You are on page 1of 92

mamanshakur Is all about novels.

Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KABILAR MU 45 TO ENDKAINE SIRRI NA 9 &10 →
KAINE SIRRI NA 1 TO 8
Posted on April 28, 2016 by mamanshakur
[4/25, 1:25 PM] Aishat Muhammad: [4/25, 9:10 AM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌
1
Sakamakon jin danayi anyi littafi maisuna “RA’AYINA”yasa na chanza na maidashi
“KAINE SIRRI NA”.

Ahankali nake tafiya cikin wani babban wuri wanda aka radama suna THE ATTORNEY ‘S
WORLD. Office din lawyoyi ne sunfi dari aciki,an kawata su da fulawowi da wasu irin
madubai da wutan lantarki masu kyau daban shaawa, koni m shakur na shigo wurin ne
Dan neman lawyer dazan bude company a wurin shi. Tafiya na cigaba dayi harna kai
gaban wani office sai naji ana hayaniya dariya nadanyi nace nafasa bude kampanin
dole na daukoma matsoyana wanga rahoto lol.

Bismillahi Rahmanir Raheem.

“RA’AYINA ne MUZZAMIL bazan auri wacce batai graduating ba,bazan auri under
graduate ha, nafison na auri wacce ta gama school,ta waye, duk inda zan shiga zan
iya zuwa da ita batare dajin ko darr araina ba”…da sauri dayan ya tari numfashin
shi yace “B maisa kakeda tsatsauran RA’AYI? Kaga niko Kullum burina na auri yar
sacandari, wacce zan koyamata komi,soyayya,girmamawa, biyayya, tsorona everything
B,duk yanda naso tayi zatayi,zan lankawasa na tankwara ta zuwa kowani position
danaga dama, kai mesa ka banbanta da sauran mutane?” Dan murmushi B yayi yace “RA’
AYINA kenan”, daukan keys din motarshi dake kan table yayi ya dago yana gyara
buturan gaban rigan shi daya bude idanunshi nakan bituran dayake makalawa yace
“dama na shigo ne nafada ma gobe zan shiga minna,Niger state, akwai wasu case
danakeda shi akasa, 3 days zanyi in sha Allah”. Muzammil yadan zaro ido yace “garin
da akai earthquake(girgizan kasa) jiya ne zaka?” Yakarasa maganan yana kallon B
dake kokarin makala neck tie dinshi batare da wani damuwa akan fuskarshiba,
Muzammil yace “badakai nake magana ba,earthquake akayi fa koyau saida nakara
karantawa a news kuma daga site wanda basa sa karya wato Vanguard news…” B ya dafe
kanshi murya chan kasa yace “God!” Dago kanshi yayi ya kalli Muzammil yace “will
you just listen to me, ba earthquake akayiba, Wani babban ginin bene ne ya rushe
mutane 5 sun mutu Allah ya jikansu, Gobe nidai zanje nai abunda yakaini” Muzammil
yaraka shi har wurin mota, shiga motar yayi ya zauna zaro taba kwara daya yay ya
makala a bakinshi, lighter ya dauko zai kunna yaji an fizge taban Muzammil yace
“Allah nakusa fadama mum kanashan taba,kasan baida kyau amma kaitayi niba gashi
nadena ba amma kai kaki”… B na ganin zai batamai rai yaja motan yay gaba batare
daya ce mai komiba.

Su uku aka zakulo daga ginin daya rushe ayau ranan jumma’a, inda jiya aka samo
biyar matattu,wurin gabaki daya bama ka iya ganin kona kusa dakai saboda kura dake
tashi,sai kukan mutane kakeji wayanda yan uwansu suka mutu sakamakon rushewan da
gidan benen yayi. Daya daga cikin Daktan da gwamnati ya kawo wurin dan bama wayanda
sukaji rauni taimakon gaggawa. duba mutane ukun yayi wanda da alamu baba Mata da
yarsu ne, ya dago ya kalli sauran yan uwanshi dasuka zageyeshi cikin rashin kuzari
yace “parent din are already dead yarinyar kuma ta bugu but tanadai rai, yanzu ai
informing government mutane 7 suka mutu, wayanda suka samu injury 35 hade da
yarinyar nan”.

Wani irin ihu yarinyar tasaki ta zabura tafado daga gadon, wurin iyayen nata tayi
tana kuka sosai babu wanda yahanata zuwa inda suke, tsayawa tayi tana kallonsu
idanunta sunyija sosai, tai shiru ganin haka likitan yabada umarni a wuce dasu
asibiti inda ake ijiye gawawwaki idan aka nemo yan uwansu sai abasu suje su burne.
Itakuma aka daurata kan gado ganin yanda jikinta ke rawa, aka bata magani sanan
suka cigaba da duba sauran wayanda sukaji ciwo. saukowa tayi daga gado batare da
kowa ya lura da itaba tafita daga barandan da gudu.
Gudu take iya karfinta tana share hawaye bata ganin na gabanta bata ganin na
bayanta ita tadaisan tana daga kafa tana gudu iska na kadata kwakwalwar ta abu daya
kawai take hango Mata lokacin da suke kan dining suna breakfast da Abba da Umma da
ita, sai sukaji Kara sukaji ginin na rawa ji tayi Abban ya janyota ya turata cikin
jikinshi ya daura bayanshi kan nata daganan saitaji jikin Abba yay Kara kaman
ballewan kashi, ahankali ya furta laa’ilaha illallah, tadaiji nauyi sosai ajikinta
takumaji abu nabin jikinta kaman ruwa, ihu ta dingayi tana neman taimako tana kiran
umma harta sume. Saikuma yanzu data farfado taji Abba da Umma sun mutu. Kara gudu
tayi na bala’i hawaye na tsiyaya daga idanunta Abba maisa baka bari ginin yafadomin
ba nima dukanmu mu mutu tare Maisa? Kummmm kakeji tabugu dawani gini block tafadi a
wurin sumammiya jini nafita daga goshinta.

Maman Abd Shakur😘


[4/25, 11:23 AM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

2
*washe gari*

11 na safiya tamai cikin garin Minna ahankali yake Jan motarshi ganin yakusa kaiwa
inda zaije. dan gajeren tsaki yaja awahale “mtswww” ya paka motar a gefen
hanya,juyowa baya yay ya mika hannunshi yadauko goran ruwan polar water dake back
seat, sanan yay amfani da dayan hannun ya bude motar yafita yafara waige-waige,
wurin shiru babu mutane dayawa sai kwarori dake wucewa, tafiya kadan yayi ya shiga
wata yar karaman hanya haka jikin wani dan gini inda yaga babu mai wucewa ya tsaya
yay abunda zaiyi ya maida zip yaja sanan ya juyo zai koma wurin motarshi yaji
alumun numfashin mutum, cigaba da tafiya yayi dan atunaninshi wani naman daji ne,
kaman ance ya kalli kasan wurin saiya ga jini, tracing dige digen jinin ya dinga bi
haryakai bakin wani gini da anfara ba’a karasa ba, tsayawa yayi shi bai shiga ba
shikuma bai juyaba waigawa ko ina yayi yaga babu kowa awurin yakara kallon kasan
yadaiga ga jinin da alamun koma wanene yana cikin ginin, bismillah yayi ya shiga
kai tsaye yafarabin sahun jinin harya kai bangon karshe, ganin mutum yay akwance
shame shame baya ganin fuskan daga inda yake saidai yaga zanin atampa ajikinta,
karasa wa yayi ya tsugunna gabanta yana kallonta sama da kasa, numfashi yaji tanayi
ahankali awahale hakan yasa yakai hannu ya juyo da ita yana mai karema fuskan ta
kallo “Subhanallah” ya furta ganin yanda goshinta ke fitar da jini da sauri yasa
hanunshi a aljihun wandon shi handki yaciro yadaura akan goshi yafara kallon ko ina
ko akwai any clue dazai gane daga ina take Kokuma yan uwanta,ko waya kowani abu,
dawo da idonshi kanta yayi jin tafara numfashin tana fito da harshe hakan yasa
yagane ruwa takeso rike kanta yay yadau ruwan yana bata ahankali ta shanye tass
sanan jikinta gabaki daya ya saki a hanunshi da sauri ya dagata yafito da ita daga
wurin har bakin titi yasata cikin motarshi sanan yaja da sauri dan nemamata lpy,
agaban wani babban hotel yay horn aka bude ya shiga ciki yay parking a wurin paka
motoci wasu mutane uku dukansu maza kowananen su rike da wata yar karaman littafi a
hannu suka budemai motan da sauri daya daga cikinsu yace “is already 12:PM, and
case din damuke dashi 12:10 za’a shiga” Fuzar da iska yayi ya dafe kanshi batare
dayace komiba, daya daga cikinsu yace ” your breakfast is ready ” da sauri na ukun
yace ” you have visitors sir” gajeren tsaki yasaki yay gaba, sai kuma yajuyo
akasalance yace ” akawai yarinya a mota, Johnson take her inside,and u Solomon ka
kira Dr ya dubata” yajuya yahau bene, dakin da aka tanada mussamman saboda duk
lokacin daya sauka ya shiga direct bayi yaje yay wanka ya chanza kaya suwa suit
baki da wandon shi sai takalmin min baki cover mai sheki, ya cire tabaran idonshi
da ruwan wanka ya tsalla akanshi ya goge ya mayar, ya fesa designers turare mai
suna kingdoms ya mike tsaye ya daura necktie sanan yafito daga dakin. dakin dake
kusa da nashi ya shiga yaga Dr Faruk yana dubata, kallon agogon hanunshi yayi sanan
ya kalli Dr Faruk yace “am late, anjima I will see yhu” ya bude kofa yasakai yafita
saikuma ya juyo kallon fuskan yarinyar yayi nadan tsawon sakonni sanan yasakai
yafita daga dakin P.A na binshi abaya da jakan laptop dawasu takardu a hanunshi.

Maman Abd Shakur😘


[4/25, 1:23 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

3
Karfe 4 na yamma yagama abunda zaiyi shida P.A a high Court na Minna suka fito,
saida yay sallan la’asar sanan suka dauko hanyar gida. yay wanka ya chanza kaya
zuwa na Shan iska ya zaro taba yana zuka anishadan ce wakan awww na tashi,
idanunshi a lumshe yaji anyi knocking bude idonshi yayi sanan yabada izinin shigowa
P.A ne ya shigo yace “kanada baki sir, tunna dazu ne basu tafiba” wani kallo yama
P.A tareda busar da hayakin taban sanan yace ” waiba nace karku fadama kowa zan zo
Minna ba, cases dake kaina are enough, banason anymore wahala” da sauri P.A yace
“ka gafarce ni, wasu couple s ne for d past one month sukeson ganinka kullum suna
kira nace musu bakanan, saisa nafada musu yanzu kazo” batare daya kalleshi ba yace
“sujira ni, ina zuwa”, saida yagama Shan taban sanan ya mike yadau lemon mint
yajefa abaki, yafito zuwa office dinshi nacikin hotel din yabada izinin ashigo
dasu, yana zaune aka bude kofa aka shigo Babban magidan cine da matarshi fara
kakkyawa mai kama da balarabiya, da sauri ya mike ya mikama mutumin hannu suka
gaisa ya nuna musu kujera suka zauna Alhajin yay magana da murmushi yace “BARRISTER
BARRAQ,tun randa mukaga firan da akayi dakai a African independent television (AIT)
my wife here, ya nuna hajiya tace dole mune meka,kallo daya mukaima mukasan kanada
gaskiya, kallo daya mukaima mukasan zamu iya fadama matsalan mu,haka kuma kaji
kakuma taimaka mana, kanadaga cikin lawyoyin kasar Nigeria masu tsayawa kan
gaskiya,da bima talakawa hakkinsu ga yawon taimako,kafin mu sanka muke jinka da
alkhairan ka ga jama’a” yakarasa maganan yana kallon fuskan B da kanshi ke kasa
baka gane yanayin dayake ciki, Alhaji ya cigaba ” yace aranan ashirin ga wata
agusta ta shekara 2015 muka wayi gari bamuga yarmu tilo maisuna RUFAIDA ba,munsan
agidan ta kwana tare mukaci abincin dare komi tare amma muna tashi bamu gantaba,
saidai mukaga dakin ta abude da alamun tafita, tundaga ranan babu inda bamu shiga
nemanta ba, mun sanar a kafafan sanar wa amma babu ita babu alamunta gashi shekara
na neman tafiya batare da munga yarmu ba har polisawa mun sanar mawa amma
shiru,tunda mukaji kana Minna yasa mukataho tundaga legas dan sanar dakai komi”
Matar da idonta yaciko da kwalla tace “Barrister shekaran yata 16 kacal a
duniya,dan Allah ka taimake mu ka nemo mana ita” takarasa maganan bakinta na rawa,
B ya sauke ajiyan zuciya yace “am sorry but aikin polisawa ne neman wanda yabata
baniba… Da sauri matar tace “Barrister ni nasan wani abu akaima yata amma Alhaji
yaki yarda,inaji ajikina wlh batun yauba dan Rufaida banda makaran babu inda take
zuwa”, Alhaji ya kalleta yace “zaki farako” tafashe da kuka sosai B ya saukar da
kanshi kasa dan ya tsani yaga manya na kuka, Alhaji yace ” Barrister wato tanada
abokiyan zama ne,sai jiya taji abokiyan zaman tana waya tana fadin suda ganinta har
abada wlh tariga ta shiga duniya kaman yanda tsuntsun ya shiga duniya… Shine fa
tunda taji take cewa itace tama yarta wani abu ta bace” B yadade yana nazarin
zancen, daga bisani ya kalle matar yarasa dawani suna zai kirata sai kawai yace
“Umma” ta dago tace “naam Dana” yace “zanyi nazari,zan kuma nemeku akaro na biyu in
sha Allah yarku takusa bayyana”, ya yagi wata paper yace “gashi komi kan yarku Ku
rubutamin, nadaga shekarun ta, yanayin ta,makaran ta datayi kawayen ta dadai komi”
Alhaji shiya rubuta sanan yabashi ya karba, Alhaji ya yaga check yarubuta kudi mai
yawa ya mika mai B ya girgiza kai yace “ganinta shine farko kafin payment Alhaji
nabarku lpy” yarakasu suka shiga mota matar nata godemai tana yaba halinshi na
kirki saida sukabar haraban hotel din sanan yakoma ciki, dakin yarinyar daya tsinta
ya wuce kai tsaye dan duba lafiyarta.

Tsayawa yayi akanta yana kallonta, ansa mata Karin ruwa ga bandeji a goshi, sai
ciwukan jikin ta da hanunta an wanke su,tai wani fayau da ita tai haske kaman Mara
jini. Murmushi yadanyi tunawa da duk inbaida lafiya Mum na zama taita Karanta mishi
English novels masu dadi tun yana Yaro,duk in yatambayeta maisa takeyi mai haka in
baida lafiya, saita cema Karanta ma Mara lafiya stories yana sa ya warke da wuri.
Murmushi yadan karayi yace ” O mother I missed yhu dayawa dayawa” yace “nima bari
na karantama dis little lady stories, yadan tabe baki yace who knows maybe itama ta
warke da wuri takoma wurin iyayenta dan anywhere dey are suna nemanta suma” yajuya
dan zuwa dakinshi ya dauko novel ya karanta ma yarinyar haryasa hannu zai bude kofa
yafita yaji tana magana” Mami tsuntsun mai dago baki yana Jana,zai tafi…Mami dani
zai tafi…Mamina “.

Maman Abd Shakur😘


[4/26, 9:02 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

4
Dawowa cikin dakin yay ya tsaya gaban gadon, addu’oi ya tofa mata saiyaji tai shiru
ta sauke ijiyan zuciya ta cigaba da bacci. Ya tsaya akanta nadan sakonni sanan ya
juya yabar dakin. ya dauko novel yana karanta mata a natse.

Karfe 10 na safiyan washegarin ta farka da addu’a a bakinta,ahankali take bude ido


bataga kowa a dakin ba, sai wani bakin akwati a gefen gadon,da katon littafi akan
drawer, mikewa tayi tadan zauna dudda batajin karfi ko daya a jikinta tana karema
dakin kallo komi pink. ruwan dataga yanabin hanunta ta cizge tareda wata yar Kara
“wayyo umma zafi” fadin sunan Umma yasa ta tuna da sun rasu fa yanzu, ta fashe da
matsanancin kuka.

Tsagaitawa tai da kukan tafara kalle-kallen dakin “to ina nake? Inane nan?wanan
hadadden daki fa?” Dakyar ta tashi tsaye taje gaban kofan data gani tana jijjigawa
amma taji arufe bayama girgiza,zama tayi a wurin ta dasa sabon kuka na rashin
iyayenta,masu sonta,masu walahan neman kudi dan suga tai karatu,wayanda suka mutu
ta sanadiyya ta tafashe da wani kukan toni maisa ban mutuba, banda kowa banda
DUDUWA.

Haka tacigaba da kuka sai Wuraren sha biyu sanan ta share hawayen, ta mike tsaye
tana neman makewaya dan fitsari takeji sosai, ganin wani kofa yasa tafada ciki
takoga bayine batasha wahalan bude shawan ba saboda inda Abba yasamu aiki irin
bayinne a wurin, wanka tayi tai brush ta wanke kayan data cire, sanan ta daura
sabon towel din data gani tafito tana dingisawa, akwatin kayan data gani gefen
gadon tabude, kaya tagani aciki kala biyu da hijabi baki, daguwan rigan ciki ta
dauka tasa tadau hijabin tasa ta kabbara salla, da kyar take sallan saboda jirin
datake gani, tana idarwa ta tashi zata koma gado, saidai tana mikewa ta zube a
tsakar dakin saboda jirin daya dibeta, adaidai lokacin ya bude dakin da sauri ya
shigo yana sanye da kayan Shan iska yakaraso da ya dagata ya daurata kan gado. Juyo
da fuskanta tayi dan taga Wanda taji yadaga ta, idanuwanta suka sauka kan kakkyawan
namiji, shiba saurayi ba shikuma ba Babban mutum ba,farine tarr kana ganinshi kasan
akwai jinin bature tattare dashi,idanunshi dauke da farin glas maikama Dana masu
ciwon ido.

Dago kanshi keda wuya sai idanunsu suka hade, kulle idonta tayi da sauri ta
kankame jikinta ganin yanda yacika mata ido,dakuma yanda kwayar idonshi ke bata
tsoro.

Baice mata komiba,ya komar da kanshi ga wayan dayake dannawa. Bude kofa taji anyi,
saikuma taji ance thanks Johnson, saitakara jin an bude kofa anfita. kara kankame
jikinta da idanunta tayi dan tsoron shi taji Allah ya saukar mata shikenan gidan
yan yankan kai! Cikin natsatsiyar murya taji ance “tashi kici abinci”, ko motsi
batayi ba, takarayin lamo, ahankali yakai hanunshi bakin katifar yadan bubbuga ” Hi
tashi kici abinci ” da sauri ta tashi zaune ta bude idanunta ahankali ganin abinci
tayi agabanta mai rai da lafiya,tea mai kauri saikuma faten wake dake dauke da
hanta da green vegetable sai aka zuba soyayyen plantain a sama,Satan kallonshi
tadanyi taga news paper yake Karantawa. zamo jikinta tayi ta zauna akasa dan ita
ko agida saidai Umma a Abba su zauna a dining ita akasa takeci, data zauna ta sauko
da Trey din abincin a gabanta, tadau tea din tafara sha harta shanye tass, sanan ta
jawo faten waken tana wasa dashi, tun tana yar karama batacin wake, sai kallon
waken take ita bataci ba ita batai magana ba,bude kofa taji anyi an shigo yace
“gani sir” batareda ya kalleshi ba yace “take d Beans away,ka kawo mata wani abinci
batacin beans” da sauri ta kalleshi saikuma ta sauke kanta tana mamaki ya akayi
yasan batacin wake?

Maman Abd Shakur😘


[4/27, 9:30 PM] Aishat Muhammad: [4/27, 8:35 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

5
Shinkafa Johnson ya kawo mata ta karba tadanci kadan tasha ruwa ta tura gefe taci
gaba da wasa da yatsunta. kaman daga sama taji yace” kina bukatan wani abu kuma”
girgiza mai kai tayi, bai Kara cemata komiba yacigaba da karatun news paper dayake
yi.

Karfe 6 ya linke newspaper ya kalleta yaga har yanzu tana zaune a kasa da
zumbulelen hijabin tai wani iri kaman marainiya, tausayi kawai yaji tabashi
yakaraso gaban gadon ya tsugunna kusa da ita da sauri ta kulle idonta gam, dan
murmushi yayi sanan yace “ya sunanki?” Batace komiba, akaro na biyu yace “bude
idonki” ahankali take budesu tadan kalleshi ganin ita yake kallo yasa ta kauda
kanta ta kalli gefe, hannunshi ya daura akanta ya juyo da fuskanta suka fuskanci
juna yace”I said ya sunanki?”

Kukan datake kokarin hadiyewa ya kufce mata ta fashe da kuka sosai ko ina na
jikinta na rawa,ganin haka yasa yacire hanunshi daga kanta yadan ja baya. a natse
yay magana ganin ta tsorata dashine”Hi am not going to hurt yhu, taimakon ki zanyi
karki tsorata dani kinji? dazaran kin warware zan maidake,don’t be afraid of me”
shiru yadanyi ganin ta tsagaita kukan tana share jajayen idanunta tana kallonshi
adan firgice,yakara kwantar da murya irin na lallaba wanda ya tsorata yace ” ki
kwantar da hankalin ki kinji,zanje masallaci kinason na siyo miki wani idan zan
dawo?” Ta girgiza kai tana share hawaye, yace “ok,oya tashi kije kiyi sallan kema”
da sauri ta mike kaman jira take tayi hanyar bathroom tana kallonshi kaman zaibita
kumm! ta bige kanta da kofan bayi garin kallonshi rike goshin tayi ta shiga bayi da
sauri ta Danna key. Girgiza kanshi yay yatashi yafita daga dakin.

Bayan sallan isha ya bude kofa ya shigo dakin tana zaune kan dadduma da sauri ta
mike tsaye ta make ajikin bango, ajiye abunda ya shigo dashi yayi yajuya yafita
daga dakin. sauke ajiyan zuciya tayi sanan tacire hijabin jikinta ta zauna abakin
gado ta bude ledan, lemun kwali ne da kaza,dayan ledan kuma chocolates ne da
cingums, ajiyesu kawai tayi tafada kan gadon ita kadai tasan yanda takeji.

Maman Abd Shakur😘


[4/27, 9:28 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

6
Kwananta uku tana jinya harta warke tai ras,tsawon kwana ukun nan magana baitaba
hadata da mai gilashi ba( sunan data rada mishi) saidai abunda tagane game dashi
“mutum ne mai tausayi gashi da lallaba Mara lpy, kullum haka yake riritata yana
tambayan metakeso yakawo mata,kayan kwalama kala kala yake kawo mata kaman baby,
amma bazata taba bashi amsaba, yacika tausayi danta lura ya tsani yaga tana kuka.
Itadai har yanzu mai gilashi tsoro yake bata saisa ko eh bai taba hadata dashiba
baitabajin ya muryarta takeba”.

Tana cikin tunani taji anbude kofa, da sauri ta gyara hijabin jikinta, kallonta
yadan yi wani abu yadan gitta zuciyarshi me yar yarinyar nan ke nufi? Maisa duk
lokacin dazata ganni sai tawani sa hijabi? Mezanyi da ita? Mezan gani? Metake
dashi? Abun yadan batamai rai amma saiya basar yakaraso ya zauna akan kujera.
kanta na kasa yace ” petient naga kin warke ko?” Ta girgiza kai,yace “to
Alhamdulillah, inaso nasa a komar dake gidanku ne dama saboda nasan duk inda
iyayenki suke suna neman ki, and also maiya faru dake harna ganki a wurin nan a
sume?”

Dago kai tayi zatai magana saitaga ita yake kallo. kaman kullum jikinta yahau bari
ta fashe da kuka, kuma takasa daina kallonshi, mamaki take bashi wai yarinyar nan
is she alright, anya batada matsala, da sauri yadan ja kujeran shi ya matso kusa da
gadon ahankali yace “ke kurma ce?” Da sauri ta dagamai kai, tausayin ta yaji sosai
yace “to ai basaikinyi kuka ba idan namiki magana kinji?” ta girgiza kai, yace “to
share hawayen ki” ta share da gefen hijabin jikinta, “Kinyi iya rubutu?” Yakara
jefo mata wani tambayan, ta girgiza kai alamun eh. mika mata byro da memo yayi
“rubutamin inda iyayenki suke” kallonshi tayi ta kalli memo dayake mika mata da
fararen hanunshi, kasa karba tayi, ganin haka yasa ya ajiye mata akan cinya “oya
rubutamin na Karanta” ahankali tadau memo tafara rubutu kaman haka
“Abba na da umma na sun ra..
Kasa karasawa tayi ta kifa kanta a book din tafara kuka dan mutuwar takara dawo
mata, tashi yayi ya daga kanta ya zari memo ya karanta sanan ya kalleta yace “sun
rasu??” Dagamai kai tayi cikin kuka, yakara jefo wani tambayan “ance wani gida ya
rushe mutane sun mutu dayawa kune,iyayenki na cikine?” Da sauri ta girgiza mai kai,
“dis morning naji a news ana neman wai young lady iyayenta sun mutu amma ita an
nemeta an rasa,cos gamnati nason bata tallafi,kece yarinyar?” Ta girgiza kai cikin
kuka, dafe kanshi yadanyi sanan ya zauna akan gadon ya dago kanta yakai hanunshi
ya share mata hawayen “is OK,in sha Allah nai alkawarin I will help yhu kinji” ta
dagamai kai tareda matsawa baya. “Kinada yan uw… Bai karasa maganan ba saboda jin
ana knocking, bada izinin shigowa yay Johnson ya shigo Sir kanada bakuwa? Yace
waye? Is Nana sir” dan karamin tsaki yayi yace ina zuwa ”

Baikara cewa komiba, yay shiru tadan kalleshi taga kaman ranshi abace yake hakan
yasa takara makewa a jikin gadon, kusan minti 5 sanan ya mike ya kalleta idan
kinason zuwa waje kisha iska dakina shine agaban naki ki shigo kifada min zansa
akaiki yajuya yafita.

Shiga dakinshi yayi ya mugun daure fuska ganin wacce ke tsaye cikin wani arnen kaya
wanda dashi gwara babu, kakkyawar budurwa ce ajin karshe,tana zaune kan gadonshi.
“u again! Nana maiya kawoki wurina? Nafada miki stay away 4rm me”Fari tayi da ido
ta langabar dakai “haba My B,maisa kakemin wulakanci dan kaga kanada kyau na mutu a
kanka,ina sonka?” Tsaki yay yadafe kanshi kafin yadago yace “kitashi ki fita, get
out kafin nakira securities su fitarmin dake” kada kai tayi “ok shikenan inkasan
wata bakasan wataba, kakosan wacece mac.. “I said get out Nana” ya daka mata
razanan nan tsawa batare da yabari ta gama magana ba. mikewa tsaye tayi tana
kadamai jiki da kayan dasuka mugun matseta, matsawa gefe yayi dan ta wuce, saida
tazo daidai kusa dashi cikin kyaftawan ido batare daya luraba yaji ta zare glass
din idonshi, tasa cikin jaka da sauri takoma gefe tana dariya.

Cikin fushi yace “kiban glas dina,wai wot is ur problem Nana” “ai wlh My B kafin
nabar dakinan saina tabbatar nadau cikinka Kota yayane sai Inga idan ka isa kace
bazaka aureniba bancin inada cikin ka” ahankali yake daga kafa yana mika hannu
kokarin shi shine ya gano saitin datake magana, dariya tayi ciki ciki ta koma gefe
tana cire kayan jikinta.

Masu karatu makaho ne wai?ko matsalan ido gareshi?

Maman Abd Shakur😘


[4/28, 9:51 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

7
Ya dakamata tsawa Nana! “Kiban glass kafin na saba miki wlh,nace kiba..”bai karasa
maganan ba saboda jin bakinta acikin nashi tana wani shasshafa bayanshi, jikinshi
yaji yamutu yakasa tureta, yakasa aiwatar da komi. yana kokarin magana takara tusa
harshenta cikin nashi…
Ahankali take tura kofan dakin tanadan hawaye, yatsanta na jini saboda yankewan
datayi da nail cutter dabata taba ganin irinshiba. Shiganta dakin keda wuya tasaki
wani razanannen ihu wanda saida yasasu firgicewa Nana tasakeshi da sauri tana
kokarin jawo abu tarufe jikinta, ihu tacigaba dayi ta kukkulle ido dan ita bata
taba ganin mace ba kaya a jikinta ba. Nana takoma baya dan kallon aljana take mata
dan bataji alaman shigowan mutum ba saidai ihu, Barraq ne yadan tattaro karfin
magana yace “ban eyeglasses dina” da sauri Nana ta dauko jakanta taciro glass din
jikinta na rawa ta sakamai a hannu, sawa yayi yajuyo yana kallon yanda take ihu ta
kulle idanu tsugunawa a gabanta yayi yace” lafiya ” Kara fasa ihu tayi tana
cukuikuye hijabin jikinta tana Kara matsawa jikin garu, ganin kaman ta zare yasa ya
juyo da kanshi ya kalli Nana datake tsaye tana kallonsu kauda kanshi yay yace
“malama kisa kaya kificemin daga daki,believe me inna dawo na ganki u will see my
other part” ya tashi ya dagata chak yafita da ita daga dakin, Kara kurma ihu tayi
tana wunsula kafa ya bude dakinta ya wurgata kan gado tacigaba da ihu. ” keep
quiet! Ya dakamata tsawa Idanunshi sukai jajir “one more ihu saina zaneki wlh,
spoiled brat” ya fice daga dakin tareda bugo kofan yakoma dakinshi dancin uban
Nana, saidai yaga batanan tariga ta tafi, zama yay gefen gado ya zaro taba ya kunna
yafara zuka saida yasha Kara 4 sanan yaji bacin ran dayake ciki yaragu, bayi ya
shiga yakarayin wani wanka yasake kaya.

Wayanshi tayi Kara ganin sunan mai kiran yasa ya dau wayan da sauri tareda zama
akan kujera.
” Barrister Barraq! I just got ur email, so yanzu yarinyar natare dakai?” Ya amsa
“eh tana tareda ni,u can come over ka ganta,badai tagama warkewa bane,tunda tamin
bayani itace wacce parent dinta suka rasu shine nace is better na sanar daku dan
adaina nemanta,but plan dina sir zan riketa I will train her and sponsor her
education, inajinta kaman sister na,zanyi signing everything gobe inmun hadu a
Court, tadawo under my custody,mace ce abu kadan ne zai iya lalata mata rayuwa,idan
ban dauketaba bansan ina gawmnati zata turataba,orphanage?gidan marayu? Who knows,
zan dauketa kawai” dayan yace “ok,I trust yhu Barisster, nasan u will take good
care of her,come over later ka karbi kudin da government yabata” Barisster yadan
yamutse fuska “no need of dat sir inada enough money dazan kula da ita” Minister
yace “but still gawmnati yabata,kazo ka karban mata is her right” Barisster yace
“ok,anjima zanzo na karba, thank yhu sir,I appreciate”
Tashi yayi yadau 1st aid box yafito ya wuce dakinta ganinta yay zaune kan gadon,
tana ganinshi taja baya, baice mata komiba dan yasan yanda taganshi da Nana ne
yajawo haka, “ban yatsan” Kalmar daya fada kenan, ahankali ta mika mishi tana
matsar kwalla sai alokacin yagama karamin ciwone, yadan wanke jinin sanan yace
“dena kukan ki kwanta kiyi bacci” kwanciya tayi ta lumshe ido shikuma yakoma kan
sofa ya zauna yana karanta newspaper.

Ajiye newspaper yayi ya dafe kanshi yana cije lips, kwata kwata ya rasa
natsuwarshi,Nana ta dagulamai lissafi tsaki yayi yazaro taba daga aljihun rigan
dayasa ya kunna yafara zuka. Jin warin taba yasa ta bude ido ta juyo da kanta da
kalleshi gabanta yay mummunan faduwa ganin yanda yakeshan taba, lumshe ido tayi
tana maganan zuci na shiga uku,wlh bazan kwana anan ba yau,gwara na koma wurin
Duduwa koda kasheni zatayi, wanan mutumin dan iskane, malam ma yace Annabi yahana
zaman mace tareda namijin daba muharraminta ba a wurin daya. wayyo umma na maisa
kuka mutu? Yanzu waye zaitaba rikeni?? hawaye take sharewa tana tausayin rayuwar
ta, jin anbude kofa yasa ta juyo da kanta taga fita yayi.
Daki yakoma ya chanza kaya zuwa suit mai ruwon toka ya fashe jikinshi da turare
yafita yaja mota zuwa gidan Minister.

kallon kujeran daya tashi tayi taga wallet dinshi akan kujeran daya tashi, ahankali
ta mike tsaye tana gyara hijabin jikinta takarasa wurin wallet din ta dauka hanunta
na rawa budewa tayi taga yan dubu dubu ne sababbi hannu ta rawa yafara da kyar ta
iyakai hannu ta zaro dubu daya guda biyu ta maida ta ajiye jikinta na rawa tajuya
tafita daga dakin da gudu, waige-waige tafara dan batasan hanyaba bene ta hango tai
gudu tabi benen har ta sauka kasa tafito compound din sai alokacin tagane hotel ne
danga sunan anrubuta Barraq’s aroyal hotel. Saidai inda tafito taga bangarene daban
da fannin hotel din, gate tabi tafita da gudu tana share hawaye “dan Allah
kayakuri, in sha Allah zan biyaka kudinka,wlh bana sata,niba barauniya bace, bazan
iya zama da dan iskaba” takara gudu dan taji anfara kiraye kirayen mangariba,
tana kaiwa titi ta tare adaidaita ta shiga wuf yace “malama ina za’a kaiki?”tace
“tashan shiga mota”.

🖌KAINE SIRRI NA🖌

8
Isansu tasha keda wuya tabiya mai adaidaita kudinshi dari biyu, sanan ta shiga
motan daizai kaita garin Jigawa! Ta biya kudi 1500.
Kuka sosai take acikin mota tana tuna farkon ranan dasuka zo daga kauyen gunjugu
itada Abba da Umma zuwa nan garin Minna, wai yanzu shikenan Abba da Umma sun tafi?
Duniyar kenan cewar wani bangaren zuciyar ta,addua kawai zaki dinga musu. matar
dake gefenta tace “lpy baiwar Allah kike kuka?ko tsoron tafiyan dare kike?”
Girgiza kai tayi tace “a’a Mama kaina ke ciwo”, “Allah sarki Allah sawake, ya
sunanki?” Cewar matar, lumshe ido tayi tabude sanan tace sunana “RUFAIDA”!.

Maman Abd Shakur😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 1 TO 8KAINE SIRRI NA 11 to 13 →
KAINE SIRRI NA 9 &10
Posted on April 29, 2016 by mamanshakur
[4/29, 8:37 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

9
Wuraren karfe 11:30 na dare ya dawo, Solomon yakira ya kwaso mishi kayan cikin
motan,katon ganamasgo ne wanda naira miliyan 2 ke ciki,wanda gwamnati yabata sai
katoton akwati daya biya super market yayo mata shopping kaya nasawa da dama dakuma
hijabai manya tunda ya lura ita ustaziya ce, saikuma dan kayan ciye ciye daya siyo
mata,murna sosai yake dan gobe bayan yadawo daga Court zai koma Abuja, visa zai
mata yakaita Russia wurin Mum,tana mugun son yara,shikadai ta haifa dan yama sanar
da ita yasamo mata yarinya,iyayenta sun mutu,mamarshi tanata murna zata samu yarda
zata kula da ita. zai kaita wurin Mum tai makaranta a wurin.. maganan Solomon ya
katse mai tunani “sir dakinka zankai kayan kona madam?”da murmushi akan fuskanshi
yace “shigar dasu dakinta ka ajiye, idan nai wanka zan shiga wurin”, ya wuce
dakinshi yayinda shi Solomon ya bude dakinta ya ajiye kayan a gefen gado bai damu
da rashin ganinta ba dan yazaci tana bandaki ne yafito ya mayar da kofan yarufe
yatafi wurin kwananshi.

Bayan ya gama wanka,ya sanya pyjamas din bacci ya kalli agogo lokacin yaja dare
yariga yaraba, dan alokacin 12 na dare yadan gota, tunanin dayayi nacewa yanzu haka
tadade dayin bacci yasa kawai yaja bargo yay baccinshi gobe da safe kafin sutafi
Abuja yamata bayani.

Karfe hudu na asuba tai musu a tashan garin Jigawa,sauka tayi sukai sallama da
matan,tace” to Rufaida Allah Kara hada fuskokin mu,mijina yazo daukana”ta sunkuyar
da kanta tana wasa da yatsa “to Mama Allah kaiki lpy,agaida yara”. Tasamu tadan
zauna akan wani kujera da aka tanadarma masu tafiya bacci yadan dibeta sai Wuraren
5 na safiya sanan ta tashi taje jikin wani dan masallaci dataga mutane ta dibi ruwa
tai alwala sanan takoma Chan gefe guda tai sallolin da ake binta,sanan tai
ra’atanil fajir saitai sallan asuba.
Karfe shida ta shiga motan dazaikaita kauyen GUJUNGU itakadai ne aciki ta biya dari
biyu kudin mota. tai shiru kaman marainiya tana kallon mutanen wurin dasuke Shan
koko da kosai,kaman taje ta roka saboda yunwar dake cin cikinta hakanan ta daure
sai Wuraren 8:30 motar ya cika sukadau hanyar kauyen gujungu.

Bayan yagama al’adunshi na safe,ya fito cikin 3quater dayar short sleeve dinshi
fara fat yana rike da karamin kofin coffee ya tura kofan dakinta ya shiga,ganin bai
gantaba yasa yakoma kan kujera yay crossing legs yana Shan cofee a nishadan ce,
yadau remote ya kunna TV bango,atunaninshi tana bayi, ajiye cup din coffee yayi
akan stool din gefen kujeran ya kalli agogon hanunshi almost 15 min da shigowan shi
batafito daga bayi ba kuma baimaji alamun saukan ruwa a bayin ba. Tashi yayi da
sauri ya tsaya a gaban kofan bayin ya kwankwasa ” Hi sister kina ciki?” Yaji shiru
da sauri ya bude bayin yaga babu kowa aciki, a rude yasaki kofan bayin ya juyo sai
alokacin idonunshi suka sauka kan wallet dinshi daya gani a bude wasu ID dinshima
akasa sun zube karasawa yayi yadaga ya mammaida ya kulle sanan ya fita zuwa kasa
dakinsu Johnson ya tambaye su kunga yarinya na? Kowa yace a’a,yace “Solomon jiya
dakaje ajiye kayan nan baka ganta acikiba?” Yace “no sir,babu ita I thought tana
bayi saisa ina ajiyewa na fito na kulle kofan”, Barr yace”God! I pray yarinyar nan
ba guduwa tayiba” yakarasa wurin securities masu tsoron gate ya tambayesu wanda ke
duty jiya yace “Sir jiya duk Wanda suka shigo hotel dinan dawayan da suka fita babu
wacce tasa hijabi,sai wata yarinya black beauty haka sir,batada kiba sosai, kuma
batada tsawo sosai,quite sure naga daga part dinka tafito da gudu,she was crying
self lokacin datafita”.

Barr Barraq yace” damn it,wot is your problem mandawari?,kaga karaman yarinya
tafito daga part dina tana kuka baka tsayar da itaba”,yakara dakamai tsawa “Kaine a
duty ranan Dana kawo yarinyar nan wurin nan,u saw lokacin dasu Johnson ke shigar da
ita ciki,but duda haka u let her go”, mandawari jikinshi na rawa yace “sorry sir,a
gafarceni,wlh ranan ba kalli fuskanta da kyau bane” ya kalleshi da jajayen idonshi
yace “u no nothing akan job dinka,so just pack ur things nd go, nakore ka” yajuya
yakoma ciki Johnson da Solomon suka rufamai baya,mandawari yafashe da kuka ya zube
akasa “dan Allah kayakuri sir,wlh bazan Kara kuskure hakaba” ko juyowa baiyiba daki
yakoma ya dauko car keys,ya fito ya shiga yaja motan da bala’in gudu yana zukan
taba yabar hotel din.

Maman Abd Shakur😘


[4/29, 8:37 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

10
A daidai kauyen gujungu aka sauketa,ta sauka tana tunanin uban tafiyan dazatayi
kafin takai cikin kauyen, a hankali take daga kafa take tafiya tana Kara kallon
kauyen rabonta da kauyen kusan wata shidda kenan, cikin sa’a taga mai amalan ken
data Sani abokin Abba ta tsayar “Baba ina wuni” tafada tana murmushi Kara kallonta
yayi yana goge idanu “wanake gani? Rufaidatu ce?” “Eh Baba nine”, ya sauri yace” a
hayo, hayo mana, hannu Rufaidatu” tahau kan amalan ke,ya shau dama jakunan bulala
suka fara tafiya, sanan yace”Rufaida ya hakuri? munji Malam Musa,da Asiya sun rasu
daga bakin Duduwa,dan hargarin nan wasu polisawa sukazo ana nemanki,aka kuma sanar
damu rasuwan iyayenki ta hanyar rushewan gini”. Hawaye ya cika mata ido
“Alhamdulillah Baba” yace” Amma Rufaida maiyasa ki kara dawowa kinsan yanda Duduwa
ta tsaneki,duk yanadaga cikin abunda yasa Musa marigayi ya Tattraku yabar kauyen
daku saboda jaraban mahaifiyar shi Duduwa” cikin kuka tace “Baba banda kowa, sai
Duduwan dole na dawo koda kasheni zatayi”, girgiza kanshi yayi yace”hakane Rufaida
karki damu Allah natare dake,ki dage da addu’a Allah ya dauraki akanta ” tace” to
Baba nagode”.

Haka suka dinga fira sama sama harsuka shigo cikin kauyen. Kauyene sosai, ko ina
yara da yanmata anci atampa daban riga daban dan kwali daban ga dige dige a
fuskannan sai kallonta suke dan basu ganetaba tasha hijabi abinda basu saba ganin
yan matan garin na sawaba, a kofar gidan Duduwa ya sauke ta, ta sauka amma tasami
kanta da kasa shiga gidan saboda tsoron Duduwa, kuka tafashe dashi sosai tana
yarfe hannu, Baba ya tausaya mata yace” Rufaida ki shiga da bissmillah Allah na
tare dake kinji yata karkiji tsoro” ta goge Hawayen wasu na zubowa tace “to Baba
nagode”

Bude buhu kofar gidan tayi ta shiga ahankali tana tafiya a zauren, kunenta suka
juyo muryan Duduwa na rera waka”Ladi mai kidan kwarya aja kida asha dadi …ari, kai
anata sabon daa wayake ta tsohon da.. Ari, saidai munafukai su kalleni Niko ai
inada nerori ..Ari, Alhakumu aljanna kubari infadi da hillanci.. Ari”

Hawayen idonta ta share, jikinta na rawa, ahankali ta rera sallama “Assalamu


alaykum”

Maman Abd Shakur😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 9 &10KAINE SIRRI NA 14 to 16 →
KAINE SIRRI NA 11 to 13
Posted on April 30, 2016 by mamanshakur
[4/30, 10:47 AM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

11
Duduwa ta bude zip din lalitar jikinta ta zaro yar guntuwar goronta ta Balla sanan
ta amsa”waalaika salamu,higo” ta shigo cikin gidan jikinta na rawa “Duduwa ina
wuni”, da sauri Duduwa ta ijiye tabaryan hannunta ta mike tsaye baki abude tana
kallon Rufaida, ” bakar mayya mekika dawoyi? Kindawo kasheni ne nima? Kin kashe
Dana Musa da matarsa Asiya shine yanzu kika biyoni nima ki kashe” Rufaida ta tsaya
tana share kwalla tace “wlh banina kashe suba Duduwa,gini ne yafado akansu” da
sauri Duduwa tace “to dan ubanki juya kibar gidana,dama ai duniya kika shiga ki
koma Chan inda kika fito ki barmin gida,Alhamdulillah dama Wanda ya kawoki ya mutu
dan haka babu Wanda ya isa yanzu yahana ni koranki, wuce kibarmin gida” kuka
tafashe dashi sosai tazo dagudu ta tsugunna agaban Duduwa ta dan Allah Duduwa karki
koreni babu inda zani banda kowa wlh” ta hankada ta”,sakenmin kafa, da Chan dakika
shiga duniya dawakike tare,kina gidan karuwai ko?” ta girgiza kai tace “A’a, dan
Allah Duduwa kibarni na zauna”, Duduwa ta turata da kafa ta fadi “dan ubanki tashi
ki barmin gida bazan iya zama da karuwa irinki ba, nizaki rainama wayau kafin a
haifeki da shekaru dari nake duniya,daga ganin yanda kikai danya danya dinan
kinwaniyi huras(fresh) cikin shegema gareki” ta finciki tabaryan datake daka fura
dashi tace “tashi ki barmin gida” da gudu ta mike tayi hanyar fita tana kuka kaman
za’a zare ranta, Duduwa takoma tacigaba da dakanta tana sauraran yanda Rufaida ke
banka uban kuka, kome ta tuna sainaji tace “Faida” da sauri Rufaida dake kuka a
zauren tace “naam” Duduwa tace “yaki” ta shigo, “dau tulu kije ki dibomin ruwa a
rafin,idan kin gama ciccika randunan saikije ki gyara bukkan Chan shine dakinki” ta
nuna mata wani bukkan Kara,da ake ajiye tumakai aciki da.

Murmushi tadanyi saboda dadin Allah ya daurata kan Duduwa zata yarda ta
zauna,”bazaki wuce ki dauki tulu ki tafi ba shegiya mai kama da ifiritu”cewar
Duduwa, da sauri taje kusa da kitchen tadau tulu ta juya zata tafi Duduwa tace
“zonan” taje gaban Duduwa tana dar dar,mekuma tayi?
wukar dake gefen Duduwa ta dauka saida Rufaida taji tsoro Duduwa tasa wukan ta
kyasta hijabin dake jikinta tundaga sama har kasa tana masifa “da da wanan shegen
kimar(dogon hijabi) dinan zaki fita, shegiya rubabbiya, bakisan aurar dake
zanyiba,kinwani sa wanan abun wazaiga jikin naki haryaso,wlh duk randa nakara ganin
kinsa kimar kin fita saina kusa kasheki da duka,wuce daki zakiga wani tsumma danake
goge kasa ki dauka kisa ki cire wanan na jikinki,anjima idan dillaliya tazo na
siyar nasamu kudin saro sabuwar gyara”.

Ranta baiso ba,dan taso ta dinga tuna mutumin daya taimaketa ta hanyar ganin wanan
doguwan rigan mai kyau kullum,chanza kayan tayi tasa tsumman da Duduwa tace sai
warima suke hakanan tafito tadau tulun tace “Duduwa natafi” ko kallonta Duduwa
batayi ba kirga fura take. Tajuya tafita tana tafiya ahankali, daga gidansu zuwa
rafi badai nisaba,dan kusan karshen kauyen rafin yake.

Maman Abd Shakur😘


[4/30, 11:03 AM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

12
Barr Barraq babu inda baije ba agarin Minna neman taba,hatta inda ya tsinceta saida
yaje,ranshi yabaci iya baci,yanzun ina taje? Ina ta shiga? Ga dukiyarta a hanunshi
yazaiyi da ita? yunwa yasa ya kalli agogo yaga karfe 4 na rana a bakin wani
masallaci ya paka yay salla sanan yabiya wani eatery yasai meat pie da Vita milk,
dawowa mota yayi ya zauna ya dauko meat pie din zaici jiyayi ya tsani meat pie din
yay wurgi dashi ta glass din mota, ya kunna taba kawai yaja motan yay gaba hotel
yakoma su Johnson namishi magana ko kulasu baiyiba ya wuce dakinshi ya fada kan
gado. Saikuma ya tashi yadauko wani karan taban yasha sanan yadanji bacin ran
yaragu. wani dan abu naga ya danna a gefen gadonshi saiga Solomon ya shigo ahankali
yace “kiramin P.A” ba adadeba PA ya shigo, Barr ya kalleshi yace “PA inaso kaje
banki ka bude new account ka zubamin wanan kudin aciki,gobe ne zamu koma Abuja,
bazamu iya komawa yauba” PA ya amsa da to yadau Ghana masgon da yaga Barr na
nunamishi yafita daga dakin, tashi yayi yawuce yay wanka.

Sai Wuraren issha tagama cika randunan da Duduwa tace ta cika,ta gaji iya gajiya
taje zata dibi ruwa taje tai wanka taga Duduwa ta haskota da tocula ” mezaki min da
ruwa?”da sauri ta rufe randar tace”dama wanka zanyi” Duduwa cike da masifa tace”
akace miki wanan ruwan na wankan ki neko,shegiya mai kama da ifiritu,idan zakiyi
wanka kinsan hanyar rafi kuwuce kije ki debo,ruwan nan bana amfanin ki bane” ta
tashi daga wurin tadau buta tai alwala, kallon dakin Duduwa tayi taga bata falo
alamun tana uwar daka, da sauri taje dakin mamarta kafin subar kauyen ta shiga da
kyar ta lalubo wani yamutsartsen hijabi hakanan tasa tai salla sanan tacire tafito
ta zauna abakin kofan Duduwa tai shiru. gyangyadi na daukan ta saboda gajiyar
datayi. Kwal taji anbuga mata wani abu abaya da sauri ta tashi tana Sosa wurin
saboda azabar zafin dataji, Duduwa tace “wanan kazamtacciyar jikinki zaki wani
kwantamin a tsaftatacciyar bakin kofana mayya, yi Chan” ta nuna mata gaban
bukkanta,tajuya tana Sosa wurin da Duduwa tabuge ta tana kuka,”zonan! Duduwa ta
daka mata tsawa “ungo”,Tamika mata ragowan tuwon dataci tarage,da sauri ta karba
tareda fadin “nagode Duduwa”, taje gaban bukkanta ta zauna taci ko koshi batayi ba
amma bata damuba tunda tama samu Tabata, ta tashi zataje tasha ruwa,harta bude
randa Duduwa ta haskota da tocula “wlh inkika tabamin ruwa sainaci kan ubanki,kona
alwala Dana bari kikayi shima dan ubangiji zakima ibada wuce kibar wurinan ki shige
dakinki kiyi bacci”.

Da sauri ta shiga bukkan, ta zauna ta baki-bakin kofa,dan cikin bukkan duhu bata
ganin komi,gashi kauyen ba wuta,tsoro takeji na bala’i. a zaunen tafara bacci sama-
sama jin kaman kwaro nabin jikinta yasa tasaki ihun bala’i tafito tsakar gidan tana
ihu, da sauri Duduwa tafito daga dakinta tana Kara gyara daurin zani ta daura mata
dundu abaya tace ” shegiya bakar mayya,to wlh Kinyi kadan kihanani bacci, lpy
kikemin ihu?” Da kuka tace “Duduwa kwaro kebin jikina wlh” Hannunta Duduwa taja ta
haska dakin da tocula duk kyankyasai na bayi kebin kashin ragunan wurin,Rufaida
takara ihu tarike Duduwa tace “kingansu kk Duduwa” Duduwa ta hankadata ciki,ta
jawo kofan bukan ta rufe tana masifa “dan ubanki su cinyeki,Allah sama ki mutu
kaman yanda kika kashemin Dana da matarshi”, ta ciro kwado daga lalitar jikinta
tasa tajuyo tanajinta tana ihu amma ko das bataji arantaba, saima masifar data
cigaba dayi “Marigayi Musa bakajin magana, kawai ka tsinto yarinya ka tsinto
jaraba,gashinan ta hanani yin bacci,to wlh duk maitarta Ni bata isa ta lasheni ba,
yanda kika kashemin da Ni da wahala zan aikaki barzahu” tahau yar gadon bunun ta ta
kwanta,tana korafi.

Maman Abd Shakur😘


[4/30, 12:17 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

13
Rufaida dataga ihu da jijjiga kofa bazai fisheta ba saita make ajikin kofan tama
kasa hawaye,Umma tafado ranta,””lokacin kafin Abba yasamu aiki subar kauye suje
Minna Duduwa ta taba kulleta a wanan dakin lokacin tun ragunan ma naciki,haka Abba
da Umma suka roketa amma taki budeta,Umma tadaga haka saitazo ta tsaya a bakin
kofan tace Rufaida ki dinga fadin A’uzubikalimatillahi tammat min kulli sha’in ma
kalaq” tunawa da addu’a da Umma takoya mata yasa tafarayi ahaka har bacci ya
kwasheta Wuraren karfe 1 na dare batare dataji kwaro yahau jikinta ba ko wani abu
ya cijetaba.

Karfe 5 na asuba taji an zaulamata zabori a cinya, a firgice ta mike tsaye taga
Duduwa ce, tace”Ina kwana Duduwa ” Duduwa ta kalleta shekeke tace” karuwa,watoma
yanzu baccin karuwai kikemin a gidako? Bacci babu zani a jikinki”da sauri tadau
zaninta daya warware saboda nauyin bacci ta daura,Duduwa tace “wuce ki share tsakar
gidan nan tass,sanan kidau gero ki surfa na fura,wuce kitafi kin tsàya kina
kallona” da sauri tafita daga bukkan tana daga kafanta da kyar saboda mugun ciwon
maran datake ji, haka takarasa sharaan gidan ko salla Duduwa bata bari tayiba
tamiko mata geron tace “ungo surfe min su” ta karba ta yayyafa ruwa ta juye a
turmin tafara surfewa Duduwa ta wuce daki danshan kokon ta da kosai.

Jin cikinta na ciwo sosai yasa ta rike tabaryan ta tsugunna a wurin tana cije lebe,
ahankali taji abu nabin cinyoyinta wanda tasan tabbas bakon watan natane,cusa kanta
tayi a cinya tana cije lebe saboda zafin ciwon Mara,tanajin jini nabin jikinta amma
to mezatayi,Abba da Umma masu siyan mata audugar mata(always) basa duniyar
yanzu,kuka takeyi ahankali saboda kar Duduwa taji.
Duduwa ce ta fito daga dakinta “ke mekikeyi a tsugunna ba surfe nasakiyi ba”,
mikewa tsaye tayi tace “Duduwa cikina ke ciwo”
Da sauri Duduwa tace “to kimutu mana,ganin abu kaman jini jini a kasan wurin yasa
Duduwa karasowa wurin da sauri tabi zanin jikinta da kasan wurin da kallo tafara
tafa hannu tana salati tana sallallami”Faida” ta ambata tareda rike haba,tacigaba ”
habawa ni dama nace karuwan ci kikeyi,dama naga alamun kinada ciki jiya,shine yanzu
kikazo gidana kina bari?” Rufaida takara tsugunna wa saboda ciwon cikin datakeji,
duka Duduwa tarufeta dashi tana kuka yanzu dama ciki kikaje kika dauko yarnan,shine
kikemin bari a gida,nida nake shirin aurar dake, saida tagaji da dukanta sanan ta
saketa ta mika mata tulu,wuce kije rafi ki debomin ruwa kuma wlh ahaka zaki tafi
saina tona miki asiri,duniya tasa cikin shege kikayi yar iska,haka Rufaida tafita
daga gidan tana kuka jikinta da zaninta dukya baci,sai kallonta ake, haka taje
tadawo tajuye takoma nabiyu,kuka kawai take ahanya ita bama kukan ana kallonta take
ba kukan yanda jikinta yabaci take haka taje rafin tadebo ruwa tajuyo tana tafiya
ahankali jin tafiya na neman gagaranta yasa ta sauke tulun ta tsugunna akan hanya
ta rike cikinta wayyo cikina. Rufaidatu taji anfada da sauri ta dago kanta taga
Baba ne, yadanyi murmushi “Ashe kece yata,me kikeyi anan wurin kin tsugunna,a’a
tashi mana yata”,ahankali ta tashi kallon kafanta yayi yaga jini wani nabin wani ga
zanin jikinta tama haka da sauri ya sakko daga kan amalanken yazo kusa da ita ya
dafa kanta “Rufaidatu menene? Maiya sameki? Wanan jinin dakebin kafanki fa” kuka
tafashe ma Baba dashi sosai tanajan numfashi “Baba cikina ke ciwo,Duduwa tace wai
bari nakeyi” takarasa maganan tana kuka, Baba ya share hawayen idonta yace “ba
bakon watanki bane?” Ta sunkuyar da kanta tana hawaye, daukan tulun ruwanta yayi ya
daura akan amalanken yace “hau muje gidana ki gyara jikinki yata” da kyar ta iya
hawa, ya duba aljihun shi yaga dagashi sai naira hamsin ya ciro yabata yace “gashi
ki rike ki ajiye duk rana irin haka kyayi amfani dashi kina siyan magani kinji idan
kuma inanan kizo wurina nabaki sayawa kisha, yanzu muje gidana Maman talatu tabaki
magani” yahau suka tafi.

