin da yake yi domin ɗakin da aka
saka shi kamawa da wuta yayi ya ƙone. Sannan kuma Merry ta gargaɗe ni a kan kar in kuskura in faɗawa
kowa domin idan nayi hakan tsinuwar zata bibiyi zuri'a ta. Wannan dalilin ne ya saka nayi kuka a ɗaki ban
faɗawa kowa ba." Duk wannan maganar da suke yi, ita Sarah hankalinta baya jikinta tun sanda Aina'u ta
shaida mata tana da ciki, sai gaba ɗaya maganganun Baba Samuel yayi ta mata amsa kuwa a kunne. Da
sauri kuma tayi a'uziyya don bata son gasgata maganar mashuriki, sai ta bar hakan matsayin kintata da
suke yi da kuma aiki da aljanu. "John, Joshua kuje kuyi bincike wanene wannan Pastor William ɗin nan mai
ci da addini, ku tabbatar kun samu hujjoji a wajensa, zan haɗa da ƴan sanda bayan kun isa. Sai an kwace
wannan church ɗin a hannunsa kuma sai an masa hukunci." Rungumeta Lami tayi tana kuka tare da faɗin,
"Thank you Mama, thank you very much!" Tana gama faɗin haka ta ƙarisa kusa da Aina'u ta shiga tattare
inda aka Aina'un ta ɓata, sai a lokacin su Uncle Joshua suka iso ɗakin suna ƙara kallon Aina'un da kyau.
"Praise the Lord!" Pastor Emmanuelle Deborah ta faɗi da ƙarfi, gaba ɗaya tawagarta suka furta,
"Hallelujah!" Nan pastor Emmanuelle ta shiga kwararo addu'o'insu suna yi suna ihu tare da haɗawa da
waƙa. Su Na'ima gaba ɗaya barin ɗakin suka yi suka fito waje, Aina'u kuwa ji tayi kamar ta ɗaura hannun a
kai tayi ta rusa ihu saboda wannan abun da suke yi ƙara mata azabar ciwo kawai yake yi. Bayan sun gama
duk wannan iface-ifacen sai Pastor Emmanuelle Deborah tace, "Lami ki goge mata jiki don wanka ba zai
yiwu ba a wannan jikin. Asibiti zamu kai ta, don zama a gida ba zai yuwu ba." Gyaɗa mata kai Lami tayi tare
da fita daga ɗakin sauran suka biya mata baya. Su Uncle John kuma suka wuce inda Pastor ta aike su domin
kwamushe Pastor William. Tunda Sarah ta shiga daƙin ta faɗa bayin dake ciki ta kulle kanta tare da kunna
fanfo tayi ta rusa kuka kamar ranta zai bar jikinta, "Ɗan mijina kuma ɗan ƙanwata!" Ta maimaita a zahiri
tare da rushewa da kuka. Na'ima da tun shigowar Sarah cikin ɗakin ta biyo baya amma sai ta samu har ta
shige bayi, zama tayi a bakin gado tare da zabga tagumi tana jiran fitowarta, shuru-shuru bata fitowa sai ta
tashi ta nufi bakin ƙofar ta kara kunnenta sosai, jin ƙaran ruwa kuma da shashsheƙar kuka ƙasa-ƙasa sai ta
hau buga ƙofar da sauri tana kiran sunan Sarah. Sarah na jin muryan Na'ima tayi saurin goge hawayen ta
tare da wanke fuskan sosai sannan ta nufi ƙofa ta buɗe tare da fitowa. Hannunta Sarah ta kamo tare da
zaunar da ita a bakin gado ta shiga faɗin, "Kiyi haƙuri ƙanwata, na san abun da ciwo kuma akwai zafi ace
ƙanwarka uwa ɗaya uba ɗaya tana ɗauke da cikin mijinka bayan kuma ba mutuwa ko rabuwa suka yi da
mijin ba, ta hanyar zina aka sami cikin. Kiyi haƙuri Sarah, Kar wannan dalilin ya saka mijinki ya fara fita a
ranki ko kuma kiyi tunanin rabuwa dashi." Ɗago jajayan idanunta tayi tare da kallon Na'ima bayan ta saki
wani malalacin murmushi tare da faɗin, "Na'ima! A duniya kina tunanin akwai abunda Khalil zai min inji ya
fita a raina ko kuma inji ina son rabuwa dashi? Na'ima bari kiji, da wannan idanun nawa na kama Khalil da
Aina'u haihuwar uwarsu kuma a gaban ƴaƴana suna kwanciya, wannan bai saka naji tsanarsa ko inji ina son
rabuwa dashi tun a wancen lokacin ba sai yanzu?" Girgiza kai tayi tare da cigaba da faɗin, "Wallahi, tallahi
zan iya riƙe ƴaƴan Khalil guda goma ko da ace duk ƴaƴan karuwai ne, halaccinsa a gare ni ba zan taɓa iya
biyansa ba har gaban abada. Kin san irin wuyar da nasha kuwa? Tsutsotsi marasa kyan gani, ni kaina da
suke fitowa daga jikina kyamar kaina nake yi, amma sau ɗaya bawan Allahn nan bai taɓa ko canza mun
fuska ba, balle kuma ya raba shimfiɗa dani, ga uban warin da nake yi kamar mushen jaki, amma Khalil ko
toshe hanci bai taɓa yi ba bare ya tsirtar da yawu. Wallahi samun irin Khalil a matsayin miji aljannar duniya
ce kuma ba ko wacce mace bace ke dacen miji irin nawa ba, sannan ni kuma na samu nayi sake! Bayan
idan laifi ne shi akai wa amma duk da hakan bai juya min baya ya bini har cibiyar mahaifina ya dawo dani
gida. Aina'u ta cutar da mahaifiyarsa da ahalinsa dashi kansa, amma duk da haka bawan Allah ko ɗigon son
da yake min bai ragu ba. Har ƙanwarsa Aina'u ta kashe, amma bai wulaƙantani ba duk da ya san gaskiya,
sai nice zan gujesa! Ai ko alkhairin da yayi maku kawai yaci a riƙe masa ɗansa ko da kuwa karuwan ce ta
haifesa kuma a cikin hayyacinsa yayi mata cikin. Khalil mutun ne Na'ima, ba zan taɓa iya rabuwa dashi ba.
Shi bai rabu dani ba, sai nice zan rabu dashi? Na'ima abunda Aina'u zata haifa, ɗana ne ko ƴata ce har
abada!!" Rungumeta Na'ima tayi tare da fashewa da kuka mai ciwo tana faɗin, "Ubangiji Allah yasa ni da
ƴan uwana kamun mutuwar mu mu ɗanɗani daɗin aure. Allah ka yafe mana dan girman zatinka ka sada
mu da mazajen mu." "In Sha Allah Na'ima kuma zaku samu miji, mai wuyar ita ce natsuwar, kuma
Alhamdulillah an natsun. Miji kuma zai zo in Sha Allah." "Ni da su Hassana, za muje mu gyara gidanki tasss
yau ɗin nan, in Sha Allah. batyan mun kammala komi kuma zuwa daddare mijinki zai zo ya ɗaukeki ki koma
gidan ki. Babu amfanin cigaba da zama anan. Ki kira Khalil ɗin ki faɗa masa." Faɗin Na'ima. Gyaɗa kai Sarah
tayi tare da kai hannu kan ƙaramin fridge ɗin dake ɗakin ta ɗauko wayarta. Ringing ɗaya Khalil yayi
rejecting tare da biyo kiran, "Assalamu alaikum, mine kin tashi lafiya?" Gyaran murya Sarah tayi tare da
faɗin, "Lafiya ƙalau Happiness, Ina kwana yasu Hajiya?" "Lafiya ƙalau duk suna gaishe ki, Ni kuma in nan
ina ta missing ɗinki." "Su Na'ima ne za suzo anjima kaɗan suyi gyaran gidan." Faɗin Sarah. Tashi Zaune
Khalil yayi tare da faɗin, "Allah yayi wa Aunty Na'ima albarka, don na san ita ta kawo wannan zancen, kice
anjima kawai in zo in ɗauki matata. Kuma dama anjiman nake son zuwa in gaida su ba Lukman in ƙara
ganin lafiyar baba, don so nake in maido shi asibiti a cigaba da duba lafiyansa. Yanzu dai ki faɗawa su
Aunty Na'ima su kasance cikin shiri gani nan zuwa in kawo su gidan, sannan za'a kwashe komai na
ɓangarenki a fitar dashi a gidan don bani son in riƙa ganin komai don zai riƙa tuna min da pass." Ɗan shuru
Sarah tayi, cikin zuciyarta tana mai faɗin, "Akwai wani babban lamari dake gabatowa wanda dole ya riƙa
tuno maka da komai, don zai kasance babban taɓo a gare mu gaba ɗaya. "Kin yi shiru love!" Faɗin Khalil
yana kallon wayarsa kamun ya mayar kunne. "Ok tom bari na faɗa mata." Sarah ta faɗi. "Bye, I love you. Sai
na ƙariso." Ya faɗi tare da kashe wayar bayan Sarah tace, "I love you too." Kalonta Na'ima tayi tare da
faɗin, "Mai yace?" "Cewa yayi za'a kwashe komai na ɓangarena a fitar dashi a canza sabo saboda ganin
tsoffin zai saka ya riƙa tuna abunda ya faru a baya, sannan kuma ya ce ku shirya gashi nan a hanya domin
ya kai ku can gidan." Dafa kafaɗanta Na'ima tayi tare da faɗin, "Ki kwantar da hankalinki, in Sha Allah
komai zai zo da sauƙi. Ni bari naje na sanar dasu Hassana domin su shirya kar yazo kuma a ɓata masa
lokaci." Na'ima ta faɗi tare da fita daga ɗakin. Sarah kuwa haɗa kai tayi da cinyoyinta ta fashe da kuka........

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[14/11, 12:31 PM] Matar Sayyadee: "Hassana, kuyi maza ku shirya yanzu dan Allah, Khalil na hanya zai zo
ya kai mu can gidansu zamu gyara gidan don anjima Sarah zata koma gidanta." Faɗin Na'ima tare da nufa
wajen fanfon dake tsakar gidan daga can gaba domin ɗaukar bokiti. "Ai wallahi kam gwanda, don ban ga
amfanin zamanta a cikin gidan nan har yanzu ba." Faɗin Marfu'a. "Ni a shirye ma nake, hijjab ɗina kawai
zan ɗauko in saka idan ya ƙariso." Hassana ta faɗi. "Ni kuma Na'ima na fitowa zan shiga bayi nayi wanka
sharp-sharp." Faɗin Nuratu tana mai mayar da hulan kanta don har ta soma tsifa. "Sai dai idan baki so
wankan ba, amma ga bayin mama, ga kuma na tsakar gida tun da Na'ima na ɗakinmu ta shiga." Faɗin
Hassana. Harararta Nuratun tayi tare da matsawa dai-dai kunnanta tare da faɗin, "Kakarki Pastor Debora
tana cikin toilet ɗin mama tana ta sakin zawo tashin hankalin ganin halin da Aina'u take ciki. And ba zan
ƙara amfani da bayin mama ba sai nayi masa wankan tsarki. Yanzu haka idan aka ce maki gaba ɗaya
bangon bayin mama an gama fitsare shi, kar kiyi musu." Dariya Hassana tayi tare da faɗin, "Kin iya sharri
Nuratu. Sai kace wata shanu da za kice ta gama fitsare bango." Watsa hannu Nuratu tayi tare da faɗin, "To,
kin san dai daga matansu har mazansu a tsaye suke fitsari, kuma kin san dai su uncle John suna using bayin
tunda anan suke yini kamun su tafi masaukinsu." Girgiza kai Hassana tayi tana dariya tare da faɗin, "Allah
ya shiryaki Nuratu!" Tana gama faɗin haka ta wuce ɗaki. Ɓangaren Khalil, yana yanke wayar ya mayar da
akalar kiran zuwa Turkish furniture yayi ordering latest furniture for both down and upstairs sannan ya fito
ya nufi ɗakin Hajiya, sai da yayi knocking sannan ya murɗa handle ya shiga. Tare ya ganta da ƴan
kanzaginta sai faman lissafi suke. "Yauwa zauna nan Ibrahim, dama kamar kasan yanzu zan aika Lauratu ta
kira min kai." Faɗin Aunty Yagana. Zama yayi a ƙasa a kan carpet yana kallonsu, domin wasu uban leces da
atamfofine akan gadon birjik. Hajiya kuma sai wani kallon banza take yiwa Khalil ɗin. "Ibrahim,
Alhamdulillah an saka bikinka nan da sati biyu masu zuwa. In Sha Allah Abdullahi dasu kawunanku Ameeru
da Shamsu zasu juyo yau. Yayanka Abdullahi ya biya maka sadaki Naira miliyan biyu. Da cewa suka yi sai da
sisin gwal, amma daga baya kasancewar duk abun na gida ne, sai suka karɓi kuɗi. Yanzu hidima ce babba a
gare ka, don wannan bikine na musamman ba irin bikinka na fari ba. Bikine na arziki, don haka sosai zaka
saki bakin aljihu don naira za tayi kuka tabbas! Don akwati kawai za kayi dozen kuma sai huɗu." Da sauri
Khalil ya ɗago tare da faɗin, "Aunty Yagana, mai za'a saka haka a cikin akwatin zoden har set uku? Kusan
akwatina kusan arba'in da takwas fa!" "To ka cike su zama hamsin!" Faɗin Hajiya a gadarance. Tsuke baki
Khalil yayi ba tare da ko tari ya kuma yi ba. Aunty ya gana tace, "Yanzu transafer za kayi mana na 5million
domin haɗa lefan, idan basu isa ba kuma zan neme ka. Sannan idan zaka tafi Maidugurin, tare zamu tafi
domin akwai abunda zanje in yi a can ɗin. Kasan dolene mu je mu tambayi yana jin shirye-shiryen su
domin mu tsara komai a dai-dai. Kai kuma zaka san abubuwan da amaryan take buƙata, kuma ƙawayanta
kaf kai zaka yi masu duka anko ɗin da suka fitar ka kuma biya masu kuɗin ɗinki." Wannan karan ma shuru
Khalil yayi yana kallon ƙasa. "Wai Ibrahim baka ji abunda ake cewa bane don ubanka." Ɗagowa Khalil ɗin
yayi tare da kallon Hajiya sannan yace, "Hajiya duk naji, amma abunda ban sani ba shine, ita wa take da
suna, idan ta tashi zuwa haɗota za ayi da wani abun sana'a mai girma ne haka? Naji kuɗin da kuke kira ne
kamar za'a saka hannun jari a wai kamfani." Daƙuwa Hajiya tayi masa tare da faɗin, "Mu kake faɗawa
wannan banzan maganar Mu'azzam? To buɗe kunnuwanka da kyau ka saurareni, kuɗi dole ne ka bayar tun
da kana da su. Ita wancen ƴar so ɗin, lokacin aurenta ai rawar ƙafa ka riƙa yi kana watsi da kuɗi kamar a
bola kake tsinto su. Don haka dole ne ka bayar." "Aunty Yagana, account details ɗinki in tura maki kuɗin."
Faɗin Khalil yana mai fiddo wayarsa. "0134.... Aisha Yagana Musa, Uba bank." Faɗin Aunty Yaganar. Nan
take Khalil ya mata transfer ɗin kuɗin. Washe baki Aunty Yaganar tayi tare da faɗin, "Sun shigo, ko kai fa
Khalil?" "Hajiya zan iya wuce wa?" Faɗin Khalil. "Eh, Allah ya ƙara buɗi. Ka tabbatar ka kira yarinyar nan
Habbooba ka bata hakuri ita da mahaifiyarta kamun zuwanka Maidugurin ka bayar fuska da fuska." "To
Hajiya." Shine kawai abunda yace tare da miƙewa. Har ya kai bakin ƙofa, sai kuma ya juyo tare da faɗin,
"Hajiya anjima in Sha Allah zamu dawo tare da yayyin Sarah, zasu gyara mata ɓangarenta." Taɓe baki
Hajiya tayi tare da faɗin, "Uhm, kace mu nemo manya-manyan radio domin sauraran ƙira'ar Alkur'ani
tunda dangin matsafa zasu shigo gidan." "Sai na dawo!" Shi abunda Khalil ya sake faɗi tare da fitowa daga
ɗakin ransa a matuƙar ɓace da sauyin halin hajiyan. Saboda tsaikon da ya samu a wajen Hajiya, yana fitowa
ya jiyo horn ɗin motar Company Turkish furniture. Ya fahimci hakane kayan da ya ango ta saman gate. Mai
gadi ya wangale masu gate ɗin suka shigo suka yi parking. Shi ya ƙarisa har inda suke ya ba kowanne su
hannu don sun kai su bakwai. Haƙuri ya basu tare da shaida masu yanzu zaije ya taho da waɗanda za su
wanke daƙunan su gyara sai su kuma su shigar da kayan su danka. Nuna masa suka yi babu komai ya tafi ya
ɗauko su zasu jira a cikin mota. Da sauri Khalil ya koma mota ya tada tare da barin gida. Ko da ya isa gidan,
bai shiga waya kawai yayi wa Sarah akan su Na'ima suyi sauri su fito. Kasancewar duk sun gama kimtsawa,
Sarah na faɗa masu saƙon Khalil ɗin sai suka fice da sauri shi kuma ya kwashe su zuwa can gidan ya ajiye su
tare da basu key sannan yayi maza ya juya domin komawa gidansu Sarah don ya gaida su Nnanne ya kuma
ga jikin Baba Nuhu. A ɓangaren su Na'ima kuma, ko da Khalil ya sauke su, side ɗin Hajiya suka nufa.
Knocking suka yi fuskansu, "Ku zauna, barin na kira wo Hajiyar tana ciki." Faɗin Laure tare da saurin
wucewa kitchen ta ɗauko masu ruwan gora da kuma lemun roba ta ajiye sannan ta nufi ɗakin hajiyan. Tura
ƙofar tayi ta shiga tare da faɗin, "Hajiya kin yi baƙi suna parlour." Ba tare da Hajiya ta kallate ba saboda
ɗaɗɗaga kaya da take yi, kallon Aunty Yagana hajiya tayi tare da faɗin, "Yagana a cikin sets ɗin akwatunan
guda hamsim, dole a cire kamar set goma manya-manyan a cika su da lafayas masu tsada, kin san dai
kayane na gado." "Ai hakan na cikin burina." Faɗin Aunty Yaganar. Sai a lokacin Hajiya ta kalli Laure tare da
faɗin, "Laure, su wanene suka zo?" Washa baki Laure tayi tare da faɗin, "Yayyin matar ya Khalif ne suka zo
gaishe ki." Wani irin wuntsilowa Hajiya tayi tana mai faɗin, "Qalu Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! kin
kashe mu, kin kashe mu Laure!! Dangin matsafan kika bari suka shigo min parlour ba tare da kin kunna
mana karatun Alƙur'ani ba. Maza fita ki kunna min karatu a parlour ki ƙure min ƙara. Zanin Hajiya har
kwancewa yayi saboda yanda ta wuntsilo daga gado, ba tare da ta ɗaura da kyau ba ta buɗe ƙofa ta fito
tana ruwan bala'i, kuma su Na'ima dake parlour suna jiyo komai don tana yine su Aunty Yagana na taya ta.
"Dangin bala'i dangin matsafa. Kin barsu sun shigo su ƙarisa abunda ƴar uwarsu ta soma kenan tunda ita
alƙadarinta ya karye. Allah ka shiga tsakanin nagari da mugu!" Hajiya ta faɗi tana nufowa parlourn zani a
hannu. Na'ima kuwa kallon ƴan uwanta ta shiga yi, suma suna kallonta. "Aouzu bikalimatullahit tammat
min sharri ma qalaqa!" Faɗin Hajiya tana mai bin parlourn tana tofewa. Lokaci guda su Na'ima suka miƙe
suna kallon Hajiya, babu wanda gabansa bai faɗuwa a cikinsu. "Ina wuni Hajiya?" Suka haɗa baki duka suka
faɗi. Da ƙarfi Hajiya ta kuma faɗi, "Aouzu bikalimatullahit tammat min sharri ma qalaqa!" Tana mai nuna
masu ƙofa da hannunta don ko kalma ɗaya bata son ta shiga tsakaninsu. Ɗaya bayan ɗaya su Na'ima suka
fita daga ɗakin kowa na saƙe-saƙe tsakanin su. Sai bayan sun tsakar gidan ne Na'ima ta ɗaura hannu a kai
tare da faɗin, "Ƴan uwana, Aina'u ta kashe Sarah a cikin gidan nan, ta shafa mata baƙin penti. Khalil ne
kawai ke sonta. Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Ta ƙarisa maganar tana mai zubar da hawaye. "Aina'u
gube mai mummanar dafi. Ta lalata alaƙar dake tsakanin hajiyan Khalil da Sarah! Allah ubangijin kowa da
komai, ka sassauta zuciyar baiwar Allah akan ƙiyayayar da muka gani a cikin idanunta." Hassana ta faɗi.
"Aina'u ta ruguza jin daɗin Sarah a cikin gidan nan." Na'ima ta kuma faɗi. Girgiza kai Marfu'a tayi tare da
faɗin, "Ƴan uwana, Aina'u bata isa ta yanke jin daɗi da kwanciyar hankalin Sarah a cikin gidan nan ba,
tabbas naga ƙiyayyar Sarah a cikin idanun Hajiya, amma ina so ku sani, shi Allah kullum a bayan mai
gaskiya yake. Ina sha Allah addu'a da kuma ɗabi'un Sarah, shi zai dawo da martabarta a cikin idanu da
zuciyar Hajiya. Ni ina ji a jikina, Hajiya zata huce kuma ta riƙe Sarah hannu biyu, amma fa a wannan gaɓar
sai tayi mugun haƙuri da kau da kai. Ni wallahi naga ƙoƙarin Hajiya sosai, domin da wata uwarce akai mata
abunda a kai wa Hajiya, wallahi ko da lu'ulu'u aka yi Sarah sai Khalil ya rabu da ita. Aina'u fa tayi masu
mummunar tabo a zuciya, gashi kuma yanzu tana ɗauke da ciki, ko ya Hajiya da shi kansa Khalil ɗin zasu
ƙarbi wannan zancen cikin?" Faɗin Marfu'a. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un, kaiiiii Allah ya tsinewa
Aina......" Saurin toshe mata baki Na'ima tayi tare da faɗin, "Kar ki ƙarisa Hassana." Girgiza kai Hassana tayi
tana mai tsiyayar da hawaye har da shashsheƙa. "Ku muje mu wanke ɗakin mu su taya mu, mu fitar da
komai. Mun bar su suna ta jira." Faɗin Nuratu ganin suna ta koke-koke. Ita kanta ba ƙaramin daure
zuciyarta tayi ba. Sai taji gaba ɗaya bata tausayin Aina'u ko kaɗan, ji take ma halin da take ciki yanzu dama
Allah ya nunka mata azabar. A can gidan su Sarah, bayan Khalil ya gama gaisawa dasu Nnanne suna ta saka
masa albarka, sai ya kalli ba Lukman tare da faɗin, "Ba Lukman ina tunanin fitar da Baba India, in Sha Allah
zai samu kulawa sosai kuma zai warke." Abunda ya bawa Kowa mamakin a ɗakin, jin muryan Baba Nuhu
yana faɗin, "Ibrahim, Nagode sosai da ɗawainiyar da kayi dani da kuma ƴaƴana, Allah ya duba maka naka
ƴaƴan kai ma. Ni zuwan Mahaifiyata da kuma ƴan uwana nan muka gane ya fiye min komai. Ko yanzu Allah
ya ɗauki raina Alhamdulillah. Bana buƙatar zuwa wata ƙasa domin duba lafiyata, Ni n na san lokaci kawai
nake jira. Nnanne, ki yafe min duk abunda na aikata maki cikin rashin sani da kuma sani, ƴan uwana kuma
ku yafe min. Ku faɗawa, Saratu ɗiyata, Nuratu, Hassana, Na'ima, Marfu'a, da Lukman na yafe masu har
abada, Allah kuma yasa su gama da duniya lafiya. Ibrahim, na bar amanar Sarah a hannunka, kace mata
ban yafe mata ba idan har yaƙi bin uwarninka da bai saɓawa Allah ba. Ƴan uwana, kar ku yarda ku bar
kaduna ba tare da duka ƴaƴanku ba, Sarah kawai zaku bari a Kaduna, ita ma aure ne ya ceceta." Kuka
Nnanne ta fashe dashi tare da kama hannunsa ta shiga faɗin, "Nuhu cuta ba mutuwa bace, in Sha Allah
wannan cutar ba ajalinka bane." Girgiza kai kawai Baba Nuhu yayi tare da kallon gefe yana tsiyayar da
hawaye. Duk second na rayuwarsa, hoton abunda ya aikata da Aina'u yake gani yana masa gizo shiyasa
gaba rayuwar ta gunduresa. "Allah ya isa tsakanina da ke Aina'u!" Baba ya faɗi a bayyane tare da fashewa
da kuka. Ba shi kaɗai ba, gaba ɗaya ɗakin kuka suke yi har da Khalil daya sunkuyar da kai ƙasa. Da ƙyar
Lami ta iya gogewa Aina'u jiki, duk inda ta taɓa nama ne ke yankowa ya faɗo sai tsutsotsi su biyo baya.
"Lami ruwa, ki bani ruwa in sha!" Faɗin Aina'u don abunda ke iya zama a cikinta kenan. Ruwan Lami ta
ɗauko tare da buɗe goran ta kafawa Aina'u a baki. Kuka Lami ta fashe dashi ganin rabin ruwan na
tsiyayowa ta maƙogoronta yana zubowa har cikinta, hannun Lami rawa yake yi tana kallon yanda
maƙogoron ke sama da ƙasa. "Yesu kayi mana tsari da shaithan mai sanya aikin zunubi a zukata. Yanzu kalli
yanda kika mayar da kanki Aina'u! Wannan shine sakamakon duk wani bawa mai aikata zunubi. Zunubanki
sun yi yawa Aina'u. Ke sheɗan ce da kanki. Ko Rose Merry da ta kaii ki wajen boka, kin fita mugunta a
zuciya!" Faɗin Lami tana share hawayen ganin halin da Aina'u take ciki. "Lami cikina, kaina, bayana, idona,
cinyata, wayyoooo Allah cikina Lami. Yana min zafi sosai!" Shine abunda Aina'u take ta faɗi. Fita Lami tayi
daga ɗakin tana kuka don bata da abunda za tayi wa Aina'un. Bayan Khalil ya fito daga ɗakin Baba, ya gama
yanke hukuncin in Sha Allah nan kusa zai tura Baba India. Fita yayi ya koma mota sannan ya kira Sarah a
waya, bayan ta ɗaga yace mata ta same shi a waje a cikin mota. Hijjab ta saka sannan ta fita tare da buɗe
motar ta shiga sannan ta rufo motar. "Ina wuni?" Ta faɗi tana kallon ƙasa, taƙi yarda ta ɗago su haɗa idanu
saboda yanda idanunta suka yi jazuuur alamar taci mugun kuka. "Mine!" Ya kira sunanta yana mai tsura
mata idanu. Ɗagowa tayi suka haɗa idanu tayi saurin mayar da kanta ƙasa. "Mine meke damunki haka?" Ya
faɗi a ruɗe tare da kamo hannayenta. Kuka ta rushe dashi har da shashsheƙa tana mai damƙe hannunsa
tare da rufe idanu. Sai da ta jima a wannan yanayin sannan ta soma magana bakinta na rawa, "A yau na
samu labari guda biyu da suka girgiza ni kuma suka saka zuciyata tayi tsalle." Ganin Khalil na faɗuwa yace,
"My endless bliss, wani labari ne waɗannan?" Idanunta a rufe tace, "Happiness, don zaka yi aure shine
baza ka iya faɗa min ba sai dai in tsinci maganar a wani waje?" Wani irin bugawa zuciyar Khalil yayi tare da
faɗin, "A ina kika ji wannan maganar Sarah?"

