You are on page 1of 8

Aske wani sashi na gashin kai (Al-Ƙaz’u)

Ya tabbata a cikin Sahihul Bukhari da Muslim, daga Abdullahi bin Umar (a)
cewa: Manzon Allah ‫ ﷺ‬ya yi hani game da yin Al-Ƙaz’u. Ma’ana aske wani sashe
na gashin kai, a bar wani sashen. Shi kuwa hani yana bayuwa ne zuwa ga haramci.

Ma’abota ilimi suka ce: “zai shiga cikin wannan aski da aka hana (Al-Ƙaz’u),
mutum ya aske wani wajen a gashin kansa, ko ya aske tsakiyar gashin, ya bar sauran
ɓagarorin kamar dai yadda yawancin Nasara (Kiristoci) suke yi, ko kuma mutum ya
aske gefen gashin, ya bar tsakiyarsa, kamar yadda yawancin wawaye suke yi, ko ya
aske gaban gashin ya bar bayansa.

Yin lalle a gashin Manzon Allah ‫ﷺ‬:

Malamai ma’abota ilimi sun yi saɓani; wajen tabbacin shin ko Manzon Allah ‫ﷺ‬
ya yi wa gashinsa lalle? A cikinsu akwai waɗanda suka kore hakan. Akwai kuma
waɗanda suka tabbatarwa. Sai dai abin da ya fi inganci shi ne cewa; Manzon Allah
‫ ﷺ‬ya yi lalle.

HaƘiƘa an tambayi Abu Huraira (a) shin Manzon Allah ‫ ﷺ‬ya yi wa gashinsa
lalle? Sai ya ce: (Ƙwarai kuwa.) Imam Tirmuzi ya ruwaito wannan Hadisi, a cikin
littafinsa (Ash-shama’il), kuma Imam Albani ya inganta Hadisin.

Kamar yadda Bukhari ya ruwaito daga Hadisin Abdullahi bin Wahab ya ce: “Na
shiga wajen Ummu Salama (a), sai ta fito mana da gashi daga cikin gashin Manzon
Allah ‫ ﷺ‬wanda aka yi wa lalle”.

Daga ibn Umar (a) cewa: Annabi ‫ ﷺ‬ya kasance yana sanya takalmin
jemammiyar fatar Saniya, kuma yana rina gemunsa da warsu ,da za’afaran, Ibnu
Umar a ya kasance shi ma yana aikata haka. Abu Dawud da Nasa’i sun fitar da
wannan Hadisi, kuma Imam Albani ya inganta shi.

133
Tsokaci:
Babu laifi maza su rina kansu da lalle. Saboda abin da malaman Hadisi suka
ruwaito daga Abu Zarrin (a) daga Annabi ‫ ﷺ‬ya ce: “HaƘiƘa lalle da katamu su ne
mafi kyawun abin da zaku sauya gashinku da shi”. Imam Albani ya inganta wannan
Hadisi.

Sai dai rina kai da baƘin lalle tsantsa; bai halatta ba ga maza da mata. Saboda
faɗin Annabi ‫ ﷺ‬cewa: “Ku sauya wannan furfura, amma ku nisanci (baƘin) lalle”.
Muslim ya ruwaito wannan Hadisi.

Kamar yadda Abu Dawud ya ruwaito, daga Ibn Abbas (a) cewa: Manzon Allah
‫ ﷺ‬ya ce: “Akwai wasu mutane da za a yi a Ƙarshen zamani, suna sa baƘin lalle (a
gashinsu), kamar gashin Ƙirjin tantabaru, ba zasu taɓa jin Ƙanshin Aljanna ba”.

Abin da yake wajibi shi ne, an hana duk wani irin rini, ko lalle da zai zama mutum
yana kama da mata, saboda hanin da Manzon Allah ‫ ﷺ‬ya yi game da kamanceceniya
da mata, da kumaa tsinuwar da ya yi ga wanda yake hakan.

Umarni da a cika gemu:

Manzon Allah ‫ ﷺ‬ya yi umarni da a cika gemu. An karɓo daga Abdullahi bin Umar
(a) ya ce: Manzon Allah ‫ ﷺ‬ya ce: “Ku aske gashin baki, ku cika gemu”. Bukhari
da Muslim ne suka ruwaito wannan hadisin.

A cikin wata ruwayar ta Bukhari da Muslim ya ce: “Ku saɓa wa Mushirikai, ku


kai matuƘa wajen aske gashin baki, kuma ku cika gemu”.

Abin da wasu mutane suke yi na aske gemu, ko kuma rage tsayinsa, ko faɗinsa
hakan bai halatta ba. Saboda hakan ya saɓa wa tafarkin Manzon Allah ‫ﷺ‬, da ya yi
umarni da a yawaita gemu.