Maman Abd Shakur😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 11 to 13KAINE SIRRI NA 17 to 20 →
KAINE SIRRI NA 14 to 16
Posted on May 1, 2016 by mamanshakur
[4/30, 7:18 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

14
Kwanaki sunja tafiya yay tafiya,walaha da azaba sunma Rufaida yawa, bata magana da
kowa a kauyen sai Baba,haryau batasan menene Kawa ba dan bamata da ita, takara baki
takara ramewa rabonta da kitso tun kafin Abba da Umma su rasu,kannata ya dankare.
Ayanzu haka ta tara naira 100 wanda Baba yabata,boyesu take cikin bukkarta dan
haryau bata manta da dubu biyun mai gilashi data dauka ba,kuma tai alkawari komin
daran dadewa saita bashi kudinshi wanan kenan.

Zaune yake cikin Asalin office dinshi na garin Abuja,yana karkada kafa,kallon
agogon hadadden office din yayi yaga karfe 5,dan tsaki yayi ahankali yace “wot is
taking u so long Muzzamil?”,gama fadin haka yaji anbude kofa an shigo hararan shi
yayi yacigaba da Danna waya,Muzzamil yay dariya yarike baki,yamaida kofan office
din yarufe sanan yakarasa ciki ya zauna Barraq yace” shine…kafin yakarasa maganan
Muzzamil yatare mai numfashi, “I know, I know, nabatama lokaci kayakuri, wlh ba
laifina bane inacikin driving Babyna takira”ya dagama Barraq dake kallonshi gira
cikin zolaya yace” u know now,I just can’t resist it,dole nai parking a gefen hanya
mukai magana,nabama babyna lokacin ta” yakarasa maganan yana kallon fuskan Barraq
dake kallonshi. Ajiye jakan laptop din hanunshi yayi akan kujera tare da cire coat
din suit din jikinshi ya makala akan wani dan karfi da aka tanada a office din da
makala coat yasa yannu yana kwance tie din wuyanshi ya kalli Barraq yace “nafadama
gaskiya B, nakosa 2 weeks dinan suyi wlh, can wait to become ango,kai kace dole sai
graduate, graduate yaushe ta iya shagawa da dan yarintar nan dayan sweet
16,17,18,sukeyi? men ranan daza akawomin ita daga Jigawan nan en” yadan kulle ido
ya rungume kirjinshi sanan yace “ranan will be hmmm”saikuma yafashe da dariya yana
kallon B.

Murmushi Barraq yayi ya gyara zaman eyeglass din idonshi sanan ya kalli Muzzamil da
haryanzu yana rungume da kirjinshi yace” will u just sit down and stop dreaming
about hw ur 1st nyt will be” Muzzamil ya zauna yana dariya shima Barraq maganan
dayayi yabashi kunya da dariya,yadanyi dariya kadan sanan ya kalli Muzzamil dake
dariya har alokacin yace “ha’a! dariyan ya isa haka mana,muyi magana” da kyar
yasamu Muzzamil yay shiru. Tashi yayi ya bude karamin safe ya ciro wani Babban gift
box ya mikama Muzzamil, Muzzamil ya karba yana kallonshi “nawaye?” Barraq yace
“yours, ka duba mana”,ahankali ya warware dan kyallen sama sanan ya cire marfin ya
ajiye a gefe idanunshi suka sauka kan hadaddun katunan bikinshi,da murmushi akan
fuskanshi ya dauko daya ya karanta harda event kusan 3 types da Barraq yahada musu.

Kallon Barraq yayi murna yama hanashi magana da kyar ya iya furta kalman”am
speechless” kwalla yadan cika idonshi Wanda ni M shakur nakirasu da tears of joy.
da sauri ya sharesu yakara kallon fuskan Barraq dake kallonshi yanajin wani irin
kaunar abokin nashi,Muzzamil ya tashi ya zagayo ta inda Barraq yake yabashi hug
tareda fadin “thank you Friend”.
Kwankwasa kofan da akayi yasa Muzzamil yasakeshi yakoma wurin kofan ya bude wani
Babban Alhaji ya shigo,Muzzamil yace”B bari naje mosque dinku nai salla”Barraq yace
“ok” sanan yafita yabar Alh da Barraq a office.
Maman Abd Shakur😘
[4/30, 7:31 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

15
Barr Barraq ya kalli Alh yace”hw can I help you Alh namatazu mai jirage?” Alh
yadanyi dariyan shu’uman ci sanan ya daga katon briefcase din daya shigo dashi ya
daura kan table ya bude sanan ya juya yanda Barraq zaiga abunda ke ciki, Barr
Barraq ya kalli abunda ke ciki sanan ya dago kanshi ya kalli Alh yace” dollars,
for?”Alh yadan yi murmushi tareda gyara zama yace”Barr Barraq next Monday za’a
shiga kotu,I know you very well, nakuma San kanada all the evidence(shaidu/proves)
wayanda zaka iya nunama court asan cewa Ni drug dealer ne(masu saida kwayoyin maye)
so nakawo maka wayanan kudin wayanda idan ka lissafasu kan naira wanan kudin naira
biliyan 50 ne duka nakane inhar zaka rufamin asiri a kotu”. Yakara sa maganan yana
kallon Barr Barraq dake kallonshi batare dako digin murmushi akan fuskarshi
ba,ajiyan zuciya ya sauke sanan ya kalli Alh yace”unfortunately Alh bana karban
bribery(rashawa/cin hanci),kadau kudinka katafi saimun hadu ranan Monday a Court,
idanun Alh sukai ja,aranshi yace Yaro baisan wutaba saiya taka,danma na lallaba ka,
Alh yakara tattaro murmushi yace “wot if na ninka maka wanan kudin sau uku?” Barr
Barraq yadau wayanshi yana dannawa batare daya kalleshi ba yace “u heard wot I
said,bana karban bribery kafita daga office dina kafin nai disgracing dinka a
public”, Alh yay dariya yace “ok-ok Yaro,ya isa”ya kulle briefcase din sanan ya
kalli katinan bikin da muzammil yabari akan table sa hannu yayi ya dauka ya kalla
sanan ya kalli fuskan Barraq dake kallonshi yace”so Babban abokin naka guda aure
zaiyi on Saturday dat is two days kafin mu shiga kotu ko?” Barraq yadan kalleshi
kafin yace “eh, a Jigawa state za’ayi daurin auren,muna gayyatar ka” Alh yakara yin
dariyan shakiyanci “aiko zanzo,zanzo ma da babban gudumwama kam” ya tsaya yana
kallon yanayin Barr dabaiga ya chanza ba yay murmushi shima yace”saika zo”. Alh
yajuya yafita daga office din yana rayawa a ranshi kafin ka tozartani a kotu zan
aikaka cikin kasa.

Maman Abd Shakur😘


[4/30, 7:51 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

16
Bayan fitarshi Muzzamil ya shigo da sauri yace “B me wanan Alh ke nema?” Barr yace
“yaso yabiyani narufa mishi asiri akotu ne,baisan Ni am not his type ba”,Muzzamil
yace “Allah karemu daga shairin irinsu” batare da Barr yace Ameen ba yatashi yadau
car keys ya kalli Muzzamil yace “muje nama auta promise zan kaita yawo yau”
Muzzamil yatashi suka tattara kayan suka fito kowanensu ya shiga motanshi sai gida.

A haraban gidan babanshi yay parking yafito yana tafiya ahankali ya shiga cikin
gidan Babban falon mahaifinshi ya shiga wata kakkyawar mace yagani zaune da wata
yarinya dabazata wuce shekara 11 ba taci gayu cikin atampa riga ja tana zaune kusa
da matan datai masifan kama da ita, tana ganinshi ta taso da gudu ta rungume shi
“uncle B oyoyo, kadade yau”dagota yay daga jikinshi yace “sorry autan Mama”,
yakalli matar dake musu murmushi yace “ina wuni Amma”da murmushi tace” lpy Barraq
kadawo? Ya aikin” yace “Alhamdulillah”,tace “abincin ka na dining” da sauri yace
“no Amma saidai anjima da daddare, yanzu wanka zanyi nakai auta yawo” ya kalli auta
yace “auta bari naje na shirya sai mutafi ko” karban jakan hanunshi tayi yarike
mata hannu tarakashi har part dinshi sanan tafito takoma part dinsu,tafada jikin
Amma tace”mummy ban kayan dazansa ” Mum tai murmushi tace “saima nacemai yafasa
fita dake” tai maganan da wasa,ta tashi auta tabita abaya suka tafi daki ta
shiryata sosai.

Sallamanshi dataji afalo yasa ta fizge jikinta daga hannun Amma tafito da gudu
“Uncle B wlh kaga nariga na shirya” tajuya mai baya “amma danja min zip din”Jan
kunenta yayi yace “keko shine baki bari amma takarasa shiryaki ba” Jan mata zip din
rigan yayi ta saka pink karamin hijabin ta da takalmin ta pink tarike mai hannu
sukama Amma sallama suka tafi. har cikin ran Amma tanajin dadin yanda Barraq ke
kula da Bintu(auta) daidai daso daya bai taba nuna mata ita ba Mamarshi bane,haka
kuma bai taba treating dinta kaman step Mum dinshiba.

Yau takama jumma’a, baisamu yabi Muzzamil tun jiya Thursday zuwa Jigawa state ba
saboda aikin dayamishi yawa tunda sassafe yadau hanyar Jigawa.

Karfe 2 na rana yasoma shiga cikin garin Jigawa a daidai lokacin Alh namatazu mai
jirage ke gaban na’urar computer yana kallon Barr Barraq da yanda yake tukinshi
dariya yayi sosai yace”is time lokacin ka yayi Yaro”. Yana cikin tuki yaji karan
waya dauka yayi da hannu daya yaji Muzzamil ne yace “kana ina,u know I need yhu ko”
murmushi yayi yace “albishirinka gamani masoma shigowa Jigawa… Jin motan dayake
tukawa yawani karkace akan titi tayan baya suka fita, take motan yafarayin cikin
daji da gudun bala’i birkin dayake takawa ma yaki aiki kum! Motar da bugu dawani
dutse Wanda hakan yasa kanshi ya buge glass din gaban motan eyeglasses dinshi suka
fita daga idonshi.
Motan yaji yakara komawa baya sanan yayo gaba yacigaba da kutsawa cikin daji motan
na bubbuge bishiyoyi wanda hakan yasa ya bugu sosai, tsayawa motar tayi chak sanan
tayoyin gaban suka fashe tareda sakin Kara mai karfi “tusss” karan dayasa Rufaida
data debo ruwa daga rafi tana tafiya ita kadai a hanya ta saki ihu harda barar da
ruwan kanta tulun ya fashe. Tace “na shiga uku bomb”, hango hayaki na tashi tayi
daga Chan gaba bata ganin abunda ke hayakin saboda bishiyoyin dasuka kare ahankali
take tafiya kaman wani abu na fizgan ta zuwa wurin datake hango hayakin.

Farfadowa yayi daga gajeruwar suman dayayi sakamakon buguwan dayayi,ahankali yake
laluben eyeglass dinshi baiji alamun suba, hakan yasa yafara tattaba gefenshi dan
gano inda zai danna kofar motan ya bude saboda warin petir dayaji alamun tank
yafashe hakan zaisa motan takama da wuta any moment, amma yakasa gano wurin, tari
yafara sosai yana bubbuga glass din gefen motan da hannu ya daura kanshi kan glass
din,ahankali bakinshi ya furta “ataimakamin, somebody help me” Karasowa wurin
Rufaida tayi ta tsaya gaban motan dataga yana hayaki,gashi abu kaman ruwa na zuba
takasa, juyawa tayi zata koma saikuma taji kaman ana magana,Kara matsowa jikin
motan tayi ta daura kanta a jikin glass din motar ta Kara hannayenta ta gefen
fuskanta dan ta hango abunda ke cikin motar, da gudu ta matsa baya tana zare ido,
dafe kirjinta tayi tace “mai gilashi!” .

Maman Abd Shakur😘[4/30, 7:18 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

14
Kwanaki sunja tafiya yay tafiya,walaha da azaba sunma Rufaida yawa, bata magana da
kowa a kauyen sai Baba,haryau batasan menene Kawa ba dan bamata da ita, takara baki
takara ramewa rabonta da kitso tun kafin Abba da Umma su rasu,kannata ya dankare.
Ayanzu haka ta tara naira 100 wanda Baba yabata,boyesu take cikin bukkarta dan
haryau bata manta da dubu biyun mai gilashi data dauka ba,kuma tai alkawari komin
daran dadewa saita bashi kudinshi wanan kenan.

Zaune yake cikin Asalin office dinshi na garin Abuja,yana karkada kafa,kallon
agogon hadadden office din yayi yaga karfe 5,dan tsaki yayi ahankali yace “wot is
taking u so long Muzzamil?”,gama fadin haka yaji anbude kofa an shigo hararan shi
yayi yacigaba da Danna waya,Muzzamil yay dariya yarike baki,yamaida kofan office
din yarufe sanan yakarasa ciki ya zauna Barraq yace” shine…kafin yakarasa maganan
Muzzamil yatare mai numfashi, “I know, I know, nabatama lokaci kayakuri, wlh ba
laifina bane inacikin driving Babyna takira”ya dagama Barraq dake kallonshi gira
cikin zolaya yace” u know now,I just can’t resist it,dole nai parking a gefen hanya
mukai magana,nabama babyna lokacin ta” yakarasa maganan yana kallon fuskan Barraq
dake kallonshi. Ajiye jakan laptop din hanunshi yayi akan kujera tare da cire coat
din suit din jikinshi ya makala akan wani dan karfi da aka tanada a office din da
makala coat yasa yannu yana kwance tie din wuyanshi ya kalli Barraq yace “nafadama
gaskiya B, nakosa 2 weeks dinan suyi wlh, can wait to become ango,kai kace dole sai
graduate, graduate yaushe ta iya shagawa da dan yarintar nan dayan sweet
16,17,18,sukeyi? men ranan daza akawomin ita daga Jigawan nan en” yadan kulle ido
ya rungume kirjinshi sanan yace “ranan will be hmmm”saikuma yafashe da dariya yana
kallon B.

Murmushi Barraq yayi ya gyara zaman eyeglass din idonshi sanan ya kalli Muzzamil da
haryanzu yana rungume da kirjinshi yace” will u just sit down and stop dreaming
about hw ur 1st nyt will be” Muzzamil ya zauna yana dariya shima Barraq maganan
dayayi yabashi kunya da dariya,yadanyi dariya kadan sanan ya kalli Muzzamil dake
dariya har alokacin yace “ha’a! dariyan ya isa haka mana,muyi magana” da kyar
yasamu Muzzamil yay shiru. Tashi yayi ya bude karamin safe ya ciro wani Babban gift
box ya mikama Muzzamil, Muzzamil ya karba yana kallonshi “nawaye?” Barraq yace
“yours, ka duba mana”,ahankali ya warware dan kyallen sama sanan ya cire marfin ya
ajiye a gefe idanunshi suka sauka kan hadaddun katunan bikinshi,da murmushi akan
fuskanshi ya dauko daya ya karanta harda event kusan 3 types da Barraq yahada musu.

Kallon Barraq yayi murna yama hanashi magana da kyar ya iya furta kalman”am
speechless” kwalla yadan cika idonshi Wanda ni M shakur nakirasu da tears of joy.
da sauri ya sharesu yakara kallon fuskan Barraq dake kallonshi yanajin wani irin
kaunar abokin nashi,Muzzamil ya tashi ya zagayo ta inda Barraq yake yabashi hug
tareda fadin “thank you Friend”.
Kwankwasa kofan da akayi yasa Muzzamil yasakeshi yakoma wurin kofan ya bude wani
Babban Alhaji ya shigo,Muzzamil yace”B bari naje mosque dinku nai salla”Barraq yace
“ok” sanan yafita yabar Alh da Barraq a office.

Maman Abd Shakur😘


[4/30, 7:31 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

15
Barr Barraq ya kalli Alh yace”hw can I help you Alh namatazu mai jirage?” Alh
yadanyi dariyan shu’uman ci sanan ya daga katon briefcase din daya shigo dashi ya
daura kan table ya bude sanan ya juya yanda Barraq zaiga abunda ke ciki, Barr
Barraq ya kalli abunda ke ciki sanan ya dago kanshi ya kalli Alh yace” dollars,
for?”Alh yadan yi murmushi tareda gyara zama yace”Barr Barraq next Monday za’a
shiga kotu,I know you very well, nakuma San kanada all the evidence(shaidu/proves)
wayanda zaka iya nunama court asan cewa Ni drug dealer ne(masu saida kwayoyin maye)
so nakawo maka wayanan kudin wayanda idan ka lissafasu kan naira wanan kudin naira
biliyan 50 ne duka nakane inhar zaka rufamin asiri a kotu”. Yakara sa maganan yana
kallon Barr Barraq dake kallonshi batare dako digin murmushi akan fuskarshi
ba,ajiyan zuciya ya sauke sanan ya kalli Alh yace”unfortunately Alh bana karban
bribery(rashawa/cin hanci),kadau kudinka katafi saimun hadu ranan Monday a Court,
idanun Alh sukai ja,aranshi yace Yaro baisan wutaba saiya taka,danma na lallaba ka,
Alh yakara tattaro murmushi yace “wot if na ninka maka wanan kudin sau uku?” Barr
Barraq yadau wayanshi yana dannawa batare daya kalleshi ba yace “u heard wot I
said,bana karban bribery kafita daga office dina kafin nai disgracing dinka a
public”, Alh yay dariya yace “ok-ok Yaro,ya isa”ya kulle briefcase din sanan ya
kalli katinan bikin da muzammil yabari akan table sa hannu yayi ya dauka ya kalla
sanan ya kalli fuskan Barraq dake kallonshi yace”so Babban abokin naka guda aure
zaiyi on Saturday dat is two days kafin mu shiga kotu ko?” Barraq yadan kalleshi
kafin yace “eh, a Jigawa state za’ayi daurin auren,muna gayyatar ka” Alh yakara yin
dariyan shakiyanci “aiko zanzo,zanzo ma da babban gudumwama kam” ya tsaya yana
kallon yanayin Barr dabaiga ya chanza ba yay murmushi shima yace”saika zo”. Alh
yajuya yafita daga office din yana rayawa a ranshi kafin ka tozartani a kotu zan
aikaka cikin kasa.

Maman Abd Shakur😘


[4/30, 7:51 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

16
Bayan fitarshi Muzzamil ya shigo da sauri yace “B me wanan Alh ke nema?” Barr yace
“yaso yabiyani narufa mishi asiri akotu ne,baisan Ni am not his type ba”,Muzzamil
yace “Allah karemu daga shairin irinsu” batare da Barr yace Ameen ba yatashi yadau
car keys ya kalli Muzzamil yace “muje nama auta promise zan kaita yawo yau”
Muzzamil yatashi suka tattara kayan suka fito kowanensu ya shiga motanshi sai gida.

A haraban gidan babanshi yay parking yafito yana tafiya ahankali ya shiga cikin
gidan Babban falon mahaifinshi ya shiga wata kakkyawar mace yagani zaune da wata
yarinya dabazata wuce shekara 11 ba taci gayu cikin atampa riga ja tana zaune kusa
da matan datai masifan kama da ita, tana ganinshi ta taso da gudu ta rungume shi
“uncle B oyoyo, kadade yau”dagota yay daga jikinshi yace “sorry autan Mama”,
yakalli matar dake musu murmushi yace “ina wuni Amma”da murmushi tace” lpy Barraq
kadawo? Ya aikin” yace “Alhamdulillah”,tace “abincin ka na dining” da sauri yace
“no Amma saidai anjima da daddare, yanzu wanka zanyi nakai auta yawo” ya kalli auta
yace “auta bari naje na shirya sai mutafi ko” karban jakan hanunshi tayi yarike
mata hannu tarakashi har part dinshi sanan tafito takoma part dinsu,tafada jikin
Amma tace”mummy ban kayan dazansa ” Mum tai murmushi tace “saima nacemai yafasa
fita dake” tai maganan da wasa,ta tashi auta tabita abaya suka tafi daki ta
shiryata sosai.

Sallamanshi dataji afalo yasa ta fizge jikinta daga hannun Amma tafito da gudu
“Uncle B wlh kaga nariga na shirya” tajuya mai baya “amma danja min zip din”Jan
kunenta yayi yace “keko shine baki bari amma takarasa shiryaki ba” Jan mata zip din
rigan yayi ta saka pink karamin hijabin ta da takalmin ta pink tarike mai hannu
sukama Amma sallama suka tafi. har cikin ran Amma tanajin dadin yanda Barraq ke
kula da Bintu(auta) daidai daso daya bai taba nuna mata ita ba Mamarshi bane,haka
kuma bai taba treating dinta kaman step Mum dinshiba.

Yau takama jumma’a, baisamu yabi Muzzamil tun jiya Thursday zuwa Jigawa state ba
saboda aikin dayamishi yawa tunda sassafe yadau hanyar Jigawa.

Karfe 2 na rana yasoma shiga cikin garin Jigawa a daidai lokacin Alh namatazu mai
jirage ke gaban na’urar computer yana kallon Barr Barraq da yanda yake tukinshi
dariya yayi sosai yace”is time lokacin ka yayi Yaro”. Yana cikin tuki yaji karan
waya dauka yayi da hannu daya yaji Muzzamil ne yace “kana ina,u know I need yhu ko”
murmushi yayi yace “albishirinka gamani masoma shigowa Jigawa… Jin motan dayake
tukawa yawani karkace akan titi tayan baya suka fita, take motan yafarayin cikin
daji da gudun bala’i birkin dayake takawa ma yaki aiki kum! Motar da bugu dawani
dutse Wanda hakan yasa kanshi ya buge glass din gaban motan eyeglasses dinshi suka
fita daga idonshi.
Motan yaji yakara komawa baya sanan yayo gaba yacigaba da kutsawa cikin daji motan
na bubbuge bishiyoyi wanda hakan yasa ya bugu sosai, tsayawa motar tayi chak sanan
tayoyin gaban suka fashe tareda sakin Kara mai karfi “tusss” karan dayasa Rufaida
data debo ruwa daga rafi tana tafiya ita kadai a hanya ta saki ihu harda barar da
ruwan kanta tulun ya fashe. Tace “na shiga uku bomb”, hango hayaki na tashi tayi
daga Chan gaba bata ganin abunda ke hayakin saboda bishiyoyin dasuka kare ahankali
take tafiya kaman wani abu na fizgan ta zuwa wurin datake hango hayakin.

Farfadowa yayi daga gajeruwar suman dayayi sakamakon buguwan dayayi,ahankali yake
laluben eyeglass dinshi baiji alamun suba, hakan yasa yafara tattaba gefenshi dan
gano inda zai danna kofar motan ya bude saboda warin petir dayaji alamun tank
yafashe hakan zaisa motan takama da wuta any moment, amma yakasa gano wurin, tari
yafara sosai yana bubbuga glass din gefen motan da hannu ya daura kanshi kan glass
din,ahankali bakinshi ya furta “ataimakamin, somebody help me” Karasowa wurin
Rufaida tayi ta tsaya gaban motan dataga yana hayaki,gashi abu kaman ruwa na zuba
takasa, juyawa tayi zata koma saikuma taji kaman ana magana,Kara matsowa jikin
motan tayi ta daura kanta a jikin glass din motar ta Kara hannayenta ta gefen
fuskanta dan ta hango abunda ke cikin motar, da gudu ta matsa baya tana zare ido,
dafe kirjinta tayi tace “mai gilashi!” .
Maman Abd Shakur😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 14 to 16KAINE SIRRI NA 21 to 24 →
KAINE SIRRI NA 17 to 20
Posted on May 2, 2016 by mamanshakur
[5/2, 7:44 AM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

17
Jikinta na rawa,kirjinta na bugawa da karfi saboda tsoro, juyawa tayi tafara tafiya
da sauri duk ta rude tace “wlh ni banda kudin ka,banda kudin dazan biyaka”.

Barr Barraq ya lumshe ido, dan gabaki daya kanshi juyawa yake, jiri yakeji
sosai,da kyar yadaga kanshi daga jikin glass din motar ya maida akan kujera.
ahankali yake kukkulle ido harya rufesu ruf.

Kaman ance takara waigowa,tanako waigawa taga hayakin dake tashi daga motar yafi
nada ma, girgiza kanta tayi hawaye yadan zubo ahankali ta furta ” wlh bazan
iyaba,baida lpy ai,naga jini a goshinshi” da gudu ta fanfala zuwa wurin motar,
hannu tasa ta rike mabudar motar taja, sai taga motar yabude, ta tsugunna agaban
motar tana kuka tace “kafito mubar nan, motarka na hayaki” sai taga ko motsi
baiyiba, hanunta na rawa takai kan cinyarshi tadan girgiza shi tace “kaji, katashi
motar ka na hayaki”,Ganin ko motsi batayi yasa tafashe da kuka tana kallon
fukarshi,cikin kuka tace “mutuwa kayi?” Kara sautin kukan tayi tana girgiza kai
“dan Allah karka mutu, kanada kirki kaji dan Allah”.
Goge Hawayen ta tayi ta kalli gabas,kudu,yamma da arewa kozata ga wani mahalukin
dazai tayata fito dashi daga motar, amma bataga ko mutum daya ba, dayake kusan duka
yan kauyen da safe suke zuwa rafi diban ruwa,basu zuwa da rana. Kifa kanta tayi
akan cinyarshi takara kecewa da sabon kuka,kaman wacce aka tsikara ta tashi da gudu
ta fanfala zuwa inda tulun ruwanta yafashe kozata samu ruwa a wurin, cikin ikon
Allah taga wani dan bangaren tulun da akwai dan Karamin ruwa akanshi tsugunna wa
tayi ta dauka ahankali ta juyo tana tafiya, koda tafito fili saitaga tsabagen
hayaki bama ta ganin motar da kyau,hayakin yariga ya rufe motar, sauri takara
batai wata wata ba ta shige cikin hayakin ta tsugunna tana laluban bakinshi da
hannunta, taba lips dinshi yasa tagane bakinshi ne, tashi tsaye tayi da ruwan ta
daga hannunta dake dauke da ruwan ta Kara ajikin lips dinshi tace “kasha dan
Allah”,ta juye akan lips dinshi kadan ya shiga bakinshi sauran ruwan ya zuba a
kirjinshi hakan yasa yaji sanyi ya saki numfashi tareda bude idonshi kadan
“ahhhhhh” kokarin lumshe idonshi yake yasa ta kama fuskarshi da hanunta biyu ta
girgiza shi “katashi dan Allah, kaji katashi motar na hayaki, mufita daga ciki”,
bude idonshi yay da kyau saidai kash baya iya ganin mai wanan zazzakar muryar,gashi
kanshi na masifar juyawa saboda buge kan dayayi sosai, ganin yanda ya tsareta da
ido yasa tace “kaji” Hawaye ya gangaro daga idonta ta daura hannayenta akan nashi
tace “ga hannuna ka rike mufita”kasa kama hannunta yayi kawai saita cire tsoro
takama nashi tace “yauwa to tashi” taja hanunshi, da kyar ya iya tattaro karfinshi
ya damke hanunta da karfi yatshi yafito daga motar. yakara rike hannayenta gam tana
tafiya da baya da baya shikuma yana binta ahankali kanshi na juyawa jiri na
dibarshi sosai.

Sunyi kusan taku ashirin(20) yana layi, adaidai lokacin motar ta kama da wuta,
tsabagen tsoro ganin motar yakama da wuta yasa Rufaida tafara sauri tana janshi da
sauri,mugun tuntube taci da dutse, dayake dabaya take tafiya tafadi akasa timm,
batare dayasan maiya afkuba shima yaci tuntube da dutsen ya fada kanta dan ba
ganin gabanshi yakeba.
Ihu tasaki da karfi” wayyo Allah na,ka dagani”.

Maman Abd Shakur😘


[5/2, 8:22 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

18
Hadadden Hall ne cike da jama’a kowa yaci gayu,kida kawai kateshi kana ganin
fuskokin mutanen wurin kasan suna cike da farin ciki banda mutane biyu, Muzzamil
dayasha blue shadda ta bugu sai sheki take da Matar dazai aura Beeba. kwata kwata
natsuwarshi baya tareda shi karkada kafa yake yana kallon agogon hanunshi.
kakkyawan amaryan shi dake gefenshi itama cikin damuwa ta matso da bakinta saitin
kunenshi tace “Honey wai har yanzu Uncle B bai isoba? gashifa 4 yayi” cike da
damuwa Muzzamil yace “wlh nima ban saniba baby” tace ” to kodai wasa yakema sai
gobe zaizo?”
Muzzamil ya girgiza kai”abu daya dana Sani game da abokina shine baya karya,baitaba
karyaba, tunda yace yataso yataso dinne” amaryan tace”ok,Allah kawoshi lpy to”
Muzzamil ya mike tsaye yace “baby bari naje nakira Dad just na sanar dashi”.

Zagawa bayan Hall din yayi inda ba kida sosai yaciro wayarshi yay dailing number
Daddy Barraq, ringing daya Dad ya dauka,kafin yay magana Muzzamil yace”Daddy na
damu wlh har yanzu Barraq bai isoba ” da sauri Dad yarufe newspaper hanunshi
yace”Barraq din?,yanzu fa is 4,yaron da tun sassafe yamin salllama yatafi”,Muzzamil
yace”Dad inata kiran wayarshi baya shiga,wlh nadamu” Dad yace “don’t worry Muzzamil
it might be motarshi tasamu yar matsala a hanya ne, idan yakai har mangariba bai
isoba just let me know,mubashi nan da 7’oclock ” Muzzamil ya numfasa yace”to Dad ”
ya katse wayan yakoma Hall din badan ranshi yasoba.
*****
Da kyar ya iya Jan jikinshi ahankali ya sauka zuwa gefenta,numfashi ta sauke mai
karfi tareda tashi tsaye tana kakkabe jikinta, ganin yana juye juye yasa ta tsayar
da kakkabe jikin datakeyi ta kalleshi, kafin ta Ankara taga yafara Kwara amai a
kwance ya rike cikinshi, warin petir din daya Shaka ya batamai ciki,tsugunnawa tayi
a gefenshi a raunane tace “sannu” ya mugun galabaita daga kanshi yayi kawai dan
jikinshi yay zafi, dankwalin kanta ta cire ta mikamai tace “gashi ka share rigan
ka” hanunshi ya mika yana laluben abunda take bashi, Rufaida ta kalleshi muryanta
na rawa sosai tace “baka ganine?” Kanshi yadaga mata ahankali, kuka yaci karfinta
tsugunnawa tayi ta share mai aman daya bata gaban riganshi, sai bayan tagama cikin
kuka tace “tashi muje gidanmu nabaka nabaka magani” da kyar ya iya mikewa yadan
cije lebe tareda rike kanshi dayakeji kaman zai cire, sannu tace mishi sanan ta
mika hanunta yana rawa tarike mai tafin hannu, wani dan yanayi taji ya ajikinta
sanan tace “muje” ahankali yake daga kafa hanunshi daya na rike da kanshi, sundanyi
tafiya kadan jin zaifadi yasa yace “sister zan huta” akasan wani bishiyan lema ta
taimaka mai ya zauna,itama ta zauna kusa dashi jikinshi yay zafi radau, sanan tace
“zaka iya tafiya yanzu?” Ya gyada kai sanan suka mike akalla sun bata kusan awa
daya kafin sukai gida saboda suna tafiya yana hutawa,zazzabi sosai yakeji da ciwon
kai banawasa ba.

Gidan suka shiga, hamdala tayi tadaga Duduwa bata gida bukkarta ta shigar dashi ta
zaunar dashi akasa sanan tace “ina zuwa” fita tayi da gudu takoma tsohon dakin
mamarta nada, tsofaffin kayan mamanta da labulaye ta kwaso dayawa ta shigo dakin
tasame shi harya kwanta akasa shame-shame ya rike kanshi, shinfidasu tayi akasa ta
daura wani akan wani saboda yadanji taushi tazo ta tsugunna agabanshi tadan tabashi
ya bude idanunshi dasukai jajir tace “taso ka kwanta akan shimfida”,ta rike mishi
hannu, tashi tsaye yayi da taimakon ta yadan kwanta akan shimfidar.

Ta Kara tsugunnawa tace”bari naje nasiyo ma magani kaji,kai bacci dan Allah duk
Wanda kaji yay magana karka amsa kaji?ko Duduwa tai sallama karka amsa” Bai
amsataba,tai fuskan tausayi tace “in sha Allah zaka warke kanada kirki” ta tashi da
sauri tadau yar karaman jakan buhu taciro naira Darin da Baba yabata tafita daga
dakin da gudu.

Maman Abd Shakur😘


[5/2, 8:37 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

19
Gidan wata mata dake saida magani a kauyen taje,saidai matar batanan sai yayan ta
yan mata guda uku da bazasu wuce sa’ointa ba.
Sallama tayi suka amsa suna mata kallon banza tace “abani maganin ciwon kai da
zazzabi” tashi daya daga cikinsu tayi ta dauko mata wani kullin maganin gari guda
biyu. Rufaida ta karba ta mika naira hamsin, yarinyar tana karba tace”jar
ubanchan,lallai nema yarnan, dan kin rainamin hankali antaba saida maganin zazzabi
da bauri naira hamsin?ko angaya miki na gadon ubankine?” Rufaida girgiza kai tace
“wlh hamsin gareni,dan Allah kiyakuri wlh Mara lafiya zanba “sauran yayyin yarinyar
biyu suka taso sukace “maiya faru lami”yarinyar tace “ba wanan jikar Duduwan bace
wai magani naira dari taban hamsin” da sauri Rufaida tace “dan Allah kubini bashi
wlh Mara lpy zanba” takarasa maganan da muryan tausayi, Babban yarsu tace “zaki
kawo cikon kudin gobe, inba hakaba wlh saimun tareki abakin rafi mun miki dukan
tsiya,mu daki kudinmu”. Rufaida tace “na yarda, tajuya tabar gidan da gudu tabiya
shago tasai buredin ishirin sai madara cow bell ta goma da choco na goma sai sigan
goma.

Ta shiga gidan hartana tuntube saboda sauri,har alokacin Duduwa bata dawoba,kofi ta
dauka ta jika mishi garin maganin,sanan tadau wani kofi ta kada mishi tea da ruwan
sanyi duk takai dakin sanan ta tasheshi, “ga magani kasha”, da kyar ya zauna ya
jingina da bango daukan kofin maganin tayi takai bakinshi tace “bude bakinka” bude
bakinshi yayi ta zubamai maganin, feso maganin yayi a fuskatta batare daya saniba
ya yamuse fuska saboda wani azaban daci d bauri dayaji, ta share fuskan ta batare
data damuba tace” kasha dan Allah” girgiza mata kai yayi. Tace” ga tea kasha” shima
girgiza mata kai yayi ta tashi daga wurin takoma gefe tana kallon yanda yake mutsu
mutsu. Kara dawowa kusa dashi tayi tarike mai hannu tafashe da kuka sosai, dudda
cikin ciwo yake amma saiyaji kukan kaman na kurman yarinyar nan dayahadu da ita a
Minna. Tace”Dan Allah ktashi kasha,kanka naciwo,wlh bazan iya inta kallonka kana
ciwo ba kaji,kanada kirki Allah” wani iri yaji datana kuka ahankali yace “ban
nasha”daukan magananin tayi tabashi da kyar yasha rabin kofi yana tabe baki sanan
yakoma ya kwanta zama tayi a gefenshi tasa hannu tacire mai takalmin kafanshi sanan
tadau mahici tana fifitashi ganin yana zufa.

Gafaradai mutan gida. Sallaman Duduwa yasa Rufaida tayar da maficin ta mike tsaye
ta rike kirji Duduwa tadawo,arude tasa bakinta a kunnenshi tace “kakata tadawo dan
Allah karkai magana taji kaji?” Tsigar jikinshi yatashi yarr, tashi tayi tafita
daga bukkan ta rufo kofan ta tsaya a wurin tana kallon Duduwa dake kallon ta, “ina
ruwan danace ki debo?” Rufaida takara makewa ajikin bango tana makyarkyata “Duduwa
wlh tulun yafashe ahanya, ba laifina bane Allah bom… Duduwa ta daka mata tsawa ”
ke! yimin shiru shegiya mai kama da ifiritu, wlh tunda kika fasamin tulu wlh saina
fanshi abuna ajikin ki zaki gamu Dani,laifin ki biyu baki debo ruwa ba ga fasa
Randa, bazaki zo nanba ina magana dake kina kallona da bakaken idonki” Rufaida
tunkafin takai tafara matsar kwalla,Takai gaban Duduwa ta tsugunna “gani”, katuwar
buhun danyar gyadar dake kanta ta jefa mata ajiki, Rufaida tasaki ihu mai karfi
wanda yasa Barr Barraq tashi zaune da sauri, wai mafarki yakeyi,yanzu yakarajin
muryan kurman yarinyar nan daya taimaka a Minna, itace? Kwanciya yayi da sauri
saboda yanda kanshi yasara.

Rufaida tace “Duduwa kiyakuri bazan karaba” saida Duduwa taga tana zufa sanan ta
janye buhun gyadan daga jikinta tace “dan ubanki tashi kije ki wankesu ki daura a
wuta, inyayi zakikai dandali,sai bayan kin dawo zanci ubanki kuma wlh saikin biyani
tuluna” ta sakar mata rankwashi aka,Rufaida ta share hawaye ta dauko langa ta juye
gyadar ta wanke ta,taje ta hura wuta da kyar sanan ta daura akan wuta, kuka take
acikin kitchen din tana Sosa jikinta rabonta da wanka kwana 5 kenan Duduwa tahanata
jikinta kaikayi yakeyi sosai,kullum kaya daya take sawa salla ko saida da daddare
tayi su duka aboye dan Duduwa bata barinta salla daga safe har dare aiki take bata
zama hutawa ko sau daya arana.

Maman Abd Shakur😘


[5/2, 9:10 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

20
Karfe bakwai Muzzamil yakara kiran Dad yace “Dad har yanzu bai isoba fa,nadamu
wlh,nasan ba lafiya ba,Dad I can feel it”Dad yace ” me too Muzzamil, yanzu yaza
ayi?” Yace”Dad zanbi hanya Nagani” Dad yace “ka sanar da police, in sha Allah inhar
bakuga komiba very early gobe zan biyo flight” Muzzamil yace “to”tareda katse
wayan. Daukan keys yayi yafita daga hotel din dashi da friends dinshi sukai
lodging.
*****

Sai Wuraren mangariba tagama dafa gyadar, idanunta sunyi jaa saboda zafin hayaki,
tsumma ta dauka tarike tukunyan zata juye gyadar a langa garin juyewa ruwan ya zuba
a hannunta ihu tayi ta saki tukunyan a wurin ragowan gydar tazube akasa,da sauri
Duduwa tafito daga daki tana sallallami “Allah yasa ba zubarmin da gyada mayyar nan
tayiba” ta shigo kitchen din Rufaida dake kuka tarike hanunta tana ganin Duduwa
takara rudewa tafara ja baya, bata ankaraba taji takara taka rushi a kafanta ihun
dayafi nada tasaki zata gudu Duduwa ta damki hannunta”zonan ballagaza”iche ta dauka
ta bubbuga mata ajiki “kika bararmin da gyada,kinsan da Yaya nasamu nasiyo gyadar
nan akasuwa kuwa?” Rufaida tsabagen azaba tama kasa kuka sai ihu “bazan karaba
Duduwa, yakuri bazan karaba, wayyo Umma na” saida Duduwa taga tana neman sumewa
sanan ta ajiye ichen ta wurgota tsakar gida, ta kwashe gyadar kasan sanan ta fito
tazuba gyadar a faranti ta daura gwangwani Kwara daya akai da fara leda tazo gaban
bukkan da Rufaida ke kuka tace “dan ubanki tashi kuwuce dandali inba asiyaba komin
dare kije har bakin titi ki tsaya sai ansiye tass sanan zaki dawo, kina jina?”
Rufaida ta girgiza mata kai,Mari to koda mata tace “cemin to” Rufaida tace “to”
tana kuka. Duduwa tasa hannu ta tunbuke dan kwalin kanta ta barbaza gashin kanta
dake wari saboda rashin wankewa tace “ahanka zaki tafi saboda aga tsayin gashinki
asiye gyadan duka”,ta daura mata farantin gyadar dakeda zafi akai tace “wuce
kitafi, gwangwani daya naira goma ne” haka ta tafi,tana tafiya tana dingishi saboda
konewar kafanta,tana tafiya tana girgiza hanunta dayay bororo saboda zafin
kunar,garin ma yay duhu dan tuni akai sallan mangariba.

Dandali takai ta zauna a gefe guda,tana kuka ahankali babu Wanda yazo yasai
gyadarta amma anata siyan na sauran dasuka kawo duk Wanda yazo gabanta saidai yace
mata kazama suwuce ganin babu Wanda yasiya yasa ta roki yarinyar kusa da ita ta
daura mata gyadar akai saboda hannunta dayay bororo,aiko ta daura mata haka tayi
tafiya har takai asalin bakin titin garin tasamu guri kusada wani mai saida lemu
da ayaba ta zauna, tai shiru tana kallon hannunta bororon yakara girma, kwalla ta
share ta daga kai tana kallon motoci dake wucewa kan titi dare yayi amma batasan
karfe nawaba yanzu,sanyi da isakan titin da wahalan dukan datasha yasa taji wani
wahalallen bacci mai dadi yay gaba da ita a wurin. jin ana shafa cinyarta yasa
tabude ido da sauri tareda Sosa kanta tana turo baki, “Ahha lallai jikar Duduwa
nason abun jibi yanda take wani zumburo baki,alamun abun namata dadi ” da sauri ta
daga kanta taga wasu matasa ne su biyu sai warin taba suke da sauri ta mike tsaye
taja baya Ku rabu dani baruwan Ku dani , daya daga cikin samarin yace “baby ki
kwantar da hankalin ki munsan abunda Duduwa ke miki, da zaran kin bari munyi bazamu
Kara bari tabaki wahala ba,wanan gashi haka aiyau saimunyi gaskiya” turo baki tayi
cike da tsiwa tace “Ku matsamin nadau gyada tani,bana magana da maza” samarin suka
kalli juna sanan suka matsa mata zuwa tayi zatabi tsakiyar su tadau gyadarta bata
ankaraba taji andaga sama sunyi cikin daji da ita iya karfinta take ihu amma kafin
ta Ankara sun soma barka rigan jikinta, iya karfinta take ihu tana kururuwa hasken
motan dasukaga ya haskosu tarr yasa suka saketa suka mike tsaye, itakuma ta tashi
tsaye ta falla da bala’in gudu tafita daga dajin tana kuka da hasken farin wata ta
kekketa bishiyoyin hanyar harta kawo cikin kauyen su tana kuka tashigo gida tana
kuka. Duduwa ta haskota da tocula tafito daga dakinta tana gyara daurin zani,
haskata tayi sama da kasa taga rigan jikinta dukya barke hartana ganin albarkatun
kirjinta gashin kanta duk kasa yabata, kafanta kuwa dama ba silifas, bata damuba ta
tabe baki tace” ina kudin gyadata?” Jikinta yafara rawa tace “Duduwa wasu suka
dauken suka kaini cikin daji suna barkamin rigana”,Duduwa takara daure fuska “ina
kudin gyadata nace?” Jikinta ya Kara rawa tace “Duduwa yabace gya..bata karasa
maganar ba Duduwa ta turata tabugu da bango “wlh yau kashe kine bazanyiba a gidanan
Rufaida”, Duduwa ta koda mata Mari tana jijigata ta bugata abango, Rufaida ahankali
ta sulale a wurin sunamniya, Duduwa data haukace saboda ko gyadar ma bashi ta karbo
akasuwa, ga yar iskan yarinyar nan ta batar, zuwa tayi ta dauko ruwa ta juye a
jikinta ihu Rufaida tayi ta farfado,Duduwa ta shiga daki ta dauko wayar wuta “wlh
saina kasheki” Rufaida lumshe ido tayi ta sadaqar mutuwa yau zatayi,zatabi Abba da
Umma. saitaji maganar Baba yace “wlh wlh Duduwa inkika kashe yarinyar nan saimun
dauko miki hukuma,da daddaren nan karfe 12 lokacin daya kamata yar yarinyar nan
tana bacci shine zaki kasheta da duka?” Duduwa tace ” gafa munafukai an shigo” ta
kalli Rufaida tai kwafa “zamu gamu da safe”. Tawuce dakinta tana masifa Baba ya
daga Rufaida da take kuka ya shafa kanta yace” jeki kwanta Allah zai saka
miki”,yabata toculan hanunshi yace “ga tocula ki haska” ta karba,da dingishi take
tafiya tabude kofan bukkan ta shiga ciki ta mayar ta rufe tana kuka sosai, ga
mamakin ta ganin Barr Barraq a tsaye tayi yana juye juye ahankali yace “Rufaida
kece kika shigo? ban hanunki”hannunta mai lafiya tasaka a hanunshi tana kuka
sosai,ya zauna itama ta zauna yama kasa magana saboda yanda ranshi ke zafi, mai
wanan yar karaman yarinyar data taimakeshi tayi Duduwa ke dukanta haka? Mesa wasu
mutane are just wicked? Jin kukan nata yaki tsayawa yasa yadaga hannu yana laluban
kanta cikin sa’a yaji hanunshi cikin gashin kanta ahankali yace “ya isa Rufaida
kidena kuka” takasa yin shiru saima Kara sautin kukan datayi tana sauke ajiyan
zuciya, jin bazai iya daurewa ba,kukan na mugun tabashi yasa ya jawo kanta zuwa
kirjinshi ya rungume tsam yana jijjigata.

Masu karatu ya za’ayi Barr Barraq yasamu eyeglasses dinshi?


Shin Muzzamil daya fita duba hanya zaiga Barr?

Wanan motar data haska yan shaye2 da Rufaida, motar waye? Kodai na Muzzamil ne?

Maman Abd Shakur😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 17 to 20KAINE SIRRI NA 25 to 33 →
KAINE SIRRI NA 21 to 24
Posted on May 5, 2016 by mamanshakur
[5/3, 3:16 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

21
Fisge jikanta tayi daga nashi ta mike tsaye takoma Chan gefe nesa dashi, rigar data
yage na jikinta ta cire ta ajiye, zanin jikinta ta kwance ta daura a kirji sanan ta
kwanta akasa tana kuka. Barr Barraq ya dafe kanshi sanan ya sauke ajiyan zuciya
“please Rufaida kiyi shiru kinji” bata saurareshi ba tacigaba da kuka, wanan karan
kukan nata na mugun damun ranshi fiye da tunanin mai karatu kama kanshi yayi yace”O
I said kiyi shiru” yafadi maganan yana mai daure fuska,da sauri taja bakinta tai
shiru jikinta na rawa yace “zonan” tashi tayi tazo gabanshi tace “gani” hannu
yadaga mata ta mikamai hannunta ya zaunar da ita akasa yace “kiyi shiru kidena
kuka,I promise yhu bazaki dawwama ba cikin wahalan nan kinji?”tace “to” yace “yauwa
oya kwanta a nan kiyi bacci” kwantawa tayi agabanshi ta lumshe ido tana sauke
ajiyan zuciya irin na wayanda sukasha kukan nan yana rike da hanunta ahaka tai
bacci, dayaji hannunta yay fayau a cikin hanunshi yagane tai bacci ajiye hanunta
akasa yayi yakoma gefe yana addu’a.
Da asussuba yaji alumun an bude kofa “Rufaida, Rufaida wlh gwarama kifito inba
hakaba na lahira zai fiki jin dadi” jin haka yasa yafara tattaba kasa dan gano inda
hannunta yake yatashe ta bayason takara dukanta yau,jin hanunshi sun sauka akan
lafiyayyan cinyarta mai taushi yasa ya daga hannun da sauri yana ajiyan zuciya
saboda yanda yaji,ahankali yace”Rufaida, Rufaida ” umm tace cikin bacci yace “tashi
kije kakarki na kiranki karta Kara dukanki” da sauri ta zabura ta mike ta daura
zaninta da kyau tabude kofa tafita. Duduwa tace “sai yanzu kikaga daman tashi? Wuce
ki share tsakar gidan nan,kidau gero ki surfa sanan kitafi deban ruwa,inkin dawo
kezan dauka inkai kasuwa mai gyadar dakika batar ya jibgeki bayan yagama jibgarki
yay amfani dake hala inyay hakan yahakura ya yafemin kudin gyadar” Rufaida ta matse
kwalla ta wuce ta dauko tsintsiya ta share gidan tass tai surfen geron shima tass
wuraren goman safiya. sanan tadau tulu taje gaban dakin Duduwa tace “Duduwa dan
Allah kiban riga, banason naje rafi ahaka da daurin kirji” Duduwa tace “kan ubanki
shegiya rubabbiya idan nafito nasameki abakin kofana wlh saina parka miki ciki” da
sauri tabar wurin tadau tulu tana kuka ganin Duduwa nacikin daki yasa ta bude
bukkarta cikin kuka tace “zakaje Rafi?” Da sauri tace mata eh,ta riko hanunshi suka
fito batare da Duduwa ta gansuba.

Saida suka fito waje sanan ya tsaya t-shirt din dake jikinshi taga yacire ya mika
mata yace”gashi kisa bai kamata mace nafita babu rigaba” kallon shi tayi cikin
rawan murya tace “ai Duduwa zata dakeni inta ganni da rigan” yace “ko zata dakeki
kisa” ta karba tasa shikuma da singlet a jikinshi suka cigaba da tafiya suna cikin
tafiya ta hango yan matan nan dake saida magani da sauri ta boye Barr a bayan
bishiya tace “dan Allah ka tsaya a nan,kome zakaji karka fito dazaran angani dakai
zasa jefeni a bayan gari” itakuma tafito ta tsaya, suna hangota suka sauke tulunsu
a gefe suka karaso gabanta kowaccen su tarike kugu sukace “malama ina cikon kudin
maganin dakika siya jiya?”

Maman Abd Shakur😘


[5/3, 9:53 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

22

Rufaida taja baya tace”ku


yakuri, Allah idan nasamu kudin zan kawo muku” dariya sukayi Babbar tace”wlh
dukanki zamuyi mudaki banza,ahayye nanaye yarinya sa guiwan ki akasa, kinsan
sharadin damuka yi jiya,sa guiwan ki akasa kawai” babu musu ta tsugunna tasa
guiwanta akasa, Babbar yarsu takatso reshen dogon Yaro tace “Ni zan miki bulala
goma,lami bulala goma sai sailuba tamiki bulala goma a matsayin naira hamsin din
damuke binki”, Rufaida ta matse kwalla tace” na yarda ku dakan” yayar tazo tafara
shaula mata da karfin gaske Rufaida tafara ihu kaman ana yankata, Barr Barraq
yafito daga inda taboyeshi ahankali yake tafiya yana kokarin bin inda yakejin
kukanta yace “Ku maitai muku?for godsake yarinyar nan wai jakace,kawai kun maidata
jaka” Duk suka matsa baya suna kallon kakkyawan baturen dake magana, Rufaida ta
mike tsaye taje inda yake tana kuka yace “mekika musu?” kafin tai magana babbar tai
magana tace “bashin magani na ciwon kai da bauri tazo ta karba jiya bata bada
kudinba saisa zamu daketa,kuma ai kakarta tamaidata jaka bamuba ehe, dan haka mudai
abamu kudinmu ko aradu mu ballata mu balla banza”, cije lebe yayi inama yana
ganinta da wlh saiya balla mai mishi rashin kunyar nan. hannu yasa a aljihun wando
yazaro kudin dabaima San konawa bane ya jefa musu suka dauka sanan yar takalli
Rufaida tace “kaman mai gari da Duduwa sunji maza kikebi, wlh saimun fadi komi,yau
bayan an jefeki sanan a koreki daga garin,shegiya yar baka mai wari” suka dau
tulunsu suka bar wajen suna waka.

Rufaida ta tsugunna a wurin tafashe da kuka mai tsumma zuciya tana na shiga uku,
idanun Barr Barraq yay ja kaman yay kuka yanzu dama kanshi aka daketa? Taje takarbo
magani tabashi?wani irin shauki da son yarinyar yaji yabi jijiyoyin jikinshi,why?
Inama ace inada glass naga fuskar kakkyawar halitar nan mai taimakona?..

Magananta yaji tace”kaga idan ka mike hanyar nan sambal zata kaika har titi saika
shiga mota ka koma gida”,tasa sanda a hanunshi tace “kadinga duba hanya da sandar
nan,kayakuri katafi banason ka shiga matsala saboda ni? tunda aka gammu tare sai an
daureni an jefeni, katafi kaji insha Allah babu abunda zai sameka,nagode sosai da
abunda kamin a rayuwa,Duduwa yau saita kasheni hala, sai anjima” da sauri yace
“Rufaida, Rufaida” amma ta falfala da gudu. Ahankali yace”to mena mata arayuwa
datakemin godiya?anyway koma wacece ke Alkawari daya zan miki saina fitar dake daga
kangin nan dakike ciki” yajuya yana dogara sandar yana tafiya.

Dad polisawa da Muzzamil tsaye agaban motar Barraq daya Kone. Muzzamil yace” Dad
jiya tunda nazo bakin titin nan naga tayoyi biyu Dana duba naga tayan motar B
ne,hakan yasa na dinga tracing tire tracks cikin Daren nan harnazo nan, and d worse
part naga karfen glass dinshi a motar, kenan duk inda yake baya gani baya tareda
glass dinshi. Dad kataho da sapayan eyeglass din dana fadama yauda safe?” Dad ya
dafa kan Muzzamil yace”eh,son naji,yanzu nida inspectors zamu shiga cikin kauyen
nemanshi,kawuce katafi 11 za’ayi daurin auren ka gashi yanzu 10:30″ Muzzamil yace
“Dad… Dad ya girgiza kai banason musu just go,today is a special day 4 yhu” yajuya
badan ranshi Yasoba kwalla yataru a idonshi yafara tafiya dan karasawa bakin titi
ya shiga motarshi daya paka a wurin. Yayinda Dad da yansanda suka shiga cikin mota
suka wuce cikin kauyen.

Shiga motarshi yayi ya kifa kanshi a kujera kaman yafashe da kuka haka yakeji,
gajeren hawaye daya zubo yadan goge sanan ya Danna key zai tada motar ya dago
kanshi yana kallon titi. hango Barr Barraq yayi a tsakiyar titi yana dogara sanda
ga motoci sun taho da gudunsu dayake express road ce, da gudu yafito daga motarshi
ya fanfala da gudu ya bude muryarshi yace “B stay still,just stay where u are,am
coming” yama motocin dasukai layi alamun su wuce duk suka wuce sanan ya shiga cikin
titin,kamo hannun Barraq yayi suka tsallako sanan yama Barraq dake fadin Muzzamil
kaine muryan ka naji, kakkyawan runguma Muzzamil yabashi tareda fadin is Me,I
missed yhu B”.