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[14/11, 12:31 PM] Matar Sayyadee: Murmushi mai ciwo Sarah tayi tare da faɗin, "Happiness ba wai auren
da zaka yi bane yafi ɓata min rai, ɓoyewar da kayi min ne yake ci min zuciya!" Ta ƙarisa maganar tana ƙara
fashewa da kuka. Gaba ɗaya Khalil sai ya rasa inda zai saka kansa, riƙe hannunta yayi gam tare da faɗin,
"Look Sarah, wallahi tallahi ba'a son raina zan ƙara wannan auren ba, Hajiya ce ta matsa sai na aureta
domin ƙarfafa zumunci. Ki yarda dani, wallahi ko fuskan yarinyar nan ban taɓa gani ba. Wallahi ni ke kaɗai
ce zaɓina. Ban taɓa jin a cikin zuciyata ko na second in ƙara aure. Wallahi ke kaɗai kawai kin isheni. Ke four
in one ɗina ce. Ba zan iya ja da maganar Hajiya ba shiyasa na amince da wannan auren. Auren da zan yi ba
zai taɓa rage ƙaunar da nake maki ba ko kuma darajarki. Ke ɗin ta daban ce a cikin zuciyata Sarah." Wani
irin natsuwa da daɗi kalamansa suka yi mata a cikin zuciya. Sai dai still gabanta bai daina faɗuwa ba a duk
sa'ar da ta tuno maganganun Hajiya lokacin da ta kira ta ɗazu a waya. "Assalamu alaikum hajiya ina
kwana?" A matuƙar murtuke Hajiya ta soma magana, "Ba gaisuwarki na kira domin na amsa ba. Na kira ne
inyi maki gargaɗi da babban murya, ki kiyaye ni idan har kina son cigaba da zama da ɗana! Idan shi kun
shanyesa, to ni nafi ƙarfin tsafin iyayanki wallahi. Kuma aurene kamar anyi an gama tsakanin Ibrahim da
Habbooba in Sha Allah. Tsafinku zai ƙare a kanku!!" "Hajiya don Allah kiyi haƙ........" Tun kamun Sarah ta
idasa Hajiya ta yanke wayar bayan ta saki dogon tsaki. Sauke wayar Sarah tayi a kunne tare da fashewa da
kuka tana faɗin, "Aina'u kin ga abunda kika jawo min ko? Aina'u kin gani ko?" Taɓa ta Khalil yayi ganin tayi
nisa a tunani. Firgigit ta kalleta tare da faɗin, "Hajiya tana fushi dani ko, Happiness?" Girgiza kai Khalil yayi
tare da faɗin, "Kar ki saka komai a ranki, Sarah. Everything will be alright in Sha Allah! Bana son kina tada
min da hankalinki, dubi yanda duk kika bi kika rame!" "Aina'u ta tarwatsa mana farin cikin mu, Happiness!"
Sarah ta faɗi tana zubar da hawaye. "Baki ga yanda Allah yayi da ita ba, ai duk mugun mutumin da bai
tuba, Allah baya barinsa sai ya soma nuna masa ƙarshensa tun a duniya." Shuru Sarah tayi tare da
sunkuyar da kai tana tunanin ta yanda zata fara shaida masa Aina'u na ɗauke da cikinsa. "Mine, speak up!
Akwai abinda kike ɓoye min." Ɗagowa tayi ta kallesa tare da buɗe baki za tayi magana sai wani kukan ya
kuma kufce mata, "Oh Inna lillahi! Please talk to me, Sarah." A hankali Sarah tace, "She's pregnant."
"Who?" Ya yafe mata tambayar yana kallonta da mamaki don bai san ko a kan wa take maganar ba.
"Aina'u! Aina'u tana da ciki." Shuru yayi na ɗan wasu sakonni kamun yace, "Wacece Aina'u ma?" Ya faɗi
don gaba ɗaya he's totally confused. "Aina'u ƙanwata. Kuma cikin naka ne." Da wani irin mahaukacin
tsawan da tun da suke tare bata taɓa jin irinsa ba yace, "What nonesense are talking about? Wannan wani
irin magana da shirmen banza ne? Kar ki ƙara min wannan magana Mine. Ni? Allah ya tsare ni in haɗa jini
da Aina'u. Sam ba cikina bane, ta tafi can ta nemo uban cikinta." Da idanu kawai Sarah ke binsa ba tare da
ko tari kwakwkwara ba. "Dan ubanta ni zata laƙawa cikin dake jikinta!" "Uban Aina'u shine yayi silar
zuwana duniya, Khalil. You should please watch your tongue!" Ta faɗi da ɗan ɓacin rai a fuskanta. "Ok, kin
yarda cikina ne a jikinta kenan? Don kawai na kwanta da ita ba cikin hayyacina ba, sai ta ɗauko ciki ta laƙa
min? To ba zai yiwu ba Wallahi!" "Ina ce kai medical doctor ne? Kuma bugu da ƙari kana da babban asibiti
mai ɗauke da ingantattun kayan aiki. Sai ka ɗauke ta kaje asibiti ayi DNA test ka gano shin cikin naka ne ko
ba naka bane. Thanks God your are the one that told me, DNA test can be done during pregnancy." Tana
gama faɗin haka ta buɗe motar ta fice, "Mine, mine, Sarah, maman twins!" Haka ya dunga kwala mata kira
amma ko waigowa bata yi ba bare ta saurare shi. Da ƙarfi ya buga steari motar tare da faɗin, "Damn it!"
Yana nan zaune a cikin motan ya hango Lami da Suhana suna ƙoƙarin buɗe gate. Buɗe murfin motan yayi
tare da ƙarisawa inda suke ya taimaka ya buɗe masu gate ɗin, "Idanunka kenan abban twins?" Suhana ta
faɗi tana dariya. Ɗan murmushi yayi tare da faɗin, "Na shigo ai, kece dai ban gani ba." "Ina ɗakin mama ina
bacci ina ga lokacin, to ya gajiyanmu?" Faɗin Suhana. "Gagiya kam tabi lafiya." Ta faɗi. Gyaran murya Lami
tayi tare da faɗin, "Ɗana, ko zaka ɗan shigo daga ciki muyi magana, don dama yanzu nake shirin neman ka
a waya. Mamana ke son kai Aina'u asibiti, to kuma ina son yin wata magana da kai kamun tafiyarmu." Ɗan
gaba Khalil yayi gabansa na faɗuwa, don haka kawai yaji a jikinsa magana za tayi masa akan cikin da
Aina'un ke ɗauke dashi. Hanya ta nuna masa tare da faɗin, "Mu shiga ciki, mamana da uncles ɗin su Sarah
duk suna ciki." A hankali Khalil yayi gaba yana tafiya kamar kwai ya fashe masa a ciki. Takalminsa ya cire
sau ciki ya rage sai bakar Safar ƙafa sannan yayi sallama kasancewar Lamin ta faɗa masa su ba Lukman
suna ciki. Daga ciki duk suka amsa tare da bashi izinin shigowa. Bayan Khalil da Lami sun zauna, sai ɗakin
yayi tsit babu abunda kake ji sai ƙarar fanka. Sun ɗauki a ƙalla mintuna biyar kamun Pastor _Emmanuelle
Deborah Gabriel_ ta soma magana, "Zan fara magana da sunan Yesu Almasihu mai ceto, Ya Ubangiji
Madaukakin Sarki, Ina rokonka tsari daga makiyi na bayyane dana ɓoye, kada ka bari wani abu ya cutar da
mu, ka tsarkake mana ranmu, hankalinmu, zuciyoyinmu. Ka kawar da duk wani mummunan kuzari daga
rayuwarmu da gidanmu, Ka kare mu daga dukkan sharrin da ke zuwa gare mu, ka ƴantar da mu daga
dukkan haɗari, ka taimake mu cikin bukatu, ka taimake mu, ka ba mu ƙarfi da kuzari bisa ga baƙin cikinmu,
da kasala. bacin rai da nauyi. Ubangiji, kai mahiliccin komai, ka cece mu daga maƙiyi, daga mugun jijjiga.
Kada ka bari maƙiyi ya yi nasara, ka yi nasara da shi da ikonka, Ka lulluɓe ni da mayafinsa mai tsarki, domin
ya sami kuɓuta daga dukan haɗari. Sunanka yana da iko, bari in yi amfani da shi don kau da mugunta,
kuma mugunta ba ta zo mini ba. Kai ubangiji ne, ba zan daina yabonka ba, ni baiwarka ce. Rundunonin
mugaye suna yaudara, masu rauni ne kawai za su iya kama su, saboda ba su da lafiya. Ka ba ni damar
dawwama a gare shi, in ci gaba da sonsa, ka kiyaye ni, koyaushe zan bi ka, in naimi albarkaka, domin kai ne
hasken da ke haskaka matakai na, alheri koyaushe yana cin nasara a kan mugunta, ina rokonka, ya
Ubangiji, a koyaushe. Ka kiyaye ni, ni baiwar ce. Amin." Gaba ɗaya su ba Lukman suma suka ce amin ganin
ba addu'a tayi mara kan gado ba. Sai ta kalli Khalil tare da faɗin, "Yarona, nasan cewa yarinyar ta cutar da
kai. Ni ba zan iya buɗe baki in ce ka yafe ta ba, amma zan iya baka haƙuri duk da na san akwai ciwo mai zafi
a ƙirjinka. Kayi haƙuri! Kayi haƙuri!! Kayi haƙuri ku duka har da mamanka!!! Kuma mu gode, mun gode
sosai da soyayyar da kake nunawa jikata Serah. Sannan abu na biyu, ina mai baƙin cikin sanar da kai,
saduwa da kayi da Aina'u sakamakon amfani da tayi da sihiri, ta samu ciki. Yanzu haka tana ɗauke da
cikinka a jikinta!" A mugun razane Khalil ya ɗago yana jujjuya kai amma ya masa motsa laɓɓansa kuma
yana son yin hakan. "Ban tari numfashinki ba Deborah, amma ta yaya, shin kuna da hujjar da zai tabbatar
da cikin dake jikin Aina'u na Ibrahim ɗin ne?" Wani irin ajiyar zuciya mai ƙarfi Khalil ya saki wanda ya saka
gaba ɗaya ɗakin suka kallesa. Babu kuma abunda yake yi illa fifita da hulan kansa. Ɗaga kafaɗa Pastor
Emmanuelle Deborah tayi tare da faɗin, "Well, I heard that he's a medical doctor. Sai yiya mata test ya
gano hakan." "Amma ba naji ance sai an haihu ake irin wannan gwajin ba." Faɗin Nnanne. Wannan Karan
Khalil ne yayi maganar, "Nnanne ana yi idan cikin ya kai wata biyu. Ba dole sai ta haihu ba." "To
Alhamdulillah, zaman me muke yi a nan? Sai mu tafi asibitin ko?" "Hajiya zuwanmu duka bashi da wani
amfani a yanzu, domin fitowar sakamakon zai iya ɗaukar kwanaki bakwai zuwa takwas. Yau ɗin sample ɗin
kawai za'a ɗauka." Khalil ya faɗi. "To babu damuwa, sai ku tafi da ita mahaifiyar yarinyar da kuma Lukman
da Debora. Idan sakamakon ya fito, maji. Allah yasa muji alkhairi." Da "Ameen" duk aka amsa sannan gba
ɗaya suka miƙe, Khalil ne ya soma fita daga ɗakin yana zufa.
_Na san tabbas babu yawa, amma da babu gwara babu daɗi. Har yanzu ban samu natsuwa bane. In Sha
Allah gobe zan yi ƙoƙari nayi maku mai yawa. Nagode._