134
Sheik bin Baz ya ce: “Duk wanda ya kafa hujja da maganar Ibn Umar (a) cewa
ai ya rage gemunsa, na abin da ya Ƙaru da kamu ɗaya, to mutum ba shi da wata hujja
a cikin hakan. Domin wannan ijthadi ne daga wajen Ibn Umar (a). Ita kuma hujja
tana cikin abin da ya ruwaito, ba cikin ijtihadinsa ba.

Gemun Manzon Allah ‫ﷺ‬:


Gemun Manzon Allah ‫ ﷺ‬cikakke ne, mai kauri. HaƘiƘa Nasa’i ya ruwaito daga
Barra’u bin Azib (a) ya ce: “Manzon Allah ‫ ﷺ‬ya kasance mutum…mai yawan
gemu, kuma gemunsa mai kauri ne”.

An karɓo daga Aliyu bin Abi Ɗalib (a) cewa, Manzon Allah ‫ ﷺ‬ya kasence yana
da gemu mai yalwa. Ahmad ya ruwato shi, Albani ya ce: “Hadisin mai kyau ne”.

135
Auna Fahimta

 Rubuta taƘaitaccen bayani a kan Muhimmancin karanta halayen Manzon


Allah ‫ﷺ‬.

--------------------------------------------------------------------------------------------------

--------------------------------------------------------------------------------------------------

--------------------------------------------------------------------------------------------------

 Yaya Turawan yamma suka nuna gamsuwarsu da Manzon Allah ‫ ?ﷺ‬Kuma


hakan me yake nuni a kai?

--------------------------------------------------------------------------------------------------

--------------------------------------------------------------------------------------------------

--------------------------------------------------------------------------------------------------

 Siffanta kamannin fuskar Manzon Allah ‫ﷺ‬, da gashin kansa, da gemunsa ‫ﷺ‬.

--------------------------------------------------------------------------------------------------

--------------------------------------------------------------------------------------------------

--------------------------------------------------------------------------------------------------

 Shin Manzon Allah ‫ ﷺ‬ya yi wa gashinsa lalle? Kawo hujjoji cikin abin da zaka
faɗa, kuma mene ne hukunci yin baƘin lalle?

--------------------------------------------------------------------------------------------------

--------------------------------------------------------------------------------------------------

--------------------------------------------------------------------------------------------------

136
 Cikin abin da ka karanta a wannan babi, bayyana yadda aka hana
kamanceceniya da kafirai.

--------------------------------------------------------------------------------------------------

--------------------------------------------------------------------------------------------------

--------------------------------------------------------------------------------------------------

Ta yaya zaka bayar da amsa ga wanda yake cewa, cika gemu ba wajibi ba ne?

--------------------------------------------------------------------------------------------------

--------------------------------------------------------------------------------------------------

--------------------------------------------------------------------------------------------------

137
Zubin halittar jikin Manzon Allahn ‫ﷺ‬:

Anas bin Malik (a) ya faɗi wata Magana cikakkiya game da jikin Manzon Allah
‫ ﷺ‬ya ce: “Manzon Allah ‫ ﷺ‬ya kasance mai kyakykyawan jiki” Tirmuzi ya ruwaito
Hadisin Albani kuma ya inganta shi.

Barra’u bin Azib (a) ya ce: “Ban taɓa ganin wani abu da ya kai Manzon Allah
‫ ﷺ‬kyau ba”. Bukhari da Muslim sun ruwaito wannan Asari.

Tirmuzi ya ruwaito a cikin littafinsa (Ash-shama’il) da isnadi ingantacce, daga


Aliyu bin Abi Ɗalib (a). ya ce: “Manzon Allah ba dogo ba ne, kuma ba gajere ba
ne. Yana da kauraran tafikan hannaye, da kuma digadigai. Yana da yalwataccen kai,
yana da Ƙasusuwa manya, yana da dogon gashin Ƙirji”.

A cikin Hadisin Anas (a), yana Siffanta Annabi ‫ ﷺ‬ya ce: “Ya kasance tsaka-
tsakin mutane, shi ba dogo ba ne, kuma ba gajere ba”. Bukhari da Muslim sun haɗu
wajen ruwaito wannan Hadisi. Amma wannan lafaizin Bukhari ne.

Barra’u (a) ya ce: “Manzon Allah ‫ ﷺ‬ya kasance tsakatsakin mutane. Akwai
tazara tsakanin kafaɗunsa”. Faɗinsa (kuma da tazara tsakanin kafaɗunsa) wato
saman bayansa.

An ruwaito daga Al-jariri cewa, (wata rana) yana yin ɗawafi tare da Abuɗ Ɗufail,
sai ya ce: “Na ga Manzon Allah ‫ﷺ‬, kuma babu wanda ya yi saura a ban Ƙasa cikin
waɗanda suka gan shi in ba ni ba. Sai na ce: “Siffanta mini kamanninsa” sai ya ce:
“Ya kasance fari kyakkyawa madaidaici”.

Faɗinsa: madaidaici, wato wanda ba mai Ƙiba ba, kuma ba ramamme ba. Ba dogo
ba kuma ba gajere ba.