Maman Abd Shakur😘


[5/4, 9:06 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

23
Suka kankame juna daga baya Muzzamil ya sakeshi yace “bari nakira Dad” ba’afi minti
20 da fadama Dad ba suka zo wurin shida polisawa,Dad yazo inda suke tsaye ya
rungume Barraq tareda fadin”Alhamdulillah, Alhamdulillah,my little champion is safe
and sound ” Barraq yay murmushi da kyar ya iya furta “Dad am hungry, yunwa nakeji
sosai wlh”Dad yace” muje kaci abinci” yajuyo ya sallami poliswan tareda basu kudi
mai yawa ya dawo ya shiga motar Muzzamil yajasu sai cikin garin Jigawa
state,anguwar GRA suka sauke Dad suka fara saukewa a wajen daurin Auren,Muzzamil
yace “Dad musai munje mun shirya zamu zo,nasanma Kawu yariga ya karbi auren”
Dad yace “ok nidazaran angama daurin auren zan tafi inada meeting” yabude jakar
dake hanunshi yaciro wani dan karamin akwati yasama Barraq a hannu yace “your
eyeglasses son,take good care of yourself” Dad din Muzzamil yakaraso wurin
yanamishi magana yayinda Muzzamil yaja motar da sauri dan yasan fada Dad zaimai
suka tafi hotel dinsu.

Dakin Muzzamil suka shiga, sai alokacin yabude akwatin yaciro glass din yasa,
ahankali ya furta “Alhamdulillah” Muzzamil dake gefenshi yay murmushi yace”Ala
kulli hal”zama Barraq yay akan gado, tashi yayi yace “Men yimin order din
abinci,bari nai wanka” yawuce bathroom.

Fitowa yayi daure da towel daure a kwankwaso sai aranan nakare mai kallo,namiji ne
kakkaura,fari tass yake jajjir kana ganinshi kasan yahada jini da turawa,yanada
yawan gashi ajiki, ga gashin kanshi mai yawa baki sidik,lips dinshi Jane sosai
idonunshi manya ne,amma kwayar idon wani irin blue ne, yanada tsayi jikinshi a
mummurde.
Zama yayi yadau coffee dake gefen abincin da aka kawo mishi ya shanye tass sanan ya
dauko Basmatic rice da aka dafadashi da cactus da green beans, yadanci badayawa ba
sanan ya tura gefe Muzzamil yafito daure da towel shima Barraq kalleshi yace”ina
kayan dazan sa?” Muzzamil yabude wardrobe ya dauko mai shadda fara iri daya datashi
ya bashi Barraq ya kallai yace but… Muzzamil da sauri yatareshi yace”I know
nasani,B bayason manyan kaya but kasamana just 4 today kaji” Barr Barraq yay
murmushi ya tashi yasa kayan sunmai mugun kyau. Karfe 12:30 suka gama
shiryawa,Muzzamil yace” B munyi mugun latti,maybe ma anriga ankai baby na,cos I
arrange everything dazaran an daura aure za’a tafi da ita saboda cocktail night
dazamuyi a Abj by 8 nadare” yadanyi murmushi “but lemmi call just to confirm”.
Yakira Yusuf ya dauka yace”ango hope anga B?mu gamunan a hanya zamu wuce da amarya
Abuja” Muzzamil yace”thanks Yusuf, gashinan tareda ni, muma yanzu zamu zamu taho
muhadu later just handle everything”, sukai sallama da Yusuf ya katse wayan.

Yan kayayyakinshi na hotel din ya tattara yakai car,sanan yay settling bill yadawo
daki yasamu Barraq zaune kan kujera ya lumshe idanu. dafashi dayaji anyi yasa ya
bude ido yana kallon Muzzamil, Muzzamil yace”meke damunka,why all d sudden
thinking?Tundazu na lura da hakan?”
Lumshe ido yayi ya bude sanan yatashi yajuya ma Muzammil baya ahankali yace
“Muzammil kwana daya kacal nayi tareda ita,bansan taba bansan kamanintaba,but all I
can tell u is,am in luv with Rufaida, ina sonta,nd is time to save d luv of my
life” yana karasa fadin hakan yay sauri yabude kofa yafita,Muzammil ya mike tsaye
cikeda mamakin abokin nashi Barraq in luv? Ahankali yace”abun mamaki” da sauri
yabishi yatarar dashi a zaune a mota kanshi nakan kujera ya lumshe ido Muzammil ya
zagayo ya zauna a mazaunin direba ya kunna motan sanan yakalli Barraq yace “ina
mukayi B?” Barr Barraq ya kalli Muzzamil da dan gajeren murmushi yace”kauyen daka
daukoni shinake so ka kaini,idan muna kan hanya I will tell yhu everything about
her life” sanan yay sauri ya juyar da kanshi ganin Muzzamil na neman mishi dariya.
Ya kadakai kawai yatada mota aranshi yace Barraq in luv,hmm wot a surprise!.

Maman Abd Shakur😘


[5/4, 9:24 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

24
Ganin boyewan datayi akan bishiya bashi zaisa yau afasa jefeta ba yasa ta sauko
daga kan bishiyar mangoron tana kuka na fitan hankali da tulunta a hannu, tafiya
take kowa na kauyen ana nunata ana cewa “ga wacce za’a jefe a kofar gidan mai gari
anjima,ankamata da namiji suna lalata,namijin ma bature fa” ko kallon mazan da suke
magana batayi ba saidai ma takara fashewa da kuka tawuce gida shiga gidan tayi da
sallaman ta takarasa tsakar gida ganin Duduwa dawasu kattan maza su uku,Duduwa na
zaune akasa suko suna tsaye bakake dasu hakan yasa tasaki tulun akasa,batasan
lokacin da wani zazzafan fitsari ya tsiyayo yabi cinyar ta zuwa kasa ba.

Duduwa ta taso tazo gabanta tace “aikuwa gaskiyar su laminde,gako rigar maza nan
ajikin ta, wlh yau saikin kusa mutuwa saboda azaba Rufaida” taja hanunta Rufaida
tafara tittirjewa tana ihu dan “Allah Duduwa karki kaini gurinsu, mezasu min?” tana
ihu haka Duduwa tadinga janta akasa ta kukkuje,Duduwa ta jefata tsakiyar mazan
tace”Mujittafa gatanan ka daketa,kaimata bulala dari, kadaki bashin gyadar ka data
batar, sanan kushiga daki dukanku kuyi duk abunda kukaga dama da ita,dama ai tadawo
karuwa inkunga damama dukanku Ku ukun Ku afka mata a lokaci daya ba matsala ta
bace”. Mujittafa yasa hannu yadaga Rufaida tsaye dake kuka sosai yana karemata
kallo sama da kasa da wararran bakin nan nashi da ba hakoran gaba yace”ahh Duduwa
ai wlh bama saina daketa ba,kawai afka mata kadai idan nayi nabar miki bashin
gyadar ” Duduwa da sauri ta mike kaman mahaukaciya tace”ninace kuyi mata bulala
dari,maza takebi” da sauri ta shiga daki taciro sharbebiyan dorunar ta mai baki 4
da wayan wuta tahadesu ta nannade tana mikama Mujittafa tace “gashi kacimin ubanta
yanda bazata Kara neman mazaba” Rufaida tafasa ihu ta kankame jikinta tana kuka.
Mujittafa yace”haba Duduwa saikace ba jikarki ba zakice azaneta da wanan doruna
haka”Duduwa ta nuna kirjinta” Ni Ni nace kadaketa da ita,kuma Rufaida ba jikata
bace ban hada jini da itaba,yar tsuntuwace, asiri nake rufamata danama bari ta
zauna Dani ina bata abinci,Ku cimin ubanta kuma kasheta Ni banda asara, kumata
bulala dari sanan Ku wurgata bukka Ku afakama bunsurar” Mujittafa yakara washe
jajayen hakoran yace “kwantar da hankalin ki Duduwa dole mu ladaptar da shegiyar da
duka,sanan dukanku mu afka mata mu yagata,yanda bazata Kara marmarin bin mazaba”,
Duduwa takara gyara daurin zani tace “yauwa haka nakeso” ta nuna sauran mazan tace
“Ku dagata kujumai ita yamata dari abaya”.

Rufaida na ihu, kururuwa, kuka,shesheka, haka suka dauketa, daya ya rike hannuwanta
dayan kuma kafafunta suka juyata, Duduwa tasama Mujittafa dorinar a hannu tace
“yauwa cimin ubanta”. Mujittafa iya karfinshi ya zaula mata daya abaya, ihu
Rufaida tasaki tawani bankare kaman zata fadi akasa saboda azaba, Duduwa tace”
kuriketa da kyau yar yarinyar nan tafi karfin kune?,kaikuma Mujittafa haka ake
dukan mazinaciya budurwa yimata da karfi”. Mujittafa yakara daddagewa yakara zubama
Rufaida abaya Wanda saida rigan Barr Barraq ya barke ta baya, masu karatu Ni kaina
kasa daurewa nayi nafito daga gidan dan duba wai har yanzu su Barraq basu
isobane???.

Paka motan sukayi ahanya Barraq yaga wata yar yarinya dauke da tulu zata wuce
yace”dan Allah baiwar Allah inane gidan Duduwa? ” yarinyar tajuyo tace $Chan cikin
kauye ne” Muzammil yace “zaki iya shiga mota ki kaimu?” Da sauri ta bashe baki
“eh,eh wlh zan kaiku, zaku Sani a gaban mota?” Muzammil yace “eh muje” da sauri
taje tana bubbuga kofan ita adole zata bude Muzammil ya bude mata ta shiga ya kulle
sukaja motar tana nuna musu hanya har kofar gidan Duduwa, yarinyar tace “ga gidan
nan”, Barraq ya dago kanshi kirjinshi yace Dumm ganin yanda yan mata da matasa suka
taru a kofar gidan ana leken cikin gidan, ahankali suke tafiya yarinyar na gaba
suka kukkusa mutane dake kallonsu. tunkafin sukai ga zauren sukejin ihu Wanda yasa
jikin Barr yafara rawa dan yagane ihun Rufaida ne, muryan Duduwa sukaji tana yauwa
hamsin kenan, kai Mujittafa wanan na hamsin din bai shigeta ba,da karfi sosai
zakayi sai ansake Mujittafa ya zuba mata daya lafiyayya Rufaida bakajin ihunta
saboda muryarta ta dishe gabaki daya da sauri suka shiga gidan,aiko mutanen kofar
gidan suka biyosu, jikin Barr yahau rawa ganin yanda kattai suka tale Rufaida suna
duka ya kalli Duduwa, yarinyar data rakosu tace “ga Duduwa Chan ga Rufaida nan ana
duka”, dunkule hannu Barr yayi Muzammil ya rikeshi amma ina ya fizge jikinshi
yakarasa wurin dawani irin mugun zuciya Mujittafa ya daga dorinar zai shaulama
Rufaida yaji an shakemai wuya,Barraq ya shakemai wuya da karfi kanshi na girgizawa
tsabagen fushi, Mujittafa ko motsin kirki baya iyayi, Duduwa tazo tana rikemai
hannu” Malan kai waye, mutum na hukunta jikata kazo ka shakemai wuya?” Hannu daya
Barr yasa ya ingiza Duduwa ta zube a wurin, suko wayanda suka rike Rufaida suna
ganin bature ya shigo ya shake wuyan Mujittafa suka saki Rufaida akasa suka arce
aguje, Ganin Barr na shirin kisa yasa Muzzamil yazo yace “B control ur temper, just
let him go” da kyar ya fizge hannun Barraq daga wuyan Mujittafa, Barraq ya fizge
hannunshi daga hannun Muzammil yahau dukan Mujittafa Kota ina yana buga kanshi da
bango hawaye na zuba daga idonshi, Muzzamil ya fizgoshi ya rikemai kafada yana
jijjigashi “B I said is OK,control ur anger,Les just take her to hospital” Barr
yasa hannu ya goge Hawayen idonshi yaje gaban Rufaida dake akife jini yabata
bayanta, duka rigar ta farfashe saboda duka, ya dauketa chak ya daurata kan
cinyarshi ya rungume ta sosai ya lumshe ido,hawaye yakara gangaro wa daga
idanunshi.

ya mike ya dagata kaman tsintsiya a hanunshi yay hanyar fita da sauri Duduwa ta
tashi kaman mahaukaciya tana dukan bayanshi” ina zaka kaimin jika? wayyo jama’a
kutaresu masu Satan yara ne” haka suka fita daga gidan babu Wanda yay gigin zuwa
inda suke, ya shiga bayan mota har alokacin yana rungume da ita,Muzammil ya rufe
kofan yakoma gaba ya zauna sanan yatada motar, kalma daya Barraq ya iya
fadi”kaisauri mu kaita asibiti,bata numfashi “.
Maman Abd Shakur😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 21 to 24KAINE SIRRI NA 34 to 37 →
KAINE SIRRI NA 25 to 33
Posted on May 12, 2016 by mamanshakur
[5/6, 9:51 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

25
Wani asibiti dasuka gani a hanyar barin garin Jigawa suka tsaya,Barraq ya dauko ta
suka shiga ciki, kin dubata sukayi waisai suntaho tareda police dakuma record din
abunda yafaru dahar aka mata wanan mugun dukan. fitowa sukayi Barraq ya shigar da
ita baya,ya kwantar da ita a kife saboda yanda bayan ke jini,ya kalli Muzzamil
yace”mutafi Abuja kawai,zan kira family Doctor dinmu ” yakoma gaba ya zauna
Muzzammil ya tada motar suka dau hanyar Abuja.

Wuraren 5 na yamma suka isa Abuja yace ma Muzammil” just kaini gida,kaisai kawuce
kasan friends dinmu na nemanka yanzu” Muzammil ya saukeshi akatafaran harabar
gidansu Barraq yadan mishi murmushi yace” thanks for everything, katafi they need
you more than I” Muzammil ya kada mishi kai kawai Barraq ya fito ya bude kofar baya
yasa hannu ya dauketa yay side dinshi da ita, ahankali ya kwantar da ita kan gado,
yacire tazarcen dake jikinshi yafito daga bedroom din yafita daga dakin zuwa dakin
Amma, da sallama ya shiga, Amma ta amsamai da murmushi tace”ahh mutanen biki har an
dawo” yay murmushi yace “eh amma”, yadan Sosa kai yace”emm Amma dama damuna mota
nakira Dr Faruk nacemai muhadu a gida yazone?” Amma tadanyi dariya tace”oh,tsufa
yasoma kamani,abunda fa zan fadama kenan, yazo dazu yanama falon baki” Barraq yace
“ok ina auta?” Amma tace “auta tatafi islamiyya” yace “ok”.

yajuya zai fita Amma tace “kaine bakada lpy?incedai ba nama kaci dayawa ba?” Ya
girgiza kai tareda fadin “no Amma bani bane” yasakai yafita daga dakin, dakin baki
yaje yasamu Dr Faruk a wajen suka gaisa sanan yace “muje ka ganta”. yana gaba Dr
Faruk na baye dashi,har bangaren shi, bedroom yabude suka shiga kwance take rubda
ciki saidai fuskarta na kallon hanyar kofa, mamaki yahana Barraq magana saidai
yadaga hannu yana nunata,da kyar bakinshi ya iya furta “Ku..kur..ma! Dama kece
Rufaida??” danshi kwata kwata sai yanzu ya lura dama fuskanta,sai yanzu ya kalli
fuskarta. Dr Faruk dake bayanshi yace”lpy Barr naga ka tsaya ne” Barr yadan girgiza
kai tareda fadin no,shigo kaduba bayan ya matsa ma Dr Faruk yakaraso cikin dakin
Barr ya jingina da bango yay shiru yana mamaki to maizai sa farkon haduwarshi da
Rufaida tamai karya? Maganan Dr Faruk yadawo dashi daga duniyar tunanin daya lula
yace”amm Barr zan samu light shimi haka da karamin bowl” Barr yace “eh,I think so”.
yafita zuwa shashin Amma kitchen ya shiga ya dauko karamin bowl saiya wuce dakin
auta, wani Babban akwati daya kawomata lokacin dayaje Russia ya dauko ya bude wani
shimi na mata mara nauyi mai dan girma ya dauko yafito daga dakin yakoma shashin
shi, ya shiga bedroom din yabama Dr Faruk ya karba,almakashi Dr yasa ya yaga rigan
dake jikinta daga sama zuwa kasa ta baya, bayanta gabaki daya ya bayyana, duk tabon
bulala sai fitar da jini suje, Dr Faruk yajuyo ya kalli Barr yace”dis is child
abuse, waye ya daketa haka 4godsake?”Barr yay folding hannu a kirji ya sauke ajiyan
zuciya ahankali yace”her Grandma, labarin nada tsawo” Dr Faruk ya girgiza kai kawai
yabude jaka ya ciro wayansu gora guda biyu da allurai biyu ya yanko auduga da
almakashi ya tsoma audugar a cikin ruwowin daya hada a bowl sanan yakai bayanta
yadaura kan ciwon ihu tasaki tareda kama zanin gadon da karfi tana shure shure da
kafa, Barr ya lumshe ido, ganin bazai iya daurewa ba yasa yafita daga dakin ya
zauna akan kujera ya dafe kanshi yana huci, jiyake kaman ya dauke mata ciwon.
Maman Abd Shakur😘
[5/6, 10:06 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

26
Fitowar Dr yasa ya dago kanshi ya kallai tareda fadin “hw far Dr?akwai any ciwo?”
Dr Faruk yace “no any ciwo,kawai yarinyar na bukatan hutu tareda abinci mai
kyau,yanzu tana bacci zata iya farkawa yau, hala kuma sai gobe ko jibi ma self,cus
nabata allurai dazasu sa jikinta yay relax” Barr yace “to thank you” yamikamai
hannu sukai sallama yatafi. fadawa kan kujera yayi tareda fadin “why Rufaida? Maisa
kikaimin karya? Duda kin ganni a kauyen Ku baki taba nuna kinsani ba”, da sauri
yace “to kodai shine d reason y take yawan cemin inada kirki? Ko saisa ta taimake
ni cus nima nataba taimakon ta?” Ahankali ya furta yess hakane yanzu na samamma
tambayata amsa. Dan murmushi yayi yace “in sha Allah wahalar ki takare,is a promise
Rufaida, saina share miki hawaye, iyayenki dakika rasa saina maye gurbinsu” lumshe
ido yayi tareda gyara kwanciya akan lumtsatsiyar kujeran yadaura hannu kan zuciyar
shi saikuma yarufe ido da sauri yanadan murmushi daban gane maanar shiba.
Ringing din dayar wayarshi daya bari a gida yasa ya mike a kasalance ya jawo wayar
dake kan center table,ganin sunar daya bayyana a screen yasa yay murmushi ya dauka
harda daga kafa yace” mana!I missed yhu” daga dayan bangaren naji matar da yaren
turenci tace” my baby I missed you ya kk?” Yay murmushi yace “mee too mummy ya
jikin ki? Hope kina zuwa check up dinki?” Tace “yes ina zuwa”. bayan sunyi dan
maganganunsu na da da uwa sanan ta magana cike da damuwa tace ” son har Yanzu
bakaga yarinyar dakace zaka kawomin ba,nagaji da zama nikadai no grandson, no in-
law, inason wani dazan kula dashi and pamper with luv”murmushi yayi yace”Mummy na
ganta,but batada lpy”arude ta tambayi maiya sameta? ya sanar da ita komi kan
Rufaida, kuka sosai Mum din Barraq tai a waya da kyar ta iyayin shiru sanan
tace”son I beg yhu duk yanda zakayi kayi kamata visa yau tomorrow ka kawomin ita,I
need to shower her with my luv,zan zame mata uwa data rasa,banga Rufaida ba amma
inason Rufaida, banga Rufaida ba amma Rufaida tadawo yata,just try son, ka kawomin
ita gobe,I need to take good care of her” ajiyar zuciya yayi sanan yace”ok mummy,
in sha Allah gobe zankawota” sukai sallama ya katse wayan sanan yatashi ya shiga
Bathroom yay wanka anan bayin falon,yawuce bedroom dan dauko kayan dazaisa yatafi
yaga ko zai iya samarmata visa, bude kofa yayi adaidai lokacin tana fadin “Umma
tsuntsun,zai kamani,wayyo Umma yana Jana yana bina”.. Da sauri yakarasa cikin dakin
ya tsugunna agaban gadon yana hura mata iska a fuska tareda shafa zufan daya gani a
goshinta,ya saka hanunshi cikin nata yana kallon fuskarta dayay fayau, gashi
gashin gefen fuskarta sun kwanta lub tai wani irin simple kyau, ahankali yakai
bakinshi kan goshin ta ya sunbaci goshin tareda sa hannu ya share wurin yana
murmushi yana kallon fuskarta yace” wani tsuntsu ke damun min baby na? Koma wani
tsuntsu ne just go, yabarmin baby na tai bacci” ahankali yaga ta sauke ajiyar
zuciya tacigaba da bacci tareda kankame hanunshi sosai.

Maman Abd Shakur😘


[5/10, 5:55 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

27
Ahankali ya zame hanunshi daga nata yadau kayan dazaisa yafita daga dakin yaje falo
ya shirya tsaf ya fesa turare, sanan yadawo dakin ya tsaya a gaban gadon yana
kallon ta hanunshi ya zura cikin aljihu ya dauko wayarshi ya tsugunna ya dauketa
hoto yana mai murmushi ahankali yace”sleeping beauty, maybe I can use it as her
passport”. yadau car keys yafita daga dakin.
******
Bayan kwana biyu.

Yau takama litinin,fitowarshi daga kotu kenan shida PA,sai murmushi yake,kokari
press suke suga sunmai yan tambayoyi danyau ya kayar da Babban mai saida miyagun
kwayoyi,yatona mishi asiri shida mukarraban sa inda aka kaisu gidan yari amma baida
lokacin amsasu dan tafiya gareshi yau. Tun kafin yakai wurin mota aka budemai ya
shiga da sauri yana duba agogon hanunshi tareda dafe kai”Lord! Nakusa lattin flight
to Russia ” ya kalli bodyguard dake tuki yace” kai sauri 5 flight dinmu zai tashi
and dis is already 4:00pm”.
Suna isa gida yafito daga mota, yana cikin sauri yaje dakinshi yaji an fado
bayanshi ana “uncle B oyoyo”, juyota yayi yana murmushi yaja kunnen ta “auta bakiji
ko”, tadanyi Kara ya sake kunen, rikemai hannu tayi suka cigaba da tafiya tana
bashi labarin school yau, saida yakai bakin kofa ya tsaya. auta ta kalleshi, yay
mata murmushi yace “yauwa Auta oya tafi kinji anjima zanzo, ki gaida Amma” ta noke
wuya tana murmushi. yadan daure fuska tareda fadin “tafi mana”tai zuru-zuru tana
kallonshi tace” uncle B kullum kullum yanzu baka bari nashiga dakin ka why? Abu
kake boyemin ko?amma ai kace ni kawarka ce ko? Kuma ina fadama all my secrets”
tabashi tausayi dakuma dariya yadan rage tsawo tareda sa hannu ya share dan guntun
hawayen daya zubo a idonta yana murmushi ya girgiza kai yace “kinsan banason kuka
ko?” Ta dagamai kai, yace” ok, ai mun riga mun kulla fadama juna secret, banason ki
shiga dakinne cus is too dirty, kuma nasan bakison datti ai,oya tafi anjima zansa a
gyara sainakira kizo kinji” Ta girgiza kai tareda juyawa dan tafiya shikuma ya bude
kofa ya shiga dakin.

Auta na ganin ya shiga tajuyo tana dariya,”ai wlh sainaga yanda dakin Uncle B yay
datti,dama Amma tace dakinshi baya datti wai yanada tsafta, yau sainaga dattin
dayayi ” tasa hannu ta bude dakin a ahankali ta shiga, ganin bataga datti a falon
ba yasa tai dariya tareda kwafa, tayi hanyar bedroom dinshi tasa hannu ta bude
kofan a hankali dan karyaji motsinta, ganin mace a kan gadon Uncle B bayanta a bude
duk shaidan bulala dasukai wani iri ba kyan gani ga gashin kanta duksun barbasu
akan gadon hakan yasa Auta tasaki ihu tareda kankame jikinta.

Maman Abd Shakur😘


[5/10, 6:19 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

28
Da sauri B yafito daga bathroom yana kallon auta dake ihu, jikinta yahau rawa
ganinshi rai abace,yana tsaye inda yake yace mata “zonan” kuka tasa sosai dan tasan
yau saita gane kurenta, tafara sharban hawaye tana “yakuri Uncle B, wlh zan dinga
jin magana, bazan karaba dan Allah karka daken”, fizgo hanunta yayi takara fasa ihu
tana” kayakuri,plz-plz-plz!” tausayi tabashi sosai,hakan yasa yafasa dukanta yace
“wuce kitafi kafin na bata miki rai” juyawa tayi ba musu tafara tafiya hartakai
kofa tasake juyowa tana kallonshi yace “what?” tace “Uncle B batada lafiya ne?”Tai
maganan tana nuna Rufaida dake kan gado, daga mata kai yayi shima tareda kallon
Rufaida dako numfashin kirki batayi, Auta ta girgiza kai “Allah sarki,Uncle indan
je intabata?” Ya dade yana nazarin ta kafin ya daga mata kai, da sauri auta taje
gaban gadon ta tsugunna ta kama hannun Rufaida tana kuka ahankali saboda yanda taji
tabata tausayi sosai tasake juyowa ta kalli B tace”Uncle B baka kaita asibiti
ba,ciwonta nata jini,kaga yama bata zanin gadon,ka kira mata Dr Faruk,wlh ina sonta
Uncle ” Barr yakaraso wurin shima ya tsugunna yakama dayan hanun Rufaida yarike
sanan yace”banason nasake kiranshi dan banason kowa yagane tana gidanan, yau zan
kaita wurin Mummy a Russia, za’a kaita asibiti achan” .

Yasake kallon Auta dake kallon Rufaida tana hawaye,tana hura iska akan ciwon yace
“Auta”, tajuyo ta kallai yace” karki fadama Amma kinga Mara lafiya adakina, is our
little secret kinji?” Tasa hannunta a harshe tareda fadin “I promise uncle “. ya
shafa kanta tareda fadin “good Gurl, kinsan wheelchair din Daddy dayay amfani dashi
lokacin da baida lafiya?” Ta girgiza kai da sauri tace “eh nasani,ai yanama cikin
store dinmu nan Amma ta ajiye” yace “yauwa jeki dauko min” tafita da gudu kafin ta
shigo yagama shiryawa, tana shigowa da wheelchair din ta ajiye tazo kusadashi ta
tsaya tace “Uncle yanzu zaku tafi airport? ” yace “eh”, ta kalli Rufaida sanan ta
kalleshi tace “but ai wanan kayan jikinta sun baci da blood, ka chanza mata wasu”
yadan tabe fuska yace”auta Ni ban iya samata kayaba, abarta ahaka kawai intaje
wurin Mommy tasa mata” yay maganan kaman wani Yaro ,auta tace “laaa nidai na iya,
bari na dauko mata wayanan kayan dakasiyomin manyan nan, Wanda sukamin yawa”, kafin
yay magana harta fita daga dakin da gudu ko minti biyu batayiba ta dawo dauke da
wani Jan dogon sket da shimi baki very light, saidan karamin hijabi da bathroom
slippers mai kyau baki shima.
Ta ajiye kayan kan gado Uncle B ya matso kusa da ita yace “auta keda Amma kesa miki
kaya balle har ki iya sama wani?” Buga kafa tayi a kasa tace “ai wlh na iya,ni
kawai dagamin ita ta zauna saina sa mata” yay kwafa tareda fadin “ok”, ya dawo kan
gadon ya dago Rufaida ahankali ya zaunar da ita akan jikinshi yace “oya samata”,
Auta ta tsaya agabansu tana kallon fuskarshi yace “what again?” Tace “to Uncle baka
rufe idoba, ba Amma na tace babu kyau babban namiji ya kalli jikin wata ba…” bata
karasa maganar ba ya kulle ido da sauri. Auta tasa hannu tacire shimin dake jikinta
da, ta samata Wanda ta dauko,sanan tace “nagama saura sket” ya kwantar da ita duk
idonshi arufe Auta tasamata sket,tasa mata karamin bakin hijab, da slippers sanan
tace “to bude idonka kagani”ya bude ya kalleta yaga tamai kyau Sosai murmushi yayi
ya daurata akan wheelchair Auta tarakosu har wurin mota yasata a ciki,ya shiga PA
ya shiga ya jasu sai airport. Suna zuwa da sauri suka shiga jirgi,jirgi ya daga sai
Russia.

Maman Abd Shakur😘


[5/10, 6:37 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

29
Karfe 7:00am agogon garin Russia ya nunamin, adaidai wanan lokacin Babban jirgin
dasuke ciki na Emirate Airline yay landing, dauko wheelchair yayi yabudeshi ya
kwance mata belt ya dauketa yasata akai sanan ya gunguro ta suka fito, lumshe ido
yayi lokacin da sassanyar iskan garin ya bugi ilahirin sassan jikinshi sanan ya
bude idanuwanshi yana kallon filin jirgin. hango wasu motoci su uku dayayi hadaddu
bakake sai sheki suke an rubuta a jikin license plate din ADANMA MATTHEW yasa yay
murmushi yace”das my Momma” yakara sauri suka suka sakko daga benen jirgin, Wuraren
motocin ya dosa yana kaiwa ya ajiyeta a wurin sanan yasa hannu zai bude marfin
motan yaji muryan wata mace da harshen turenci tace”basai ka bude kofa ba,your
Momma is right here champion” dawani irin ihu Barr Barraq ya juyo ya rungume wata
kakkyawar dattijuwa, baturiyar mace,tana sanye da doguwar riga baki,idanunta sanye
da farin glass wacce nasan na matsalar ido ne,ga bodyguards a bayanta kusan su
goma,Barraq ya rungume ta yana mata kiss a kumata “I missed yhu mommy!miss yhu soo
soo much”chusa hannu tayi acikin gashin kanshi tadan Sosa sanan tace “aika kyaleni
na duba daughter na ko” langabe kai yayi tareda fadin no,ya daura kanshi abayanta
ahaka suka karasa wurin motar, da sauri yadaga kanshi daga jikinta yakarasa wurin
Rufaida daya gani shame shame akasan wurin ga wheelchair ma yafadi, sai alokacin
yatuna dayana saurin zuwa rungume Mom yaji yature wani abu, dagata yayi da sauri ya
rungume ta “am sorry Rufaida, kiyafemin dan Allah..” Mom ta tsugunna ta karbeta
daga hannun Barraq ta rungume ta.
Dago kanta tayi ta shafa fuskarta tace “my Preety daughter” ta manna mata miss a
goshi,kallon bodyguards tayi da ido suka bubbude kofofin motar Barraq ya karbeta
yasata a cikin mota,Mom ta shiga sanan Barraq ya shiga ya daura kanshi akan kafadar
Mum yana mata shagwaba”Mum am hungry wlh,I missed wanan miyan mushroom dinan dakike
min” dan harara tamai sanan ta shafa gefen fuskar Rufaida dake kan cinyarta tace”
karka daman,Ni yanzu damuwata yata tasamu lafiya” Barraq yay murmushi tareda daga
kanshi daga kafadar Mum kaman yay fushi, Mum ta juyo ta kalleshi tai murmushi kama
hanunshi tayi ya kalleta ahankali tace “dont be jealous, u will always be my little
boy,my little champion and my handsome boy” hawaye yadan ciko idonta ta shafa gefen
fuskar shi”u are all I have,I soo much luv yhu son”murmushi yayi ya daura kanshi a
kafadarta yace”luv u 2 Mummy ” ta sa hannunta ta shafa kunnenshi dayan hanunta kuma
ta shafa kan Rufaida ta lumshe ido tareda fadin”I luv yhu both”.

Maman Abd Shakur😘


[5/10, 8:32 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

30
Wani Babban gida suka sauka, san kowa kin Wanda yarasa gidan daya wadatu da
ma’aikata sanye da kayan aiki, suna sauka security ya dauko wheelchair Barraq da
kanshi ya fito da ita dan yana kishin yaga wani yataba mai Rufaida ya daurata akan
wheelchair chair zai gungurata mum ta rike hannunshi tareda girgiza mai kai,
tace”let me,is my duty as a mother nakula da yata”ahankali Barraq ya zame
hannunshi, da kanta ta gungurata har cikin main palor, inda wasu manya likitoci su
biyu suke gaisheta,bata kulasu ba tawuce bedroom dinta da Rufaida, sanan tafito
falo ta amsasu cikin raha kafin su dunguma zuwa bedroom dinta. bayan sun duba bayan
tane likitan daya shahara kan matsalar fata yace kawai sufita subashi wuri he can
handle d situation. duk suka fita kusan awaya daya yayi a dakin sanan yafito yakira
Mum, Barraq yabita suka shiga daki anan yake musu bayanin yamata allurai sanan yasa
mata wasu magungunan a ciwon yarufe su da bandeji, kwana bakwai zai dawo ya cire
bandejin zasuga ciwokan sun warke tabon yabace. Barraq yace “Dr farfado wan tafa?”
Dr Yay murmushi yace “anjima kadan zakuga tafarfado,karku damu” mum tai settling
din aljihun shi yatafi.
Zama Mum tai akujera da sauri Barraq ya sanya kanshi akan cinyarta, ya sauke ajiyan
zuciya “Mom am so tired” Mum tai murmushi tace”Son Dad dinka yamin complain akanka,
anjima idan kaci abinci ka huta Me and yhu will have a serious talk” akasalance ya
tabe baki yace”okkk” ya tashi daga jikinta yace” Mum a aikomin da abinci dakina,
zanje nai wanka yanzu” ya wuce, juyowa yayi ganin Mum na magana da maid din dake
in charge of girkin gidan yasa ya shiga dakinta da sauri ya maida kofa ya rufe. ya
tsaya yana kallon yanda aka nannade ta daga wuyanta zuwa kwankwasonta da bandeji,
sai sket din da Auta ta tasa mata ne kadai a jikinta. karasowa ciki yayi ya zauna
a gefen katafaren gadon yakama hanunta yarike ya sauke ajiyan zuciya sanan
yace”mekike jira Rufaida da haryanzu kinki farkawa na nuna miki asali so? Don’t
yhu think dat I need yhu Rufaida? I luv yhu d way u are” yakai hanunta bakinshi ya
sumbaci hannun sanan ya kifa kanshi kan hannun”I beg yhu Rufaida kitashi,lokaci
yayi dazan nuna ma Dad ke a matsayin matata” maida hanunta yayi ya ajiye sanan ya
mike tsaye tareda chusa hannu cikin aljihun wandon shi yana huci, juyawa yayi
yafita daga dakin,kalle -kallen yayi ganin Mum bata wurin yasa yajuya da sauri
yatafi part dinshi,Mum tafito daga inda ta labe tana murmushi “so he luvs her” Bude
kofar dakin tayi ta shiga tana mai farin ciki.

Part dinshi yatafi kallon dakin yayi yaga komi yana nan yanda yake har ankawo mishi
breakfast dinma,murmushi yay ya wuce wurin wardrobe budewa yayi yazaro old sim card
dinshi na garin ya bude wayarshi yacire na Nigeria yasa ya kunna ya cilla wayan kan
gado, ya shiga bayi yay wanka yafito daure da farin sabon towel a kwankwaso, fadawa
kan gado yayi sai bacci.
Bashi yatashi ba sai daya na rana, bayi ya shiga yasake wani wankan yay alwalan
salla, yafito yasaka kayan Shan iska yay salla. Part din Mum yatafi dancin lunch
bai ganta afalo ba yawuce dakinta yana tafiya ahankali tun kafin ya shiga dakin
yake fadin”Mommyyyy am hungry “a shagwabe yake magana, bude kofa yay ya shiga dakin
yace” Mommy am hung…” Bai karasa maganar ba ganin Rufaida na mutsu mutsu tana
kokarin fadowa daga gado, da gudu yakara sa bakin gadon ya tsugunna kafin yay wani
yunkuri tafado kan jikinshi, da sauri ya rungume ta a kirjinshi,ganin tadena motsi
yasa ya kwantar da kanta akan cinyarshi yana shafa gashin daya kwanta a goshinta
yana murmushi. Ganin idanunta na motsi,su na rawa yasa yace”Rufaida! ” ahankali
take bude idanunta tun tana ganin dishi-dishi har idanun suka washe, kyawawan
kwayoyin idanunta suka sauka kan kakkyawan fuskar Barr Barraq dake sanye da
eyeglasse,lumshe idonta tayi takara budesu tagadai shine yake kallonta kuri, Ihu
tafasa mai Wanda saida yakusa fasamai dodon kunne yunkurawa tayi zata mike takara
sakin wani ihu jin azababben zafin da bayanta yake, karasa mikewa tsaye tayi jin
zafin yay yawa yasa tafara tangal tangal zata fadi,luuu tayi zata fadi tajita
tafada hannun wani, bude ido tayi taga Barr Barraq da sauri ta maida idon ta kulle
gam jikinta na rawa hawaye na bulbulowa ta gefen ido suna gangarawa kunnenta. Murya
Chan kasa taji yace”tsoron kallona kike saboda kinsan ke mai laifice ko?maiyasa
zakimin karya?” kwace kanta tayi daga jikinshi tana kuka a duke tafada gadon data
gani ta matsa Chan jikin bango ta kankame jikinta tana kuka sosai jikinta na rawa”
jawo stool yayi ya zauna a gaban gadon yana kallonta cikin tsawa yace “answer me!
Maisa kikamin karya?”.
Maman Abd Shakur😘
[5/11, 4:16 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

30
Wani Babban gida suka sauka, san kowa kin Wanda yarasa gidan daya wadatu da
ma’aikata sanye da kayan aiki, suna sauka security ya dauko wheelchair Barraq da
kanshi ya fito da ita dan yana kishin yaga wani yataba mai Rufaida ya daurata akan
wheelchair chair zai gungurata mum ta rike hannunshi tareda girgiza mai kai,
tace”let me,is my duty as a mother nakula da yata”ahankali Barraq ya zame
hannunshi, da kanta ta gungurata har cikin main palor, inda wasu manya likitoci su
biyu suke gaisheta,bata kulasu ba tawuce bedroom dinta da Rufaida, sanan tafito
falo ta amsasu cikin raha kafin su dunguma zuwa bedroom dinta. bayan sun duba bayan
tane likitan daya shahara kan matsalar fata yace kawai sufita subashi wuri he can
handle d situation. duk suka fita kusan awaya daya yayi a dakin sanan yafito yakira
Mum, Barraq yabita suka shiga daki anan yake musu bayanin yamata allurai sanan yasa
mata wasu magungunan a ciwon yarufe su da bandeji, kwana bakwai zai dawo ya cire
bandejin zasuga ciwokan sun warke tabon yabace. Barraq yace “Dr farfado wan tafa?”
Dr Yay murmushi yace “anjima kadan zakuga tafarfado,karku damu” mum tai settling
din aljihun shi yatafi.
Zama Mum tai akujera da sauri Barraq ya sanya kanshi akan cinyarta, ya sauke ajiyan
zuciya “Mom am so tired” Mum tai murmushi tace”Son Dad dinka yamin complain akanka,
anjima idan kaci abinci ka huta Me and yhu will have a serious talk” akasalance ya
tabe baki yace”okkk” ya tashi daga jikinta yace” Mum a aikomin da abinci dakina,
zanje nai wanka yanzu” ya wuce, juyowa yayi ganin Mum na magana da maid din dake
in charge of girkin gidan yasa ya shiga dakinta da sauri ya maida kofa ya rufe. ya
tsaya yana kallon yanda aka nannade ta daga wuyanta zuwa kwankwasonta da bandeji,
sai sket din da Auta ta tasa mata ne kadai a jikinta. karasowa ciki yayi ya zauna
a gefen katafaren gadon yakama hanunta yarike ya sauke ajiyan zuciya sanan
yace”mekike jira Rufaida da haryanzu kinki farkawa na nuna miki asali so? Don’t
yhu think dat I need yhu Rufaida? I luv yhu d way u are” yakai hanunta bakinshi ya
sumbaci hannun sanan ya kifa kanshi kan hannun”I beg yhu Rufaida kitashi,lokaci
yayi dazan nuna ma Dad ke a matsayin matata” maida hanunta yayi ya ajiye sanan ya
mike tsaye tareda chusa hannu cikin aljihun wandon shi yana huci, juyawa yayi
yafita daga dakin,kalle -kallen yayi ganin Mum bata wurin yasa yajuya da sauri
yatafi part dinshi,Mum tafito daga inda ta labe tana murmushi “so he luvs her” Bude
kofar dakin tayi ta shiga tana mai farin ciki.

Part dinshi yatafi kallon dakin yayi yaga komi yana nan yanda yake har ankawo mishi
breakfast dinma,murmushi yay ya wuce wurin wardrobe budewa yayi yazaro old sim card
dinshi na garin ya bude wayarshi yacire na Nigeria yasa ya kunna ya cilla wayan kan
gado, ya shiga bayi yay wanka yafito daure da farin sabon towel a kwankwaso, fadawa
kan gado yayi sai bacci.
Bashi yatashi ba sai daya na rana, bayi ya shiga yasake wani wankan yay alwalan
salla, yafito yasaka kayan Shan iska yay salla. Part din Mum yatafi dancin lunch
bai ganta afalo ba yawuce dakinta yana tafiya ahankali tun kafin ya shiga dakin
yake fadin”Mommyyyy am hungry “a shagwabe yake magana, bude kofa yay ya shiga dakin
yace” Mommy am hung…” Bai karasa maganar ba ganin Rufaida na mutsu mutsu tana
kokarin fadowa daga gado, da gudu yakara sa bakin gadon ya tsugunna kafin yay wani
yunkuri tafado kan jikinshi, da sauri ya rungume ta a kirjinshi,ganin tadena motsi
yasa ya kwantar da kanta akan cinyarshi yana shafa gashin daya kwanta a goshinta
yana murmushi. Ganin idanunta na motsi,su na rawa yasa yace”Rufaida! ” ahankali
take bude idanunta tun tana ganin dishi-dishi har idanun suka washe, kyawawan
kwayoyin idanunta suka sauka kan kakkyawan fuskar Barr Barraq dake sanye da
eyeglasse,lumshe idonta tayi takara budesu tagadai shine yake kallonta kuri, Ihu
tafasa mai Wanda saida yakusa fasamai dodon kunne yunkurawa tayi zata mike takara
sakin wani ihu jin azababben zafin da bayanta yake, karasa mikewa tsaye tayi jin
zafin yay yawa yasa tafara tangal tangal zata fadi,luuu tayi zata fadi tajita
tafada hannun wani, bude ido tayi taga Barr Barraq da sauri ta maida idon ta kulle
gam jikinta na rawa hawaye na bulbulowa ta gefen ido suna gangarawa kunnenta. Murya
Chan kasa taji yace”tsoron kallona kike saboda kinsan ke mai laifice ko?maiyasa
zakimin karya?” kwace kanta tayi daga jikinshi tana kuka a duke tafada gadon data
gani ta matsa Chan jikin bango ta kankame jikinta tana kuka sosai jikinta na rawa”
jawo stool yayi ya zauna a gaban gadon yana kallonta cikin tsawa yace “answer me!
Maisa kikamin karya?”.

Maman Abd Shakur😘


[5/12, 7:48 AM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

31
Girgiza mai kai tayi tana hawaye “kayakuri bazan karaba”, ya tsareta da ido hakan
yasa takara birkice wa “kayakuri dan Allah…” Bude kofar dakin da akayi yasa Barr ya
juyoda kanshi Mom ce, da sauri takaraso cikin dakin tana ma Barraq kallon tuhuma
cikin harshen turenci tace “maikai ma yarinya na?mesa take kuka?” Barraq yay shiru,
zama tayi kan gadon kusa da Rufaida dake Kuka ta dafa kanta cikin harshen hausa
dabata kware sosai ba tace”daughter na kin tashi?” Rufaida ta daga mata kai jikinta
na rawa tana Satan kallon Barraq da yay folding hannu a kirji yana kallonsu, lura
da hakan yasa Mum ta juyo da kai ta kalli Barraq tadan ballamai harara tace “wuce
katafi tsoranka take” saida ya kalli fuskar Rufaida dashi take kallo da sauri ta
dauke kai sanan yay murmushi yajuya yafita daga dakin.
Mum takara matsowa kusa da ita takama habarta tasa hannu tana sharemata hawayen
dasuke gangaro wa tana girgiza kai tace”shin a matsayina na uwa ya dace naga yata
na kuka na barta taitayi?” Rufaida tai shiru dan ita bata gane yanda take turenci
da sauri sauri. Mum takama hannun Rufaida tarike, da gurbatatchen hausarta
tace”daga yau ni ne mamarki kinji” Rufaida hawaye ya zubo daga idonta tana kallon
Mum, Mum tadan daure fuska tace “banason na Kara ganin hawaye sun zubo daga
idonki,oya tashi muje bayi kiyi brush da wanka sai kici abinci ” da taimakon Mum
Rufaida ta mike tsaye suka shiga bayi Mum taimata brush tareda wanke mata fuska da
kafa da hannu saboda wanka ayanayin da take bazai yuwu ba. Fitowa sukayi Mum ta
Danna wani kararrawa wata maid da kayan aiki a jikinta ta shigo da katon akwati ta
ajiye a gaban Mum sanan ta koma gefe ta tsaya. Mum ta kalli Rufaida tace “zabi
kayan dazaki sa” Rufaida ta kalli kayan kyawun kayan kadai yasa batasan lokacin
data saki murmushi ba,Mum tace”zaba mana kina murmushi” da sauri Rufaida ta chusa
kai a cinya tanamai jin son Mum a ranta dan saitaga wani abubuwan ta kaman na
marigayiya Umman ta.
Mum da kanta ta zabar mata kaya wani pink Daisy gown anmishi ado da fulawowi baki
da pink pant ta ajiye gefen Rufaida tace “ga Wanda nazaba miki daughter” yar aikin
ta rufe akwatin sanan tabar dakin. da kyar kunya yabar Rufaida tasa kayan Mum tasa
aka kawo mata tea mai kauri tasha da indomie da aka dafa mata dan batajin zata iya
cin abincin suba.

Dakinshi ya shiga ya zauna kan sofa karan taba yajawo daga aljihun shi ya kunna
yahau sha yana lumlumshe ido. Maisa duk in Rufaida na kuka tana mugun bashi
sha’awa? Barinma dazu? Inda ace Mum bata shigo ba maybe hala sai yay wani abu
stupid, dafa kanshi yayi tareda fadin “ya Allah don’t let me go astray” yacigaba da
Shan tabarshi kafin daga bisani ya jawo wayarshi yafara neman number Muzammil Ango.

Maman Abd Shakur😘


[5/12, 8:01 AM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

32
Muzammil ya dauka da sauri ganin number Russia dan yasan bazai wuce Barraq ba,”Hey!
I Miss yhu B yaushe zaka dawo ne abeg tunda ka kaita?” Barr yay murmushi tareda
fadin”look who is talking, u miss me a ina? Bayan amarya ta mantar dakai ni”
Muzammil yace” haba man! Kaima kasan u are constant in my heart,hw far ya jikin
Rufaida? ” Barr ya sauke ajiyan zuciya “fine, although Dr yace next week zaizo
yabude,ina amaryan?” Muzammil yace “I no dey house o,nabarta agida nazo chemist ne
zansai pregnancy test nakai mata ta gwada” yabama Barr kunya sosai yadanyi dariya
kafin yace”kai man bayau 3 days dayin auren ba,even though I don’t know much about
medical stuff but nasan is impossible ciki ya shiga a 3 days har yabada symptoms”
Muzzamil yay dariyan shakiyanci yace”sit-down dere, no go marry and know how d
system dey work,sai tsufa kake kaki kayi aure kai sai graduate ko” yay maganan
cikin sigan zolaya dan yasan yanzu Barr Rufaida yar yarinya yakeso. Barr yadan Sosa
kai tareda yin shiru yana murmushi mai sauti,Muzammil yace”answer me now,Ina
ra’ayin naka yaje? Anyway na manta nafada ma jiya naje office dauko wasu files
nahadu da Nanan ka, she was crying telling me u are d luv of her
life,dis,dat,kagane ai bla-bla-bla. Ta tambayen kana ina I have no any other option
but to tell her kana Russia… ” “for God sake Muzammil kadena min maganar Nana, I
hate her,I hate her generations,banason anamin maganar ta, banason mace Mara kamun
kai, ko narasa macen aure bazan aureta ba”, yadan yi tsaki yace “u just ruin my
afternoon, talk later” ya katsa wayan yana huci.

Wacece Nana?
Yar Alhaji Asha jiko Babban abokin Dadin Barraq, Nana tai graduating daga American
university of Nigeria (AUN) inda ta karanci English, Ta waye iya wayewa,ga rashin
kamun kai,tunda ta daura ido kan Barraq ranan da akai hira dashi a AIT taji tana
mutuwar son baturen,yaro jinin turawa,jinin yan Nigeria,ga kudi,ga aji,ga kyau.
Cikin ikon Allah tagano Ashe dandan abokin baban tane,tama baban ta magana,yay ma
Dadin Barraq magana,da murnan Dad yakira Barraq yamai magana Barraq yace shi
bayason ta,inlokaci yayi zai nemi matarshi da kanshi hakanan da sanyin guiwa Daddy
yabama Alh hakuri. Tundaga lokacin Nana tahana Barraq sukuni har tsiraicinta tana
nuna mishi kawai dan ya sadu da ita, amma hakan yaki faruwa Barraq yakibi takanta
duk inda yaganta Koran kare yake mata danya lura inya biye mata wataran zai fadama
halaka haryay abinda takeso wanan kenan.

Maman Abd Shakur😘


[5/12, 8:25 AM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

33
Kwanan Rufaida 7 a Russia taji sauki sosai likita yazo yabude ciwon ya warke tass
har tabon sun bace tasha kuka saboda zafi,Mum na bata kulawa naban mamaki,wani irin
shakuwan d’a da mahaifi ya shiga tsakaninta da Mum,Mum naji da ita,tana kokarin
chaba mata yar hausan data iya idan taga taimata magana da turenci bata ganeba.
Rufaida najin dadin zama da Mum saboda ta lura Mum nada hankali ga yawan kyauta.
tundaga ranan Rufaida bata Kara ganin Barraq ba,hakan yasa hankalin ta ya kwanta
batada matsala Mum tariga tabata labarin yanda akayi tadawo Russia,aranan ne ta
lumshe ido a zuciyarta takira Mai gilashi da Hakika yakasan ce SHINE SIRRIN TA dan
yataima keta daga hannun Duduwa yakawota wurin mamarshi mai kirki mai sonta, Mai
gilashi-KAINE SIRRI NA!.

zaune suke ita da Mum a falo,sanye take da Jan doguwan riga a jikinta Gashinta ba
dankwali Mum na duba gashin tace”daughter anjima zansa akaiki wurin gyaran gashi
cus hair dinki is too dirty” Rufaida tai murmushi tace”to Mummy nagode “suka cigaba
da kallon TV dake falon, jin anbude kofa tareda yar karaman sallama ciki ciki yasa
Mum batare data juyoba tace” Son yanzu is 11 Am,tun safe kafita jogging maisa
kadade?” Karasowa falon yayi ya zauna akan kujeran dake kallon na Mum yadan saci
kallon Rufaida wacce tunda taji Mum tace son tarufe ido,dauke kai yayi kafin ya
cire headphone din dake kanshi yanadan tabe fuska,Mum tace”bakada lafiya ne akira
Dr?” Girgiza kai yayi kafin ya mike tsaye yadau headphone yarike a hannu yana
jujjuyawa yadan kalli Mum murya Chan kasa yace”Mummy am hungry, abama wanan
breakfast dina takawo min part dina,am going to shower ” yafice daga dakin yana
tafiya ahankali tareda rera yar waka.
Mum ta kalli Rufaida tace”Rufaida” ahankali tabude ido ta dago kanta ta kalli Mum
tace” naam Mummy ” Mum ta sakan mata murmushi dan har cikin ranta tanajin dadi duk
lokacin da Rufaida xata amsata da naam Mummy. Mum tace”kije wajen lidiya(mai musu
girki) tana kitchen kice tabaki abincin son ki kaimai dakinshi kinji” Rufaida ta
girgiza kai tareda mikewa kaman kwai yafashe mata aciki ta karbo abincin tayi
hanyar waje waige-waige take dan batasan dakin ba,hango wani mai kula da fulawowin
yasa takarasa wajen ta tambaya ya nuna mata wani hadadden bangaren gidan tayi
wajen, tsayawa tayi abakin kofa takasa shiga,takasa kwankwasa wa,takasa magana ta
shiru hanun data rike abincin yana rawa.

Mai kula da fulawowin ne yazo watering shukokin wurin ya ganta a tsaye yace”ha’a my
lady ai nanne part din my boss,bude kofa ki kaimai abincin kafin ya huce,my boss ya
tsani abincin daya huce” yana gama fadin haka yacigaba da aikin daya kawoshi,da
kyar tasamu karfin bude kofan ta shiga ta mayar tarufe tana numfashi da sauri.
Lumshe ido tayi ta budesu ahankali, kwayoyin idanunta suka sauka akan fuskar mai
gilashi dake zaune akan doguwar kujera yana kallonta,da sauri ta juyar da kanta
tana kallon wani bangare hawaye na shirin zubo mata.

“Am very much hungry” taji anfada hakan yasa ta juyo da kanta taga ita yake kallo
da sauri ta juyar da kai, ta daga kafarta da kyar ta iso gabanshi ta ajiye tray din
abincin akan center table din gabanshi kanta na kasa tai shiru, “zubamin Rufaida”
taji yakara fada hakan yasa ta mika hannu tadau plate ta bude kullan abincin,
hanunta na rawa sosai tadau cokali tafara diban shinkafan duk hanunta na rawa tana
zubar da Rabi a table Rabi a plate, bin hanunta da kallo kawai yake zara zaran
yatsayen ta na burgeshi gadan karamin Jan abu a duka kunbunan ta dasuka
burgeshi(Jan lalle). ganin yanda hanunta da jikinta ke rawa tana zubar da abinci
yasa ya mika hanunshi ya rike hanunta dake dauke da cokalin abincin, wani irin
rikon hannu yamata, yatsun shi biyu na tsakiya na cikin tafin hanunta ukun yatsayen
sun zagaye tsintsiyar hanunta. Idanunshi suna kallon fuskarta dake kallon farin
hanunshi daya rike nata,kallon dan zufan dayabi goshinta Wanda hakan yasa dan
gashin gaban kan ya kwanta yay lub. jin yaki sakin hanunta yasa tadago kanta
ahankali ta kwalalo idonta dake gab da zubar da hawaye ta kalleshi, ita taga yake
kallo,Kara kwalalo idon tayi a tsorace hawaye ne ya gangaro daga idonta ya sauka
akan kuncinta.

Maman Abd Shakur😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 34 to 37KAINE SIRRI NA 49 →
KAINE SIRRI NA 35 to 48
Posted on May 24, 2016 by mamanshakur
[5/24, 07:58] Fauzee Preety: [5/13, 3:54 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

34
Ahankali ya zame hannunshi daga nata dayaga yana rawa yace “barshi zan zuba da
kaina” da sauri ta mike tsaye zata fita daga dakin yace “amm nace ba” tadan juyo ta
kalli center Capet din dake kasar dakin jikinta na rawa. yace”idan aka wanke miki
gashin amiki kitso kinji” dagamai kai tayi, tafita daga dakin da sauri hartana
tuntube. girgiza kai kawai yayi yanzu shine keson wanan yarinyar,lallai soyayya
bakama Barraq adalci ba.

Tana komawa part dinsu tawuce dakinta ta kwanta akan gado tanamaida numfashin
tsoro. kai mutumin nan yacika bata tsoro, to maisa lokacin dabaida glass banji
tsoron shiba?take ma kanta tambaya a zuci.

Da yamma Mum tasa aka kaita wurin wanke gashi, wanke mata gashin sosai akayi aka
mata kitso irin na turawa nan kaman kalaba tai kyau sosai banbancin ta da turawa
fari kawai zasu nuna mata dan itabaka ce.

Zaune take a dakin Mum tagama yima Mum gyaran daki duk tai zufa Mum ta shigo
tace”daughter kije kima son sallama,yau zai koma Nigeria ” da sauri Rufaida ta
kalli Mum saikuma ta maida kanta kasa, Mum ta dauko wani magazine dake kan drower
ta zauna kan gadon tana Karantawa. Ahankali ta mike tabar dakin. dakinta taje
tasako karamin bakin hijab dinta akan riga da slet din kantin dake jikinta ja,tayi
part dinshi, bude kofan tayi ta shiga jikinta na rawa ta tsugunna a kasa ta chusa
kanta cikin cinya batare data kalli wani abu na falon ba.