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[14/11, 12:31 PM] Matar Sayyadee: Yana isa ƙofar gida ya buɗe mota ya shiga tare da kullewa ya haɗa kai
da steari yana faɗin, "Ya Allah, don son da kake wa mafificin halitta, ka taimaki bawanka kasa wannan ciki
dake jikin yarinyar nan ba nawa bane!" Yana gama faɗin haka Hajiya ta kuma faɗo masa a rai, "Inna lillahi
wa'inna ilaihir raju'un! Bala'i, tashin hankali da masifa kiyi kwanciyarki kiyi bacci dan Allah!" Ya kuma fadi
yana mai kaiwa steari duka. Wayarsa ce ta soma ƙara, firgigit ya ɗauko wayar yana kallon screen ɗin, ganin
ya Abdullahi ke kiran wayar yayi saurin picking gabansa na faɗuwa. "Assalamu alaikum, ya Abdallah ina
wuni?" Daga ɗayan ɓangaren ya Abdullah yace, "Lafiya ƙalau Khalil. Yasu Hajiya?" "Suna nan lafiya." Khalil
ya amsa. Gyaran murya ya Abdullahi yayi tare da faɗin, "Ibrahim, naso daga Maiduguri in dawo nan
Kaduna domin inyi magana da kai fuska da fuska amma sai na samu urgent call daga wajen aiki shiyasa na
yanke hukunci magana da kai ta waya kawai." "Ina jinka ya Abdallah." Khalil ya faɗi with soo much respect.
"Khalil, dan Allah ka bi Hajiya a hankali. Na fahimci ciwon da take ji a cikin zuciyarta. Ina baka wannan
shawarar ne matsayin babba wanka kuma makwafin uba. Biyayyar da za kayi mata akan wannan auren
shine kawai hanyar da zaka faranta mata kuma ka dawo da ƙima da mutuncin matarka a idanun Hajiya. Ka
nuna mata kana son auren with all your heart, Kar ka nunawa yarinyar ita zaɓin Hajiya ce ba naka ba. Na
sani, You don't have feelings for her, amma haka zaka daure, domin muddin ka soki auren, kamar kana ƙara
cusa tsanar matarka ne a cikin zuciyar Hajiya. Ka nuna Hajiya you accept Habbooba with all your heart.
Idan so samu ne, ka nuna mata zumuɗi akan auren. Hajiya za tayi farin cikin sosai, kuma Khalil ka rage
nunawa kana matuƙar ƙaunar matarka a idanun Hajiya, wannan zumuɗin, tashin hankali da ɗimaucewa,
duk ka rage. Don su mata suna da wani abu a cikin kwanyansu, idan abu nasu ne, to abun nan ya sosu su
ɗaya kawai. Kuma duk tsufan mace ba'a rabata da wannan kishin. You should try to control your
unconditional love for your wife in front of your mother, Khalil. Ina fatan ka fahimta." Gyaɗa kai Khalil yake
yi kamar yana gaban Ya Abdullah tare da faɗin, "Na fahimta yaya." "And lastly, Khalil yanzu zaka zama mijin
mace biyu, You have never have the experienced before. Alai, Allah yayi masa rahama, har ya koma ga
Allah Hajiya ce kawai matarsa, ni ban taɓa yi ba, Abdul-Hakeem bai taɓa ba, Barrister ma haka. Don haka
You have to be very very carefull! Ita mace a koda yaushe so take a nuna mata ita ɗaya, tafi kowa a duniya,
a kullum a riƙa appreciating ɗinta. So wannan shine aikin ka, ko waccen su ka nuna mata ita sarauniyace,
amma fa bance ka soki ɗaya a wajen ɗaya ba, ko ka ɗauki maganar ɗaya ka kaiwa ɗaya. Sam babu ruwana
don wallahi _munafikin mata_ zaka zama. Ni dai abunda nake nuna maka shine, "You try t create peace
and harmony in your house. Ko wacce ka bata haƙƙinta, kar ka yarda son da kakewa ɗaya a cikinsu ya
rinjayeka har ka shiga haƙƙin wata. Na san dole ne akwai wacce kafi so, but you should try to hide it from
the other idan kana son zaman lafiya da kwanciyar hankali. Khalil wannan shine abunda na kira in faɗa
maka. Allah yasa ka fahimta." Khalil wani murmushin jin daɗi yayi ganin wan nasa ya saka shi a hanya tare
da faɗin, "In Sha Allah, zan yi duk shawarar daka bani. Nagode sosai yaya, Allah ya ƙara girma!" "Ameen.
Nasan Hajiya ta faɗa maka nan da kwana sha huɗu za'a ɗaura maka aure ko?" Faɗin ya Abdullahi. "Eh ta
faɗa min. Nima kuma yaya akwai abunda nake son faɗa maka." Khalil ya faɗi zuciyarsa na harbawa. "Ina
jinka Ibrahim." Ɗan shuru Khalil yayi sannan ya soma bashi labarin cikin dake jikin Aina'u da kuma
hukuncin da aka tsayar yanzu. Sai da ya Abdullahi ya gama salati sannan yayi, "Hajiya ta san da wannan
maganar?" "A'a ban faɗa mata ba!" Faɗin Khalil. "Good! Kar ka faɗa mata yanzu. Hukuncin da kuma tsayar
yayi. Idan result ya fito, ina son zama mutum na farko da za'a faɗawa sakamakon." "Ina sha Allah yaya."
Faɗin Khalil. "Allah yasa muji alkhairi. Sai ka kira nin." Wani ɗan relief Khalil ya samu a cikin zuciyarsa. Zai
danna number ɗin Sarah kenan ya hangota cikin dogon hijjab ta nufo motar. Cikin saurin tun kan ta ƙariso
ya buɗe mata gidan gaba. Tana shigowa ta rufe motar, ba tare da ta kallesa ba tace, "Kayi haƙuri da abunda
ya faru ɗazu. Hakanan naji kawai raina ya ɓaci sosai!" Hannunta ya riƙe tare da faɗin, "Ni ya kamata na baki
haƙuri Mine, bai kamata nayi maki tsawa ba. Ruɗewa nayi. Amma don Allah kiyi haƙuri." Murmushi tayi
tare da faɗin, "Ya wuce. Naji hukuncin da kuka yanke. Nima hakan yayi min. Gasu can ma sun fito." Faɗin
Sarah tana kallon gate ɗin gidan da Pastor Emmanuelle Deborah ke ƙoƙarin fitowa da mota. "I you going to
follow us?" Ya faɗi yana kallonta. Gyaɗa masa kai tayi tare da faɗin, "Yes!" Tada motar yayi tare da yin
reverse suka ɗau hanya, su Pastor Emmanuelle Deborah biye dasu a baya. Ko da suka isa asibitin, ba
Lukman ne ya cicciɓo Aina'u kamar tsumma har cikin lab. Basu jima ba aka gama duk abinda za'a yi. Suna
dawowa a kan hanya Na'ima ta kira Khalil tare da shaida masa sun gama komai. Sai da ya sauke Sarah a
gida sanan ya juya kan motar zuwa gida domin ɗauko su Na'imar. Lokacin da Khalil ya shiga side ɗinsa, ba
ƙaramin daɗi yaji ba, domin an canza komai na gidan. Harda su kitchen utensils. Kasancewar suna da yawa
masu aikin shiyasa nan da nan suka gama. Su Na'ima ko a fuska basu nunawa Khalil abunda Hajiya tayi
masu ba. Sai dai basu yarda suka koma suka yi mata sallama ba. Haka bayan Khalil ya dawo dasu, basu faɗa
Sarah komai ba, sai ma koɗa gidan da su kai ta yi. Bayan magriba Sarah ta shirya tsaf domin komawa
ɗakinta, yayyinta gaba ɗaya da Suhana suma sun shirya domin rakiyarta, haka Nnanne da Pastor
Emmanuelle Deborah da Aunty Grace, aunty Delilah da Aunty Roth. Na'ima ce ta kira Khalil ta ce masa ba
sai yazo ba. Pastor Emmanuelle da ƴan uwanta a mota ɗaya, sai motar ba Lukman kuma su Na'ima da
Sarah ne a ciki, kuma Na'imar ce ke jan motar don ta iya mota. Tafiyar mintuna ashirin ya kawo su ƙofar
gate ɗin gidansu Khalil, horn suka yi mai gadi ya wangale gate su kuma suka tura hancin motar ciki. Pastor
Emmanuelle na fitowa daga mota ta ƙarewa gidan kallo cike da farin ciki tare da faɗin, "Praise the Lord!"
Da ƙarfi su aunty Roth suka ce, "Hallelujah!" Sannan suka haɗa baki gaba ɗaya suka hau waƙar coci. Daga
side ɗin Hajiya duk suna kallo kuma suna jin komai ta sama ita dasu Aunty Yagana. "Yagana kar a sake a
bari waɗannan kafuran su shigo min sashe, idan sun yo nan kuce masu ina bacci, ko parlour kar su shigo."
"Bari ki gani ina sauka ƙasa in faɗawa wannan wawuyar don zata iya barinsu su shigo." Faɗin Aunty
Yaganar tare da fita daga ɗakin ta nufi ƙasa. "Mun dawo dake cikin gidanki da sunan Yesu Almasihu!" Faɗin
Aunty Roth tare da kama hannun Sarah, a kunne Na'ima tace wa Sarah, "Kiyi bismillah sannan ki shiga da
ƙafar dama!" Jinjina mata kai tayi tare da yin bismillah sannan ta shiga da ƙafar damar tana mai sakin ajiyar
zuciya. Da idanu Sarah tabi ɗakin murmushi ɗauke a fuskanta ganin yanda ɗakin yayi masifar kyau fiye da
lokacin da kawota tana amarya. Lungu da saƙon ɗakunan sama da ƙasa suka dunga bi suna gani. Nnanne
sai faɗin, "Ma sha Allah!" Take yi. Bayan sun ɗan huta sai Nnanne tace, "Debora, ya kamata mu ɗauki
yarinyar nan muje can sashin uwar mijinta, muyi masu gaisuwa da kuma ban haƙurin aika-aikar da Aina'u
tayi masu." Jinjina kai tayi tare da faɗin, "Hakan na da kyau. Muje to." Gaba ɗaya suka fito suka nufi can
ɗin, sai dai bugu duniya anƙi zuwa a buɗe masu ƙofar. Haka suka gashi suka juya suka dawo ɗakin Sarah jiki
a sanyaye. Nnanne da Pastor Emmanuelle Deborah suka saka Sarah a tsakiya suka yi ta mata nasiha mai
ratsa zuciya, kuma cikin dabara ta jeho maganar auren Khalil, nan ma cikin hikima Nnanne tayi ta mata
nasiha tare da bata tips na zama da kishiya da yanda zata kau da kai akan duk wani abun ɓacin rai da
Hajiya zata nuna mata, don it obvious hajiyan bata so dawowar Sarah gidan ba, Nnanne ta fahimci hakane
tun sanda Khalil ya basu labarin auren da Hajiya ta ce yayi duk da shi bai faɗa masu Hajiyar bata son Sarah
yanzu ba. Da zasu tafi, ba ƙaramin kuka Sarah tayi ba, don sallama suka yi mata gaba ɗaya. Pastor
Emmanuelle Deborah nan da kwana uku zata koma Nasarawa, su Nnanne kuwa jira kawai suke result ɗin
DNA ya fito su wuce amma ba Lukman zai zauna don tare zasu wuce India domin jinyar Baba. Ana idar da
sallah Khalil ya shigo gidan, kai tsaye ɗakin Hajiya ya fara isa. Yana shiga daga Hajiya, Aunty Yagana da
Aunty Yaana harara suka jefe sa dashi. Murmushi yayi don ya riga da ya san dawan garin. Zama yayi a
daidai ƙafar Hajiya tare da faɗin, "Hajiyata, ɗazu mu kayi waya da yaya Abdallah, ya faɗa min komai game
da shirye-shiryen auren. Ashe sati biyu aka saka bikin!" "Oh! Da ɗazu da nake faɗa maka ina ka ajiye
hankalin naka?" Hajiya ta faɗi tana mai ƙara tsuke fuska. "Ji nayi kamar kin ce sati Uku Hajiya." Faɗin Khalil.
"To sati biyu ne!" Hajiya ta ƙara faɗi a dake." Hannu ya kai kan hanci sannan ya ce, "Hajiya so nake na
kammala duk wani abu da zanyi anan Kaduna sai na wuce Maidugurin. So nake idan naje ba zan dawo ba
sai da amaryata. Kamar irin saura kwana huɗu bikin haka. Shiyasa ma yanzu nazo domin in ƙara jin tsare-
tsaren idan da bukatar ƙara kuɗi sai in ƙara yiwa Aunty Yagana transfer." Gaba ɗaya a tare suka washe baki,
Aunty Yaana har da kai masa duka a kafaɗa tare da faɗin, "Ja'iri! Ashe kana so kake kaiwa kasuwa." Shima
dariyar yayi yana mai kai hannu inda Aunty Yaana ta dake shi tare da faɗin, "Aunty wa zai ƙi ɗan uwansa.
Ina sonta mana!" "Allah yayi maka albarkar Khalil. Ai na ɗauka da farko dangin matsafa da arna sun lashe
min kurwan ɗa." Faɗin Hajiya tana dariyar jin daɗi. "Yauwa kana jina Khalil? Mun yi waya da Hajiya Mariya,
ta faɗa min list ɗin komai. Ka ga dangin mahaifiyar Habbooba, kowace ƴar uwarta ta kusa sai kayi masu
kaya, a talauce dai ko wacce ta samu manyan zani kamar kala bakwai-bakwai haka da takalmi ƙafa biyu da
lafaya ɗaya. Sannan dangin mahaifinta ma haka. Mahaifin Habbooba za ayi masa akwati, haka mahaifiyarta
da ƙanwarta. Mai kitson Habbooba ma dole ayi mata nata kayan, haka ƙawayenta. Sannan zaka tura kuɗin
turare miliyan biyu, sannan zaka aika masu da kuɗin suger da flour na cin-cin ɗin da za'a taho mata dashi
domin mutane." Haɗiye miyau kawai Khalil keyi yana kallon Aunty yaana. "Amma aunty Yaana Ina ce a
cikin waɗannan akwatinan da kika lissafa za'a cire na uwa dana uban?" Gyaɗa kai Aunty Yagana tayi tare da
faɗin, "Eh suna cikin wannan 48 set of boxes ɗin." "Ya zaki ce 48? Ai nace ya cika su zama 50." Faɗin Hajiya.
"Haka, na tuna." Faɗin Aunty Yagana. "To yanzu nawa kenan zan ciko?" Khalil ya faɗi. "Ƙaro 4million kawai,
ina ga zasu isa. Sai ina turawa hajiya Mariya da miliyan biyu kuɗin turaren. Kasan za ayi wushe-wushe, to a
wannan ranar ne za ayi presenting kayan ƴan uwan." Gyaɗa kai Khalil yayi, a cikin zuciyarsa kuma yana
faɗin, "Ku tsotsen tattalin arzikin ku huta. Tashin farko na tura maku almost 10million sai kace zan auri
gwal." "Allah yayi maka albarka Ibrahim. Yanzu yaushe zaka tafi Maidugurin?" "In Sha Allah, biki ya rage
saura kwana uku zan tafi." Khalil ya faɗa yana fatan kar Hajiya ta ce bata yarda ba, to his surprise sai yaji
tace, "To Allah ya kai mu da rai da lafiya." Miƙewa yayi tare da faɗin, "Sai da safe!" "Allah ya tashe mu
lafiya!" Duk suka haɗa baki suka faɗi shi kuma ya miƙe ya fita. Sai da ya biya wajen motarsa ya ɗauko ledan
daya shigo dashi sannan ya nufi side ɗinsa. Hannu ya saka ya murɗa ƙofar sannan ya shiga da sallama.
Babu kowa a parlour ɗin. Sai da ya fara shiga kitchen ya ɗauko plate da cup sannan ya kashe wutan ko ina
ya haura sama. Yana buɗe ƙofar ɗakinta ballon ya fashe fass a fuskansa, wani multicolour sparkle ya fashe
a sama ya watsu ko ina a ɗakin. Shigowa yayi gaba ɗaya tare da ajiye abinda ke hannunsa yana ƙarewa
ɗakin kallo. Gadon an lailayeshi da flowers masu kyau. A tsakiya kuma wani red-white zani ne mai shape
ɗin heart an rubuta *_I LUV YOU_* da manyan ɓaki. Bangon gadon kuma an rubuta _Happy birhrday love!
_ Ta bayansa yaji an rungumesa, dai-dai saitin kunnensa ta soma rera waƙa, *_Happy birhrday to You!
Happy birthday to you!! Happy birthday, happy birthday, happy birthday to you!!!_* Wani irin juyo da ita
yayi tare da rungume ta ya shiga kissing goshinta, kumatunta, idanunta, hancinta da kuma bakinta yana
faɗin, "Thank you, thank you, thank you. Thank you Soo much my endless bliss." Ya faɗi hakane tare da
ɗaukar ta cak ya kwantar a kan gado tare da hawa kan gadon ya cigaba da kissing ɗinta sannan ya ɗagota
ya haɗe goshinsu waje ɗaya tare faɗin, "What a surprise my lovely wife! Kin san kuwa yanda naji daɗi! I'm
very very excited wallahi. Nayi missing ɗin ki my dear wife." A kunne ta raɗa masa, "And I'm here! And do
you know what, I'll make sure duk wani lungu da saƙo da yayi missing ɗina a jikinka sai ya san na dawo
kusa da mijina." Ta ƙarisa maganar tare da raɗa masa magana a kunne. Waro idanu yayi tare da faɗin,
"Wayyo Hajiya, Sarah zata lalata maki ɗanki!" Dariya suka kwashe dashi duka a tare. "Sauko, let me feed
you. Don na san wannan cikin babu komai a cikinsa." Sai da ya tabbatar ta ƙoshi da gasasshen naman da
kuma fresh milk sannan ya mayar da komai ya ajiye ya dawo ɗakin. Sarah har ta canza kaya zuwa wasu
crazy night gown masu ɗaukar hankali. Gaba ɗaya santala-santalar cinyoyinta a waje. Wani ajiyar zuciya
Khalil ya sauke tare da kashe wutar ɗakin. Washa gari sai 11am suka farka tun komawar sallar asubah. Don
jiya kusan raba daren suka yi suna abu ɗaya. Don sai da Sarah ta gogewa Khalil haddansa tsaf har yana
mamakin ita ce kuwa. "Morning my prince!" Faɗin Sarah tana mai hura masa iskan bakinta don ta riga shi
tashi har ta haɗa breakfast duk da kuwa irin nauyin da jikinta ke yi mata. Hannunta ya fizgo ta faɗo jikinsa
gaba ɗaya tare da faɗin, "Shine kika gudu kika barni ko?" Tana kallon kyakkyawar fuskansa tace, "Bana so
ka farka babu abunda zaka ci ne, You must be hungry. Muje in baka abinci ɗan jariri na!" Waro idanu yayi
tare da faɗin, "Realy!" Sauka tayi sannan ta kama hannunsa tare da jawosa ta saƙalo hannayensa ta
kuiɓinta, shi kuma ya kwantar da kansa a kafaɗanta. A haka suka fita har parlour. A can gidan Lami kuwa, a
cikin daren su uncle John suka yi nasarar kama Pastor William tare da abokan cin mushensa suka miƙasa ga
hukuma tare da shedu sannan suka dawo da Lukman gida wanda gaba ɗaya ya gama ficewa daga
hayyacinsa don ko gane mutane bai yi. Aunty Rose Merry tana daga cikin manya-manyan mutanan dake
kawowa Pastor William ƴaƴan jama'a yana lalatawa tare da turasu ƙasar waje yana sayar dasu. Pastor
Emmanuelle Deborah Gabriel ɗaga tafiyar tayi har sai an gama Shari'a an yanke hukunci tukun. Kwana biyu
tsakani aka turasu kotu wanda hakan ya ɗan tada ƙura domin mabiyan Pastor William basu yarda da
tuhuman da ake yi masa ba, sai zanga-zanga suke yi a gari har hakan ya kusa tada faɗa tsakanin Musulmai
da Christian saboda suna ganin iyayen Lukman musulmai ne sun yi hakane domin kawai su lalatawa Pastor
suna don ba addini ɗaya suke ba. Sai da hukuma suka shiga sosai sannan ƙuran ta ɗan lafa, shima kuma
saboda hujjojin da aka riƙa bayyanarwa a kotu ne da kuma wasu mabiyansa da suka fito suma suna faɗin
abubuwan da ya aikata masu sannan kuma yayi masu warning idan wani yaji sai ya tsine masu sannan
kuma ya kashe su. Bayan sauraran ƙara da kuma hujjoji, kotu ta yankewa Pastor William da mabiyansa
hukuncin zama gidan kaso sai mutuwa ce zata raba, ma'ana _Life in prison_! Pastor Emmanuelle Deborah
har wani kwarya-kwaryan shagali ta haɗa na farin cikin cikar burinta, washa gari kuma ta haɗa ƙan
ƙannanta da kuma ƴarta Elizabeth (Lami) suka tafi Nassarawa, don cewa tayi tare zasu tafi tunda su baba
Nuhu India zasu je jinya, don haka itama tana bukatar ganawa da ƴarta. Bayan kwana shidda, Khalil ya cikin
office, nurse Raliya tawo sakamakon DNA. Gabansa harbawa kawai yake yi. Hannu ya saka ya ƙarba tare da
faɗin, "Thanks!" Sannan ya ajiye akan table. Bayan fitanta, ya ɗauki paper ɗin ya warware yan mai karanto
duk addu'ar da tazo bakinsa. Sai dai inaaaa, addu'arsa bata ƙarbu ba, domin dai gashi nan ɓaro-ɓaro ya
nuna cikin jikin Aina'u, nasa ne. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" Yayi ta maimaita har ya ɗan samu
natsuwa sannan ya ɗaga waya ya kira ya Abdallah ya shaida masa komai. Magana suka yi mai tsayi, a
ƙarshe kuma yace masa ya bari kar ya faɗawa Hajiya komai yanzu, shi da kansa zai faɗa mata amma sai
bayan biki. Tun da Khalil ya ɗaura kansa a kan desk yake kuka yana kuma faɗin Inna lillahi wa'inna ilaihir
raju'un at the same time. Ya kusan awa guda kamun ya tashi ha ɗauki key da kuma result ɗin ya fito ya nufi
gidansu Sarah. Kana kallonsa kasan bai cikin natsuwarsa. Ko da ya shiga ɗaki inda su Nnanne suke gaba
ɗaya. Tun da ya miƙa masu takardar ya ɗukar da kai yake tsiyayar hawaye masu zafi. Dafa shi ba Nura yayi
tare da soma karanto addu'a yana tofa masa. Sai da zuciyarsa yayi sanyi tukun sannan Baba Lukman yace,
"Cikin naka ne ko?" Gyaɗa masa kai Khalil yayi yana mai share hawayen da suka kwaranyo masa. Nnanne
ɗauke wuta tayi tana mai bala'in jin tausayin Khalil. "Kai kuma irin taka ƙaddarar kenan Ibrahim?" Baba
Nuhu da Khalil a tare suka fashe da kuka mai sauti, "Ni Nuhu, bazan taɓa yafewa Aina'u ba. Kowa a ɗakin
nan ya shaida, na cireta daga cikin sahun ƴaƴana, kuma in Sha Allah sai duniya ta san abunda ta aikata, sai
kowa yayi mata tofin Allah tsine. Ko a lahira ban so ganin fuskar Aina'u." Baba Nuhu na gama faɗin haka ya
shiga wani irin mugun tari yana feso aman jini. A ruɗe Khalil yayi kansa domin cetonsa. Kinkimarsa yayi
gaba ɗaya yayi mota dashi su ba Lukman suka rufa masa baya zuwa asibitin. Sai da numfashinsa ya daidaita
kuma ya daina aman jinin sannan ba Lukman ya zare jiki ya dawo gidan ya nufi ɗakin da Aina'u ke zaune ita
kaɗai cikin azaba. Kanta a ƙasa tana kuka ta soma magana, "Kowa ya tsane ni, wacce ta kawoni duniya ma
ta tsallake ni tayi tafiyarta. Kaicona! Da nayi haƙuri nabi Allah da yanzu ina cikin ƴan uwana shiryayyu. Ni
na san ni ƴar wuta ce! Ku taimakeni Baba, idan Allah yayi na haife abunda ke cikina, ko fuskata kar ku nuna
masa, kar ya sanni da tarihina har abada." Hawaye Baba ya share tare da faɗin, "Kin yi mummunar kuskure
a rayuwarki Aina'u. Kin cuci kanki! Kinyi aikata zunubi mafi muni a duniya. Kin haɗa Allah da wani, kin yi
Zina, kashe rai, kin yi kwanciyar aure da mahaifinki, wa'iyazubillah! Aina'u kaiconki!! Aina'u kin ga Zina!
Zina!! Zina bala'i ce babba.Zina wata irin dau'da ce wacce idan ta kama zuciyar 'dan Adam tana da wuyar
wankuwa.. Kuma ko da ta wanku, batta wankuwa gada daya sai kaga gurbinta yana nan. Duk zuciyar da ta
riga ta cuɗanya da Zina, ta zama zuciya mai ha'inci. Kuma ma'abocinta ba zai ta'ba zama cikakken mumini
ba. Sai dai idan ya tuba.Hakanan Mace idan ta zama Mazinaciya, babu wani Minti guda acikin rayuwarta
fache ta tanadeshi ne domin aikata zina ko kuma aikat duk abinda zai ja hankalin mazinata 'yan uwanta.
Zina mugun ciwo ne wanda yakan kashe mutum ta ciki, tun kafin ya kasheshi ta waje. Wannan yasa
Manzon Allah (saw) yace "MAI ZINA BA MUMINI BANE SHI, YAYIN DA YAKE ZINA". Awani hadisin kuma ya
lissafa _TSOHON MAZINACI_ acikin mutanen da ba zasu shiga Aljannah ba. Zina idan tayi nisa azuciyar
mutum, takan lalata mafiya yawan zuriarsa.... Koda bayan ransa sai kaga ana samun yawaitar masu koyi
dashi acikin zuriyarsa! Kun cuci kanki Aina'u! Domin Zina itace tushen duk wani mugayen abubuwan da
kika aikata a doron ƙasa!" Wani irin kuka Na'ima ta fashe dashi, don tun shigowar ba Lukman ɗin ta biyosa
a baya, kuma tun farkon maganar da yakewa Aina'u take tsaye a bayansa. Juyowa yayi ya kalleta tare da
faɗin, "Kwarai kuwa Na'ima, Zina ciwo ce babba!" "Baba kenan ƴaƴan da zamu haifa dole sai sun taho da
ɓurɓushin zina!" Faɗin Na'ima. Ajiyar zuciya Baba yayi tare da faɗin, "Allah mai kare wanda ya kare kansa
ne Na'ima. Ɓakar tukunya tana fidda warin tuno. Ba lallai bane abunda uwa ta aikata mara kyau ya samu
abunda ta haifa idan har an kiyaye dokokin Allah kuma anyi taubatan nasuha." Zama Na'ima tayi tare da
faɗin, "Ba Lukman ta yaya ko da nan gaba ne zamu iya kare kanmu da ƴaƴanmu daga aikata Zina?" Jinjina
kai ba yayi tare da faɗin, "Akwai hanyoyi guda goma sha biyu kamar haka; Babban Maganin da zai hanaka
yin Zina, shine:
1. tsayuwa abisa tafarkin Allah da gaskiya. 2. Cikakken Tsoron Allah a zuciya. Tare da kwadayin samun
Rahamarsa. 3. Kulawa da yin Sallah akan lokaci, kuma acikin Jam’I. Tare da neman ilimin sanin Sallar. 4.
Zikirin Allah safe da yamma tare da neman tsarinsa daga Sharrin Shaitan ako yaushe. 5. Tuna girman Allah
da kuma Kusancinsa gareka/gareki. Yana tare dakai/dake alokacin da kuke aikata wannan Kaba’irar.
6.Tunowa da girman azabar da Allah ya tanadar ma MAZINATA a lahira. 7. Tuno wa shaiɗan da kuma
kaidinsa da yake ƙullawa domin hallakar da ƴan Adam. 8. Gujewa kaɗaituwa da duk wata matar da ba
Muharramarka ba/ko Namijin da ba Muharraminki ba. 9. Kaucewa kalle-kallen fina-finan batsa. Ko kuma
wakoki da hotunan batsa. 10. Kaucewa abota ko ƙawance da duk wani saurayi Mazinaci ko budurwa
Mazinaciya. 11. Addu’ar neman tsari daga munanan ayyuka, da mummunan tunani. “Allahumma inni a’uzu
bika min Munkaratil Akhlaaqi wal Af’aali wal Ahwa’I.” 12. Ka tuna cewar Wannan da zaka yi zinar da ita: Ƴar
wani ce. Ƙanwar wani ce. Ɗiyar wani ce. Watarana kuma zata zama Uwar wani. To yadda kayi Zina da ita,
kaima sai anyi Zina da Uwarka, ko ƙanwarka, ko ɗiyarka, ko ‘ƴar da ka haifa. Ƴan Uwa, mu nisanci ZINA
kuma mu nisanci duk masu yinta... Domin ita ɗabi'ar takan yi naso ne. Hakika kin aikata kuskure babba.
Domin kuwa bayan shirka babu wani zunubi mafi girma awajen Allah kamar zina. Manzon Allah (saw)
yace : “MAZINATA ANA HURA MUSU WUTA NE BISA FUSKOKINSU (RANAR ALKIYAMAH KENAN)(Imam
Tabaraniy ne ya ruwaito). Sannan acikin hadisai da dama Manzon Allah (saw) ya bayyana cewar Akwai
wani ruwa mai bala’in doyi wanda ke fita ta farjojin Mazinata acikin Wuta. Wannan ruwan dashi ake yiwa
sauran ƴan Wuta Azaba. Sannan acikin wani Sahihin hadisi wanda Imamul Mundhiriy ya ruwaito acikin
Targheeb wat-Tarheeb, Manzon Allah (saw) yace: “ALLAH YANA KUSANTOWA GA BAYINSA, SAI YAYI
GAFARA GA DUK MAI NEMAN GAFARA. AMMA BANDA MATAR DAKE ZINA DA FARJINTA…. “. Ya zama wajibi
kiji tsoron Allah ki dena domin kuwa wannan laifin zai iya janyo miki bala’i da tozarta da wulakanta dake da
danginki da iyayenki tun daga nan duniya. Aranar lahira kuma Farjin naki da kike zinar dashi, da kuma
sauran gabobin jikinki sune zasu tona asirinki agaban Zatin Allah, ga dukkan halittu suna kallonki. Da fatan
Allah shi kiyayemu daga wannan mummunan aiki."