Faɗinsa: kuma babu wanda ya yi saura a ban Ƙasa cikin waɗanda suka gan shi in
ba ni ba. Hakane saboda Abuɗ Ɗufail, shi ne Amiru bin Wasila Al-laisi (a), shi ne
138
Ƙarshen mutuwa cikin Sahabbai. An haife shi a shekarar da aka yi hijira, da mutuwar
shi ne aka rufe sashin Sahabbai masu girma da karamci.

Ibnul Ƙayyim ya ce: “Allah ya cika duk wani matakin kyawu na fili da na ɓoye ga
Manzon Allah ‫ﷺ‬. Annabi ‫ ﷺ‬ya kasance shi ne mafi kyawu cikin halittun Allah.
Kyawun hallita da na halaye, kuma mafi kyawun sura da ma’ana”.

HaƘiƘa (Ibnul Ƙayyim) ya ambaci cewa, wani daga cikin sahabbai ya haɗu da
wani malamin Nasara, sai ya ce da shi: “siffanta mini kamannin Manzon Allah ‫ﷺ‬,
kamar ina ganinsa, domin haƘiƘa na ga siffofinsaa cikin Attaura, da Injila, sai kuwa
wannan Sahabi ya yi ta ambaton kamanninsa. Ya ce: “Bai kasance dogo sosai ba,
kuma ba gajere ba ne”. Ya dai ambaci wasu daga cikin siffofinsa, ya ce: “sai wannan
Malamin Nasara ya musulunta”.

Launin fatar Manzon Allah ‫ﷺ‬:

Manzon Allah ‫ ﷺ‬fari ne da yake haɗe da ja, wanda ya yi kama da sirki da duhu.

Bukhari da Muslim sun ruwaito daga Anas bin Malik (a) ya ce: “Manzon Allah ‫ﷺ‬
ya kasance ba fari fat ne, ba kuma baƘi ba ne).

A cikin wata ruwayar ta su: “Ya kasance mafi kyawun launi. Shi ba fari fat ba ne,
kuma ba baƘi ba ne”.

Al’amhaƘ: Shi ne fari fat irin launin zabiya.

Al’adamu: Kuma shi ne jan da ya yi baƘi, ko duhu sosai

Azhar: Kuma shi ne farin da yake haɗe da ja, (shi ne kalar launi fatar Manzon Allah
‫)ﷺ‬.

139
Tambarin annabta:

Akwai alamar annbtaka a jikin Annabi ‫ ﷺ‬mai daraja. Wato hakan wata alama ce
daga cikin alamomin annabtakarsa.

Ga alamar da wani malamin Nasara da Salman Al-farisi ya rayu tare da shi ya ce


da shi: “Yanzu me zaka umarce ni da shi?” Sai ya ce: “Ya kai ɗana. HaƘiƘa zamanin
wani Annabi da za a aiko da addinin Ibrahim ya zo, zai fito a Ƙasar Larabawa. Zai
yi hijira zuwa wata Ƙasa tsakanin baƘaƘen duwatsu biyu. Garin yana da bishiyun
dabino a tsakaninsu. Yana da wasu alamomi da basa ɓuya. Yana cin kyauta, amma
ba ya cin sadaka. A tsakanin kafaɗunsa akwai tambarin annabta. Idan har zaka iya
zuwa wannan garin; to ka tafi”. Ahamad ya fitar da Hadisin, Albani ya inganta shi.

Wannan ita ce alamar da Bahira Malamin Nasara ya gane Manzon Allah ‫ ﷺ‬da ita.
Har ya ce: “Wannan shi ne shugaban talikai. Wannan shi ne ɗan aiken Ubangijin
talikai. Wanda Allah zai aiko domin rahama ga talika”.

Sai Abu Ɗalib da wasu manyan Ƙuraishawa suka ce da shi: “Ta ya akai kasan
hakan?” Sai ya ce: “Domin lokacin da kuka taho daga hanyar dutsen can, ba wani
dutse, ko wata bishiya da ta tsaya, face sai da ta faɗi tana yin sujjuda, kuma su ɗin
ba sa yin sujjada sai ga wanda yake annabi. Ni kam tabbas na gane shi da alamar
Annabtaka da take daura da allon kafaɗarsa, kwatankwacin tuffa”. Tirmuzi ya
ruwaito wannan Hadisi. kuma ya inganta shi.

Daga Jabir bin Samura ya ce: “Alamar Manzon Allah ‫ ﷺ‬-wato wacce take
tsakankanin kafaɗunsa – wata ƴar tsokar nama ce, tsakanin naman jikinsa, da kuma
fatar jikinsa, da jaja-jaja a jiki”.

A wata ruwayar ta Muslim ya ce: “Na ga wannan alamar a wajen kafaɗarsa,


kwatankwacin Ƙwan tantabara, kuma ta saje da jikinsa”.

140

You might also like