“Zan koma Nigeria yau,kina bukatan wani abu?” Sassanyar muryarshi ya bugi kunnenta,
Kanta akasa ta girgiza, yace”are u sure?”ta sake dagamai kai batare data kalleshi
ba. Ahankali yace “Rufaida” tadago kanta taga sun hada ido da sauri ta kauda kai
dudda yamata kyau sosai yau,yana sanye da suit mai ruwan toka,da neck tie mai gida
gida,gashin kanshi yakara yawa gashi ya kwanta. maganarshi ta tsinkaya yana
fadin”yau lesson teacher zai fara zuwa yana miki lesson just to keep u busy,and dan
kituna abunda kika sani abaya, meanwhile innakai Nigeria zan nema miki certificate
da testimonial na primary school, sai na JSSE,zan saki a school a garinnan, inaso
kifara daga Ss1,dazaran nadawo zaki fara school kinjiko Rufaida” ta dagamai kai,
yadan kalleta kafin ya dauko wayarshi daga kan table yana daddannawa yace”lastly
banasonki da wasa,banason na ganki da any friends, be very very serious da karatun
ki,dan banason Wanda bayason karatu,ki zama mai kokari da kwazo banda yawan
wasa,and ki kasance mace mai kamun kai, da sitirce kanki,karkice dan kinga yanda
yan garin ke shiga da aladarsu kice zaki dauka banaso,banason yawan surutu, take
good care of ur self Rufaida, kafin na dawo naga kin iya duk abunda lesson teacher
ki ya koyamiki,and I also want u to be social, kidinga zama tareda Mummy kina koyan
abubuwan datake yi kinji da yanda take interacting da mutane?” Ta girgiza mai kai
hawaye na zuba daga idonta, ya mike tsaye yana kallonta kafin yace “zan tafi”.

Ahankali itama ta mike tana share hawayen datake yi amma sun kasa daina zubowa,
yadau yar karaman jakarshi yay hanyar fita, ya daura hanunshi kan door handle yaji
kukanta yakara karuwa sama danada,juyowa yayi yana kallonta da sauri ta juyamai
baya tana kuka, “kidena kuka Rufaida in sha Allah bazan dadeba,nasan Ni kadai kika
sani, but karki damu Mummy zata kula dake more than yanda zan kula dake, karki
manta abubuwan Dana fada miki,ga dakina nabar miki akwai wasu abu Dana ajiye miki a
bedroom kije ki dauka,saina dawo Bye”. yajuya yafita daga dakin Rufaida takara
fashewa da kuka, ahankali ta furta ” KAINE SIRRI NA Mai Gilashi, Allah ya kaika
lpy”.

Maman Abd Shakur😘


[5/13, 4:02 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

35
Saida tagama cin kukan ta sanan ta shiga dakin tadake tsammani shine bedroom
din,hadadden dakine an mai fenti Golden Brown, babu wani tarkace banda wardrobe na
bango sai kuma katon table da computer kekai, gefeshi kuma wani farin karamin
fishbowl ne da kifaye yan kanana aciki. Hango Babban akwati akan gado yasa
takarasa wajen,ta bude akwatin. kayane na sawa kala kala, sai Novel na turenci
guda uku, dawani littafi mai suna ” Educative Lady Behavior” ahankali ta mayar da
komi ta kulle akwatin tana kallon dakin kafin taja akawatin tabar dakin, taje ta
nunama Mum kayan.
Mum ta dinga murna tana shima Barraq Albarka.

Aranan karfe biyu lesson teacher yazo sai biyar yatafi. Hankalin Rufaida yatashi
dan bata gane komiba Maths da Biology yamata ita turencin shima ne bata ganewa,
tadau littafin ta dinga Karantawa, ganin taki ganewa yasa tai salla biyu na nafila
taroki ubangiji yasa ta dinga ganewa. Cikin ikon Allah washegari dayazo yay mata
English tadan gane ba laifi ahaka ahaka ajin yacigaba da tafiya harna tsawon wata
biyu Wanda a yanzu Rufaida na gane komi daidai gwargwado, akwaita da kwazon ganin
ta iya abu. Tana yawan zama da lidiya a kitchen tana koyan girkin da akeyi, gata da
gyara jikinta koda yaushe tsaf tsaf take saisa Mum ke alfahari da ita. Tanajin
dadin zama da Rufaida har cikin ranta, dan akwaita da girmama na gaba da ita gata
da son aiki, kiri-kiri tahana masu gyarama Mum daki gyarawa,ita keyi da kanta, idan
washing machine ya wanke kayan Mum ita kezuwa ta shanya idan sun bushe ta kwaso ta
gogesu,Mum tai magana tadenayi akwai masuyi har tagaji ta kyale Rufaida dan taki
denawa. aganin Rufaida tahakanne kadai zata saka musu abunda suka mata,sun haskaka
rayuwarta sun mayar da ita mutum bayan rasuwar su Umma, sun tsamota daga wahalar
Duduwa, sun kuma sota,sun nuna mata kauna tomeza tamusu daya wuce kyautatawa da
musu biyayya??..

Rufaida kenan akwaita da tunanin manya wani zubin.

Maman Abd Shakur😘


[5/13, 4:24 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

36
Zaune yake a office shida Muzammil. “Muzzamil wlh nakosa nagama abubuwan gabana
natafi Russia, dan nasa Rufaida a school, gashi Dad kullum damuna yake da
aure,saisa dukna kosa nabar Nigeria gaba day…a” Wayarshi yay ringing kallon wayan
yayi yaga baisan number ba, ya share ganin ansake kira yasa Muzzamil ya kalleshi
“pick d call mana,it might be important” yadau wayan ya kara a kunne tareda amsa
sallaman dayaji an mishi a natse, Alhaji yace”dafatan ka ganeni Barrister ,Wanda
yataba kawoma complain kan yarshi tabata,da sauri Barr ya rike kanshi kwata-kwata
yamanta da alkawarin dayama mutanen nan zai nemo musu yarinyar su, baimasan inda
paper dasuka rubutamai yanda yarsu take yakeba. Da kyar Barr yace” Alhaji am very
sorry wlh aiyuka sunmin yawa,but gobe munada wani meeting na Barristoci a Lagos
zanbi nyt flight cus meeting is around 8 nasafe,so idan mun gama by 1 zanzo
wajenka mu tattauna da kyau kan yarka, ban address din wurinku ” nan Alhaji yabashi
address dinshi sukai sallama.

Muzammil ya kalleshi yace “maisa zakaje gidanshi?” Barr yace “yakamata naje,dannai
bincike,kuma kasan dole daga gidansu bincike zaifara,anan ne zan iya gathering all
d necessary clues”. Muzammil yace” hakane fa” suka cigaba da fira.

Zaune take a garden ita kadai tasa jumpsuit ja,yay mata kyau gashinta dayasha gyara
a sake sun zubo har bayanta,littatafan assignment na gabanta. da alumu tai zurfi
cikin tunani dan hankalin ta baya kan book din. Jitayi an dafata, afirgice tajuyo
ganin Mum ne yasa tai murmushi tace”Mummy”Mum ta zauna a gefenta tarike hanunta
cike da damuwa tace” daughter dis days kina yawan tunani meke damunki tell me d
truth ” Rufaida tai shiru kaman bazatayi magana ba, saida ta sauke ajiyan zuciya
sanan kwalla yacika idonta tace”Mummy nima bansani ba,tun shekaran jiya nai
mafarkin wata mata fara kakkyawa nada cikin 9 month,naga tana rashin lpy
sosai,hawan jini yakamata,she is really suffering kuma tanata kiran sunana waini
take nema,nine sanadin ciwon ta”, takarasa maganan tana kuka sosai. Mum ta rungume
ta tana bubbuga bayanta tace “is ok, kidena tsoro is just mafarki,be prayerful
kinji” ta dago kanta daga jikin Mum tana murmushi tana share hawayen.
Juyawa tayi tadau littafin gabanta ta bude ta mikama Mum tace” take a look at this
Mummy ” Mum ta karba, ihun murna tasaki tareda mikewa tsaye tace “who Drew dis
daughter?” Cike da Murna tace”is me,Nina zanaki Mum dazu” Mum ta kalli drawing din
sosai,taga exactly fuskarta ne, ta kalli Rufaida tace”dama kin iya Zane haka? ”
Rufaida tadanyi tsallen murna tace “Mum nima kawai naga hannuna nata zanaki,ni
bansan yanayi ba”, Mum ta kalli drawing din taga dan karamin signature na zanen
baby(jariri) tace” Rufaida wanan signature fa?”Maisa kikai signature na Zane?” Tayi
dan dariya tace”Mummy wlh bansani ba,nadaiji da ina zanen kaman ina son baby,kawai
sainaga na zana small baby as my signature ” Mum ta tafa mata very good daughter,
zan siyo miki abubuwan drawing saiki dinga yi,kin fito da sabon samfarin signature.
Rufaida tai ihu ta rungume Mum.

Maman Abd Shakur😘


[5/13, 4:38 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌
37
Karfe 2 na rana taima Barr Barraq a kofar gidan Alhaji Muhammad. Da kanshi Alhaji
yamai iso zuwa Babban falonshi inda aka wadata gaban Barr da kayan ciye-ciye da
shaye-shaye.
Bayan wani dan lokacin gaisuwa da labarta bayan rabuwa, Barr Barraq ya kalli Alh da
matarshi dayagani da katon ciki haihuwa yau ko gobe yace” nazo nan gidanne cus
inaso nahada all d necessary abubuwan daya kamata nasani kan yarku”. Yabude jakan
laptop din jikinshi ya zaro wata zungureriyar takarda ya kalli Hj,yace”I will start
with u Ma, cus kece uwa,u know ur daughter morthan anybody so inaso kibani labarin
yarki takowani bangare”.

Hj ta sauke ajiyan zuciya kafin tafara magana””nidai sunana Maryam Muhammad yar
fulanin yolace,mun dade dayin aure bayan kusan shekara 12 dayin auren mu Allah ya
azurtamu da yarmu tafarko mai suna “Rufaida” sunar kakarta taci saisa Dani da
babanta muke kiranta da “MEEMA”. Barr ya kalli yanayinta yadanyi rubutu kadan kafin
ya dago kanshi yace ” cigaba ma” tace” Rufaida ko kuma ince Meema yarinya ce shiru
shiru,ko kadan Meema batada fada,batada karfi kona digi,tun tana karama bata iya
shiga cikin sa’ointa suyi wasa,cus dukanta ake, har wanda Meema ta girma ma saiya
daki Meema kaga tana kuka batare data iya ramawa ba,wanan dibi’an Meema na rashin
karfin fada na damuna gata da yawan kuka,abu kadan kesata kuka,gata da yawan tsoro.
Haka nacigaba da kula da ita muna nuna mata so da kulawa,nida babanta mune
kawayenta,dan bata iya shiga cikin yara, dazaran tadawo daga makaranta tana tareda
mu adaki,ahaka Meema takai shekara 14 batareda Kawa ko dayaba, hartafara abun namu
namata Wanda yazo mata da gardama tanada ciwon Mara sosai, dan akwai lokacin da
muka kaita asibiti akace mumata aure, babanta bai dau maganar komiba dan aganinshi
yarinya yar 14 zaima aure? Aibata isaba, haka muka dawo gida muna kulawa da ita.
Har babanta yakara aure “Salameme” wacce itace mutum ta farko danasan batasan Meema
kullum saita daki Meema,saidai inbata gantaba,ban taba mata magana akan tadena
dukan Meema ba dannima banason hayaniya.

Bana mantawa da watarana Meema na 15 ta shigo dakina tana kuka nace mata menene
tacemin Anty(salameme) tace mata wai watarana saitasa ta manta da mamarta da
babanta ya zamto batasan kowaba,ta manta mu a duniya, maganar ta dami Rufaida
tanata cemin yanzu Amma wai zan iya mantaki a duniya keda Abba?. Nace mata karki
damu bazaki taba mantamuba Salameme wasa take miki,da kyar na lallabata tai shiru
nabar dakinta nakoma dakina ina tunanin maisa zata fadama Meema irin maganar nan,
ina zaune a wurin naga Meema ta shigo dakina da murnar ta tana rike dawasu
cardboard paper farare guda biyu ta shinfidasu agabana naga sak zanena Dana Baban
ta ne, na tambayeta me dalilinta na zanamu tace toba Anty tace zan mantaku ba,kinga
tunda nazanaku ai bazan taba mantaku ba,kallon zanen nayi ina dariya sainaga tayi
signature da zanen baby Dana tambayeta dalili saitace min… Kuka yaci karfinta, Alh
ya shafa bayanta yana fadin ya isa kuka baida kyau agareki yanzu. Da kyar tai shiru
tace”Dana tambayeta dalili saitace min”Amma inaso ki haifamin kanwa ko kani,halan
idan ina amfani da signature na baby ki haifamin baby ” dariya kawai nayi ina
mamakin yarintar Meema, tundaga lokacin babanta ya bude mata wani Babban daki a
gidanan inda take Zane zanen ta. Barr Barraq yace “zan iya ganin dakin?” Suka
kaishi har dakin Zane kala kala duk Wanda tayi saitadan zana karamin baby
akasa,bayan yagama rubuce Rubuce suka dawo falo. Barr ya kalli Alh yace”sir banda
ciwon Mara batada wani ciwo? Maybe Aljanu haka or something else kaga sai muyi
tunanin ko sune suka dauketa??” Alh ya girgiza kai,gaskiya Rufaida batada wani ciwo
sai na Mara,Wanda nasan duk inda take yanzu tana wahala da ciwon. Barr yasake wurgo
wani tambayar “dayar matar kafa” Alh yace “tunda naga tadami uwar gidan na chanza
mata gida,naraba su”.

Barr Barraq yay rubuce-rubuce ya maida paper cikin jaka kafin ya dago kai ya
kallesu yace”Alh, Umma banason nabaku much hope,even though bansan adininmu sosai
ba,but d little I know daga abokina Muzammil shine duk Wanda ya dogara ga Allah,to
Allah ya isar masa,watakila wanan itace jaraba warku,Ni ban isa na nemo muku
Rufaida ba,saida yardar Allah,haka wayau na ko wayanku bazaisa a gantaba” ya kalli
Amma yace”Umma have faith, trust in Allah,ki yarda shikadai zai iya bayyana miki
yarinyar ki, ki kwantar da hankalin ki ki sauka lpy,in sha Allah za’aga yarku. I
will try my best na nemota,da gobe zanyi tafiya but nadaga tafiyan sai next month”.

Ya mike tsaye tareda daukar jakanshi yace”nabarku lpy” Alh da Umma sukamai godiya
da shatara na arziki duk bai karbaba haka yatafi suna mai yabon kyawawan dabi’un
Barr Barraq.

Maman Abd Shakur😘


[5/24, 13:44] Fauzee Preety: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

38
Zaune yake adakinshi yadan kishingida da gado yana zukar tabarshi, kayan bacci ne a
jikinshi dan bai dade da shigowa ba yay wanka yay salla. Jin knocking din da’ake yi
a sitting room yasa ya mike tsaye ya bude kofar dazata sadashi da sitting room,
Wurgar da karan taban hanunshi yay akan tiles yasa kafa yatake kafin yakara sa
wurin kofar ya bude Daddy ya shigo dakin sanye da farar jallabiya ya zauna akan
kujerar zaman mutum daya yahade rai, ahankali Barr ya maida kofan yarufe yakaraso
tsakiyar dakin ya zauna akan kujera kanshi akasa yace “Good evening Daddy “,Dad bai
amsashi ba cikeda bacin rai ya kalli Barr da kanshi akasa yace” Mummy ka tafada ma
sakona” Barr ya girgiza kai tareda furta”eh Daddy tafada min,but Dad banda wacce
zan aura” Dad ya dakamai tsawa just shout up!, I said shout up Barraq, duk matayen
dake duniyar nan ace ka kasa picking one ka aura,kullum tsufa kake karayi 35years
is not a joke. Barr ya dafe kanshi dan mugun darawa yake bayason yaga yanada Dad
fushi but amma me zaiyi baida wacce zai Aura maganar Dad yadawo dashi daga tunanin
dayake “ina shekara 75 ku biyu kacal Allah yabani a duniya dakai da Auta,don’t you
feel ashame of ur self Barraq, All ur friends sunyi aure banda kai” zama yayi yana
sauke ajiyan zuciya kafin yace” Barraq ina bukatan jikoki dazanyi wasa dasu,yace
just take a look at dis big house kullum empty babu yara masu wasa,I want my house
to be full with children, Barraq banason nai forcing dinka ka aure Nana saboda
banason nama yarona abunda bayaso but listen” ya daddaki hannun kujera tareda nuna
Barraq da yatsa “wlh,billahil azim Barraq nabaka two weeks ka kawomin matar dazaka
aura inba hakaba u will see my… Da sauri Barraq ya sakko daga kan kujera yarike
kafan Dad hawaye ya cika idonshi ya kifa kanshi akan kafar hawayen shi na zuba akan
kafar Dad hakan ya mugun karyama Dad zuciya yadau hanunshi ya chusa a cikin gashin
kanshi murya Chan kasa yace” Son ko bakada lpy ne? Tell me d truth “Barr ya girgiza
kai,Dad yasa hannu ya dago kanshi ya rike kuncinshi kafin yasa hannu ya share
hawayen daya zubo daga idonshi ahankali yace to meke damunka Barraq maiya hanaka
aure?”

Ahankali Barraq muryan shi na rawa yace “Dad inada wanda nakeso,but yarinya ce
karama,iyayenta sun rasu,tanada grandma data tsaneta sosai,and the law has given me
her custody…” Nan yaba Dad labarin Rufaida gabaki daya batare daya boyema Dad ko
abu dayaba,daidai da yanda ta taimake shi a kauye saida yafadan ma Dad.

Saida yagama fadanma Dad komi sanan Dad yace”maisa zaka boyemin all dis things
Barraq,kama ubanka adalci kuwa harka tsinci yarinya gwamnati tabaka kudinta,shari’a
tabaka yarinyar ta dawo karkashin ka saika boyemin duka ka kyauta?” Barraq ya
girgiza kai yay kneeling agaban Dad yana girgiza kai araunane I was wrong Daddy dan
Allah kayafemin,wlh Dad nai hakane saboda tsoron na tunkareka da zance,I thought
bazaka saurare nibane” Dad ya girgiza kai “bazan taba ganin zakai taimako nahana
kaba Barraq” ya girgiza kai ahankali yace zauna, Barraq ya zauna Dad ya daura
hanunshi akanshi yana murmushi yace “am proud of you son,ina alfahari dakai,ina
godiya da Allah daya bani kai a matsayin da,duk wanda Allah ya azurtashi da d’a mai
jinkan wasu,mai tausayi da taimakon marasa karfi to hakika Allah yamai Babban
kyauta,Allah maka albarka”ahankali Barraq yace” Ameen Daddy” Dad yace ” dudda law
ne yabaka Rufaida dagayau duk wani abu nata na dauka yadawo kaina, daga yanzu nine
mahaifin Rufaida, zan zame mata mahaifin data rasa,haka zan hadata aure da Dana
danasan dan arziki ne,dan bazan bama yata abunda zai cutar da itaba. Barraq baisan
lokacin da murmushi ya subuce maiba.

Dad yakara kallonshi yace”gobe zan kira Mum dinka ta tahomin da Rufaida, sudawo
Nigeria zan aurar da Rufaida gareka, kaje ka fara shirye shiryen Aure in 2weeks,
ina certificates din daka samo mata?” Barraq yatashi ya shiga bedroom dinshi ya
kawoma Dad ya karba ya dudduba sanan ya sauke ajiyan zuciya yace “zan nema mata
makaranta,amma tana dakinka zata fara karatu,Allah sanya maka albarka, Dad ya fita
daga dakin dauke da certificates din a hanunshi. Wani irin ihun murna Barraq yay
yafara neman wayanshi yana Muzammil must here dis good news, wani tsalle yayi
yafada gado zan zama ango in 2weeks.

Maman Abd Shakur😘


[5/24, 13:45] Fauzee Preety: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

39
Zaune suke a cikin jirgi,Rufaida ta kankame Mum jikinta na rawa Mum nata mata
dariya tana kai daughter na kincika tsoro,a shagwaban ce ta dago fuskarta daya cika
da hawaye ta sharbe hawayen tace”Mummy ai jirgin yanasa naji hanjin cikina kaman
zasu fitone” Mum takara tunsurewa da dariya tace”Relax daughter, ai ganinan tareda
ke,bazan taba bari wani abu ya sameki ba” lumshe ido Rufaida tayi ta daura kanta
akan kafadar Mum tace “thank yhu Mummy, u mean everything to me Mother” Mum tasa
hannu ta shafa kumatun ta “don’t thank me kinfi haka a wurina,I will give yhu
everything idan inadashi” hawaye ya zubo daga idonta “I soo much luv yhu Mummy,
keda Ummana nafiso a duk duniya” Mum ta lumshe ido tana murmushi “keda Barraq kune
komina na duniya,banason wani abu dazai tabamin ku,inason ku sama da komi a duniyar
nan” Rufaida ta kankame Mum tana dariya ahankali.
Kama hanunta Mum tayi tana kallon yatsun hakan yasa Rufaida ta natsu tana kallon
Mum, Mum ta sauke ajiyan zuciya tareda maida hanun Rufaida kan cinyarta tace “Tun
ranan farko da Son ya kawoki wurina nagane akwai soyayyar ki atattare dashi da
sauri Rufaida ta dago kanta daga jikin Mum ta kalleta,murmushi Mum ta sakar mata
tareda jawo kanta ta maida jikinta tana shafawa” kubiyu nafiso a duniya,saisa naso
Ku biyu Ku auri juna saboda nasamu jikoki daga abu biyu danafi so aduniya wanda
hakan zaisa nai farin cikin daban tabayi ba aduniya” tadan dukar da kanta dan taga
yanayin Rufaida sai taga idonta a lumshe tai lamo da kanta a jikinta, murmushi Mum
tayi”Daughter zaki iya cikamin wanan burin nawa?zaki iya taimakamin ki auri Dana
mai sonki?” Rufaida tai shiru jikinta yafara rawa, jin shiru nakusan yan mintuna
yasa Mum tace”idan kincemin a’a daughter I will understand and consider, bazan
tabajin haushin kiba,and bazan taba tursasa kiba,niba Mum dinki…” Da sauri Rufaida
ta dago da kanta takara hanunta abakin Mum tana girgiza mata kai”u are,and u will
always be my Mummy, kinmin komi,kinban kaya, happiness,abinci,ilimi yaza’yi nakasa
cikina uwata burinta Kwara daya,ur only wish Mummy? Dabanzama yatagari ba,na yarda
zan aureshi,zan kula dash…” Mum tasa hannu ta share mata hawayen idon “banason ki
tursasa kanki,banason kiga natakura miki,kaman ina saki dole” Rufaida ta girgiza
kai “Mum kin isa ki tursasa min,kin isa kitakura min,kin isa kisani dole saboda ke
uwata ce,karki Kara tunanin kin tursasa ni Mommy wlh bakiyi ba,kuma baki tababa” Da
sauri Mum ta rungume ta ta sumbaci goshinta daidai lokacin da jirginsu yay landing
a Abuja Airport.

Sakkowa sukayi hanunta na cikin na Mum,sai kalle kalle take,ahaka harsuka fito daga
arrival inda suka tarar da Amma a tsaye sai duba agogon hanunta take,Mum ta karaso
wurin kafin Amma taji an rungumeta bazata ba tsammani dariya sukayi kafin Mum ta
saketa Amma ta karbi handbag din hanun Mum tace “Mum Barraq ya hanya” da harshen
turenci,Mum tai murmushi tace “lpy ina auta na maisa baku taho tareba?” Amma tai
murmushi “kema kin Santa tanachan tana kwainane wai itama zatama amaryan Uncle B
girki,Mum tai dariya dasauri Amma tace” ina maganan Amaryan ina take na ganta? Da
sauri Mum ta juyo tana daughter ahankali Rufaida tafito daga bayan Mum kanta akasa
tana wasa da yatsar ta muryanta na rawa tace ina wuni, Amma takamo hannayen ta biyu
tadan tsunguli kumatun ta ahankali tace”bazan amsa gaisuwar kiba,shine kika boye
abayan Mummy saboda bakiso na ganki ko?” Rufaida ta girgiza kai yakuri, da sauri
Amma ta kama baki dena bani hakuri amaryan Dana muje gida kici abinci ki huta gwara
baniso ki wahala dan daki wahala gwara tsohuwar nan ta wahala ta nuna Mum tana
dariya,Mum ma tai dariya kafin su shiga mota driver yajasu zuwa gida.

Maman Abd Shakur😘


[5/24, 13:45] Fauzee Preety: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

40
Fitowa sukayi daga cikin motar Amma ta rike hannu Rufaida datake shirin kuka tana
kallon Mum, Mum ta girgiza mata kai alamun kartayi da kyar ta iya hadiye hawayen
suka cigaba da tafiya auta ce tafara artowa aguje ta rungume Mum tana ihu”big Mummy
oyoyo” bama tajira amsan Mum ba tasake ta ta rungume Rufaida da saida takusa faduwa
Amma ta sakin mata rankwashi zaki fadar da itane Mara natsuwa,Auta ta bare baki Mum
tarike ta tana lallashin ta tace muje ciki nakawo miki tsaraba Auta tace to amma
bari naje nafadan ma Anty Hafsat (amaryar Muzammil) matar Uncle B tazo dan tana
kitchen kafin Mum ta amsa tayi ciki da gudu. Kan Rufaida akasa harsuka shiga mai
falo suka zazzauna ana hira Auta da wata kakkyawar mace doguwa tana sanye da brown
dinkin doguwan rigar shadda taji aiki hanunta dauke da tray na drinks tana murmushi
tajawo center table ta daura drinks din tana gaishe da Mum,Mum ta amsata sosai da
faraa dan tasan Muzammil. Amma tace sannu da aiki Hafsat tun safe kinki hutawa
kinata aiki,da sauri tace laaa Amma bakomi Uncle B yace nakula da Mum da amaryar
shi da kyau kafin yadawo ta dawo kusa da Rufaida ta zauna tana kallonta Rufaida ta
dukar da kai taki bari suhada ido,Mum tai dariya tace daughter na tacika kunya
dauketa Hafsat Ku shiga ciki tayi wanka tagaji. Hafsat ta rike hanunta tana
murmushi tace to muje,Rufaida ta mike ahankali ta daga kanta karaf suka hada ido da
Hafsat da sauri Rufaida ta dukar da kai,dariya Hafsat tayi tace aita boyemin fuskar
Nanda sati biyu dole muga fuskar da kyau,suka fara tafiya wani bangare daban da
Amma ta nuna mata takaita,ta ajiyeta a hadadden bedroom kafin tace to bari na dauko
miki kayanki ko Kai akasa tace to” Hafsat tai murmushi takoma shashin Amma wayarta
ta dauko ajaka ta kira number Mijinta ringing daya Muzammil ya dauko yace baby na
ya? ” da sauri Honey sun iso, Muzammil yace da gaske baby na sun iso?” Barraq dake
gefenshi yana duba wasu takardu Zane ya ajiye da sauri ya matso kusa da Muzammil
yana kallonshi “su Mum ne suka iso?” Muzammil ya ballamai harara tareda juyamai
baya yace “baby na kinaji ki kula da ita,jeki zauna da ita kartai kewa…” Fisge
wayar yaji anyi daga kunenshi Barraq jikinshi har wani bari yake yace”madam kikace
sun iso?”dariya Hafsat tayi tace eh Uncle B, da sauri yace tana ina?” Tana
daki,Barr yace babu wani abu dake damunta ko?,taci abinci?,tai wanka? Tagaji sosai
ko halan,Abba ya ganta?” Hafsat ta rike kai o Uncle B ko kunyana bakaji wanan
tambayoyi haka,yadan Sosa keya yana murmushi, nabarta zata shiga wanka saita fito
ne zataci abinci ” Barr yace “ok,plz nabaki amanarta kinji madam,da zaran mun gama
binciken damuka zoyi zamu biyo flight mudawo” Hafsat tai dariya sosai tace naji
bama honey tabe baki yayi ya mikama Muzzamil dake kallonshi Hafsat tace Honey Allah
dawo daku daga Lagos din lafiya.yace Amin takatse wayan takoma sitting room tadau
jakar da Mum ta nuna mata na Rufaida ta wuce shashin da Rufaida take.
Samunta tayi a zaune daure da towel
[5/24, 13:45] Fauzee Preety: *KAINE SIRRI NA*

42
Kuka tafara sosai harda shesheka tana mammatse kafa kaman tanajin fitsari. yadade
yana kallonta kafin ya zaro Biro daga aljihun gaban rigarshi ya ijeye mata akan
table ya kalleta yace”ki tayani solving. Naje makarantu da wuraren Zane a Lagos
yau, anyway kiduba zakiga komi saikimin lissafi” hannu tasa ta share hawayen idon
nata tadau biron ta bude littafin tafara Mai lissafin,yayinda shikuma yadau remote
ya kunna TV yana kallon channel news ganin taki sakewa.

Wuraren 10:30 tagama ta dago kai ta kalleshi amma takasa mai magana,haka tai shiru
ga bacci na kamata. kwantar da kanta tayi a kan center table din ahaka har bacci
yay gabada ita.
Karfe shadaya yagama kallon news din,ya kashe kafin yazo inda take ya tsugunna yana
kallon fuskarta,ahankali yakai bakinshi goshinta ya sumbaceta kadan sanan yadago
yana murmushi”I luv yhu Rufaida with all of my heart” ya sumbaci hanunta “ina sonki
sosai matata sama da yanda kike zato”bakinshi yakara sakin wani tattausan
murmushi,fararen hakoranshi suka bayyana. Rike kanshi yay”duk lokacin Dana ganki
konake taredake jinake kaman zuciyata zata fashe saboda irin son danake miki
Rufaida” jin ana kokarin bude kofa yasa yasaki hanunta yadau memo da Biro ya Mike
tsaye da sauri Mum ta kullo kofan tana karemai kallo”what are yhu doing here?bakaga
tai bacci ba?” Yadan Sosa keya “news NA kalla” yabata amsa atakaice yabita gefenta
yafita daga dakin. Mum tai murmushi takada kai tana mamakin dannata,kamar mafarki
yaron da bayason auren kananun yara shine yau ya mutum ma Rufaida.

Maman Abd Shakur.


[5/24, 13:45] Fauzee Preety: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

41
Da sallama suka shiga falon Dad ya amsa Hafsat ta gaishe da Dad sosai kafin ta fice
daga dakin,Rufaida ta zauna kusada kafar Mum murya Chan kasa tace”ina wuni Daddy ”
da tattausan muryarshi yace”lpy lau yata,ya lesson din da ake miki hope kina ganewa
kuma kina kokari?” Ta dagama Dad kai, Daddy yace to Alhamdulillah, in sha Allah
bazaki taba nadamar zamanmu iyayenki ba,in sha Allah bazaki taba Dana sanin
saninmuba,Allah zai albarkaci rayuwar ki kinji yata?” Ahankali tace”Ameen nagode
Daddy”.

Yace Rufaida inaso nahada ki aure da dana dan yazomin da maganar yana sonki,a
tsarina da tsarin dayake raina tun kafin nama haifi ya mace shine duk Randa Allah
yabani mace zan aurar da ita tana shekara16-17 saboda aure shine gatan dazakama
yarka mace. Tunda yanzu Allah ya banike Rufaida zanso na aurar dake yanzu inyaso
bayan anyi aure kya cigaba da karatun ki but dudda wanan dogon burin nawa bazan iya
bama Barraq keba saida yardar ki da amince warki,kin yarda zaki auri Barraq? Dukar
dakai Rufaida tayi ita batason yanda suke tambayar izininta saikace tafi
karfinsu,wlh banda kowa daya wuce Ku aduniya bantaba sanin bayan rasuwar Abba da
Umma zan sami wayanda zasu soni kaman kuba,kowa kuka bani zan aura,zanmai biyayya
zanmai komi inhar hakan zai baku natsuwa da farin ciki kwatankwacin irin wanan
dakuka bani ayau.
Muryar Dad taji yace”to Alhamdulillah yata,Allah ubangiji yamiki Albarka,sati biyu
za’a dauka kafin a daura muku aure Allah miki albarka kinji tashi kitafi kunya taji
yakamata ta chusa kanta a cikin cinya tana kuka sosai. Mum ta mikar da ita suka
fita daga dakin.

Daki Mum ta kaita takawo mata abinci ta tasata agaba taci daidai cikinta kafin
tabar dakin Hafsat na janta da hira sunayi sama-sama. 9:30 PM suka shigo gidan
agajiye,Muzammil yace”gaskiya gobe ne zan dawo nagaisa da Queen of ur heart dan
right now I need a hot shower, kuma baby nace zatamin” Barraq ya kalleshi batare
dayace mai komiba yafito daga motar Driver yafito yamika ma Muzammil key. Muzammil
yay murmushi kafin ya Sosa gemu yace”jimana” Barraq yajuyo hanunshi na aljihu fuska
a daure “wot?” Muzammil yay dariya kafin yace haba abokina ainace gobe zanzo ko,ko
kafiso naje haka duk munyi datti,yanzu dai dan kiramin baby na tafito mutafi
gida”Barraq ya ballamai harara” I be ur messenger? ” yajuya yayi ciki Muzammil
yafashe da dariya yaciro waya daga aljihu yay dailing number Hafsat ta dauka yace
ina waje kimusu sallama kifito mutafi dare yayi sai gobe zamu dawo mu gaisa,Hafsat
tace to kafin ta katse wayan. Ta kalli Rufaida dake kallon TV tace”zan tafi gobe
zan dawo,hope zaki tattaro hirarraki dazamuyi ko?” Rufaida tasaki mata tattausar
murmushi tareda dukar da kai tana wasa da yatsun ta”eh Anty Hafsat” Hafsat tai
murmushi “kunyar nan taki na burgeni, gashi idan Kinyi murmushi sai dimple dinki su
lotsa,anyway natafi saida safe” Rufaida ta mike tsaye tace”Bye nagode, Allah kaiku
lpy” Hafsat tajuya tafita daga dakin ta rufo kofar,ahankali Rufaida ta zauna kan
kujera tacigaba da kallon walking dead din daya dauke hankalin ta,dudda film din
nabata tsoro amma kuma tanajin dadinshi.
Shiga motar Hafsat tayi ta zauna bayan tafito daga shashin su Amma yimusu
sallama,kallon hanunta tayi ta fade kai” God! Namanta ban bataba. Muzammil yace me
baki bataba?” Wlh wani abu gashinan ajakata nakawoma Rufaida na manta ban
bataba,Muzammil yace yi sauri kije kibata mutafi gida danyau I need yhu badly baby”
dariya tayi taja hancinshi”Allah dan albarka?” Kokarin chafketa yayi tafita daga
motar da gudu tana mishi gwalo, shashin da Rufaida take ta tsaya agaban kofa ta
kwankwasa hankalin Rufaida nakan kallo taji ana buga kofa mikewa tayi tatafi kofa
ta bude ganin Hafsat yasa tai murmushi “Anty Hafsat” Hafsat ta shigo dakin ta kulle
kofa ta mikama Rufaida wata yar karaman koriyar leda tace”ga wanan ki dinga cin
abubuwan ciki kullum sunada amfani kinji” Ganin Rufaida batada shirin amsa yasa ta
saka mata a hannu tajuya tafita da sauri, kullo kofan Rufaida tayi takoma ta zauna
kan kujera tana kokarin bude ledar, idanunta suka sauka kan wani hadadden kwaku
meti shi taciro daga ledar ta ijeye saura abubuwan a gefe tanacin kwakumetin tana
kallon walking dead ta zame dan kwalin kanta gashin kan ya zubo har baya.

Knocking data karaji yasa tadan tabe fuska dan kallon yafara mata dadi,debo
kwakumeti tayi a hannu ta mike tsaye tana tafiya tana waigen TV bude kofa tayi da
dayar hanunta batare datama kalli kofan ba hankalin ta nakan kallon,Takara bude
baki ta zuba kwakumetin tana taunawa ganin wani bakin dodo yazo Zai cinye wata
hakan yasa ta sandara ihu “wayyo Allah na Mummy” Kara bude ido tayi ta kalli TV
ganin dodon nacin mutum taga kaman ita yake cinyewa yasa tafasa ihu zata tajuya
zata fita daga dakin karo taji taci da mutum tai baya-baya zata fadi da sauri ya
riketa,kwalalo ido tayi kalleshi ganin dai tabbas shine yasa ta kulle idonta gam
tai lamo a jikinshi tareda kara kankameshi jikinta na rawa.

Chak ya dagata yazaunar da ita akan kujera,ya maida kofan yarufe kafin yadau remote
ya kashe kallon duk kanta na kasa tana Sosa kai,”karki Kara kallon irin film dinan
tunda firgita yake saki”. Kai kawai tadaga mai kafin ta tashi tayi hanyar bedroom
da sauri harda tuntube “ina zaki?” Juyowa tayi kanta akasa muryarta na rawa sosai
kaman mai shirin kuka tace ” ai,ai bacci nakeji” zoki zauna anan sai 1 zakiyi bacci
yau.

Ta dawo ta zauna jikinta na rawa. “Ya karatu?” Kallon fuskarshi tadanyi da sauri ta
juyar da kai tasa bayan hanunta ta goge Hawayen dake shirin zubo mata. Ya dade
yana kallonta kafin yay murmushi yace “coconut chips(kwakumeti)din harsun ishe
kine? Naga kinata ci dazu”girgiza kai tayi hawaye ya gangaro zuwa kunncinta, shida
yarasa maisa takejin tsoronshi haka anywayno insun hadu da Muzammil ya fadamai
maybe yasamu solution daga wurinshi. Wani dan karamin book ya ajiye mata akan
center table” help me. maman Abd Shakur 😘
[5/24, 13:45] Fauzee Preety: *KAINE SIRRI NA*

45
Ina mai alfahari da zamanki matata,and I promise zan kula dake,namiki komi ,I will
be d best husband kinji” hannunshi yasa ya kamo hanunta ya rike da sauri tadan zaro
ido tana kallonshi tattausan murmushi ya sakar mata. yadau ko wata yar karaman
akwatin dake kan tray ya bude wani farin zobe mai kama da azurfa anmai ado dajan
zanen zuciya ajiki ya ciro ya zura mata a yatsa ya dago kanshi yaga Rufaida na
kallonshi idanun na gab da zuboda ruwa, girgiza mata kai yayi ta hadiye hawayen.
yasa hannu ya shafa zoben “u are special Baby”yafada yana kallon kwayar Idonta.
ahankali ya zare hijabin jikinta, ta zaro ido jikinta na bari. Champagne ya dauko
daga kan tray din ya bude ya zuba a glass cups guda biyu ya mika mata daya takasa
karba,da kanshi yakai bakinta saida ta kalleshi ya lumshe mata ido sanan ta kurbi
kadan. ya ijiye kofin akan table ya kwanto da ita a jikinshi yana sauke ajiyan
zuciya a natse yana shafa bayanta. jikin Rufaida yafara rawa tafashe da kuka sosai
dago kanta yay “nadena bakiso?” Girgiza kai tayi a tsorace tace”zan tafi,bacci
nakeji,dama Mummy ce tace nazo nama sallama gobe zamu tafi” ganin yanda jikinta ke
bari hawaye na tsiyaya yasa ta mugun bashi tausayi yaji yafasa abunda yay niyyan
yi. Mikar da ita tsaye yayi yadau hijab dinta yasa mata, wasu jajajen fulawowi da
aka daure a wani irin leda(red roses) yasa mata a hannu ya kawo bakinshi kunenta
“symbol of my luv”taji ya ambata sanan ya koma gefe. da gudu ta juya zata fita
daga dakin, chak taji an rike hanunta,a tsorace ta juyo ta kalleshi bakinta na
rawa, ahankali ya sanya hannayen shi ya rike bayanta yana kallon kwayar idonta
kafin yadan rage tsawo yakai bakinshi yahada da nata.

Maman Abd Shakur.


[5/24, 13:45] Fauzee Preety: *KAINE SIRRI NA*

43
Tun daga ranan Rufaida bata sake ganin Barraq ba,hakan yasa hankalinta ya natsu
bata tunani. Saidai taga an mayar da ita wani bangare daban a gidan babu Wanda ke
shigowa daga mummy said Amma sai Hafsat matar Muzammil. Saikuma wata mata da suke
kwana tare dataji Mummy na kiranta da buzuwa. kullum tana bata wasu abu
taci,Tasha,Dana wanka dana tsarki, Rufaida dukta gaji dan har asalin abinci ma
andena bata Saidai na magani. Kullum idan Mummy ta shigo ganinta saita mata kuka
tana cewa ita batason abunan da ake bata Dan yana sata kiba tanajin wani iri Mum
saidai tai dariya ta lallabata ta tafi.

Yau takama Friday ranan da za’a fara sha’anin biki,tana zaune tanacin wani indomie
da buzuwa ta dafa mata da magani tana kuka hanunta da kafafunta sunsha hadaddun
baki dajan lalle na amare,gashinta yasha gyara wanda duk buzuwa ce taimata. Hafsat
ta shigo dauke da wani katuwar akwati a hanunta da sallama “wow!” Ta furta tana
kallon Rufaida dataga gabaki daya ta chanza bakin fatarta na wani irin sheki,ta
chiko sosai kirjin nan ya ciko daidai ita, karaso wa tayi ta zauna kusa da Rufaida
da murnanta “anty Rufaida kinyi mugun kyau Wlh, idan uncle B ya ganki saiya rude”ta
daga hanun da akamata zanen lalle tana kallo tace”waya miki wanan lallen?harda
gyaran gashi” Rufaida ta turo baki idanunta yakawo ruwa tace”ba buzuwar nan dasu
Mummy suka kawo bane,kullum saitabani magani wasu da dadi wasu da shegen daci,taita
shafamin wani black and yellow-yellow(kur-kur da dilka) things on my sick. takara
fashewa da kuka muryarta na rawa”and am sure they have side effect, cus they have
one kind of disgusting odor yayanya,huum” tana maganan tana turo da tabe baki.
Hafsat ta rike kuncin ta tana kallon Rufaida dariya ke neman subuce mata amma
batason tayi hadiye dariyan tayi tadanyi murmushi kafin tace “kai amma buzuwa bata
kyauta mana ba,yanzu tashi ga kayan dazaki sa nakawo miki yaune walima
kinji”Rufaida tadan zaro ido “waliman bikin wai haryazo ba sati biyu akasa ba?ai
batayi ba saigobe ne fa anty Hafsat “Hafsat tai dariya mujeto kiyi. ahankali ta
mike suka shiga bayin, Buzuwa ta shigo tahada mata wasu abubuwa a ruwan Rufaida ta
zumburo baki Hafsat tafito tana dariya bata wani jimaba tafito Buzuwa ce tai mata
wani irin hadadden make up, Hafsat saibin buzuwa da kallo take tana mamakin yanda
ta iya komai gyaran jiki,lalle,gyaran gashi gakuma make up. Sai bayan angama tasa
mata kayan doguwar rigace har kasa ja,sai kuma dige digen baki ga takalman ta hill
aka samata, tai kyau sama da tunanin mai karatu Hafsat tarike mata hannu suka fara
tafiya,juyowa Rufaida tayi ta kalli Hafsat tace”anty bantaba sa Hill ba ya akayi
naga na iya tafiya dashi?” Hafsat zatai magana Mum takaraso wurin tabama Rufaida
kakkyawan runguma ta kalli Buzuwa tace “thanks for everything friend” Mum tarike
mata hannu har gaban wata hadaddiyar mota tasa hannu tabude tasa Rufaida aciki ta
kullo,su da wasu manyan matayen turawa suka shiga sauran motocin da akayi layi dasu
a wurin suka wuce wurin walimar.

Wa’azi sosai wasu manyan malamai sukayi mai ratsa jiki,da ilmantar wa,Rufaida tasha
kuka bana wasaba. Karfe 7:00pm aka dawo gida, bayan sallan issha dad ya aika aka
kiramai Rufaida.

Wa’azi da nasiha da uba yakamata yayma yarshi dad yayma Rufaida. Rufaida tasha kuka
a wurin anan yake sanar mata da Barraq yace a Russia yakeso tai karatu,dan dazaran
yagama wani case dake gabanshi yanzu na neman wata yarinya zai koma Russai da zama.
so saisa na nema miki makaranta a Chan ranan Monday zasu koma keda Mum kinji yata?
Rufaida tamai godiya ta karbi wani akwatin da yabata tafita daga dakin.
Washe garin ranan aka daura Auren BARRISTER BARRAQ da RUFAIDA akan mafi karancin
sadaki Barraq yarasa Inda zaisa kanshi saboda murna burinshi daya kawai yaga
Rufaida.

Sosai zazzabi yarufe Rufaida idanunta sukai ja sosai jikinta zafi. Amma takira
family Doctor yadubata aka bata magunguna. Mummy ta zauna ta daura kanta akan
cinyarta tana shafa cikinta dataji ba nauyi. Tea Hafsat takawo mata da kyar tasha
kadan tana kuka. Mum dukta damu tace”for godsake Daughter meke damunki? Tell me
kinji banason kina ciwo” Rufaida takara narkema Mummy tana kuka”Mummy promise me
dake zan zauna,wlh Mummy ni banason akaini wurin Uncle B,tsoronshi nakeji Nafison
zama dake” takarasa maganan tana kuka, Mum tai murmushi “OK naji,only if u
cooperate kika warke dan baki sun cika gida anason ganinki” ta share hawayen to
muje naji sauki.

Maman Abd Shakur.


[5/24, 13:45] Fauzee Preety: *KAINE SIRRI NA*

44
Duk shagalin da aka hada Rufaida bata halarta ba saboda zazzabin dake damunta. Da
kyar Mum ta lallabata tai bacci ta lullubeta tafito daga dakin lokacin ma haryan
biki sun watse.

Dakin Mum ya shiga ganinta tareda wata bakuwa suna magana yasa ya zauna a gefen
gado yana danna waya. Mum taraka bakuwar tareda rufo kofa tazo kusada Barraq ta
zauna tana kallonshi”Muzammil na nemanka dazu,Hafsat nata amai zai wuce da ita
hospital “Barraq ya daura kanshi a kafadarta “ya ganni lokacin ina falon Daddy ina
magana da Alh nan dana fada miki yarshi tabace” Mum tace”ayya,har daurin auren
saida yazo,yanada kirki, Allah yasa yaga yartashi” Barraq yakara wani narke mata
“son am very tired, me kakeso saboda wanka nakeson shiga yanzu” Barraq yay shiru
baice komiba. “O ur wife, tana wurin buzuwa,tana bacci karka tasheta” murmushi yama
Mum ganin ta kafeshi da ido. mikewa tsaye yayi yafita daga dakin da sauri Mum ta
girgiza kai “sarkin kunya”.

Hango Buzuwa dayayi a dakin zaune tana kallo ta window yasa yaji wani haushi
yakamashi dan yaso yaduba lafiyar matarshi. haka yawuce side dinshi yafada kujera
ya dauko taba yafara zuka.

washe gari yakama lahadi taji sauki sosai saidai tai zuru zuru gashi batada abokin
hira dan Hafsat batazoba Mum tace batada lpy.
Wuraren 9:00 Na dare Mum tafito daga side din Buzuwa ganin Barraq tsaye a wurin
yana leken windo yasa Mum tace”wot are yhu doing son?” Da sauri ya juyo ya kalli
Mum “nothing “yaba Mum amsa atakaice yajuya yabar wurin da sauri. Ajiyan zuciya Mum
tayi tajuya takoma ciki. Rufaida dahar ta kwanta ta tashi da sauri ta yaye bargon
jikinta “Mummy na kindawo ki karanta min story ne?” Mum ta zauna gefen gado ta
girgiza kai “no,kije kima Son sallama,kinga gobe zamu koma kinji daughter “Rufaida
ta gyada kai”to Mummy” tadau hijab tadaura kan kayan baccin jikinta tajuya zata
fita Mum tace “come” tadawo Mum tadau turarurruka masu cool kamshi ta shafa mata
sanan tabata izinin tafiya.

Knocking tayi “who?” Taji yafada,muryarta na rawa tace”Ni…ni…nin..nine..” bata


karasa maganar ba yabude kofar da sauri taja da baya tana kuka hanunta na rawa ta
kulle idonta gam”.
Wani sanyi yaji a ranshi ganin Matarshi ce aranshi yace luv yhu Mummy.
Tattausan hanunta yakama ya shigar da ita cikin dakin. zaunar da ita yay akan
kujera ya maida kofar yarufe ahankali yadawo ya tsugunna a gabanta ya daura
hanunwanshi akan cinyarta ko ina na jikinta rawa yake murya chan kasa yace”relax
luv!u are with me, open ur eyes “kankame jikinta tayi tana sosa idanunta dake fitar
da ruwa. zame hanunshi yayi daga cinyarta yatashi ya shiga bedroom yay kusan minti
biyu kafin yafito sanye da white singlet da gajeren wando baki,hanunshi dauke
dawani dogon silver tray ya ijiye kan center table yadawo kusa da ita ya zauna
jikinshi na gogan nata, jawota jikinshi yay yarungume. ihu tasaki tana kokarin
kwace kanta takasa, ahankali yace”shiii!banason kuka, keep quiet and open ur eyes
kinji baby na “girgiza mai kai tayi,sanan yasaketa ta zauna tana share hawayen da
bayan hanunta “Rufaida “Taji ya kirata hakan yasa ta daga kai ta kalleshi “I luv
yhu, ina sonki sosai”.

Maman Abd Shakur .


[5/24, 13:45] Fauzee Preety: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

46
Da kyar ya iya sakin bakin nata yana kallon yanda take kuka yasa yatsa ya share
hawayen murya chan ciki yace”shiii,banason kuka, abunda nai miki is normal, haka
miji kema matarshi kinji baby na ” ta dagamai kai jikinta na rawa. harshen shi yasa
yadan lashi lips dinta dasukai ja yace”good girl,ina kara sonki ne saboda kinajin
magana,muje naraka ki ki kwanta dare yayi” hanunta yarike suna tafiya ahankali tana
binshi luuu dan gabaki dayan jikinta ya saki.

Saida ya bude kofar dakin Buzuwa sanan yasaki hanunta yana mata murmushi”sleep like
an angel Baby”ta shiga ciki da sauri ya kullo kofan yajuya yatafi side dinshi cike
da tunaninta. Da kyar bacci ya kwashi Rufaida dan takasa manta yanda taji yanata
tsotsan bakinta.

Washe gari da wuri Mum tasata ta shirya dan jirgin karfe tara zasubi. Buzuwa tahada
mata kayanta gabaki daya da wasu gangariyar magani. Rufaida ta shirya cikin wani
dogon brown skinny jeans da light brown armless shirt ta daura brown boyfriend
jacket a saman su, ta yane kanta da gyalle, kafarta na cikin wani hill browm mai
shegen kyau. tafito daga part din Buzuwa ahankali take takunta mai daukan hankali
harta bude kofan dazai sadata da dakin Mum da sauri ta juya zata koma “karki koma
ki shigo I missed yhu” ahankali ta shigo kanta akasa tana watsa da yatsun hanunta
ta tsaya, jawota jikinshi yayi ya daurata akan cinyarshi yana kare mata
kallo,ahankali yasa hannu yana warware gyalen da ta nade kanta “Baby dis kand of
dressing is for me only,bakisan inada kishi ba” hawayen ta ya diga akan
hanunshi,murmushi yay ya daga hanunta yana kallon zanen lallen hanunta”I luv
dis,yama hanunki kyau “ahankali yasa hannu a kafadarta yana sabule boyfriend jacket
din jikinta harya cire duka ya ijiye a gefenshi yana karema jikinta kallo batare
daya mata komiba. Rufaida tacigaba damai kuka ahankali tana shesheka,kanta akasa
taki hada ido dashi “Mummy kike nema?” Ta dagamai kai,”Mum na wurin Dad tajemai
sallama”.

“Mesa kike tsorona?ni dodo ne?” Ahankali tace”uhm uhm”ya leko da fuskarshi zai
kalleta da sauri ta juyar da kanta gefe,juyo da fuskarta yay ya kwanto da ita
kirjinshi yana shafa bayanta ahankali ya sauke ajiyan zuciya”I will miss yhu idan
kun tafi,but dazaran nagama case din dake gabana nanda 3 or 4 weeks zanzo,just take
good care of ur self for me Baby, I luv yhu” takara kulle ido jikinta na rawa dago
ta yay yahada goshin shi da nata murya Chan ciki yace “duk lokacin dakike wanan
tsorace tsoracen,da koke koken da kulle kullen idon, karajin sonki nake a zuciyata
cus I luv it,everything fits yhu Rufaida my little Baby ” yakai bakinshi kan nata
yabata light kiss “Ina sonki matata” chusa kanta tayi sosai a kirjinshi tana mutsu
mutsu saboda kunya, abun yabashi dariya sosai yadan dara “nacigaba da kissing dinki
ne baby na ? ” ta boye fuskarta a kirjinshi tana shesheka bude kofa da akayi yasa
ya dago kanshi Mum ce da sauri Rufaida ta sauka daga jikinshi ta koma gefe Mum tai
kaman bataga komiba tace”Daughter kin shirya?” Barraq ya tashi yana sosakai Mum ta
bishi da kallo harya fita ya dawo ciki da sauri Rufaida ta sadda kanta akasa kallon
Mum yayi kafin yace”kisa Hijab,karki fita ahaka ” ya juya yafita da sauri yana
murmushi.

Maman Abd Shakur😘


[5/24, 23:18] Aishat Muhammad: [5/24, 21:46] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌
47
Kimanin sati 3 uku kenan da komawarsu Russia. Tuni Rufaida tafara makaranta mai
suna KINGSLEY DAISY’S SCIENCE SCHOOL. aka mata interview taci sosai hakan yasa
suka sata a class 2(SS2 a Nigeria ). Karatu take sosai tana da kokari daidai
ita,batada kawa ko daya dazaran lokacin tashi yayi Mum zata turo Driver yadauko ta.
Mum nabata kulawa bata sakaci da magungunan da buzuwa tahada mata dakuma na asibiti
da aka bata saboda yawan ciwan maran datakeyi kowani wata.

Bangaren Barraq kuwa ya dukufa neman Rufaida, saboda yanda yaga Umma da Ahj na
wahala danko haihuwar datayi saidai aka mata aiki aka ciro baby boy. Gashi yanzu
kusan sati uku kenan yanabin makarantu gidan marayu na garuruwa daban daban yana
neman Rufaida da aka mishi kwatance. Aikin da yansanda yakamata suyi amma tausayin
su Alhj yasa shiyake yi dakanshi. Matsalanshi daya yakasa samun kishiyan Umma suyi
magana duk inyaje Lagos Alh yakaishi gidanta basa samunta har abun yasoma bashi
mamaki. Yafadan ma Alhj zai dakatar da binciken yaje yaduba matarshi a Russia. Alh
yamai addu’a Umma tahada tsaraba dayawa tabama Barraq yakaima matarshi da kyar suka
samu ya karba Alh yakaishi Airport yabi jirgi yakoma Abuja.