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[15/11, 5:05 PM] Matar Sayyadee: Gaba ɗaya jikinsu yayi sanyi, barin ma Na'ima da ta faɗa dogon tunanin
akan past ɗinta, domin baza ta iya tuna adadin mazan data kwanta dasu ba, wasu ma ko a hanya suka
haɗu ita dai baza ta gane su ba sai dai su wataƙila su mazan su gane ta. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!"
Na'ima ta faɗa wani ruwan dana sani yana kwaranyowa daga zuciyarta. "Aina'u shifa sharri ɗan saƙo ne,
duk wanda ka turawa sai ya dawo maka. Ko bature yashe, _Life is the principle of retribution, what you
sow is what you reap!_ kinyi mummunar kuskure a rayuwarki. Kiyi gaggawan tuba tun kan mutuwa ta riske
ki, shi ubangiji maji roƙon bayinsa ne." Girgiza kai Aina'u tayi tare da faɗin, "Ba Lukman babu wannan
buƙatar, domin shi Allah bai yafe laifin dake tsakanin bawa da bawa sai dai idan wannan bawan ne da
mutum ya cuta yayi masa gafara. Ba Lukman ƙaddara Babana, Khalil, Aunty Maryam, Mijinta da kuma
mahaifiyarsu sun yafe min, ina zanga sauran domin neman yafiyarsu? A lahira? Ba'a fafe gora ranar tafiya
ba Lukman. Na riga na bar ginina tun zane! Ni ina ji a jikina ƴar wuta ce!!" "Subhanallah!" Baba ya faɗi
yana kallonta. Jinjina kai Aina'u tayi tare da faɗin, "To mecece makomar duk wanda ya haɗa Allah da wani?
Nayi shirka, nayi zina mafi muni kuma na kashe rayuwa, sannan na fita daga addinin gaskiya na koma na
ɓata wanda kowa ya san cewa duk wanda yake yin wani addini saɓanin musulunci har ya mutu a haka ɗan
wuta ne." Riƙe hannunta ba Lukman yayi tare da faɗin, "Ba'a yanke rahamar daga Ubangiji Aina'u. Har
yanzu lokaci bai ƙure maki ba. Zaki iya yin tuba kuma in Sha Allah, zai karɓi tubanki domin shi maji roƙon
bayinsa ne." "Muminai ba!" Aina'u ta faɗi tana hawaye. "Aina'u kice La'ilaha Illallah, Muhammadur
Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallama!" Baba ya faɗi yana mai matsowa kusa da ita. Buɗe baki tayi amma
sai taji kamar an bugeta da guduma a bakin sannan bakin yayi mata wani irin bugun nauyi. Kuka ta fashe
dashi tare da faɗin, "Ba zan iya ba, Baba bazan iya ba Wallahi. Baki na nauyi yake yi duk lokacin da nayi
yunƙuri." Kuka ba Lukman ya fashe dashi tare da saurin fita daga ɗakin. A can asibiti kuwa, Khalil ya samu
nasarar ceto ran Baba, sai dai duk da haka yana cikin mawuyacin hali. Waya ya ɗaga ya kira Sarah, ringing
biyu ta ɗauki kiran tare da karawa a kunne, "Happiness!" Ta furta a hankali kamar tana yi masa busa a cikin
kunne. Lumshe idanu yayi tare da jingina da kujera ba tare da ya amsa mata ba. "Happiness, meke
faruwa?" Ta tambaya hankalinta na tashi don tana jin saukar numfashinsa. "Cikin jikin Aina'u nawa ne!"
Rintse idanu Sarah tayi tana maimaita, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un!" A zuciyarta. "Gani nan zuwa
asibitin yanzu, everything will be fine in Sha Allah!" Tana gama faɗin haka ta yanke wayar tare da haurawa
sama ta ɗauko hijjab ɗinta, su ƴan biyu dama suna ɗakin hajiya. Ɗakin hajiyan ta nufa itama domin tayi
mata sallama, knocking tayi sannan ta murɗa handle ta shiga. Suna parlour suna ta shirye-shiryen auren.
Don gidan har ya fara cika. Wasu sun yi Maiduguri, wasu kuma suna kaduna kasancewar gaba ɗaya bikin
tuwona maina ne. Su matar ya Abdallah da ya Barrister duk sun zo tare da ƴaƴansu. Har ƙasa Sarah ta kai
sannan ta soma gaida manyan. Babu yabo babu fallasa duk suka amsa, amma banda Hajiya da ta murtuke
fuska ta kawas da kai. "Hajiya zan ɗan je asibiti ne." Ba tare da hajiyan ta kalleta ba tace, "Allah ya kiyaye
hanya." Miƙewa Sarah tayi tare da faɗin, "Ameen!" Dai-dai fitowar Laure daga ɗakinta hannunta riƙe dasu
twins. Hannu su twins ɗin suka ɗaga mata tare da faɗin, "Bye-bye mummy." Itama tace masu, "Bye!"
Sannan ta fice. Da harara Hajiya ta bita tana mai faɗin, "Bita zai-zai! Asibitin sai an bi shi can." Dariya wasu
daga ciki suka kwashe dashi. Babbar jikarta ƴar wajen ya Abdullahi tace, "To ke Hajiya mai kika sani? Ai
wannan shi ake kira love!" Daƙuwa Hajiya tayi mata tare da faɗin, "Da wannan makircin love ɗin duk ake
yaudaranku, ku ƴan zamani!" Wannan karan ma dariyar duka aka sake yi. "Hajiya to be sincere, aunty
Saratu mutuniyar kirki ce. Da zaki gane, da kin haƙura da wannan tsanar da kike mata. Sarah irin surukan
nan ne da ake kira one in town, wallahi zuciyar zinari gare su. Ni ina jin wani abu game da ita a cikin jikina,
wallahi ina sonta sosai!" Throw pillow ɗin dake gefenta. Sarah na fita ta samu abun hawa kasancewar suna
kusa da bakin titi. Mintuna sha biyar ta isa _Khalilullah specialist hospital_. Sauka tayi ta biya kuɗin
adaidaitar sannan ta shiga cikin asibitin. Direct office ɗinsa ta nufa tare da knocking sannan ta murɗa
handle ta shiga. Zaune ta same sa ya cire jacket ɗin coat ɗinsa ya ɗaukar akan table shi kuma ya ɗauka
kansa akan table ɗin. A hankali ta isa garesa tare da dafa kafaɗunsa ta furta, "Shi ɗan Adam gaba ɗaya
rayuwarsa akan ƙaddara yake, shi kuma musulmi mumini sanin sa aka yi da yarda da ƙaddara mai kyau ko
akasin haka! Ba wai don mutum ya furta kalmar shahada ba shikenan baza a jarabce shi ba. Tabbas Allah
shi da kansa yace kada kuyi tunanin don kun ce kunyi imani ba zan jarabce ku ba. Kayi haƙuri Khalil kaci
wannan jarabawar da Allah ke yi maka, in Sha Allah silar shiga aljannarka ce. Ka daure ka danne ka cije,
nasan abun da zafi kuma yana da matuƙar ƙuna. Don mai ƙaramin ƙwaƙwalwa ma zai iya zaucewa. Amma
abunda nake so da kai, kayi ta maimaita Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un a duk lokacin da kaji ƙunci ko ka
tuna da Aina'u a cikin ranka. Ni nasan it will be very hard for you, but I assure you everything will be alright
by the grace of Allah. Zamu riƙe abunda Aina'u ta haifa tare, zamu yi yaƙin tare kuma muyi rainon tare. Ka
saka a cikin ranka abinda Aina'u zata haifa, zata kasance fitowa tayi kawai daga jikin Aina'u, amma kuma
nice uwata, zan shayar mana da ita, zan raine ta kuma taso bata san kowa matsayin uwa ba sai ni, I will
make sure bata san ba nice na na haifeta ba. Abunda za kayi kawai, you should try to convince Hajiya da
sauran ƴan uwanka da kuke thesame father the same mother only. Su goya maka baya kada duniya ta san
cewa Aina'u ita ce asalin mahaifiyar abunda ke cikint. Ni a wajen ƴan uwana babu matsala in Sha Allah!"
Ɗagowa yayi tare da jawota ya zaunar da ita a kan cinyarsa tare da faɗin, "I'm glad you're here for me,
Sarah! Ban san ya zanyi ba idan babu ke a cikin rayuwata. Nagode da care and support ɗinki Mine. Thank
you Soo much and I'll always love you till the day I day." Kumatunsa ta kama tare da faɗin, "Har bayan
mutuwata kan nan." Ta ƙarisa maganar tare da nuna saitin zuciyarta. "Nima haka!" Ya faɗi tare da manna
bakinsa a kan nata dai-dai lokacin da wata nurse ta murɗa ƙofar ta Shigo, da sauri ta juya tana faɗin,
"Sorry! I didn't knock" tare da saurin fita har tana karo da bango. Tsaki Khalil yayi tare da faɗin, "I'll fire her,
sam bata da natsuwa." Leɓensa taja sannan ta saki ya bada sautin ɗal sannan tayi saurin sauka daga jikinsa
tana dariya tare da faɗin, "I'm going." Miƙewa yayi tare da faɗin, "Muje ki fara ganin Baba tukun." A ruɗe
ta juyo tare da faɗin, "Mai ya same shi?" Kafaɗunta ya riƙe tare da faɗin, "Ki kwantar da hankalinki, in Sha
Allah zai samu sauƙi, na riga na kammala komai, kamun na tafi Maiduguri zasu tafi India shi da ba
Lukman." Sarah na jin kalmar Maiduguri tayi saurin juyawa zata bar office ɗin don har kumallon matan ya
motsa. Wani murmushin jin daɗi Khalil yayi, don yana son yaga irin wannan kishin nata mai tafe da aji da
kuma ƙauna. A baya ya bita har zuwa emergency inda baba Nuhu yake ciki. Ba Lukman ne tsaye, Nnanne
kuma zaune a kujera ta zuba tagumi tana kallon Baba Nuhu, Ba Nura kuwa zuciyar mata gare shi, yana
tsaye a kan Baba Nuhu yana tsiyayar da hawaye hannunsa ɗaya a cikin na baba Nuhun. Sarah kallon Baba
Nura tayi sannan ta kalli Baba Nuhu, mutum bai isa ya bambance su ba saboda tsabar kamannin da suka yi
da juna, amma tsabar rashin lafiya da kuma halin da yake ciki yanzu ya saka gaba ɗaya kamannin nasa sun
canza ta yanda a kallo ɗaya baza ka iya ganin kamamnin da suke yi da juna ba. "Baba!" Sarah ta kira
sunansa tana tsiyayar da hawaye. A hankali Baba Nuhu ya juyo yana kallonta da murmushi a fuskanta tare
da zame hannunsa dake cikin na baba Nura ya miƙa mata alamar ta taho gare shi. "Da gudu ta ƙarisa tare
da duƙewa a ƙasa ta kamo hannun nasa ta riƙe ga. Ɗayan hannun ya ɗago da kyar tare da ɗaurawa a kanta
yana faɗin, "Allah yayi maki albarka Saratu, Allah yasa ki gama da duniya lafiya. Ni dai baki yi min komai ba,
idan ma kin yi ni na yafe maki har abada. Wasiyyata a gareki shine, dan girman Allah Saratu kiyiwa mijinki
biyayya. Ɓacin raina ko a cikin kabarina shine ki ɓatawa wannan bawan Allah rai da gangan. Ya gama maki
komai a duniya Saratu. Da wani namijin ne, ba Aina'u kaɗai ba, hatta ke kanki damu danginki baza mu sha
ba don sai ya ɗaure mu. Amma bawan Allahn nan mai zuciyar zinari, maimakon ya ɗauki wani mataki, sai
ya barwa Allah kuma bai yi watsi da ke ba, ya tsaya maki ya biki har mahaifata kuma ya tsaya a kan rashin
lafiyar mahaifinki. Saratu, ko mai zai faru idan har bana cutarwa ban yarda ki juya masa baya ba. Ki zame
rumfa kuma bango majingina. Wannan shi ne wasiyyata a gareki." Ya ƙarisa maganar yana kallon Khalil.
Murmushi yayi masa tare da yafito sa da hannu. Ƙarisowa Khalil yayi tare da duƙawa kamar yanda Sarah
tayi a gaban gadon baban. Hannunsa Baba ya kama ya haɗa dana Sarah tare da faɗin, "Gata nan na barta a
hannun Allah da kuma hannunka. Ka kula da wannan marainiyar, ka ɗaurata a hanya. Idan tayi maka laifi ka
zaunar da ita ka nuna mata kuskurenta, kar kayi gaba da ita, kar ka gujeta dan Allah. Duk abunda tayi
maka, ka tsawatar mata matsayinka na wanta, ɗan uwanta, kuma jininta. Don na baka ita, ko da ace ba
aurenta kake ba Ibrahim Ni zan iya damƙa maka Saratu domin ta zauna ƙarƙashin tarbiya da kulawarka."
Jinjina kai Khalil yayi tare da faɗin, "Na amsa! Na amsa Baba da hannu biyu da kuma duka zuciyata. Zan
kula da Sarah kamar yanda zan iya kula da Aysha da Nafeesa da kuma ƴaƴan cikina. Kuma in Sha Allah zaka
warke Baba. Jibi zaku bar ƙasar nan." Girgiza kai Baba yayi tare da faɗin, "Alfarma ɗaya ɗana, don Allah
kayi haƙuri ka bar maganar barin ƙasar nan don asarar kuɗinka kawai zaka yi." Girgiza kai Khalil yayi tare da
faɗin, "Baba zaka warke in Sha Allah. Za ku je India domin a duba jikinka." Damƙe hannunsa Baba yayi tare
da faɗin, "A yanzu ina maka magane matsayin mahaifi idan har na isa! Ka janye maganar zuwa wata ƙasa
dani domin jinyata. Anan ɗin menene ba kuyi min shi? Kuna iya ƙoƙarin ku kuma ingantattun kayan aiki na
zamani, fita dani wata ƙasa a gareni waste of money ne. Dan girman Allah ku barni in cika a ƙasata." Kuka
Sarah ta fashe dashi yayin da ba Lukman ya ce, "Nuhu ya zaka ce haka? Ka bari a fita da kai ɗin wata ƙila sai
kaga an dace." Share hawaye Nnanne tayi tare da faɗin, "Ku barshi, kuyi yanda yace. Ina sha Allah a nan
ɗin ma zai samu lafiya. Ni zan zauna in cigaba da kula dashi a nan ɗin. Ina so ku koma Nasarawa, ku tafi
dasu Lukman, ku bar min Na'ima da Marfu'a kawai su riƙa tayani da ayyukan gida kamun muga abunda
Allah zai yi." Jinjina kai ba Lukman yayi tare da faɗin, "Yanda kika ce haka za ayi. Amma jinyar namiji sai
namiji Nnanne. Ni zan zauna, sai Nura ya tafi da yaran idan yaso sai daga baya ya dawo." Khalil yace, "Ina
ga har Hassana ma ta zauna idan ba wanin abun za suy ba. Don Aina'u ma zata zauna a nan asibiti under
observation har ta haihu." Rintse idanu baba Nuhu yayi don ko sunan Aina'un bai ƙaunar yaji. Sai yaji
gabansa na faɗuwa kuma babu abunda ke zuwa bakinsa sai kalaman tsinuwa. "Babu matsala, duk su zauna
ɗin. Kai Nura sai ka tafi da Lukman kawai." Faɗin Nnanne. "Nnanne har shima Lukman ɗin da naso mu fara
kaisa rehabilitation center tukun yayi koda wata uku zuwa huɗu." Khalil ya faɗi yana kallon Nnanne. "Shi
santa (Centre) ɗin na menene?" Yanda ta faɗin Centre ɗin sai da ya saka Sarah ta ɗan murmusa. "Wajen
kula da masu ta'amuli da miyagun kwayoyi ne. Idan har mutun yayi zama a wajen, to in Sha Allah idan ya
fito ko warin hayaƙin murhu ba zai so ba bare ya kai wani kayan maye baki." Faɗin Khalil. "Hala mugun
mugu suke yi?" Nnanne ta tambaya. Girgiza kai Khalil yayi tare da faɗin, "A'a! Yanda suke kula da mutum
ba lallai bane ma ya sami irin wannan kullawar a gaban iyayensa." "Kai dai yaron nan Allah Ubangijin yayi
maka albarka ya saka maka da aljanna mafifici. Allah ya Kula maka da zuri'arka kamar yadda kake kula min
da nawa zuri'ar." "Ameen Nnanne." Khalil ya faɗi. Sarah kuwa kallonsa kawai take yi tana jin wutar
ƙaunarsa na ruruwa a duk sassan jikinta tare da mugun tausayinsa. Miƙewa Sarah tayi tare da ƙarisawa
gaban Khalil ta zube guiwowinta a ƙasa tare da faɗin, "Mijina, Nagode da karanci da kuma kyautatawar da
kake min ni da iyaye da ƴan uwana. Nagode sosai and I promise you that I'll always be the best wife for
you, and the best mother for your children in Sha Allah!" Ɗagota yayi tare da faɗin, "Allah ya dafa maki
Sarah. Ni kuma ya bani ikon yi maku adalci." Murmushi tayi tare da faɗin, "Ameen." Gaba ɗaya sun burge
kowa da yake ɗakin. A ranar Khalil suka tafi can gidansu Sarah suka ɗauko Aina'u tare da su Na'ima suka
dawo nan asibiti aka bata ɗaki domin kula da lafiyarta dana abunda ke cikinta. Da daddare bayan sun gama
cin abinci, yara sun yi bacci Sarah ta kai su bedroom ɗinsu. Khalil ya kamo hannun Sarah tare da faɗin,
"Mine, ki faɗa min ƙasar da kike burin zuwa, domin ina dawowa daga Maiduguri zamu tafi honey moon, sai
munyi 3month zamu dawo." Waro idanu Sarah tayi tare da faɗin, "You must be joking! Ta yaya zan kwashi
ango in tafi honeymoon har na tsawon watanni uku? Fito fili kawai kace min za kuje honeymoon kai da
amaryarka. Well, babu matsala, ni dai kawai Umurah nake son inje ko 3weeks inyi domin in roƙarwa
Babana lafiya a gaban ka'aba. Ina da buƙatu da dama da nake son faɗawa Allah." Harara ya jefa mata tare
da tsungulin ta sannan yace, "Ki kiyayi duniya Saratu! Ana maganar hankali kina kawo na akasin haka!
Amaryo ba amarya ba." Dariya tayi tare da faɗin, "Uhmm, amarya dai ko ta buzuzu ce, zumuɗinta ake. Juya
mu gani, naga kamar kwanan nan kana fama da basir! Dole nayi maka tsome na gyara ka da kyau kar
amarya ta raina ka." Ya kai goran ruwa baki bai san sanda ya feso da ruwan bakinsa ba yana mai faɗin,
"Maimaita, mai kika ce?" Dariya ta kwashe dashi tare da yunƙurin matsawa kusa dashi amma tuni ya
cafkota tare da faɗin, "Zan tabbatar maki basir bai cinye ni ba, idan kin ga Khalil ya kyale ki yau, to ki
tabbatar amai yaga kina yi ko kuma numfashinki na ƙoƙarin barin jikinki." Hannu Sarah ta ɗaura a kai tare
da faɗin, "Na shiga uku na tono tsuliyar dodo!" Hannu ya kai ya jawo ta gaba ɗaya jikinsa tare da kashe
wutar ɗakin yayi mata runfa. "Wayyo Allah marana?" Faɗin Sarah tana kai masa tsunguli a cinya. "Ban ji ba,
ɗaga murya tukun." Khalil ya faɗi yana mai ƙara sakar mata nauyin. Bayan kwana biyu, Ba Nura ya saka
Lukman a gaba suka wuce Nassarawa bayan Khalil ya cika su da abun arziki. Shima kuma gobe zai tafi
Maiduguri don saura kwana huɗu ɗaurin aurensa. Duk wannan hidima da ake yi, ko sau ɗaya Khalil bai yi
magana da Habbooba ba, a gaban Hajiya dai yana nuna yana son auren har ma da nuna ƙosawarsa. Tsaye
yake a bakin ƙofa ya harɗe hannunsa yana kallonta sai saka sabbin kayansa take yi cikin wani ƙaramin
akwatinsa. Ajiyar zuciya ya sauke tare da faɗin, "I'm going to miss you my wife." Ba tare da ta ɗago ba tace,
"I'm going to miss you too." Zama yayi a gefenta tare da rufe akwatin ya matsar dashi gefen ya ɗaura kanta
a kan cinyarsa tare da faɗin, "Wallahi ban son wannan tafiyar. Ban ƙaunar abunda zai nisanta ni dake
Mine." Hawaye ne suka gangaro daga gurbin idanunta tayi saurin saka hannu ta goge tare da faɗin, "Tafiyar
kwana uku ce kawai. Kamar yau ne za ka ga har ka dawo!" Juyo da fuskanta yayi ya ƙurawa idanunta tare
da faɗin, "Are you crying, wife?" Girgiza kai tayi tare da faɗin, "Why will I? Ba kuka nake yi ba. Kawai dai ina
jin kewarka ne tun yanzu." Rungumeta yayi tare da faɗin, "It obvious my wife. Ko makaho ya shafi fuskanki
ya san kuka kike yi. Ki faɗa min gaskiya mai ya saka ki zubar da wannan hawayen naki masu matuƙar
tsada?" Ko kamun ya ida maganar ta fashe da kuka tare da ɗagowa ta ɓoye fuskanta akan ƙirjinsa. Shafa
bayanta ya shiga yi yana faɗin, "It's okay! I'm really sorry, Sarah. Na san kishiya bata da daɗi. Amma kin fi
kowa sanin idan nawa ra'ayin za'a bi, ke kaɗai kin isheni rayuwar zaman duniya. I always tell you, you're my
four in wife. Kamar yanda kika yi min nasiha a wancen ranar, nima yau zan yi maki kwatankwacinta! Ki
ɗauki zuwan Habbooba gidan nan matsayin matata a cikin ƙaddararki, kuma kada ki taɓa bari hakan ya
taɓa rayuwarki. Habbooba bata isa ta rainaki a cikin gidan nan ba, dole tayi respecting ɗinkin a matsayin
beloved First wife and mother of my children. Ba wai ina faɗa maki wannan maganar bane so that you
should look down on her, sam a'a. Ina faɗa maki abunda ke cikin zuciyata ne. Ke kin sani, kowa kuma ya
sani kece zaɓina kuma abun ƙaunata. Yes, ina son Habbooba sabida jinina ce kuma ƴar uwata musulma.
Amma a zahiri ke ɗin ce dai muradin zuciyata. Wallahi babu wata mace a cikin duniyar nan da zata saka in
wulaƙantaki kuma ina cikin hayyacina. Ke, amma ba na raini ba, na yi imani da Allah babu wani asiri da zai
ƙara tasiri a kaina domin na riga na ɗauki lesson tun a kan Aina'u. Azkar ba zai taɓa barin baki da ruhina ba,
haka kema ina horonki da ki riƙe Allah ki kuma riƙa ambatonsa a duk halin da kike ciki, girki ne, gyaran
gida, ke koma menene, nayi maki imani da Allah idan muka riƙe wannan, ba ɗan adam ba ko Shaiɗan da
aljani basu isa su kusanto inda muke ba. Zan ɗawo da duk wani abunda Alai ya gina a gidan nan, ai mu
mutanan Borno wajen ambaton Allah da karatun Alƙur'ani kowa ya sara mana. Saboda haka dole wannan
abu da Alai ya gina ya dawo daram acikin gidan muma mu ɗaura daga inda ya tsaya. Ki kwantar da
hankalinki matata, aure ba zai taɓa canza maki ni ba. Nasan abunda kike gudu kenan!" Rungumesa tayi
tare da faɗin, "Nagode sosai mijina. In sha Allah tun daga yanzu umarninka zai fara aiki. Bani kaɗai ba har
da ƴaƴanka sai sun horu da ambaton Allah." "Ɗan ɗaga Ni kaɗan." Ya faɗi yana ɗan karkacewa ita kuma ta
miƙe. Wayarsa ya zaro tare da yin danne-danne. Cikin mintuna biyu Sarah taji ƙarar message a wayarta.
Kasancewar wayar a kusa da ita take, sai ta miƙa hannu ta ɗauko wayar tare da shiga inbox ɗin. Wani irin
waro idanu tayi jikinta na rawa har wayar na suɓucewa a hannunta Khalil yayi saurin taro wayar. "Menene
wannan ka tura min, Happiness?" Riƙota yayi da kyau tare da faɗin, "Malama kar ki sume min mana,
Please! Baki taɓa ganin alert haka bane?" "Ta ina zan gani? Ni dai don Allah ka kwashe abunka." Sarah ta
faɗi still jikinta na rawa. "Nuna min inda nayi ɓarin sai in kwashe." Shima ya faɗi yana dariyar. Ƙara leƙowa
tayi ta kalli screen ɗin wayarta dake hannun Khalil. Still dai 10 ta gani da zero shidda wanda ke nuni da yayi
mata transfer na 10million.................

