Professional Documents
Culture Documents
Illar Auren Macce Guda (Full Paper)
Illar Auren Macce Guda (Full Paper)
Gabatarwa
Da sunan Allah mai Rahama mai jinkai. Godiya ta tabbata ga Allah SWT
wanda ya halicce mu daga rai guda. Mun shaida cewa babu abin
bautawa da gaskiya sai Allah Shi kadai, ba shi da ko mata ko kama ko
wani abokin tarayya ko mataimaki. Mun kuma shaida cewa Annabi
Muhammad (SAW), Bawan Sa ne kuma Manzon Sa ne wanda ake koyi
da Shi akowane hali, tsira da amincin Allah su tabbata gare Shi da
Alayen sa da Sahaban sa da wanda su ka bi tafarkin Su har ranar tashin
kiyama.
Bayan haka, wannan Takarda mai taken “Illar Auren Macce Guda” na
rubuta tane a matsayin goron Sallah karama ga Yan Uwa Musulmi.
Haka nan kuma idan wata jarabawa ta fada mata kamar ta rashin
haihuwa ko hauka ko shafar aljannu, to mutum na iya tsintar
kansa cikin kuncin Rayuwa.
Mutun mai Arziki, mai cikar kamala da wadata da kuma addini, bai
kamata yayi koyi da karatun su ba. Idan muka dubi Magabatan
mu, Iyayen mu, Maluman mu da kuma shuwagabannin mu duka
mata fiye da guda ke garesu. Kai su suna ganin ma idan mutum
nada mata guda to bai cika kamala ba, kuma ko alkalanci da
shugabanci ba’a bashi.
Amma idan mutum nada mace fiye da guda, koda irin haka ta
faru, sai sauran matar ko matan su rike gidan da diyan mamaciyar.
Maccen da take ita kadai bata da hutu a gidan mijinta. Bata yin
tafiya zuwa wani gari wajen biki ta kwashe kwanaki masu yawa.
Ko tayi sammako wurin ziyarar dangi ba tare da ta dafa masa
abinci ba ko kuma tayo dare. Babu ranar da ba ta girkin ta ba,
balle a dafa a kawo mata tana mike da kafafu.
B. Rashin lafia: Randa Macce bata da lafiya, idan ita dai take wazai
rika mata aiki? Da yawa zasu iya cewa diyanta ko yar aiki, to idan
bata lafiya wa zai rike mata shimfidar Mijinta a cikinsu?
Haka nan akwai rashin kwanciyar hankali idan tayi tafiya, wa zai
kula mata da diyanta musamman mata. Wata kuma tayi zargin
mijin na iya kawo wata a cikin gidan. Babban rashin kwanciyar
hankali ga mai tunani shine idan ta mutu, wa zai ci gaba da
tarbiyantar mata da diyanta, yaya makomar diyan zata kasance
tunda basu saba da kowa bas ai ita. Shin wadda mijin zai auro
zata ci gaba da zama dasu koko yaya?
Haka kuma akwai illar sonkai ga duk matar dake zaune ita kadai a
wajen mijinta domin zaa wayi gari taji bata son ko wace diya
macce ta shigo gidan aurenta. Sauran matan dake waje duk yanda
zasuyi ohonmata. Bata kula da ana iya wayewar gari wani mai
mata yazo auren diyarta shin idan shima matarsa ta hana shi ya
zataji.
RUFEWA:
Wannan matsala ta auren mace guda ta mutanen Birni ce. Ba’a cika
samun ta ga mutanen kar-kara ba. Ko cikin mutanen Birnin kuma anfi
samunta ga ‘Yan Boko akida da dai-daikun yan kasuwa, kosu badon
basu so ba, amma sai don tsoron fitinar iyalan su na gida.
Haka kuma wasu na kyamar auren Macce fiye da daya don tsoron
Talauci, sun manta da cewar arzikin ciyarwa gabadai ga Allah yake.