“What are U saying murtala (PA)?Danme nake biyanka da bazaka sanar dani wanan
babban maganar ba? Har saida tai tsami harma tafara wari kafin naji?” PA yace “haba
Nana ai kyamin uxuri ,har gidanku naje danna fada miki amma akace kinje Dubai toya
zanyi?” Nana ta dafe kai tana huci “yanzu Barraq dinane yay aure? Ya auri wata
batare da nasani ba. Nooo!” Ta buga glass cup din hanunta akasa yafashe TASS. “Wlh
bazai yuwu ba,Bazata sabuba bindiga a ruwa, nikadai ce matar Barraq bai isa ya auri
wataba, am d only one dat is meant for him”. PA ya gyara neck tie din wuyarshi
yace “better do something, dan gobe zai tafi Russia ganinta,zai kuma Dade,and d
worse part is bantaba ganin Barr in luv kaman yanda naga yakamu dana yar yarinyar
nan ba,gashi kowa nason yarinyar barinma Mum dinshi,wlh I can tell you tafison
yarinyar kan Barraq her own son”. Da sauri Nana tace”flight din karfe nawa zaibi?”
PA ya balla mata harara “biyani kafin nabaki information, kinsan yanda kike
biyana”. Nana takai mishi kiss abaki “just tell me I promise zamu hadu a hotel
anjima kafadan min”. PA yace “flight din karfe 2:30 zaibi na rana ” Nana ta suri
jakarta tafita daga dakin da sauri.
“Nariga nasan matsalar ki,maikike so yanzu ama Barraq abin kaunar ki?” Nana tai
shiru tana tunani kafin ta sauke ijiyan zuciya “Bokana inaso ama Barraq abunda
zaisa Mamarshi ta koroshi daga Russia, matar tashi ta tsaneshi,ta tsorata dashi,ya
shiga cikin damuwa, sanan yazamto mai yawan bukata yanda zan samu shiga a wurinshi
da wuri takuma sauki”
Boka yay ihu ya bugi kasa maiyake zuciyarki ayanzu dakikafi so amishi,dannaga akwai
abunda ke ranki ?” Nana tarike haba tana tunani kafin tace “Mamar Barraq babbar
mace ce a garin Russia, itace shugabar kwatar ma mata hakkinsu da yancinsu,tana
fighting child abuse, dakuma issues din yima mata fyade. A garin Russia idan aka
kama namiji yama mace fyade zaa kulleshi,a hukuntashu,kokuma aka kama wani namiji
ya shiga mace harya yagata yay mata illa sai an hukuntashi. To plan dina anan shine
karka manta inaso Mum taji haushin Barraq harta koreshi, sanan inaso yar iskan
yarinyar ta wahala takuma azabtu sosai” tama boka fari da ido kafin tace”Bokana
nakaina abinda nakeso shine a gusar min da hankalin Barraq, ya haukace, to a
haukacen zai afkama Rufaida ta sanadiyar wata muguwar shaawa dazaka samai,idan ya
afka mata inaso ya barkata,ya zagata ta azabtu ta wahala sosai yanda zatai nadaman
auren wanda nakeso, kai idan zaka iyama ka aikamin da ita lahira alokacin, ta mutu
kawai sai bayan yagama hankalinshi zai dawo,to dazaran Mum taga abinda yama
yarinyar ranta zai baci, zata tsani Barraq har hakan yay sanadiyyar tace yabar mata
gida kagane Bokana, karka damu biya biyu zanma dana jikina dana kudi”. tamai fari
da ido boka ya washe jajayen hakoranshi angama tawan.

Yafara wasu surkulle cikin karamin lokaci wani hadadden chocolate ya bayyana a
hanun Boka gwanin ban sha’awa mai kyau an rufeshi dawani irin jan Leda da akama ado
da jan fulawowi ya mikama Nana yace”ki tabbata yasha,dazaran yasha zai haukace
saiyama yarinyar illa zai dawo hayyacin shi” Nana ta mika hannu ta karba tanamai
shu’umin murmushi tasaka acikin jaka kafin su shige daki dan mishi biya na farko.

Maman Abd Shakur.


[5/24, 23:15] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*

48
Barr Barraq tsaye a haraban gidansu yana magana da Dad. bayan sun gama maganan
yakaraso inda PA ke tsaye rike da jakarshi Barr yabude mota ya shiga “mutafi” PA
yasa jakar a boot yadawo gaban mota ya xauna yana kokarin kunna mota Barr
yace”Oops na manta wani Abu, abunda nasaima matata bari na dauko”. PA yay murmushi
Barr yafita daga motar. fitarshi keda wuya PA yaciro wayarshi yay dailing number
Nana ringing daya ta dauka yace “kina ina dan gashinan harya shirya zan kaishi
airport sai wani murna yake dan iskan tuzurun ?” Nana ta tabe baki tana taunar
cingam “ina Airport mana ina jiranku” kashe wayan yay da sauri hango Barr na tahowa
yana shigowa yaja motar sai Airport.
Parka motar PA yayi a parking space da aka tanada a airport Barr ya fito yana gyara
eyeglasses dinshi ya karbi jakarshi yanama PA murmushi ya mikamai hannu suka gaisa
yace”thanks,I appreciate everything dakakemin,shawarwarin ka,da taimakona da ayyuka
dakeka thanks,saina dawo” yazaro sabuwar check din dubu dari biyar ya mikamai PA ya
karba yay godiya yaja mota yatafi. ahankali Barr ke tafiya cike da natsuwa jin ance
“Barrister “yasa ya juyo da kanshi ganin Nana tsaye cikin kayan arna da gashin doki
yasa yajuya da sauri yacigaba da tafiya. Tasha gabanshi ta tsugunna tana haki
tahade hannayenta tana rokanshi “Barr dan girman Allah ka saurare ni, kadena
wulakantani plz” Barraq ya kalli agogon hanunshi da yanda mutane ke kallonsu
yace”wot?Me kikeyi anan bazaki rabu daniba am married,so no chance and no space 4
yhu ” Nana tafara kuka sosai “I know nasan kai aure,nasan ka tsaneni nakuma hakura
dakai amma son danake ma yasa naimaka chocolate da kaina a matsayin gudunmawana na
auren ka. “And who d heck told you I need ur chocolate, look Nana am sick of ur
drama, ki matsamin daga hanya na wuce” yabi ta gefenta zai wuce ta kama rigarshi
tana kuka sosai mutane suka soma taruwa a wurin “Dan Allah ka karba,idan harka
karba kaci at least zanji dadi dudda baka soniba amma kaci wani abu da hannuna
yahada Barraq” tafashe da kuka sosai wanda hakan yadan taba zuciyan Barraq mutane
suka taru ana kallonsu ahankali Barraq ya juyo ya mika mata hannu “kawoto” da sauri
ta share hawaye ta dauko daga jaka ta bashi “nagode Barr, zakaci ko?,dan Allah
kaci”. Barraq yadade yana kallonta kafin ya gyada mata kai “zanci”ya bude jakar
laptop ya saka ciki yay maza ya bada ticket dinshi yay sama.

Karfe 4 narana ya sauka agarin Russia. Mum tai mamakin ganinshi dan baifada mata
zuwan shiba, sai kalle kalle yake kozaiga Rufaida Mum tai murmushi tace”O ur
wife,bata dawo daga school ba,Driver yaje daukota” ya tashi bari naje nai wanka”
Mum ta kalli agogo “am going out son,inada meeting sai 6 zamu fito, ga lunch dinka
a dining ” akasalance yace”ok Mummy, bari nafara wanka nahuta xanzo naci saikin
dawo” tareda Mum suka fito Mum ta shiga mota shikuma ya shiga dakinshi.
Fitan Mum keda wuya motar kai Rufaida school ta shigo. fitowa tayi ahankali dauke
da jakarta abaya tana tabe baki dakinta ta wuce direct ta cire kayan makarantar ta
shiga bayi ta watsa ruwa. tana fitowa ta zira wata yar shimi iya guiwa pink ta ta
kama bakin jekar all back din da aka mata guda biyu da pink rubber band tafito tana
kwallama Mum kira tun kafin takai dakinta. Lidya tace Mum tafita taje meeting.
Fadawa kan kujera tayi ta zauna “am hungry ni Wlh” Lidya tai dariya toga abinciki
chan a dining Rufaida ta mike tsaye taje dining tabude kulolin ta maida tarufe
batacema Lidya komi ba tawuce kitchen indomie biyu ta dauko da kwai biyu sai bake
beans tahada tadafa indomie. Tana gamawa ta juye a karaman bowl mai kyau nacin
abinci tadau fork tafito daga kitchen din tana rera yar waka tana tafiya tanakuma
kokarin debo indomie da fork taci, tsayawa tayi agaban dining tabama dining baya ta
zuba abakinta tahadiye murmushi tayi ahankali tace”yummy ” ta maida fork din cikin
indomie tayi hanyar dakinta. “Baby” dataji an kira ahankali yasa ta waigowa,ganin
Barraq yana zaune a dining yana mata wani sassanyar kallo dauke da murmushi yasa
jikinta yafara rawa ta zaro ido tana kallonshi. Ahankali yasa hannu yature abincin
gabanshi ya mike tsaye yafara tafiya ahankali harya iso gabanta ya tsaya yana kare
mata kallo daga sama har kasa. indomie hanunta tasaki ya bare a kafarta ihu tasaki
saboda zafi ta rikeshi tana kuka.

Maman Abd Shakur😘

mamanshakur Is all about novels.

49
Ya riketa da sauri “O sorry Baby na muje kitchen ki wanke” kin motsi tayi hakan
yasa ya dauketa tana wuntsila kafa bai ajiyeta ba sai abayin dakinshi ya kunna tap
da sauri ya debi ruwa a cup ya tsugunna yana zubawa a karfarta yana wankewa tana
kuka. saida yagama ya kara daukarta yafito da ita ya ijiyeta akan gado ta cusa
kanta a cikin cinya tana kuka. dauko vaseline yay ya shafa akan kafar yana hura
mata ahankali.

Dago da kanta tayi ta kalleshi ganin ita yake kallo yana hura ciwon yasa ta dauke
kai tana share hawaye da bayan hanunta “ya dena zafin nizan tafi”Tafada ahankali,
sakin kafar yay yatashi ya hayo gadon yana kare mata kallo kaman ba ita tai magana
ba murmushi yay ya daura kanshi a kafadar ta yana kallon fuskarta “Wify look me
mana, nadawo ko welcome kiss dasu oyoyo hugs and everything bakimin ba instead
saikika konamin wanan kakkyawar kafa ta danake ji da ita, is dat fair Baby?”
Rufaida ta sharce kwalla tana kokarin fizge kafadar ta. Zame kanshi yay daga
kafadar ta ya fizgota tafado jikinshi ya kwanta akan gado yana karema fuskarta
kallo yanda ta runtse idanunta gam. Sa hannu yay yakara kwanto da ita gabaki daya a
kirjinshi ahankali ya janyo filo ya daura kanshi akai yacigaba da shafa bayanta
yana sauke numfashi a natse yanajin yanda zuciyarta ke bugawa da sauri lumshe ido
yay “I missed ur soft skin, nai kewanki sosai Matata, ya school kina gane karatun
kuwa?” Rufaida takara runtse ido tanajin wani iri saboda yanda yake shafa bayanta.
Ahankali ya dagata yaga yanda ta kulle ido yay murmushi”jekici abinci,nasan kinajin
yunwa,I will join yhu in a minute zan tura wani email ne” ya shafa cikinta “tonight
anan dakin zaki kwana” ya saketa da sauri ta sauka tai hanyar fita daga dakin yabi
bayanta da kallo hartasa hannu zata bude kofa tafita yace”Rufaida “ta dago kai ta
kalleshi “I luv yhu ” da gudu tafita daga dakin yay dan dariya “my fear-fear wife”
yakada kai tareda zamowa daga kan gadon yadau jakar laptop dinshi ya bude ya janyo
laptop ya ajiye akan table din wurin. Maida jakan yay zai ajiye chocolate din da
Nana tabashi ya fadi akasa, ahankali ya ajiye jakar ya tsugunna yasa hannun shi
yadau chocolate din yana kallo, kara gyara glass din idonshi yay yana kallon
chocolate din ahankali yace”nasan da wani abu a chocolate dinan 4rm d reaction din
Nana when she was giving me,what are u up to dis time around Nana?wot game are you
trying to play ” ajiyan zuciya ya dan sauke tareda ajiye chocolate din akan table
yace “I will take it to lab tomorrow to examine it,koma me aciki I will know and
dat I will show you my hmmm Nana “. yay kwafa ya zauna kan kujera yabude laptop
yafara abunda zaiyi.

Bai koma side din Mum ba sai bayan sallan issha. Yana sanye da jallabiya Mum yasamu
zaune tana kallon news,Rufaida na gefenta tana assignment. “Evening Mummy ” Mum
tace “Son ya kake, ga dinner ka a dining “ya shafa cikinshi “thanks Mummy dama am
pretty hungry “yay hanyar dinning Mum ta kalli Rufaida “daughter jekiyi serving
dinshi” ta rufe books din ta mike yana zaune ko taba abincin baiyiba kanta akasa
tafara zubamai white Rice hanunta taji yarike ta kalleshi da sauri “ya isheni”
tasamai stew asama tajuya da sauri zatabar wurin yakamo hanunta ya daurata akan
kujeran kusa dashi”sit here” ta zauna tana wasa da yatsa ahankali yakecin abincin
yana kallonta “Baby na je bedroom dina na manta dazan shigo ban dauko miki tsaraban
kiba, jeki dauko kizo” tashi tayi tafara tafiya ahankali yabita da kallo tafiyar ta
na burgeshi bana wasaba. Ina zaki daughter? Cewar Mum uncle B yace nadauko mai
abu adaki tawuce.
Ahankali tabude kofar bedroom dinshi ta shiga tana waige waige, hango wata bakar
jaka agefen gadonshi yasa tai wurin zata dauka hartakai hannu zata dauka idanunta
suka sauka akan chocolate din dake kan table da sauri tai wurin tana murmushi “yes
chocolate, my favorite, thank yhu uncle B” ta dauka tayi hanyar fita da sauri ta
dawo ta zauna kan gado tana zaro ido”Mum tahana ni cin chocolate, dazaran tagani
zata kwace, d best thing naci abuna anan” fadan hakan keda wuya ta bude chocolate
din har yawunta na tsinkewa ta gutsuro tasa abakinta yana wani juya ido” yummy ” ta
hadiye.

Shirun dayaji yasa yay tunanin hala bataga tsaraban bane. Ya mike yabi bayanta.
Ahankali ya bude kofar bedroom Rufaida dataci kusan rabin chocolate tanaji an bude
kofar bedroom ta tashi tsaye tana zaro ido, wani irin jiri jiri tafara
ji,idanuwanta na juyawa tafara layi kamar wacce tasha giya. Barraq ya kalleta 4rm
head to toe ganin chocolate din da Nana tabashi a hanunta yasa ya rufe kofa da
sauri ya shigo dakin alokacin harta zube akasa tana mutsu mutsu tarike cikinta gam,
dago kanta yay ya daura akan cinyarshi yana girgizata “wot is wrong with yhu
Baby?”hango chocolate din hanunta abude harta maci kusan rabi yasa yasaki
ihu”Noooo! Maisa kikaci darling?” Dagota yay ya chusa yatsarshi a makogoron ta
saboda tai aman chocolate din amma yaga batayiba, saima kokarin barka rigar
jikinshi datake yi.

Maman Abd Shakur.😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 49KAINE SIRRI NA 52 →
KAINE SIRRI NA 50 & 51
Posted on May 26, 2016 by mamanshakur
[5/26, 11:31] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

50
Ganin da gaske take tana kokarin barka shirt din jikinshi yasa yakama hannayen ta
yarike yana kokarin gano wani abu daga yanayin ta. dago kanta daga cinyarshi tayi
ta chusa a kirjinshi sosai kaman zata fasa tana shinshinawa, tana numfashi sama-
sama tasa hannu takama kwalar shirt dinshi tana janshi. Barraq yama rasa mezaiyi
mata,zame jikinshi yay ya rike fuskarta yana girgizata tareda kiran sunanta
“Rufaida Baby darling ” ahankali ta kalleshi da idanuwanta dasukayi wani irin ja
kafin ta lumshe su tana takara fadowa jikinshi takamashi tarikeshi gam ta matse
kafa tana kuka. Barraq yakai hannu ya dauko chocolate din yana kallo ganin Rufaida
na birgima akasa tana wuntsila kafa yasa ya ajiye da sauri yazo inda take ya dagata
idanunshi sunyi ja yafara tunanin kodai yakira Mum ne saikuma yafasa. bakinshi
tafara shafawa da hannu tana nishi kaman maijin kishin ruwa, idanuwanta sun
kankance sosai tana shafashi tana wani irin chusa jikinta a nashi,tana kamo
hanunshi tana daurawa ajikinshi.
Kwalla yacika idon Barraq sosai “Nana mekika samin a chocolate dinan da matata
taci?”Hannun dayaji Rufaida tasa tana balle boturan kayanshi yasa yarike hanunwanta
da sauri yana girgiza mata kai. fizge hanunwanta tayi daga nashi tareda fashemai da
kuka ta maida hannun tana bude boturan rigarshi,kama hannuwan yay hawaye ya zubo
daga idonshi yana girgiza mata kai ” No Baby,dis is not yhu,bazan iya miki abunda
kikeso ba,kome zai faru na auratayya nafiso yafaru dukanmu muna cikin hayyacin mu,
dannasan bakya cikin hankalinki yanzu, something is definitely wrong ” ya rike
mata hannaye gam yana girgizata. mutsu mutsu tafara da kafa tana kokarin kwace
hanunta amma takasa, tafara mai ihu sosai tana wani irin kuka kaman ba itaba, da
sauri ya saki hannunta yana kallon ta, tashi tayi tsaye da kyar tana wani irin layi
da tangadi ta zare doguwar rigar dake jikinta, yarage daga wando sai bra ajikinta
da sauri Barraq ya kawar da kanshi. Jin takara fadowa jikinshi tana lashemai gefen
wuya yasa ya dauketa chak ya jefata akan gado, da sauri yadau wayarshi dake kan
table yafita daga dakin, tareda kullo kofar da sauri yasaka key.

Rufaida da hankalin ta baya jikinta bata ganin komi na dakin sai Barraq, yana fita
tafara ganin duhu matse kafa ta dingayi tana mutsu mutsu akan gadon hartaji ta
tafado kasa, ta buge hannu sosai, bubbuga kafafuwan ta tadinga yi akasa, tana wani
irin birgima tana bankarewa, tana ihu tana dukan kasa da hanunwanta. gatanan ne
kaman mahaukaciya, kaman mayya saboda yanda take zazzago harshe. Kaman tababbiya.

“Listen B cool ur mind,yanzu ba lokacin tunanin abunda Nana tayi bane, bcus zata
iyayin worse dan wanan ma,yanzu tuananin wot will help Rufaida zamuyi,dan inhar
kwayoyin sha’awa tasa a chocolate din zaiyi affecting Rufaida sosai ” Barraq da
muryarshi ke rawa sosai yace “Muzammil I don’t know,is all my fault, I left d
chocolate on my table, nasan she thinks shine tsaraban saisa taci, bansan mezan
mataba, she is suffering alot,yanzu hakama inajin ihunta da buge bugen datakeyi”
yasa hannu ya goge kwallar dake neman zubomai. Muzammil yace ” kabata ruwan lemun
tsami Tasha,ko kuma kamata powerful alluran bacci dazai sa bacci mai karfi ya
dauketa,I think hakan zai rage mata abunda takeji,kafin da safe ka kaita hospital”
ahankali Barraq yace ” hakan xaiyi solving problem din?” Muzammil ya nisa “inbai
yiba I guess u have to think 4 another alternative, hakanan kai saika bata maganin
dake tareda kai tareda mata addu’oin tsarin nan dana koyama” Barraq yace “thanks
friend” yakatse wayan. Fita yay yabama gateman kudi mai yawa yaje pharmacy ya
siyomai alluran barci mai karfi, yawuce part din Mum bai sameta a faloba ya wuce
kitchen yaga lemon tsami dayawa ya yanka ya matse su a cup yatafi dasu part dinshi
ahankali yake bude kofar yana shiga yaga Rufaida na.

Maman Abd Shakur😘


[5/26, 11:31] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

51
Ta tsugunna ta rike cikinta gam, tana kakarin amai,gashin kanta duksun barbaje
ajikinta. da sauri ya maida kofan yarufe ya karaso ciki da sauri ya ajiye kofin
agefe yasa hannu ya dagata “my Baby” ya daurata akan jikinshi, gabaki daya yaji
jikinta yay laushi,yasaki yakuma dau zafi sosai. tarike shi gam,hanunshi yasa
yatattara gashinta ya tufke mata a tsakiyan kai. Ya kauda kanshi da sauri ganin
surarta yasoma tayarmai da hankali, dauko ruwan lemon din yay ya ciro kanta daga
wuyarshi yakara mata abaki “drink, sha kinji Baby na zaisa ki warke” jujjuya fuska
ta farayi tana neman maida kanta jikinshi,hanunshi daya yasa ya matse bakinta
ahankali ya zuba mata lemun tsamin a baki tahadiye tana tabe baki,da kyar dai
yasamu tasha rabin cup ya ijiye sauran a gefe yana shafa kanta yana hura mata iska
a fuska hawaye yacika idonshi sosai “zaki warke kinji Baby na,be strong ” hawaye
yaga ya tsiyayo daga gefen idanunta tai wani lagab, jikinta ko ina yasaki ko karfi
daya bataji sai muguwar shaawa datakeji da wani irin sarawa da kanta yakeyi, jin
anyi knocking kofa yasa ya dauketa ya daurata kan gado,yadan ja bargo ya rufe mata
jikinta yajuya ya gyggyara jikinshi da boturan rigarshi kafin ya bude kofa, maigadi
ne ya karbi alluran da sabuwar sirinjin ya shigo daki ya maida kofa yarufe. saida
yafara karanta bayanin alluran bayan ya tabbatar na bacci ne ya bude bakin alluran
yasa sirinji ya zuko allurar ya ajiye kan table spirit dinshi da cotton wool ya
ciro daga drawer ya jika yazo yacire bargon jikinta yamata alluran wanda yasa
tasaki dan karamin ihu.

Ya zauna yana shafa gashinta yakara karfin AC ganin yanda take zufa. Har karfe 2
dare yaga batai bacci ba saidai ko motsin kirki bata iyayi. ta harde kafafunta
kawai hawaye na zuba daga idonta. Barraq yarike hanunta yana kuka. har karfe 3 dare
ganin takiyin bacci sai wahala yasa ya dauko ragowan lemun tsamin addu’oin yay
aciki da karatu yakara mata abaki tasha kadan ya ijiye a gefe ya hayo gadon ya
daura kanta akan cinyarshi yana shafa kanta ahankali yaga tai shiru ta natsu tadena
matse kafafun sai kallon gefe daya datakeyi ahaka suka zauna har karfe shidan safe.
Ya zame kanta daga cinyarshi ya shafa fuskarta “my Baby” yaga ta kalleshi da
kananun idanunta “bari nai salla kinji” ya shiga bayi ya sakin ma kanshi shower
yana wanka. karan dayaji yasa ya kashe shower jin tabbas karan buga abune yasa
yadau jallabiyar shi dake rataye abayin ya zira yafito da sauri ganin Rufaida akasa
tana bubbuga kanta ajikin gado tana bubbuga kafarta akasa tana ihu, da sauri yazo
wurin ya tsugunna ya daura hanunshi abayan kanta “Rufaida! ” buga jikinta tayi
akasa ta kwanta tana wani irin birgima tana kakarin amai, amma komi yaki fitowa.
ringing din dayaji wayarshi nayi yasa ya dagata ya daura akan gado yakoma ya daga
wayar ganin Mummy yasa gabanshi yafadi ya dauka “Son kasan Rufaida zata school
ko,is already after 6 now, bazaka barta tazo ta shirya ba ” muryar shi na rawa yace
“gatanan zu..zuwa” yanayin yanda Mum taji muryarshi yasa tace” is everything
alright? ” Barraq ya saki wayan akasa yana kiran “Rufaida, Baby” ganin tana wani
irin jan numfash tafado daga kan gado.

Maman Abd Shakur😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 50 & 51KAINE SIRRI NA 53 →
KAINE SIRRI NA 52
Posted on May 26, 2016 by mamanshakur
🖌KAINE SIRRI NA🖌

52
Ya dauketa da sauri yasata ajikinshi yana shafa fuskarta “my luv” rirrikeshi tayi
gam ta lumshe ido tana Jan numfasi da sauri, tana wani irin mika ajikinshi.
knocking din dayaji anyi yasa ya daurata akan gado yaja bargo ya rufeta, yadau
rigarta data cire ya wurga a toilet dinshi sanan yay wurin kofar ya bude, ganin Mum
a wurin yasa zuciyarshi ta buga “ina daughter na ?” Mum ta tambaya ganinshi
abirkice, ya shafa kanshi yana waigen baya, “I said ina daughter na, I know
something is wrong,maiya sameta ” yabude baki zaiyi magana kenan sukaji karan buga
abu, da sauri yajuya yakoma ciki,Mum tabi bayanshi suka shiga cikin dakin, Rufaida
sukagani tafadi akasa takifa cikinta akasa tana kwara wani irin bakin amai, da
sauri Barraq ya shiga bayi Mum ta tsugunna tasa hannu takamata tarike, Barraq
yafito dauke da bowl din ruwa da karamin towel. Mum tasa ta share mata baki da
jikinta tareda kasan wurin, Barraq ya maida ruwan bayi yafito ya tsugunna a gabansu
yana kallon Rufaida dake kallonshi da kananun Idonta. da karfi Rufaida ta fizge
jikinta daga Mum tafada jikin Barraq tana jan kwalar jallabiyar shi idanunta arufe.
Mum ta kalli Barraq “maiya sami Daughter?” Barraq yay shiru kanshi akasa dan
baimasan tayaya zaima Mum bayani ba, ahankali ya dagata yamaida ta kan gado ya
lullube ta da bargo tana mutsu mutsu “I said wot is wrong with my girl?”Mum ta
tambaya azafafe. Barraq ya dafakai yace “I,I, I don’t know Mummy,she just ate
chocolate din daaka bani, shine tadawo haka, takoma haka” Mum ta kalleshi ganin
shima dukya daburce gashi Rufaida saijan jallabiyar shi take hakan yasa tace “sit
down & carry her” ya zauna ya dauketa yana shafa mata kai, Mum ta kwantar da murya
idanunta akan Rufaida dataga tawani chanza ta rame idanunta sun kumbura sunyi ja
sosai gashi sun kankance “Son wot happen to my baby? ” ahankali cikin natsuwa
Barraq ya fadinma Mum komi, tundaga lokacin da Nana ta bashi chocolate har zuwa
yanzu da safe. Idanun Mum yacika da hawaye sosai dan tagane sexual inducement
chocolate Nana tabashi shine Rufaida tasha, ta kalli Rufaida dake juye juye ajikin
Barraq gwanin ban tausayi.

Ahankali ta tashi taje gaban kofa tarike Door handle, tajuyo da kanta ta kalli
Barraq da ita yake kallo “am a mother! uwa bata iya jure ganin yaranta na ciwo! tun
kana karami Barraq idan kana ciwo,kana wahala, inhar aka cemin ga kaza shine zaisa
kadena shan wahala, kadena ciwo zan karba nabaka kasha ka warke koma menene,kawai
bukatana ka warke” ta sauke ajiyan zuciya “my daughter has been suffering tun jiya
da daddare, and u know d actually cure dazaisa tadawo normal, ta warware but ka
kyaleta,kabarmin y’a tanata wahala akan abunda kasan it was meant 4 yhu! kanajin
dadin yanda take wahala ne ahaka,are yhu happy?” Barraq ya girgiza mata kai hawaye
na neman zubomai “Mum listen bahaka.. ” ta dagamai hannu” banason naji komi, I
will not lie 2 yhu Barraq, 4 d 1st time yau kabatamin rai, U hurt me deeply,abunda
kayi ya sosamin rai” ta share hawayen daya zubo mata takara kallon Rufaida “just
take a look at her,jibi yanda tadawo, U allow my baby to suffer 4 d past 11
hours,Inda haka na raineka idan kana ciwo inada maganin dazan baka kasha ka warke
ban bakaba da kakai haka yanzu?dakama rayu?” Barraq ya girgiza kai yafashe da
kuka yana kallon Mum dake fadanmai maganganun dake tabamai rai sosai. Mum ta dauke
kai daga kallonshi “just do something, kabama daughter na maganin daya dace,wanda
kasan shizaisa taji normal, inka gama mu wuce da ita hospital ” tabude kofa tafita
tareda bugo kofar.

Barraq yakara fashewa da kuka ya dago Rufaida ya rungumeta yana jijjigata “Wlh,Wlh
Rufaida I luv yhuu soo much,ban barki ahaka bane danna wahalar dakeba,I soo much
care about yhu my luv, am sorry, am sorry dana barki kika wahala tun jiya batare
dana miki maganin matsalan kiba” dago kanta yay yana shesheka yarike fuskarta,
ahankali yahada bakinshi da nata da sauri ta chafke tareda sauke wani irin ajiyan
zuciya, hakan yasa hawaye yakara zubomai saboda tausayinta.

Ahankali yake shafa jikinta har hanunwanshi suka sauka a maballin Bra dinta,ya
ballesu a natse,ya zamesu daga jikinta, Bakinshi yacire daga nata ya kwantar da ita
kan gado tana mutsu mutsu tana kokarin rikeshi ya kalleta kafin yakara daukota ya
maidata jikinshi. ahankali yake shafa wuyanta har yakai hannu yafara wasa da
kirjinta.

Maman Abd Shakur😘

53
Wasanni yacigaba da aikamata dasu masu zafi, tana kara shihshige mai jiki, harshe
shi yakai cikin kunnenta, hannayenshi yana yawo dasu ajikinta tana mutsu-mutsu. Da
karfi yaji ta rike kwalar rigarshi, tana bankarewa, da sauri yazaro harsheshi daga
kunnenta yasaketa. Amai tafara kwarowa nawani irin bakin abu, tun tanayi abu
nafita hartazo babu abinda kefita daga cikinta.

Barraq yariketa da sauri ganin tana neman shidewa “is OK” a dauko tissue dake gefen
gadon ya share mata baki, ya kwanto da ita jikinshi yana jijjigata, Ahankali
yaga tabude idonta dasuka kankance ta kalleshi, murmurs hi Ya sakar mata tareda
shafa cikinta “Alhamdulillah, u are fine ,kinajin yunwa?”Kadan kadan yaga tana
kukkulle ido, har idon suka rufe ruf,ta sauke ajiyan zuciya tareda gyara kwanciya
ajikinshi. Murna yakamashi daya tabbatar da bacci ne yay gaba da ita. Zamo da ita
yay ahankali Ya kwantar da ita kan gado,surarta dayake gani nawani irin figarshi
. dauke ido yay yatashi yaje wardrobe yaciro sabon zanin gado ya lullubeta dashi,
kafin Ya cire jallabiyar jikinshi Ya dauko mop ya gyara inda tai aman. Sai alokacin
ma yatuna baiyi sallan safeba bayi ya shiga yay wanka Ya dauro alwala yafito daure
da towel Ya xauna abakin gadon Eyeglasses din idonshi yaciro ya goge ruwan dake
jiki ya maida a idonshi yatashi yabude wardrobe Ya dauko kaya riga da wando yasa
Ya shimfida dadduma yay salla kafin ya kishigida bacci na neman daukarshi, da sauri
yatashi Ya zira takalmi yafito yay part din Mum. Zaune yasameta akan kujera tana
kallon CCTV kallo daya tamai ta dauke kai “ina Daughter na?” Ahankali Ya xauna kan
kujeran nesa da ita ” tana bacci adaki” takada kai kafin tace” idan ta tashi ka
kawomin ita xan kaita hospital ” ahankali ya gyada kai yana kallon ta,”am sorry
Mum, plz kiyakuri kinji baxan karaba” bata ko kalli inda yakeba yatashi ahankali
yajuya zai fita “jekasha coffee dinka yana dining ” dawowa yay yawuce dining ya
xauna yature kayan tea yakifa kanshi akan dining yama rasa mekemai dadi. Jin an
dafa kanshi yasa yadago Mum yagani tanamai murmurs hi da sauri ya rungumeta “am
sorry Mum, plz forgive me” shafa kanshi tayi “is ok,amma karka kara barin daughter
na tawahala ko kadan banaso” taja kujera ta zauna da kanta tahadamai coffee ta
dinga bashi yanasha. Sai bayan yagama sha ta shafa kanshi “yauwa tashi katafi wurin
Daughter idan ta tashi sai mukaita hospital akara dubata ko?” Yace to Mummy yamata
peck yafita yana Murna. Yana shiga dakin yaga Rufaida tsaye tarike kanta dake
sarawa sosai. Karasawa inda take yay yadafa wuyanta “my Baby kanki na ciwo”
afirgice Rufaida ta bude ido tareda ja baya tana kokarin kare jikinta da zanin
gadon .

Maman Abd Shakur😘

Maman Abd Shakur😘


[16/06 2:15 pm] Saudat: *KAINE SIRRI NA*

54
Da kyar tasamu ta tattaro zanin tarufe jikinta dashi, jikinta na bari. karaso wa
cikin dakin yay hanunshi cikin aljihu yazo gabanta Ya tsaya dab da ita yana
kallonta, shiru tayi kanta akasa tana shakar kamshin ruraren shi. Hanunta yakama
“muje kiyi wanka”. ahankali take binshi ba musu har suka shiga bayin yamaida kofa
yarufe, daddana shower yay yamaida shi na ruwan dumi, sanan yajuyo inda take tsaye
kanta akasa yay murmuahi ya tsugunna ya nannade jeans din kafarshi,ya mike ya
nannade hannayen rigarshi yazo dab da ita ya tsaya yana kallon zara zaran gashin
idonta, murmushi yadan saki aranshi yace”I must make u talk today,yau sainasa
kinmin magana,I wonder maisa take yawan kin min magana” gama zancen zucin yasa
yakai hanunshi zai kwance zanin da sauri ta rike zanin tareda dago kai ta kalleshi,
ganin ita yakema wani irin kallo yasa tasauke kanta da sauri ahankali yasa
hannunshi yacire hanunta yafara jan zanin gadon da sauri tarike hanunshi jikinta na
rawa”no plz” .

Ahankali yarada mata akunne “wanka zan miki babyna ” bai jira amsan dazata bashiba
yafizge zanin gadon, ta kwalla ihu,tareda taugunnawa a wurin “wayyo Allah mumyna”,
murmushi yay tsugunna a gabanta, yakai hannushi kan gashinta yana warware tufkan
dayay mata kafin yace”mummy na dakinta, is only you and your husband here my
darling angel” daidai lokacin ya gama warware tufkan ya bazar mata da gashi a baya
ya riqe hannunta yace”tashi muje inmiki wankan” ta maqe kafada “uhm uhm”,cikin
muryanta na shagwaba tace ” plz kadena, dan Allah” murmuahi jin dadi yay ganin
yafarasa tanamai magana. Ahankali yasa hannu ya dauke ta kaman yarinya tana
wuntsila kafa yakaita wurin wankan ya rufesu dawani irin glass kafin ya direta da
sauri tai kasa zata taugunna tana rurrufe jikinta tana kuka sosai “plz Uncle B
kafita, dan Allah” kai hannu yay zai kunna shower amma saiya fasa jintakira
sunanshi dabai tabaji takira ba, tsugunnawa yay yasa hannu yadagota tsaye da sauri
ta shige jikinshi tana kuka sosai, “shiiiii ba’a kuka ko magana abayi my luv” “plz
plz Uncle B kafita, kadena kallona plz plz plz am begging yhu dan Allah”. Duk tana
kan kirjinshi take maganar nan. Bayanta ya shafa yana murmushi “am ur husband
right, so say no more baby, time to take a hot shower ” hannu yasa ya kunna shower
dake zubo da ruwa mai dumi ajikinsu. Rufaida takara kankameshi tana kuka. Hannu ya
chusa cikin gashin kanta yana yatmusa mata,kafin yakai hanunshi ya danna wani dan
karami button saiga shower cream ya zubo ajikinsu. ahankali yake shafa bayanta
kafin yace” Rufaida ” ta dago kai ta kalleshi idanunta sunyi ja fuskarta ya shafa
kafin yasa hannu yarage gudun shower, ruwan na zuba akansu kadan kadan “fushi kike
saboda mijinki namiki wanka?” Girgizamai kai tayi batare data kalleshiba yajawota
kirjinshi ya rungumeta sosai tareda fadin”good girl” yakai hannu yakarama shower
gudu, sosai dumin ruwan ke ratsa jikkunansu,Rufaida najin wani iri gamedashi.
Yayinda Barraq keji kaman su dauwama ahaka.

Idanunshi a rufe nata arufe, yafara juyi da ita, ruwan na dukan ko ina nasu “I luv
yhu Rufaida ” takarayin lamo a kirjinshi batare data bashi amsaba.

Ahankali yakai bakinshi saitin kunnenta yakara matseta ajikinshi yana murmushi
kafin yace ” am soo happy dana sameki amatsayin mata” Ya sauke ijiyan zuciyan ruwan
na gangara akan fuskarshi ” kin tuna abinda yafaru jiya?”yasa hannu ya shafa kanta
yana murmushin tsokana ” unforgettable night, night din da matata kissed
me,remember?? ” .

Maman Abd Shakur AKA the professional love story writer tana mika gaisuwarta ga
masoyanta😘

: *KAINE SIRRI NA*

55
Da sauri ta fizge hanunta daga nashi tafita daga bayin tana kuka, sai yanzu take
tuna abunda yafaru jiya,towai mesa taihaka? Why?amma tarasa amsar dazata bama
kanta. Abunda zata rufe jikinta dashi tafara nema amma batagani ba, ganin wata
rigarshi akan gado yasa ta dauka da sauri tasa, ya tsaya mata iya guiwa tayi
hanyar kofa tana daura hanunta akan kofa yafito daga bayin, kokarin kiranta yake
amma da sauri tafita daga dakin da gudu tana kuka har part dinsu, Allah yasa babu
wanda yaganta ahaka tana shiga palo taga Mum zaune akan kujera da sauri tafada
jikin Mum tana kuka.

Biyo bayanta yay yaganta ajikin Mum, Mum ta kalleshi yay maza ya dauke kai,
ahankali tace”jeka shirya mutafi hospital ” saida yadan kalli Rufaida dayaga tawani
narke ajikin Mum tana kallonshi adan tsorace da hawaye a idonta kafin ya daga mata
gira da murmushi akan fuskarshi yajuya yafita.

Mum ta dagata suka shiga daki tabata kaya masu kyau tasa, tabata wani magani tasha
sanan suka fito yana zaune cikin mota yana kallonta ta madubin mota yanda dan
karamin bakin hijabin da jan gown din datasa yay mata kyau, kanta akasa tana tafiya
ahankali. Murmushi yadanyi kafin ya lumshe ido ina sonki Rufaida sosai ba kadan
ba.

Bude motar dayaji anyi yasa yabude ido ya kalli baya yaga Mum da Rufaida zaune.
Turo baki yay ya kalli Mum “nidai ba driver mata bane” Mum tadanyi Murmushi dan
tagane abunda yake nufi ta kalli Rufaida tace” Daughter koma gaba” ahankali Rufaida
tabude kofa tafita kanta akasa tabude nagaba ta shiga ta kullo tana watsa da
yatsunta.

Sai bayan yamayar da hankalinshi akan tukin dayake yace “Mum I will be going to
Nigeria tomorrow, 10:15am flight “da sauri Mum tace “4 wot son?,bakace min kagama
shari’oin dake gabankaba?” Mum i have to go,is urgent bazan dadeba I promise “kafin
Mum tai magana taji ya paka motar ganin harsun kawo asibitin yasa tabude kofa
tafita, ganin haka yasa Rufaida tabude kofa zata fita taji anrike hanunta,bata
juyoba dan tasan shine sumbatar hanunta yay kafin yasaki da sauri ganin Mum ta
ballamai harara dariya yayi yafito daga motar ya kulle kofa suka shiga cikin
asibitin atare.

Maman Abd Shakur.


[6/2, 17:47] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*

56
Likita ya dubata sosai, kafin ama Mum da Barraq bayanin babu wani ciwo dake tattare
da ita banda ciwon kan,aka rubuta musu maganin ciwon kan Barraq yaje pharmacy
yasiyo su kuma suka zauna a cikin mota jiranshi Rufaida na gaba Mum abaya tana
waya.

Fitowarshi daga pharmacy hanunshi dauke da ledar magani, yana cikin tafiyar shi
takasaita yaji ance “B “juyowa yay ganin wata class mate dinshi baturiya tun a
university tare suka karancin law yasa yay mamaki. Karasowa inda yake tai ta mika
mishi hannu tana Murmushi “is been long B” daidai lokacin Rufaida ta daga kanta ta
hangoshi tareda mace ta mikomai hannu,batasan maisaba amma taji kirjinta yabuga
dumm ganin yanda yake mata Murmushi hakoranshi awaje.

Barr ya mika mata hannu suka gaisa, tace da harshen turenci “yakake ,naga ka
chanza,ka kara kiba, looking good, handsome and fresh sama da da” Barr yadanyi
Murmushi “so har yanzu kinanan da surutunki Saira,anyway yanzu nai aure inada
family, and my wife always took good care of me saisa kikaga I looked fresh”.
“Congratulations, am happy for u,family is everything” Barr yadan girgiza kai yana
mata Murmushi kafin yace”kinzo dubiya ne? ” girgiza kai tayi hawaye ya ciko idonta”
I came for my check up, inada cancer, takarasa maganan tana kuka,I have only two
months B,nakusa mutuwa,haka Dr yafadamin” abunku da turawa tafada jikin Barraq tana
kuka bil hakki. Barraq ya shafa bayanta “is OK, ciwo baisa amutu sai lokaci yayi,be
strong saira kaman yanda nasanki da,fight d cancer kinji”, dagowa tayi daga
jikinshi tana share kwalla ta mugun bashi tausayi kafin ta mikamai hannu sukara
gausawa” thank you B,I appreciate,kaifa ya idonka?” “Yananan yanda yake, still
can’t see without my eyeglasses, nai magani harnagaji,na kalli abun kawai gado nai
tunda Dad dina nada partial blindness, Mum kuma bata iya ganin rubutu ,my own is d
worse bana iya gani without eyeglasses, so I just accept it,haka ubangijina yaso
ya ganni”.

Saira tai fuskan tausayi,”am sorry, take care B,bari natafi” suka gaisa kafin
tawuce tashiga motar ta yana daga mata hannu harta fita daga asibitin. Ahankali ya
juyo yana tafiya, abu na farko daya hango fuskar Rufaida ce ta cikin glass din
gabar mota tana kallonshi kuri da ido ko kyaftawa batayi,abunda yasan bata taba
yiba tunda yasanta ta kalleshi ido da ido, ahankali hawayen ya gangaro ya sauka
akan kuncinta, da sauri yakaraso ta window datake zaune, dukar da kanta tayi ta
dena kallonshi. Mum da sai alokacin tagama waya ta kalleshi tace “ka shigo mutafi
mana son” to yace a sanyaye ya zagayo yana kallon Rufaida dayaga hawaye na diga a
hanunta.

Maman Abd Shakur.


[6/2, 19:37] Aishat Muhammad: *kAINE SIRRI NA*

57
Mota ya shiga yana tukasu ahankali, rabin hankalinshi nakan tuki,rabi nakan Rufaida
daya lura kuka take dan hawaye nata diga akan hanunta dake kan cinyarta,yarasa
maiyay mata data mai wanan kallon,zullumi ya dingayi aranshi ahaka har suka kai
gida yay parking da sauri yaga tasa hannu zata bude kofa hakan yasa yarike hanunta
gam,taso ta fizge amma takasa Mum tai kaman bata gansuba tabude kofa ta fita daga
cikin motar tawuce ciki. Kaman jira Rufaida take takara rushewmai da kuka sosai,
Barraq ya jawota jikinshi zai rungume a tsiwace ta kwace jikinta “don’t touch
me”,yasaki baki da mugun mamaki yana kallonta dan bata taba mai ihu hakaba irin
nayau,ahankali yakai hanunshi zai rike mata hannu takara dauke hanunta tanajin wani
irin zafi a zuciyarta “dont touch me”, bai daddaraba yasa hannu yakama kafadar ta
“menayi baby na ?plz forgive me” idanunta sun rufe da kishi dawani irin zafin
zuciya cikin muryarta dabata iya fada ba mai sanyi tace “forgive yhu?kataba wata,
harda rungumeta kana cewa na yafema,kayi dan kabatamin raiko?” Ta kalleshi tana
kuka harda shesheka “den Congrats, saboda kabatamin rai, raina yabaci ” da sauri
tabude kofa tafita tana kuka tana share hawaye, Mum na saman bene jikin window ta
hango Rufaida tafito tana kuka sosai, Murmushi tayi kafin tasaki labulen ta zauna
tace “Alhamdulillah,Allah nagode ma daka nunamin Rufaida nason dana da gaske,
hartanama kishin shi,dama rana irin tayau nake jira nagani kafin nabashi
matarshi,dan ko kadan banason na shiga hakkin yar Amanar mu,amma yau na tabbatar
tanason mijinta”.

Barraq ya dafe kai,yana huci “mekayi Barraq? God nabatama matata rai,mezanyi yanzu
na gyara kuskuren dana tapka?” fitowa yay ya Kulle motar yawuce side dinshi.

Maman Abd Shakur.


[6/2, 21:43] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*

58
dakinshi ya shiga yafara gabatar da sallan magrib kafin ya dau waya yayi odan
flowers pink ya zauna shiru yana jira, duk yay wani iri.

Yana zaune aka bubbuga kofa ya bude ya karbi flowers din dashi kanshi suka birgeshi
ya ajiye kan kujera kafin ya shiga daki ya chanza kaya zuwa nashan iska yafito
yadau flowers yay part dinsu. Cikin sa’a yasamu babu kowa afalon haka yabashi daman
yin hanyar dakinta da sauri yabude kofa ya shiga.

Zaune yasameta kan gado bata kuka amma idanun sunyi ja ganinshi yasa ta tashi da
sauri zata shiga bayi ya riko hanunta tana kokarin fizgewa da karfin gaske ya
rungumeta “am so sorry Baby na, wlh bazan karaba,I promise kinji dan Allah” lamo
tayi ajikinshi tana sheshekara ta girgizamai kai yajata ya zaunar da ita akan gado
“plz karki kara fushi dani kaman nayau kinji?” Ta girgiza mai kai kanta akasa, ya
dauko flowers din yasamata akan cinya” for yhu my love” daukansu tayi tana kallo
tareda shafasu batasan lokacin da murmushi ya subuce mata abaki ba yay shiru yana
kallon yanda take shafa flowers din da hanunta.

Kama babbar yatsarta na hannu yayi kafin yace “my Baby” bata kalleshiba amma ta
tsayar da abunda takeyi “dama kina sona? “Batace komiba tacigaba wasa da yatsar ta
hannu yasa yadaga habarta duddua haka taki yarda su hada ido “so yhu love your
husband ” ture hanunshi tayi da gudu ta shiga bayi ta garkame da kwado tana
Murmushi dabatasan dalilin yinshiba ta kifa jikinta a kofar, tasowa yay shima ya
kifa jikinshi akofar murya chan kasa ya shafa kofan yay Murmushi yace “luv yhu too
wify,my shy-shy, fear -fear matas” yadan bugi kofan “luv yhu lyk crazy, kifito kiyi
salla kafin kiyi bacci” yajuya yabar dakin ranshi wasai,farinciki fal aciki.

Zai fita waje kenan yaji Mum takirashi ansawa yayi yawuce dakin Mum yasameta zaune
yaje ya zauna kusa da ita gani Mum. Ya daura kanshi akafadar Mum. Mum ta sauke
ijiyan zuciya kafin tace “kariga kayi booking flight din dakafadamin dazu ne?” Ya
girgiza kai “no Mummy, kawai nadai duba online ne naga available flights,amma ban
riga nayi booking ba, yanzu nakeso naje nayi” Mum ta sauke ajiyan zuciya jin bata
tafka kuskure ba Barraq ya kalleta Mum menene? Ta girgiza kai, “Son lokaci yayi
dazan mika maka matarka,tuntuni Dad dinka ke damuna nabaka ita amma ina yawan fada
mishi lokaci baiyiba, but yau na tabbatar lokaci yayi hakanne ma yasa nai muku
booking flight katafi da ita Nigeria,saboda kakoma bakin aikin ka”.

Barraq datunda tafara maganan yakejin wani dadi yace “Mum school dintafa?” “Ni
nafiso idan kukaje Nigeria zaka iya nema mata lesson teacher adingamata lesson
lokacin biyan jarabawa nayi abiyamata tayi jarabawar fita daga secondary saitaciga
ba da karatun” Barr yay shiru kawai yana kallon kakkyawar fuskar mahaifiyar shi,
tashi tayi ta dauko wasu keys dazasukai goma ahade ta dawo ta zauna tasakama Barraq
ahannu “wanan shine gift dina gareka son na auren dakayi,gida na ginama a maitama
estate, idan kukaje anan zaku sauka, nasama Rufaida komi dazata bukata
agidan ,lokaci yayi dazakuyi zaman miji da mata,plzz ka kularmin da yata, karka
wulakantamin ita,nabaka amanarta kaji” Barraq ya girgiza mata kai “I soo much love
you Mummy na ” ya rungumeta sun dade ahaka kafin yatafi bangarenshi.

Washe gari suka shirya Rufaida tasha kuka saboda doguwar hudubar da Mum tamata akan
zaman aure, ta bata wasu magani tasha. ita da kanta Takaisu airport saida jirginsu
yadaga tadawo cikeda kewan yaranta datafiso aduniya.

Karfe 9:30 nadare jirginsu ya sauka a Nigeria,driver da Mum ta aiko musu ya daukesu
dan kaisu gidansu a maitama,tuni Rufaida tai bacci kanta akan kafarshi. Wayarshi
tai ringing da sauri ya dauka gudun karya tashi Rufaida “yes mun shigo Muzammil ”
yay shiru kafin yace”take her to daddy’s warehouse, Baby tariga tai bacci danazo”
yadanyi shiru kafin yace “yes,ai bazan taba mantawaba,in fact chocolate dinma na
cikin jakata,ai wlh yanda matata taci ta wahala, itama saitaci,kawai dai saimun
hadu gobe ka gaida Madam” ya katse wayan.

To masu karatu inamai baku hakuri. Sai bayan salla zan cigaba da KAINE SIRRI
NA,azumi ya gabato.

Maman Abd Shakur😘

: *KAINE SIRRI NA*

59
Saida sukai parking akatafaren gidan sanan direban yafito yabude musu baya.
ahankali Barraq ya ciro keys din yamika mishi yawuce yaje yabude musu main kofar
flat dinsu, Barraq ya dauki Rufaida ahankali yafito yakaraso wurin tareda karban
keys din ahanun direban ya shiga ciki. gidan fes babu kura da alamun mum tasa an
gyara, duplex ne mai tsari mai kyau,ya yaba kyan gidan kafin yafara hawa
matattakalar benen dakin farko yafara shiga yaga tsarin yay mai kyau bismillah yayi
ya kwantar da ita kan gado ya tsugunna ya cire takalman kafar ta kafin yamanna mata
kiss a kananun yatsunta,ya tashi ya shiga bayi yay wanka yafito daure da towel
sauka yay yatafi kitchen din kasa bincike yafara yaga akwai komi naci gas ya kunna
yatafasa ruwan zafi, sanaan ya hada pancake da kyar, dukya kone ,haka yahadasu a
tray yadauka yatafi sama dasu ya ajiye akasa kafin yahau kan gadon yarike hanunta
ahanKali yake kiran Baby, shiru ko motsi batayiba,murmushi yadanyi kafin yakai
hanunshi kasan rigarta yana shafa cikinta ahankali yana kallon fuskarta turo baki
tayi cikin muryan bacci tace”mummy uhnnn” ahankali yadan tuntsure da dariya kafin
yasa hannu ya dagata ya zaunar, hakan yasa ta bude idonta ta kalleshi,yarr yaji
gabaki daya ya daure yarike hanunta “tashi kici abinci baby na” turomai baki tayi
tana sosa ido takoma zata kwanta, rikota yayi oya tashi muje kiyi wanka, zame
jikinta tayi ta tashi tsaye ahankali tana waige waigen dakin tashi yay yarike
hanunta yabude bayin yasata aciki “jekiyi ko kisano namiki ne ? ” Da sauri ta
girgizamai kai yay murmushi yaja hancinta yafita tarufor kofan da sauri kafin
tafara wankan tai brush tadau kayan jikinta tamaida sanan tabude kofa tafito yana
zaune yana shan coffee yabita da kallo kanta akasa tazo ta zauna kan kujeran data
gani gaban table ruwan gashin kanta na tsiyaya a bayanta duk rigarta tajike.

Kaman an tsikareshi yatashi yafita daga dakin ba’ajima ba ya shigo da jakunkunan


kayansu yadau nata yabata “baby na ki chanza kaya karki jike” ahankali ta tsugunna
ta bude jakar tadauko rigar baccin ta da abunda take bukata ta mike tsaye karaf
suka hada ido,sunkuyar dakai tai hanyar bayi,ta shiga ta chanza kayan tasashi
doguwace cotton ja ta wuce guiwa maidan kauri ce rigar tanada laushi sosai taimata
kyau, yakuma fito da surarta sosai, goge ruwan gashin kanta tayi tafito ahankali
yabita da kallo tamai kyau sosai dudda rigar is not dat sexy but yamai ahaka, zama
tayi kan kujeran ya kalleta yace”Baby na zokici abinci” tashi tayi tazo inda yake
nuna mata ta zauna tahada tea tafara sha kafin tadau pancake daya ta gutsura tanaci
ahankali ahankali yace “Baby na iya pancake?” Kallonshi tadanyi kafin ta dauke kai
da sauri batason ganinshi ahaka ba riga, shanye tea tayi ta dau tray din zata fita
ya karba ahanunta “jekiyi bacci” yafita dashi, kwanciya tayi akan gado taja bargo
ta lullube ahankali bacci yasoma dibanta.
Shigowa dakin yay bayan yagama dauraye kwanukan a kitchen yaganta akawance bacci
take hankalinta kwance, yaye bargon yay idanunshi suka sauka akan santala santalan
cinyoyinta da kyar yamaida bargon yarufe ta tareda kashe wutan dakin yahau gadon ya
kwanta,gabaki daya yaji yasoma rasa natsuwarshi, ahankali yafara shafata kaman
amafarki taji ana shafa cikinta, jin ana lashe bakinta yasa tazabura ta tashi zaune
jikinta na rawa sosai tana kuka tana kiran Mummy, da kyar Barraq ya mikar da
hanunshi Ya kunna bedside lamp ya kalli Rufaida dake kuka sosai yace “kwanta Baby
na “make kafada tayi tana kuka, da kyar yatashi zaune yana fuzar da iska idanunshi
sunyi ja sosai ahankali yace “yi bacci bazan karaba” da kyar ta yarda ta kwanta
tana dar dar ya lullubeta da bargo kafin yaja filo ya wurga akasa yafada kan filon
yana nishi da karfi yarike cikin shi.

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 52 to 59KAINE SIRRI NA 63$64 →
KAINE SIRRI NA 60 to 62
Posted on June 20, 2016 by mamanshakur
[6/15, 10:36] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*

60
Da sauri Rufaida ta sakko daga gado tana kuka sosai, tazo kusa dashi ta tsugunna
tana kallon yanda yake cije lebe muryarta na rawa tace “Uncle B menene? ” da kyar
yabude ido ya kalleta ya mata murmuahin dole yace “am fine baby, jekiyi bacci”kuka
tafashemai dashi tana girgizamai kai. Jawo hanunta yay ya kwantar da ita a gefenshi
yana share mata hawaye kafin yatashi da sauri yaje wurin jakarshi yabude yadau
kwalin taba da lighter yafita daga dakin, kasa ya sauka Ya zauna a falo yazaro kara
biyu yafara zukarsu atare da sauri har tari yake kaman mahaukaci Saida yasha kusan
5 sanan yaji daiddai yay bacci awurin.