_Next page will be the final episode. You have to be little petient domin sai nan da two days zan baku shi
don gaskiya page ne mai tsayin gaske! Thank you all🥰👌_

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[19/11, 12:25 PM] Matar Sayyadee: Kallon fuskansa tayi tare da faɗin, "Happiness, 10million? It's too
much, wallahi zan iya haukacewa! Duk mai zan yi da wannan uban kuɗin?" Zama yayi tare da faɗin, "Ok,
idan shawara kike buƙata to ga wata. Wannan kuɗin kiyi amfani dashi ki soma wata sana'a da zaki riƙa
juyawa haka. Kin ga kina da iyaye da ƴan uwa wanda zasu iya buƙatar taimakonki, idan kika yi amfani da
kuɗin wajen yin sana'a zai amfane ki wataƙila har dani wata rana. Misali yanzu Allah ya dafa maki kika
soma kama wasu billions haka nan gaba, ko ranta nayi na biya ki daga baya ai na ƙaru dake." Ya ƙarisa
maganar yana yi mata gwalo. Tsungulinsa tayi a damtsensa still tana mamakin yawan kuɗin. "Maganar
gaskiya, ki naimi shawarar ƴan uwanki, duk abunda suka ce sai ki zauna kiyi nazari a kanki, but for me I'm
suggesting ki fara harkar kiwo." Kama hannunsa tayi tare da faɗin, "Wallahi abunda nake faɗi a zuciyata
kenan, ina son layers domin su riƙa min kwai, da raguna idan so samu ne har da shanu. Infact gidan gona
kawai zan buɗe." Hannu ya bata su kai shaking tare da faɗin, "An gama. Zan ara maki filina da yake
Kinkinau, flot biyu ne a wajen an zagaye shi da katanga kuma an saka gate. Idan na dawo daga Maiduguri
sai muyi shirye-shiryen komai tare." Rungume shi tayi tare da faɗin, "Nagode mijina! Allah ya ƙara nisan
kwana da buɗi. Yau kam akwai gagarumar tukuici." Da sauri ya soma cire agogon hannunsa tare da faɗin,
"Haba dai masoyiyata! Kice inje in ƙara watsa ruwan ɗumi in ƙara jin ƙarfi a jikina." Dariya tayi tare da
faɗin, "Bari na taho mu watsa muji ƙarfin tare." Washa gari jirgin ƙarfe biyu Khalil zai bi. Ya gama shiri tsaf
amma sai narkewa Sarah yake yi kamar ba zai tafi ba. Agogonsa ta ɗauka ta ɗaura masa a hannu tare da
faɗin, "You're going to miss your flight fa idan kana wannan narkewar!" Riƙo waist ɗinta yayi tare da faɗin,
"Ni dama zan yi missing flight ɗin kowa ya huta wallahi." "Aiko bazan bari haka ta faru ba kam!" Sarah ta
faɗi tana ɗan dariya ƙasa-ƙasa. "Wannan dariyar ta mecece?" Khalil ya faɗi yana zan kumatunta. Gashin
kansa ta shafa tare da faɗin, "Kayi kyau sosai. Zan yi missing ɗinka da wannan ƙamshin naka." Zama yayi
akan kujeran mirror tare da kama hannunta yana kallonta. Sanye take cikin atamfa straight gown wanda
yasha stones tun daga sama har ƙasa sai walwali suke. Ta buga ɗaurin nan da yake bala'in so ta Kuma ɗan
turo shi gaban goshi kaɗan, ta ƙeyanta kana hango gashinta da tayi masa kamu bakwai da ribbons. Hannu
ya kai ya shafi fuskanta tare da faɗin, "You look very beautiful my wife. Kamar ba kece kike haifi su twins
ba." Kamun tayi magana wayarsa ta hau ruri, hannu ya kai aljihu ya ciro wayar tare da amsa kiran ya ƙara a
kunne. "Wai Mu'azzam baka kallon lokaci ne? Ga Aysha nan har ta kammala shiri tuntuni kai kawai take
jira." Faɗin Hajiya. "Na gama shiryawa Hajiya, gani nan zuwa yanzu." Ya faɗi tare da yanke wayar ya miƙe
tsaye. "Amma dai zaki min rakiya zuwa airport ko?" "Of course!" Sarah ta faɗi tana mai ɗaukar hijjab a kan
gado da ta fito dashi tuntuni ta saka sannan taja troley ɗin tayi gaba shi kuma ya bita a baya suka fice daga
ɗakin. Part ɗin Hajiya suka nufa, danƙam yake da mutanan Hajiya da ƴan uwa da suka zo ayi hidimar biki
dasu. "Ango! Ango!! Ango!!" Abokan wasan Khalil mata na wajen dangin babansa suka shiga faɗi suna
zaulayarsa. Ba tare da ya biye masu ba ya shige ciki domin zuwa ɗakin Hajiya. "Yauwa gashi nan ma ya
shigo." Faɗin Aunty Yagana tana nuna Khalil ɗin. "Khalil, kuɗin nan fa basu ishe iyayen Habbooba yin
hidimarsu ba. Kasan dai gobe in Allah ya yarda za ayi wushe-wushe ko?" Fadin Aunty Yaana. "Wai har
yanzu ba'a daina wannan bidi'ar ba dama?" Daƙuwa Aunty Yagana da aunty Yaana suka yi masa tare da
faɗin, "Ungo nan! Lokacin aurenka da jikar Samuel da Deborah, Ina ce har dinner kuka yi? Don bazan
manta ba matan zumunta haka suka dunga sakin maganganu da haukansu irin tasu ta ƴan coci. Shine har
kake da bakin zagin al'adarmu ta kakanni! To wallahi baka isa ba." "Yi hakuri auntyyyyyy! Ba haka nake nufi
ba. Waneni in soki al'ada? Yanzu nawa ake da buƙata in tura?" Ajiyar zuciya Hajiya ta sauke don da har ta
hau sama, Aunty Yagana kuma tace, "Ai yanzu maganar tura kuɗi ya ƙare tunda Maiduguri zaka tafi. Dama
wai in faɗa maka ne ka tafi cikin shiri don za'a buƙaci kuɗi a wajenka." Murmushi yayi tare da faɗin, "Khalil
ɗan tattalin arzikin naka sai ya ƙare." A cikin zuciyarsa. Amma a zahiri sai cewa yayi, ".Ba matsala Aunty.
Hajiya, mu zamu wuce kada muyi missing Flight. Ayi mana addu'a." Gaba ɗaya suka haɗa baki suka ce,
"Allah ya kai ku lafiya, ya sa ayi a Sa'a." Da "Ameen" ya amsa tare da fita daga ɗakin. Ƴan parlour ma yayi
masu sallama ya fita suna masa tsiya. A wajen mota ya samu Aysha da Sarah Suna jiransa, buɗe boat yayi
duk suka ajiye troley ɗin da yake hannunsa sannan Aysha ta rufe boat ɗin ta buɗe gidan baya ta shiga don
Sarah har ta shiga mazaunin gaba. Key Khalil yayi wa motar suka bar gidan. Suna isa airport, saura mintuna
goma sha biyu jirginsu ya ɗaga. Aysha har ta ɗauki jakarta tayi gaba. Hannun Sarah Khalilullah yayi kamo
tana kallonta tare da faɗin, "I'm going to miss you my dear wife." "Same to me here!" Sarah ta faɗi tana
narke fuska. "Haɗa goshinsa yayi da nata tare da faɗin, "ki kula min da kanki kamun na dawo, kin ji?"
Gyaɗa kai tayi shi kuma yayi mata kiss a kumatu da hannunta sannan ya saki hannun nata tare da faɗin,
"Sai na kira ki idan na isa." Ɗaga masa hannu tayi tare da faɗin, "Allah ya tsare ya kiyaye hanya, ango!"
Yatsa ya nuna ta dashi yana mata gargaɗi lokaci guda kuma yana murmushi tare da tafiya da baya da baya.
Matsawa tayi baya, troley ɗin kayansa ya bayyana. Cak ya tsaya ya kallonta tare da faɗin, "It is obvious yau
zan rasa Flight ɗina duk da gani a airport." "Ba zan bari haka ya faru ba." Ta faɗi tare da isa inda yake ta
miƙa masa troley ɗin. Hannunta ya cafko tare da matso da ita jikinsa sosai. Da sauri ta kalli gefe da gefe
tare da faɗin, "People are watching!" "And so fucking what!" Ya faɗi yana mai kaiwa kuncinta kiss. "Zaka
fara amfani da bad language ɗin naka ko?" Jan kumatunta yayi tare da faɗin, "Sai ma na dawo tukun!" Ya
faɗi tare da ɗaukar troley ɗin yana mata waving. Da ƙarfi ya ɗaga murya tare da faɗin, "I love Soo much,
wifey!" Gaba ɗaya mutane dake wajen suka dawo da idanunsu akan Khalil da kuma Sarah. Itama Sarah
ɗaga hannun tayi tare da faɗin, "I love you too, happiness. Safe journey!" "Drive safely dear." Ya kuma
faɗin still yana tafiya da baya-baya. "In Sha Allah." Ta faɗi tana dariya. Sarah bata bar airport ɗin nan ba har
sai da jirginsu ya ɗaga sannan ta koma mota cike da kewan mijinta zuwa gida. 1hour 22minute suka sauka
Maiduguri International Airport. Ko da suka isa, mota na nan na jiransu tun kamun su sauka. Daga nan
airport ɗin 40minute ya kawo su _Waziri Road_. A ƙofar gate driver yayi horn mai gadi ya wangale ƙofa
suka shigo. Gidan cike yake da mutane sai zirga-zirga ake yi kasancewar gobe za suyi wushe-wushe. Wani
kyakkyawan saurayi ne ya nufo wajen motar yana murmushi tare da kai hannu ya buɗe gidan gaba inda
Khalil yake zaune tare da, "Marhaban ya akhie!" Dai dai lokacin da Khalil ɗin ya fito daga motar shi kuma
saurayin nan ya rungumesa tare da kama hannunsa zuwa cikin gidan ta baya. A hanya suka haɗu da
autarsu Habbooba, baki ta saki tana kallon Khalil tare da soma yin magana cikin sauri da yaren shuwa.
Murmushi Khalil yayi don sarai yaji abunda tace don cewa tayi, "Yaya Waheed, wannan kyakkyawan shine
mijin Habbooba? Gaskiya ta dace miji." Gyaɗa mata kai yayi tare da faɗin, "Ki faɗawa Habbooba ta kawo
masa abinci a ɗakina kamun baƙi su ragu ya shigo ya gaida Ummee." Gyaɗa kai tayi tare da kallon Khalil
tace, "Marhaban!" Shima hakan yace mata babu yabo babu fallasa sannan suka wuce ɗakin Waheed ɗin.
Da gudu Layla ta kwasa tayi ɗakin da Habbooba da Ƙawayenta suke ciki tare da faɗin, "Habbooba kin ga
mijinki kuwa? Wallahi kinyi Sa'a. Kyakkyawa sosai ɗan gayu. Kici kwalliya ki baza turare ki tafi ɗakin Akhie
Waheed ki kai masa abinci. Ɗan ɗago idanu tayi ta harari Layla tare da mayar da idanunta kan ja da baƙin
lalle da ta wanko yanzu ana shafa mata turaren lallan a ƙafa da hannu. Habbooba irin matan nan ne masu
nuna isa da taƙama ga kuma matuƙar kishi, sam bata ƙaunar raini ko daga uban wanene, shiyasa ma yanzu
da Layla ta kawo mata zancen zuwan Khalil bata wani nuna zumuɗi ba saboda kada ƙawayenta dake cike a
ɗakin su rainata ko kuma su fahimci babu wani doguwar soyayya ko shaƙuwa tsakaninta da Khalil ɗin.
"Habboo....." "Ke dallah fita!" Ta daka mata tsawa tare da nuna mata waje duk da kuma can ƙasan
zuciyarta tana son ganin Khalil ɗin. Bayan fitar Laylan, ɗaga daga cikin ƙawayen Habbooba ta miƙe tare da
buɗe wardrobe ɗin Habbooba ta ɗauko mata wani faransa kaya, doguwar riga ce har ƙasa wacce taji wani
irin rantsantsane ɗinki irin nasu na Shuwa Arab sai mayafinsa. "Booba, tashi za kiyi na ƙara gyara maki
fuskanki. Ke Anni miƙo min wannan kwalbar turaren na kusa dake." Ta ƙarisa maganar tana mai nunawa
ɗaya ƙasar turaran dake kusa da ita. Wani irin taɓe baki Habbooba tayi tare da kau da kai. "Malama ajiye
wannan girman kan da jan ajin za kiyi a gefe kije ku gana." Habbooba bata kalleta ba ma balle ta bata
amsa. Bayan Amina ta gama shafa mata turaren lallen, sai wannan ƙawar tata ta ƙarisa kusa da ita ta soma
gyara mata fuska. Cikin mintuna biyar fuskan nan ya ƙara wani irin kyau. Gashin kanta ta warware mata
wanda ya sauka har tsakiyar bayanta ta kuma taje mata shi sannan ta kama mata tare ɗaura mata
kwalliyarsu ta goshi da kuma ƙafa sannan ta miƙa mata doguran rigar tare da faɗin, "Don Allah ki shiga ki
saka ki fito." A yangance ta karɓi rigar sannan ta shiga ɗaya ɗakin ta kullo ƙofar. Hannu ta saka a ƙirjinta
dake bugawa da sauri ta dafe tana mai jin matsananciyar farin ciki, don da har ta cire rai zai zo. Rigar ta
saka daya hau jikinta yayi mata wani irin kyau. Kallon kanta ta riƙa yi a madubi tana jujjuyawa. Ta ɗan jima
a ɗakin kamun ta fito. Gaba suka ce "Wow!" Gaba ɗayasu turare suka dunga fesa mata masu ƙamshi banda
wanda aka dunga turare mata jiki dashi don hatta ruwan wankanta turare ne. Amina kuma tayi saurin
ɗaukar mayafin tare da yafa mata sannan ta ɗauke ta hoto. Daidai nan Akhie Majeed ya shigo tare da
faɗin, "Habbooba kina hauka ne? Mijinki na can na jiran ki a ɗakina fa. He must be hungry!" Ba tare da
tace komai ba ta gitta shi ta fita daga ɗakin ta nufi kitchen ɗinsu. Kiciɓis suka yi da Ajiddeh, "Yauwa maza
kitchen ki haɗa min abinci, mijina yazo. Ki tabbatar kin wanke hannunki kamun serving mijina, sannan
ɗakin Akhie Majeed zaki kawo abuncin." Kai a ƙasa Ajiddeh tace, "To Aunty Habbooba." Tsaki Habbooba
tayi tare juyawa ta soma tafiya majestically ta nufi ɗakin Akhie Majeed. Sai da tayi knocking sannan ta
murɗa handle ɗin. Tun daga buɗe ƙofar wani baƙon fitinanniyar ƙamshi ya daki hancinsa da ya saka ya
ɗago daka danna wayar da yake yi ya zubawa ƙofar idanu. Sai da aka ɗauki wasu daƙiƙu kamun Habbooba
ta ziro fara tas ɗin ƙafarta wanda yasha lallan da ya ƙara fito da asalin kyawun ƙarar sannan sauran gangan
jikinta ya shigo ɗakin. Kau da kai Khalil yayi daga kallonta ya mayar kan wayar tasa, kuma dama number ɗin
Sarah yake ta kira amma bata shiga. Samun waje tayi ta zauna akan ɗaya daga cikin kujerun ɗakin. Shuru
ɗakin ya ɗauka, ita tana jin girman kanta da jiƙimarta ba zai iya bari ta fara yi masa magana ba, shi kuma
yana jin ba zai iya mata magana ba tunda bata iya sallama da gaisuwa ba. Kusan mintuna biyar babu
wanda yayi tari a cikinsu. Knocking Ajiddeh tayi tare da yin Sallama, Khalil ne ya amsa tare da bata izinin
shigowa. Har ƙasa ta gaida shi ba tare da ta kalli fuskansa ba sannan ta ajiye tire ɗin data ɗauko ta fita da
sauri. Habbooba kallon tire ɗin tayi sannan ta kalli Khalil ɗin tare da faɗin, "Bismillah, ga abinci kaci!" Ba
tare da ya ɗaga idanu ya kalleta ba yace, "Sai da matata ta cika min ciki kamun na taho nan. Ki kwashe
abincinki!" Wani duka ƙirjinta yayi tare da jin wani irin matsanaicin kishi da tashin hankali. Bata iya cewa
komai ba, kuma bata tashi ta fita ba. Ajiye wayarsa yayi a gefe tare da kallonta karo na biyu na kusan
second biyar sannan yace, "Indeed she's very beautiful lady, sai dai babu tarbiya. Kwakwalwar cushe take
da girman kai da jiƙima!" A cikin zuciyarsa. Miƙewa tayi ta soma tafiya a hankali, har ta kai ƙofa sai yayi
tunanin yanzu haka tana iya fita ta kira Hajiya a waya, shi kuma ba tashin hankali yake so a wannan yanayin
ba. "Muhibba!" Ya kira sunan. A karo na biyu ta kuma jim wani malulu ya tsaya mata a maƙoshi jin ko
sunanta bai iya kira da kyau ba. "Habbooba!" Ta faɗi a fusace bayan ta zuba masa kyawawan idanunta.
Murmushi yayi don ya fahimci abun yayi mata ciwo. "I'm Sorry!" Ya furta yana mai taɓa hanci wani dariyar
na son kufce masa. "Dawo ki zauna amaryata muyi magana!" Ya faɗi yana mai nuna mata kujerar kusa
dashi. Sai da ta kalli kujeran sannan a hankali ta taka ta isa wajen ta zauna tana cika tana batsewa. "Nifa ya
kamata nayi fushi ba ke ba." Da gefen idanu ta kallesa tare da faɗin, "Oh, haka ma zaka ce?" Gyara zama
yayi tare da faɗin, "Kin shigo babu ko sallama bare kuma gaisuwa, bayan ni ɗin babban baƙonki ne."
"Hakan ne ya saka ka faɗa min magana!" Ta faɗi tana wasa da jelar gashinta daya leƙo ta ciki gyalenta. "Da
nace maki me?" Kau da kai tayi don ko a mafarki bata som tunawa yana da mata. Murmushi ya ƙara yi tare
da faɗin, "To ya kike, ya kuma shirye-shiryen baki?" "Alhamdulillah!" Ta faɗi tana kallonsa ta gefen idanu.
"Kiyi haƙuri, naso nazo tuntuni mu tattauna amma hakan bai samu ba sai yanzu." Kallonsa tayi kai tsaye
tare da faɗin, "Kuma baka da waya ko? Ko sau ɗaya ka kira ni ne?" Girgiza kai Khalil yayi tare da faɗin, "Na
amince nayi laifi, amma ayi min afuwa, kin ji amaryata?" Murmushi tayi tare da faɗin, "Na haƙura, amma
sai kaci abinci." Saukowa yayi daga kan gadon tare da faɗin, "An gama my dear." My dear ɗin da yace mata
yasa taji kanta ya ƙara ƙato. Tana kallonsa yayi serving kansa ba tare da ta sauko ba. Sinasir ne da miyan
taushe da yaji namomi, sai farfesun naman kai da kuma dambun nama. Sinasir ɗin ya saka pieces uku, sai
ya saka miya da nama ya rufe tukunyar. Sai a wannan lokacin ta sauko tare matso masa da wani bowl ɗin
da zai wanke hannunsa tare da rufa, "Thanks!" Yace mata sannan ya soma wanke hannun nasa ita kuma
tana tsiyaya masa ruwan. Duka ya cinye sinasir ɗin nan guda uku, duk da dama ƙanana ne mara nauyi ko
kaɗan, naman ne yaci guda biyu kawai ya wanke hannunsa tare da goge baki da tissue ya matsar da tire
ɗin gefe. "Thanks again, amaryata." Ya faɗi yana mata murmushi. "You're welcome!" Ta faɗi tana wani
farrrrr da idanu daidai lokacin da wayarta yayi ƙara. Kallon wayar tayi, ganin mahaifiyarta ke kiranta sai tayi
picking tare da karawa a kunne, cikin harshen shuwa ta soma faɗin, "Eh, gashi nan yanzu ya gama cin
abinci. Yanzu zan kawo shin?" Tana gama faɗin haka ta yanke wayar tare da kallonsa tace, "Muje ciki ku
gaisa da Ummee da ƴan uwanta." Gyaɗa mata kai yayi tare da faɗin, "Ok ban few minutes na canza kaya
sai ina fito." "Ok." Shine abunda tace tare da ƙara gyara zama akan kujeran. Ɗan kallonta yayi sai kuma ya
miƙe ya shige bedroom inda Akhie Majeed ya ajiye masa akwatin kayansa tare da rufo ƙofar. Tana nan a
parlourn har ya canza kaya ya fito. Wata skyblue yadi ya saka irin mai taushin nan kuma transparent don
hatta vest ɗin da ya saka a ciki ana iya hangowa. Ba ƙaramin kyau ya ƙara yi ba sosai. Miƙewa tayi tana
murmushi tare da faɗin, "kayi kyau!" "Har na kai ki?" Ya faɗi yana kallonta. Matsawa tayi inda yake tare da
miƙa masa wayarta bayar ta cire code, "Ka fini tsayi, kayi mana pictures." Karɓa yayi tare da yi masu hoton
yana kallonta itama tana kallonsa. With his surprise kawai yaji ta kwanto a ƙirjinsa har da lumshe idanu, shi
kuma ya ɗauke su hoton a haka. Haka suka yi ta yin style yana ɗaukarsu. Sun ɓata lokaci wajen ɗaukar
hoton kamun suka fita domin zuwa side ɗin Ummee mahaifiyarta. Kasancewar gaba ɗaya babu bare a ciki
don duk dangi ɗaya ne. Don mahaifiyar Habbooba da mahaifiyar Khalil, uwa ɗaya suke uba kowa da nasa.
Yana shiga ɗakin yaji kansa na neman juyawa saboda wani irin mahaukaciyar guɗa da gaba ɗaya ƴan ɗakin
suka saki sannan suka hau yi masu wanka da turare. Aysha ƙanwarsa da kuma yayyin Hajiya da suke uwa
ɗaya uba ɗaya da kuma ƴan wa da ƴan ƙani suka hau yi masu liƙi kamar kuɗi suyi kuka don both familyn
uwa da uba akwai dukiyar. A ranar dai Khalil sai da jikinsa yayi tsammi tsabar yanda aka yi ta jansa kamar
igiya. Shine can gaida dangi, can gaida dangin baban Habbooba kuma kuɗin jikinsa sun yi kuka. Bashi ya
samu sukunin yin waya da annurin ransa bai can wajajen goma na dare. Ringing ɗaya, biyu tayi picking tare
da faɗin, "Happiness!" Cike da wani irin salo mai tafe da shagwaɓa ta kirasa. "Na'am, Mine!" Ya amsa yana
mai sakin miƙa don gaba ɗaya muryanta ya kashe masa jiki. "Tun da rana nake ta kallon wayata ina jiran
kiranka. Da naji ringing nake zuwa da gudu amma sai inga ba kai bane." Miƙa ya kuma yi tare da faɗin, "I'm
so sorry, wife! Wallahi mutane suka cika inda nake, gashi kuma daga can, sai inyi can ina gaido da dangi tun
da na sauka wallahi. Shiyasa ban samu sararin kiranki ba, amma kina cikin zuciyarta." Ajiyar zuciya ta sauke
tare da faɗin, "To ya mutanan Maidugurin da kuma shirye-shiryen biki?" "Alhamdulillah. Ina twins ɗina?"
"Gasu nan suna bacci kusa dani, sunyi kewarka sosai." Ta faɗi tana kallon fuskansu. "Nima nayi kewarku
sosai. Duk ba daɗi nake jina saboda bana tare daku. Amma ai in sha Allah, jibi ina nan dawowa." "To ya
ƙanwar tawa?" Sarah ta faɗi. "Bari idan mun gama waya zan tura maki number ɗinta sai ki tambayeta da
kanki, Ni yanzu kira nayi domin inyi hira da matata inji daɗi ko na samu nayi bacci mai daɗi." Dariya Sarah
tayi tare da faɗin, "To shikenan naji." Daga nan suka tsunduma kogin soyayya, basu suka kammala waya ba,
sai pass 12am. Washa gari da sassafe Hajiya ta kira Khalil a waya, don itama ma sau ɗaya suka yi waya jiya
lokacin da ya haɗa su magana da wata tsohuwa. Katse kiran yayi sannan ya kirata, bugu ɗaya ta amsa kiran
tare da faɗin, "Assalamu alaikum." Khalil ya amsa tare da faɗin, "Hajiya ina kwana, an tashi lafiya?" Amsa
ta bashi da, "Lafiya ƙalau. Na kira ka ne domin in tambayeka ina zaka saka Habbooba? Domin yanzu
maganar da nake maka bamu jima da gama waya da mahaifiyarta ba, ƴan kawo kaya suna hanya tun
asuba." Ɗan shuru Khalil yayi don har ga Allah ya manta da maganar wajen zama. "Hajiya zata zauna ne a
nan ɓangarenki a sashena kamun na ayi mata nata ginin a filin gaban sashen ya Abdul-Hakeem." Wani
mahaukacin harara Hajiya ta jefi wayar dashi kamar Khalil ɗin take gani tare da faɗin, "To ubanka yayi
kaɗan! Nike auranta da zata zauna min a sashe? To saurareni da kyau, ka kira matarka ta kira ƴan uwanta
suzo su kwashe kayanta na parlourn ƙasa kaf da bedrooms ɗin, nan Habbooba zata zauna. Idan yaso idan
ka gama ginin sai ta dawo. Wannan shine hukuncina." Da sauri Khalil yace, "Hajiya dan gir......" Katse shi
tayi tare da faɗin, "Wallahi, tallahi yanda nace haka za'a yi. Zan iya ara maku guest room ɗin Alai domin ku
saka kayan a can. "To shikenan Hajiya." Khalil ya faɗi a sanyaye yana jin ba daɗi a cikin zuciyarsa. Dakyar ya
iya samun kwarin guiwar kiran Sarah a waya, kai tsaye bai tunkareta da maganar ba har sai da ya gama
kashe ta da maganganun soyayya da kwantar da hankali sannan yace, "Mine, don Allah ina neman wata
alfarma a gare ki!" Zama Sarah tayi kasancewar da a kwance take tare da faɗin, "Faɗi maganarka kai tsaye,
ko kuma ince maka umarninka. Babu wata alfarma tsakanina da kai sai umarni." A hankali Khalil yace,
"Nagode sosai Allah yayi maki albarka ya saka da alkhairi." Sai kuma yayi shuru na wasu sakonni kamun
yace, "Don Allah dama aron ɗakunanki na ƙasa nake so, zan ɗa ajiye yarinyar nan ne kamun na yi mata
nata, in Sha Allah ba zata wuce 3months a wajen ba." Wani murmushi Sarah ta saki tare da faɗin, "Dama
wannan maganar ce ka kasa faɗin ta kai tsaye? Babu komai Happiness, tazo muyi ta zama tare, fatana dai
Allah ya bamu zaman lafiya ya kau da shaiɗan da fitina. Yanzu zan kira su Na'ima suzo su tayani kwashe
kayan." Ɗif Khalil ya ɗauke wuta yana mai jin wani irin ƙima da darajar Sarah na ƙara ninkuwa a cikin
zuciyarsa. "Sarah idan har ni zan ɗaga maki ƙafa ki shiga aljanna, wallahi na ɗageta har abada. Ƙofofin
alkhairi da lada suyi ta zuwa gareki. Aljanna ita ce sakamakon abunda kike min, Sarah. Bakina ba zai iya
misalta yanda nake jinki a zuciyata ba. Ke na mallaka maki ni gaba ɗaya. Kiyi yanda kika ga dama dani!"
Dariya Sarah tayi tare da faɗin, "Idan har ba zan iya yi maka biyayya ba, to ban ga amfanina a wannan
duniyar ba. Idan za kayi min magana mijina, kayi shi kanka tsaye cike da umarni, Ni ɗin mai biyayya ga
maganarka ce idan har bai saɓawa mahalicci ba." "Ina sonki Sarah, Ina ƙaunarki sosai." Khalil ya faɗi yana
jin kamar ya fashe da kuka. Bayan sun gama waya da Khalil, sai ta kira su Na'ima da Hassana kawai domin
su taya ta kwashe kayan. Sai dai bayan kamar mintuna talatin ta fito domin zuwa sashin Hajiya ayi aiki tare
da ita, sai ta taras da maza huɗu cikin jeans baƙi da Orange ɗin t-shirt mai rubuce da sunan Companyn da
suke aiki a jiki. "Ina kwana Madam? Oga ne ya kira ya turo mu mu zo mu kwashe kaya zuwa wani ɗakin a
cikin gidan nan." Murmushi tayi tare da faɗin, "Babu matsala, ku ban mintuna biyu ina zuwa." Ta faɗi
hakan tare da komawa ciki ta kira su Na'ima tace suyi zamansu ba sai sun zo, su bari gobe sa zo biki Khalil