Wuraren 5:00 na asuba yabude ido ganin Rufaida zaune agabanshi kanta akan kujeran
dayake kwance tana bacci hawaye a gefen idonta yasa yaji wani irin sonta da
tausayinta, hanunshi ya daura akanta ahankali yace”Allah yay miki albarka matata”
tashi zaune yay ya dauketa yakaita daki,ya shimfideta kafin yaje bayi brush da
alwala yafito Ya zira jallabiya,saida yakara dawowa gaban gadon ya kalleta ya
sumbaci goshinta kafin yafita zuwa masallaci.
Baidade dafita ba tatashi ta shiga bayi tai wanka tareda dauro alwala tazo tai
sallah. Bayan ta idar ta linke dadduman, tunawa da abinda Mum tafada mata yasa ta
dauko riga da sket daga akwatinta pink tasaka, rigar ta matseta ga wuyan rigar V
neck gareta hakanan tasa saboda duk sauran kayan English wears ne. hakama sket din
ya kamata. tana gamawa tai kwalliya ba sosai ba amma tai kyau barin gashin kanta
tayi abude. Ta gyara dakin koina. ganin 6:30 tayi ta sakko tana neman kitchen.
Shiga kitchen din tayi ta gyara kafin tafara dafa ruwan zafi ta juye a flask, ta
soya plantain da egg duk takai dining ta jera tadawo tai toasting bread tadai hada
komi ta kara gyara kitchen din. Da sauri takoma daki tabude akwati taciro turaren
wutar da Mum tabata ta kunna,ko ina yadau kamshi sai murmushi take tunawa datayi
yanzu fa tanada lada takoma daki ta tafesa turarukan da Mum tabata sanan ta dauko
Biology note dinta tafito tadawo kasa ta zauna akan doguear kujera tana karantawa.
dukta gaji da zama ita daya, kukan tsuntsaye kawai akeji,ba motsin kowa,tsoro ma
yacigaba da kamata. Wuraren 8 Ya shigo gidan da sallama kanta akasa ta amsamai,
yana karasowa cikin falon ta zamo daga kan kujera ta tsugunna tareda furta “ina
kwana “murmuahin jin dadi yay yakarasa gabanta, yasa hannunshi biyu ya dagota ya
rungumeta “Hey Baby na,kidena tsugunna wa inzaki gaidani” yakara matseta ajikinshi
yana jin dadin kamshi dake tashi ajikinta,”inasonki sosai” lamo tayi ajikinshi
murya chan kasa tace”namaka breakfast “cikeda murna ya dago da kanta yana
murmushi,komar da gashin dake neman sshigan mata ido yay gefe ahankali yadan rage
tsawo ya sumbaci goshinta da sauri ta lumshe ido “thank you Baby na,kayannan sun
karbeki” tadanyi murmushi jin dadi, yace”naje nai wanka kafin nazo naci?”
Yatambayeta yana kallon fuskarta kanta akasa tace “eh” kiss yamata agoshi kafin ya
zaunar da ita yatafi sama donyi wankar. Kusan minti talatin ya
dauka sanan ya sauko kasa sanye da suit baki,sai kamshi yake zubawa,ahankali ya
karaso gaban kujerar datake,ya mika mata farin hanunshi alamun ta tashi,kasa mika
mishi nata tayi ta kara dukar da kanta kasa, murmushi yadanyi kafin ya kama hanunta
ya dagata, sai wani noke kai take ahaka har sukakai dining sakin hanunta yay yaja
kujera ya zauna yana kallonta,saida tadan saci kallonshi da sauri ta dauke kai
ganin ita yake kallo,tadau plate tai serving dinshi ta hadamai tea a cup sai binta
da kallo yake yanda take komi a natse,bayan takai komi gabanshi tajuya harda
saurinta zatabar dining taji ya damko hanunta, ahankali ya janyota ya daurata akan
cinyarshi hakan yasa wani irin kunya yakamata ta kulle ido tana kokarin boye
fuskarta, fork ya dauka ya dauko plantain daya dashi yakai saitin bakinta “open ur
mouth ” kara juyar da kanta tayi tana kokarin tashi daga jikinshi, “open baby ” da
kyar ta juyo mai da kanta ta bude bakin ahankali ya sakamata ta gutsiri kadan taci,
yacinye saura yana karemta kallo yanda taki bude ido. Haka yaacigaba da bata har
suka cinye. Karan wayarshi dasukaji yasa yace “daukomin wayana,yana bedroom”
ahankali ta bude ido ta saukesu akan fuskarshi, ta mike zata tashi ya fizgota
takara fadowa jikinshi, da sauri ta tashi da gudu tahau bene ta shiga dakin tana
haki daukar wayar dake ringing akan gado tayi tajuya tasa hannu zata bude kofar
kenan ya shigo yana mata murmushi da sauri taja baya. Maman Abd
Shakur😘
[6/19, 09:38] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*

61
Tanaja baya yana binta harsukakai jikin bango ahankali yariketa yace “wana kama?”
Murya Chan ciki tace ” am thorry” hanunta yaja ya zauna abakin gado ya daurata akan
cinyarshi kafin yace “who called? “Mikamai wayar tayi ya karba ya duba muzammil
ne,yadafe kai yace “O,nama manta”,Ya kalleta “u see kinsa namanta da kowa” kokarin
kiran layin Muzammil yay yaji busy, dan tsaki yadanyi “who are u talking to again”…
bai gama maganan ba yaga kiran Muzammil ya shigo da sauri ya dauka “am sorry
mana,ganinan zuwa, just make sure u close her mouth, I’ll be there in a minute “.
Ya katse wayan tareda kallon Rufaida daya lura tunda yafara wayan take kallonshi.
sa hannu yay yadaga fuskarta tadan kalleshi “am going out,ki kula da kanki kinji
baby na, mezan siyo miki?” Gizgimai kai tayi, zaunar da ita agefen gado yayi
yatashi yadau wata yar jaka yarike kafin ya dawo wurin yamata kissa agoshi “I luv
yhu, bye”. Hawaye yacika idonta sosai, yajuya zai fita yaji tafashe da kuka da
sauri yajuyo “Baby menene kike kuka?” Kai ta girgiza mai “am scared, banason zama
nikadai,tsoro nakeji” masauki yamata a kirjinshi ya daura kanshi akan nata ya
lumshe ido, yana shafa bayanta “don’t worry,babu abunda zai kamaki,kinji . inkira
miki auta ta zauna dake kafin nadawo?” Da sauri ta dagamai kai, hannu yasa yashare
hawayen idonta “ok to dena kukan” zama yay akan gado ya daurata ajikinshi kafin ya
ciro wayar shi yabata “tayani dailing number Amma” saida tadan kalleshi kafin ta
karba ta nemo number daga contact dinshi tai dailing tabashi, kanta akasa karba yay
da hannu daya yakara a kunne cikin girmamawa ya gaida Amma yamata bayanin yanason
Auta tazo anjima zai dawo da ita, Amma tace to barita shirya direba yakawota,
Barraq yace to tareda mata godiya, kafin yakira direban gidansu yaymai kwatancen
gidan sanan ya ajiye wayan yana kallon Rufaida dayaga tana wasa da yatsunta. Kama
yatsun yayi yajuyo da ita yasa hannu ya daga kanta, dan murmushi tayi dimple dinta
suka lotsa, Barraq ya hada kanshi da nata “Rufaida!” Ta dago ido ta kalleshi “I luv
yhu sosai” lumshe ido tasakeyi,tareda sakin tattausan murmushin dake kashema Barraq
jiki. “Duk randa narasa ki,ranan na tabbatar zan rasa raina,zan shiga mawuyancin
hali, kona haukace ma,bansan mesa nake sonki ba, kawai all I know is I luv yhu
darling, u are special ” zamewa tayi daga jikinshi taruga da gudu zata shiga
bathroom dan wani irin kunyan magananshi takeji yarike hanunta,yakara jawota yahada
hannayensu akan cikinta ya lumshe ido, itama ta lumshe ido “ninasan danni aka yiki,
bantabajin son wataba sai ke my pretty angel,zamu gina soyayya mai karfi,na amana
da kauna, zaki haifamin plenty babies ko?” Fizge jikinta tayi tafada kan gado taja
bargo tarufe fuskarta tana murmushi ahankali, maganarshi kunya yake bata, Barraq
yazo kusa da ita akan gadon yakara bakinshi a kunenta yana murmushi yace “Inason
kunyarki,everything fits yhu,everything namiki kyau”daga kanta tayi ta chusa hannu
akunnen ta tana jujjuya kanta cikin yar karamar muryar ta tace “Uncle B plz
stop,kunya nakeji” jawota yay kan jikinshi yana murmushi,”to bari nakori kunyar”
ahankali yakai hannu kan zip din bayan rigarta ya zuge,yafara wassanni da ita na
fitan hankali. Ina ganin haka nafito daga dakin. Direba ne ya sauke Auta a haraban
gidansu,da gudu ta diro tun a tsakar gida take kwalamai kira “Uncle B,Uncle B, i
missed yhu”,falo ta shiga tafara waige waige tana kwallamai kira, tahau bene da
gudu tai sama da kyar Barr ya iya sakin Rufaida dakemai kuka tana kakkare
kirjinta,murmushi yay ya lashe lips dinta yace”get dress and come downstairs ga
auta hartazo” yamike yana gyaggyara suit din jikinshi sanan yafita daga daki, cin
karo yay da Auta tana waige waige wani ihu tayi ta dane jikinshi “Uncle B oyoyo”
shallata sama yayi yana murna,, sanan ya ijiyeta akasa da sauri tafara waige waige
“uncle ina Anty Rufaida baka tahomin da itaba? Amma fa tacemin tare kukazo”. ta
marairaice tanason tai kuka. Hanunta yakama suka fara sauka daga kan stairs yace”
gatanan zuwa,tana dan aiki ne ” chak auta ta tsaya ta kalleshi yace”wot again?” Ta
marairaice tace “nidai ka goyani nagaji da tafita akan bene”, Barraq ya rike
harbarshi yace”shows! Wai bakisan kin girma ba yanzu?”kuka tafaramai “wlh ni har
yanzu am Auta 11 and half nefa shekaruna, ni dai ka goyani, kaga kai kadaine yayana
ai kadinga jidani,hakama Anty rufaida zata dingamin”. Kada kai yayi ya tsugunna ta
dane bayanshi da gudu yatashi sanan suka karaso kasa ya sauketa duk suka zauna.
Kayan jikinta takarasa cirewa tadau wani pink fitted doguwan riga na cotton
yakamata sosai yafito da shape dinta,gyalenshi ta yane kanta dashi tadau turare
tafesa fuskarta ba kwalliya amma tai kyau, kayan sun mugun amsanta, ahankali tasa
hannu ta bude kofa tafito tana tafiyanta a natse mai daukar hankali. Kamshin daya
bugi hancin Barraq da Auta dake zaune suna hira yasa suka dago kai, Barraq mutuwar
zaune yay Auta ta tashi tsaye da sauri tana ware idanu tace “wow! Anty kinyi kyau”
daidai nan Rufaida takaraso kasa tasakarma Auta murmushi cikin muryarta mai Sanyi
tacema Auta “nibaza kimin oyoyo ba?” ta budema Auta hannu da gudu Auta tafada
jikinta ta rungume hartana neman fadar da Rufaida. Barraq dai yana zaune yana
murmushi,Rufaida takama hanun Auta suka zauna kan kujeran dake nesa da Barraq suna
hira,auta tace” Anty Amma tace nakawo miki wanan ” da gudu Auta ta dauko Jakarta
tabama Rufaida dambun naman kaza dayawa, Rufaida tai murmushi jin dadi takarba.
Barraq dai dayaga ko kallonshi basayi Auta sai dariya takesa Rufaida yasa yakoma
yadauko jakar da keys din motarshi yafito, Ya kallesu yace”natafi anjima kadan zan
dawo,Rufaida kanta nakasa dan mugun jin kunyar kallonshi take saboda yanda yay wasa
da jikinta dazu kanta nakasa tace “saika dawo,Allah kareka” Autama tamishi saiya
dawo. Ameen ya amsa musu yafita suka cigaba da hira,tana jin dadin yanda Auta
kebata labarai kala-kala.
Maman Abd Shakur😘
[6/19, 11:16] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*

62
Banban wajene katoto babu komi awurin sai goods dake cikin manya manyan kwalaye.
Nana nagani akan kujera tana sanye da kayan banzan data saba sawa an daure
kakafunta da hannayenta an rufe bakinta da salataf sai mutsu mutsu take alamun
tanason tai magana. Muzammil dake zaune kan kujera yataso yazo gabanta ya tumbuke
salataf din da karfi Nana tai ihu “auch Muzammil bazakamin ahankali ba,matsalan
mutum talaka fa kenan, shege boyi boyin Barraq,yaga saurayina maikudi jinin yan
Russia, wlh dazaran ya aureni zanrabaku.” Muzammil bai ce komiba illa cewa dayayi
“mekikeso kiketa mutsu mutsu?” Nana tamai wani fari da ido Tace” sonake ka Kwance
ni, natafi kafin B yazo,nai alkawari zan shayar dakai xuman dabaka tabashan
irinshi ba wlh”. Muzammil yay tsaki “yhu are damn crazy Nana,bana neman HIV, karki
damu lokacin danakeso yashige ni zan nemoki ki samin” zatai magana yadau salataf
zai manne bakin kenan Barraq ya shigo. bude ido Nana tayi tana kallon Barraq yanda
yay kyau yakara haske gashin kanshi yakara yawa da cika kaman wani balarabe.
rungume juna sukayi shida muzammil Nana ta runtse ido” B dan girman Allah ka
rungume ni, maisa nakeson haka B, wlh I will kill dat ur mumu wife,wanan yar
kauyen,shegiya mai kama mayu, B maizakayi da yarinya yar kauye dabazata wuce 16
years ba,gani jibenifa”,tadan jijjiha jikinta “me tafini? Wayewa? Hasken fata?
Ilimi ko diri”? Kaman zararriya tai ihu “I just can get it why did yhu hate me
Barraq? Bayan kasan dani kadai zaka iya more rayuwar aure?” Barraq baice mata
komiba saima cigaba da maganan da yakeyi da muzammil yayi. da karfi Nana tace
“Barraq! Yajuyo ya kalleta” wlh ,wlh inhar baka auran ba bazaka taba samun zaman
lpy da matarka ba, saina addabeku, saina kashe matarka, nakashe ka,sanan nakashe
kaina. I luv yhu alot”.

tafashe da kuka. Sai alokacin Barraq yay magana yace “u don’t luv me,wot u feel is
not luv Nana is Obsession! Idan kinasona bazakizo ki cutar daniba”. Nana taware
ido “wlh bazan taba cutar dakaiba in my life, I swear by Allah” Barraq yay
murmushi yabude yar jakan hanunshi yaciro chocolate din da Nana tabashi har Rufaida
taci rabi tabar sauran, tundaga lokacin yake preserving chocolate din afirij babu
abunda yayi saidan chabewa dayayi yace “mekikayi niyyan yimin da abunan?” Nana ta
zaro ido tana kame kame ya daka mata tsawa “mekikasa a chocolate dinan?” Tai shiru
batace komiba. “Matata taci abinan, she suffered, alkawari daya na daukarma kaina
duk Wanda ya wahalar da matata saina rama mata, nasa ankamoki ne only dannasaki
kema kici chocolate dinan,I want yhu to feel wot she felt alokacin”. Nana ta zaro
ido “plz karkai haka B,forgive me, karkaban, sonka ne yaja naihaka”. Barraq
yakarasa gabanta da sauri Nana tace “wait, inhar kamin haka wlh sainaje na dauko
kakar matarka daga kauye DUDUWA! kasan duk duniya babu wacce matarka ke tsoro kaman
DUDUWA, Barraq am warning yhu don’t mess with me,yhu have no idea wot am capable
of” . Barraq ya kalleta “waye baki information akan my family and everything about
me? Ya akayi kikasan DUDUWA? Yama akayi ranan kikasan zanje Russia? harkika saman
a airport, I know is not co incident, I don’t believe in co incident, tell me”
Nana tai murmushi tana kadamai idanu “I will only tell yhu if u spend a nyt with
me Barraq, just one nyt.

Idanun Barraq sukai ja,”stay away from me and my family Nana, nafada miki be very
careful. Karki tabamin Rufaida cuz I can do anything akan Rufaida, I mean
anything!” Nana tai ihu “stop calling her name, I hate her! wlh sainasa an farke
shegiyar” Barraq ya falla mata mugun mari saida bakinta yafashe, zai karamata wani
Muzammil ya rikeshi Ya girgizamai kai, Barraq yasa hannu ya matse bakinta Ya
chusa chocolate din ciki ya rike hancinta ba shiri Nana tahadiye tana ihu “wlh
saina kasheta, u will see” warwareta muzammil yayi yarufe bakinta da salataf ya
jefata a boot din motarshi yaja motar har kofar gidansu Nana, bakowa a anguwar, ya
bude boot yaga idanun nana sun chanza, rumgumeshi tayi da sauri ya hankadata ya
cizge salataf din bakinta,yabude gate ya wurgata cikin gidansu ya koma motar shi
yaja da sauri yabar kofar gidan.

Maman Abd Shakur.

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 60 to 62*KAINE SIRRI NA 65$66 →
KAINE SIRRI NA 63$64
Posted on June 26, 2016 by mamanshakur
[6/26, 11:19] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

63

Nana na hango mai gadi tafada kanshi tana jijjigashi,atorace mai gadi yace “hajiya
lpy? Wani laifin namiki yau? ” Nana ta girgiza kai “kodai Kai shiru muje daki kona
koreka daga aikin ka”. Da sauri mai gadi yatashi Nana tabi bayanshi tana tafiya
aduke, suna shiga tafada jikin mai gadi batare data damu da mugun warin dayake ba,
mai gadi yasamu abunda yake nema, yau zai dandana matar birni, hakanan suka fada
duniyar nikuma nafito daga dakin.
Muzzammil ya dafa kafadarshi “B karka bari maganan Nana ya tsayama arai,trust me
Nana bazata iyama komiba sai abunda Allah ya kaddara zai sameka”. ahankali Barraq
yace” hakane”Kafin ya Mike suka fito daga warehouse din suna hira kowanne ya shiga
motarshi suka tafi. Abakin wani babban super market ya tsaya yasai musu chocolate
dayawa different type, da icecream yabiya yafito ya shiga mota. Ganin ana kiran
sallan laasar yasa ya tsaya yay sallan sanan yatafi. Parking yay bayan ya gaisa
damai gadinsu ya wuce ciki. Hango Auta dayayi a dining sai nadan abinci take tana
hangoshi ta taho da gudu tanamai oyoyo yace”me kikeci haka?” Dariya tayi kafin tace
“Anty rufaida ce tamin cookies, saikuma tadafamin friedrice mai dadi ,Uncle B harda
kidney aciki wlh” tanamai magana Amma hankalinshi baya kanta kallon fallon yake bai
hango Rufaida ba, zaiyi magana kenan yaji sassanyar muryar Rufaida mai ratsa
jikinshi tace “Auta I need help with dis zip,kizo” da karfi Auta tace”to Anty”
tasaki uncle B zata tafi,da sauri uncle B ya riketa” ba abinci kikeci ba?”Auta ta
girgiza kai,”oya jeki cinye abincinki, I will help her with d zip” Auta tace to
batare da tunanin komiba takoma dining, shikuma yahau sama dakin yabude ya shiga
batare da yay sallama ya tsaya yana kallonta. batare data juyoba tace “thank
God,kinga nakasa zage zip din”murmushi yayi ya ajiye ledan agefen gado yakaraso
inda take tsaye yahada zip din zaija, bayanta ya kalla yaga har yanzu tabon dukan
nan basu gama bacewa ba,hawaye yacika idonshi, baisan lokacin dayakai hannu ya
shafa tabon ba,Rufaida taji sanyi “Auta ur hands are cold,by d way mekike tabamin
baya?kija zip din,and take ur hands off dere” ahankali Barraq ya chigaba da shafa
tabon yanamai jin tsanan kanshi daya bari akama Rufaida wanan dukan, Rufaida jin
Auta taki dena shafawa yasa hawaye ya ciko idonta ahankali tace “are u looking at d
bruises?,grandma dita Duduwa tasa aka zaneni” takarasa maganan muryarta na rawa,
ahankali taji an rungume ta sosai an matseta “I luv yhu Rufaida, ina sonki, namiki
alkawarin babu wanda zaisake miki wanan dukan, I promise” lumshe ido tayi jin
muryan mijinta sun dade ahaka kafin ya dagata ya zage mata zip din tajuya da gudu
zata fita yariko hanunta yana murmushi yana kallon riga da siket din jikinta mai
ruwan sky blue “kinyi kyau” Ta rufe fuskarta tana murmushi, yana rike da hanunta ya
dauko ledan chocolate din yasa mata ahannu “ga tsaraban ki”. Ya saketa ahankali
tace “thank yhu” tajuya zatabar dakin yace”Baby” tajuyo kanta akasa “am hungry, plz
serve me”kunya taji daya cemata plz komawa kasa tayi tahado mai abinci shi a tray
takawo mai ta ajiye, yanata kallonta ta zubamai a plate ta mikamai,karba yayi Amma
saida yahada da hanunta ya sumbaci hanun sanan ya saki ya dibi abinci yasa abaki
lumshe ido yayi kafin yace “hmmm” da sauri Rufaida ta kalleshi yace”delicious, good
cook baby na”dadi taji yanda ya yabi abincin,tashi tayi zata fita yace “ina zaki?”
Kallon yatsunta tayi kafin tace “sitting room, wajen Auta”. Yadade yana kallonta
kafin yace “ok, but just for today,duk randa nakecin abinci nanne wajen
zamanki”,yanuna Mata cinyar shi tafita da sauri,harta fita ta tuna da chocolate din
tadawo cikin dakin yabita da kallo,hannu tasa tarufe fuskarta tana murmushi tazo
kusa da Shi tadau chocolate din takoma baya da gudu ganin yanason kamota tafita
daga dakin,daga murya yayi yace”baby na yhu guys should get ready idan nagama ci
abinci zamu tafi”. Maman Abd Shakur.😘
[6/26, 13:42] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

64

Amma ba karamin murna tayiba ganin Rufaida sai wani ji da ita takeyi,hakama Dad
bayan yadawo yaga Rufaida yay murna yahadasu yay musu waazi sosai sanan yama
Rufaida kyautan kudi taki karba, chusa kanta tayi acinya tace daddy dan Allah ka
barshi. dad yaji dadi yakuma kara yaban natsuwan Rufaida Barraq yaba kudin yace
gashi ka iniyema daughter na abunta.
Duk suna zaune afalo suna kallo harda Dad, Amma, Auta, da B Rufaida taji mararta ya
murda, cize lebe tayi Barraq na lura da ita, tun 3 days ago takejin cramps Amma
bakon bai isoba. Ganin murdawan yasoma yawa yasa tafara girgiza kafanta ahankali
tanajin azaba, Barraq ya cigaba da kallonta cikin sa’a ta dago kanta suka hada ido,
da ido yamata tambayar “menene?” Langabe mai kai tayi hawaye ya ciko idonta da
sauri ya girgiza mata kai kafin ya tashi tsaye yadau carkeys dinshi yace “Dad, Amma
zamu tafi”, Dad da Amma suka rakosu har mota Amma tabama Rufaida abubuwa a leda
tareda cewa zan kiraki, Rufaida tai godiya ahankali ta shiga motar, Barraq yaja
suka fita daga gidan. chusa kanta tayi a cinya tafashe da kuka sosai. da sauri
Barraq ya paka motar agefen hanya yajawo ta jikinshi “Babyna menene,meke miki
ciwo?” Kuka takara kecewa dashi ahankali tace “I want to talk to Mummy”, yay juyin
duniya taki fadamai itadai da Mummy zatai magana hakanan yakira mum ringing biyu ta
dauka “Son ya kk?” Arude yace “Baby nata kuka wai zatai magana dake”, Mum tace
“bata” Rufaida ta karba jin yanda take Kuka yasa mum tace “menene?” Cikin kuka tace
“Mommy ciwo yakemin sosai”Mum tagane abinda take nufi tace “toba nace kidena kuka
ba,be strong zai dena daugther na, yaushe yafara” tace “dazunan” ok ba son wayan
tamika ma Barraq wayan, Mum tamai bayani tareda fadamai sunan maganin dazai siyan
mata murmushi yay yace to. ya kunna motan yaja a wani babban pharmacy yasiyo
maganin yadawo mota yasameta tarike cikin, sannu yamata yaja motar da gudu zuwa
gida, parking yayi ya fito ahankali tafito ganin tafiya na neman gagararta yasa ya
dauketa dakinshi sukaje yabata magani tasha da kyar. ahankali ta zamo daga gadon
tafita tatafi dakinta bai hanata ba, dakinta ta shiga tai wanka ta gyara
jikinta,duk dauriyarta takasa daure zafin ciwon mara tasaki kuka jin anbude kofa
yasa ta tashi da gudu tafada jikin Barraq tana kuka, shafa bayanta yay da hannu
daya yatura kofar suka shigo dakin yana shafa bayanta kiyi shiru zai dena ciwon
kinji ta dagamai kai, da kyar ranan tai bacci.
Kwanansu 4 ahaka, taji sauki Barraq dai da kyar yake daurewa dan yanda take kwana
ajikinshi na haddasamai bukatuwarta dayawa,da kyar yake daurewa yana azumi kullum.
Yau kwanansu 6 tunjiya tafara salla bata fadamai ba,Dan kunyan fadamai ma take.
sanye take da rigar bacci baby pink,Dan shara-shara ne,Dan tashinta daga bacci
kenan saboda kukan hadarin dataji alamun zaayi ruwa dan garinma yay duhu sosai,
wutan dakin ta kunna, ta zauna abakin gado,idanunta suka sauka kan ledan da Amma
tabata, da sauri ta dauko taga an rubuta yanda zatai amfani dasu aiko taci naci
tasha na sha saboda zaki. Tunawa da tun asuba da Uncle B yatasheta yatafi masallaci
bata kara ganinshiba, ahankali ta mike bari nafara wanka saina duba koya dawo,
wata zuciyar tace fara dubashi saiki dawo kiyi wankan. gama tunaninta keda wuya
tafita daga dakin gashinta duk abarbaje tayi hanyar dakinshi, ahankali ta tura
kofar dakinshi, dakin duhu ahankali tace”Uncle B kadawo? ” jin shiru yasa tafara
neman switch din kunna light tana Kunnawa ta hango Uncle B akan gado yana mutsu
mutsu,zaro ido tayi takarasa wurin gadon tana girgiza shi” uncle B, Uncle B “da
kyar yabude ido ya kalleta ahankali idanunshi suka sauka kan kirjinta saboda yanda
ta duko rigarta ya zazzago, lumshe ido yay ahankali tareda fadin “baby na why are
you here?yaushe kika tashi daga bacci?” Cikin kuka tace “Uncle B you are running
temprature, nakawoma paracetamol? ” girgiza mata kai yayi jeki kullo kofar sitting
room, ki kashe wutar nan kizo kiban magani”. Da sauri ta girgiza mai kai tana kuka
tafita da sauri. tausayi yaji tabashi sosai,yaso ace takara girma kafin yay rayuwar
auratayya da ita, amma matsalan dayake ciki bazai bariba, akalla yanada 36 -37
yanzu, shigowa dakin tayi takashe wutar kaman yanda yafadi mata tazo gabanshi ta
tsaya tace “Uncle B ina maganin na daukoma kasha?” hannu ya mika mata yace “zoki
kwanta zan fadamiki menene maganin anjima” ahankali ta laluba hanunshi tarike tana
kuka sosai “but uncle B u are running temprature, jikinka zafi,u are sick, dan
Allah kasha magani dan Allah plz” Da kyar ya janyota tafada kanshi ya kwantar da
ita gefenshi tana shesheka. Hannunta yakama yarike yace”is
ok,stop crying inba hakaba tsawanan da akeyi zai fado akanki” da sauri tai shiru
daidai lokacin aka fara ruwan sama mai karfi. Chusa hancinshi yayi acikin gashinta
yana shakan sassanyar kanshi da yakeyi. Murya chan kasa yace “Rufaida” ta
amsa da Naam. “Karkimin kuka kome kikaga inayi, banason tsawa yafado kanki dan
mutuwa akeyi kinji”da sauri ta girgizamai kai, fuskarta ya shafa yace”good gurl”
“karkuma kiji tsoro dan dazaran kinji tsoron POP dinan zai dare ruwa yadinga zuba
akanmu kinji” tasake girgiza mai kai. Ahankali yace” lastly kome zanyi karkiyi
magana, dan hakan zaisa tsawan yafado akanki,kuma zai cinyeki” da sauri ta
kankameshi tanamai jin tsoro dan duk iya tunaninta da gaske yake. Ahankali yakai
bakinshi saitin kunenta yace “I luv yhu soo very much baby na”. Hanunshi yakai
jikinta ya tumbuke yar rigar baccin dake jikinta yana mai wasa da kowani bangare na
jikinta. Rufaida ta zaro ido takasa magana,takasa kuka,ko kakkwaran motsi takasa
saboda tsoron tsawan dataji anayi tareda ruwan saman da ake tsugawa kaman zai fasa
gidan kasancewa watan ruwa ake watan agusta. Ahankali Barraq yace”good gurl,karfa
kiyi kuka ko magana kinji “tasake girgiza mai kai tana hadiye hawayen dake neman
zubo mata. Ihu tasaki da karfin
bala’i tana neman guduwa,da ceto saboda wani irin zafi dataji nabin jijiyoyinta har
zuwa kwakwalwarta amma Barraq bai saketaba. Maman
Abd Shakur😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 63$64KAINE SIRRI NA 67 TO 69 →
*KAINE SIRRI NA 65$66
Posted on July 10, 2016 by mamanshakur
[6/30, 09:37] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌
65

Ruwa ake tsugawa kaman zai fasa gidan,inda badan ruwan da akeba daba abunda zai
hana mai gadi jin ihun Rufaida, tun tana iya ihun tana tureshi hartazo bata iyawa
tai shiru tana sauke ajiyan zuciya.
Barr bai san inda yakeba saida ya gurjeta sosai,dan yiyake kaman yasami babbar mace
wacce tasaba,sanan yaji natsuwa ya shigeshi. ya tashi da sauri yanemi wuta ya kunna
yana kallon Rufaida, ya mugun tsorata ganin numfashinta nafita sama-sama, idanunta
akafe suna kallon gefe daya, dagata yay da sauri ya rungume ta yana jijjigata “Baby
na plz kiyakuri dan Allah” baimasan mezaiyi ba dukya rude tunanin maganan da
Muzzammil yataba fadamishi yafado ranshi, da sauri ya ijiyeta ya shiga bayi yahada
mata very hot water, kasancewar har lokacin ruwa bai tsayaba, garin da sanyi, yana
gama hadawa yafito ya dauketa ya shigo da ita bayin ya tsomata cikin ruwan zafin da
kyar ta sauke ajiyan zuciya, batare datai ihuba ta kaĺleshi, ahankali ya tsugunna
ya shafa gashinta” am very sorry my angel, dan Allah kiyakuri kinji”kuka tafashe
mai dashi sosai tana rerawa kamar karamar yarinya, ahaka yagama gasata ya mata
wankan tsarki ganin ko hanunta bata iya dayawa. Lullubeta yay a towel ya kaita
dakinta ya shimfideta akan gado ya shafa kanta” ina zuwa, bari nakawo miki abinci
kici” idanunta a lumshe yadau bargo ya lullubeta yafita dakin da sauri dakinshi
yakoma ya yaye zanin gadon ya shiga bayi ya jefashi a washing machine yay wanka a
gurguje kafin yafito ya zira jallabiya ya sauka kasa ya shiga kitchen yahada mata
tea mai kauri a cup, ya dauki paracetamol yafito. ahankali ya bude kofar dakinta
ya ajiye abincin akan stool, yakarasa jikin gado yana dubata yaga wani wahalallan
bacci yay gaba da ita, sauke ajiyan zuciya yay tareda zaunawa abakin gadon yana
shafa kanta, yayinda yake tariyo abunda ya gudana tsakaninshi da ita awanni dasuka
wuce ,ahankali ya saki yar murmushi yana kara kallon fuskarta ahankali ya furta
“thank yhu Baby na dakika kawomin budurcin ki, u made me happy today,na dandana
matata yau, yakara murmushi tareda kai yatsan shi kan karamin lips dinta “d
sweetest experience ever,Allah miki albarka Rufaida, ya rayamin ke, Allah ubangiji
ka barmu tare da matata,ka tsare min ita,I promise zan koya miki sona,I will teach
u everything my fear-fear baby” ganin karfe one tayi yasa yakara gyara mata lulluba
yafita zuwa dakinshi danyin sallan azahar. Ahankali take bude ido da
kyar ta iya mikewa ta zauna akan gado saboda zafin da zugi datakeji,gashi zazzabi
ya lullubeta,kuka take sosai tana tunanin me uncle B ya mata yau mai shegen zafi da
ciwo haka?Ahankali ta sauke kafafun ta akasa tareda kara gyara daurin towel din
jikinta,mikewa tsaye tayi da sauri tasaki ihu takoma ta zauna tana kuka. karan
bude kofan dataji yasa ta daga kanta ganin shine yasa ta dauke kai da sauri,
tacigaba da kuka. da sauri ya je gabanta ya tsugunna ” Baby na kin tashi?”bata
cemai komiba sai cigaba da matsan kwallan datake yi dudda Uncle B yakasance SHINE
SIRRIN TA amma yau ya zalunceta,batasan me abunba,ammadai yau yamata abu mai zafi
da wuyar fassarawa, ita kadai tasan azabar datasha. Rungumeta Barraq yay muryarshi
a raunane yace”O baby na plz forgive me kidena kukan nan wlh banaso kinji” fizge
jikinta tayi daga jikinshi ahankali tace “nidai ka maidani wurin Mommy bazan kara
kwana a gidanan ba tunda dai kai…”takasa karasa maganan tacigaba da goge kwalla.
Barraq yay shiru yanajin ciwon yanda take kuka dan har idonta sun kumbura “bazan
taba barinki kije ko inaba,bazaki kara barin inda nakeba, ina sonki sosai wlh dan
Allah kidena maganan zaki koma wurin Mum kinji I can’t take it,call me wat ever u
want inhar zaisa kihakura” Cikin muryarta mai sanyi ita ahakan masifa take ganin
tanayimai tace “to mekamin dazu? Kamin muganci ko? inacema kayakuri
kakiji,kanatamin zalinci,saboda kaga babu mommy ko?” takarasa maganan tana kuka.
Barraq yay shiru yana kallon zallan yarinta, amma akwai yaran shekara 16 dasukasan
kan komi na aure, ya akayi Rufaida bata saniba. Koda yake tunda na santa ban taba
ganinta da any friend kullum tana tareda Mum.
Bai bata amsa ba saidai riko hanunta dayayi yace “Ok-Ok am sorry, bazan karaba I
promise” fizge hanunta tayi takara mikewa tsaye ihu tasaki ta zauna tana kuka sosai
tana kiran Mummy tana yarfe hannu. lura dayayi bayi zata hakan yasa ya dauketa
tana kokarin fizge jikinta amma yariketa saida yakara mata wanka ya gasata sanan ta
dauro alwala suka fito taki kallonshi sai gimtse dariya yake. Haka suka wuni ranan
fada fada kuka kuka ga zazzabi sosai take taki shan magani, da kyar da daddare
bacci yay gaba da ita sanan ya lallabo ya shigo dakin dan koranshi tayi dazu.
Maman Abd Shakur😘

[7/9, 17:41] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


66
Shigowar shi kenan daga masallaci. sama yafara zuwa yaga har alokacin Rufaida na
bacci, ajiyan zuciya ya sauke kafin ya koma kasa, wuri yasamu nesa kadan da
thermostat dayasa gidan dumi saboda sanyi da garin yayi sakamakon wuni da akayi ana
ruwa jiya.
Rungume guiwowinshi yayi da hannu tareda chusa fuskarshi a tsakakannin guiwowin ya
fuzar da iska tareda lumshe ido “ya Allah ina rokonka kasa Rufaida karta tashi da
ringima, ko kuka yau, plz Allah ka taimakeni” da sauri yamike jin alamun motsi sama
yahau ya shiga dakin Rufaida a tsaye yaganta tana tafiya ahankali da kyar zata
shiga bayi murya chan ciki yace “baby na kintashi?”girgiza mai kai tayi batare da
ta kalleshi ba, tadan rage tsawo kadan tunawa datayi yahanata tsugunna mai tace
“ina kwana” dadi ya lullube mai zuciya yakaraso zai riketa da sauri ta shige bayi
ta rufo kofa yayinda shikuma yakama iska. knocking dayaji anayi yasa ya koma kasa
abincin dayay order aka kawo ya karba yabiya kudi ya kaimata abincin daki yaga bata
fito ba, zama yay abakin gadon yana duba wayarshi jin an bude kofar bayi yasa ya
ijiye wayan ya waiga Rufaida yaga tafito daure da towel tazo ta bude wardrobe tadau
kayan dazata sa takoma bayi aranshi yace uhm baby na ashedai da sauran aiki har
yanzu da sauran kunya. salla tayi sanan taci abincin da kyar takoma kan gado.
“Baby na wai menene?are yhu still angry with me ne? banyi komiba yau, kinki shan
magani, kuma kinki kulani is dat fair?so kike nai loosing mind dina?u want me to go
gaga right? for Allah’s sake nace kiyakuri,I just luv yhu Rufaida,kuma bansan iya
adadin son danake miki ba,dan Allah kiyakuri plz kidena fushi kin…” Da sauri
yatashi yafita daga dakin saboda yanda muryarshi tai rauni,tana rawa. Rufaida
tafashe da kuka itama sosai tana dukan filo,cike da yarinta tace “ni to menama?
Wurin Mummy na kawai nakeson na koma nothing else”,da karfi, da ihu, da kuka tace
“nidai wurin mummy zani, am tired of dis house,am sick of it”.
Barraq dake tsaye jikin kofar ya shanye da guntun hawayen dake neman zubomai ya
chusa hanunshi a aljihu yawuce dakinshi. Misalin karfe
11 na safiya yana zaune gaban laptop dinshi da copin cofee a gefe yana sipping
kadan kadan yaji ana knocking kofar downstairs jallabiyar shi ya dauka ya zira
tareda sakkowa kasa yaje ya bude kofa ganin Muzammil da Madam Hafsat yasa yasaki
murmushi . Muzzammil yace “abeg comot 4 road make my hajiya pass” Barraq yadan Saki
dariya kadan tareda kaima Muzzammil dukan wasa a kafada, daga bisani suka dunguma
suka shiga falon kowa yasami wurin zama fira ya barke tsakanin Muzammil da Barraq
ganin sun manta da ita yasa hafsat tace “Uncle B ina Rufaida?” Yadanyi jim nayan
sakanni kafin yace”tana upstairs”ahankali Hafsat tahau bene daki nabiyu ta bude da
sallamar ta. Barraq ya kalli muzzammil yadan
fuzar da iska ya mike tsaye “care 4 some cofee” Muzammil ya gyada mishi kai.
Kitchen ya shiga ya dafa musu cofee a teapot ya juyo a kofuna ya dauko yafito.
Muzammil yadanyi sipping cofee dinshi kafin yace”i know something is bothering yhu,
u can always count on me,mecece matsalar?” sassanyar kamshin turare ya daki
hancin Hafsat, kafin takai kallonta ga Rufaida datagani tai lamo akan gado ahankali
tace “Anty Rufaida ” Maman Abd Shakur😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← *KAINE SIRRI NA 65$66KAINE SIRRI NA 70 to 76 →
KAINE SIRRI NA 67 TO 69
Posted on July 12, 2016 by mamanshakur
[7/12, 08:10] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA *
67

Da sauri ta tashi ta rungume Hafsat tana mai tsanin farin ciki. Hafsat ta dagota da
sauri”Anty Rufaida jikin ki zafi sosai, baki da lafiya ne?” Ta girgiza kai “ni
wurin mummy zani, banason gidanan, plz kicema Uncle B ya maidani wurin Mummy kinji,
plzzzz” ta kifa kanta akan cinyar Hafsat ta saki kuka. Ahankali Hafsat ke shafa
bayanta “Rufaida ke matar aure ce,gidan mijinki shine gidanki, dakinki,rufin asirin
ki, da martabar ki, masu iya magana suna kiran aure da YAKIN MATA,dudda Mum mamarki
ce amma bazataji dadi taganki har kinzoba kwata kwata kwananki nawa da dawowa nan?
ai seta zata kunyi fada ne,ko wani abun ya faru ko…” Rufaida cikin kuka tace “ai
wani abunne yafaru, wlh uncle B mugu ne sosai Anty, ni gaskiya wurin Mum zan koma”
Hafsat data gane abunda Rufaida ke nufi saitai murmushi “Anty Rufaida auren kenan,
kowace wace undergo hakan,so is normal, zancema Uncle B asaki a islamiyyan da
Muzzammil yasani”. Rufaida ta girgiza kai”Banason islamiyya, idan naji ana karatu
kaina na ciwo bazan shigaba!. Ahakadai suka cigaba da hiran har daya tayi atare
suka shiga kitchen bayan Rufaida ta gaida Muzzamil.
Ahankali Muzzamil yace “B call Dr, ur Ajiya need a Dr kaga yanda take tafiya”.
Barraq yadan saci kallonta hanunta rike da spatula a kitchen, yadawo da kallonshi
ga Muzzamil a raunane yace”bazata yarda ba,fushi take dani,wlh I don’t know abunda
zanyi,ta hargitsa min tunani gabaki daya,but is not my fault I need her dat time
badly”. Muzzamil pat his shoulder ahankali yace”calm down,is normal fushin
datake,nasan yanda kakeji, just give her some time zata huce, karamar yarinya ce
kaine zaka koyamata komi” Barraq ya sauke ajiyan zuciya yace” to,ran Monday zanyi
resuming office “. Sai 7:00 na yamma sukabar gidan Barraq ya wuce
masallaci. Sai wuraren 9 ya shigo gidan sama yahau ya tura kofar dakin Rufaida
ganinta akwance yasa ya juya zai fita da siririyar muryarta takirashi “Uncle B”
juyowa yayi da sauri hannu ta mika mishi ya rike da sauri ya karaso ya zauna kusa
da ita “jikin ki zafi Baby na nakira Dr?” Ahankali ta dagamai kai,tai rau-rau da
ido “promise bazaimin allura ba” murmushi yayi yace”naji bazan bari amiki allura
ba”. Zamowa Tayi ta tsugunna agabanshi ta hada hannayeta biyu takai wurin bakin
ta “Uncle B plz forgive me, bazan Kara cewa ka kaini wurin Mummy ba, I was rude I
know, plz forgive me kaji”takarasa maganan tana kuka. Barraq ya girgiza mata kai ya
mika hannu ya dagota “is ok yawuce, bakimin komiba kinji baby na,we are good”.
Kwalalo ido tayi ta kalleshi wot?ya tambaya,”plz karka karamin abunan na jiya ,is
too painful, banaso plz” shiru yayi nayan sakanni yana tunani I was happy baby na
tai magana batare data sako any childish abuba, amma gashi tasako, alright lemme
answer yhu in a childish way too. Gyara gashin kanta yayi ya shafa kumatun ta”ok my
Rufaida, bazan karaba, but duk randa kikai rashin ji,ko kika batamin rai,hmmm ranan
sainayi ” da sauri ta kankame shi tana kukan shagwaba “Allah ni bazan ma rashin
jiba I promise”. knocking akayi yasa ya tashi “I guess d doctor is here” fita yayi
ya shigo da likitar. Yabasu wuri ta duba Rufaida magunguna ta rubuta musu tareda
mishi fada akan yanda yabita sanan ta musu sallama ta tafi.
Maman Abd Shakur😘
[7/12, 12:43] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*
68

Misalin karfe 2:00 na rana Barraq ya shigo gidan sanye da suit baki hanunshi dauke
da briefcase, yayinda PA ke biyedashi abaya suka shigo gidan PA ya zauna akan
kujera yana karema gidan kallo, Barraq yace “bari nakira madam ku gaisa” PA yace to
to. Barraq yay sama dan kiran Rufaida.

Dakinshi yafara shiga yay shower agurguje, ya sauya kaya zuwa na shan iska three
quater da white shimi kal yana mamakin me baby keyi dabata ji shigowan shiba.
Turare ya fesa kafin yafito ya shiga dakinta sassanyar kamshin dakinta ya bugi
hancinshi hangota dayayi akan gado tana bacci,ahankali tana sauke numfashi yasa yay
murmushi turo kofan yayi yakarasa gaban gado yay tsaye yana karamata kallo sanye
take da shimi yar karaama an mata zanen daisy ajiki pink,sai skin tight dogo fari,
gashinta tai katon kalaba dashi. hannayen ta yakama ya rike kinyi kyau my angel.
Yakara bakinshi akunnenta yace”wake up ga Mommy tazo” cikin bacci Rufaida taji ance
Mummy da sauri ta tashi tana waige waige Mummy taga Uncle B a gefenta “Uncle B ina
mummy na?” Shiru yay yana mamakin yanda Mum da Rufaida keson junansu. Dagata yayi
muje PA yazo ku gaisa. Bayi ta shiga ta daurayo fuska Ya mika mata hijabi tasa
tana turamai baki ya rike mata hannu yana dariya “naji naji anjima u will call
mummy kuyi magana sanan” tai tsalle suka sauka. gaisar da PA tayi takawo musu
abubuwan kwalama sanan takoma sama. Aranan da daddare Barraq yakaita shopping
yasaimata waya mai kyau Apple da kaya suka biya gida suka gaida Amma da Dad
Rufaida nata murna zatai waya da mummy.
Kimanin watan Barraq da Rufaida uku da sati biyu kenan da dawowar Su Abuja. Babu
abunda yakara shiga tsakanin su,Barraq yay hakuri yana koyamata wani irin sonshi da
shakuwan daya wuce misali dasukai kwanan nan. Rufaida tai kyau sosai,takara kiba
ta cika dam ga yawan zazzabin safe datakeyi ga bacci tarasa meke damunta.
Breakfast suka gama tana kusa da Barraq zaune take ta daura towel fari ajikinta
ajiye spoon din hanunshi yayi ya shafa kanta “baby na yau da wuri zan dawo na kaiki
hospital,banason wanan zazzabin dakikeyi every morning” ya debo kwai yakai bakinta
kawar da fuska tayi ta yamuse fuska “banaso” “O haba my baby mekikeso to nadafa
miki kafin na fita?” girgiza mai kai takara yi”zanci ragowan shawar mana najiya
“Barraq ya girgiza kai “idan zan dawo I will branch nasiyo miki more shawarma tunda
shikadai kikeso, plz don’t fall sick be strong kinji darling “ta gyada mai kai ya
mike tsaye yadau briefcase dinshi kafin ya tsugunna ya sumbaci goshinta “I luv yhu,
natafi” ya mike yay hanyar fita harya rike door handle Rufaida tace”uncle B “da
gudu ta tashi tafada jikinshi tana kuka sosai duk sai shima yarude “baby na
menene?”cikin kuka tace”am scared gabana faduwa yake since morning,bansan
mesaba,plz stay,something is going to happen ” ajiye briefcase din yayi akan kujera
ya kwanto da kanta kirjinshi yana shafa bayanta”Dear listen, nothing is going to
happen, akwai enough securities, ga mai gadi babu abunda zai kamaki”.
Maman Abd Shakur😘

[7/12, 12:58] Aishat Muhammad: 69- “Inada urgent case ne a supreme court yau daban
fitaba,kuma yau mutumin nan na Lagos da matar shi wanda yarsu tabata zasuzo
gaidamu, zan dawo da wuri, kije kiyi bacci kafin nadawo nakaiki hospital jikinki
yafara zafi”. Kama hanunta yay oya muje kisa kaya tana manne dashi sukaje daki
doguwar riga ya ciro mata ta karba ta shiga bayi tasa tafito yay murmushi baice
mata komiba, ya dauko mata shawarman taci agabanshi, yabata paracetamol, tasha
sanan yace ta kwanta ta shagwabe” a falo zan kwanta zan kalli series ne “Love is
timeless ” to muje yadau filo da blanket ya kwantar da ita ya lullubeta da blanket
ya kunna mata kallon sanan yamata kiss a goshi yadau briefcase dinshi yafita.
Murmushi tayi tace “luv u too” sanan ta gyara kwanciya tacigaba da kallon ba dadewa
bacci mai nauyin gaske yay gaba da ita.
Tic-tic-tic-gilin agogon garin Abuja ya nuna 11:00Am na safiya.
Zaune mai gadi yake yana jin sakon gaisuwan radio yaji anama gate bugun hauka, da
sauri ya tashi yabude dan karamin marfi ya hango wata yar tsohuwa,baka, zani daban
riga daban sai irin dankwalin da dinan ga wani uban goro a hanunta tana gutsura.
jin takara bugawa yasa yace “wonene? Cikin hausar shi mara kyau “Nice dan uwarka
wurin jikata nazo” mai gadi bai bude ba dan atunanin shi mahaukaciya ce. Securities
dake hanyar shiga part dinsu Barraq Su biyu da kakin sojoji ajikin su yaje wurinsu
yace “mahaukaciya kuzo ku koreta” daya daga security yabi bayan mai gadi bude gate
yayi tsohuwar ta shigo da sauri ciki security yace” Hj nan ne gidan Barrister
Barraq,nuna mana ID card dinki?” Tsohuwar tace” kaci ubanka menene kuma idi ked?”
ta balli goro kafin tace” ka matsa na shiga wurin yata”, Dadai security yaga kaman
ahaukaciyar ce yasa ya sassauta murya “Mama ba’a shiga gidan Barrister idan baka da
ID card,kokuma bakada appointment dashi for security purpose, mussamman gwamnati ta
nadamu, aikin mune kula dashi da iyalenshi,Babban Barrister ne a Abuja,saboda
tsaro, bamusan kiba dan Allah kiwuce kifita kafin mu koraki mama” tsohuwar ta zaro
ido “yanzu nida gidan jikata zaku koreni?,Ah lalle, ke duniya mekika zama??nazo
ganin jikata ne, kuma nan ne gidan nasani,shine zaku koreni??” ta tsugunna a wurin
ta fashe da kuka security ya tsugunna “mama kodai kin batane?” cikin kuka tace” wlh
nanne,nanne gidan” tadanyi shiru tana kokarin tuno yanda aka koya mata maganan da
zatama security tasake cewa” nine kakar Rufaida matar Barraq din,bakistan dakake
fada ai suruki nane, Duduwa ce fa,kakarta ce, koku bani hanya nawuce ciki konasa
Barraq ya koreku inya dawo wlh. Sainasa kun rasa aikin ku shegu masu kama da
samudawa,ga shegen girma, ga bakin fata, ga fuska ba rahama,Ga uban muni kaman
kacin wanda yasha zobo. Maman Abd Shakur 😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 67 TO 69KAINE SIRRI NA 77to87 →
KAINE SIRRI NA 70 to 76
Posted on July 14, 2016 by mamanshakur
[7/12, 18:21] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*
70

Ganin jikin sojan damai gadin yay sanyi jin maganar datayi yasa ta mike tsaye tana
kakkabe bayan zaninta” zaku nunamin dakin jikata ko saina sa Barraq ya koreku inya
dawo?” Da hannu security ya nuna mata part din ta wuce abinta.
Bude part din keda wuya Duduwa ta kwalalo ido “aljannar duniya,wanan daula wlh dole
kifita daga ciki Rufaida” katuwar tv bangon dake aiki ta kurama ido, ganin mutane
kaman zasu fito. kalle kalle tafara da tabe tabe, tunawa ana jiranta yasa ta fara
waige waige neman kofar uwar daka. tafiya tafara takaraso asalin tafkeken falon
ganin kaman mutum a chukuikuye cikin bargo akan kujera yasa ta yaye bargon
ahankali. ganin kamar fuskar Rufaida kaman kuma ba itaba yasa ta tottafa miyau a
hanunta ta malka a idanunta ta dirza kafin ta kara kallon fuskar Rufaida,tabbas
itace amma ya akayi mayyar nan tai kyau haka??tai kiba??ahankali ta kama hanunta ta
duba tafin hanunta, salati ta buga “Hasbunallahu! yanzu yarnan ciki gareki,cikin
shege Rufaida?” hannuwanta ta dunkule guda biyu iya karfinta ta sakinma Rufaida
dake bacci nushi aciki tus! Rufaida dake bacci tasaki ihun wahala ahh! Wayyo
cikina Mummy” ta tashi zaune ta rike cikinta tana kada kafa saboda azaba. Kaman a
mafarki taji muryar Duduwa tace”dan kan ubanki tashi ki tattara kayanki mutafi
kauye, tunda zaman karuwan ci kike, hakanan dan kija Allah yajefani a jahannama
kinzo kina zama da namiji har ciki yamiki” Rufaida da idanunta ke juyawa saboda
azaba ta kokarta takai dubanta ga kafan Duduwa ahaka har takai dubanta ga fuskarta
batasan lokacin data zube akasa jikinta na rawa tace”ina kwana Duduwa” Duduwa
tasaki shewa” lalle Rufaida, da namiji kike zama ko?” Rufaida ta girgiza kai duk
jikinta na rawa, ta fashe da kuka” wlh bada namiji nake zamaba, dan Allah Duduwa
kiyakuri karki daken bazan karaba ” Duduwa tai dariya “ai idan banci ubankiba, ba
sunana Duduwa diyar mai mandiri jikar mujittpa ba, sainai miki lilis sanan zaki
tattara kayanki mu koma kauye ” wiwi Rufaida tafashe da kuka cikinta da maranta na
wani irin juyawan azaba da ciwo. Duduwa ta cire gyalen jikinta taci
dammara dashi tanabin Rufaida tana ja baya tana kuka “dan Allah kiya kuri Duduwa,
dan girman Allah, wlh zan biki amma karki daken wlh banison duka plz”. Duduwa ta
kifa mata mari a fuska” yimin shiru kama bakin kidena min ihu kafin arnayen chan
suji su shigo” Rufaida ta rike bakin ta tana kuka sosai jijiyo yin kanta sun fito
radau, saboda kuka da tsoro zaka iya ganin yanda kirjinta ke bugawa da sauri fat-
fat-fat. “Waya miki ciki?” Duduwa ta tambaya a masifan ce. Rufaida ta zaro ido tana
kallon Duduwa bata gane maganar datake ba Duduwa tasa kafa ta take kafar Rufaida.
Rufaida ta fasa ihu ta rike baki Duduwa tace” oya yi magana waya miki ciki?” Cikin
kuka Rufaida tace “wlh wlh wlh Duduwa banda ciki, kalli cikina,baiyi girma ba”
hannu biyu Duduwa tasa ta ture Rufaida tafadi akan tiles tasaki karan wahala da
kuka, alokacin taji abu mai dumi nabin kafanta cikin karamar murya tace “dan
darajar Allah Duduwa kidena dukana, zan mutu wlh,banason duka,kiya kuri”. “oya
tashi ki hado kayanki mutafi” Duduwa ta fada tanamai tura kan Rufaida. Rufaida
takasa tashi. Duduwa ta daka mata tsawa “tashi nace! Da rarrafe Rufaida ta tashi
Duduwa na biye da ita tahau bene tafara tafiya jin kafafunta sun rike yasa ta
tsugunna tafara Jan jiki da kyar tanabin benen Duduwa na lura da jinin dakebin
jikinta taji dadi bazan taba bari ki haifama bature masu kudi yaroba. a tsiyace
zaki mutu shegiya yar tsuntuwa. ahaka sukakai daki Rufaida tadau akwati tafara
diban duk kayan da idanunta dake juyawa sukaga tana lodawa a akwati harya cika ta
rufe Duduwa tace “bazaki sauriba ko saina ballaki ki”. tafashe da kuka cikin
dashasshiyar muryar ta tace “dan Allah karki daken Duduwa” ahaka suka fito tanajan
jiki suka sauko kasa Duduwa tai gaba wurin kofa ta juyo taga Rufaida tsaye tana
kuka ahankali Rufaida tace “Duduwa indan kirashi nafada mai? ?wlh inbaki yardaba
nafasa ” maganar ta mugun batama Duduwa rai “ah lalle yarinya nikike fadama zaki
kira wanda yamiki cikin shegen nan” ta kama wuyar rigar rufaida ta jijjiga ta
Rufaida taji wasu abubuwa masu dumi sunabin kafarta, idanunta suka fara juyawa da
kyar tace “Duduwa zan mutu, ki dena dan Allah” daga hannun da Duduwa tayi zata
daki Rufaida taji an bude kofa. Maman
Abd Shakur 😘

[7/12, 22:53] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


71

Barraq ya tsaya chak yana kallon jinin daya gani a stairs,da Rufaida dake hannun
Duduwa tana numfashi kamar wacce taga mutuwa. Duduwa na ganin Barraq tsaf ta
ganeshi, jiki na rawa ta saki Rufaida. Rufaida tai baya zata fadi da sauri Barraq
yay gudu ya tareda tafado jikinshi,ya rungumeta kafin ya daura kanta akan cinyarshi
yana shafa kanta, yama kasa magana saboda yanda zuciyar shi ke mugun tafarfasa,
idanunshi da fuskarshi harma da kunnenshi sunyi bala’in ja,abunku da farin mutum.
dago kanshi yayi ya kalli Duduwa saida dan guntun fitsari ya zubo mata saboda
tsorata dashi datayi dan gani tayi idanunshi kaman jini,gabaki daya fuskarshi tai
ja juyawa Duduwa tayi zata fita tana neman kofar daya shigo da ita dakin bata
ankaraba taga kofunan da windunan falon sun kulle da kansu, Duduwa tajuyo a rude
tace” kabude min kofa, zan fita natafi kauye, kabude min nace”. bai ce kalaba ya
dauko wayarshi yakira wata number ahankali yace “I need ambulance” sanan ya katse
wayan ya ijiye. kan Rufaida ya shafa zuciyar shi na mugun kuna da tafasa, ahankali
ya kai hanunshi kasanta yaji har alokacin jini na zuba ,jijjiyoyin kanshi ne suka
kara tsattsowa ya matse Rufaida a jikinshi,cikin fushin yake kokarin tunanin meke
sata bleeding bayan yasan tana salla. “are yhu pregnant Rufaida? ?”tambayar ta fado
ranshi. Tunowa da news din daya kalla jiya ana hira da wata Dr hartake fadin
alamomin mace nata ciki yasa ya lula duniyar tunani. tun na farkon nan Rufaida bata
kara fashin salla ba,ga zazzabin safe, ga yawan bacci, ga selecting abinci,and
kirjinta were far too full kwanakin nan ahankali yace”u are pregnant with my own
baby Rufaida,my child” ganin yanda take bleeding yasa yace “and matar nan ta zubar
min da cikina,u killed my baby” ya kalli Duduwa” waya baki izinin tabamin matata
har kika kashemin da, waye? ?” Duduwa da takarasa sakin sauran fitsarin ta rike
labule gam da hannu, jikinta na rawa” yo uban wayace ka sacemin jika,ka tambayi
izinina kafin ka tafi da itane? bazan taba bari ta haifi shege ba, saisa na daki
cikinta da hannayena biyun nan, dan ta mutu cikin ma ya mutu” Barraq jikinshi
yafara rawa ya kwantar da Rufaida akasa “kece zaki mutu yanzu ba matata ba” taku
biyu ya kaishi gaban Duduwa wacce ta daga murya ta tsala ihu tana neman taimako
“wayyo Allah, zai kasheni, ayi taimako zai kashe kakar matarshi” Barraq ya daga
hannu zai wanketa da mari kenan yaji muryan Dad yace “Barraq! Chak ya tsayar da
hannun batare daya kai fuskar Duduwa data make a labule ba, kuma bai sauke
hanunba,Amma tai sauri takarasa inda Rufaida ke kwance tafashe da kuka “Wlh hukuma
ce zata rabamu dake”. Dad
yakarasa wurin ya kama kafadar Barraq ya matsa da karfi “dan ranka yabaci bazaisa
kai abunda bai kamata ba,idan rai yabaci hankali karya gushe! maizaka daka a jikin
tsohuwar nan da akalla tai clocking 80 years?wot will yhu archive?and kakar matar
ka for dat matter!,Kul!Ahir gareka ya Barraq karka fara kadaga hannu wataran kace
zaka daki wacce ta isa ta haifeka, koma wanda ya girmeka,ba tarbiya bace, dan haka
za’ama iyayenka kaima wataran, no matter wot she did ka barta da halinta, duniya
nada fadi and Allah subhanahu wata ala never sleep. Yana ganin komi”. Sakin kafadar
Barraq yay Ya kalli Duduwa yace “Mama tafi abunki” Barraq ya kalli Dad afusace “wot
are saying Dad?dis woman killed my unborn child Dad,my Baby!she have to pay for her
crime Dad”. John! Joseph! Yakirasu dawani irin muryar zaki, suka shigo dakin da
sauri ta kofar kitchen, ya nuna musu Duduwa” lock her up! Da sauri sukazo zasu kama
Duduwa Dad hana”let her go” alokacin Amma tasa baki tace “akulle ta, koma wacece
she must pay for her crime, ku tafi da ita ku kulle ta cus wot she did is
unforgivable “. Dad baice komiba saidai taku biyu dayayi yakaishi gaban Duduwa ya
mika hannu ya riketa, Duduwa data mugun rudewa bata tabajin tsoro irin nayau ba
arayuwar ta, tabishi luuu ya kai ta har kofar gida sanan yaciro dubu goma ya bata
yay murmushi manya yace “mungode hajiya,kome kikama Rufaida kin isane saisai, Allah
kaiki lpy” Jikin Duduwa yay sanyi ta karbi kudin tajuya tana tafiya ahankali tana
waigen Alh( Dad). Tare da motar
ambulance Dad ya shigo, Barraq na tsaye inda Dad ya barshi zuciyar shi tai baki,
ahankali Amma ke maimaita mai kalmar La ilaha illallah. Daukar Rufaida akayi
akasata akan wata yar gado aka samata oxygen a hanci sanan aka gungurata aka fitar,
Barraq dayaki kallon Dad saboda fushin dayake ya kalli Amma yace “Amma zanyi baki
daga Lagos any minute from now,Dan Allah ki tsaya idan sun iso entertain them,if
they insist zasu ganni ki kawosu hospital”. Amma tamika mishi tissue ganin hawaye
nabin idonshi. Tace “take it easy Barraq komi zai dawo normal I promise” bai ce
komiba yajuya yafita da sauri ya shiga motar ambulance din ya rike hanun Rufaida
gam hawaye na sintiri a kumatun shi masu zafi. aka wangale gate suka fita,dad ya
shiga motarshi ya bisu abaya akabar Amma kadai a gidan. Ko minti
15 ba ayi da fitar motar ambulance dinba wata hadaddiyar Benz baka har walkiya take
ta shigo gidan. Magidancin Alhaji ya fito dauke da yaro tareda matarshi data zagaya
ta bude baya ta ciro stroller sanan ta karbi kakkyawan yaron ta saka cikin
stroller. Ta kalli mijinta tace”Ragadada maigida nakaina” yace”naam Ragadada uwar
gida takaina” wlh naji wani iri dana taka kasar gidanan why??”. Maman
Abd Shakur😘

[7/13, 08:50] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


72

Dad na shiga gida wata arniyar bakar mota ta paka a gaban Duduwa a guje, da sauri
Duduwa taja baya tana haki tazaci Barraq ne yazo harbeta. aka bude mata kofa ta
shiga da kyar ta zauna ta jawo kofar ta rufe. cikin bacin rai ta cikin motar tace
“ina Rufaida?Ya aka kare? Naga shigan motar Barraq, sanan naga shigar motar
gidansu kaman ta Dad dinshi maiya faru??” Duduwa ta gyara zama “nai miki aikin
dayafi na komar da Rufaida kauye, ciki gareta kuma saida na zubar da cikin”. “Wot!
ciki??Har Barraq yama yarinyar nan ciki?Maiya gani ajikinta? Maitake dashi?? Yanzu
ya aka kare??” Duduwa ta gytsuri goro “Barraq yakusa kasheni dayaga jini na zuba
daga jikin matarzhi, amma babanshi ne ya taimaken, dan abunda namata hala ita kanta
Rufaida bazata rayuba, mutuwar ta nakeso dan ita takashemin yara”. Nana ta sauke
ajiyar zuciya da tattausan murmushi” good tsohuwa,kinyi kokari” Nana ta kunna motar
tace “muje nabiyaki, gobe PA zai maidake kauye”. Suna cikin tafiya amota DUduwa ta
kalli Nana nayan sakanni kafin tace “ke ciki gareki,kuma danyen ciki” Nana tai wani
irin take burki akan hanya Duduwa tafasa ihu” wlh ban shirya mutuwa ba”. Nana
tace”nikeda ciki??To saidai inko a ruwa nasha, Alhaji na tun wata hudu dasuka wuce
yatafi US ban kara hada jikina da wani ba,ke bamani da ciki”. Duduwa tai shewa”
hala kam dai a ruwan kikasha dan ciki gareki yarinya”. Nana ta gangara motar zuwa
gefen hanya hankalinta atashe” towa yamin ciki??kodai danaje club aka ban maganin
bacci nasha akamin??” Chan wani bangaren zuciyarta yace”sama’ila mai gadi! Shikadai
nai tarayya dashi,randa Barraq yaban chocolate dinan. Ihu tayi wayyo Allah na!wlh
bazan taba daukan cikin mai gadi ba Allah kyauta” tacigaba da sumbatu Duduwa na cin
goro tana kallonta. A
Bangaren su Alhaji Amma ta wadata su da abun ciye ciye sunci suka kumayi addu’a
Allah ya tsayar da cikin. Suka karbi address din asibitin sukace gobe da yamma
zasuje su gaida Barraq da mara lafiyan sanan suka tafi. Amma sai kallon karamin
yaron hanunsu take yanda fuskarshi tai mugun kama dana Rufaida Allah mai iko da iya
sarrafa hallita daban-daban,kala-kala.
Har karfe 9:00pm likito ci basu fito ba,Barraq na zaune nesa da Dad da Amma wace
bata dade da zuwa ba,Dad yay yunkurin magana da Barraq amma dazaran yazo Barraq
saiya tashi yabar wurin. ahankali Dad yace”kadade bakai irin fushinan ba Barraq!
mutum daya ne zai iya kwantar ma da hankali. Yajuya yafita daga haraban asibitin.
Sai wuraren 10:30 likita yafito Barraq ya tashi likita yace “Barrister muje office”
Barraq yabi bayanshi kirjinshi na bugawa, Dad da Amma ma haka likita ya zauna ya
nunama Barraq wuri ya zauna, ya girgiza kai Dad ya zauna da Amma Barraq ya tsaya
yana kallon Dr da rinannun idanunshi. Dr ya gyara zama” sakamakon dukan da akama
matarka a ciki,da kuma tsorata datayi wanda kowa yasani tsoro in not good for a
pregnant woman munyi mata hotuna a ciki da…” Barraq ya dafe kanshi “let’s skip d
talk and cut to the chase,menene condition din matata yanzu??” Dr yadanyi shiru
kafin yace”we tried our possible best muyi saving baby ka hakan ya gagara,am sorry
Barrister Barraq cikin matar ka ya zube! Barraq ya kalli Dr da rinannun idanunshi
kafin ya rike kujera ya tsugunna ganin zai fadi. Dad ya taso ya bubbuga bayanshi
“is ok son,kaya kuri,ka dauki ranannan a matsayin jarabawa” Barraq yakai kusan
minti 5 ahaka kafin ya janye hanun Dad daga kafadarshi ya tashi ya kalli Dr
ahankali yace “can I see her” Dr yace “of course u can” yajuya da kyar yafita daga
Dakin Dad zai bishi Amma ta rikeshi “Alhaji barshi Barraq needs to be alone now” Dr
ya karbe da hakane ku barshi ya duba matarshi. Barraq ya shiga
dakin ya maida kofar ya rufe ahankali yakarasa gaban gadon da Rufaida take, ya
tsaya yana kallonta tai haske sosai tana numfashi kadan kadan, jan kujera yayi ya
zauna ahankali ya daura hanunshi kan cikinta, muryarshi ta dishe,takuma yi rauni,
ya runtse idonshi gam yana shafa cikin da hannu, hawaye nabin kumatun shi “we lost
our baby my Rufaida,we lost our Baby”. Ganin yakasa controlling hawayen yasa ya
nemi hanunta ya rike gam ya sumbace su”get well soon My Rufaida,I luv yhu soo very
much”. Sakin hanunta yayi ya kifa kanshi akan gadon yarasa mekemai dadi.
Jin anshafa mai kai yasa ya dago kanshi ganin Mummy shi idanunta sunyi jaa yasa ya
rungumeta da sauri kukan dabaisan daga ina yazoba yasake shi da karfi,Mum ta shafa
bayanshi “is ok son,be strong “ahankali ta zaunar dashi kan kujera ta rike kumatun
shi da hannayeta ta share mai hawaye,ta sumbaci goshin shi. Gilashin idonshi
ta zaro ta chusa hannu a Jakarta ta ciro clean tissue ta share hawayen jiki sanan
ta maida mai idonshi. “How did yhu get here Mum?”ya tambaya ahankali Nuna mai
agogo tayi yaga karfe 2:30 na dare,” is a long story son, we will talk about that
tomorrow. Just sleep,get some rest, cuz u need its”. zaiyi magana tace”shii”ta
zauna akan gado ta daura kanshi akan cinyarta ta, Barraq ya rike hanunta daya gam
yana sauke ajiyan zuciya, yayinda ta daura dayan hannunta akaan Rufaida tana shafa
gashinta kadan kadan. Maman Abd Shakur😘

[7/14, 10:55] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


73

Da asuba yafita yay salla a masallacin dake wajen private asibitin. bayan ya dawo
ya tarar da Mum zaune kan dadduma ta idar danata sallan. Ya gaidata ta amsa kafin
ya duka ya sumbaci goshin Rufaida ahankali yace “morning Baby na” bude kofa akayi
aka shigo Dr ne dawayan su nurses suka bukaci abasu wuri suduba Rufaida atare Mum
da Barraq suka fita. Fitar su keda wuya suka tarar da Dad awajen wurin ciki ciki
Barraq ya gaidashi “morning Dad” bai jira amsar shiba ya bar wurin da sauri. Dan
Restaurant dake wajen asibitin ya shiga ya zauna waitress tazo ta tabambaye shi
maiyake so,da kyar yace”coffee” yana zaune yana jiran coffee dabaima jin zai iya
shaba yaga Mum da Dad sun shigo wajenshi sukazo sukaja kujeru biyu suka zauna. da
sauri Barraq ya tashi zaibar wajen Mum tai magana “koma ka zauna” yakoma ya zauna
“Saboda Baban ka yahana ka kadaki tsohuwar dat is old enough ta haifeni shine kake
fushi dashi?Haba son haka na tarbiyan tar dakai?” Barraq ya girgiza kai “am not
angry Mum,Bana fushi,kawai abun yamin ciwo ne yanda Daddy yabar matar data kashemin
da walkout from my house free,yamin ciwo sosai,I want justice to be serve,I wanted
to interrogate her,yanda zansan wanda ya nuna mata gidana,cus dat old woman bazata
iya kawo kanta Abuja ba,someone must be behind all dis,someone dat hate me and
Rufaida,koma wanene I want dem to pay,I want dem to pay Dad,banason Rufaida to face
any more problem in her life,she is under my custody” ya karasa maganan muryarshi
na rawa sosai, Dad ya daura hanunshi akan na Barraq “komi ya wuce son, babu wanda
ya isa ya cutar dakai ko amfanar dakai a duniyanan sai ubangijin ka yaso yakuma
basu iko, dat is d fact! Komi ya faru ne saboda tun fil azal Allah ya kaddara
hakan,ina tare da Amma securities dinka suka kirani wai sunata kiran number ka
akashe I have to come something is wrong, sunji kukan Rufaida,na tambaye su tana
tareda wanine sukace min eh kakarta tazo. inajin haka namike tsaye arude nakashe
wayan nadau car keys Amma tabi bayana muna zuwa mukaga kofa a kulle shine mukabi ta
kofar baya ta kitchen. Naga kana shirin dukanta which is wrong,Barraq learn to
forgive and forget kome tayi itada Allah yawuce,nakifa jin zafin abunda tama yata,
nafika son jikana data kashe,amma Allah daya bamu shizai sake bamu wani” Ya shafa
kumatun Barraq” ka manta da zancen tsohuwar nan and be happy my son, Allah zai bani
wani jikan very soon” Mum tace “Ameen” yayinda Barraq yace”I luv yhu Dad”,Dad
yace”luv u too son,Allah maka albarka”. Tare sukasha coffee sai labari dad da Mum
ke bashi naban dariya saboda yadan sake hakan yafaru yadan sake kadan suka tashi
suka koma cikin asibiti. Karfe
4:10 na yamma Dad da Mum da Amma ne adakin Rufaida, Suna hira sama sama,Dr yace
musu jikin da sauki halama ta farka yau. yayinda Barraq yafita haraban asibitin
shigo da bakinshi na legas dan sun dan bata. Shigowa asibitin sukayi sukai parking
a inda aka tanada na parking, Barraq yakara so wajen da waya a hanunshi yana
murmushi anatse. fitowa sukayi daga motar,Barraq ya karbi karamin yaron daga hannun
matar yana murmushi “Umma ina yini” ta amsa a fara’ance, ya juya ya mikama Alh
hannu suka gaisa “Barrister yamai jiki?hope taji sauki”. “Alhamdulillah sir taji
sauki, unfortunately we lost d baby” Alh da Umma suka nuna damuwar su sukaima
addu’a “Allah kawo rayayye,Allah sa mai ceton kune ” Barraq yay M urmushin dayafi
kuka ciwo ya rike hanun karamin baby dake tsalle a jikinshi yana kokarin ciremai
gilashin idonshi yace”Ameen Nagode” sai kallon yaron hanunshi yake yaga kamar yaron
dana Rufaida ya baci. Amma ta bude bayan motar ta dauko wata katuwar ledar shopping
din da Alh yamusu tabisu abaya.
Barraq yasa hannu ya bude kofar dakin da Rufaida ke kwance “Bismillah sir” ya shiga
ciki dauke da yaron, Alh da Hj na biye dashi Barraq yace”Mum, Dad meet my client d
one I told yhu about, wanda yarshi tabace almost 2years a…” Karrraras! karan
zubewar abu wanda har saida yaron hanun Barraq ya firgita yasa Barraq kasa karasa
maganar shi ya juyo da sauri yaga Alh da Umma suna kallon Rufaida, yayinda Umma ta
daga hannu ta dake rawa ta nuna Rufaida tace”Ru..r..Ru…fai. ..”bata karasa kiran
sunan ba tai baya luuu zata fadi.
Maman Abd Shakur😘

[7/14, 21:07] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


74

Alh ya rike mata hannu da sauri, Dad yatashi daga kan sofan dayake Alh ya daurata
akai, kowa ya mike tsaye,Amma ta dauko goran Eva water mai sanyi ta mikama Alh ya
bude yaba Umma tasha kadan tana Nuna Rufaida da hannu. Barraq dake dauke da yaron
su a hannu ya juya dan ganin abunda Umma ke nunawa ganin Rufaida yasa ya dawo da
kallonshi garesu a natse yace”Umma itace matata Rufaida,mesa kike nunata?” Alh ya
mike tsaye ya share dan guntun hawayen idonshi”itace Rufaida dana fadama case dinmu
akanta,wlh yarmu ce! Rufaida yar muce! Dad, Barraq,Amma da Mum suka hada baki
alokaci daya sukace “what?! Umma ta daga kai cikin kuka ta kallesu tace “wlh yarmu
ce,Rufaida baby na,i missed u” ta tashi zataje wurin gadon Barraq ya tsaya agaban
ta “don’t touch my wife Ma,imma turoku akayi kutafi,inma set up ne to it won’t
work,cuz Rufaida iyayen ta sun mutu, a minna parents dinta suke aiki amma asalin su
yan kauyen gujungun ne na jahar jigawa, gini yafado ma iyayen ta ,nida kaina naje
na karbo kudin da Gov. Sukaba duk family da ginin yafado musu,so yhu guys should
cut d drama,I respect yhu alot Alh,ku barmin matata tahuta,why soo much hate??kowa
yatashi Rufaida, everything Rufaida, wani laifi yar yarinyar nan tayi dat deserves
all dis wahala?? Yhu guys should get out of dis hospital before I call security”.
Ya mikama Alh yaron. Umma ta tsugunna tafashe da kuka sosai Alh yace”wlh wlh Barraq
yarmu ce,itace Rufaida damuke ta nema”. Barraq cikin daga murna yace”I know is all
a setup,idan itace Rufaida ku maisa baka taba nunamin hoton taba duk zuwana
gidanku? “Alh yay shiru yakasa magana ga yarshi amma ana karyata shi, da kyar ya
tattaro karfinshi yace”dan girman Allah ka yarda damu Barraq, wlh yarmu ce,ban taba
tunanin nunama hoton taba but look inada hoton Rufaida a cellphone dina” Barraq
yace” I don’t want to see, just get out of dis hospital now” Idanun Barraq yay ja
dan duk atunanin shi wata kullalliyar aka kullo. Umma takara fashewa da kuka takama
kafar Mum tace”Hajiya wlh yarmu ce,Rufaida nace, kice yabar mu muganta”. Mum ta
girgiza kai “Hajiya batar fuska kikayi,Rufaida nan iyayen ta sun rasu, dan Allah
kutafi murabu ta arziki inma turoku akayi mun gane bazaiyi aiki ba kutafi” Umma
taki tashi, Alh yaki matsawa yaron hanunshi na kuka sai alokacin Dad yay magana
“Alh wanan ba itace Rufaida kuba, kutafi kafin akira security bamuson tashin
hankali”. Barraq ya daga murya yana kiran security! Security! Umma takara kecewa da
kuka yaron hanun Alh ya fashe da kuka, hayaniyan dayacika dakin da koke-koke yasa
Rufaida tafara motsi, kafafun ta suka fara rawa ahankali tace”wayyo Mummy,Uncle B
Duduwa “da sauri kowa ya juyo inda take Barraq yakarasa wajen da sauri yarike
hanunta ahankali yace”Baby ni ne, open ur eyes” ahankali ta bude ido tana ganin
Barraq ta kankameshi tana kuka sosai “zata dakeni,plz kace karta daken Uncle B,
banason duka ” Barraq ya cireta daga jikinshi yasa hannu ya share mata fuska
yace”Hey!calm down,look nikadai ne sai Mummy da Daddy dakuma Amma,babu wanda zai
dakeki,bazan kara bari acutar dakeba” da kyar ta iya maimaita abinda yace saboda
zafin dataji cikinta namata tace”Mummy?” Barraq ya girgiza Mata kai” yes!mummy tazo
tun jiya” matsawa gefe yayi Mum ta bayyana agaban ta tana murmushi,Rufaida ta bude
ma Mum hannu tanason ta rungume ta, da sauri Mum ta rungumeta. Sai alokacin idanun
Rufaida ya sauka kan wata yar mata a tsugunne idanunta hawaye shabe shabe,sai
kallonta take da wani mutume yana dauke da yaro shima sai kallonta yake. ta dago da
kanta daga jikin Mum tana kallon mutanen dabatasaniba, Mum da kowa na dakin yabi
Rufaida da kallo. Umma ahankali takara matsowa jikin gadon ta daga hannu tana
kokarin taba Rufaida da sauri Rufaida ta shige jikin Mum tadanyi ihu “Mummy wacece
wanan?maisa take kuka?maisa itada wanchan suke kallona? ” kafin Mum tai magana Umma
tarigata tace”Rufaida nine Mummy ki, Umma,kin manta ni Rufaida? ” Umma ta tashi da
sauri tariko hanun Alh tace “kinga ga Daddy ki shima kin mantashi??” Rufaida ta
girgiza kai “nidai kidena kuka,Ga Mummy na nan,asalin Amma na da Abba na sun
rasu”idanunta yakawo kwalla Barraq yace”look sir kufita daga dakin nan,kunga bata
da lpy,kundai ji tafadi muku da bakinta bata sanku ba”. Saida aka kira security
sanan Alh da Umma sukabar asibitin. Da kyar Alh ya kwantar ma da Umma hankali
yace”Alhamdulillah ma munganta,mun kuma san tana hannu nagari masuji da ita,masu
sonta,matsalar da tambayar daya ce tak! maisa Rufaida ta manta damu??Maisa? “.
Maman Abd Shakur😘

[7/14, 23:04] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


75

Da kyar suka kai hotel din dasuka sauka, Abba yakira kanninshi dasuke kano ya sanar
dasu anga Rufaida,amma anhana su ita, kowa yahau murna, sukai alkawarin zasuzo gobe
da sassafe Abujan, ayita a waje dole suji daga garesu. Yakira amintaccen mai
gadinshi dayake yanada makullin gida yace ya shiga dakin Rufaida ya bude wardrobe
dinta ya kwaso albums din hotunonin su duka da kayan makaran tarta da jakar makaran
tarta yahada su waje daya gobe zai turo wani abokinshi akaishi Airport yazo Abuja
yarike katin zaben shi dan zaa tambaya. Mai gadi ya amsa da to Alhj ya shiga gida
yahada komi tsaf dan shirin zuwa Abuja gobe sai murna yake zai shiga jirgin sama.
Yau Babbar rana ce ga Alh,Umma da yan uwan su harda mai gadi. Misalin sha biyu na
rana kowa ya iso daduk all evidence da shaidun da suka nuna cewa Rufaida yarsu ce.
Manyan motoci biyu suka cika aka tafi asibitin dashi. Koda suka isa ba’a barsu sun
shiga ba wai ba visiting hour bane. suna tsaye saiga Dad yazo zai wuce Alh yamai
magana ya tsaya suka gaisa sanan sukaja Dad gefe daya tiryan tiryan yayan Alh yama
Dad bayanin komi tareda nuna mishi hotunan Rufaida tun tana karama har girmanta. Da
kyar suka samu Dad ya yarda dasu saida shima tashi tambayar daya ce “maisa Rufaida
ta manta dasu,maisa ta manta da iyayen ta? ” Sai alokacin kanin Alh yay magana
yace”inaga aljanu ko sammu ne suka shafi Rufaida, dan mutum baya manta iyayenshi
haka inbadai matsalar kwakwalwa yasamu ba,nataho da magani da addu’oin dazan mata
in sha Allah zamuji gaskiyar abun,komi zai warware”. Dad yace “shi kenan bari
nakira muku Barraq,saina nemi sallama wurin likita dan mutafi gida ayi komi achan”.
Sukaima Dad godiya sosai.
Dad ya shiga dakin ya tarar da Barraq naba Rufaida tea tana sha ahankali Mum na
bandaki,Amma ta tafi gida yomusu abinci da sauri Rufaida ta kawar dakai ganin Daddy
ya shigo murmushi dad yayi ya kalli Barraq “ana nemanka awaje son” Barraq ya amsa
da to. Dad ya juya yafita yacigaba dabama Rufaida tea,ture cup din tayi tadan ya
mutse fuska “am okey” Barraq ya ajiye tea agefe “saina miki dure tunda bakicin
abinci yanzu”. tashi yayi daga kan gadon ya tsugunno yama goshin ta kiss “I luv
yhu Baby na” ya juya zai fita harya bude kofa ya tsaya yana kulle boturan rigarshi
yaji muryar Rufaida tace”Uncle B” da sauri ya kalleta “Naam Baby na” hannuwan ta
tarufe fuskarta dashi”I love you” kulle ido yayi ya bude,kafin yasa hannu ya
mintsili kanshi so ba mafarki yakeba Ahankali yace “mekika ce??” Tajuyar dakai tana
murmushi Mum tafito daga bayi tsayawa yayi agaban kofa yana kallonta Mum na zama
agadon Rufaida ta tashi da kyar ta rungume Mum fuskarta na kallon Barraq ta bude
baki ta Furta mai I love you, lips dinta ya karanta yagane abunda tafada. fita yay
daga dakin yana M urmushin da saida duka hakoranzhi suka bayyana. Koda yaga su Alh
ne yajuya zai koma “Umma tace dan girman Allah Barr ka tsaya” bai musu ba ya tsaya,
ahankali kowa ya gabatar mai da iya gaskiyar su da hotunan, yakuma kara ganin kaman
da Rufaida tayi da Rayyan kaninta but still yace “Alh mu shiga asibitin nan ayi DNA
test,Dad dake karaso wa yace”Son shiga mota mutafi gida”Barraq ya juya yaga Amma
riqe da Rufaida dake tafiya da kyar Barraq yace”But Dad…”Dad ya katseshi “No but
Barraq,is time to know d actual Truth,is time dazamu san maisa dat old woman hate
Rufaida sosai,less go” kowa ya shiga mota Rufaida na jikin Mum tana numfashi da
kyar ita yanzu tsoron mutane take bana wasaba. Maman Abd
Shakur😘

[7/14, 23:15] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRINA* 76

Babban falon Daddy aka sauke bakin. Dad,Mummy,Amma,Barraq,sai Rufaida daya rike
mata hannu gam kamar zata gudu. Bangaren su Alh kuwa daga shi sai Umma,sai Babban
wanshi,da kannenshi biyu da mai gadi agefe. Ba abunda sukeyi sai kallon Rufaida.
Rufaida ta rike hanun Barraq gam kaman za’a saceta. Dad ya kalli kanin Alh
yace”Bismillah” Mutumin ya kalli Rufaida yace “zo,Al Qur’ani mai girma zan karanta
akanki” Rufaida ta rike Barraq gam tana kuka,Barraq yakara riketa shima bayason
taje danshi bai yarda da abinda zasuyi ba. Dad ya kalli Rufaida yace”Daugther na”
ta kalleshi yace “jeki”. Da taimakon Barraq ta iya tashi yakaita gaban malam ya
zaunar da ita, sanan ya koma wurinshi ya zauna mutumin yay isti’aza da basmala
cikin kira’a mai dadi, cikin kuka Rufaida tace “Dan Allah tsaya,wlh ni banason
karatunan dakake min, yana tadamin da hankali” mutumin yacigaba batare daya
saurareta ba. Rufaida takara fashewa da kuka tana mikama Barraq hannu jikinta ko
ina na rawa, Barraq yay kaman zai tashi Dad ya ballamai harara, yakoma ya zauna
karatu yay karatu ayoyin Allah sun soma ratsa kan Rufaida ahankali ta sulale ta
kwanta akasa flat idanunta suka kankance, Barraq ya zabura ya tashi Mum ta zaunar
dashi ta rikemai hannu. mutumin ya kalli su Dad “dama nace da abunda akama
yarinyar nan,sammu ne yanzu kuma zan karyashi da izinin Allah, sammun zai koma kan
wanda yamata” kowa yay shiru mutumin ya dauko jakarshi ya dibi garin tafarnuwa
dawani bakin magani da garin habbatus sauda ya hada yasama Rufaida abaki, ya diga
ruwan zamzam so uku abakinta yahade mata bakin ya rufe ya matse hancinta nadan
sakanni saida yaga tahadiye sanan ya saketa “Rufaida! Rufaida! Rufaida! Ki mantasu
arayuwar ki! Ki manta Abban ki da Umman ki, ki shiga duniya karku sake
haduwa…”Barraq ya mike”Dad do something I hate all dis stuff,wot is he doing to
her? Wot is she saying?” Dad ya nunamai kujera alamun ya zauna yako zauna. Chan
kuma saita shiru. Tana buga kanta akasa sosai Barraq ganin bazai iya juran ganiba
ya chusa kanshi a tsakakanin kafafunshi yana goge hawaye. Dakin yay
shiru Rufaida ta dena abinda takeyi. Mutumin ya cigaba da rera karatun Al Qur’ani
a gefenta. Tadau minti talatin ahaka kafin ta bude idanunta ta kalli saman
dakin. Saikuma ta zabura tamike tsaye har saida mutanen dakin suka tsorata, tadanyi
kara ta rike cikinta”auch” idanunta arufe tace “Umma gari yay haske baki tashen
daga bacci ba,uh cikina na ciwo,banasom nai lattin school munada test yau” da sauri
Barraq ya daga kanshi ya kalleta. Barraq yataso yazo kusa da ita”Baby na are yhu
ok?Dr yace cikin zai rage miki ciwo nan da gobe” ahankali ta cire hanun daga
cikinta ta bude idonta ahankali tana kokarin ganin fuskar husky muryar dayay mata
magana yanzun nan. Sauke idonta datayi akan wani kakkyawan bature,ga gashin
baturai,ga wani hadaddan farin gilashi a idonshi yana mata murmushi yasa ta juya
tana karema mutanen dakin kallo,waige waige tafara hango Umman ta datayi akan
kujeran karshe rike da karamin yaro yasa tajuya da sauri tana rike da cikinta
takarasa wurin tafada jikin Umma tariketa gam tana kuka, Umma ma kuka. Da karfi
tace”Umma kalli-kalli”tace “auch Umma cikina ciwo yake” sanan ta nuna
Barraq,Mummy,Daddy da Amma “Umma suwaye wayanan turawan?” Barraq ya zaro ido yana
kallon ta, yatako zuwa gaban kujeran datake ahankali yace”Rufaida ” murguda mai
baki tayi ta kalli Abban ta tace “Abba wai waye wanan baturen? Baffa a ina kuka
samo turawa?”. Maman Abd Shakur😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 70 to 76KAINE SIRRI NA 88 TO D END →
KAINE SIRRI NA 77to87
Posted on July 25, 2016 by mamanshakur
[7/25, 20:28] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*
77

Kafin Umma tabama Rufaida amsa takara jeho wata tambayar “Umma maisa naga duk sunsa
gilas?Umma daga ina zukazo? “Tafadi maganar tana kallon fuskar Mum. Umma takasa
magana tarasa maizata yi awanan gaban farin cikin ganin yarta,harta tunasu ko bakin
cikin ta manta wayanda suka taimaketa, ciki harda abin kaunar ta,mijinta. Umma
takara kecewa da kuka, Alh yay jarumtar yin magana ta hanyar kallon kanin nashi
yace”Young malam meke faruwa? ?explain kasamu aduhu? Maisa ta manta mutanen dasuka
taimaketa da mijinta?” Mutumin ya gyara zama yace”yaya amma Rufaida sammu ta manta
iyayen ta gabaki daya,da rayuwar ta nada,ta shiga duniya kaman yanda kukaji tafada
dazu, duk wani Rayuwa datayi bayan ta bar gidanku tayishi ne bata cikin asalin
hankalin ta,tana cikin sammu,saisa ta manta su,amma zata tunasu nan bada jimawa
ba,tashin ta yanzu taganine kaman daga bacci ta tashi,rayuwar datayi kaman mafarki
ne,sai ahankali zata dinga tunasu kadan kadan,kubata lokaci zata warke duk zata
tunaku,wanan bawata babbar matsala bace” Rufaida data kwantar da kanta ajikin Umma
ahankali tace “maganar wa Baffa yakeyi Umma?” Umma tadan shafa kanta “zan fada miki
anjima”. Sai alokacin Mum tai magana “nakasa gane dis whole thing,suyawe iyayen
Rufaida dahar suka mutu?ita Duduwa data kira kanta kakar Rufaida who is she then??a
ina suka san Rufaida?”. Dad yay gyaran murya” d only person dat can answer
that question is Duduwa! Barraq cikin fushi yace”babu wacce zai kira matar nan
gidanan, juyamin kwakwalwar mata sukayi ,dey did something to her” yakama kwalar
malamin “mekama Rufaida?”kowa na falon ya mike tsaye Dad ya rike hannu Barraq “son
let him go,ka sakeshi,ba abunda yama Daugther,I said let him go” da kyar Barraq ya
sakeshi idanunshi sunyi ja Dad ya zaunar dashi yadawo yana bama malamin hakuri
wanda ya nuna bakomi. Dad yakoma kan Barraq yana mai fada”nasha fadama idan rai ya
baci kar hankali ya gushe,idan kai tunanin komi everything make sense zaiyu yaron
Duduwa ya tsinci Rufaida ya dauketa saisa ma Duduwa hate her soo much,understand
and get it once rayuwar da daugther tayi damu tayishi ne kaman amafarki,she will
remember us amma ba yanzu ba” Barraq yay shiru ya daura kanshi akan cinyar
shi,yarasa mezaiyi yaji dadi,zuciyarshi na mugun zafi,kanshi kaman an zuba
garwashi” Karan wayar dayaji yasa ya dago kanshi ahankali suka hada ido da Rufaida
harara ta balla mishi saboda taji haushin yanda ya shake baffan ta. Jin maganar Alh
yasa kallon yakoma kanshi arude yace”garin yaya?ganinan dawowa,kuhadu ku kamata a
kulle yanda bazata fitaba” ya katse wayar tashin hankali ya bayyanah karara a
fuskarshi Umma ta fara tambaya “lafiya Alh?” Share gumin kanshi yayi yace “mai
gadin gidan hajara(kishiyar Umma) yakirani wai Hajara ta haukace, tafito sai raye
raye take tana cire kaya tana kiran Rufaida,ankasa kamata dole natafi Abuja yanzu”
ya kalli Dad yace”Alh dan Allah inason keban cewa da yan uwana da Rufaida Alh” Dad
ya washe baki “to ba matsala”. Yatashi Mum da Amma sukai gaba Barraq yaki matsawa
daidai danan da chan Dad ya rike hanunshi suka fita daga dakin. Alh ya fuskanci
yayan shi yace”yaya inaso ku saurare ni, munga Rufaida shine kuma abunda muketa
addu’a akai ko?”Suka amsa da haka ne. “Amma da muka ganta mun tarar da ita a
matsayin matar aure, kuma ga miji salihi mai taimako ga tausayi maikuma sonta”,
tashi yayi ya matsa kusa da Umma dake kallonshi ya rike hanunta “abunda nake shirin
fada nasan zaimiki wuyan yi, amma inaso ki duba mutuncin mutanen nan, dakuma abunda
sukama yarmu na nuna mata so,kulawa,suka aurar da ita ga miji nagari” yadanja
numfashi kafin yacigaba”Alhamdulillah mun godema Allah daya bayyana mana yarmu,
dudda Rufaida bata tunasu ba bazaisa mutafi da itaba,bata karkashin mu yanzu,tana
karkashin mijin ta, hukuncina shine zamu barta anan mutafi madinga zuwa dubata”
yakarasa maganar yana kallon Umma dake hawaye. Ahankali ta girgiza mai kai,”na
yarda da abunda kace na amince,bazamu taba karbar Rufaida daga hannun Barraq ba” ya
kalli Yayan shi shima ya nuna amince warshi. Kowa na dakin ya nuna amincewar shi.
Alamu Alh yay ma Umma da ido. Umma ta share hawayen ta tajuya ta kalli Rufaida
tarike mata hannu tace”Baben Mama” Rufaida ta kalleta Umma tace”inaso ki zauna a
gidanan da wayanan turawan zamuje gida Anty ki batada lpy zamu kaita asibiti kinji”
Rufaida ta lankwasa kai”Uhm Uhm Umma nidai bazan zauna dasuba, bana sonsu banason
gidan,inason naje school gobe tunda nariga nai latti yau ” Umma ta mikama Alh
Rayyan dayay bacci ta juyo ta fuskanci Rufaida tace “Bebin mama inaso ki saurare ni
kiji abunda zan fadan miki,…”Umma tafadin ma Rufaida komi,kan Rufaida yay chaji
kalma daya kwakwalwar ta yafi rikewa “ke matar aure ce!matar Barraq!. Kanta ta
chusa a cinya tafara rafka uban kuka bana wasaba, “wlh bazan yardaba,Allah bana
sonshi, mutumin daya shake wuyan Baffa yanzu nan wlh bana sonshi,nibazan zaunaba,
kuzan bi muje gidan mu”. Yayan Alh yatashi yazo gabanta yace”Rufaida! Ya daga
mata tsawa,jikinta yafara rawa dantana mugun tsoron Baffa Yaya yacika fada,ga
fushi.”idan naji kin kara cewa bakison Barraq saina karyaki,young Malam yace zaki
tuna komi so dolenki ki zauna dasu,yanda kika zauna dasu da haka zaki zauna dasu
yanzu,shashanci banza kawai, yanzu bamu da iko dake sai yanda mijinki yace, muba
butulu bane da zamu goya miki baya ba,bazamu taba godema mutanen nan tahanyar
tafiya dakeba kinajina” ta dagakai da sauri tana zaro ido. ya kalli mai gadi
yace”kirasu mungama” mai gadi yafita dan kiransu.
Maman Abd Shakur 😘

[7/25, 20:28] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


78
Shigowa su Dad sukayi kowa yanemi wuri ya zauna Barraq idanunshi nakan Rufaida
dayaga tana kuka sosai kaman yay magana saikuma yay shiru ya dukar da kanshi akasa.
Alh yay gyaran murya yace “Alh zamutafi” da sauri Barraq ya dago kanshi ya kalli
Alh. Alh ya sakinma Barraq tattausan murmushi kafin ya juya ga Dad yace”mun gode
da kula da yarmu dakukayi da zaba mata miji nagari dakukayi nagode Alh. Babbar
gaisuwata da fatan alheri gareka Barr Allah yakara daukaka ka yabaka zuri’a nagari,
nagode da bama yata so da kulawa”. Barraq ya sadda kanshi kasa,Alh ya cigaba “ga
Rufaida nan, in sha Allah zamu dinga zuwa dubata,Allah ya saka muku da alheri” ya
juya ya kalli Rufaida yace “kima mijinki da iyayenki biyayya, inhar aka kawomin
karanki saina saba miki kinajina ko?” Ta gyada kai tana share hawaye. Dad yay
magana “bazaku tafi da ita tadan zauna daku ba?munsan kuna bukatar yarku itama
haka,abun zai mata yawa ta warke kuma tacigaba da zama da wayanda batasani ba” Alh
yay murmushi “tasan ku, saitana zama daku dinne ai zata tunaku,yanzu bata
karkashin mu tana karkashin inuwar auren Barraq ne, haka Allah ya kaddara, mun gode
kwarai,”ya kalli mum yace mun gode ma ya kalli Amma yace mun gode ma Umma da su
Baffa suka goggode musu kafin kowa ya mike tsaye zasu tafi duk suka tashi Rufaida
tarike zanin Umma tana kuka “ni wlh kidawo,banason gidanan,zan biku” Umma ta shafa
kanta “banace zan dawo ba? kiyakuri kinji Baby na” Rufaida ta make kafada tana
kuka. cikin Bacin Rai Baffa sarkin masifa ya daka mata tsawa “yimana shiru kafin
nafasa bakinan,sake ta” bakinta tarike tana hawaye, Ya kalli Barraq yace”kaita
daki tasha maganin ta tai bacci, bata gama warkewa ba bata bukatan all dis stress”.
Ahankali Barraq yatako inda take ya mika mata hannu make kafada tayi da Baffa
yamata wani mugun kallo batasan sanda tabashi ba tana tafiya ahankali suka fita
daga dakin part dinshi yakaita yabude suka shiga. sukama su Alh sukabar gidan Dad
dasu Amma suka dawo ciki kowa yana mamakin abunda yafaru yau.
Suna shiga dakin ta fizge hanunta tana turo baki”kuma ni mutum yasake ni tunda dai
ba hanunshi ya rike ba” Ta nemi kujera ta zauna ahankali tana cije lebe. Barraq
baice komi ba saidan Murmushin dayayi aranshi yace so real Rufaida nada masifa O
God save me!. Fita yayi daga dakin yatafi bangaren Amma yaganta tareda Mum
yace”Mummy ina magungunan ta?” Mum ta dauko tabashi ya juya zai fita takirashi Son
ya dawo “kabi Daugther ahankali, kayi hakuri dakome zatayi kaji, karka bata mata
rai, kadaiga batada lpy anjima zan shigo naganta” ya juya yafita koda ya shiga
dakin ya tarar da ita a zaune tadena sai kumbure kumburen datakeyi. ya dauko goran
ruwan faro da maganin daya kamata tasha ya ballo ya mika mata “sha maganin ki Baby
na”ta kalleshi ta ballamai harara “ni bazan shaba malam, kumani kabani kayan sawana
zanyi wanka na chanza kayan nan” yadade tsaye yana kallon yanda take murguda mai
baki. Tsugunnawa yayi agabanta yace”naji but plz take it and drink,baki da lafiya”
“ance baza ashaba,wai ni dole ne wlh niba ruwana da mutum, wai mijina ne, aibani
nace inaso ba, nigidan mu zaka kaini gobe ehe” tana karasa maganan tabi ta gefenshi
tayi hanyar wata kofa data gani,tasa hannu ta bude tabi wurin takara ganin wani
kofa ta bude taga bedroom takarasa shiga dakin tanemi bakin gado ta zauna da kyar.
Ta sauke ajiyan zuciya tana shafa cikinta “wai meyasa cikina ke ciwo?wayyo zapi
wlh” tafada araunane. zip din rigarta ta zage, ta cire rigar daga jikinta dan
warin asibiti rigar yake mata wanda hakan keson yasata amai. Yarage daga ita sai
sket da Bra, ta tashi tsaye tana kokarin zage zip din sket din taji an bude kofa
an shigo ganin Barraq dauke da maganin ahannunshi yana wani irin kallonta yasa
tafara neman rigarta dake kan gado. Barraq yamata kuri rabon dayaga jikinta harya
manta. Sa hannu yayi ya tura kofar tarufu sanan yakara sa shigo wa dakin “wai
mehaka?can’t u see dat am changing,kafita? ” Rufaida tafada a masifance, Barraq ya
sakin mata murmushi tareda lankwasa kai alamun a’a kaman yanda takeyi. Daukar
rigar tayi tasa agaban kirjinta tana nunashi da yatsa “wai kai baturen nan wani
irin maye ne? ” saida takai bango sanan yasa hannu shi ta bayanta yahada ta da
jikinshi, Rufaida ta rufe ido gam jikinta ko ina na rawa murmushi yasake yi aranshi
yace”one character in common Rufaida den and now duk matsorata ne” duko da kanshi
yayi yakai bakinshi saitin kunnenta yace”ni mayen Rufaida ne ” Rufaida ta sa hannu
ta rufe kunnenta rigar tafadi akasa. Bude ido tayi suna hada ido tasake kulle
idonta “let me go,wai mehaka,I hate dis stuff,plz let me go ” Barraq yasa hannu
yakai wuyan ta yanama ta waiwayi zuwa kasa “only if u take ur drugs ” jin hannunshi
nagab da kaiwa kirjinta ta rike hanun muryar ta na rawa sosai tace”to bani zansha
“. Maman Abd Shakur😘

[7/25, 20:28] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


80

“”Plz Don’t kill him am begging yhu P.A, wlh inason Barraq sosai,plz! P.A. ya
kalli Nana da jajayen idonshi “kowa na zaban Barraq kaina” ya girgiza kai “no I
can’t take dis anymore, I can’t stand everyone choosing Barraq over me, nooo” yasa
hannu ya daga Nana ya jefar da ita kan gado yasake daga karfen zai chakama Barraq
Nana tai ihu daga kan gadon” shift to the left Barraq! Daidai lokacin da karfen ke
sauka Barraq yadan matsa karfen ya yaga fatar gefen cikinshi sosai jini yafara
bulbulowa, farar rigar dayasa ta batci da jini Nana tafashe da kuka tana ihu “u
killed him PA ,ka kashemin Barraq dina, I hate yhu I hate yhu”. Sakin karfen P.A.
yayi ya tsaya gaban Barraq ganin baya numfashi jini nabin bakinshi kanshi da
cikinshi yasa yay murmushi. wandon shi dake kan gado ya dauka yasa yadau shirt
dinshi yasa ya fizgo gashin Nana dake kuka sosai kan gado yakama less go,Nana ta
fizge kanta “am not going anywhere, ka kasheni nima na bishi just kill me”. PA ya
fashe da dariya yana cizan lebe hanunshi yasa ya matso kirjinta da karfi saida tai
kara “ta yaya zan kasheki kinada abubuwan more rayuwa haka?bazan taba kashekiba
kindawo sex machine dina,my prisoner”ya tura keyanta gaba tana kuka ya tusata cikin
motar ta ya shiga yaja motar da gudu yabar anguwar gabaki daya. Ahankali
Barraq ke lalube neman abunda zai daura akan ciwon saboda kar jininshi ya kare,
kamo wani abu da baisan meba yadaiji taushi ya dunkule ya daura kan ciwon yana
numfashi kadan-kadan Ahankali bakinshi ya furta Baby na…”.
A firgice Rufaida ta farka daga baccin tana turo baki “ni ba Baby ka bane, mutum na
baccin shi kana wani kiranshi ni “jin shiru yasa ta waiga bataga kowa adakin ba
Amma ai taji muryan baturen nan yakirata. Gefen cikinta taji yana mata zafi sosai
Bargon jikinta ta yaye ta kalli wurin taga jini,hannu tasa a wurin taga babu ciwo
amma ga jini. Jin zuciyarta namata zafi da zugi kaman tai kuka gashi sai kawo mata
bature yake yasa ta tashi tsaye. batabi takan batasa rigaba tadau hijabi tasa
tafara bin dakuna tana budewa taga bashi fitowa daga part din gabaki daya tayi ta
tafi part din dazu tana shiga taga Dad da Mummy da Amma, agogon dakin ta kalla taga
biyar da rabi. Mum ta kalleta”Daughter na kin tashi?dazu na shigo kina bacci”
Rufaida ta kallesu alamun damuwa karara a fuskarta tace”ina baturen nan?” Amma
tace”dazu na ganshi dazai fita yacemin zaije ya kwaso miki kayane”. Rufaida tafashe
da kuka”nidai ku kirashi ya dawo, inajin wani iri ajikina,duk inda yake he is not
safe,nidai ku kira baturen”takara sa maganan tana kuka sosai. Dan tasamu kwanciyar
hankali yasa Dad ya daga waya yakira Barraq sau uku ba a dagaba ajiye wayan yayi
yace bai daukaba. Rufaida ta fashe da kuka Amma tace “halama yanzu meeting ya shiga
ko wani uzuri”. Mum tai shiru tana kallon Rufaida itama tun dazu takejin wani iri
kodai gaskiyan Rufaida ne he is not safe??something is wrong, definitely! Ta kalli
Dad tace “Alh tura wani yabi bayanshi plz” Dad yace ok. Dukan
sitairin mota Muzzammil yayi “damn dis holdup,haba dan Allah,Nigeria jaga -jaga
komi suffer-suffer,am sick of dis country” cikin iko da yarda Allah yaga motoci sun
fara tafiya yay maza yay gaba. Wuraren 6:00 yakara so gidan Nana dake water board.
Ganin motar Barraq yasa yay murmushi “baiyi zuciya yatafi ba kenan, yana jirana”.
paka motarshi yay da kyau yafito yacire necktie din wuyarshi ya wurga cikin motar
ya rufe yay hanyar shiga gidan ahankali ya tura gate ya shiga cikin gidan. Ganin
kofar sitting room abude yasa dan mamaki ya shigeshi gashi gidan shiru. Saka kafa
yayi ya shiga falon ganin ba kowa a falon yasa yaji gabanshi yadan fadi ina
Barraq??yaga motarshi awaje fa. Ganin kofar bedroom adan bude kadan yasa ya daga
kafarshi dayaji yasoma sanyi yakai wurin, bai tura kofar ba ya tsaya abakin wurin
ya bude murya yace”Guy are yhu in dere?” Yaji shiru he feels strange yarasa maisa,
hannu yasa yakara sa tura kofar ahankali yakebin jini daya gani akasa kallo, hango
Barraq dayayi warwas akasa yasa yakara sa ciki da gudu ya tsugunna agabanshi yasa
hannaye biyu ya tallabo fuskar Barraq “who did dis to yhu Barraq ” where are ur eye
glasses?”yafada yanamai waige waigen dakin hango gilashin afashe ya ruguje yasa ya
kankame Barraq a jikinshi sosai yana kuka “who did dis to yhu Friend?” Barraq ya
lashe lips dinshi dasuka bushe ahankali hawaye nabin gefen idonshi “take good care
of Rufaida Muzzammil plz,katafi kabata maganin dare kaji,karka bari wani ya cutar
min da Baby na, plz Muzzammil” yafadi maganan ahankali Muzzammil yarufe mai baki
yana girgiza kai”stop talking as if u are going to die,yeah yeah yeah! I will take
good care of Rufaida,amma kadena min magana kaman kana min wasiyya,zaka warke,but
who did dis to yhu?” Barraq ya kara matse Hanun Muzzammil tareda rike inda ke
jini acikin shi ahankali yay magana Muzzammil yakara kunenshi a bakinshi “DUDUWA!
NANA!P.A! P.A! P.A!..” Muzzammil ya rufemai baki da sauri ganin cikinshi na bulbulo
da jini,bakinshi ma Haka “keep quite Boo,u are bleeding, lemme call an ambulance”
Barraq ya girgiza mai kai”I need water friend ” Muzzammil ya kwantar dashi ahankali
yafita daga dakin neman ruwa fridge yaje ya dauko bottle water ya dawo dakin ya
tsugunna ya taba jikin Barraq yaji sanyi baidamu ba ya dagoshi ya daurashi akan
cinyanshi “B ga ruwan bude baki kasha ” yaji Barraq shiru yadan girgizashi “B”
yasake jin shiru!. Maman
Abd Shakur😘