ya riga ya turo masu kwashe kayan. Bayan ta katse kiran, sai ta kira Khalil. Katse kiran yayi sannan ya kirata.
Bugu ɗaya ta ɗaga tare da faɗin, "Happiness, naga ka turo masu kwashe kayan ma." Daga can yake, "Ke
dasu Na'ima baza ku taɓa iya kwashe kayan ba shiyasa na kira Company kawai. Kije wajen Hajiya zata baki
makullin guest room ɗin Alai. Acan zaku saka kayan. Ki kular min da kanki kin ji?" Gyaɗa kai tayi kamar
yana kallonta tare da faɗin, "In Sha Allah!" Sannan ta kashe wayar tare da fitowa tayi can side ɗin Hajiya.
Sai soye-soyen kaji da ƙatuwar san da aka yanka da raguna huɗu suke yi. Bayan ta gaishe su da aiki sannan
ta nufi ɗakin Hajiya. Ita da ƴan uwanta su Aunty Yagana da kuma wasu daga Maiduguri ne a ɗakin sai hira
suke suna dariya. Har ƙasa Sarah ta gaishe su sannan tayi wa Hajiya maganar ɗan mukullin sashen Alai.
Miƙo mata makullin tayi tare da faɗin, "Ki tabbatar an share komai!" "In Sha Allah!" Sarah ta faɗi tare da
ficewa daga ɗakin. Aunty Yaana da Aunty Falmata suka kalli juna. Aunty Falmata tace, "Haba ya Bilki! Ni
sam ban sanki da wannan halin ba. Ki sassautawa yarinyar nan wallahi yarinya ce mai hankali da natsuwa.
A wannan zamanin da muke ciki ka samu suruka mai haƙuri da biyayya irin matar Khalil ai wallahi sai dai
godiyar ubangiji. Ke da kanki kamun shaiɗaniyar ƙanwarta ta lalata komai, kin sha kiran mu a waya kina
shaida mata Khalil yayi sa'ar mata. Ta ɗauke ki tamkar mahaifiyarta. Kirki manta, laifin wani bai taɓa shafar
wani. Kiyi haƙuri ki bar abunda ya wuce kar wata rana kiji kunya. Yarinyar nan bata yi maki komai ba,
ƙanwarta ce tayi maki laifi kuma kin san cewar babu hannunta a ciki don itama kanta ba kyaleta tayi ba."
Taɓe baki Hajiya tayi tare da faɗin, "Uhm! Baku san yanda nake jin ciwo a raina bane. Aina'u ta saka gaba
ɗaya ban ganin alkhairan yarinyar nan, ta saka ta fita daga raina. Ni kaina wani lokacin ina jin kamar in
tausaya mata in bar komai ya wuce, amma idan na tuna kisan wulaƙancin da Aina'u tayiwa Nafeesa da
mijinta da kuma jariyarsu ta kuma raba ni da ƴaƴana na shekaru biyu sai inji duk na tsani zuri'arsu gaba
ɗaya." Aunty Yaana tace, "Hajiya, haƙuri za kiyi an riga da an zama ɗaya tunda har kina da jikoki daga
gareta. Kun riga kun cakuɗu har abada." Shuru Hajiya tayi bata kuma cewa komai ba. A can Maiduguri
kuwa, tun safe aka kafa tantuna a harabar gidan nasu aka shimfiɗa kilisai na alfarma aka ajiye kujera na
gani na faɗa, irin kujerun nan masu taushi. Gaba ɗaya an zagaye wurin da kwalliyoyin zamani tare dana
al'adun shuwa'arab ɗin,
cikin kujerun kuwa a tsakiyar kujerun akwai na ango da amarya wanda sunayen su ke rubuce a kansu sai
na ƙawayen amarya da abokan ago suma duk sunayen su na rubuce akan kujerun nasu. Gaba ɗaya filin ta
kowani kusurwa har cikin flowers kaskon turaren wutane wanda ke ci yana fitar da hayaƙin mashahurin
ƙamshi mai sanyaya zuciyar mai shaƙa. Tun da aka haifi Khalil sau ɗaya ya taɓa ganin wannan bikin al'adar.
Akhie Majeed ne ya shigo ɗakin tare da faɗin, "Akhie sun iso tun ɗazu. Yanzu zan je in ɗauko su a hotel ɗin
da suka sauka." Da mamaki Khalil ke kallon Majeed tare da faɗin, "Su waye kenan." Shafa kai Majeed ɗin
yayi tare da faɗin, "Sorry, na manta in faɗa maka na kira abonka na Kaduna, yanzu haka suna hotel domin
bikin da za ayi yanzu dole muna buƙatansu. Hannu Khalil ya ɗaura akan goshi tare da faɗin, "Inna lillahi! Ni
fa ban taɓa basu labarin zan ƙara aure ba." Dariya Majeed yayi tare da faɗin, "Ai suma sun yi ƙorafin hakan,
amma sun ce halinka ne don ko na farkon ma baka faɗa masu ba. Kuma kasan wanene ya kira su?
Abutturab!" Waro idanu Khalil yayi tare da faɗin, "Inna lillahi! Gaskiya ka kashe ni Majeed. Yau she rabon
ko waya muyi dashi." "Ai suna can gaba ɗaya jiranka kawai suke." Faɗin Majeed. "Muje! Muje!! Muje!!!"
Khalil ya faɗi yana tura Majeed ɗin gaba. Shi ya fara tura ƙofar ɗakin da suke ciki a hankali ya turo kansa.
Kwam yaji an jehosa da takalmi a tsakiyar kai. Da sauri ya tura ƙofar ta buɗe gaba ɗaya yana mai susa
kansa tare da faɗin, "Auuch! Sarah da Habbooba zasu kashe muku Ni!" Abutturab dake bayansa ya tallabi
ƙeyarsa tare da faɗin, "Khalil kai ɗan iskan abokine wallahi. Sam baka da zumunci. Ko don kayi kuɗi shiyasa
duk ka watsar damu?" Faɗin Abutturab ɗin. Doctor Kamal kuwa cewa yayi, "Ku bari in baku labarin ɗan
iskan! Muna gari ɗaya, asibiti ɗaya amma sai in kwashi sati ban gansa ba, sai dai idan theather za muyi tare
shine nake samun damar ganinsa. Yanda kuka san wani mace haka yake behaving." Dariya Khalil yayi tare
da zama akan gadon yana mai faɗin, "Duk abunda zaku ce yau shuru zan yi." Ya faɗi yana mai ziping
bakinsa. "Saboda kasan baka da gaskiya ba. Da badan Abutturab ya kira mu ba, da sai dai muji a sama ka
sake aure duk da na farkon ma ba faɗa mana kayi ba." Faɗin Doctor Kamal. "Yanzu dai don Allah ayi min
haƙuri daga yau zan gyara!" "Allah yasa!" Gaba ɗaya suka haɗa baki suka faɗi. Daga nan kuma aka hau
hirar yaushe gamo da kuma tuno lokacin ƙuruciya. Su bakwai ne, Abutturab, Doctor Kamal, Nasir, Bash,
Muhammad, Imran, Khalil sai Majeed cikon na bakwai duk da shi ba abokinsu bane. Anan Khalil yayi shirin
wushe-wushe Kasancewar Majeed ya koma ya ɗauko masa kayansa a gida. Kiran da ka riƙa yi masu a
wayane ya saka cikin saurin suka gama shiryawa cikin ankon ash ɗin shaddar da suka yi, sai da na kalli kalar
emerald green ne wanda yaji wani irin ɗinkin mai matuƙar kyau daya hau kayan da kuma jikinsa. Baƙin
hula ya saka da bakin half cover shoe mai kwalliyar touch of emerald green ɗin. Gaba ɗayansu sai ƙamshin
turare suke, kowannensu aljihunsa cike yake da ƴan dubu-dubu da kuma ɗari biyar biyar. Har cikin gidan
motocinsu yayi parking suka fito, sai kallo ya koma sama, gaba ɗaya gidan ya ɗauki guɗa. Sanyayyar waƙar
larabawa aka sanya masu suka iso har wajen zamansu. Kowa ya zauna a inda yaga sunansa a rubuce, bayan
kamar mintuna biyar sai ga Aysha ƙanwar Khalil hannunta riƙe dana amarya wacce taci uban kwalliya da
white and touch of emerald green lafaya, hatta fuskanta a rufe yake. A hannun wata yayar mahaifiyar
amaryar ta damƙa Habbooba, ita kuma yayar mahaifiyar tata ta kaita wajen zamanta kusa da ango ta ajiye
ta. Ƙawayen amarya ma shiga suka yi ta fararan lafaya mai zanen flower green ko wacce ta zubo da
gashinta kuma dama gasu farare kuma kyawawa. Bayan zaman amarya sai ƴan uwa da abokan arziki suka
hau yiwa amarya liƙin kuɗi da kuma gudunmawarsu. Bayan sun gama nasu liƙin, sai Khalil ya tashi shima
ya soma yin nasa. Tun daga tsakiyar kanta kuɗi ke zuba har ƙasa. Nan da nan abokansa suma suka tashi
suka soma haukan liƙi, tuni wurin ya ɗauki wani irin ihun guɗa. Haka taron ya cigaba da gudana.
Shahararriyar mawaƙiya wannan zamanin tazo wato *_NAADA_*, ta waƙe amarya da ango. Anyi ɓarin nera
kamar ba nemo su ake yi ba. A daran social media ta fashe da wannan taron bikin. Domin ƙawaye da ƴan
uwan amarya suka dunga ɗaurawa a duk wata kafar sada zumunta. Washa gari bayan saukowa daga sallar
juma'a aka ɗaura aure Ibrahim Khalilullah da amaryarsa Ramlat (Habbooba) Yusuf akan sadaki Naira
miliyan biyu. Sarah ita ta fara kiransa a waya tayi masa Allah ya sanya alkhairi. Jiya da kyar ta iya bacci
saboda ganin shagalin bikin da aka yi a social media. Sai da tayi danasanin hawa ta gani. Babu abunda ke yi
mata gizo sai lokacin da Khalil ke buɗe fuskan Habbooba fuskansa ɗauke da wani irin murmushi. Gaban
Sarah sai da ya faɗi lokacin da tayi arba da fuskan Habbooba sabida tsananin kyawun da tayi. Tafi awa tana
kallon kanta a cikin madubi. Duk da tasan cewar itama fara ce tas kuma kyakkyawa ta bugawa a jarida.
"Bata fini komai ba" ta faɗi tare da bawa kanta kwarin guiwa. Jirgin ƙarfe biyar suka bi, Khalil da abokansa,
Habbooba da ƙawayenta biyu da iyayenta guda huɗu sai sauran kayan Habbooba na turare da cincin,
diblan da alkaki. Isha'i a ƙofar gida tayi masu. Tun daga wajen mota aka kunna turarukan tsinke, ƴan uwa
na nan gida da suka san al'adar suka taho da rushi, nan da nan aka saka turaren a kasko mata goma a baya,
goma a gaba Habbooba kuma a tsakiya har ɗakin Hajiya. A gaban Hajiya aka duƙar da ita, bakin Hajiya
kamar zai yage tsabar murna, sai sanyawa Habbooba albarka take yi. Wani ƙatoton jaka ta ajiye a gaban
Habbooba tare da faɗin, "Ga nawa gudunmawar na uwa!" Guɗa dakin ya ɗauka da kuma godiya sannan
suka ɗauki kayan tare da ɗago Habbooba suka nufi ɗakinta. A tsakiyar gado aka ajiyeta sannan suka ƙara
gyara mata ɗakin suka bulbule da turare sannan suka ɗurka mata kayan mayan sannan suka haɗa mata
ruwan wanka mai masifar ƙanshi tayi wanka, ko da ta fito ta iske kaskon turaren da za tayi tsuguno, bayan
ta gama tsugugon sai suka bata wani mai a kwalba mai ƙamshi ta shafe jikinta dashi sannan suka bata kaya
ta saka suka sake naɗe mata jikin da lafaya. Sannan suka gyara komai suka fita daga ɗakin. Sarah tana can
sama ko leƙowa bata yi ba ita da su Na'ima, duk a tunaninsu za'a kawo masu amaryar kamar yanda ake yi a
al'adance. Su Na'ima sai kwantar mata da hankali suke yi. Ba su suka tafi ba, sai da Khalil ya shigo ɗakin.
Sarah tayi ƙoƙari sosai wajen danne kukanta, amma suna haɗa idanu ta fashe da wani irin kuka tare da
faɗawa jikinsa ta ƙankamesa. Shima rungumetan yayi sosai tare da soma hura mata kunne yana lallashinta.
Har sai da tayi bacci ya kwantar da ita sannan ya bar ɗakin bayan ya gyara mata gashin da ya rufe mata
idanunta. Ya jima a parlour tare a tsaye yana tunani. Kitchen ya nufa ya ɗauko energy drink ya buɗe tare da
kai baki, wani irin dariya ya fashe dashi tuno abunda Sarah tace masa rannan, "Naga kamar basir ya gama
cinyeka, muje inyi maka tsome kada amarya ta raina ka!" Girgiza kai yayi tare da faɗin, "Mine, mine, Allah
ya shirya min ke!" Ya faɗi tare da shanye energy drink ɗin sannan ya nufi ɗakin Habbooba bayan ya ɗauki
plate din kazar daya juye tare da cup da Holandia milk. Bakinsa ɗauke da sallama ya shiga ɗakin. Ƙofofin
hancinsa ya ƙara buɗewa yana shaƙar ƙamshin da ɗakin yake yi. Ajiye komai dake hannunsa yayi akan
Centre rug ɗin ɗakin sannan ya isa wajen gadon tare da kamo hannunta ya zaunar da ita kusa dashi sosai
tare da faɗin, "congratulations Mrs Ibrahim Khalilullah Nurudden. Sauko kici abincin nasan wannan cikin
babu abunda kika saka masa." Noƙewa tayi har dasu haɗe kai da kafaɗanta tare da faɗin, "I'm full!" "Ban
yarda ba!" Khalil ya faɗi tare da sauka ya ɗauko tray din ya ajiya a kan gadon sannan ya kai hannu ya
warware lafayan jikinta ya ciresa gaba ɗaya sannan ya zauna tare da faɗin, "Haba, kin lulluɓe jiki kamar
wata ƙonanna. Let me feed you!" Ya faɗi tare da buɗe gasasshiyar kazar ya ɗauko cinya ɗaya ya kai bakinta
ta kawas da kai. "Allah ki karɓa idan ba haka ba ranki zai ɓaci." Ya faɗi yana murmushi don gaba ɗaya tuno
da first night ɗinsa yake da Sarah. "Unforgettable day kenan!" Ya faɗi wani yana wani irin murmushi. Don a
rayuwarsa ba zai taɓa iya mantawa da first night ɗinsa da Sarah ba. "Za kaji min ciwo Khalil." Ya tuno
abunda Sarah take ta faɗi wancan lokacin. "Ba zan ji maki ciwo ba, amma zan biki a hankali!" A bayyane
yayi maganar wanda bai san ya fito ba, don gaba ɗaya tunaninsa ya tafi wajen First Night ɗinsa da Sarah.
Ita kuma Habbooba rufe fuska tayi da sauri alamar kunya don a tunaninta da ita yake yi. "Buɗe bakinki
kinji." Ya faɗi bayan ya dawo daga nisan tunaninsa. Wannan karan bata yi musu ba ta buɗe bakin ya saka
mata. Duk da haka kaɗan taci tasha holandia ɗin, shi kuma yaci sosai ya ƙoshi sannan ya mayar da komai
ya dawo ɗakin tare da umartanta ta tashi tayi alwala. Babu musu tayi alwalar ta dawo lokacin shima har
yayo nasa a ɗaya ɗakin. Darduma ya shimfiɗa ya tada masu sallah, bayan ya idar ya ce mata, "Ki canza kaya
mana ki saka sauƙaƙƙa, kema kyafi jin daɗin jikinki." Yana gama faɗin haka ya fita domin ya bata damar
canzawa. Sai da ya tabbatar ta canza sannan ya dawo ya kulle ƙofar tare da kashe wutar ɗakin ya hayo
gadon. "Wai jama'a zaki tara min ne?" Ya faɗi mata a kunne saboda yanda ta ke ihun azo a cece ta. Sarah
ce ta faɗo masa a rai, tuno nata first night ɗin yanda ta daure. Muryanta sam bai fita da kururuwa kamar
na Habbooba. Sosai ya samu peace of mind akan Habbooba jin ita ɗin cikakkiyar budurwa ce, hakan ne
kuma ya saka ta samu waje a zuciyarsa. Sarah kuwa ba ita ta farka daga bacci ba sai da taji wani abu yana
mata waiwayi a kunne. Buɗe idanun tayi a hankali sai suka yi idanu huɗu da Khalil. Da sauri ta tashi zaune
tare da faɗin, "Happiness, mi kake yi a nan a wannan lokacin?" Murmushi yayi tare da faɗin, "Na zo tashin
matata tayi sallah ne." Hannu ta saka ta dafe goshinta, can kuma ta sauko daga kan gadon tare da kamo
hannunsa ta kawo shi har ƙofar ɗaki sannan tace, "Thanks for waking me up. Amma ka koma wajen
amaryarka ka kula da ita." Da sauri yace, "Kar ki rufe ƙofar nan Mine." Ko kamun yayi wani yunƙuri har ta
tufo ƙofar tana dariya. Sosai taji daɗin zuwan da yayi ya tasheta. Bayan idar da sallah, Sarah bata koma
bacci ba, kitchen ta nufa ta haɗa breakfast mai rai da lafiya ta ɗauka ta nufi parlourn amarya ta jera a
dinning sannan ta koma sama ta ɗan kwanta saboda wani irin kasala da ciwon gaɓoɓi da take ji kwana
biyun nan. Ƙarfe goma da mintuna biyar wani mahaukacin guɗa ya kaure parlourn kamar kunnuwa zasu
tsinke don sai da Sarah ta firgita. "Yarinya ƴar albarka jinin gidan tarbiya. Dama mu ai tsatsonmu tsatso ne
mai kyau da tarbiya. Alhamdulillah yarinya ta kawo budurcinta gidan mijinta. Kai babu abinda yafi kawo
mutunci gidan miji daɗi! Ai rayuwar zubda mutunci da rashin kamun kai bai bi ko kaɗan. Alhamdulillah duk
gidanmu babu mai yawon ta zubar!" Ƴan uwan Habbooba ne ke ta wannan yada habaicin. Murmushi kawai
Sarah tayi duk da maganar tayi mata ɗaci amma sai ta danne. Shi kuwa Khalil tunda ya fita daga ɗakin
wajajen ƙarfe takwas bai dawo ba, yana can yana duba wajen da za ayi ginin Habbooba shi da wasu
architectures. Nan suka yi ta al'adunsu. Bayan sun ƙara taimaka mata ta gyara kanta Banda wanda Khalil
ɗin yayi mata, sai suka kai ta har gaban Hajiya. Warwaron gwal dake hannunta guda uku ta cire ta sanyawa
Habbooba a hannun cike da farin ciki. Daga nan suka ƙara ɗaukarta suka mayar da ita ɗakinta. Kwanan su
uku suka bi jirgi suka koma Maiduguri wanda Khalil ne ya biya kuɗin. Sarah jikinta yaƙi daɗi, amma duk
lokacin da Khalil zai shigo sai ta danne taƙi nuna masa, kuma kullum sai tayi girka breakfast, lunch and
dinner. Khalil yayi-yayi da ita ta daina amma taƙi, wai sai amarya tayi 1week tukun. Kuma a haka kullum sai
taje asibiti ganin Baba, wanda jikinsa sai dai ace Alhamdulillah kawai. Ranar da Habbooba ta cika sati Ɗaya
da aure, a ranar Lami ta baro Nassarawa ta dawo Kaduna domin hankalinta yaƙi kwanciya akan halin da ta
bar mijinta. Sai bayan tafiyarta tukun ta fahimci rashin hankalin da tayi daga itan har mahaifiyar tata wato
Pastor Emmanuelle Deborah. Kai tsaye asibiti ta nufa. Tana ganin halin da Baba Nuhu ke ciki ta ɗaura
hannu a ka ta rushe da kuka. Sai da taci kuka ta ƙoshi sannan ta faɗa masu daga Abuja take wajen Lukman,
don kwanansa ɗaya a Nassarawa Khalil ya tura kuɗi aka tafi dashi Abuja can rehabilitation center. Baba
Nuhu yayi wani irin ramar da kana hango ƙasusuwansa (Ribs) a waje. Lokacin da ta shiga ɗakin da aka ajiye
Aina'u kuwa, sai da ta suma ganin halin da take ciki, gaba ɗaya ta koma kamar tsumma. Zaka iya
nannanɗeta ka saka cikin jaka gari yai zafi. Maƙogwaron nan nata a buɗe, duk abunda taci wasu sai sun
zubo waje, kaɗan ne ke shiga cikin. Saboda zaizayewar da tsokar jikinta ke yi ya saka duk ta tsamure.
Tsohuwa mai shekaru ɗari a duniya ta fita kyan gani. Cikin jikinta kuma cikin ikon Allah yana nan lafiya
ƙalau. Ya shiga na wata biyu da sati Uku. Yau da daddare dai jikin Sarah ya tona mata asiri, domin jikin yayi
zafi rau, kuma sai kelaye amai take yi. Yanzu haka aman ta gama ta wanko fuska ta dawo gado ta kwanta
tare da lulluɓewa da bargo. Khalil na shigowa ya nufi gadon da sauri tare da yaye zanin ya kai hannu jikinta
yaji rau. "Mine, dama baki da lafiya shine kika ƙi magana kuma kullum sai kinje asibiti amma baza ki iya
zuwa in duba ki ba?" A hankali ta furta, "Wallahi ban ɗauka zai kwantar dani haka ba. Na ɗauka gajiya ce
kawai." Janyota jikinsa yayi tare da faɗin, "Mai ke damunki?" Nan tayi masa bayani. Janyeta yayi ya fita da
sauri, can sai gashi ya dawo da tsinken PT da kuma ƙaramin container a hannunsa. "Muje kiyi fitsari anan."
Ya faɗi tare da taimaka mata zuwa bayin. Yana saka tsinken ko second biyar ba'a yi ya nuna layi biyu ɓaro-
ɓaro. Wani irin rungumeta yayi a cikin bayin tare da faɗin, "I knew it! Alhamdulillah ya Allah." Ya faɗi hakan
tare da cicciɓanta ya dawo da ita ya kwantar. Tun daga wannan rana da cikin ya bayyana. Sai laulayi yayi
sallama. Wannan karan babu abunda take sha ya zauna a cikinta sai orange juice. Gaba ɗaya sai rawan kan
Khalil ya ƙara ninkuwa akan wanda yakewa Sarah da. Habbooba kuwa ba ƙaramin shaƙa take yi ba, don
idan har ba ranar girkinta bane, sau biyu take sanyasa a idanu, daga safiya sai dare idan zai yi mata
sallama. Ita kuma ga shegen girman kai da jiƙima. Ko gaishesa bata yi idan ya shigo ɗakinta da safe. Akwai
dai aukin kwalliya da sanya turare, amma kuma girki zero, ladabi zero, iya magana zero, komai dai zero sai
ɗan banzan kishi da gaban tsiya. Don idan tana fushi dashi sai kowa fahimta a gidan don sai ta kulle kanta
tsayin sati a ɗaki ko shi mijin bata buɗe masa ƙofa. Hajiya kuwa ko a waya bata ɗaga kiranta. Idan ta gaji da
kiran Habbooba taƙi ɗauka, sai ta biyo tayi ta bugun ƙofa, tana ji amma sai taƙi buɗewa haka hajiyan zata
gaji ta tafi. Idan Khalil ya dawo Hajiya tayi kiransa tayi ta zazzaga masa bala'i, wani lokacin a maganganunta
kusan kamar har da Allah ya isa take cewa. Haka Khalil ɗin zai saka Habbooba a gaba yayi ta lallashi tana
botsarewa, kuma shi yana yi ne duk don hajiyan kada ɓacin rai ya saka tayi masa kalmar da zata dawo tana
nadama da kanta. Watan ta ɗaya itama ciki ya ɓulla a jikinta. Nan wani sabon fitina da kisisina ya tashi,
idan yana ɗakin Sarah babu zaman lafiya, domin haka zata zo tayi ta bugun ƙofa tana kuka wai cikinta na
ciwo, haka Sarah zata haƙura tace ya koma can, tayi hakan ya kai sau biyar. Ranar da tayi na ƙarshe, daga
ita har Saran da tace ya tafi ya wanke tasssss da soso da sabulu sannan ya kora Habbooba tare da ja mata
dogon warning akan kar ta kuskura duk lokacin da yake ɗakin sarah ta kuma zuwa ta buga masu ƙofa. Haka
tana kuka ta juya ta sauko ƙasa. "Haba Happiness, mai yasa za kayi haka?" Faɗin Sarah bayan ya shigo. Zaro
mata idanu yayi tare da faɗin, "Kiyi man shuru. Duk ranar girkinta ciwon cikin bai tashi sai na dawo nan?
Wannan makircinta ne kawai saboda bata son in kasance tare dake." Washa gari Hajiya ta kira meeting ɗin
gaggawa ta yanke hukunci cike da isa, "Ni uwarka nace Sarah ta baro sashenka gaba ɗaya ta dawo ɗakinka
na nan sashe na! Habbooba tace bata son sabon da ake ginawa, wannan da kuke ciki take so. Don haka a
yau ba gobe ba ta kwaso kayanta ta dawo nan idan ka kammala ginin naka sai ta koma." Khalil ya buɗe
baki zai yi magana Sarah tayi saurin girgiza masa kai. Wasu irin ruwan hawaye ne ya taru a idanunsa.
Namar jikinsa har rawa take saboda ɓacin rai. "In Sha Allah hajiya zan kwashe kayan a yau. Maganarki
umarni ce a Wajen mu." A fusace Hajiya ta ce, "Da ɗana nake magana! Kar ki kuskura ki kuma saka min
ƙazamin bakinki a cikin maganata da ɗana." Sunkuyar da kai Sarah tayi. Khalil kuma ɗagowa yayi ya kalli
Sarah tare da faɗin, "Tashi kije, Mine." Kamar tana jira ta miƙe wuuf ta fita. "Hajiya!" Ɗaga masa hannu tayi
da sauri tare da faɗin, "Na gama magana." Jinjina kai yayi tare da faɗin, "Na sani Hajiya, na amince Sarah
zata dawo nan ɗin, amma wallahi, tallahi billahil azim idan na gama ginin can yarinyar nan ta nuna tana
son wancan ɗin, to ban san mai zan iya yi ba." Yana gama faɗin haka ya tashi ya fita. A parlour ya taras da
Sarah, da sauri ya ƙariso tare da buɗe baki zai yi magana tayi saurin ɗaura yatsarta a kan bakinsa tare da
faɗin, "Su iyaye ba'a musu dasu Happiness. A kullum ƙoƙari ake yi a rabu dasu lafiya. Menene a ciki idan na
koma can ɗin? Ni da wata rana ƙasa zan koma cikin tsukukun ɗaki." Rufe idanu Khalil yayi sai ga hawaye
shaaa sun zubo. Hannu ta saka ta rufe masa baki tare da faɗin, "It's okay!" Khalil yace "Yarinyar nan so take
Hajiya ta tsine min!" Faɗin Khalil. "In Sha Allah haka ma baza ta faru ba." Ta faɗi dai-dai lokacin da wayarsa
tayi ƙara. Kallon wayar yayi tare da picking ya kara a kunne. "To shikenan yaya Allah ya kawo ka lafiya!"
Bayan ya gama wayar ya kalli Sarah tare da faɗin, "Ya Abdullahi ne zai zo jibi domin yin magana da Hajiya
akan batun cikin dake jikin Aina'u." Shuru Sarah tayi tana jin kamar Hajiya baza ta yarda da shawarar da
suka yi ba na kar a sanar da kowa. "Kin yi shiru, Mine!" Ajiyar zuciya ta sauke tare da faɗin, "Allah ya kawo
shi lafiya." Dafata yayi tare da faɗin, "Muje in tayaki ki ɗauko kayanki da nasu twins kawai." Tare suka
haura sama su, shiya dunga kwaso kayan yana sauko dasu ƙasa don ya hanata ɗaukar abu mai nauyi
saboda cikin jikinta. Bayan kwana biyu Habbooba ta kuma fito da wani sabon iskancin na zuwa kullum da
dare tana ihu da kuka wai ta kasa bacci ana bata tsoro kuma mararta ciwo yake. Haka Hajiya zata ruɗe ta
turo Laure tayi ta buga masu ƙofa har sai Khalil ɗin ya fito, haka zasu kwana akan ta su huɗu, Hajiya, Khalil,
Sarah da Laure. Safiya nayi zata warware sai ta koma ɗakinta tayi ta kwasar bacci. Yau ma abunda tayi
kenan. Abun kuma ya fara isar Sarah, sai ta ƙudiri aniyar gyara masu zama daga Habbooban har hajiyan.
Suna fitowa parlour inda Habbooban keta murɗa-murɗan ciki sai Sarah ta saki wani irin ihuu da ya ɗauki
gidan gaba ɗaya kuma dama gashi dare mai ɗaukar sauti. Ba Khalil kaɗai ba hatta Hajiya sai da ta ruɗe.
Habbooba kuwa tashi tayi ta zauna da ɗuwawunta.