[7/25, 20:28] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


79

Barraq yay murmushi okay! Ya mika mata maganin ta karba cikin sarkewan murya
tace”ai sainasha ruwa zan iya sha” Barraq yakara murmushi ganin dukta rude ya mika
mata ruwan goran hanunshi, tasha kafin ta runtse ido ta watsa maganin a bakinta ta
hadiye takara shan ruwa da sauri sanan ta rufe goran ruwan. Tai shiru yamata wani
baken baken yaki bari tawuce. Dago idanunta tayi taga ita yake kallo,da sauri ta
juyar da kanta tareda folding hannayenta akan kirjinta tana kunkune “ni ni ni fa
nagaji da kallon nan, ni mutum ma yabani hanya na wuce,sai wani kallona ake, to
tubarkalla masha Allah, ni kambun baka baya kamani iyayena sun tofeni da li’ilafi”.
Hannu Barraq yasa ya juyo da fuskarta ta fuskan ce shi,batai tsammani ba taji
yahada bakinshi da nata tai kokarin kwacen kanta takasa, saida yay wasa da ita
sosai sanan ya saketa tafashe da kuka tana bugamai rigarta, dariya yayi sosai kafin
yasa hannu ya rike rigar “oya tashi kije kiyi wakan mutafi gidanmu yanda zamufi yin
amarcin da kyau ko?”ya karashe maganan tareda kashe mata ido daya. Bakin ciki kaman
ya kasheta cike da masifa tace”babu inda zani anan zanta zama na,kuma wlh ni saika
kaini gidanmu,kuma saina hadaka da baban mu ince tabani kakeyi” Barraq ya zaro ido
yana murmushi “Haba Baby na kullum fa haka mukeyi da,harda ma wanda yafi
wanan,shine yanzu zaki fada, amiki dariya ace kina tona asirin mijinki” tafashe da
kuka tadau bra daga kan gado daya cire mata ta bugamai abaya”ni karka sake cewa
haka,bana komi da kai,ni banama sonka banason bature, basu da karfi, kuma basu da
karfin kashi,kashin su gabaki daya biscuit bone ne,abu kadan ku karye,gasu da yawan
yin ciwo,ragwaye ne ku woyii”tamai gwalo. “mune ragwaye Baby na?” ya taso zai
kamata tajuya zata gudu cikinta yawani murda hakan yasa tai baya zata fadi Barraq
ya rike ta da sauri “Baby na are yhu okay?” Rikeshi tayi da karfi tana cije
lebe”auch!cikina ciwo” tafada ahankali tana shirin kuka “Barraq yace”sorry zan
fadanma Dr”,hannunshi ya daura kan cikin nata yana shafawa ahankali tai lamo
tanajin saukar dumin hanunshi acikin cikin nata, hakan yasa taji ciwon na raguwa
kadan kadan. “I can’t forget lokacin dakika ce i luv yhu Uncle B” gyara kwanciya
tayi a jikinshi ta kuramai ido “nina ce haka?”ta murguda mai baki”i dont luv yhu”ta
lumshe ido ahaka bacci mai nauyi yay gaba da ita. Kwantar da ita yayi akan gadon
“I luv yhu soo much”yay ma goshinta kiss yaja bargo ya lullubeta. Bayi ya shiga yay
wanka a gurguje ya shirya yadau car keys dinshi yafita.
Kwaso mata kayanta yayi a babbar akwati yasaka a boot sanan ya koma ya kulle gidan,
ya shiga mota mai gadi yabude mai gate sanan ya dawo ya tsaya wurin glass din
driver ganin hakan yasa Barraq ya kashe motar ya juyo yace”any problem Samaila?PA
bai biyaka albashin ka bane? ” mai gadi ya girgiza kai “Barr yabiyamu,akwai abunda
nakeson fadama” Barraq yafito daga motar yarufe”muko ma inuwa mufita daga rana”
bayan sun zauna akan bencin mai gadi sanan mai gadi yafara magana “ranan da matarka
tarasa baby ta akwai wani abu daya faru mai gidana” Barraq yabashi duka hankalin
shi “bayan Jonathan yabar kakar matarka ta shiga gida, ninace bari naje shago na
siyo garin rogo,koda nafita naji ankira salla saina tsaya a massallaci nai salla
bayan na idar ne natafi shago na siyo garin kwaki,ina fitowa naga kakar matarka
natafiya tana waige waige saichan naga wata katuwar jeep ta faka agaban ta ta
dauketa ” cikin sauri Barraq yace “kasan wanda ke motar?wanda ya dauketa?” Mai gadi
yace”Oga Nana nagani,Nana wanda lokacin kana zuwa dani office dinka take zuwa
nemanka, ita nagani ta dauki matar,inata mamaki ya akayi Nana tasan kakar matarka
saisa nace duk inna ganka zan fada maka”. Barraq ya mike tsaye yana huci”Thank yhu
Samaila,zan ganka gobe “samaila ya washe baki yasan ganin alheri Barraq
zaimai,Nagode yallabai Allah karemana kai,Allah ja zamaninka” Barraq ya shiga
motar shi da sauri yaja da karfin tsiya ” tukin hauka yake kanshi yay chaji yanzu
ina zaiga Nana?ina zai ganta? Tunani kadan yayi ya dauko wayarshi yay dailing
number Muzzammil ringing biyu ya dauka “Hello Boo I need yhu,ka samen a gidan gonar
Nana dake water board” Muzzamil yace”B Nana again? Maikuma yafaru?” “Just muhadu a
wurin ina jiranka” Barraq ya daki sitarin motar dan gani yake baya sauri “bana
forgiving abunda akama Rufaida,Nana ke kika turo aka kashemin Da, aka wahalar da
matata” kara gudun motarshi yayi. Paka motarshi yayi a wajen gidan ganin
motar Nana yasa ya tabbatar tana nan. Ya bude gate ya shiga. ahankali ya bude
kofar dazai sadashi da falo ya shiga yana tafiya ahankali babu kowa a falo sai
warin giya dake tashi dakuma bra da dan wando daya gani akan sofa, tsaki yayi
yadaga kafa yacigaba da tafiya ganin wata kofa yasa ya daura hannu akan handle din
zai bude jin numfashi da gurnani yasa ya tsaya yakasa kunne “Nana ki barni na shiga
karna mutu,kin tayarmin da hankali ahhh plz”, muryan Nana yaji tace “saika fadan
min cikin ya zube?dan Duduwa tace min ya zube Barraq ya tabbatar ma da hakan?”
Barraq ya rike zuciyar shi da karfi dayaji P.A. yace”dazu da safe saida mukai waya
dashi, yamace karnazo aiki,cikin ya zube zai kula da yarinyar kafin yay resuming,
yanzu dai barni na shiga bayan haka komi kikeso zanyi koda zuwa dauko miki Duduwa
ne daga gujungu”. Barraq baisan lokacin dayasa kafa ya daki
kofar ta bude ba,wani tsalle yayi yahau gadon ya shako wuyar P.A. yafara duka yana
jijjigashi “hw could yhu?”ya daki cikinshi,ya shakemai wuya gam P.A. yafara kakarin
mutuwa. Nana data nemo zani ta daura tazo tarike Barraq “B let him go,ka
sakeshi”jin muryar Nana hallittar dayafi tsana a duniya yasa hankalin shi yakara
gushewa hankada P.A. yay akasa ya juyo ya kwashe Nana dawani gigitacchen mari. Ya
rufeta da duka yana ball da ita tana ihu. Ahankali Barraq yaji saukar abunda baisan
takamaiman me ba akanshi,yaji abu nabin kanshi wanda yakasa gane jini ne ko ruwa?.
juyowa yayi dan damkar P.A. yaji an fizge gilashin idonshi an yar. Duhu ya bayyanah
a ganinshi. PA ya daga dogon karfen mai tsinin baki yakara bugama Barraq akai,
take Barraq yaji jiri na dibanshi amma yaki barin kanshi yakai kasa,ya rike
guiwarshi yana tofar da jini daga bakinshi, P.A. ya daga kafa yay ball da kafar
Barraq, Barraq yay kara ya zube akasa yafara tabe tabe yana neman gilashin idonshi.
PA ya take hannun Barraq dayaga yana gab da tabo gilashin, yasa dayar kafanshi yay
ball da gilashin glass din yafashe. PA yay dariya mai kara”I’ve always hate yhu
Barraq,ban taba sonka for a single minute ba,am jealous of yhu,kullum ni kenan ka
maidani mutum mara amfani,mai aiki a karkashin ka,mai kwasoma takardu yasama
amota,mai biyan workers dinka”. Ya ciji lebe” I hate u Barraq,u killed my
future,saisa duk wani abu dazai cutar dakai nakeyi amma tunda yanzu kaga noni I
will just take ur life”. ya daga karfen ya saita tsinin akan cikin Barraq,
hanunshi ya daga zai chakama Barraq aciki. Ahankali Barraq ya saki
kara,Nana ta saki ihu noooooo! Why PA?I love him,I always do,why???”
Maman Abd Shakur😘

[7/25, 20:28] Aishat Muhammad: 81- hannunshi ya daura akan kirjin shi yaji zuciyar
shi bata bugawa ta tsaya chak “Innalillahi wa inna ilaihi raji’un ” Muzzammil
yafara Marin fuskarshi yana kuka “am dreaming, mafarki nake katashi daga mafarkin”
daura kanshi yayi akan kirjin Barraq ya girgizashi “Noooooo!karka tafi ka barni
plz, kadawo Barraq kadawo” daga jikinshi yayi daga na Barraq ya cire rigar jikinshi
ya rufe fuskar Barraq dashi. Ya zauna a wurin ya tankwashe kafa yana kuka sosai
banawasa ba. Karan wayarshi data dameshi ya dauka ganin Daddy
Barraq yasa yay picking kafin yay magana Dad yayi”son kana tareda abokin naka ne,
Rufaida nata kuka wai taji ajikinta he is not safe,kuna tare ne kabani shi muyi
magana??” Muzzammil ya share hawayen idonshi muryar shi na rawa yace “Dad kabar
inda suke zan fadama wani abune ” Dad ya kalli Rufaida dake kallonshi da Mum yamusu
M urmushin yaki kafin yafito daga dakin da sauri yace”menene Muzzammil tell me?is
Barraq okay?” Muzzammil yakasa rike kukan dake neman kwacemai yafashe da Kuka sosai
“Dad yace “Muzzammil is everything okay?where is Barraq? ” Muzzammil yace”Daddy u
have to come to No 37 water Board area, gidan Nana” Arude Dad yace”meke faruwa
Muzzammil? ni namiji ne I can take and handle it,tell me” Muzzammil yace”Daddy just
come,they’ve killed him, they’ve killed Barraq, Dad sun kashemin abokina Barraq is
Dead Daddy…” ahankali wayar dake hanun Daddy ta sulale tafadi akasa
tartsatsatsas!” Maman Abd Shakur😘

[7/25, 20:28] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


82

Ahankali yadaga kafa ya juya ganin Mum tsaye abayanshi hawaye na kwarara a fuskarta
yasa ya kakalo murmushi ya sakar mata yazo zaibi ta gabanta ya wuce tarike
hanunshi”dont hide anything, maiya sami Son?I know something is wrong I can feel it
here”ta nuna mishi zuciyarta tana kuka sosai. Dad ya rungume ta yana shafa bayanta
ahankali yace”Adama kisan Allah shike hallito bawa yakuma dauke abinshi idan yaso
ko? “Ta girgiza kai tare da rike kirjinta “karkiji tsoro,ki dake kikuma yarda da
kaddara,Barraq ya rasu! “Amma da karaso warta kenan wajen tace”what! Mum ta rike
rigan Dad gam tai kasa zata fadi Dad ya riketa da sauri yana lallashin ta, Amma
tafashe da kuka tazo ta kama hannun Mum tana kuka. Mum ta kalli Amma “wasa yake
dena kuka Maman Auta dena kinji”. Dad da idanunshi yay ja yace”Amma take her inside
ki dau Rufaida ki kaita part din Barraq banason tasan komi,batada lapiya kar
ciwonta ya dawo sabo,bari naje mutaho dashi”. Dad yay hanyar gate yay magana damai
gadi maigadi ya dafe kanshi kafin ya bude gate din da sauri Dad ya shiga katuwar
jeep yaja yafita mai gadi yarufe gate da sauri yafita ya shiga mota suka tafi tare
da Dad. Dad yana tuki yana kiran mutane da yan uwanshi saida ya biya yadau imam din
anguwar su da wayansu mutane dasukayi mota guda dan ansan Barrister Barraq ko ina.
Ahankali Imam ya tura kofar bedroom din gidan Nana dan tunda suka shiga gidan Dad
jikinshi yay sanyi idanunshi sukai jajir sukai zuru zuru. hango Muzzamil zaune
gaban Barraq da fuskarshi ke alullube duk jini yasa Dad ya rike zuciyar shi
Muzzammil ya dago jajayen idanunshi ya kalli su Dad ciki harda Dadinshi da sauri
yatashi ya rungume Dadinshi yasaki Kuka. Kafin yasaki dadin shi ya rungume Dadin
Barraq yana kuka sosai. Dad ya shafa bayanshi Muzzammil ya sakeshi ya koma gefe.
Dad ya karaso ya tsugunna yasa guiwowin shi akasa yakai hanun damanshi ya yaye
rigar Muzzammil dake kan fuskarshi, ganin Fuskar Barraq dinshi ya bayyana yasa ya
daga hannu ya kulle bakinshi yana kokarin hana kukan dake neman zuwan mishi ganin
gawan danshi agaban shi. Ahankali ya dukar da kanshi ya sumbaci goshin Barraq
yamai addu’a ya lumshe idonshi yana tunanin randa Barraq yacemai I luv yhu Daddy a
restaurant din wajen asibiti. Wani mugun kuka ya kufcemai. Daddy ya girgiza kai
“Barraq noo, u can’t die! Barraq kai kadaine dana namiji ku biyu gareni,narasa
grandson dina,banason rasaka yanzu dan Allah kadawo”Baban Muzzammil ya kama
kafadarshi ya murza alamun ya yakuri Dad ya juyo ya kalli Muzzammil cikin
dishahshiyar muryarshi yace “waya mishi haka?waya kashemin da?” Imam ya girgiza kai
“wanan za yishi anjima, yanada kyau akai gawa makwancinta da wuri mutafi” ya daga
Dad ahankali. Yayinda mai gadi ya kawo pakaceciyan tabarma Imam Daddy da Dadin
muzzammil suka daga Barraq suka sashi aciki aka nannade shi suka daukoshi aka fito
dashi aka sashi a dogon bus din da Dadin muzzammil yazo dashi. Duk aka shishiga
mota aka kama hanyar zuwa gida dan yimishi sutura. Alokacin gari yasoma duhu dan
mangariba ta wuce amma isha bai riga yayiba.
Rufaida dake zaune akan gado Amma a gefenta idanunta yay jajir tadai daure takiyin
kuka dan kar Rufaida ta gane wani abu. Zumbur Rufaida ta mike ta rike zuciyar ta
gam tana hawaye Amma ta tambaya “menene “Rufaida ta fashe da kuka sosai “bakin ciki
nakeji sosai azuciyata, jinake kaman zan mutu,wlh bature kawai nakeson gani. Inajin
alamun shi araina,kaman yana cikin gidanan yanzu,naji kamshin turaren shi”.
Ahankali Amma ta zaunar da ita “zauna Rufaida, nanda anjima zai dawo meeting ya
tsareshi”ta share hawayen ta”are yhu sure?” Amma ta gyada mata kai. Zaunawa Rufaida
tayi shiru Amma ta tashi cikin dabara tadan bude labulen window hango maza an cika
gidansu ga su dad sun dauko abu a tabarma ya tabbatar mata Barraq ne kasa rike
hawayen ta tayi da sauri ta gogesu ta saki labulen ta kalli Rufaida datai tagume
gwanin ban tausayi tace”bari naje nakawo miki abinci,ki jirani karki fito” tafita
daga dakin da sauri batare data jira amsan Rufaida ba.
Minti 30 da fitar Amma Rufaida ta tashi ta bude kofa ganin maza an cika ko ina a
gidan wasu na kuka yasa jikinta yafara rawa taji wani irin motsi acikinta kaman na
yaro, ganin wani dan tsoho na kuka agefe yasa Rufaida taje wajenshi “Baba meke
faruwa? ” “yarinya mutumin daya taimake ni arayuwa yabani jari,yarana mata uku sun
tashi aure Banda komi ya dauken mun nauyinsu,yamusu komi na daki yabiya kudi akama
matata aikin cancer a nono datake dashi,shine yarasu,wasu mugaye suka kasheshi”.
Rufaida ta rike cikinta gam ta tsugunna a wurin “Baba ya sunanshi menene
kamanininshi?” Tsohon ya sharce majina “Barraq!Rufaida ta zaro ido dan taji dazu
abbanta yakira baturen nan da Barraq. Ahankali Muryarta na rawa tace”Baba bature
ne? ” Baba ya girgiza kai “eh jini biyu ne dai”Mamar shi yar rasha(Russia)babanshi
dan Nigeria”. Rufaida ta tsala wani irin uban ihu tafashe da kuka tai hanyar part
din Daddy yanda maza suka cika wajen yasa tajuyo takoma dakinsu tana kuka wardrobe
ta bude taga suit baki daukowa tayi tasa ta daure wandon da dankwali saboda yamata
yawa tasa necktie, rasa yanda zatayi da uban gashin ta yasa ta dauko wani facing
cap data gani tasa ta dunkule gashin aciki tana kuka sosai”wlh saina ganka, saina
kutsa cikin mazanan na ganka,dan Allah karka mutu” kara rike cikinta tayi dataga
yakara motsi ta tashi da kyar tafito. Koda takaraso wurin taga an lullube abu da
fararen kaya ansa amakara jiri tafara gani batasan lokacin data shiga cikin
dandazon mazan nan ta dinga kutsawa har saida ta taba makarar ta rike gam tana
kuka. Muzzammil dake hawaye ya juyo dan yaga me bugeshi garin kokarin kama makara.
Ana saka makarar a mota Rufaida tariga kowa fadawa ciki ta chusa kanta a cinya tana
kuka. Tadaiji mota natafiya wanda hakan yasa ta dago kanta ta kalli kowa Daddy
kadai ta gane acikin mutanen Motar. Kuka tasake fashewa dashi sabo kafin ta zabura
saboda motsin dataji cikinta nayi ta rike cikin gam tana kuka cikeda ihu
tace”kadena min ciwo,wlh saina raka bature gidan gaskiya,inason shi,Allah ya jikan
mijina ” kowa na motar ya zabura yana kallon mutumin da akaji da muryar mace, Dad
yakai hannu ya cire hular gashin ta ya zuba akafada atare Dad da Muzzammil sukace
“Rufaida! Kuka tasake fashewa dashi tana wani irin haki kaman zata mutu, ganin
kowa na motar take biyu biyu ta hade hannayeta da kyar ta iya magana “Dad dan Allah
karka koran zan bishi ne, idan kace a’a zan mut…”bata karasa maganan ba idanunta
suka fara juyawa wani irin mugun jiri ya kwasheta ta sulale kwance a wurin hannunta
daya ya sauka akan farin kyallen da Barraq ke ciki”. Dad
yay salati Muzzammil yaza. ..” Muzzammil yace”Daddy look” ganin farin kyalle na
motsi sosai yasa sauran mutanen cikin motar suka fara neman wurin guduwa. “Daddy
budeshi, doguwar suma ce,he is alive!
Maman Abd Shakur😘

[7/25, 20:28] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


83

Muzzammil yataya Dad suka ciroshi Dad ya warware kyallen jikinshi. Ahankali Baban
muzzammil ya paka mota agefen titi sauran motoci da machina dake binsu abaya duk
suka paka suna mamakin maiya tsayar da motar daya dauko gawa.
Daddin Muzzammil ya bude mota ya fito,Imam ma yafito suka zagayo baya,Muzzammil ya
bude musu da sauri hawaye na kwarara a idonshi ahankali yace “Daddy da ranshi
doguwar suma yayi,mutafi asibiti kawai” Dadin muzzammil yakai dubanshi ga Dadin
Barraq dayasa Barraq a kirji yana hawaye sosai ahankali Barraq ya furta “Boo
water,I need water” Dad ya dago kanshi da sauri yace”Muzzammil bamu ruwa ” kafin
kace kwabo mutanen da suka zageye motar kowa yafara gudun nemo ruwa a shagunan dake
kan hanya. Wani bawan Allah yasamu aka dinga pasin pasin goran ruwan faro saboda
yanda jamaa suka taru har ya iso cikin motan muzzammil ya karba ya bude yabama
Dad,Dad ya saka abakin Barraq da sauri yafara sha rabi na zuba akasa, Dadin
Muzzammil ya gyara mai bakinshi ajikin ruwan yadan sha dadan yawa sanan Dad ya cire
goran a bakinshi. ahankali Dad yace “mutafi asibitin”. Da kyar jama’a suka matsa ma
Dadin Muzzammil da Imam suka fito suka shiga mota akaja, yayinda Muzzammil ya rufe
kofa. Jama’a anata al’ajabin al amarin wato daguwar suma yayi. Aka koma mota wasu
suka bisu wasu kuma suka juya gida tareda fatan Allah bashi lafiya.
Karfe 10:30 P.M. suka isa Baban asibitin garin Abuja mai suna “Handsome Shakur
Specialist Hospital” kwararun likita suka karbi Barraq da Rufaida da gaggawa. Anata
yima Dad gaisuwar Allah bashi lpy mutane na tafiya. Muzzammil yasamu yadan kebe ya
ciro wayarshi ganin kusan 35miss calls din Hafsat yasa yakirata da sauri yay mata
bayanin abunda yafaru. labarin ya girgizata Muzzammil yace duk dare zai dawo
tanuna mai bakomi,ya kula da abokinshi zuwa gobe yazo ya dauketa yakaita ta dubasu
sukai sallama suka katse wayan. Yana gama wayan kiran Mum ya shigo wayarshi da
sauri ya dauka Mum da muryarta ya dishe sosai tace”Muzzammil neman Daugther muke
bamu ganta ba,kuyi sauri ku dawo” Muzzammil yay murmushi dimple dinshi suka bayyana
“Mum kira Daddy danshi yakamata ya baki goodnews dinan” ya katse wayan yayi dailing
number wani abokinshi ishak babban police ne,daya rike matsayin DpO yamai bayanin
komi,DPO yace”gobe da safe zasuzo idan lokacin Barraq zai iya magana dole suyi
magana dashi dan yamusu bayanin maiya kaishi gidan Nana,da sauran vital
informations. Muzzammil yay godiya ya katse wayan tareda komawa cikin asibitin.
Maman Abd Shakur😘

[7/25, 20:28] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


85

Suna fitowa suka tarar da Amma da Muzzammil da Auta dake zaune kusa dashi yana
lallashinta. Dad ya zauna Amma ta tambayeshi ya jikin murmushi ya sakar mata
“cikin nanan bai zube ba,nakusa zama grandpa”.
Farin ciki ya lullube fuskarta. Mum ta zauna gefen Amma tace”any news akan
son ?”Amma ta girgiza kai “har yanzu Dr bai fito yamana bayanin komi ba”. Mum ta
rike kuncinta tana sauke ajiyan zuciya damuwa ya bayyana akan fuskarta. Amma ta
dafa kafadarta “Hey!don’t worry,Barraq is a fighter zai warware,komi zai koma
normal kaman da I promise” Mum ta daura hanunta akan na Amma ta lumshe ido”thank
yhu Amma,tashi muje mu duba daugther” suka mike atare Mum ta bude dakin da Rufaida
ke ciki suka shiga har alokacin tana bacci ana kara mata ruwa. Suka zazzauna.
Dad ya dauko waya ya kira iyayen Rufaida ya sanar dasu komi daya faru bayan tafiyar
su salati Alh yayi ya sanar da ubangiji yace”Allah yabashi lpy, in sha Allah zamuzo
gobe mu dubasu”. Dad yace”no need kaida kakeda maras lafiya” Alh ya sauke ajiyar
zuciyar yace”Akwai abunda ban fadama ba jiya bayan mun dawo,cikin haukar ta ta
sanar mana ita tama Rufaida asiri ta manta damu ta shiga duniya, she’s paying for
wot she did,baruwana da haukan ta ramin muguntar data hakane tafada ciki nida Umman
Rufaida zamuzo gobe, Allah kara musu lafiya yasa kaffara ne ” Dad yace”Ameen”.
Dad ya kalli Muzzammil yace”son kaje gida mana Daugther na nemanka ” Muzzammil ya
girgiza kai “sai B yatashi zan tafi, Dad ina sapayan gilashin shi? ” Dad yadanyi
shiru “baida wani sapayan gilass ,normally a eye clinic dinshi na India idan
gilashin sukai expire yaje biyu suke bashi,so lokacin dayay hatsarin nan a kauyen
Duduwa da bikin ka har gilas dinshi ya kone na tahomai da sapayan yasa,yanzu dole
mu fitar dashi a duba idon achan kafin sumai gilashin dayay suiting idon a yanzu,
but dat will be bayan ya warke ” Muzzammil ya sauke ajiyan zuciya “Allah sa muji
alkhairi” Dad ya amsa da “Ameen “.
Suna zaune a wurin DPO da wasu polisawa guda uku suka shigo Muzzammil na hangoshi
ya tashi ya shigo dasu inda suke ya kalli Dad yace”Dad nakira sune saboda na fadin
musu abunda Barraq yafada min da iya abinda nasani,dan duk wanda yayma Barraq
abunan saina kulleshi” DPO ya mikama Dad hannu suka gaisa kafin su zazzauna.
Ahankali Muzzammil yamusu bayanin komi tun lokacin dayake office Barraq ya kirashi,
harya iso yaga Barraq cikin jini da abunda yafadan mishi. Dad yay mamaki
yace”Nana?Nana dai dana sani? ” Muzzammil yace”Eh ita Dad” Dad yay shairu. DPO yay
rubuce Rubuce kafin ya kalli Muzzammil da Dad yace”kiran sunayen mutanen nan uku da
Barraq yayi acikin jini makes dem our suspects, PA,Duduwa da Nana. Cus muna bama
irin maganan nan amfani sosai,but still zamu so ji daga bakin Barraq idan ya tashi.
And zamu nemo Nana,Duduwa PA dan interrogating dinsu,zamu tafi yanzu zamu iya
dawowa any time dan yimuku tambayoyi idan mun shiga duhu akan binciken”. Ya tashi
yamika ma Dad da Muzzammil hannu suka gaisa. Muzzammil ya taka musu zuwa wajen
asibiti suka shiga mitarsu,kafin ya dawo ciki ya zauna kusa da Dad.
Wuraren 12 na rana likita yafito daga dakin da aka shigar da Barraq, saida ya wanke
hannu da fuska sanan ya zo wirinsu yace”congratulations sir,Barraq is safe and
sound,mutum daya kadai zai iya zuwa ganinshi for now,saidai patient din nata kiran
sunan Rufaida Rufaida sometimes yace”Baby na I suggest akai mai me sunan ya ganta
gaskiya” Dad ya washe baki yacema Dr “thank yhu sosai”, Dr yay murmushi yace “Sir
akaima patient dina abunda yaketa kira plz”,Muzzammil yace”Sure,yanzu ma kuwa”.
Maman Abd Shakur😘

[7/25, 20:28] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


84

Karfe 6 na safe taima Mum da Amma harda Auta da fuskarta tai suntum ya kumbura
saboda kuka a asibiti. Duk suna zaune Dad ya dauki Auta dake kuka yana lallashin
ta wata likita tafito daga wani hadadden Daki. Tana sanye da farin coat data daura
akan riga da wandon dake jikinta,hannayeta sanye da hand gloves,tasanya iD dinta a
wuyanta da aka rubutu sunanta ajiki “Dr Rukayya Sadau”. Takaraso ta tsaya agaban su
Dad tace”Ina iyayen Patient Rufaida? ” Dad ya mike da sauri tace”ku biyoni office ”
Dad da Mum sukabi bayanta. Ta zauna su Dad suka zauna bude file din Rufaida tayi
tana yan dube dube da karance karance. Kafin ta kalli Dad tace”Sir jiya kace bata
dade dayin bari ba da ina tambayarka akanta?” Dad ya gyada kai “yes tai bari 2 days
ago” “an mata wankin ciki ne bayan tai barin?” Dad ya girgiza kai”no,Doctor yace
cikin yariga yafita basai anyiba, kawai mu dinga bata abinci mai kara jini ajiki da
magungunan daya bamu” Dr Rookey Sadau tadanyi rubutu acikin file din kafin ta dago
kanta ta kalli su Dad murmushi Kwance akan fuskarta tace”Cikin bai fita ba,sun
tsayar da jinin da wuri,maybe saboda yanda tai bleeding din yasa basu gane da wuri
cikin nanan ba,but cikin yarku nanan for now inhar zakubi kaidodin dazan baku ” Dad
yama kasa magana saboda farin ciki Mum ce tai magana “menene kaidodin?” Dr Rookey
tace”ku hanata daga any object ko abu mai nauyi,sanan any exercise irinsu tsalle-
tsalle,guje-guje da dirke-dirke tadena yi saboda suna kawo zuban jini hakanan ko
zubar ciki ma. zaku kiyaye abubuwan cinta tana yawan cin abinci mai kara jini
sanan ta guji abinci mai siga sai shawarwarin dazan baku shine Mai ciki ta dinga
yawan cin wake saboda yana karama yaron cikinta kaifin kwakwalwa sanan yana bama
maiciki ruwan Nono sosai. Shan kankana yana gyara fatar yaro acikin ciki,kuma yana
karama yaro kaifin kwakwalwa. Cin ganyen irinsu ugu da alayyahu yana kara jini
ajikinsu,Sanan alokacin da mace keda ciki wanda ke yawan sata amai tadinga cin
kwakwa (coconuts)da rake(sugar cane) yana rage yawan amai. And suna hana yaro ya
dinga kurjaren zafi, wutar dare and d rest bayan an haifeshi,kuma suna rage ciwon
nakuda. Cin dabino(Dates) strengthen the muscles of the uterus akarshen watan
haihuwa. Kuma Yawan cin dabino yanasa mace ta bude ta cikin sauki batare da an
karata ba a lokacin haihuwa. Cin dabino ga mai ciki dama wacce ta haihu yana karama
ruwan Mama elements din da ake bukata na karama yaro lafiya da kariya daga kowace
irin cuta. Sanan sai shawarwarin kula da yanayi (mood)din datake ciki. Yanada kyau
mai ciki ta kasance cikin farin ciki kowani lokaci,ta kalli abu mai kyau,taji abu
mai kyau,ta sha abu mai kyau,ta shaki kamshin abu mai kyau. Dan ko wani hali mai
ciki ke ciki haka dan cikin ta ke ciki. Yanada kyau mai ciki ta nisanci bakin ciki
ko bacin rai,sanan kartaji haucin kowa kota tsani wani abu,ko ta dinga bakin ciki
dawani. Dan duk hali /yanayin damai ciki ke ciki yana affecting yaron cikin ta. Ta
kalli Mum tace” Ma ko film din ban tsoro baaso mai ciki na kallo inhar suna bata
tsoro irinsu vampires films,Horror films and d rest duk bai kamata ba. (It is
important to have good feelings,good thoughts, and not to carry grudges,have fear
of something or be unduly worried about something. A pregnant woman should remain
calm,happy and should not be allowed to be over concerned and allow herself to be
overtaken by grief. The thoughts you generate within urself will affect the kind of
disposition the child will have. If u are sad and miserable the child will be
equally affected. REMEMBER! it is the mother’s womb that is carrying the baby and
that the baby is affected by whatever she is thinking, feeling, reading and
listening to. It is better and advisable for a pregnant woman to keep a good
company, to read good books. Example The Holy Qur’an.) likita tace “zaku
iya tafiya sai jibi zamu sallameta dan 16prime ce,we need to monitor her” Dad da
Mum sukai godiya suka fita. NOTE:Duk abunda
nafada akan mai ciki yakama ta tayi hakane,gaskiya ne,Allah sa wasu su amfanu da my
little ilimi, Ameen.
Maman Abd Shakur😘

[7/25, 20:28] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*


86

Dr Rookie Dad yay ma bayanin komi babu bata lokaci tasa nurses suka gungura Rufaida
zuwa dakin da Barraq yake batare da anbar su Dad sun shiga dakin ba.

Da kyar Barraq ya furta “My Rufaida kece?”Jin motsin dayayi a dakin Dr Rookie tai
murmushi takama hanun Rufaida ta saka a cikin hanunshi tace”ga Ruffy dinka
anan,bacci take,karkai magana da yawa cus of ur condition,take care” tajuya ta
mayar musu da kofa tafita. ahankali Barraq ya murza hanunta tareda lumshe ido “get
well soon Baby na,naso zan iya ganinki yanzu”yakai hanunta kan bakinshi ya sumbaci
hanun ahaka bacci yay gaba da shi.
Washe gari akabar Su Dad suka shiga ganinsu har alokacin bata tashiba sai Barraq da
idonshi biyu Mum ta rungume shi gam tana kuka Auta ma haka da kyar sukai shiru. Dr
yabama Dad takardar transfer zuwa India saboda yimai gilash.
Karfe 12:Am na Rana Rufaida ta farka ahankali ta tashi zaune daga gadon da kyar
tana yatmutse fuska. Kallon dakin tafara bataga kowaba,daga hanunta dazatayi da
zumar sosa fuska taji kaman an riketa, da sauri ta juyo ganin Baturen da tasan ance
yamutu yasa taji kanta yafara juyawa yayinda zuciyarta ke tashi tanajin wani irin
amai na taso mata, bata ankara ba tafara kwara amai da bakomi ciki sai ruwa yellow
Mum dake zaune wajen dakin tana karanta jarida ta ajiye a gefe ta shigo dakin da
sauri ganin Rufaida na amai yasa takoma waje da gudu takira Dr. Dr da Nurses suka
biyo bayan Mum aka shigo dakin daura Rufaida sukayi akan gado suka fita da ita zuwa
dakinta. Barraq yace Mum maiya sami Rufaida? ?ta rike hanunshi Son karka damu amai
ne kawai.

**********

Bayan sati biyu.

Zaune Rufaida take a falon Amma ta tasa dan wake agabanta tana kallo takasa ci ko
kadan. Ta rame sosai tayi wani irin haske. Kirjin da baya ne kawai acike dam. Amma
ta zauna kusa da ita tace”Rufaida kefa kika daman na miki dan wake kuma kin kici,ko
kinfiso sai Auta ta dawo daga makaranta ta tasaki agaba tana kuka kafin kici?kin
manta fadan da Umman ki da Abbanki suka miki jiyako?” Rufaida ta girgiza kai tana
share hawaye “Amma ni bature nakeson gani,kunce yana raye amma ni ban ganshi ba,tun
randa na ganshi a mafarki harna dinga Amai ban kara ganinshi ba” Amma tai murmushi
“oya ci koda kadanne nabaki albishir mai dadi kiji” tadan kalli Amma,Amma ta gyada
mata “trust me,I promise zakiji dadin news din,amma kifara ci dan rabonki da abinci
tun jiya da daddare da Auta ta tasaki agaba kikaci yam balls,so kike bebin cikin ki
ya rame? ” Rufaida ta girgiza kai tareda sa hannu aciki plate din tafara ci
ahankali har taci rabin plate sanan ta kalli Amma nakoshi. Amma ta shafa kanta
kafin ta mika mata maganin rana tasha da kyar sanan tace “Amma fadamin?” Amma tai
murmushi “dazu kina bacci Dadin Auta yakira yace min yau zasu dawo dashi da
Muzzammil da Barraq dinki ita kuma Mum zata wuce Russia dan tanada case a chan ana
nemanta” cikin murna Rufaida ta rike hanun Amma tace”Amma wanan baturen shine
Barraq ko,shine zai dawo? ” Amma ta gyada mata kai tana murmushi, murmushi Rufaida
tasake yi tareda chusa kanta tana murmushi Amma tai dariya oya tashi ki dauko
hijabin ki na kaikai Zee Hamza saloon wata yar katsina amiki gyaran jiki dana
gashi da kunshi.
Karfe 5:00 na yamma suka dawo Rufaida sai sheki take fuskar nan tai kyau. Amma ta
kaita part din Barraq tahada mata ruwan turare tai wanka dashi. Amma tace bari naje
na duba abincin da Fauzeeya(yar aiki)ta hada. Ta wuce tafita. Rufaida tai wanka
tafito ta zauna a gaban madubi tana kallon lallin da akamata dake burgeta. Ahankali
tasake mikewa ta dauko wata katuwar handbag ta juye akan gado tana murmushi “Umma
na nagode da kayan kwalliyan da kika kawomin” kwalliya tayi sosai tai kyau sanan
tasake dauko katuwar jakar da Umma ta kawo mata taciro wani bakin 3quarter wando
wanda da kadan ya wuce guiwa da Jan shimi armless anmai kwalliya da fulawowi
bakake,saka kayan tayi ta chusa shimi cikin wandon (zanzaro)tadau wani kacha da
yazo tare da wandon a matsayin belt ta zura ta kulle tareda sakinshi yabi gefen hip
dinta ya kwanta. Zama tayi agaban madubi ta zira jan dan kunne karami yana walkina
kaman Diamond tadau wani hair clip jajaye masu suffan kananun fulawowi ta jerasu
agaban gashinta abin yay mata kyau sosai takara dawowa yarinya sak. murmushi tadan
saki ta kalli madubin tai mai fari”toni kai madubi mena kallona?,ai dai ban cema
inason bature ba “ta murguda baki”am just soo excited yau bature zai dawo” tasa
tafukan hanunta ta rufe fuskarta “to uhm, uhm ai jiya da Umma tazo tace nadinga
gayu,nai gayu sosai randa bature zai dawo” da sauri ta mike tsaye”laaa turare na da
Umma tace nasa duk randa zai dawo” da sauri tasake bude jakar ta dauko wani dan
karamin kwallba ta bude ta tsiyaya turare a hanunta ta murza ta shafe jikinta dashi
tareda lumshe ido jin wani sassanyar kamshi na shiga jikinta. Jin ana kiran sallan
mangari ba yasa ta shimfida dadduma tai salla takara gaggyara dakin ta wuce falo ta
kwanta akan kujera tana kallon “Love is timeless” ko minti sha biyar batayi da
fara kallon ba Bacci yay gaba da ita.
Suna fitowa daga bangaren ya kalleta ya shafo kanta”Auta na ki koma daki kije kiyi
karatu, ba kince min gobe kunada exam ba?”Auta tadan zumburo baki “but Uncle B i
missed yhu saisa nakeson na bika na kwana a part dinku” da kyar Barraq ya hadiye
yawun daya taru a bakinshi yadan zaro ido”Okay Okay Auta naji amma yanzu kifara
komawa part dinku revise ur book very well anjima saina zo mutafi ki kwana tareda
mu “murmushi ya bayyana akan fuskar Auta tasaki Uncle B tajuya tace”to zanyi
karatun sosai yanda bazan manta bako?” Barraq ya gyada kai good gurl tajuya takoma
part dinsu. Yayinda Barraq yay murmushi yaja trolley hanunshi zuwa part dinshi.
Ahankali ya bude kofar dakin wani sanyayyen ni’imantaccen kamshi ya ziyarci
hancinta. Ya lumshe ido ya bude.
Maman Abd Shakur 😘

[7/25, 20:28] Aishat Muhammad: *KAINE SIRRI NA*

87

Kafin ya daga kafa ya shiga falon ya maida kofa ya rufe. ware ido yayi hango abu
mafi soyuwa agareshi kwance tana bacci cikin kwanciyan hankali. Karasa wa gaban
kujeran yayi ya tsugunna yana kallon ta shimin ya zazzago yanda ta kwanta hakan
yabashi daman ganin abunda yafiso gani, lumshe ido yayi da sauri jin wani irin
shock nabin jinin shi. Ahankali yasa hannu ya shafa lallan dayaga an mata a hannu
dan ya mugun burgeshi ga fatar ta yakara taushi ya daura hannu akan cikinta ya
lumshe ido” My Baby Allah rayamin kai,baka taba gaisawa da Baban ka bako?”Yadan
bude ido kadan “don’t worry yau dole na gaisa dakai” Ahankali ya dukar da bakinshi
yakai saitin kunnen ta “My Rufaida ur Husby is back” turo baki tayi cikin barci
takara muskuta wa cikin bacci. Barraq yakai ganinshi wurin abun dake kara tadamai
hankali. Hanunta yadan daddaka ahankali”Baby na Baby na ” bude ido tayi kadan ta
kalleshi ganin bature tsugunne agabanta yakara haske gashin kanshi ya kara kwanciya
ga sabon farin gilashin da akamai yafi nada kyau da karbanshi yasa takarasa bude
ido gabaki daya ta kalleshi murmushi ya sakar mata “tashi nine nadawo” tashi tayi
zaune idanunta suka ciko da kwalla tana kallonshi “kaine ko yauma mafarki nakeyi?”
Barraq yay murmushi “nine mintsile ni kiji” ya mike tsaye itama ta tashi takai
hannu ta taba fuskarshi taji ta taba fuska kuka ya kufce mata Barraq ya bude hannu
tafada kirjinshi tana kuka sosai,ya kwantar da kanshi a kan gashinta yana shakan
kamshin dake neman sa hankalin shi ya gushe dago kanta tayi daga jikinshi ta zame
jikinta daga nashi ta juya taji Barraq ya rike mata hannu”ina zaki? ” idanunta
alumshe cikin karamar murya tace”fitsari nakeji sosai” saki ta yayi tajuya tana
tafiyan ta mai daukan hankali daya kara birkita Barraq harta shiga bayin ya sauke
ajiyan xuciya yafada kan kujera yana rage kayan jikinshi.
Koda tafito daga bayin ta tsaya tai salla issha ta cire hijabin jikinta ta linke ta
ajiye ta dawo falon daga shi saidan farin boxer ta ganshi ya rike glass cup zuma
aciki cike yana sha yayinda dayan hanunshi ke dauke da remote yana kallon News.
Baisan da shigowar taba yadaiji alamun ana kallonshi hakan yasa ya juyo da kanshi
karaf idanunsu suka hadu da sauri ta juya tana yarfe hannu bakinta na rawa
tace”na..uhm. .na. .kawoma ab…abinci?ya..ya jikin ka..?” Murmushi ya danyi ya
ajiye kofin zumar akan kujera ya tashi batai tsammani ba taji an rungumeta ta baya
jikinta yafara bari “am okay banajin yunwa “ke kinci abincin?”ta gyada mai kai tana
kokarin tureshi kara matseta yayi kafin ya juyo da ita yahada bakinshi da nata yana
tsotsa da zafi zafi.

Kuka Rufaida tasaki sosai ta tureshi “ka sakeni,me kakemin,banaso” Barraq ya


girgiza mata kai,muryarshi adishe yace”No” Fuuu tajuya ta shiga cikin daki ta bugo
kofa Barraq yakoma kan kujera ya zauna yakara sa shanye zuman shi ya kashe kallon
ya kashe wutar daki yatafi bedroom a kwance ya ganta tana dandanna waya ko kallo
bai ishetaba wutar dakin ya kashe kafin ya kwanta akan gadon yay shiru chan kuma
ya tashi yafita daga dakin da sauri ya koma falo ya kwanta akasa flat ganin hakan
yaki taimakonshi yasa yafara sit up.
Kunna wuta dataji anyi yasa ya tsayar da sit up din dayakeyi ya juyo yaga Rufaida
ce sanye da farin kayan bacci shara shara iya guiwa. yacigaba da abunda yakeyi.
Ahankali tazo kusa dashi ta zauna bai kalleta ba hakan yasa ta murguda baki “kai
Baturen nan maina barina ni kadaai adaki kasan bana iya bacci ni kadai ko?”
Yadan kalli yanda take turo baki aranshi yace”tasha kuka da rashin lpy dabana nan,
amma yanzu jibeta ta ganni tafaramin tsiwan dis new Rufaida en… kwanciya tayi akan
kafanshi “wlh bazaka sakeyin wanan abun ba,inama ma magana kayi banza dani ko?”
Barraq ya murguda mata baki,da sauri ta tashi ta zauna ta ware ido tana kallonshi
“laaa ka iya murguda baki dama? kai baturen nan kai tamace ne? ” bai kulataba sai
rungumeta tsam dayayi a jikinshi yafara aikamata da sakonni masu zafi, data nemi
kwace kanta takasa. Ahankali ya rada mata a kunne”Amarci da new Rufaida zan fara
yau”.
Maman Abd Shakur 😘

mamanshakur Is all about novels.


Skip to content
Home
About
TSAFI 1to 11
← KAINE SIRRI NA 77to87TSAFI part 2. 1-13 →
KAINE SIRRI NA 88 TO D END
Posted on July 31, 2016 by mamanshakur
[7/27, 12:44] I’m me.: *KAINE SIRRI NA*
88

Rufaida ta bude baki zatai ihu yahada bakinshi da nata yana bata wani irin hot
kiss. Kuka tafara jikinta ko ina na rawa hakan yasa ta mugun bashi tausayi. Sakinta
yayi da kyar ya iya magana “Baby na relax,am not going to hurt yhu,we’ve done dis
before kinji my Rufaida” kuka tasakin mai “Dan Allah bature kadena,ni wajen Amma
zani a chan zan kwana” girgiza kai yayi”Baby na No plzx ki yarda dani,I don’t want
to force yhu bcuz of yhur condition,ni mijinki ne karki shiga tsinurwar mala’iku
kinji”ta girgiza mai kai tana hawaye,murmushi ya sakar mata ya kwantar da ita akan
kujera yaje ya dauko bargo ya shimfide a tsakar dakin ya kashe wuta ya dawo kusa da
ita yarike hanunta yana murzawa,ahankali yake bi da ita harya cimma burinshi
Rufaida tasha kuka kaman zata mutu dan taji mugun zafi. Barraq kam babu wanda ya
kaishi farinciki dan saida ya fanshi duk watanin dabaiyi ba. Rufaida ta galabaita
iya galabaita.
Shigowar shi gidansu kenan fuskarshi dauke da murmushi alamun yana cikin farin ciki
yana sanye da faran jallabiya alamun daga masallaci yake wayarshi ce yay kara ya
tsaya yaciro ta daga aljihu dauka yayi ganin sunan friend a jiki ahankali yace”wot?
DPO wants to see Rufaida?But Boo kasan banason Rufaida takara ganin Duduwa in her
life,much less Nana,kawai ya yanke musu hukunci but Bazan bari Rufaida taga Duduwa
ba saboda yanda take tsoron ta,bye kome DPO yace just let me know,regards to Madam
da bebin daya kusa zuwa ya ganni “yay dariya ya katse wayan tareda karasawa part
dinshi.
Dakin ya shiga ganin har alokacin Rufaida na bacci yasa yay murmushi ya zauna kusa
da ita ya tankwashe kafa ya rike hannu ta “wai haka masu ciki ke yawan bacci?”yadan
lumshe ido ya bude maisa banzama likita ba?only inda hanun agogo na komawa baya da
saina komar dashi baya na zama likita for yhu Baby na” yay murmushi yakara lumshe
ido”Allah na godema da kabani Rufaida a matsayin mata,kakuma azurtani da baby,Allah
ka sauketa lpy ” Ganin 8:30 na safe yasa ya duko da kanshi yafara tsotsan bakinta
motsi tafara kafin ta bude ido ganin Barraq yasa ta maida idanunta ta rufe ruf tana
tattara zanin tana kara lullube jikinta dashi murmushi yayi ya dagata sai bayi …
saida yaga ta tada kabbaran sallla sanan ya fita dan amsa kiran Dad daya gani akan
wayarshi.
Maman Abd Shakur 😘

[7/27, 12:49] I’m me.: *KAINE SIRRI NA*


89

Falon Dad ya shiga da sallaman shi ganin iyayen Nana a zaune yasa ya gaidasu yaje
kusa da Dad gani Dad. Dad ya sauke ajiyan xuciya “zauna son magana iyayen Nana
zasuyi da kai”. Baice komiba ya zauna.
Mahaifiyan Nana yafara magana “Barraq dan Allah kayafe ma yarmu, hakika Nana ta
tafka BABBAN KUSKURE (littafi Rash kardam) wanda a yanzu take ganin sakayya kuru
kuru”Alh ya danyi shiru kafin ya cigaba “jiya misalin nine na dare,DPO ya kirani
awaya nazo police station Nana batada lpy kuma tanason ganina,koda naje naga karin
ruwa ake mata ,dana tambayeta maiyake damunta tafara kuka sosai tarikemin hannu
tace na yafe mata,nakuma rokeka kayafe mata,hakkin kane ke kamata,ban kulata ba dan
haushin ta nakeji akan abunda tamana wanda yaja yanzu zumincin dake tsakanina da
babanka na rawa, nakara cewa maiyake damunta da kyar tace min ciki takedashi” Dad
da Barraq saida suka kalli Baban Nana saboda tsananin firgici.
“Ciki gareta,na tambaya waya mata wai megadin gidanmu, wlh ban daketa bane kawai
dannasan inna tabata karasa mutuwa zatayi amma nace kotana so kobata so saita auri
mai gadi, kuma saita haifamai yaronshi. Matan mai gadi uku kuma duk suna kauyensu
yaranshi 11, namai magana yau yace yana sonta zai aureta. Da haka nake rokon ka
Barraq dan girman Allah kayafe ma Nana,ka janye shari’an,nasan itamai laifi ce amma
kuyafe mata D’A NA KOWA NE (littafin Babeelo) kuyafe mata Dan girman Allah”.
Barraq yay shiru kanshi akasa, Dad ya daura”son kayafe mata ka kuma janye case din
tunda ai cikin ma bai zubeba,kasa asaki Nana,Duduwa da shi P.A. bakomi musulmi ya
kasance mai yafiya da hakuri kaji son”.
Barraq ya girgiza kai”Daddy na yafe musu duka, dudda abunda Nana tamin abaya but
tamin abunda bazan manta dashi ba,saida tai iyakan kokarin ta na ganin ta hana P.A.
kashe ni na yafe musu,itakuma Duduwa na yafe mata saida har abadan bata ba Rufaida
tunda mun riga munsan gaskiya tafada mana danta ne ya tsinci Rufaida a kauyen
su,shikuma PA bansan mexan ce akanshi ba,but one thing is for sure inhar kace ka
tsani wani bawan Allah a kullum burinka kaga bayanshi,kokuma ka kasheshi to tabbas
wataran kanka abun zai koma,kaine zakaga bayan kanka,ka kuma kashe kanka”.
Ya ciro wayarshi atake yasa aka saki PA Duduwa da Nana. Baban Nana yay musu godiya
sosai yatafi Dad ya kalli Barraq “am proud of yhu son Allah ya maka albarka,yaushe
Daugther na zata fara antenatal?” Barraq yadan sudda kai cike da kunya ahankali
yace”very soon Dad” yafita da sauri Dad yay murmushi yakira Mum a waya ya sanar da
ita komi.
Maman Abd Shakur 😘

[7/27, 12:58] I’m me.: *KAINE SIRRI NA*


90
Aranan da karfe 4:00 ya yamma bayan an idar da sallan laasar jaama suka shaida
daurin auren Nana da mai gadi. Mai gadi bakinan kaman gonar auduga Nana tai kukan
da tunda take a rayuwarta bata tabayin irinshi ba,ta tsani mai gadi a rayuwarta, ta
tsane shi gashi kaxami, kullum doyi yake mezatayi dashi. Ahaka Dadin ta yabama mai
gadi naira dubu dari yafara sana’a idan yaje kauye yatafi da Nana su raini cikinsu
dan wata uku da kwanaki tare. Ya amsa da to yarike hanun Nana dake kuka suka shiga
adaidaita sahu dan ya kaisu tasha su shiga motar kauyen su mai suna kwarin ayuba.
Duduwa polisawa suka sata a motar dazai maidata kauye a tasha suka kara tsoratata
da bindiga duk ranan data sake dawowa Abuja saisun karyata sun kasheta ta tsorata
ainun tace billàhillaxi bazan kara dawowa ba.
P.A. kuwa aka sakeshi tareda shaidamai ko ciwo akaga Barraq yasakeyi ko iyalanshi
kowani nashi, Shi zaa kama, bashi ba Barraq haka yatafi ya tarar da gidanshi Barayi
sun shiga sunmai satan duk wani abun kudi a gidan da kadarorinshi haka ya tsugunna
ya dinga kuka…
“Bature dan Allah kayakuri karka sakeyi nagaji” Barraq yay murmushi ya sumbaci
goshinta “okay shikenan, tashi muje muyi wanka anjima zamu koma gidan mu yanda
zamufiyin soyayya da kyau ko? ” murguda baki tayi”ni ni bawani soyayya,ni banason
baturen nan” Barraq ya kyalkyace da dariya Rufaida ta turomai baki “yace ni kikace
bakiso ko?to daga yau bazaki kara ganina ba,zanje na auri mai sona” ya tashi zai
shiga bayi yaji ta riko hanunshi ya juyo ya kafeta da ido dariya na neman kwacemai
idanunta sukai raurau tadan yarfe hannu”tokai baturen nan bafa ka gane hausana
bane, ina sonka kadan fa,kaji” Barraq ya tsura mata ido da sauri tafada kirjinshi
tana kuka “Allah ni inasonka, kaji karkaso wata plzzzz” Barraq ya kara matseta a
jikinshi yana lumshe ido”I luv yhu darling Rufaida”tadanyi murmushi kafin ta dago
kanta ta kalleshi “kasan wani abu?”Ya girgixa kai “aranan da Umma tabani labarin
rayuwata nada,Mum kuma takara bani sauran labarin naji nakara sonka,inaso nagode
ma,Ubangiji Allah ya sakama da mafificin alkhairi, ka kasance KAINE SIRRI NA
ada,ayanzu kuma ka riga ka zamto KAINE SIRRI NA Uncle B” ta lumshe ido tareda kai
bakinta ta daura akan nashi kasa magana yayi saida ya gama karban sakon nata sanan
yace “Babyna you just call me Uncle B” murmushi takara sakin mishi takomar da kanta
kirjinshi “I remember everything jiya,bayan na idar da salla na bika falon Dad
inaso na gaisheshi sainaji kuna magananganu sunan Duduwa danaji Dad ya ambato yasa
kaina yafara juyawa na dawo daki da sauri na zauna, ahankali komi ya dawomin natuna
komi da komi”. Barraq ya kankameta “Alhamdulillah am Glad,I luff yhu My Rufaida
Allah barmu tare” Tare suka shiga sukai wanka Rufaida na tattalin Barraq na
musamman. Kullum tana waya da Umman ta. Yayinda sukai plan da Barraq miliyan biyun
da gwamnati suka bata zatakai miliyan daya gidan marayu daya kuma asibiti ataimaki
marasa lafiya.
Bayan shekara Uku.

Zaune Rufaida take acikin study takara kyau da kiba da haske. Katoton textbook din
Human Anatomy a gabanta tana karan tawa,bude kofan da akayi aka shigo yasa ta dago
kanta ganin Barraq daya kara murjewa yay jajir yasa ta tashi tafada jikinshi
tanamai oyoyo rungumeta yayi “Babyna har yanzu baki gama karatun ba?” Tai murmushi
“no inatayi banason na fadi a exam dina,ina karatun medicine ne bcuz of yhu My
Qalb” ta kamo hanunshi ta sumbaci hanunshi ganin yay fuskan damuwa tace”Hey!don’t
worry, bandamu ko zanyi karatu daga yanzu har jibi batare da nai bacci ba,zan zama
likitan ido ne saboda na nemama idonka magani,u did everything to me,fatana Allah
yaga zuciyata da niyya ta yacika min burina na gama karatun likitanci na na nemoma
mijina maganin ido ya warke ” Barraq ya rungumeta “am proud of yhu,ina alfahari
dake,I luv yhu soo very much my fear fear cry cry Rufaida ” ta kaimai duka akafada
tana murguda baki dat was den kaima kasani ” Barraq ya tabe baki har yanzu dai
anamin ” dukansu suka hau dariya.
Am missing Lutfullah (kindness of Allah) soo much gidan ba dadi bayanan. Barraq yay
murmushi “don’t worry nextweek Mum zata dawo dashi saboda ankusa komawa school,but
guess wot?”Rufaida ta zaro ido “Muzzammil da Hafsat zasuzo anjima zasu kawo mana
Madina zatai mana sati daya”. Rufaida tai murmushi “Oh wow,nai missing Mimi
ta,gwara su kawomin ita ta zauna dani tunda Lutfullah yabi grandma dinshi” Duk
sukayi dariya.
“Mezan dafama kasha ruwa dashi?” Kashe mata ido yayi yace”yhu’ dukansu sukai
dariya. Rufaida tace “Qalbi ya kukayi da Nana?” Barraq ya sauke ajiyan zuciya
“nabata kudi masu yawa tafara business saboda ta kula da yaranta uku tasasu a
makaranta,itakuma Duduwa nariga na biya kudin yau zaa guntule kafan dan ya rube
yana tsutsa. PA kuma nabashi gadin gidan gonan Dad das all” Rufaida ta rikemai
hannu”thanks for listening to my advice, Allah yakara ma budi, naji dadi daka
taimakesu. U are my everything, KAINE SIRRI NA”. Barraq yay murmushi KECE SIRRI NA
My Rufaida suka rungume juna ahankali yaji tarada mai A kunne “ur second Baby is on
his way,8months yarage” Barraq cike da murna yace”are yhu serious? “Ta gyada mai
kai,Oh nakosa nasha ruwa na gaisa da Baby na” tamai kiss a kumatu “bari naje nakira
Mum naji muryan kiddo”yabi bayan ta “nima am missing champion”.
ALHAMDULILLAH!
MAMAN ABD SHAKUR😘

[7/27, 13:02] I’m me.: *KAINE SIRRI NA*


ALHAMDULILLAH anan nakawo karshen littafina KAINE SIRRI NA. Kurakuren dake ciki
Allah ya yafemin.
Na sadaukar da littafin nan nawa ga marubuta uku.

Beebaluv marubuciyar SAINAGA UMMU SHAKUR $ABDUL SHAKUR.

My Tawa ce AKA Hafsat Ibrahim Marubuciyar SAINAGA HAUWA JABO DA M SHAKUR.

My Rashy AKA Rash Kardam marubuciyar BABBAN KUSKUREN DANA TAFKA.

I luv yhu All Guys Allah yabar kauna yakuma barmu tare,thanks for d luv.
Littafinan nawa tukuicine ga duk mai suna RUFAIDA, I soo much luv d name,in Allah
ya yarda duk randa ubangijin na Allah ya azurtani da ya mace zan saka mata suna
RUFAIDA.
A big thanks to my Huge fan SAFFIYYA MUHAMMAD RABI’U,I luv yhu deeply,and I
appreciate yanda kike shairing novels dina to all d needers in both Facebook and
watsapp,thanks to yhu Sofie.
My group members.

Fulani ta

Rookie sadau

Hj Ricifa

Mairo

Aisha zagee

Ruky Mama

Kunfi kowa son dis novel. I luv yhu All.

Ina gaisuwa ga masoyana na Facebook luff yhu All.


At Dis Moment I will like to ask my fans tambaya na karasa muku TSAFI kona fara
sabon novel mai suna UMMARU NA YANKA…. takenshi:Bana wasa,ban kuma san wasa
ba,chau-Chau! Story by MAMAN ABD SHAKUR and Directed by KHALEESAT HYDAR.

Masu son tsafi ko ummaru na yanka zaku iya bibiyata ta wanan nambar, wanda akafi
zaba shizanyi nan da one week.07032934950.
Follow me on

Facebook:Aishat Muhammad
Instagram:Aishat Muhammad.

Blog:mamanshakur.wordpress.com
E-mail me on

Email :sarauniyaaishat2k@Yahoo.com
Gmail:sarauniyaaishat2k@Gmail.com
I love

You might also like