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_
[19/11, 12:26 PM] Matar Sayyadee: *_FINAL EPISODE_*
Nan Sarah ta cigaba da ihun nan tana birgima a ƙasa tare da yin wani irin gunjin kuka. Can kuma ta canza
murya zaka rantse da Allah ƙato ne ke magana ta soma faɗin, "Hajiyaaaaaaaaaa!" Idan ta faɗi hakan sai
tayi kamar za tayi kan hajiyan. Hajiya gaba ɗaya ta ruɗe dama kuma gata sarkin tsoro da tashin hankali,
don har guntun fitsari ya soma zubo mata. Sarah kuwa ganin yanda da gaske hajiyan ta ruɗe sai ta ƙara
juya idanunta ta soma tafiya da baya da baya akwancen da take tana wani abu kamar mai farfaɗiya kuma
wajen hajiyan ta nufa. "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Mu'azzam ka taimaka min. Laure maza kunna
mana radio ki saka karatun Alƙur'ani. Yau mun shiga uku." Faɗin Hajiya tare da fashewa da kuka. Habbooba
kuwa can tsakankanin kujera ta raɓe jikinta na rawa don ba ƙaramin tsoron aljanu take ba. Laure na kunna
karatun Alƙur'anin sai Sarah ta fara yi kamar abun sun soma lafawa. Can kuma sai tayi tsit amma cikin
zuciyarta dariya kawai take yi. "Alhamdulillah! Ke Habbooba taho ɗakina mu kwana. Kai kuma Ibrahim,
ɗauki matarka ku wuce. Kuma ka tabbatar kun kwana da ƙira'a." Jinjina kai yayi tare da faɗin, "To Hajiya."
Sai ya cicciɓi Sarah ya nufi ɗaki da ita. Sai da ya shimfiɗar da ita a kan gadon sannan ya zauna a bakin
gadon yana kallonta. Can kuma ya fashe da wani irin dariya tare da ɗaka mata duka a cinya yace, "Allah ya
shirya min ke Mine. Naga wannan scene ɗin! Wato kema kin iya drama ko?" Sarah bata so Khalil ya fahimci
ƙarya take ba, amma kuma yanda yayi mata farin sani dole ya gane. Dariya tayi tare da faɗin, "Ka yafe min
dan girman Allah, bai kamata in tsorata mahaifiyarka haka ba. Wallahi nayi hakane don na gaji da abunda
Habbooba ke min a cikin gidan nan." Janyota yayi tare da faɗin, "Come on! Na fahimce ki ai. Ni kai na kin
taimaka min." Dariya suka kwashe dashi dukansu tuno yanda Habbooba ta shige tsakankanin kujera kuma
tuni ciwon mara yayi fatali. Washa gari ya Abdullah ya dura a gidan shi da Aysha, ya Barrister suna isowa ba
jimawa shima ya iso kasancewar ya kira su duka akan za ayi meeting. Hajiya baki sake take kallonsu su duka
ƴaƴan nata. Ya Abdullah, ya Abdul-Hakeem, ya barrister, Khalil, da kuma Aysha. "Babu sanarwa haka sai
kawai in ganku kwatsam. To ina fatan dai lafiya! Don yanda na ganku tsuru-tsuru haka na san da wata a
ƙasa." Ya Abdullahi ne ya fara magana, "Tabbas da wata a ƙasa Hajiya. Amma mun zo dukkan mu nan
ƴaƴanki domin mu tattauna da ke, kamun nan Hajiya ina son tunatar damu wani abu, _Babu hutu da
kwanciyar hankali ga bawa a wannan rayuwa ta duniya sai yayi imani da ƙaddarar Allah. Wato ya
sakankance cewa duk abinda Allah ya ƙaddara mai aukuwa ne, kuma abinda bai so faruwar sa ba, to haƙiƙa
bazai faru ba. Haka kuma lallai al'umma da zata taru gaba daya domin ta cutar da bawa da wani abu, to ba
za su iya ba sai dai da abinda Allah ya rubuta zai same shi. Hakanan da zasu hadu domin su amfanar dashi,
ba zasu iya ba face da abinda Allah ya rubuta._ Maganarmu a yau ta shafi ɗaya daga cikin rukunan imani
guda shida, wanda duk wanda bai yi imani da shi ba, ko kuma ya yi musu a kansa, to Allah ba zai karɓi
ayyukansa ko ƙanana, ko manya ba. Shi ne bayar da gaskiya da ƙaddara. Rukuni ne mai girma, wanda ta
hanyarsa mutum yake samun nutsuwa a rayuwarsa, ya kuma sami amsoshi game da abubuwa da yawa, da
suka shige masa duhu. Allah yana cewa,
(49‫[ ٍ)ِإَّنا ُك َّل َش ْي ٍء َخ َلْقَناُه ِبَقَدر‬49 :‫]القمر‬
(Mun halicci komai da ƙaddara). Kuma Allah yana cewa,
(3‫ َو اَّلِذ ي َقَّد َر َفَهَدى‬2‫[ )اَّلِذ ي َخ َلَق َفَس َّوى‬٣ – ٢ :‫]األعلى‬
(Shi ne wanda ya yi halitta, kuma ya daidaita ta, kuma shi ne wanda ya ƙaddara abubuwa, kuma ya shiryar
da su). Kuma Allah yana cewa,
(2‫[ )َو َخ َلَق ُك َّل َش ْي ٍء َفَقَّد َرُه َتْقِد يًرا‬2 :‫]الفرقان‬
“Kuma ya halicci kowane abu, kuma ya ƙaddara shi, ƙaddarawa.”
Ayoyi da suke tabbatar da wannan rukuni, sun fi a qirga, kuma a cikin sunnar Manzon Allah ( ‫ )ﷺ‬ma wuri
daban-daban, ya tabbatar da wannan rukuni mai girma. Misali, a cikin hadisin da mala’ika Jibrilu ya zo
wajen Annabi (‫)ﷺ‬, yana tambayar sa, da ya tambaye shi kan imani, sai ya ce, “Imani shi ne, ka bayar da
gaskiya da Allah, da mala’ikunsa, da littattafansa, da Manzanninsa, da ranar qarshe, da yarda da ƙaddara,
mai ɗaci da mara da.” Sai Jibrilu ya ce, “Ka yi gaskiya!” Muslim ne ya ruwaito.
Ya ku ‘yan uwa! Abin da ake nufi da ƙaddara, shi ne ilimin Allah Ta’ala, wanda ya rigaya tun fil-azal, da
abubuwa kafin su auku, kuma Allah ya rubuta su daki-daki, kafin ya halicci sama da ƙasa, da shekara dubu
hamsin, kuma babu abin da zai auku, face da ganin damarsa, kuma shi ya halicce shi. Wannan shi ne bayar
da gaskiya da qaddara wajen sahabbai, kuma shi ne bayar da gaskiya a wajen ahlussunnah. Don haka, tilas
ne ga duk wani musulmi, ya yarda cewa babu wani abu da zai faru cikin mulkin Allah, wanda sai daga baya
Allah zai san shi. A’a, Allah ya rigaya, ya san komai, tun fil-azal, kuma ya rubuta shi a allon qaddara (lauhil
mahfuuz), kamar yadda ya zo a hadisin, kuma kamar yadda Allah yake cewa,
(70 ‫[ )ِإَّن َذ ِلَك ِفي ِكَتاٍب ِإَّن َذ ِلَك َع َلى ِهَّللا َيِس يٌر‬70 :‫]الحج‬
“Lallai hakan, yana cikin littafi, lallai hakan mai sauƙi ne wurin Allah.” Don haka, babu wani abu da zai auku,
face sai Allah ya ga dama, kuma idan zai auku, zai auku ne, kamar yadda Allah ya zartar. Allah yana cewa,
(31‫ ُيْد ِخ ُل َم ْن َيَشاُء ِفي َر ْح َم ِتِه َو الَّظاِلِم يَن َأَع َّد َلُهْم َع َذ اًبا َأِليًم ا‬30‫[ )َوَم ا َتَش اُءوَن ِإاَّل َأْن َيَشاَء ُهَّللا ِإَّن َهَّللا َك اَن َع ِليًم ا َح ِكيًم ا‬:‫اإلنسان‬
٣١ - ٣٠].
(Ba kwa nufin aikata wani abu, sai Allah ya yi nufi. Lallai Allah masani ne, mai azanci, yana shigar da wanda
ya yi nufi cikin rahamarsa).
Ya xan uwa! Ka sani, babu tilas ga ƴan Adam kan ayyukansa, a aƙida ta musulunci. Mutum yana da dama,
da kuma zaɓi, na ya aikata abin da ya ga dama, kamar yadda yake cewa,
(10 ‫[ )َو َهَدْيَناُه الَّنْج َد ْيِن‬١٠ :‫]البلد‬.
(Kuma mun shiryar da shi hanyoyi biyu).
Wato na alheri, da na sharri. Don haka, shi ɗan Adam, shi ne yake zaɓar abin da ya ga dama, kuma sanin
Allah, ba ya nufin Allah ya yi masa tilas ba ne. Don ba daidai ba ne, mutum ya kafa hujja da ƙaddara wajen
saɓon Allah, kamar yadda wasu mutane suke yi.
Ibni Taimiyya ya ce, «Wannan maganar banza ce. Wato mutum ya kafa hujja da ƙaddara a kan saɓa wa
Allah, saboda imma dai ƙaddara ta zama hujja ga kowa da kowa, ko kuma ba hujja ba ce ga kowa da kowa.
To idan ƙaddara hujja ce ga kowa da kowa, to babu wanda yake da dama ya yi musu ko inkari ga wanda ya
cuce shi, ya zage shi, kuma ya kwace masa dukiyarsa, ya ɓata masa matansa, ya sare sa da takobi a wuya,
kuma ya lalata masa gonarsa da ƴaƴansa. domin ba zai cuce shi ba, sai da ƙaddara. Babu wanda zai yarda a
cuce shi, a kafa masa hujja da ƙaddara. Abu na biyu, idan ƙaddara hujja ce, to da Iblis, da Fir’auna da
mutane Annabi Nuhu da Adawa da sauran masu saɓon Allah, waɗanda Allah ya halakar da su, da sun sami
hujja. Haka kuwa abu ne da babu wani mai bin wani addini da zai yarda da shi. Abu na uku, da ƙaddara
hujja ce, to da babu bambanci tsakanin bayin Allah na ƙwarai da fajirai.Wanda ya saɓa ga tunani na
qywarai, ya kuma saɓa da faɗin Allah cewa,
(22 ‫ َوَم ا َيْس َتِوي اَأْلْح َي اُء َو اَل اَأْلْم َو اُت‬21 ‫ َو اَل الِّظ ُّل َو اَل اْلَح ُروُر‬20 ‫ َو اَل الُّظُلَم اُت َو اَل الُّن وُر‬19 ‫[ )َوَم ا َيْسَتِوي اَأْلْع َم ى َو اْلَبِص يُر‬
٢٢ – ١٩ :‫]فاطر‬.
“Makaho ba zai daidaitu da mai gani ba, haka duhu ba zai yi daidai da haske ba, haka inuwa ba za ta yi
daidai da zafi ba, haka matattu ba za su yi daidai da masu rai ba.”
Kuma yana cewa,
(28 ‫[ )َأْم َنْج َع ُل اَّلِذ يَن َآَم ُنوا َو َع ِم ُلوا الَّصاِلَح اِت َكاْلُم ْفِس ِد يَن ِفي اَأْلْر ِض َأْم َنْج َع ُل اْلُم َّتِقيَن َكاْلُفَّجاِر‬28 :‫]ص‬
(Ko za mu sanya waɗanda suka yi imani kuma suka yi ayyuka na kwarai kamar masu ɓarna a doron ƙasa, ko
kuma za mu sanya masu taƙawa su zama daidai da fajirai).
Abu na huɗu: Ita ƙaddara imani aka ce mu yi da ita, ba kafa hujja ba. Duk wanda ya kafa hujja da ƙaddara
to hujjarsa ta banza ce. Duk kuma wanda ya ba da hanzari da ƙaddara to hanzarinsa ba abin karɓa ba ne.
Da ana karɓar hujja da ƙaddara to da an karɓi ta Iblis da sauran masu saɓo. Da ƙaddara hujja ce ga bayi da
babu wani da za a yi masa azaba a nan duniya ko a lahira. Da ana hujja da maddara da ba yanke hannun
ɓarawo ba, ba a kashe wanda ya yi kisan kai ba, da ba wanda za a yi wa haddi don ya yi wani laifi. Kai da
ma ba wanda za a yaƙa, ko a yi umarni da wani abu na shari’a ko hana wani mummunan abu. Abu na biyar,
an tambayi Manzon Allah (‫)ﷺ‬, “Idan dai Allah ya rubuta komai, to meye amfanin aikin da bayi za su yi?”
Sai ya ce, “A’a! Ku yi aiki. Kowa abin horewa ne ga abin da aka halicce shi don shi.” Abu na shida, idan dai
rubutu da Allah ya yi, zai zamo hujja ga masu saɓo, to me ya sa ba zai zama hujja ba wajen ci da sha, da
makamantan haka? Ai Allah ya ƙaddara masa ci da sha, da sauransu, amma ba zai ƙoshi ba, ko ya daina ci,
sai ya ci, ya sha. Me ya sa ba zai ce, tunda Allah ya rubuta, ba sai na ci, ko na sha ba, idan na zauna haka
ma, ƙaddara za ta biyamin buƙatata? Ko kuwa haihuwa: Ai ita ma ƙaddara ce, me ya sa mutum ba ya zama,
ya ƙi yin aure, ya ce, idan dai Allah ya rubuta mini, zan same shi, ko ban kusanci mace ba. Babu mai faɗin
haka, sai wawa. To haka ma abin da yake wajen bin Allah, ko saɓa masa. Ina fatan duk kuma fahimtata
Hajiya?" Gyaɗa kai Hajiya tayi tare da faɗin, "Na fahimceka marmari. Amma gaba ɗaya jikina duk yayi
sanyi, na ƙosa naji shin wannan karo mai ya faru kuma!" Ta ƙarisa maganar a raunane. "Hajiya a kan Khalil
ne, nasan gaba ɗaya nan mun sam abunda ya faru a baya. Kuma bugu da ƙari yarinya tayi bayanin da kanta
cewar asiri tayiwa Khalil yayi ta amfani da ita dama duk wasu abubuwan da tayi ɗin. To sakamakon wannan
kwanciya da yayi da ita, ta samu ciki, Khalil bai amince cikinsa bane sai da yayi DNA test da kansa kuma ya
tabbatar shine uban cikin dake jikinta." A razane hajiya ta hau salati tana kuka sosai tare da faɗin, "Allah ya
isa tsakanina da ke Aina'u! Ibrahim Allah ya saka maka abunda yarinya tayi maka. Ta ɓata maka rakod
(record). Ni kuwa ya zanyi idan ban yarda da wannan ƙaddarar ba? Ai dole nayi haƙuri na rungumesa da
hannu bibbiyu. Khalil ɗana ne, Ni kuma uwarsa. Duk duniya idan ban rufa masa asiri ba, babu wacce zata
rufa masa. Ubangiji Allah ya baka ikon cin jarabawarka Mu'azzam!" Gaba ɗaya suka ɗauka da ameen.
Gyaran murya ya Abdullahi yayi tare da gyara zama ya cigaba, "Hajiya gamu nan dai mu biyar a gabanki,
bayan mu babu wanda ya san da maganar acikin zuciyarmu. So nake wannan magana a binneta anan,
bayan mu kar kowa yasan Khalil ya haihu da _ƙanwar matarsa_, Saratu na ɗauke da ciki, duk da ita Aina'un
zata riga ta haihuwa da wata biyu, so muke a ɓoye abunda Aina'u zata haifa har sai Allah ya sauki Saratu,
to a wannan lokacin za'a bayyanar da abunda Aina'un ta haifa a duniya matsayin ƴan biyu da Sarah ta
haifa. Ko a cikin gidan nan kada kowa ya san haka. Habbooba da Maryam kada su san wannan batun dan
girman Allah." Share hawaye Hajiya tayi tare da faɗin, "A matsayina na mahaifiyarku, ban yafewa duk
wanda ya fitar da wannan maganar a cikinku ba. Yanda Abdullahi yace, haka za ayi. Allah ya sauke su
lafiya." Wani irin ajiyar zuciya Khalil ya sauke tare da faɗuwa a gaban Hajiya yana kuka yana roƙonta gafara
da kuma godiya akan wannan abu da tayi masa sannan ya ƙara da faɗin, "Hajiya ina roƙonki wannan
alfarmar, dan darajar ubangiji kiyi haƙuri ki yafewa Sarah ku dawo kamar yadda kuke da." Ɗago shi tayi tare
da faɗin, "In Sha Allah Khalil daga yau zan canza, kuma dama can wallahi abubuwan da Aina'u ta aikata ne
ya bani tsoro har ya saka uwata Saratu ta fita daga raina, Kuma ka san ni ɗin uwace dole inji zafin kashe
min ƴa da aka yi da kuma kusan rabani da ƴaƴana. Amma komai ya wuce. Ita kanta Saratu abun a tausaya
mata ne." Rungumeta yayi tare da faɗin, "Nagode sosai Hajiyata." Tun daga wannan rana Sarah ta samu
sauƙi sosai a wajen Hajiya wanda tayi mamakin hakan sosai don Khalil bai faɗa mata shi ya taushi hajiyan
ba. Gadan-gadan ya hau yin ginin Sarah wanda har ya kai linta, lokaci guda kuma filinsa dake Kinkinau ana
ta gyara da gine-ginen wajen ajiye kaji da kuma dabbobi. Ginin da Khalil yake yi iri ɗaya ne da wanda
Habbooba take ciki yanzu. Sai dai ya fishi tsaruwa da abubuwan zamani. Nan da nan hankalin Habbooba
yayi mugun tashi ta nufi Hajiya da zancen ita wannan sabon take so. Hajiya kuma ta nuna mata sam bata
isa ba, wannan gini na Sarah ne. Tun daga wannan rana ta daina wa Hajiya magana, tsakaninsu sai habaici.
Hajiya kuma tana lure da ita amma sai tayi kamar bata fahince ta ba. Lokacin da aka kammala gini, sai tayi
tsalle tace wancen take so. Sosai Khalil ya wanke ta da soso da sabulu tace ya ƙara da aje mata rafar dubu-
dubu guda biyu yace tayi kuɗin jirgi ta koma gidansu idan baza ta iya zama a nan ɗin ba. Lafiyayyun
furnitures ya saka aka zuba mata ta tare a ɗakinta lokacin cikin jikinta watansa biyar daidai da na Aina'u
wata bakwai, Habbooban kuma wata huɗu. Tuni Baba Nuhu ya saka an dawo dashi gida wai ya gaji da
zaman asibitin, su Nnanne ma sun koma, kuma gaba ɗaya suka kwashe su Na'ima suka tafi dasu. Lukman
ma ya dawo daga rehabilitation center ya natsu sosai kamar ba shi ba. Don makaranta Khalil ya nema masa
kasancewar ko a da ɗin ya kammala secondary da ƙyar. Yanzu haka yana 100lv a University dake nan
Nasarawa. Na'ima kuwa, tunda babban ɗan ba Kamal ya ganta ya manne mata, tun tana sharewa har ta
soma kula shi. Yana da mata ɗaya da ƴaƴa uku. Magana har tayi ƙarfi ta shiga wajen manya. Nnanne tsabar
daɗi kamar ta zuba ruwa a ƙasa tasha. Hassana, Nuratu da Marfu'a kuma gaba ɗaya makaranta suka koma
suma 100lv ɗin sai course daban-daban. Wata rana Sarah na kitchen tana haɗa lunch kawai taji anyi
banging ƙofa da ƙarfi an shigo, a razane ta juyo suka yi idanu huɗu da Habbooba hannunta riƙe da wuƙa.
"Inna lillahi wa'inna ilaihir! Lafiya Habbooba?" Sarah ta faɗi jikinta na rawa. "kashe shi nazo yi domin in
zauna da mijina ni ɗaya." Zaro idanu Sarah tayi tare da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Kar kiyi
haka Habbooba, laifi babba zaki aikata." Harararta tayi tare da faɗin, "Idan har zan zauna da mijina ni ɗaya,
ban damu da inyi ko wani irin laifi ba." Tana gama faɗin haka tayo kanta da gudu. Da gudu Sarah ta kwasa
itama suka shiga zagaye kujeru tana kai mata suka ita kuma tana kaucewa har Allah ya bata nasarar angiza
Habbooba ta fita da gudu, itama miƙewa tayi da gudu tabi bayan Sarah. Ta window aunty Maryam ta
hangesu ta fito da gudu itama tabi bayansu. Ɗakin Hajiya ta faɗa tare da ɓoyewa a bayan hajiyan tana
faɗin, "Hajiya ki taimaka min zata kashe ni!" Waro idanu Hajiya tayi ganin Habbooba da wuƙa a hannu tana
nufo su. "Ke! Baki da hankali ne? Yar da wuƙan nan." Wani iri yanka ta kaiwa Hajiya aikuwa ta same ta a
hannu sai ga jini shaaa. "Inna lillahi wa'inna ilaihir!" Aunty Maryam da Sarah suka faɗi da ƙarfi tare da
ɗaura hannu a kai daidai shigowar Khalil da ya Abdul-Hakeem. Wani irin wawan mari Khalil ya ɗauke
Habbooba dashi tare da soma kwallo da ita ya ma mance da wani cikin dake jikinta. Shi kuma ya Abdul-
Hakeem yayi kan Hajiya. Ture shi Hajiya tayi tare da shiga tsakanin Khalil da Habbooba tare da faɗin, "Ka
bari nace Ibrahim! Taci arzikin cikin dake jikinta." Ita kuwa Habbooba bakinta yaƙi rufuwa sai cewa take,
"Wallahi sai na ƙone gidan nan kowa ya mutu har dani!" Kallon Hajiya Khalil yayi tare da faɗin, "Hajiya ba
zan iya zama da yarinyar nan ba, taje na sake ta saki ɗaya." Yana gama faɗin haka ya jata ƙiiiii har waje
sannan ya rufo ƙofar ya soma dressing ɗin hannun Hajiya, Allah yaso wuƙar bata shiga ciki ba. Habbooba
kuwa kamar mahaukaciya ta wuce side ɗinta fuuuuuuu ta ɗauki akwati da kuɗi ta fice daga gidan. Kallon
Khalil dake dressing hannunta tayi tare da faɗin, "Ibrahim ka yafe min, nasan baka son Habbooba amma na
matsa maka sai ka aureta. Yanzu wa gari ya waya. Da badan Allah ya tsare ba, da yarinyar nan tayi kisa
yau!" Khalil yace, "Hajiya babu abunda kike yi. Ki daina blaming kanki." Jirgi Habbooba tabi ta tafi
Maiduguri, taxi tayi shata har gate ɗin gidansu. Tana shiga taci karo da mahaifinta sai da gabanta ya faɗi.
Shi kuwa kallo ɗaya yayi mata ya fahimci bata da gaskiya. Gaba ya saka ta har ɗakinsa ba tare da
mahaifiyarta ta san da zuwanta ba. Narkekiyar bulala ya ɗauko ya shimfiɗa mata biyar lafiyayyu sannan ya
tambayeta abunda ya kawo ta. Kasancewar ta san halinsa zai iya yankata, aikuwa ta warware masa kaf
abunda ta aikata. Saboda cikin dake jikinta ne kawai ya saka bai mata dukan mutuwa ba. Amma ko
mahaifiyarta bai bari ta gani ba ya saka ta a mota ya wuce da ita can ƙauye wajen ƙanwar babansa yace ta
zauna kuma kar a barta ko waje ta riƙa fitowa sannan kuma duk wani aiki a bata kar a raga mata kuma ya
kwace wayarta yayi dawowarsa. Ba ƙaramin wahala take sha ba, kullum kuma tuwo take ci safe rana da
dare. Duk ta rame ta bushe wata ɗaya cal kawai. Dana sani kuwa tayi yafi kwando dubu. Kuka na jini ne
kawai bata yi ba. Gashi tun da Baba ya ajiyeta bai kuma waiwayo wa ba. Shi kuwa baba yana dawowa
washa gari ya taho kaduna. Har ƙasa ya ɗuka yayi ta bawa Hajiya da Khalil haƙuri har da Sarah. Duk suka
nuna masa komai ya wuce har Hajiya ta nuna Khalil ya mayar da ita amma sai Baba ya hana, yace sam bai
amince ba har sai Habbooba ta gane kuskurenta, idan yaso nan gaba idan akwai sauran shan ruwanta anan
ɗin sai ta dawo. Sarah Khalil wani irin rayuwar nishaɗi da faɗin ciki suke yi. Lokacin da cikin Aina'u ya cika
wata tara, Khalil ya saka ranar da zai yi mata CS don sam baza ta iya haihuwa da kanta ba. Sarah kuma
cikinta lokacin watansa bakwai. Ana saura kwana biyu yayi mata CS, wata rana suna bacci wajajen ƙarfe
biyun dare ya samu kiran gaggawa daga asibiti, Aina'u na fizge-fizge zata mutu. Da sauri ya diro daga kan
gadon, yana sauke ƙafarsa Sarah na ajiye nata tare da faɗin, "Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un" tana kuka
don taji duk maganar da suka yi. Yayi-yayi da ita ta zauna shi ya tafi, amma ta nuna ita sam sai taje. Khalil
na zuwa suka shiga da ita theather room, Sarah sai zirga-zirga take yi tana addu'a. Cikin mintuna talatin
Khalil ya ciro kyakkyawar baby daga cikin Aina'u mai kama dashi sak. Sai dai tun kan ya kammala ɗinke
cikin Aina'u ta hau wani irin abun kamar mai tsinkau-tsinkau. Allurar da aka yi mata bai hanata yin magana
ba, gaba abubuwan da ta aikata take ta faɗi tana haɗawa da kukan kare. A wannan dare dai Aina'u ta cika
bayan cika asibitin da tayi da ihu da kuma jikinta da haƙoranta. Khalil bai san lokacin da ya fashe da kuka ba
ya ƙarisa kusa da inda aka ajiye babyn yana kallonta yana kuka sosai kamun ya rungume ƴar a jikinsa. Sarah
sumewa tayi lokacin da Khalil ya fito daga theather room ɗin hannunsa ɗauke da babyn Aina'u. Lokacin
data farfaɗo, a kan gadon Lami ta ganta, Hajiya kusa da ita tana tofa mata addu'a. Yunƙurawa tayi zata
miƙe Hajiya ta riƙeta tare da faɗin, "Kwanta kar ki tashi Saratu." Hajiyan ta faɗi tana hawayen tausayin
Aina'u. A hankali ta miƙe ta zauna tare da jingina da gado. Can kuma da sauri ta kai hannu ta ɗauki babyn
dake kusa da ita cikin kayan sanyi tare da rungumeta, wani irin zazzafan ƙaunar yarinyar na shiga cikin
zuciyarta. Fita Hajiya tayi tare da samun Lami dake jingine da ɗakin Baba Nuhu, idanunta sunyi luhu-luhu
fuskan ya kumbura saboda kukan da taci. "Maman Sarah, kina ganin a faɗa mata mahaifinta ya rasu? Ina
tsoron halin da zata shiga." Hawaye Lami take yi sosai don har duhu-duhu take gani. A yau taga mutuwa
biyu masu girgiza zukata. Da fari ƴarta, sai kuma mijinta. Shi kuma da asuba ya cika. Don ko da ba Nura ya
tashi yayi alwala yaje yayi Sallah ya dawo, yana taɓa shi yaji alamar babu rai a jikinsa. Don shi daga baya da
aka sallami Baba Nuhu shi dawowa yayi da zama a Kaduna ya cigaba da jiyar tagwainin nasa. "A kira mijinta
ya faɗa mata cikin hikima." Faɗin Lami. Jinjina kai Hajiya tayi tare da leƙowa waje ta kira Khalil ɗin Allah
yaso dawowarsa kenan daga airport, duk da babu jirgin da zai je Nassarawa, ya Abdullahi ya bada jirgin
sojoji yaje ya dauko su Nnanne da ba Lukman domin dasu Na'ima. Gidan wani irin ruɗewa yayi kuka
lokacin dasu Na'ima suka shigo. Da sauri Sarah ta fito daga ɗaki hannunta ɗauke da babyn Aina'u.
Rungumeta Na'ima tayi tare da faɗin, "Sarah, ashe baba ya riga mu gidan gaskiya!" Wani irin wuuuuuu
Sarah ta soma ji a cikin kanta kamun tayi wani irin baya ta tafi luuuuuu, da sauri Na'ima ta riƙo babyn,
Khalil kuma ya riƙo Sarah zuwa jikinsa. Tun daga wannan lokacin Sarah Bata kuma sanin inda kanta yake ba,
sai jini ya ɓalle mata kamar dai lokacin cikin twins. Nan da nan Khalil yayi asibiti da ita, don shi bai samu
jana'izar Baba ba. Aina'u kuwa da an sakata a rami, ƙasa ke bulluƙota, sai da aka tara mutane akai ta
addu'a kamun Aina'u ta samu zama cikin ƙabari. A can asibiti kuwa, Sarah sai zubar jini take yi ga kuma
naƙuda gadan-gadan amma babu haihuwa. Hannu Khalil ya saka aka shiga da ita ɗakin theather. Cikin
ƙanƙanin lokaci aka ciro mata babynta mace mai kama da ita sak, irin hasken Khalil kawai ta ɗauko. Don
Sarah ita ja ce, Khalil kuma fari. Gyarata akai aka mayar da ita ɗakin hutu, babyn kuma aka sakata a
incubator. Sujada Hajiya tayi tare da ɗagota ta ɗaga hannu tare da faɗin, "Allah mai yin yanda yaso,
ubangiji ka nuna ikonka anan. Tabbas ayau Sarah ta haifi ƴan biyu." Lokacin da Sarah ta farfaɗo, kowa da
zullumi a cikin zuciyarsa, amma cikin ikon Allah sai ta farfaɗo da dangana, don ko hawaye bata yi ba sai
addu'a kawai da tayi ta aunawa babanta da kuma Aina'un. Satinsu biyu a asibiti aka sallame su suka dawo
gida. Dangi gama ɗaya kuma aka yi masu shelar Sarah ta kuma haifan twins duka mata. Lami duk ta zama
wani abun tausayi, don ba kaɗan ba mutuwar Baba Nuhu ya dake ta. Jin labarin yanda ƙasa taƙi amsar
Aina'u har sai da aka haɗa da addu'a ya saka wannan karon ta amshi addinin Musulunci da duka zuciyarta,
kuma Pastor Emmanuelle Deborah bata wani yi tashin hankali ba duk da zuciyarta bai so hakan ba, amma
bata takura mata ba, ta barta acewarta kowa yayi addininsa. Sai dai wata sabuwa a ɓangaren jaririyar
Aina'u, sam bata gani. Zata buɗe idanunta amma kuma bata gani, ba ƙaramin tashin hankali gaba ɗaya
zuri'ar suka shiga ba, musamman Khalil da Sarah, don haka Sarah zata sakata a gaba tana kuka. Babu irin
duba idanun nan da ba'a yi ba, amma basu ga komai ba kuma yarinya bata gani. ƴar wajen Aina'u taci
sunan Sarah amma da _DINAAYA_ suke kiranta, ta wajen Sarah kuma taci sunan Hajiya, wato Bilkisu amma
suna mata inkiya da _ALEESHA_. Ɓangaren Habbooba kuwa, ta lalace ta zama abun tausayi. A wani zuwa
da Mahaifinta yayi, shi kansa sai da ya tausaya mata, don ta saje da ƴan ƙauyen kamar ba Habbooba ƴar
gayu ba. Cikinta ya tsufa don ya shiga na wata takwas. Kuka tayi ta yi tare da riƙe ƙafafun mahaifin nata
tana faɗin tayi nadama baza ta kuma aikata abunda tayi ba. Daga nan ƙauyen ya kwasheta zuwa gida. Ita
kanta mahaifiyarta kuka ta saka lokacin da taga ɗiyar tata. Tun da ta dawo cikin Maiduguri ta samu waya
tayi ta kiran Khalil, da ya fahimci ita ce yake kashe kiran ya saka a blacklist. Haka ta koma kiran Hajiya tana
kuka tana roƙonta gafara. Hakan ya saka Hajiya ta roƙi Khalil yaje Maiduguri ya sauke nauyinsa a kanta
tunda dai tana ɗauke da cikinsa. Farko nunawa yayi ba zai je ba, amma da Hajiya ta roƙesa, sai ya amince.
Kwatsam sai ga kiran gaggawa daga ɓangaren Sarah zuwa Nassarawa idan da hali saboda zuwan dangin
mahaifin Baba Nuhu (Ina fatan baku manta cewar Nnanne da mahaifiyar Baba Nuhu, uwa ɗaya kawai suka
haɗa ba, uba kuma Kowa da nasa?) Tun da mahaifiyarsu Nnanne ta baro Bama ita ƴarta (Mahaifiyarsu
Baba Nuhu) bata kuma komawa ba, su kuma dangin mijin suka yi fushi suka bar mata aka baza su nemeta
ba tunda ta gudu. Ita kuma Rahmatu (Mahaifiyarsu Baba Nuhu) rana gudun a rabata da tilon ɗanta
shiyasa ta gudu ta bar garin bayan rasuwar mijinta. Basu kuma waiwayowa ba sai yanzu. Dama kuma tun
bayan arba'in, Pastor Emmanuelle ta ɗauke Lami suka tafi can Nassarawa sai aka saka ƴan haya a gidan. Ta
jirgi suka bi ita da Khalil da Laure mai taya ta raino. Khalil lokacin da yaga ƴan uwan mahaifin Baba Nuhu,
he was very shocked, domin ƴan uwan hajiyarsa ya gani. Su kansa da suka ganshi, mamaki ne ya kama su.
Kuma a wannan lokacin ne suka fahimci da kakan baba Nuhu, da Mahaifin Hajiya, uwarsu ɗaya ubansu
ɗaya. Cikin farin ciki Khalil ya fita ya kira Hajiya a waya yana shaida mata wannan albishir ɗin. Aikuwa
ruɗewa tayi da murna har da kuka ta saka a ranar duka ƴaƴanta suka haɗu washa gari suka taho
Nassarawa. Kuka Hajiya tayi sosai jin ashe Baba Nuhu da ƴaƴansa kaf jinin dake yawo a jikinta. Kuka tai tayi
tana tsinewa rashin kula da zumunci. Ranar kuwa Sarah da su Na'ima kamar zata mayar dasu ciki. Kwana
aka yi aka hira tana basu labarin sauran ƴan uwa da basu sani ba. Kwanansu biyu suka ɗugunzuwa zuga
guda suka yi Maiduguri ta Abuja a jirgin sama. A can ma family sun gama ruɗewa gaba ɗaya da son ganin
zuri'ar Alai Mansur wato kakansu Baba Nuhu. Rasa inda za'a saka su akayi saboda farin ciki. Wannan yace
gidansa, wancen ma yace gidansa. Sosai Hajiya tayi dana sani akan abubuwan da tayi wa Sarah. Kuma a
ranar tace ta yafewa Aina'u duniya da lahira haka shima Khalil. Tsuru-tsuru Habbooba tayi data samu
labarin Sarah ta fita kusanci ma da Hajiyan. Lokacin da suka yi branch a gidan da kukanta tazo ta durƙushe
tana neman gafarar Hajiya da kuma Sarah tare da roƙon manyan wajen akan su saka baki Khalil ya maida ta
ɗakinta in Sha Allah baza ta ƙara ƙoƙarin aikata kuskuren da tayi ba ko cikin mafarki. Sarah ce ta kalli Khalil
tare da jinjina masa kai alamar ya mayar da Habbooba bayan manya sun saka baƙi. Fuska babu yabo babu
fallasa yace, "Na maida ta." Da gudu tayi kan Sarah tare da faɗin, "Nagode, Nagode sosai." Kasancewar
tana ganin lokacin da Sarah ta gyaɗawa Khalil ɗin kai. Satinsu biyu suka dawo Kaduna har da Habbooba
bayan ƴan uwa sun yi wa Sarah wani irin gyaran fitar hayyaci irin nasu na Shuwa Arab da kuma kyautar
turaruka masu ƙamshi da tsada. Dawowarsu da sati ɗaya, Habbooba ta haifo ƴarta mace wacce taci suna
Benazir. Hankula sun kwanta sosai a gidan, musamman da aka rike Allah da kusanta kai a garesa. Sai dai
fannin Habbooba har gobe akwai wannan zafin kishin don a jininta yake. Wani wani lokaci da suka taɓa
faɗa da Sarah, har ɗaki Sarah ta bita ta karkarta mata warning, "Ke Habbooba! Ki kiyaye ni domin na fiki
bala'i, kyaleki kawai nake yi saboda Ni in son zaman lafiya. Amma idan ke abunda kika zaɓa kenan, to
daidai nake dake. Idan jini shuwa kike taƙama dashi, nima jinin na yawo a jikina." Tana gama faɗin haka ta
cusa hannu cikin gashinta ta zaro wani makami mai kamar kibiya sannan ta ɗage skirt ɗinta ta zaro wata
sharɓeɓiyar wuka sai da Habbooba ta ja da baya ta faɗi don firgita, "Kin gansu nan, dasu nake yawo a jikina
saboda ke. Don haka ki kiyaye ni ki zauna lafiya." Tana gama faɗin haka ta fita daga ɗakin. Tun daga
wannan lokacin Habbooba ta fita harkan Sarah. _DINAAYAH_ kuwa sun kai ta ƙasashe da dama amma
idanu shuru, gashi dai a buɗe amma bata gani. Haka suka haƙura suka fauwalawa Allah komai. Sarah ba
ƙaramin kuɗi take samu ba da gidan gonarta. Sai da tayi gidan gona huɗu saboda can Kinkinau ɗin yayi
mata kaɗan. Marfu'a dasu Hassana duk sun samu miji, sai dai duk masu matane, tare aka haɗa dana
Na'ima. Ba ƙaramin hidima Khalil da su ya Abdallah suka yi ba. Ya Abdallah shi yayi masu kayan ɗaki kaf,
Khalil kuma ya bawa Kowacce jari, Barrister kuma ya saya ma kowaccen su mota. Abdul-Hakeem kuma ya
ɗauke nauyin Lukman na makarantarsa gaba ɗaya. Khalil da Sarah ji suke kamar yanzu ne su kai aure
saboda yanzu ne suke jin daɗin zaman babu matsi da tashin hankali. Itama Sarah ta koma makaranta daga
200lv a kasu kasancewar tana da diploma. _DINAAYA_ ko a fuska bata taɓa sanin Sarah ba ita bace
Mahaifiyarta. Don komai sai wanda take so za ayi, akwai wani irin so da shaƙuwa tsakaninta da
_ALEESHA_. Sau ɗaya Sarah ta taɓa kama ta tana shafa fuskan hoton Aina'u. Sai ga gabanta ya faɗi.
Murmushi _DINAAYAH_ tayi tare da faɗin, "Mummy, wannan ba ke bace a hoton nan, wacece?" Kwace
hoton Sarah tayi tare da faɗin, "Nima ban santa ba. Tashi ki tafi wajen ƴar uwarki." Sosai Sarah ke mamakin
baiwar _DINAAYAH_ gata dai makauniya, amma abubuwan ta kamar na masu idanu. Ko gittawa mutum
yayi zata kira sunansa tace wane ne. Allah yayi mata wani irin baiwa. Ga saurin ɗaukar karatu da kuma
natsuwa. Don a cikinsu su ukun, _Aleesha_ da kuma _Benazir_ duk ta fisu ilimi, haƙuri da kuma natsuwa.
Khalil da Sarah suna mugun sonta.......

_ALHAMDULILLAH! ALHAMDULILLAH!! ALHAMDULILLAH!!! NAN NA KAWO KARSHEN LITTAFIN NAN NA


ƘANWAR MATATA! KUSKUREN DA NAYI A CIKI ALLAH YA YAFE MIN. NA SAN DA YAWAN KU BAZA SU
DAWOWAR HABBOOBA CIKIN RAYUWAR KHALIL BA, HAR MA DA KASANCER *DINAAYAH* A RAYE, TO DUK
KUYI HAƘURI HAKA LABARIN YAZO. WAƊANDA NAYI WA LAIFI KU YAFE MIN, SHI ƊAN ADAM AJIZI NE!_

*_SAI MUN HAƊU A LITTAFI NA GABA MAI SUNA 👇_*

🦜 _DINAAYAH SAFRAAZ_ 🦜
*_Between two lovers_*
( _The Return Of Ƙanwar Matata_)

*👭GARKUWAR MATA*
*Ina Matan suke? mata na ke kira ba muna mata ba, duk wacce ta amsa sunanta na 'Ya mace ta na tattalin
kanta da lafiyarta, Mace 'yar gayu ce mace 'yar kwalisa ce, kuma aka ce mace bata tsufa 💯muddin tana
gyara kanta, duk yawan shekarunki idan kina tattalin kanki za ki ci zamaninki sannan ki ce na wasu, Ka da
na cika ku da surutu GARUWAR MATA👭 ta zo muku da ingantattun magungun mata masu kyau da inganci
🌿🌿🌴🌴 Mussaman maganin gyaran Nono da mafi akasarin Mata suke da damuwa da matsalarsa, to
shakuruminki 'Yar uwa muna da sahihin maganin gyaran nono da zai dawo miki da martabarki duk
lalacewarsa muddin ki ka yi amfani da maganinmu za ki yi godiya, sannan muna sayar da maganin sanyi
mai kyau wanda yake kassaara kowane irin sanyi na fili da 'boye, akwai supplement gangariya masu kyau
irin wadanda ba su da matsala sai dai su gyara garkuwar jiki. Muna kuma sayar da turarukan wuta humra
perfumes sabulan gyaran fata dilka kayan gyaran jiki na amare dahuwar kaza da ciccibi zuma gumba garin
daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya
mace! GARKUWAR MATA 👭👭 fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a
zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa!
kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi💯
Nono💯
Sanyi💯
Karin kiba💯
girmar hips💯
Ni'ima💯
Sabulai💯
Humra💯
Turarukan wuta💯
Matsi💯
Miski💯
Dilka💯
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a
turai😀 ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA👭 Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*

*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID
GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*

_MATAR SAYYADEE_

You might also like